Chapter 3
Chapter 3
A'i tunda har an kawo sadaki, kuma irin wanda mama ke da muradi. Ita kam Salma zai wuya ka ga tama sanya g'yale bare har ta zauna k'yali. Gata dai mama ita tafi sawa buri, ga ta kuma y'ar _boarding_. *By* *Feenat Ja'afar*. 9/29/16, 8:52 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 6-A dai-dai k'wanar su Ja'afar take,dawo warta daga islamiya kenan,sanye take da dogon hijab ruwan kasa mai yashi har kusan kasa,rataye da jakar littafai da Qur'ani a hannu,sai dan asirin _skirt_ nata na attamfa da ya fito _green_ da ruwan kasa, duguwa ce,ba zangal ba,tana da kaurin jiki,dan ta fita sahun ramammu,tafiyarta a nut'sue tafi komai d'aukar hankali. Kamar kullum ta daga kai dan k'allon gidan su Ya Ja'afar kamar yadda ta saba k'ewar shi ta kawar da kai, sai dai taku biyu taja ta t'saya tamkar an t'sayar ta. Kanta duk'e dauke da murmushi,cikin nut'suwa ta kara k'allon kofar gidan dan tabbatar da wanda ta gani.. *"Ya Ja'afar*?...ta fad'a a zuciyarta lokacin da ya taso yana mata murmushi. Ikon Allah,wai kunyarshi kuma take ji,cikin nut'suwa ta d'auke kanta daga gareshi ganin ya karaso. "Assalam Alaikum Malama Salma.... Wani irin buguwar zuciya taji ya ziyarce ta,shekara uku da wani abin ba wasa ba,hatta muryar Ya Ja'afar ta sauya mata. Cikin nut'suwa ta dago da murmushi ta amsa mishi,kamin ta gaida shi a kunya ce, shi dai kawai k'allonta yake yana murmushi, kamar mai mamakin kara girmanta,ga wata nut'suwa da ta kara shigarta. D'uk sai ya kara yaba Salman nashi,ganin shirun yai yawa yasa da hannu ya nuna mata hanya halamar su wuce. Dan satar K'allonshi tai kan ta sunne kai suka fara tafiya. "Salma koh murnar gani baki yi,ba koh tambayar yaushe nazo? Kai duk'e tace "yi hakuri,yaushe kazo?.. Kai ya k'ada da murmushi,kan yace "jiya. Tambayar yaushe gamo yake mata, yadda take kunyar tata gun bashi amsa d'uk sai ya ji shi wani iri,mace mai kunya itace muradinsa. Da haka har kofar gida ya rakata yana mata tad'in makaranta da yadda suka juma basu gamo ba. Ummi ya k'allo achan dan nesa dasu tana tad'i, sai ya tuna mata yasha zuwa ai. Ita dai daga murmushi sai k'ada kai da Umm,a'a,d'uk ta takure yau a gaban Ja'afar d'inta. Ganin haka yasa yai mata sallama tai gida.. A katifa ta zauna tana cire hijabi,ta rasa wani irin farin ciki take ciki na ganin Ya Ja'afar d'inta yau. Sai murmushi take saka cike da kunya ita kad'ai kamar yana ganinta. A haka har Ummi ta cimmata, dan harara ta sakar mata gami da had'a rai. "Yanzu Ummi kinyi dai dai kenan? A y'atsine ta k'allo ta tana ninke g'yale, "da nai miki mey? Iya jaraba.. Kai Salma ta k'ada kan tace "dan t'sabar wulakanci ashe Ya Ja'afar yasha zuwa gidan nan nema na in yazo gari muna sa6ani sau biyu yana fad'a miki amma koda wasa baki fad'an ba? Allah kin ban haushi.. "Mtsww.. T'saki Ummin tai kan ta ta6e baki,tuni Salma ta kule,sam ta t'sani t'saki, bare ga Salma K'anwar ta. "Na zata wani abin kirkin ne wallahi, toh meye nawa dashi da zai mayarni y'ar aiken shi?.. Anki a fad'a miki d'in ki d'au mataki toh.. A tunzure Salma ta tashi tayo kan Ummin sukaji Mama na magana a kofar d'aki, "Kun fara cin kan koh? Yara kamar masu ganin hanjin junansu? Baya Salma tai tana harar Ummi, "Mama kimin tsakani da ita toh,ta fita harkata dan bata da kunya sam wallahi.. A y'atsine Ummi ta harare ta,"ka ga kunya manya,akan wannan mai dan uban d'acin ran kike wannan kumfar bak'in?...baki ta ta6e kan tace "Kin k'wa kama abga in dai Ja'afar ne.... "Ke Ummi... Bana son fit'sara fa,kullum ina sanarki Salma yayarki ce,dole ki bata girma, koh nai mugun sa6a miki.. Maza bata hakuri. Tana chunno baki ciki ciki ta bawa Salma hakuri,ita kam har ta fara hawayen bak'in ciki. "Toh fito ki biyoni.. Mama ta nuna ma ummin kofa da hannu.. *By* *Feenat Ja'afar* Like 路 Reply 路 Report 路 Jul 20 Feenat Ja'afar Novel's *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 6-A dai-dai k'wanar su Ja'afar take,dawo warta daga islamiya kenan,sanye take da dogon hijab ruwan kasa mai yashi har kusan kasa,rataye da jakar littafai da Qur'ani a hannu,sai dan asirin _skirt_ nata na attamfa da ya fito _green_ da ruwan kasa, duguwa ce,ba zangal ba,tana da kaurin jiki,dan ta fita sahun ramammu,tafiyarta a nut'sue tafi komai d'aukar hankali. Kamar kullum ta daga kai dan k'allon gidan su Ya Ja'afar kamar yadda ta saba k'ewar shi ta kawar da kai, sai dai taku biyu taja ta t'saya tamkar an t'sayar ta. Kanta duk'e dauke da murmushi,cikin nut'suwa ta kara k'allon kofar gidan dan tabbatar da wanda ta gani.. *"Ya Ja'afar*?...ta fad'a a zuciyarta lokacin da ya taso yana mata murmushi. Ikon Allah,wai kunyarshi kuma take ji,cikin nut'suwa ta d'auke kanta daga gareshi ganin ya karaso. "Assalam Alaikum Malama Salma.... Wani irin buguwar zuciya taji ya ziyarce ta,shekara uku da wani abin ba wasa ba,hatta muryar Ya Ja'afar ta sauya mata. Cikin nut'suwa ta dago da murmushi ta amsa mishi,kamin ta gaida shi a kunya ce, shi dai kawai k'allonta yake yana murmushi, kamar mai mamakin kara girmanta,ga wata nut'suwa da ta kara shigarta. D'uk sai ya kara yaba Salman nashi,ganin shirun yai yawa yasa da hannu ya nuna mata hanya halamar su wuce. Dan satar K'allonshi tai kan ta sunne kai suka fara tafiya. "Salma koh murnar gani baki yi,ba koh tambayar yaushe nazo? Kai duk'e tace "yi hakuri,yaushe kazo?.. Kai ya k'ada da murmushi,kan yace "jiya. Tambayar yaushe gamo yake mata, yadda take kunyar tata gun bashi amsa d'uk sai ya ji shi wani iri,mace mai kunya itace muradinsa. Da haka har kofar gida ya rakata yana mata tad'in makaranta da yadda suka juma basu gamo ba. Ummi ya k'allo achan dan nesa dasu tana tad'i, sai ya tuna mata yasha zuwa ai. Ita dai daga murmushi sai k'ada kai da Umm,a'a,d'uk ta takure yau a gaban Ja'afar d'inta. Ganin haka yasa yai mata sallama tai gida.. A katifa ta zauna tana cire hijabi,ta rasa wani irin farin ciki take ciki na ganin Ya Ja'afar d'inta yau. Sai murmushi take saka cike da kunya ita kad'ai kamar yana ganinta. A haka har Ummi ta cimmata, dan harara ta sakar mata gami da had'a rai. "Yanzu Ummi kinyi dai dai kenan? A y'atsine ta k'allo ta tana ninke g'yale, "da nai miki mey? Iya jaraba.. Kai Salma ta k'ada kan tace "dan t'sabar wulakanci ashe Ya Ja'afar yasha zuwa gidan nan nema na in yazo gari muna sa6ani sau biyu yana fad'a miki amma koda wasa baki fad'an ba? Allah kin ban haushi.. "Mtsww.. T'saki Ummin tai kan ta ta6e baki,tuni Salma ta kule,sam ta t'sani t'saki, bare ga Salma K'anwar ta. "Na zata wani abin kirkin ne wallahi, toh meye nawa dashi da zai mayarni y'ar aiken shi?.. Anki a fad'a miki d'in ki d'au mataki toh.. A tunzure Salma ta tashi tayo kan Ummin sukaji Mama na magana a kofar d'aki, "Kun fara cin kan koh? Yara kamar masu ganin hanjin junansu? Baya Salma tai tana harar Ummi, "Mama kimin tsakani da ita toh,ta fita harkata dan bata da kunya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41