Chapter 12
Chapter 12
other stuffs kawai nake karawa da su duk wata, saboda Mama bata yarda ta saya min irin wadanda nake so.” Idon Sumayyah har rawa yake don bacin rai, da tsoro da mamakin abinda ‘yar uwarta ta aikata, har ta fara hango irin hukuncin da Bhaiya zai mata, ta fara hango shi ya dauke Surayyah da mari kodayae Bhaiya baya duka baya zagi, amma fa bai iya fushi bay a kuma kware da (silent punishment), fatar bakinta ma rawa take yi, ta kasa murnar dawowar tasa ma don haushi da mamakin Yayar ta Surayyah, da kyar Sumayyah tace, “kin ci amana amma, Yaya Surayyah kin ci amanar Bhaiya, na rantse da Allah babu ruwa na, count me out of your dirty game”. Daga haka Sumayyah ta fice da gudu tana “Oyoyo! Bhaiya, Mama Bhaiya ya shammace mu”. Sai ga Mama ta fito daga dakin ta itama kan ta ko kallabi babu, tace “really?” Surayyah kuwa bayan gida ta shige ta boye kanta, jikin ta ba inda baya rawa. Sumayyah ta kusa kai Sarham kasa sakamakon tsallen da tayi ta shako shi da sunan murna. Haba! Sarham sai ya balle da fada blah! Blah! “Sumayyah meye haka? Baki san kin girma bane? Ko an ce miki da da yanzu ma daya ne? Bana son irin wannan haukan welcome din, an wuce wajen, kada ki kara”. Mama ta iso falon tana cewa “kai mai hali dai baya fasa halin sa, kai kuma daga zuwa sai fada kamar tsiduhu? Shekara uku ba kwana uku ba basu saka ka a idon su ba, ba dole su yi murnar ganin ka bagatatan yau ba?”. Sarham ya mike ya isa gareta ya kama hannayen Mama ya rike cikin tafukan sa, yana murmushin farin ciki ya kai su ga fuskar sa kan sajen sa, wanda a baya kafin ya tafi bashi da shi yace “My Mommah, I missed you badly kin sani. Amma autar ki bata san ta girma ba, kullum tana nan jiya I yau shiyasa bazan daina fada ba”. Kafin kace meye wannan gida ya kacame da murnar dawowar Dr. Sarham. Da Abba Prof. ya dawo murnar tafi armashi, a ranar har dare suka raba a falo suna hirar yaushe gamo, amma an nemi Surayyah an rasa a falon, tunda ta zo ta yi masa sannu da zuwa ta gudu gidan Kakar su Haj. Kulu a gadon kaya, don tayi-tayi Sumayyah ta karbi ‘yan kudin da ke hannun ta ta kai Kofar Na’isa, ta roke ta kan ta rufa mata asiri tayi maza ta kai musu tun kafin Yaya Doctor ya huta ya waiwayi zancen, wadanda ko kwatan abinda ta kashe daga abinda yake aikowa din basu kai ba. Sumayyah ta ki amsa, ta kuma ce in ta takura mata ta cigaba da saka sunanta cikin laifi nan wallahi zata tona ta, “kawai ki yi harkar ki Yaya Surayyah ki rabu da ni, ni ba maciyiya amana bace kuma ba’a shirya rashin gaskiya da ni”. Duk da ta san Sumayyah ta gaya mata bakar magana sosai amma ta kasa cewa komai wannan karon, girma da mutunci ai madara ne, kuma mutum shi yake rike kayan sa, ta yarda ita ta zubar da girman ta har Sumayyah kanwar bayan ta yau ta nemi zagin ta (in disguise). Don haka Surayyah ta ga gara ta gudu gidan Hajiya, inda ba abinda Sarham ya isa yayi mata in dai a gaban Hajiya ne koda ta bare da ita. Washegari walima sosai Mama ta hada musu a babban falon ta, ta murnar dawowar Sarham da kammala zurfafa karatunsa, wato kwas din da ya je yi na tsayin shekaru uku a (KAU, Jeddah) ta kasar Saudi Arabia, don haka aka tura direban zuwa Abba Gadon kaya don ya dauko Hajiyar Gadonkaya. Jin maganar zuwan direba daukan su daga bakin Maigadi yasa Surayyah duk ta damu, lokacin da da aka ce su fito a tafi gidan Abba, Hajiya tace ta shirya su tafi gidan nasu tare, ta yaya ana can ana murnar zuwan dan uwanta da taya shi murnar zama babban likita zata taho ta zauna ita kadai anan kamar mujiya a cikin ‘yan uwanta? Tace lallai ta shirya su wuce, bazata bar ta ita kadai a gidanta ba. Da Surayyah ta ga ba sarki sai Allah sai ta fadawa Haj. Gaskiya cikin damuwa, cewa laifi tayi masa fa, bata so ya kure ta, don zai iya dukan ta, Hajiya kuwa ta saka ta a gaba tace sai sun tafi taren, mai dukan mata ita sai ruwan sama. Mama da hannun ta tayi girke-girken walimar nan, don haka sun kwashi gara mai dadi sosai. Sarham yayi wa girkin Maman sa cin yaushe rabo! Da sweet cook din Mama!? Ba abinda bai ci ya hantse a wajen ba. Da yake magananne ne har gobe tunda ya fara cin abincin nan bai yi shiru ba, yana yi ne yana zuba santi, saida Hajiya Kulu ta saka masa filon kujera a kuturin sa, tace, “gara a saka maka waigi haka likita Sarhamu, Allah yasa dai matar duk da zaka aura mai iya girki ce. Shin ma ina aka kwana kan maganar aure? Wannan karon kam zan bada cigiyar mata har a masallatai idan bakin jini ne ya hana ka samun mata”. Daga Abba har Mama duk suka bi shi da ido kamar Hajiya ta ci musu albasa ne ta fadi abinda ke ci musu rai, suka dakata da cin abincin suma suna jiran amsar sa da zai fada, da alama dukkannin su suna da wannnan damuwar tuntuni kawai Hajiya ta riga su furtawa ne. Ai yau Sarham da karfin guiwar sa ya ce “ki kwantar da hankalin ki Hajiya, ba sai kin kai tallata a masallaci ba, an riga an bani mata cikin daraja da kima kuma wadda nake so tuntuni, ku ake jira ku je tambaya da sanya lokaci”. Mama da Abba har suna hada baki wajen tambayar sa. “Daga ina ka samo matar kuma ‘yar waye a Kano a ina suke? Tun yaushe kuke tare bamu da labari?” Yace “Mama zaki iya tuna yarinyar dana ke tare da ita tun zuwana karatu MBBS na farko? Ina nufin MADINAH. Ke ai kin jima da sanin labarin ta, wadda a baya mahaifin ta yace bazai bani ba, to ita din ce dai muka sake haduwa a wannan karon muka sulhunta, mahaifin ta kuma ya bani auren ta already ku kadai yake jira, ‘yar gidan Attahiru Habibu SoronDinki ce”. Mama da yake ta san zancen Madinah tuntuni nan da nan ta ci magani, fuska a gintse tace “shima ai ya sani” (tana nufin Abba Prof.) ta kara da cewa “ko ba yarinyar da ka kusa kashe kanka a kanta ba, saboda uban ta ya wulakanta ka? Yarinyar da ka zauna shekara bakwai cikin tuzuranci babu aure saboda an hana ka ita, sakamakon cewa sun raina arzikin mu da mutuncinmu? Itace ko ba ita bace?” Sarham yayi shiru, gaban sa da zuciyar sa na wani irin faduwa, tsoron sa Allah tsoron sa kada Mama tayi (opposing) maganar Madinah, shi kam da ya shiga uku, don in har ba Madinah ya aura ba, babu shi babu aure a duniya (ya fada a zuciyarsa). Abba ya ce “Lelen Abba rabu da Mama, yi min cikakken banyani, diyar Attahiru Sorondinki
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36