Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 32

Chapter 32

Aurenta Zanyi Book 1 Complete Hausa Novel 1,209 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

nasan idan kikayiwa uncle magana zai hkr please...! momy”. Tabbas abunda bunayya tafad’a hakane,itama bazataso acigaba da b’ata sunan y’ayanta ba, tanaso duniya tacigaba da ganinsa da k’ima da daraja dikda tasan yanzu kashi hamsin na darajarsa da kimarsa ya zube ammadai bazataso sauran yak’arisa zubewa ba kodan darajar y’arsu bunayya dakuma abunda ke cikinta. Ahankali tace “shkn, dakam nace bazansaka bakinaba sbd naso ahukuntasa daidai da lefinsa, amma yanzu nahakura zanyiwa yaya magana insha Allah” sai bunayya taji dadi hartai murmushi. Anan ta kwana washe gari taje gidansu hajiyarsu dady, ranar hajiya kamar ta goyeta dan murna itakanta bunayya saida tai mamakin hajiya, haka a b’angaren hajiyarsu ya ramadan. Sunyi farinciki sosai daganin bunayya, bata tafiba har saida su ya ramadan da abba suka dawo suka gaisa sannan da maraice ya ramadan dakansa yamaidata gida. Washe gari kuma bagudo tama sammako, hmm ranar bunayya taga gata, koda taje dik uncles d’inta basanan, sai maraice suka dawo aikwa sukaita jin dad’i daganinta, a ranar taso tadawo amma suka hanata, sai a washe gari bayan tagaza dangi ancika da alkhairai sannan uncle uthman yasaka aka maidata tareda bodyguards dinsa. Saida tak’ara kwana biyu nan kebbi arana ta uku dazata wuce taje gun dadynta, a yanda taga yazama saitaita kuka sbd dikya rame k’afar sa tazama yar k’arama dayar mai lfy tafita girma,shima dadyn kuka yadingayi yanata rok’onta yafiya cikin magiya. Dasauri bunayya tacemasa tayafe masa duniya da lahira Allah kuma yabashi lfy mai dorewa, kai daga karshema kasa jure ganinsa tai tafita dasauri tana kuka. Datakoma gidama dakyar momy tasamu tadaina kukan, bayan tadawo around 3:25pm dot suka fice. .................... Ahankali rayuwa mai cike da tarin farinciki tafara gudana acikin gidan bunayya dana momyn bunayya, bunayya sunkoma school suncigaba da karatu yayinda mashkur yafara aiki a babban companyn dadynsa dake abuja city yanzu sai weekend suke haduwa da bunayya dan itama hostel take amma dik weekend tana gida. Jira kawai yake tagama karatin yad’auketa sukoma can habujar. Cikin momy kowa sai girma yake masha Allah dik bayan sati daya ko biyu saisu bunayya sunje sunganta, a yanzu cikin yashiga wata na takwas danhaka yatsufa. Maganar ya ramadan da ruwaida kowa tazama babba har manya sunshigo sbd yaran sungama daidaita kansu, hakama mahbub aminin mashkur shima yagama daidaitawa da hamdallah k’awar bunayya, bak’aramin dady bunayya da mashkur sukajiba da wannan daddad’an lbrn. Tini aka saka ranar yin baikonsu sudika. Aranar Friday bayan ansakko da masjid akai baikon ruwaida da ya ramadan, next week kuma akayi na mahbub da hamdallah tareda saka ranar biki wata uku masu zowa. To Alhmdllh Allah inuna mana ameen. Bunayya da mashkur kowa k’aunar junansu sai dad’a k’aruwa take atsakaninsu, zaman lfy sai dada wanzuwa yake a tsakaninsu suna matuk’ar kaunar junansu kokad’an basasan abunda zai taba d’ayansu. #/Comment nd’ Share #/Aufana for life. _*AURENTA ZANYI....._*🌷 _Wattpad@Aufana8183_ _43.....END_ Rayuwa tacigaba da tafiya inda cikin yanzu cikin momy yatsufa sosai yaisa haihuwa koyaushe yanzu jiran zowan haihuwar ake. Bunayya sunshiga 300level yanzu har yanzudai haihuwa shuru ba ciki ba lbrnsa, tin abun baifara damun momy da mashkur ba haryafara damunsu musamman momy dan tamafi mashkur d’in damuwa,saidai itakam gogar ko ajikinta mamakinsu ma take yanda suketa damunta da maganar cikin. Ita bamataso tai ciki yanzu sbd ga wahalan karatu ina zata iya da wahalan ciki musamman yanda taga momy tawahala da wannan cikin, ga amai ga kyankyami wannan takeso batasan wancan, sannan bakomai takesan kamshinsa ba, ita yandama taji lbrn labour yafi d’agamata hankali shys kokadan batawani d’ana hankalinta ba. Sannu ahankali akafara shirye shiryen bikin ruwaida da ya ramadan, yanzu kusan dik bayan sati daya ko biyu sai ya ramada yazo yola gun habibiyarsa. Anacikin shirye shiryen biki kwatsam saiga haihu tazowa momy, bunayya na school aka kirata aka fadamata momyn ta tahaihu,cikin farinciki takira mashkur dake habuja shima tafada masa, dagacan school tafice kebbi. Koda taisa har sundawo daga hospital babyn na hanun yaya hauwa, cikin zumud’i da tsintsar farinciki ta karbi babyn tana tambayar yaya hauwa me aka haifa,yaya hauwa tafadamata namiji ne kamanninsa sak dady ba abunda bai d’akkoba na dady, aunty kuluwa dataji kama yaron yake da dady saitace Allah isa karya d’akko halinsa, nan akaita dariya. Ranar bunayya da momy kwanan farinciki sukai da wannan abun alkhairin daya samesu,bunayya tace “momy ashe Allah yarubuta bazaki mutuba har saikinga jininki a duniya” cikin murmushi momy tace tana shafa fuskar bunayya “bunayya koda ban haihuba harna koma ga ubangiji na bazan tabajin bak’incikiba sbd yabani ke kyauta batareda nasha wahalar nak’uda ko kayan cikiba, ke d’ayace tamkar dubu agareni, kinzamoman tamkar yaya goma koma fiyeda hakan, nasameki a lkcnda nake tsananin buk’atar yaya haka kuma kin k’aunaceni a lkcnda nai kusa narasaki kikace bakyasan kowa saini,tin a lkcn naji nadaina kwad’ayin haihuwa a duniya nad’aukeki y’ata wacca natsuguna na haifa, Sbd haka wannan haihuwar danayi yanzu wlh bawani abun dazai rage na tarin soyayyarda nake maki bunayya, tabbas kam nayi farinciki nakumayi gdy ga ubangiji daya bani haihuwar amma har jibi keta dabance a zuciyata kuma acikin y’ayana, bunayya inaso kisani naraba dukiyata biyu namallaka maki rabinta rabin kuma nabarwa wannan d’an dana haifa dama wasu dazan haifa idan Allah yabani” kwallah ke zuba a idanuwan bunayya, batasan lkcnda tarungume momynta ba cikin shauk’in soyayyar y’a da uwa. Tana fadin “ngd sosai momyna da irin soyayyarda kika nunaman tin ina acikin tsumman goyo har izowa yanzu, Allah ibarmana ke momy, yanzu kinga Allah ya amshi addu’ahta yabani d’an uwa wanda nima zan kalla ince k’anenane” sai momy tai dariya. Sai bayan kwana uku da haihuwa sannan mashkur yaiso haka shima yamak’e babyn ajikinsa kamar yalasheshi yakeji sbd mashkur akwaishi dasan yara sosai, samuwar wannan babynma saiya tasomasa da san haihuwarsa, bunayya dik kwanakinda akai tana mak’ale da babyn kota goyeshi kokuma tarungumeshi idan suna parlor, sai idan yai kuka sannan takaisa gun momy yasha nono kokuma idan yar barka sunzo. Ranar koda mashkur yazo yataddata tawani rungume babyn kamar zata bashi nono saiya harareta yace “kiyi zuciya kema ki haifomana namu babyn mana, da wannan mak’ale babyn momy dakikeyi” dariya tai sannan tace “nak’i din,anki ayi zuciyar” hassala yai yaje yamatseta tana ihu ya karb’e babyn yafita dashi, kukan shagwab’a tasamasa tana fadin “momy zoki amshi babynki ya mashkur zaitafiyarmaki da baby” momy najinsu tasharesu tana dariya kamar batajisuba. A ran daren suna dady ya aiko yana rok’on alfarma gun momy dan Allah tabada yaronshi akaimasa yagansa sbd yanzu andawo dashi gida yanacigaba da jinya sbd uncle Muhammad yace yajanye k’arar asaki dady kawai shys aka sakesa aka maidasa gida yak’arisa jinyar. Dafarko momy hanawa tai tace aje afadamasa idan yanasan yaga d’ansa to yajira har d’an nasa yagirma idan yagirma yafara yawo dakansa to watak’il Allah isa yatina dawani ubansa, idan yatina dashi yaje dakansa domin ganinsa to sai yagansa din ammadai yanzu bazai tab’a ganinsaba matuk’ar yana a hanunta sbd bai buk’aci ganinsaba. Dakyar da sud’an goshi bunayya tasamu taita lallab’anta hadda kukanta sannan ta amince, bunayya da mashkur suka d’auki babyn sukaje suka kaimasa, da kuka bunayya tadawo gida sbd ganin yanda dadynta yazama gwanin ban tausayi, idanma bakasanshi farin saniba a yanzu bazaka shaidashiba bazaka iya cewa shine ba sbd yanda yadawo. ................... Tamanin kud’i aka fitar a wannan shagalin bikin,

Table of Contents

Chapters

34 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});