Chapter 30
Chapter 30
kunu tana dauraye murfin feedern. "Sam baki da jimirin yunwa Miemie,kimin hakuri yanzun zan... Itama shirun tai dan jin sallamarshi. Da dan rarrafe da tafiyar da batayi kwari ba ta nufi gun Abban da murna. Ganin Miemien ne yasa shi dawo da hankalinshi kanta,sama yai da ita kamar kullum suna dariya. A hankali ta rufe idonta tanajin zuciyarta na bugawa da sauri,kusan wata 2 rabonta da ta sashi a idonta,jin takunshi na kusanto ta yasa ta juya da sauri tare da had'iye hawayenta. Ya sauya mata,duk ba g'yara, har wata kasumba ya had'a ta dole ta rashin g'yara fuska. Da t'sananin murnar ganinta ya karaso sai washe baki yake,da sauri tai baya ganin abinda yake shirin yi tai gun taburma ta d'akko,sai ya bita da kallo baki sake, tabbas Salma batai kewarshi kamar yadda ya mato a kewarta ba.. Koh irin d'aukin nan na ganinshi t'sawan lokaci haka bata yi. Dan dukan da Miemie take mishi ne yasa ya kallo ta,da hannu take nuna mishi kan feedern dake hannun Salman. Kan taburmar ya nufa tare da zama,so yake sai ya fassara yanayin Salman,shi yasa yake ta k'allonta. Feedern ta mika wa Miemie tana dan satar kallonshi kan ta kau da kai tace "Ina wuni.. Shiru yai mata,sai ta dan kalloshi cikin ido,shima ita yake kallo,bazata iya kallon kwayar idonshi ba,zata chaza mata matsala,da sauri ta kara dauke kai tana maimaita gaisuwar. "Mey yasa kwana biyu ba k'ya d'aukan kira na Salma?.. Ba k'ya ban amsa koh na miki text?.. Gefe ta kara yi da kanta tana kallon wani waje, kan tace "Ban gani ba ne.. Da mamaki yake kallon yadda tai maganar cikin nuna ko'in kula. "Salma kin daina so na yanzu koh?.. Yadda yai maganar yasa jin wani iri da dan tausayinshi,da jihadi ta juyo ido cike da kwalla. "Ya Ja'afar, ya dace mu fuskanci zahiri fa yanzu,mu daina yaudarar kan mu dan komai ya afku..Dole nai aure ka sani,ban maka alkawarin zama ba aure ba,bazan maka alkawarin kin kula wani ba.. Yanzu haka karatu zan koma,ka d'auka rayuwar da ta shud'e a mafarki muka yi ta, yanzu mun farka... Dole akwai cigaba a rayuwa.. Kai hakuri, amma bani da alaka da daukan kiran ka yanzu,ka manta Salma dan Allah,mu fuskanci rayuwar gaba.. Kai ta kautar tana goge hawaye, shi kam k'allonta kawai yake ba koh kiftawa. "Ke nan kina nufin son da nake miki karya ne?... Soyayyar mu hasashe ce Salma?.. Zaman mu da rayuwar auren mu wasa ne?.. Kina nufin Miemie ma mafarki ce?... Da fusata yake tambayarta,kai kawai take girgiza mishi tana hawaye. "Ba haka nake nufi ba.. "Toh mey ki ke nufi?.. Shiru tai tana cigaba da kukan ta,sai ya kada kai cikin takaici. "Salma kin d'aina so na kam.. Girgiza mishi kai tai "Ina sonka Ya Ja'afar, har karshen rayuwata.. Abu daya nake son ka gane,yanzu komai ya sauya,alakar Mimi ce kawai ta rike mu... Ka cire son zuciya aciki, dan bazan iya haramtawa abinda Allah ya halasta min ba.. "Assalam Alaikum, wannan akwatunan fa a zau... Tsaye tai ba tare da karasawa ba, kai kasa ta amsawa Mama sallama,ciki Maman ta karaso,ya gaida ta kai kasa,duk shiru sukai ba mai magana, sai muzurai Mama take ma Salman kan ta shiga daga ciki. Jiki a sanyaye ta tashi ta shiga ciki,a hankali ta sa kanta a kan katifa tana hawaye. Ba dan yaso ba ya tashi yai fita,tare da shigo mata da akwatunan ta. Har zauren Mama ta bishi ta sa sakata tana sababi kan tai gun Salman. "Wai ke baki da hankali ne Salma?.. Meye had'inki da wannan da har zai shigo cikin gida ki bashi taburma, har ki zauna a gabanshi kina wannan shashancin cin?.. Mey fa rabawa(K'ADDARA) ta raba ku har abada. Shiru tayi har Maman ta gama tana ta kok'arin shanye kukanta, ta sani da koh tayi bayani Mama bazata gane inda ta dosa ba. "Kiyi hakuri bazan sake ba. Kai ta k'ada tuni har tai laushi. "Ina kuje miki yaudara irin ta D'a namiji ne Salma,gaba in kina mishi haka sai ai abin kunya. Shiru tai tanajin wa'azin Maman kawai. G'yale ne kusan kala 5 had'add'u,tana washe baki ta fito dasu daga leda. "Ki zabi na za6a ki darje,dan zawarcin ki sai yafi y'an matanci a komai Salma, gobe kayan k'walliya zasu zo dan na bawa Hajiya Jidda kud'in kayan g'yaran jiki,ga wata yayi nisa da komai kin samu akan lokaci.. InshaAllah sai mun cike gurbin da muka rasa.. Ni da zakiji shawarata ma da an yaye Miemie a satin nan a mikata ga gidan su chan ya karata... Da sauri ta dago tana kallon Mama, Kat'seta tai da fadin "Eh man,bashi yake ikirarin yana kawo shi ba?.. Toh zamu mayar mishi da abarshi kawai. Kai ta hau girgiza ma Maman,Allah yaga ba mai rabata da Miemie sai aure. "Mama Miemie fa karama ce,kawai tai saurin tashi ne,koh fa wata tara bata cika ba.. Dan Allah kiyi hakuri,dan ba abinda zata t'sare min koh a makaranta. Harara ta aika mata, "Kina nufin da ita zakina fita?.. Kallonta take ta rasa amsar ba Maman. "Toh da sake wallahi, ba yadda za ai ina tufka kina bin bayana da warwara.. Zawarci da goyo?.. Toh da sake,dan ba mai gani ya kulaki alhalin kina sa6e da y'a. "Aikina fitarshi ta naga dama ce,in ma kince baza'a mayarta ba ni zan na miki renon,aje a dawo lafiya. Shiru tai tana jinta kawai. Washegari sai ga kayan k'walliya jibgi,su mascara, eye shadows,su sabulun g'yaran fata harda su man gashi,ga haddun man gyaran jiki,lalle Mama da gaske take. Shi kam tunda ya koma da yazo k'wanciya yake tuna dazu,lalle in Salma tasan wata toh bata san wata ba. Tazo k'wanciya taji karan wayanta,agogo ta duba, tasan ba mai mata haka sai mutum daya. Badan taso ba ta d'auka, sai dan jin dame yazo. "Naji kije makarantar, amma bisa sharad'i uku.. Baki ta bud'e cike da mamaki,wai koh ya manta bata karkashin ikon shi ne yanzun? Dan dai taji sharad'in tace tana ji. "Good. "Na daya kafarki toh kafar Miemie duk inda zaki shiga. "Na biyu ba zancen yaye sai Miemie ta cika shekara biyu kamin kiyi komai. "Na uku,fitar ki sai da nikaf da hijab,sannan ni zan sama miki mai kai ki a Napep ya d'akko ki in kin gama, dan ba ko wanne kato zai na d.. "Ka ga malam,ka bari ka fad'awa Miemie wannan dokar taka ba wai ni da nake Salma ba... Dan ba y'ar ka bace ni,ni nake da damar t'sara rayuwata yanzu ba kai ba. "Abu daya nasan na yarda zan iya shi,shima dan hakkin ka ne dole,shine yaye Miemie,zanyi yadda kace, sauran kuwa ba huruminka bane... Wayar yabi da kallo baki sake jin ta kashe kit.. Lalle Salma ba ta so zaman lafiya ba a garin nan, amma zata jidi mamakin shi. Dan shi tai mishi daidai ma da zata tafi makaranta. Tun daga ranar ya daina kiranta a ganinshi zata damu ta bashi hakuri ayi yadda yaso,sai dai ta daure ita. Ana haka ranar Abba yace ya batun makarantar da yace zai koma?.. Kanshi t'saye yace ya ma Abban ai ya fasa. Nan ya bud'e mishi wuta kan bai isa ba,duk haukar da yake ranar ya samu labari
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41