Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 34

Chapter 34

Bakin Ruhi Book 1 Complete Hausa Novel 1,234 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

yi mata magana cikin wannan salon.Yayi jiran amsarta amma shuru,kawai sai ya kira Daddy ya sanar da shi ya kamata a fara shirin yin bikinsu da Nafisa amma sai Daddy ya ce ya je can gida su yi maganar ido da ido tun da tuni ya sanar da shi bai samu damar zuwa dajin ba. Sai bayan sallar isha'i ya tafi can,a babban falo suka zauna Ammy ta kawo musu gasashen naman kaza da kuma shayi.Suna ci suna tuna baya, Uncle ne ya soma da cewa “ Abdul Hameed ka tuna lokacin da muna yara kai ne ke son gashen nama irin haka? ” Daddy yayi murmushi ya ce “a lokacin ai tantabaru ne muke gasawa,sannan muna samari ne ba yara ba” Uncle Salem yayi murmushi ya ce “ai kuwa dai ” “Kamar sati nawa kake ganin ya kamata a sa ranar bikin?” “Zuwa wata uku haka, lokacin an yi musu hutun makaranta a ranar da ta dawo sai a saka ta lalle” Uncle ya faɗa yana hasko tuni ga lokacin nan ya zo. “To babu damuwa ,amma ka samu ka sanar da Nafisar komai?” Daddy ya tambaya. “A'a tukuna dai amma ...” sai kuma ya ji nauyin abin zai ce kawai sai yayi shuru,shi ma Daddyn bai damu ba sai ma kiran Ammy da yayi ya sanar mata ,sosai ta nuna farin cikinta kafin ta fita.Bayan sun gama tattaunawa Uncle ya fito ya nufi flat ɗinsa,an gyara komai an share an goge.Wanka yayi ya shirya cikin bacci sannan ya soma yin wuridin da ya saba a kullum kafin kuma ya ɗauki wayarsa ya soma kallon hotunan Nafisa wanda a iya kallonsu kawai hankalinsa sai tashi yake yana jin buƙatar kasancewa da ita. ★ ƘWARGWAM Yau ma ban ci abinci da dare ba kawai cake na ci da chocolat,sai na saka wasu a jakata wanda zan baiwa Firdausi kamar yadda na yi alƙawari.Ina yin kwance na ce “Innarmu don Allah ki yi min gatana irin ta dogon ƙarni mai abin tsoro” “A'a Allah ya tsare ni Nafisa ,kin ga bacci ma zan yi don gobe ina son yi mana dambu tun da safe” ta faɗa tare da yin kwanciyarta gefe da ni.Na turo baki tare da lumshe ido,hoton abubuwan da Uncle yayi min duk suka dawo min.Sai wani abu nake ji yana bijiro min na shauƙi amma ban ma san taƙamaimai mene nake buƙata ba,amma sosai nake jin daɗin tunanin don abin da nake ji yana bani shauƙi sosai.Sai laɓana nake motsawa kamar wacce ke son Uncle ɗin ya ƙara shan su,a haka bacci ya ɗauke ni mai haɗe da mafarkinsa muna having sex.Yadda duk jikina ya amsa kamar a gaske yasa na buɗe idona dakyar da suka yi min nauyi,na duba lokaci a wayata sai na ga ƙarfe uku da minti uku na yunƙura na tashi zaune daidai nan hasken ɗakinmu ya ɗauke don dama ban iya bacci cikin duhu.Fitilar wayata na kunna sai dai tamkar wata wutar kyandir haka ta soma yin rawa kafin kuma ta ɗauke ɗif.Ban wani damu ba na sake ɗaukar wayar don sake kunnawa wannan karon cak screen ɗin ya ɗauka kafin kuma ta mutu da kanta. Daga bakin ƙofa na hango wata mace mai fararen kaya a tsaye gashin kanta na tashi cikin iska. “Wace ce?” na tambaya. “Deborat” ta bani amsa kai tsaye,kafin kuma ƙyaftawar ido tsundum na ganta kusa da ni a zaune muna kallon juna. Ido sune ƙofar hango ruhi, wannan yasa nake kallon ruhinta tun daga wajensa har cikinsa.“Ke ce kike yi min gatana kullum” na furta bayan na gama lalubo dukkan asalinta.Ba ta bani amsa ba sai jawo ni da ta yi ta kwantar ni kan cinyarta ta soma shafar sumar kaina,na lumshe ido don kuwa shafar irin dai ta matar da nake ji ce tana yi min haka duk dare.Sai dai wannan karon shafar ta babanta don tsintar kaina na yi a wani wurin, dube-dube na soma yi har na ci karo da allon sanarwa inda aka rubuta “DARASIN SANIN RUHANIYA” ina shiga ciki abun mamaki duk sai na tarar da kaf malaman nan da muka yi meeting da su,ga kuma su headmaster da principal su ma duk suna zaune yayin da Grand Maa ke koyar da karatu.Kamar wancan lokacin haka na zauna kusan Adama,na mayar da dukkan hankalina ga Grand Maa inda take cewa “kamar yadda vice headmaster ya faɗa muku lokacin meeting wannan school Ƙwargwam ta kasu kashi uku primary,da Sakandari sai kuma kuma Ajin Ƙwargwam wanda iya malamai ne kawai muke koyarwa” tana rufe bakinta na jefa mata tambaya,“Grand Maa me Ƙwargwam ke nufi?” “Matsafa!” ta bani amsa kai tsaye,sai na yi shuru ina tunanin zuci na ce ‘Ƙwargwam school na nufin MAKARANTAR MATSAFA? to amma su wane ne matsafan?’ Tamkar Grand Maa ta shiga zuciyata kuwa sai ta bada amsa ta hanyar cewa “darasinmu na farko shine chapter ruhi da gangar jiki,ta wannan hanyar ce ake gane matsafi” tana gama faɗar haka sai ta yi wani abu da hannunta nan take sai ga wani table ya bayyana a gabanmu,sannan a samansa wani yaro ne kwance babu kaya jikinsa da na dubi yaron sai na ga ba kowa ne ba face ɗalibina wanda ta baiwa biscuit a ɗazu ..... My book is only 500 vi 2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank DM +22795045822 [06/04 15:24] MRS SADAUKI: *MAKARANTAR MATSAFA*☠️ ```LoVe aNd HoRrOr story```👽 By Chamsiya Laouali Rabo {MRS SADAUKI💫✍️} *SADAUKARWA :* Ga dukkan Malaman makaranta. *FCWA*☀️ ________________________ Last free page 10 Ganin Grand Maa ta ɗauki wuƙa za ta tsaga cikin yaron na yi saurin rumtse idona,ina jin sautin kururuwarsa yadda yake kuka yana cewa “madam ki cece ni kar ki bari su cutar da ni ” na buɗe idona da suka yi jawurrr na sake zuba su kan Grand Maa wacce ke zuba jinin yaron nan a kofi ta hanyar saka ludayi tana wani kwaso shi. Bayan ta gama sai ta kai kofin bakinta ta sha sannan ta miƙawa principal shi kuma da ya sha ya bai wa headmaster daga nan sai vice principal da kuma vice headmaster.Grand Maa ta ƙara karɓar kofin ta ce “lamba ɗaya sha ka bai wa lamba biyu,haka za ku dinga yi har kowa ya sha” wanda aka kira da lamba ɗaya na duba, kyakkyawan saurayi ne irin sosai ɗin nan kuma sai na ga yana kama da headmaster da dukkan alamu ɗansa ne,bayan ya sha sai ya miƙawa lamba na biyu shi kuma ya miƙo min na karɓi kofin ina kallon yadda jinin ɗalibina yake kwance a ciki mugayen matsafan nan sun mayar da shi lemun sha .Na kai kofin kusan bakina na yi kamar na sha kafin na miƙawa Adama wacce ita kuma ita ce lamba huɗu,so nake na ce mata kar ta sha amma idon Grand Maa ƙurrr suke kanmu ina ji ina gani Adama ta sha jinin kafin ta ba na kusa da ita a haka har kowa ya sha aka mayar da kofin. Daga nan sai Grand Maa ta yi wani siddabarun sai ga yaron da aka feɗe cikinsa ya tashi zaune daram da buɗaɗen ciki idonsa na shatatar da hawayen jini yana kallon tsakiyar idona har yanzu kuma bai gushe da neman taimakona ba sai dai sam ban san ya za a yi na

Table of Contents

Chapters

38 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});