Chapter 87
Episode Eighty Seven : Riyadh
Sai da naji daukewar numfashinta ta cikin wayar, sai kuma ta fara maganar da sauri cikin rawar murya kamar mai shirin yin kuka "what? What did you just said? Sultan is your husband? Yana ina ? Yana kusa dake?" Nace "yana jin duk abinda kike fada ummee" ta sake cewa "what? Sultan? Kana jina? My son are you there?" Sultan ya taso da sauri ya taho inda nake zaune ya kwace yawar daga hannuna, ban ankara ba sai gani nayi ya buga ta da jikin bangon dakin, a take ta tarwatse a kasa, ya tsaya yana kallona yana numfashi sama sama tamkar wanda yayi gudu, sannan kuma ba tare daya sake cewa komai ba ya juya ya shiga kofar corridon da zata kaika bedroom dinsa, yana shiga ya bugo kofar da karfi har sai da dakin yayi motsi. Na mike tsaye ina kallon kofar, dama nasan sai munyi drama da sultan akan ummeen sa, amma na shirya damarar sai na daidaita su, so help me God. Na karasa inda pieces din wayata suke na durkusa na tsince, wannan wayar ta gama yawo sai dai kuma wata ba ita ba, na zare sim card dina da memory card na tattara sauran na zuba a wastebasket, na kashe kayan wutar dakin na rufe koina na bishi dakinsa, ina shiga na tarar dashi a kwance a kan gado ko kayan jikinsa bai cire ba, idonsa a rufe kuma nasan ba bacci yake ba, na shiga toilet nayi shirin kwanciya nazo na saka wata T-shirt dinsa babba wacce tazo min har chinya ta, har yanzu yana nan a yadda yake, na kashe fitilar dakin na hau gadon nayi addu'ah sannan na jawo pillow na can nesa dashi na kwanta na juya masa baya, ko minti biyu banyi da kwanciya ba na jishi ya mirgino ya dawo jikina, ya saka hannuwanshi ya zagayo ni ta baya, bance masa komai ba, mun jima a haka sannan naji yace "why did you call her bayan na gaya miki I want nothing to do with her?" Nace "bani na kirata ba ai, ita ta kirani" yace "amma ai ke kika saka har ta kira ki din, kina sane ai" nace "afuwan, ayi hakuri" yace "please don't call her again" nace "I don't even have her number ta yaya zan kirata? Besides, ka fasa min wayar ma" yace "I will get you another one tomorrow. Ko ta kuma kiranki kar ki dauka, am doing perfectly fine without her" na juyo ina kallonsa na bata rai duk da nasan duhu ne ba gani zaiyi ba, nace "why are you blaming her wai? Bayan kasan bata da laifi" yace "she left me, shine laifinta" nace "she didn't, a gaba na Takawa ya gaya maka a ka aka dauke ta aka fita da ita, what is her fault in that?" Yace "she should have come back for me, why didn't she look for me all these years?" Nace "bansani ba sultan, amma nasan dole tana da dalilin ta, uwa tafi gaban komai a duniyar nan. Ba zaka san dalilin da yasa bata dawo ta neme ka ba har sai ka bata chance, har sai kayi magana da ita, idan kunyi maganar kaji cewa hujjarta is not good enough nayi maka alkawarin ba zan sake yi maka maganar ta ba" na daure shi da jijiyoyin jikinsa, bashi da amsar da zai bani sai cewa yayi "maganar ta isa haka. Let's sleep".
Washegari na daura niyar fara abinda zan yiwa sultan, dan haka dana hada mana breakfast sai naci nawa a kitchen na kawo masa nasa coffee room dinsa, na tafiyata dakina, ina zaune a palo ya shigo, naji kamshin turarensa amma ban dago na kalleshi ba, yace "me yasa baki zo munci abinci tare ba?" Na bawa iska ajjiyarsa, ya karasa shigo wa dakin ya tsaya a gaba na, ya shirya alamar office zai fita, kallo daya nayi masa na dauke kaina, yace "magana fa nake miki Moon" na yamutsa fuska nace "naji ai, nafi son cin abincin ni kadai ne shi yasa" ya saka hannu ya juyo da fuskata yace "wai duk akan maganar wayar ne? Yanzu kafin inje office ma zan siya miki wata" bance masa komai ba kuma ban kalle shi ba. Ya dora lips dinsa akan nawa yana kissing, na kwace fuskata na mike na bar gurin ina juya masa bombom, ina shiga daki na bugo kofa ta da karfi irin yadda yayi min jiya.
Ranar Amir ne yazo daukar musu abinci, yana zuwa ya miko min waya yace "gashi inji oga kwata kwata, yace yayi miki charge, kuma dan Allah ki kirasa yanzu" na karba nace "to nagode" yace "ki kirashi fa, dan tun safe yana can ya kasa zana komai, yace rashin jin muryarki ne" na kirkiro murmushi nace "zan kira ai" Amir yana fita na jefar da wayar akan kujera nayi tafiya ta daki. Ranar sultan bai kai yadda ya saba kaiwa a office ba sai gashi ya dawo, ya tarar dani na tasa gyada mai gishiri a gaba ina ci, na daga kaina nayi masa sannu da zuwa na cigaba da abinda nake yi, yazo ya zauna a gaba na ya harde kafa yana leka fuska ta yana murmushi, saura kadan in mayar masa amma na daure na bata fuska, yayi ajjiyar zuciya yayi tagumi da hannu biyu yace "wa ya baki gyada?" Nace "ai kawa nayi aka siyo min" yace "amma kinsan duk abinda kike so ba tare muke zuwa mu siyo ba?" Nace "na hutashshe ka" yace "ina wayarki?" Nace "bana bukatar waya ni, tunda babu wanda zan kira da ita" Har ya tashi ya tafi kuma sai ya dawo ya sunkuya ya dauke ni chak ya tafi dani bedroom dinsa. Ban hana shi komai ba amma barinsa nayi yayi abinsa shi kadai, shi kadai yayi kidansa kuma yayi rawarsa, kamar zaiyi kuka yace "Love menene hakan ne kike yi wai. Please come back to your normal self, I don't like this new you" ba tare dana kalleshi ba nace "kai ka siya ai da kudinka" ya danyi shiru sannan yace "yanzu me kike so ayi?" Na juyo ina kallonsa nace "ka shirya mu tafi Riyadh" da sauri ya girgiza kai "no way, babu inda zamu je" na mike na dauki riga ta ina sakawa nace "ok, suit yourself" ina jin yana kirana nayi tafiyata ba tare dana waigo ba. Haka na cigaba da gasawa sultan gyada a hannu, he is beyond frustrated yanzu, ban hana shi taba ni ba amma shi kansa ba jin dadin abin yake yi ba, murmushi kuwa rabon da inyi masa tun kafin muyi waya da Ummee. Na kunna wayata na saka sim card dina saboda kar mutane suyi ta nema na, ban jima da kunna wa ba kuwa Hafsat ta kira ni "Moon me ya faru ne ranar nan? Wayar ta dauke kuma munyi ta kira shiru bata shiga? Na gaya mata duk yadda mukayi da sultan, tace "ai kuwa ta tayar da hankalinta, ranar kusan kwana tayi tana kuka, har sai da nayi nadamar tayar da maganar nan. Yanzu menene abinyi?" Nace "kin san halin sultan, and he is probing harder than I thought, amma zan cigaba da ganin yadda zanyi dashi. Ki kwantar mata da hankali, ki san abinda zaki gaya mata". Ranar hankali na ya kara tashi akan maganar ummee, na yanke shawarar zan shigar da Takawa cikin maganar. Yana zuwa da daddare na riga sultan zuwa, naje na gaishe shi ya amsa da fara'arsa yana min godiyar kokarin da nake gurin yi musu hidimar abinci. Na dauko waya ta na buda hoton Ummee na ajiye masa a gabansa ina kallon fuskarsa, ga mamaki na sai naga banga changin komai ba, ya dagi kai yana kallona yace "Hafsat ce ta turo miki?" Mamaki ya kara kamani nace "eh" ya gyada kai yace "tun washegarin ranar dana dawo hayyacina na aika har can Riyadh din nace a binciko min labarinta, an kuma bani labarin komai, nasan dan wanta ne yake auren yayarki Hafsat, har number dinta an turo min, what I lack is the courage to call her" na kalleshi da mamakin wai kamar shi ne zai ce bashi da courage, yace "yes, after all we went through together sannan kuma na tura mata da takardar saki kuma na kwace mata danta tsahon shekaru talatin, I don't know me zance mata in na kirata ko kuma na je wajanta" na sunkuyar da kaina, yace "sultan yaga picture din?" Nace "eh ya gani" yace "me yace?" Nace "he didn't say anything yet" yace "kina ganin zaije?" Nace "maybe, amma ba yanzu ba" yace "yayi fushi ko?" Kai kawai na gyada masa, kafin ya sake cewa komai sultan ya shigo dakin, ya bimu da kallo yana kallon waya ta a gaban Takawa, bai ce komai ba na mike na bar gurin, ina kallon sultan yana harara ta a raina nace yau akwai daru kenan. Ai kuwa Takawa yana tafiya sai gashi har dakina, "zancan me kuke yi dazu kafin inzo?" Nace "zancen Ummee muke yi" cikin fushi yace "dama dashi kuka hada baki kenan" na girgiza kaina nace "bamu taba maganar dashi ba sai yau, yanzun ma kuma ni ce na fara yi masa maganar, ashe duk abinda nake son in fada masa ya sani, yana da address dinta da number wayarta da komai amma ya kasa kiranta saboda bai san me zai ce mata ba" ya zauna a kusa dani yace "me yace?" Na juyo ina kallonsa nace "ya tambayeni in ina ganin zaka iya zuwa gurinta" ya mike tsaye da sauri "no, I am not going to be dan aiken soyayyar su, if he want his wife he should go get her by himself" nace "then go as her son, ba wai dan aiken takawa ba" ya sake cewa "NO, ita me yasa ba zata zo Nigeria ba? In tana son gani na tasan a inda nake, abinda zatayi kawai shine ta je airport ta shiga jirgi ya kawo ta Nigeria. Tunda kika ga tsahon shekara talatin bata zo ba to bata son ganina, ba zanje ta wulakanta ni inzo in ji haushi ba, maybe tayi wadansu yayan and she don't need me in her life" yana maganar yana zagaye dakin, nace "bata yi wadansu yayan ba, in fact vata kuma yin wani auren ba tun barinta Nigeria" ya tsaya da zagayen da yake yi ya kalle ni yace "then why didn't she come for me?" Na mika masa wayata nace "call her and ask her, ni bansani ba" ya karbi wayar ya ajiye a gefe, at least wannan karon ba'a fasa min waya ba. Na mike tsaye na karasa gabansa, na saka hannu biyu na riko fuskarsa nace "Sultan she has been crying tun ranar da muka yi waya da ita, ta gane abinda ya faru, ta gane kai ka kashe wayar saboda ba kason magana da ita, ta gane cewa fushi kakeyi da ita. Sultan mahaifiyar kace fa, kar ka bari ubangiji yayi fushi da kai akanta Sultan, ko ma menene tayi ya kamata ka saurare ta" bai ce min komai ba ya sauke idonsa kasa, amma nasan I got his attention, na jayo hannunsa muka dawo muka zauna akan kujera, yace "ni yanzu inna kira ta to me zance mata? I miss you zance mata ko me?" Nace "I miss you din ma is in order" yace "no, it's not, ban san taba ballantana inyi missing dinta" nace "then let's go to her. In baka san me zaka ce mata a waya ba in muka je ka ganta ido da ido am sure zaka san me zaka ce mata" ya girgiza kansa stubbornly, ba tare da warning ba na hade bakin mu na fara kissing dinsa da zafi zafi, nan da nan kuwa ya dauki zafi, dama abinda yake ta nema ne ido rufe naki in bashi, yau sai gashi har gida, nan na fara sarrafa shi son raina, duk abinda nasan yana so shi nayi masa double, na ruda shi sosai na rikita masa tunanin sa, duk wani stubbornness dinsa sai da na cire masa shi ya dawo a tafin hannuna, a nan kan kujerar muka sauke hajar mu. Ana gamawa Sultan yace shi kari yake so, na bata rai na juya masa baya, ya jawo ni ya kwantar a kirjinsa yayi ajjiyar zuciya yace "why do you care about her? Baki santa ba, baki san halinta ba, for all we know maybe tana zuwa gidan nan ke ce mutum ta farko da zata ce bata so" nace "maybe, maybe not. Maybe tana zuwa gidan nan son da zata yi min sai yafi wanda zata yi maka, we will never find out idan bamu je ba" ya bata fuska kamar zai yi kuka yace "please Love I really don't want to go" nace "then let me go. In kai ba zaka iya zuwa ba ni ka barni inje, Hafsat da zayed suna can, at least in naje muka yi magana da ita zan samo maka duk amsar tambayoyin ka, daga nan sai ka yanke shawarar me zakayi next" yayi shiru yana tunani, ba dan hannunsa da yake shafa cikina ba zan iya cewa bacci yake yi saboda dadewar da yayi a haka. Can yayi magana "zaki je next week, zakiyi three days a can, a gurin su Hafsat zaki sauka saboda bana son a wulakanta min ke, in na fita gobe zan fara processing tafiyar taki" da sauri na mike zaune ina rawar murna, na manta ma babu kaya a jikina sai daga baya na tuna na koma na dunkule a jikinsa, yana dariya ya dago ni yace "amma da sharadi, daga yau duk abinda nake so shi za'a ke yimin, ko yaushe ne kuma ko a ina ne, in ba haka ba an fasa tafiyar" nace "yes sir, an gama" ya mike tsaye ya mikar dani yace "yanzu sai muje daki mu cigaba daga inda muka tsaya".
Washegari duk da farin ciki muka tashi, ni ina murnar na shawo kan sultan shi kuma yana murnar mun dawo rayuwar mu dai dai, dan haka ranar da kyar ya fita office. Bayan mun kammala duk abubuwan al'ada na gyaran gida muka shiga kitchen muna kokarin dora abincin yana, sai ga yarinya tazo tace min wai nayi bakuwa, na leka palon naga Amira na rike kugu nace " au dama ke ce bakuwar zaki wani zauna a palo? Ki tashi ki cire wannan mayafin ki taho kitchen" tana dariya ta ajiye mayafin ta ta taho, a kitchen din muka gaisa sosai sannan ta gaisa da Asma'u da sauran yarana, na lura tayi sanyi sosai kuma naji ina tausayinta har cikin raina. Sai da muka kusa kammala aikin sannan muka bar su Asma'u muka dawo palo muka zauna, muka fara hira, mostly hirar da yadda kawancen mu yake, da yadda tayi ta bani shawara akan sultan ni kuma na rufe idona naki dauka, wani gurin muyi dariya wani kuma muyi jimami, ina sane na sako mata zancen Ibrahim da labarin yanzu Amina yake nema, ina maganar ina kallon fuskarta inga yadda zata dauki maganar amma sai naga babu wani chanji a fuskarta sai ma alamar tana taya Amina murna. Muna nan zaune muka ji sallama, Amira tayi saurin daukan mayafinta ta yafa, a raina nace 'har yanzu ustazancin yana nan kenan' Abbas ne ya shigo cin abinci, da yake shima yanzu anan yake cin abinci tunda har yanzu bai huce da Hajiya ba. Ina sane nace Amira tayi serving dinsa, ta harare ni na langwabar da kai na nuna mata cikina, ta tashi ta bishi dining tana serving dinsa, ina jiyo maganganun su, dan Abbas akwai surutu kamar fa'iza, saratu ce mai shiru shiru dinsu. Bayan ta gama ta dawo gurina muka cigaba da hirar mu, sam ban bata labarin komai da yake wakana a rayuwar mu da sultan ba saboda ance once biting twice shy, bayan Abbas ya tafi muma muka je muka ci abinci tare sannan ta tafi gida. Bata jima da tafiya ba sai ga Abbas ya dawo, ina ganinsa nace a raina tarko na yayi kamu kenan, yazo ya zauna yana shafa kai yace "babbar yaya wacece dazu tazo gidan nan?" Na hade rai amma cikin wasa nace "ina ruwanka da ita?" Yace "please ki dan shigar dani mana" na wara hannuna nace "a nawa? Kasan ni bana aikin banza" yace "zanyi ta yi miki addu'ah kullum idan nayi sallah. Please" nace "ni ba zan shigar da kai ba, zan dai baka number dinta ka je ka shigar da kanka" yayi godiya ya karbi number din ya fita. Asma'u tana daga kitchen ta leko tace "dama nasan za'a rina, wai an saci zanin mahaukaciya" muka yi dariya tare.
Na kira Hafsat na gaya mata an bar ni zuwa, nace ta gaya wa Ummee cewa zanzo amma ni kadai, anan take gaya min cewa khairat ta hana ta komawa gidan su zayed tun da tasan dangantakata da ita, anan gidan yanzu take sai dai zayed yazo gurinta, tace min itama tana murnar zuwan nawa nan da sati daya. Satin da sauri yazo, tun kwana uku tafiya ta na fara hada kaya, sultan kam sai kumbura yake yi, kullum sai ya tsara min yadda tafiyar zata kasance, yace gurin Hafsat zan sauka, sau daya zanje gurin Ummee, in naga babu fuska kar in sake zuwa, ni dai to kawai nake ce masa amma ni na gama plan dina, ana gobe tafiyata naje gida na wuni gurin Mommy, Daddy dama baya nan lokacin, na gaya wa Mommy komai yadda ake ciki da kuma plan din da nayi, farko ta fahimta kuma ta yarda, sai kuma daga baya ta zama alarmed, "kin ga neman takawa dama suke yi suyi masa hukuncin sace musu 'yarsu da yayi, kar kije kuma su kama ki ke" nayi dariya nace "Mommy ba abinda zasu yi min, shekara talatin fa da yin abin, besides, gurin Hafsat zanje". Sai dare sultan yazo daukana, tun a mota yake cewa shi ya akayi ya bar ni wannan tafiyar ne, a ranar yadda muka ga dare haka muka ga rana, sultan yayi nadamar bari na yafi cikin charbi, sai kara jaddada min yake yi "three days kawai, babu kari, make sure wayarki a kunne take all the time, in kinga zasu daga miki kai ko su Hafsan ne ma ki rabu dasu kije ki kama hotel ki kwana da safe kiyi tahowar ki" ni dai sai to kawai nakr ce masa. Da safe saura kadan ya saka inyi missing plight kuma nasan yana sane, so yake in fasa tafiyar amma naki. Muna zuwa airport yace "ko dai ince na fasa barinki tafiyar nan ne?" Nace "nasan ma ba zaka fadi haka ba" yace "saboda me kika ce haka?" Nace "because you are a man of your words" ya girgiza kai kawai ya fito min da akwatina, har sai da aka fara cewa za'a rufe kofar jirgi sannan sultan ya sake ni na tafi. Ina shiga jirgin ina zama naji na fara missing dinsa, na dauko waya na kira shi nace "already missing you Darling" yace "then come down ki fasa tafiyar nan please" nace "no, na riga nayi niyyar, just pray for me" ya kashe wayar bai ce min komai ba.
Wajan asr jirgin mu ya sauka a birnin Riyadh. Ina fita reception na hango Hafsat da Zayed suna jirana, na karasa da sauri na rungume Hafsat da naga ta kara kiba da kyau, jin dadi sosai ya bayyana a tare da ita, Zayed ya karbi akwatina yana cewa "welcome to my home town sister In-law, kin zama in-law dina ta two sides" muka yi dariya a tare. Muna shiga mota yace "gidan khaloo (Aunty) zamu je ko?" Nace masa "eh" ni dai duk ina feeling nervous, ban san ya zata karbe ni ba, what if sultan is right? What if ta wulakanta ni?" A hanya Hafsat take ce min wai khairat har fenti ta saka aka sakewa gidan ta na tara ta, wai yau tun safe take kitchen tana girki, ta rasa me zata dafa min, jiya kuma sam bata yi bacci ba saboda anticipation. Wannan maganar ce ta dan kwantar min da hankali.
Tun daga gate din gidan nasan an ajiye dukiya a gidan nan. Ya hadu karshen haduwa, dan bazan iya tsayawa fassara haduwar sa ba. Ni dai kawai bin su Hafsat nake a baya da sakakken baki ina kallo, mun wuce palo sunfi uku sannan muka zo inda suka ce min shine palon ta, zayed ya bude kofar da sallama sai kuma yaja baya ya bani guri yayi min alama da in shiga, na hadiye yawu da kyar sannan na daga labule na shiga da sallama. Tana zaune akan kujerar da take facing din kofa, bakar abaya ce a jikinta da rolling irin na larabawa, gashin kanta ya fito ta kasan mayafinta ya sauka har gadon bayanta, ta saka hannayenta a tsakanin cinyoyinta, ta bude idanuwanta tana kallona, she looks more like sultan in reality than in the picture. Kallo daya nayi mata naga extreme of innocence a fuskarta. Ta mike tsaye tana jujjuya hannunta, idonta ya sauka akan dan karamin cikina, naga kwalla ta fara taruwa a idonta, ta kasa cewa komai, na karasa shiga palon a hankali, kafin inyi magana wayata tayi kara, ina dubawa naga sultan, na dauka da sallama, bai amsa ba yace "kin fasa yin kwana ukun, na duba naga gobe da akwai jirgin safe daga nan Riyadh zai dawo Nigeria, ki biyo shi ki dawo" nace masa "an gama" na katse kiran, na kashe wayar gaba daya na saka ta a jaka ta. A hankali tace "Sultan ne" Nace "eh shine" Tace "he is already regretting letting you come ko?" Nace "yes" take naga fuskarta ta chanja kalar tashin hankali, tace "fushi yake yi dani and I don't blame him, sai dai bansan me zanyi masa ya hakura ba. Cewa yayi ki koma Nigeria ko?" Nace "yes. But if he wants me, he will have to come and get me?" A hankali naga damuwar fuskarta tana washewa, farin ciki yana replacing, ta karaso gurina da sauri ta rungume ni tace "thank you my daughter".
Afuwan jiya kun jini shiru, abubuwa ne suka dan sha kaina amma lafiya lau nake Alhamdulillah, nagode da kulawarku sosai. I feel loved.
MAIMOON
By
Maman Maama
Table of Contents
Chapters
- 1 Episode One : The Beginning of the Beginning
- 2 Episode Two: Meet my Family
- 3 Episode Three: Loved by All
- 4 Episode Four: Moon's Sister
- 5 Episode five: The Strangers
- 6 Episode six: The Challenge
- 7 Episode Seven: The Thin Tall Man
- 8 Episode Eight: The New Imam
- 9 Episode Nine: Give Me a Chance
- 10 Episode Ten: I Don't Know
- 11 Episode Eleven : The Protector
- 12 Episode Twelve : This is Me
- 13 Episode Thirteen : This is Me 2
- 14 Episode Fourteen : The Limit
- 15 Episode fifteen: blood is Thicker than Water.
- 16 Episode Sixteen : The Letter
- 17 Episode seventeen: Reply
- 18 Episode eighteen: what's Next?
- 19 Episode Nineteen: The Goodbye
- 20 Episode Twenty: The New Job
- 21 Episode Twenty one: Amira
- 22 Episode Twenty Two: Efisowa
- 23 Episode Twenty three: The Break up 💔
- 24 Episode Twenty Four: The Heartbreak 💔
- 25 Episode Twenty five: The Eclipse
- 26 Episode Twenty Six: A Step Further Away
- 27 Episode Twenty Eight : University of Oxford
- 28 Episode Twenty Nine: The Message
- 29 Episode Thirty : The Final Blow
- 30 Episode Thirty One: Let it go
- 31 Episode Thirty Two : Munnir
- 32 Episode Thirty Two : Mahdi
- 33 Episode Thirty Three: Zayed
- 34 Episode Thirty Four : Back to Square One
- 35 Episode Thirty Five : When Destiny Calls.
- 36 EpisodeThirtySix: Interesting
- 37 Episode Thirty Seven : The Dinner
- 38 Episode Thirty Eight : The Shadow
- 39 Episode Thirty Nine : The Shadow 2
- 40 Episode Forty :TheShadow 3
- 41 Episode Forty One : Born for This.
- 42 Episode Forty Two : Born for This
- 43 Episode Forty Three: America
- 44 Episode forty four : America 2
- 45 Episode Forty Five : The Rush
- 46 Episode Forty Six : The Repentance
- 47 Episode Forty Seven : Amir
- 48 Episode Forty Eight : Awkward
- 49 Episode Forty Nine : Ya Habeeb
- 50 Episode Fifty : Munir 2
- 51 Episode Fifty one : Mommy
- 52 Episode Fifty Two : The Journey
- 53 Episode Fifty Three : Daddy
- 54 Episode Fifty Four : Her Father's Daughter
- 55 Episode fifty five : Her Father's Daughter 2
- 56 Episode Fifty Six : What You Sow
- 57 Episode Fifty Seven : What You Sow 2
- 58 Episode Fifty Eight : I Missed You
- 59 Episode Fifty Eight : For You, Only You
- 60 Episode Sixty : The Prince
- 61 Episode Sixty One : Save the Date
- 62 Episode Sixty Two : The Manager
- 63 Episode Sixty Three : Amira 3
- 64 Episode Sixty Four : The Past and the Future
- 65 Episode Sixty Four : The Visitors
- 66 Episode Sixty Six : The Wedding
- 67 Episode Sixty Seven : The Wedding 2
- 68 Episode Sixty Eight : The Wedding Night
- 69 Episode Sixty Nine: The Wedding Night 2
- 70 Episode Seventy : The Wedding Night 3
- 71 Episode Seventy One : The Honeymoon
- 72 Episode Seventy Two : My Everything
- 73 Episode Seventy Three : His Father's Son
- 74 Episode Seventy Four : The Cook
- 75 Episode Seventy Five : The Emir
- 76 Episode Seventy Six : The Visitors
- 77 Episode Seventy Seven : Amina
- 78 Episode Seventy Eight : The Storm
- 79 Episode Seventy Nine : The Lightening and The Thunder
- 80 Episode Eighty : The Skeleton in The Closet
- 81 Episode Eighty one : The Skeleton in the Closet 2
- 82 Episode Eighty Two : The Light
- 83 Episode Eighty Three : The News
- 84 Episode Eighty Four : Little Love
- 85 Episode Eighty Five : Ibrahim
- 86 Episode Eighty Six : The Phone Call
- 87 Episode Eighty Seven : Riyadh
- 88 Episode Eighty eight :Khairat
- 89 Episode Eighty Nine : Khairat 2
- 90 Episode Ninety : His Mother's Son
- 91 Episode Ninety One : His Mother's Son 2
- 92 Episode Ninety Two and Three : Maldives 1 and 2
- 93 Episode Ninety Four : RIP
- 94 Episode Ninety Five : The Light
- 95 Episode Ninety Six : The New Bride
- 96 Episode Ninety Seven : The Real Prince
- 97 Episode Ninety Eight: My Baby
- 98 Episode Ninety Nine : New Little Love
- 99 Episode Hundred : Not The End.