Chapter 72
Episode Seventy Two : My Everything
A hankali na bude ido na ina ji a jiki na kamar assuba tayi ko kuma ma ta wuce. Dakin naga da duhu kamar cikin dare amma jikina yana bani assuba ce. Abinda ya faru da daddare ne ya fara dawo min a raina, sai a lokacin na lura cewa a jikin mutun nake a kwance. Wata muguwar kunya naji ta kamani kamar in tsaga gadon in shige cikinsa, gani nake kamar a mafarki amma kuma nasan ba mafarkin bane. Na daga jikina a hankali da niyyar sauka daga jikinsa, wata 'yar karamar kara na saki na koma na kwanta, gaba daya kafafuwana sunyi tsami, jikina gaba daya ciwo yake yi, na sake gwada kokarin tashi amma shima sai wani karin ciwon ma kamar dadamin ake yi. Na koma na kwanta ina kwalla silently. Motsin Sultan naji alamar ya farka amma na kasa dago kaina saboda bana jin zan iya hada ido dashi yanzu, ya sa hannu a hankali yana kokarin dago fuskata amma naki yarda, ya rabu dani yace "menene kuma? Sai kin kara wa kanki wani ciwon da kukan nan ko?" Banbashi amsa ba naci gaba da kukana, kokarin daga ni daga jikinsa ya fara yi, ai kuwa na saka masa kara, ya cika ni yace "ciwon ne dai?" Na gyada kaina, ya fara shafa bayana a hankali yana noticing temperature dina data fara hawa, yace "am sorry love, bara muyi sallah sai muga ya za'ayi da ciwon nan" cikin kuka nace "ni ka kaini gida gurin Mommy" da sauri yace "what? So kike Mommy ta tsire ni a kasuwa? In na kaiki gida a haka ai kamar na nuna am not responsible. Ki bari inyi sallah sai in duba ciwon in gani, in naga yana bukatar doctor da akwai doctor din gidan nan sai inyi masa magana ya samo mana gynecologist mace sai tazo ta dubaki" na makale kafada, yayi ajjiyar zuciya yace "OK, to ke ki rubutamin magungunan da kike ganin zasu yi miki amfani sai inje in siyo miki" na sake makale kafada, yace "to fada min me kike so, banda zuwa gida" nace "ni dai ka kira min Hafsat" yace "kinsan dai Hafsat tayi fushi ko na kirata ba zata dauka ba" nace "ni ka bani wayata, in na kira ta zata dauka" yace "to dagani in dauko miki wayar" na sake makale kafada, yayi 'yar dariya yace "wannan dai ba ciwon bane kadai har da shagwaba ko?" Nayi shiru bance komai ba yace "bara inyi maganin shagwabar" juyi daya yayi ya mayar dani kasa, na bude baki zanyi kara ya rufe min bakin da nasa, sai da ya tsotse yawun baccin tas sannan ya sakeni, still yana kaina amma ya rage nauyin sa da hannayensa, nace "banyi brush ba fa" yace "nima haka" daga haka ya mike ya shiga toilet, ya fito da alwala, sai da yayi sallah sannan ya dawo inda still nake kwance ba tare daya ce min komai ba ya dauke ni ya kai toilet, da gaske ciwon nake ji ba wai shagwaba bace, dan kafafuwana jinsu nake kamar lagwani, da nayi alwalar ya dawo dani daki ya sakamin doguwar riga ta da hijab dina ya zaunar dani akan sallaya nayi sallah, ina idarwa ya shigo da tea a hannunsa ya zauna ya fara bani, naki sha sai da yace min inna shanye zai kira Hafsat, na sha kamar rabi nace na koshi, kan gado ya sake mayar dani ya lullubeni. Ya dauko min wayata ya dawo kusa dani ya kwanta yace "to kira Hafsan, tunda kince ita kike so" na duba time naga 6:30, na kira number din Hafsat, ringing biyu ta dauka, sai kuma na rasa me zance mata, tace "I know u will call me dama, check your messages, na bar miki sako" daga nan ta kashe. Sultan yace "me tace?" Na gaya masa, ina duba wa kuwa naga message daga Hafsat 'you once asked me what it feels like, yanzu nasan kin sani. Was Sultan gentle? If he isn't please knock his big head for me. I left something a bedside drawer dinki and I also left you farfesu a cikin fridge, for you alone, kar ki bashi ko loma daya' ina gama karantawa na tattaro dan sauran karfin daya rage min na rankwashi Sultan aka, ya rike gurin yace "ouch, me nayi kuma?" na nuna masa message din Hafsat nace "sako ne inji Hafsat" ya shagwabe fuska "was I not gentle?" Nace "you weren't" yace "to ai ba laifi na bane ni kadai, why do you have to be so damn good. I always thought it will be good but did not expect it to be this good" nace "so it is my fault kenan ko?" Yayi dariya bai amsa ba ya mike yace "let me get sakon nata". Few minutes later ya dawo da leda a hannunsa, ya zauna a gaban gadon ya bude, magunguna ne a ciki, mostly pain relievers ne, sai wani farin gari a leda da instruction din a ruwa za'a zuba a shiga ciki, sai kuma wani paste shi kuma na shafawa ne. Yana gama dubawa ya dauki na ruwan ya tafi dashi toilet, nasan ruwa zai hada min dan haka duk na tsorata, nasan zafin dana ji a ruwan jiya, yana dawowa na saka masa kukan ni bana son shiga ruwa, da kyar muka je toilet din, amma shiga ruwan ya gagara, a karshe dai sai tare muka shiga, kayan kuwa sai a cikin ruwan aka cire su. Bansan me yake faruwa ba sai da na gama jin zafin ruwan sannan na lura da yadda muke, ai kuwa nace sai ya fita amma yaki, a dole muka gama zaman cikin ruwan tare muka fito, muna fito wa na rufe ido na wai bazan kalle shi ba tunda babu kaya a jikinsa, yayi ta tsokanata amma still naki bude idon, muna dawowa daki ya dauko na shafawar wai sai ya shafa min, na fara kokawa ya saka hannu daya ya rike ni kuma ya shafa min din. Na kwanta ina kumbure2 ya fita, har na fara bacci sai gashi ya dawo da bowl a hannunsa da kuma kwalin fresh milk, ya tashe ni zaune yace sai naci, ina ta shagwabar ni bacci nake ji amma haka ya matsamin sai da muka ci tare, muna gamawa ya dauko min magungunan wajan Hafsat ya bani nasha sannan na koma na kwanta, ban jima da kwanciya ba naji shi ya kashe fitilar dakin ya hawo gadon shima, ya jawo ni jikinsa kamar zai tsaga kirjinsa ya sakani ciki, nayi 'yar kara, yayi dariya yace "ya jikin?" Nace "da sauki" yace "Maimunatu" nayi mamaki saboda yau ne rana ta farko daya kira ni da wannan sunan, nace "Na'am" yace "thank you, I really mean thank you, for yesterday, for everything, bansan me zance miki, bansan sunan da zan kira ki dashi ba, I will continue calling you my love, saboda you are the love of my life, amma ki sani ba wannan ne kadai matsayinki ba, you are my everything, I was nothing kafin in hadu dake kuma I will be nothing without you" bance komai ba amma ina jin dadin maganganunsa har cikin raina, ina kara jin sansa yana shiga har cikin bargo na, he is mine, and I am his, forever and ever.
Ni na sake riga shi tashi wannan karon ma, na farka naga still dakin duhu, wato shi wannan dakin na sultan koda yaushe a dare yake kenan, sai mutum yayi ta bacci bai san me duniya take ciki ba. Na tashi zaune, ga mamaki na sai naji babu ciwon sam, sai dan ciwon jiki kadan, na kunna bedside lamp, na duba agogon wayata, 1:15, oh my God, nasan mutane sunyi ta zuwa suna ganin gidan a rufe, na juya na kalli sultan da yake bacci a gefe na, sai naji na kasa tashin sa, he looks so handsome, hasken lamp din yana reflecting a golden skin dinsa, na koma na kwanta a side dina ina kallonsa, I have never see him this peaceful before, na tuna maganar hausawa da ake cewa wai angwaye suna kwallin goshi, to ko dai da gaske ne? Na kai dubana kan kirjinsa, Ya dan yaye bargon ya bar kirjinsa a waje, gashin da yake kwance a kirjinsa yafi na fuskarsa kyau da sheki kamar yadda fatar gurin tafi da fuskarsa haske, a hankali na gada hannuna, na sake kallon fuskarsa naga baccin yake yi, I couldn't stop myself, a hankali na sauke hannuna akan gashin na fara shafawa ina jin laushinsa a hannuna, I was so consumed in doing what I was doing kawai naji maganarsa "hey woman, you already had me, if you want more all you have to do is ask" nayi sauri na dauke hannuna na rufe fuskata dashi, ya mirgino ya hade fuskarmu guri daya yace murya can kasa "do you want more?" Na girgiza kaina da sauri, yace "but I do want more" nace "ni fa tashinka zanyi, lokacin sallar azahar ya kusa, kuma kaga ko bude kofa bamuyi ba kar mutane su yi ta zuwa gida a rufe" yace "so what? Duk wanda bai zo jiya ba yayi wa kansa, an gama ganin gidan amarya. Let's not open the door forever, let's not get out of this bed forever" nayi dariya na dan dake shi a kafada nayi kokarin tashi ya sake dawo dani baya nace "Sultan, ka bar ni inje dakina in saka kaya, inje in samar mana abinda za muci kuma, we can't stay here forever" ya saka fuskarsa a wuyana yace "sai kace girkin ta iya da gaske. Za'a kawo abinci, za'ake kawo wa daga cikin gida har nan da seven days, kafin nan sai mu nemi cook. Yau bana son ko tashi inga kinyi, I want to treat you like the queen you are, komai kike so ni zan yi miki, duk abinda kike so shi za'ayi".
Da kyar na samu ya dauko min kayana a dakina na saka, daga nan ya tafi masallachi sallah ni kuma nayi sallah ta anan, miracle maganin Hafsat yayi min amfani sosai dan bama na tuna wa da wani ciwo sai in na yi motsi da sauri. Man sa na shafa na saka tunarensa, banyi kwalliya ba, na zauna akan kujera ina duba messages din wayata, yawanci sakonnin taya murna ne daga mutanen da basu samu damar zuwa bikin ba, anan naga sakon mahdi, yace min ya cigaba da karatunsa bai dawo Nigeria ba, na rufe WhatsApp kenan naga sakon Amira ya shigo, na koma na bude "Moon dan Allah ina so muyi magana, can I come to your house please?" Ban yi mata reply ba Sultan ya shigo, tray din abinci ne a hannunsa amma idonsa yana kaina, na karaso na karba na ajiye, bai ce komai ba ya sake fita ya dawo da still da wani abincin, na kuma karba nace "Sultan wannan abincin ya zamuyi dashi?" Yace "I don't know which one you will like, shi yasa na debo kowanne. Sun kawo abincin yana dining. Da akwai Baba Gaji Yaya ta turo ta gurinki, I told her ba zaki samu ganinta yanzu ba amma ta zauna duk wanda yazo ta raka shi yaga gida amma ta gaya musu amarya is not available" nace "ayyah, da ka barni naje baka san menene sakon Yayan ba" yace "ba zai wuce zancen masu aiki ba" zan kuma yin magana ya jawo nikan cinyarsa yace "me zaki ci?" Mun ci abincin sosai daga ni har shi duk ashe yunwa muke ji, sam ya hanai fita da kayan shi ya dauka ya fita dasu, kafin ya dawo na gyara gurin na kara freshner a dakin, yazo ya jani muka koma gado yace "ya ciwon? In duba in gani? Nayi sauri na hade kafafuwana nace "bai warke ba ai" yace "OK, kin san me za'ayi masa ya warke da wuri? Wani za'a kuma yi, nan da nan zakiga ya warke" na fara matsawa baya ina zaro ido "please Sultan, wallahi mutuwa zanyi, dan Allah karka tabani" dariya yayi sosai yace "harda mutuwa? Am just kidding, amma babu wani mutuwa da zaki yi, an gama mai zafin ai" na sake matsawa baya, ya jawo ni yace "trust me bazan miki wannan ba, I just want to feel your warmth and smell your scent" na dan saki jikina kadan amma kuma ba abinda ya fada kadai yake yi ba, sai da naga yana neman wuce gona da iri sannan na saka masa kuka, ya sakeni ya gyara min rigata sannan ya gyara min kwanciya, har na dauka yayi bacci sai naji yace "tell me about him" duk da bai fada ba nasan wa yake nufi, kuma nasan dama dole zamuyi maganar amma sai naji bakina yayi min nauyi na kasa magana, jin nayi shiru ya sake magana "I just want to know, shi kadai ne ko kuma akwai wani daban da ban sani ba" na girgiza kaina nace "shi kadai ne, sunan sa Ibrahim, he was a copper a sec sch din mu when I was in SS2, I was 14 years then" daga nan na bashi labarin duk rayuwar mu da Ibrahim him, da yadda muka rabu, da irin zaman jiransa dana zauna yi kafin haduwar mu shi (sultan), na bashi labarin har ranar da muka kuma haduwa da Ibrahim da labarin daya bani na rayuwar da yayi bayan rabuwar mu da irin abubuwan da Amira ta kulla mana, ban boye masa komai ba har wayar da mukayi dashi a phone din Amina da duk bayanin dana yi masa ya kuma nuna ya gamsu, na karasa da cewa "bansan me yasa ya aikata abinda ya aikata ranar nan ba. Am sorry na boye maka duk wanan maganar, at first I never thought zamu sake haduwa dan haka nake ganin there is no point in telling you, daga baya kuma bayan mun hadu dashi na kasa gaya maka ne saboda bana son in bata maka rai". Har na gama maganar baice komai ba,har na fara tunanin ko yayi bacci, na kalle shi sai naga yana kallon ceiling, can yace "promise me you will never see or talk to him again, my heart cannot take it" na dago kaina ina kallon cikin idonsa nace "I promise" yayi murmushi yace "thank you" sannan ya jawo fuskata ya hade bakin mu.
Table of Contents
Chapters
- 1 Episode One : The Beginning of the Beginning
- 2 Episode Two: Meet my Family
- 3 Episode Three: Loved by All
- 4 Episode Four: Moon's Sister
- 5 Episode five: The Strangers
- 6 Episode six: The Challenge
- 7 Episode Seven: The Thin Tall Man
- 8 Episode Eight: The New Imam
- 9 Episode Nine: Give Me a Chance
- 10 Episode Ten: I Don't Know
- 11 Episode Eleven : The Protector
- 12 Episode Twelve : This is Me
- 13 Episode Thirteen : This is Me 2
- 14 Episode Fourteen : The Limit
- 15 Episode fifteen: blood is Thicker than Water.
- 16 Episode Sixteen : The Letter
- 17 Episode seventeen: Reply
- 18 Episode eighteen: what's Next?
- 19 Episode Nineteen: The Goodbye
- 20 Episode Twenty: The New Job
- 21 Episode Twenty one: Amira
- 22 Episode Twenty Two: Efisowa
- 23 Episode Twenty three: The Break up 💔
- 24 Episode Twenty Four: The Heartbreak 💔
- 25 Episode Twenty five: The Eclipse
- 26 Episode Twenty Six: A Step Further Away
- 27 Episode Twenty Eight : University of Oxford
- 28 Episode Twenty Nine: The Message
- 29 Episode Thirty : The Final Blow
- 30 Episode Thirty One: Let it go
- 31 Episode Thirty Two : Munnir
- 32 Episode Thirty Two : Mahdi
- 33 Episode Thirty Three: Zayed
- 34 Episode Thirty Four : Back to Square One
- 35 Episode Thirty Five : When Destiny Calls.
- 36 EpisodeThirtySix: Interesting
- 37 Episode Thirty Seven : The Dinner
- 38 Episode Thirty Eight : The Shadow
- 39 Episode Thirty Nine : The Shadow 2
- 40 Episode Forty :TheShadow 3
- 41 Episode Forty One : Born for This.
- 42 Episode Forty Two : Born for This
- 43 Episode Forty Three: America
- 44 Episode forty four : America 2
- 45 Episode Forty Five : The Rush
- 46 Episode Forty Six : The Repentance
- 47 Episode Forty Seven : Amir
- 48 Episode Forty Eight : Awkward
- 49 Episode Forty Nine : Ya Habeeb
- 50 Episode Fifty : Munir 2
- 51 Episode Fifty one : Mommy
- 52 Episode Fifty Two : The Journey
- 53 Episode Fifty Three : Daddy
- 54 Episode Fifty Four : Her Father's Daughter
- 55 Episode fifty five : Her Father's Daughter 2
- 56 Episode Fifty Six : What You Sow
- 57 Episode Fifty Seven : What You Sow 2
- 58 Episode Fifty Eight : I Missed You
- 59 Episode Fifty Eight : For You, Only You
- 60 Episode Sixty : The Prince
- 61 Episode Sixty One : Save the Date
- 62 Episode Sixty Two : The Manager
- 63 Episode Sixty Three : Amira 3
- 64 Episode Sixty Four : The Past and the Future
- 65 Episode Sixty Four : The Visitors
- 66 Episode Sixty Six : The Wedding
- 67 Episode Sixty Seven : The Wedding 2
- 68 Episode Sixty Eight : The Wedding Night
- 69 Episode Sixty Nine: The Wedding Night 2
- 70 Episode Seventy : The Wedding Night 3
- 71 Episode Seventy One : The Honeymoon
- 72 Episode Seventy Two : My Everything
- 73 Episode Seventy Three : His Father's Son
- 74 Episode Seventy Four : The Cook
- 75 Episode Seventy Five : The Emir
- 76 Episode Seventy Six : The Visitors
- 77 Episode Seventy Seven : Amina
- 78 Episode Seventy Eight : The Storm
- 79 Episode Seventy Nine : The Lightening and The Thunder
- 80 Episode Eighty : The Skeleton in The Closet
- 81 Episode Eighty one : The Skeleton in the Closet 2
- 82 Episode Eighty Two : The Light
- 83 Episode Eighty Three : The News
- 84 Episode Eighty Four : Little Love
- 85 Episode Eighty Five : Ibrahim
- 86 Episode Eighty Six : The Phone Call
- 87 Episode Eighty Seven : Riyadh
- 88 Episode Eighty eight :Khairat
- 89 Episode Eighty Nine : Khairat 2
- 90 Episode Ninety : His Mother's Son
- 91 Episode Ninety One : His Mother's Son 2
- 92 Episode Ninety Two and Three : Maldives 1 and 2
- 93 Episode Ninety Four : RIP
- 94 Episode Ninety Five : The Light
- 95 Episode Ninety Six : The New Bride
- 96 Episode Ninety Seven : The Real Prince
- 97 Episode Ninety Eight: My Baby
- 98 Episode Ninety Nine : New Little Love
- 99 Episode Hundred : Not The End.