Chapter 25
Episode Twenty five: The Eclipse
Kuka nayi sosai ni kadai babu mai rarrashina. Saida nayi na gaji dan kaina nayi shiru. Na kashe radion na chire CD din na fito daga motar. Ta kofar baya na shiga gidan saboda bana son ganin kowa. Direct saman mu na hau na shiga daki na turo kofa. Na zauna a kan gado ina kallon rubutun jikin CD din. I LOVE YOU. Nasan Ibrahim yana sona but how much? Ni a tunani na in kana son mutum zaka so ka kasance tare dashi, ya kamata ace komai runtsi komai tsanani ace muna tare, we can face anything together. Amma yanzu ya tafi, ya kuma kashe wayarsa ma'ana baya son magana da ni, sannan kuma yace min I love you?. What kind of love is this?. Na jawo kafafuwa na na dora akan gadon da dunkule a guri daya. I wish sanda ya fara cewa yana sona nace masa no, da ban saba dashi ba ballantana har inyi kewarsa. Da yanzu bana jin radadin da nake ji a zuciya ta. Na saka hannuna na jawo bargo na kudunduna. Wa yace da Ibrahim na damu da kudinsa ko rashin kudinsa? As long as we are together, that's the only thing I want. A hankali na mayar da idanuna na rufe.
Kaina ne yake bala'in sara min, idanuwa na sunyi min nauyi. Da kyar na motsa ido na ina son in bude su amma na kasa. Muryar mommy naji can nesa tana cewa "Moon3" na motsa bakina amma na kasa magana. Can nesa naji daada tana to fa min adduoi sai kuma naji kukan mommy kasa-kasa. To ita mommy mai ya sakata kuka? Ko har yanzu zancen da daddy yayi mana ne a ranta? Ita kuma daada me ya kawo ta dakin mu? Ita da bata shigowa part din mu in har daddy yana nan. Na tattaro dukkan karfina na bude ido na dan in tabbatar me yake faruwa. Ga mamakina sai naga dakin ya chanza min, ya koma kamar dakin asibiti, ga ledar ruwa nan a sakale a kusa da gadon da nake kuma daga dukkan alama ni ake karawa ruwan saboda igiyar hannuna ta shiga. Mommy tana zaune akan kujera a kusa dani ta jingina kanta a jikin daada wacce take tsaye a kusa da ita tana lallashinta. Dama mommy ta saba, in dai wani a cikin mu bashi da lafiya to ta ringa kuka kenan har sai ya warke. Na kalli daya side din gadon. Hafsat ce a zaune a zabga tagumi fuskar ta da alamar damuwa. To da gaske ni ce bani da lafiyar kenan tunda nice a kwance. A hankali na furta "mommy" ta dago jajayen idanuwanta ta kalleni sannan ta kalli daada wacce itama ni take kallo. Gaba daya suka karaso kusa dani mommy ta rike hannuna mai dauke da drip. Nace "mommy wai bani da lafiya ne?"da sauri mommy tace "lafiyar ki kalau my daughter, kawai zazzabi ne kike yi, maybe ma malaria ce" mommy bata iya karya ba dan haka tana fada na gane ba haka bane. Hafsat ta fita sai gasu sun dawo tare da likita. Dan matashin saurayi ne haka dogo marar kiba. Ina ganin sa gaba na ya fadi. Ibrahim. This is not Ibrahim. Ibrahim is gone. Na rintse idona kaina yana cigaba da sara wa. Doctor din ya auna ni yace "zan sake yi mata allurar bacci saboda ciwon kan, kar a tasheta sai ta tashi da kanta, in ta tashi sai mu sake gwada jinin nata mu gani in ya sauka" what? Me likitan nan yake nufi in jini na ya sauka? Yaushe ya hau ballantana ya sauka? Shigar allura naji a cinyar hannuna daga nan kuma shikenan.
Sanda na sake bude ido na mommy na sake gani a zaune a inda take, amma ta chanza kaya, fuskarta harda kwalliya. Da sauri tazo kusa dani ta zauna tana murmushi. "Sannu Moon, ya jikin naki?" Nima nayi mata murmushi nace "da sauki mommy" ta dauki wayarta tana waya, daga alama Ya Walid ta kira, naji tana ce masa na farka su shigo. Ba'a jima ba sai gasu complete har daddy. Duk sunyi kwalliya kuma kowa da murmushi a fuskarsa. Nan da nan dakin ya hargitse da hayaniya kowa a cikin su na kokarin jawo attention dina zuwa wajensa. Daddy ne ya, dauko wata sabuwar system kirar apple, red colour, yace "surprise!!" Ya miko min, na tashi zaune da sauri, ciwon kan ya ragu sosai, na karba ina godiya, yace "get well soon sunshine" sannan yayi min kiss a goshina, the same spot da Ibrahim yayi min ranar da zamu rabu. Ya Habeeb ya tabe fuska kamar mai shagwaba yace "gaskiya nima bara in zo in fara rashin lafiya tunda har gift ake bawa mutun in bashi da lafiya" gaba daya suka yi dariya, nima nayi murmushi. Mommy ta dauko wayarta ta zagayo ta bayana tace "selfie" nan da nan duk suka taho kowa yana zuro guskarsa, faruk har da hawowa kan gadon da nake ya kwanta a jikina. Mommy ta nuna min hoton tace "look moon, duk ke kika chinye hoton" na karbi wayar na duba, sam banyi kyau ba, bakina duk a bushe, fuskata tayi fari tas kamar babu jini, gashina duk a tarwatse ga idona ya fada ciki kamar nayi sati a kwance. Na kalle su daya bayan daya duk suna min murmushi, na gane me sukeyi, they are trying to cheer me up saboda jini na daya hau ya sauka. They love me so much and I love them too. They mean more to me than Ibrahim ever will.
Har dare suna nan. Anan duk suka ci abincin dare. Sai lokacin na fahimci kwana na biyu a asibitin. Mommy da kanta tayi min wanka da ruwa mai zafi dan inji karfin jikina, ta shafa min mai ta chanza min kaya, ta bani kunun gyada mai zafi ta saka dole sai da na shanye cup daya. Sosai naji dadin jikina. Mommy ce ta kwana a gurina. Da daddare ta saka ni duk saida na rama sallolin da ake bina sanda nake bacci. Washegari da safe doctor yazo ya auna ni yace jinin ya sauka sosai, zasu rikeni zuwa yamma su gani, in bai kuma hawa ba sai su sallameni.
Bayan an sallame ni mun koma gida ma haka ce ta kasance, dan mommy dawowa tayi dakin mu muke kwana tare. Tace barin mu da take yi mu kadai ne ya saka nake tunani har jini na ya hau. Daddy kuma kullum sai ya shigo kafin ya fita, in ya dawo ma sai ya shigo. Kwana na biyu a gida na warke sosai, babu ciwon kan sam kuma tunanin ma ya ragu, dan sam ba'a barina ni kadai. A week after that daddy ya sake kiran mu palonsa. Muna zuwa muka tarar dashi da mommy a zaune, ya Walid da Ya Habeeb ma duk suna zaune a kasa. Muna zama sai ga Faruk shima ya shigo. Ya Walid yayi mana addu'a muka shafa. Daddy yayi gyaran murya yace "kamar yadda na gaya muku wancan zaman cewa zan neme ku bayan sati daya, rashin lafiyar moon ce ta saka har muka yi delaying zaman. Yanzu ina son in gaya miki wani abu moon, ba fa matsa miki nayi nace sai kinyi aure ba, ra'ayinki nake so inji. Kuma gashi naga har yau shi wanda nayi miki magana akansa bai zo ba, kuma ko a asibiti ban ganshi ba. Ina so inji kunyi magana dashi ne? Nayi shiru can na dago kaina nace a nutse "daddy munyi magana dashi amma na fahinci cewa he is not serious akan maganar, dan haka nima na yanke shawarar zan fara karatu na first kafin inyi aure" murmushi ne ya bayyana a fuskar mommy tace "Alhamdulillah, kafin ki gama karatu kuma insha Allah kin samu wani" ni dai na sauke kaina kasa bance komai ba. Daddy yace "to Alhamdulillah, hakan ma yayi, Allah yasa haka shi yafi alkhairi. That been said, ni da mommyn ku mun yanke shawara, tunda Walid da Habibi suna karatu a England, ga Hafsat da Moon suma sunce karatu zasuyi, to zamu tattara gabaki daya zamu koma England da zama. Dama tunda nazo nake ta chuku2n yadda za'ayi min transfer daga kasar da nake yanzu zuwa England kuma Alhamdulillah jiya aka tabbatar min da samuwar transfer di ta, mommyn ku kuwa ta rubuta leave of absence a office dinta har sai ranar da Allah ya sa muka dawo Nigeria. Faruk shi kuma tunda saura shekara daya ya kammala sec school zamu barshi anan shi da daada har sai ya kammala tukun sai ya bi mu can" tunda ya fara maganar komawa England gaba daya palon ya hargitse, kowa murna. Ni ina zaune kawai ina kallonsu suna ta tsalle suna rungume juna, at the same time ina assessing maganar daddy. Tsam na zame jikina na bar palon na hau saman mu, kofar balcony na bude na fita waje na kama railers ina kallon exact gurin da naga Ibrahim last. Dear Ibrahim, when are you coming back? Dole na san sai na bar Nigeria. Tunani na anan shine, what if Ibrahim ya dawo ya tarar bana kasar? Ta yaya zaiyi contacting dina? Na zauna na danyi tunani kadan sai na dauko takarda da biro na fara rubutu kamar haka:
Dearest Ibrahim
I may not be around when you come back. Please give the man who gave you this letter your new phone number and I will call you.
I miss you
Maimunatu.
Na ninke takardar na saka a envelope nayi sealing. Sai da naga babu mutane a compound din gidan sannan na fita na tafi gurin baba Habu mai gadi. Tun da daddy ya gina gidannan ya saka baba Habu gadi kuma har yau shine yake bude gate da rufewa. Ina zuwa na ganshi a zaune a kan benci shi kadai. Na zauna a gefensa na gaishe shi, ya amsa min da fara'arsa. Nace "baba yanzu kuwa zaka iya gane wanda ya kawo maka sako rannan yace ka bani?" Da saurinsa yace "sosai ma kuwa. Ai ina da mantuwa amma kuma ina da gane mutane" na dauko takardar hannuna na mika masa nace "baba dan Allah gashi, duk sanda yazo in bana nan ka bashi kace injini, zai baka sako ka bani. Baba dan Allah kar ka manta" ya kalleni da alamar tambaya a fuskarsa amma ya daure ya ce "in sha Allah mai sunan daada, kar kiji komai" nayi masa godiya na koma cikin gida.
Shirye shirye akeyi sosai na komawar mu England, daddy yace yana so mu je 'yalleman muyi musu sati daya kafin mu tafi, duk da dai zamu ke zuwa Nigeria in mun sami hutu.
Kafin tafiyar mu sai ga sako daga former school din mu ana gayyatar mu taron speech and prize giving day da graduation party da school ta shiryawa 'yan set din mu. Hafsat tana ta murna ni kuma nace bazanje ba. Mommy tayi tayi dani inje saboda da akwai awards da za'a bani kuma ko ba komai ai zanga friends dina za muyi sallama tunda ba lallai mu kuma haduwa da wadansu ba, ga pics da video da za'ayi na tarihi. Hafsat kamar zatayi kuka tana roko na akan inje amma naki nace har yanzu bana jin dadin jikina. Su basu san abinda yasa naki zuwa ba. I don't want to bring back the memories, which is exactly what will happen idan naje. Ina kallo Hafsat taci kalliya kamar ba gobe ta tafi, na bata sakon ta gaishe min da kowa kuma ta karbo min gift dina. Suna tafiya na koma balcony na zauna ina kallon hanyar da Ibrahim yabi. We made so many plans for our graduation party. Ibrahim cewa yayi zai yi mana anko ni da shi mu saka ranar. Nayi murmushin takaici ina tausayin Hafsat akan irin tambayoyin da zata sha a gurin 'yan ajin mu in sunga babu ni babu shi. Haka staff ma, dan kusan kowa yasan abinda yake tsakanina dashi. Na sake yin wani murmushin dana tuno yau shine exactly two years da haduwa ta dashi. Yanzu gashi mun rabu kuma ko hotonsa bani da shi, amma ina da permanent picture dinsa a zuciya ta. A hankali na furta a fili "Happy Anniversary Ibrahim
Table of Contents
Chapters
- 1 Episode One : The Beginning of the Beginning
- 2 Episode Two: Meet my Family
- 3 Episode Three: Loved by All
- 4 Episode Four: Moon's Sister
- 5 Episode five: The Strangers
- 6 Episode six: The Challenge
- 7 Episode Seven: The Thin Tall Man
- 8 Episode Eight: The New Imam
- 9 Episode Nine: Give Me a Chance
- 10 Episode Ten: I Don't Know
- 11 Episode Eleven : The Protector
- 12 Episode Twelve : This is Me
- 13 Episode Thirteen : This is Me 2
- 14 Episode Fourteen : The Limit
- 15 Episode fifteen: blood is Thicker than Water.
- 16 Episode Sixteen : The Letter
- 17 Episode seventeen: Reply
- 18 Episode eighteen: what's Next?
- 19 Episode Nineteen: The Goodbye
- 20 Episode Twenty: The New Job
- 21 Episode Twenty one: Amira
- 22 Episode Twenty Two: Efisowa
- 23 Episode Twenty three: The Break up 💔
- 24 Episode Twenty Four: The Heartbreak 💔
- 25 Episode Twenty five: The Eclipse
- 26 Episode Twenty Six: A Step Further Away
- 27 Episode Twenty Eight : University of Oxford
- 28 Episode Twenty Nine: The Message
- 29 Episode Thirty : The Final Blow
- 30 Episode Thirty One: Let it go
- 31 Episode Thirty Two : Munnir
- 32 Episode Thirty Two : Mahdi
- 33 Episode Thirty Three: Zayed
- 34 Episode Thirty Four : Back to Square One
- 35 Episode Thirty Five : When Destiny Calls.
- 36 EpisodeThirtySix: Interesting
- 37 Episode Thirty Seven : The Dinner
- 38 Episode Thirty Eight : The Shadow
- 39 Episode Thirty Nine : The Shadow 2
- 40 Episode Forty :TheShadow 3
- 41 Episode Forty One : Born for This.
- 42 Episode Forty Two : Born for This
- 43 Episode Forty Three: America
- 44 Episode forty four : America 2
- 45 Episode Forty Five : The Rush
- 46 Episode Forty Six : The Repentance
- 47 Episode Forty Seven : Amir
- 48 Episode Forty Eight : Awkward
- 49 Episode Forty Nine : Ya Habeeb
- 50 Episode Fifty : Munir 2
- 51 Episode Fifty one : Mommy
- 52 Episode Fifty Two : The Journey
- 53 Episode Fifty Three : Daddy
- 54 Episode Fifty Four : Her Father's Daughter
- 55 Episode fifty five : Her Father's Daughter 2
- 56 Episode Fifty Six : What You Sow
- 57 Episode Fifty Seven : What You Sow 2
- 58 Episode Fifty Eight : I Missed You
- 59 Episode Fifty Eight : For You, Only You
- 60 Episode Sixty : The Prince
- 61 Episode Sixty One : Save the Date
- 62 Episode Sixty Two : The Manager
- 63 Episode Sixty Three : Amira 3
- 64 Episode Sixty Four : The Past and the Future
- 65 Episode Sixty Four : The Visitors
- 66 Episode Sixty Six : The Wedding
- 67 Episode Sixty Seven : The Wedding 2
- 68 Episode Sixty Eight : The Wedding Night
- 69 Episode Sixty Nine: The Wedding Night 2
- 70 Episode Seventy : The Wedding Night 3
- 71 Episode Seventy One : The Honeymoon
- 72 Episode Seventy Two : My Everything
- 73 Episode Seventy Three : His Father's Son
- 74 Episode Seventy Four : The Cook
- 75 Episode Seventy Five : The Emir
- 76 Episode Seventy Six : The Visitors
- 77 Episode Seventy Seven : Amina
- 78 Episode Seventy Eight : The Storm
- 79 Episode Seventy Nine : The Lightening and The Thunder
- 80 Episode Eighty : The Skeleton in The Closet
- 81 Episode Eighty one : The Skeleton in the Closet 2
- 82 Episode Eighty Two : The Light
- 83 Episode Eighty Three : The News
- 84 Episode Eighty Four : Little Love
- 85 Episode Eighty Five : Ibrahim
- 86 Episode Eighty Six : The Phone Call
- 87 Episode Eighty Seven : Riyadh
- 88 Episode Eighty eight :Khairat
- 89 Episode Eighty Nine : Khairat 2
- 90 Episode Ninety : His Mother's Son
- 91 Episode Ninety One : His Mother's Son 2
- 92 Episode Ninety Two and Three : Maldives 1 and 2
- 93 Episode Ninety Four : RIP
- 94 Episode Ninety Five : The Light
- 95 Episode Ninety Six : The New Bride
- 96 Episode Ninety Seven : The Real Prince
- 97 Episode Ninety Eight: My Baby
- 98 Episode Ninety Nine : New Little Love
- 99 Episode Hundred : Not The End.