Chapter 10
Chapter 10
yaran ashe ba zai jima tare dasu ba Allah ya dauki rayuwarsa. Uwargidansa dama bata haihu ba wannan dalilin yasa ana raba gado ta tattara kayanta ta tafi garinsu. Gida ya rage Baba Asabe da 'ya'yanta, Tun daga lokacin ta kafa sana'ar sayar da abinci wanda da yawa mutane da dama suka dinga ganin rashin hankalinta a ganinsu ai bata wuce aure ba amma zata zauna ta lalata 'kuruciyarta a banza a wofi, To Duk zantukan dake yawo a gari suna dawowa kunanta, tayi banza da surutan mutane ta cigaba da sabgarta da kula da yaranta. Da yawa wasu mazan da biyu suke zuwa sayan abinci gurinta domin su kafa gwamnatinsu, cikin ikon Allah Alhaji Haruna ya samu shiga a gurinta ta kudiri aniyar auransa domin tana yi masa kallon nagartaccen mutum ashe kallon kitse takewa rogo auran beje ko'ina ba ya lalace a sakamakon nuna kyara! da hantara! da yake akan 'ya'yanta. Da farko ta nuna masa kuskuransa akan abinda yake ta kuma gargad'eshi ya daina. Sai shi kuma yayi kunnan uwar shegu da maganarta duk sanda yazo gidan to fa yaran basu da walwala sun dinga takurewa kenan gabadaya sun tsorata dashi domin kuwa wani sa'in har fakaitar idonta yake ya doke su, mahaifinsu kuwa dake karkashin 'kasa yana shan zagi! Sosai Alhaji Haruna yake *(Kishin kushewa)* akan yaran. Baba Asabe data gaji da iya shegen da yake mata sai kawai ta fito masa a mutum tayi masa wankin babban bargo, 'Karshe tace dashi babu lallai babu dole idan ba zai juri zama da 'ya'yanta ba to ya saketa domin kuwa ba zai zo har gida yana cin arzikin yara ya takura musu ba.'' Alhaji Haruna ya fusata! ransa ya baci a ganinsa babu amfanin auran macen dake da 'ya'ya tunda duk tsiya watarana sai ta tuna ubansu kuma soyayyar da take nunawa yaran ai kamar ubansu take nunawa, kawai sai ya yanke shawarar sakinta domin dai shi yana kishin ya budi ido yaga yaran a matsayin 'ya'yan wani ba nasa ba, Sai kawai ya rubuta mata saki biyu ya kama gabansa. Baba Asabe ranta ya baci sosai tayi kuka😭 mai yawa ta share hawaye ta barwa Allah lamarinsa, amma a zahirin gaskiya abin ya jima yana cin ranta ace wai shikkenan daga zarar mijin mace ya mutu ko kuma mace ta rabu da mijinta kan wani dalili shikkenan ita da 'ya'yanta sun zama abun 'kyama da wulakantawa a gurin wasu mazan, wannan ba daidai bane wallahi maza kuji tsoron Allah ku tausayawa mata mutukar mace zata sadaukar da rayuwarta a kanka da 'ya'yanka meye abin gudu a tare da ita, 'Ya'ya ne abin gudu kai ma kana dasu, kuma ba dole akace ka rike 'ya'yan da ba naka ba, *(Maza idan zaku auri bazawara to kuyi adalci kada kuso zuciyarku kan wani dalili shi aure na mutum biyu ne yarda da aminci shike janyo har a kulla auratayya amma sai kuga wasu mazan suna gudun mace mai 'ya'ya sai kace ance dole suyi wa yaran d'awainiya da d'an mutum da dukiya ba ai musu mugunta kuma ita rayuwa juyawa take wanda kake gudu sai ya taimake ka watarana)* Tun daga wannan lokaci Baba Asabe ta cire rai da aure kawai ta cigaba da neman kudinta, Allah kuwa ya shiga cikin al'amarinta tafi karfin yau da gobe da duk wani abunda ba za'a rasa ba. ******* Manyan mutane masu mutunci da dattako suka dinga turereniya gurin zuwa neman auran Mariya amma funfurus! ta shafawa idonta toka ta kore su, al'amarin daya fusata! Baba Asabe kenan ta rufeta da fad'a ta inda take shiga bata nan take fita ta cigaba da cewa"Shi wanda kike kulafuci shin kina da tabbacin zai aureki? Babu wanda be san halin Jamilu ba gurin yaudarar yaran mutane me zakiyi da Jamilu manyan mutane masu mutunci suna tururrubi akanki! Ko kin dauka kinfi karfinsu ne? to bari kiji bayan kyawun jikin da kike dashi to baki da komai sai tarin muni duk ga 'yan mata nan masu kyau a gari wanda suka fiki komai basu dauki kansu wata tsiya ba sai ke to mutukar ni na haifeki ba zaki auri Jamilu ba." Da jin wannan magana sai ta dora hannu aka ta kurma ihu! tana kiran ta shiga uku ta lalace! Makota suka shigo suna tambayar ba'asi. Takaici da bakin ciki yasa Baba Asabe kasa magana ta koma ta zauna tana me cigaba da sabgoginta. Mariya ihu! take tana fadin." Ban ta'ba yi miki rashin kunya Baba ban ta'ba bijirewa umarninki ba duk abunda kike so shi nake so, ke kika zama gatana ban taso da ubana ba amma kin share min hawayen maraicin uba ina so kiyi min adalci a rayuwata kiyi hakuri na auri wanda nake so Jamilu shine rayuwata!" Jama'ar dake tsaye a gurin suka shiga mamakin al'amarin, Baba tace."Kun dai ji da kunnuwanku abunda take fada, Shin kuna da tabbacin Jamilu auranta zaiyi ko kuma yaudararta yazo yayi sanin kanku ne kafin yazo gurinta ya yaudari 'yan mata da yawa a cikin unguwar nan to me zai sanya ina ganin kashi da rana na taka auran Jamilu bashi da fa'ida tunda shi bashi da hali uwa uba kuma bashi da sana'a" D'aya daga cikinsu mai suna Huwaila tace."Ki yi hakuri ki barwa Allah al'amarin domin kuwa shi aure nufi ne na Allah kuma naji kina maganar Jamilu bashi da sana'a Aa yana da sana'a domin shago guda ne dashi a kasuwar wambai kawai dai aure ne be yi ba ya tsaya shiririta amma ki bari ni nayi miki alkwarin zuwa gidansu domin mu tattauna da mahaifiyarsa idan da gaske yake to ya fito ayi magana idan yana yaudaran yaran mutane to mu ba zai yaudare mu ba." Baba Asabe ta sauke ajiyar zuciya da fadin." Shikkenan Huwaila Na gode Allah ya jishshemu alkairi." Huwaila ta amsa da ameen kafin ta rungume Mariya tana rarrashinta. Koda Huwaila ta samu mahaifiyar Jamilu da maganar kai tsaye tace ita sam bata ma san da maganar ba, amma idan ya dawo zata tambayeshi duk yanda ake ciki zata zo har gida tayi mata bayani. Bayan sunyi maganar da mahaifiyarsa ya nuna mata shi sam be san da wata Mariya ba ballantana ya je neman auranta saboda haka ta daina yarda da jita jitan mutane akansa aure nufi ne na Allah idan lokacinsa yayi to ko yana so ko baya so sai yayi. Sai jikinta ya mutu tace."Anya Jamilu ba zaka nemi maganin baki ba kuwa na fahimci cewar mutanan unguwar nan sun sanya maka ido." Dariya kawai yayi ya shashantar da maganar. Bayan kwana biyu da faruwar al'amarin ya zauna yayi dogon tunani akan al'amarin a zahirin gaskiya Mariya bata da wani kyawun azo a gani amma kyawun jikinta yana mutukar rud'arsa yana masifar son cikakkiyar mace amma kuma yana so ya dawo gida yaga kyakykyawar fuska nayi masa sannu da zuwa. Murmushi yayi lokacin da ya tuna ai Ubangiji Allah ya hallata masa auran mace fiye da d'aya saboda haka zai auri Mariya saboda kyawun jikinta nan gaba kuma idan ya samu fara kyakykyawa sai ya aura ya samu ta shiga cikin taron jama'a wacce zai sanya a gaban mota yana zagaya gari da ita. Ya shedawa mahaifiyarsa shawarar da ya yanke kan cewa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50