Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 76

Episode Seventy Six : The Visitors

Maimoon Book 1 Complete Hausa Novel 2,217 words 0 views Progress saved
Download Book

Ina dan bubbuga bayansa kadan nace "Nothing Sultan, You did nothing" yace "me yasa ya tsane ni to? Me yasa basu zubar da cikina ba tunda sun san basa sona?" Nace "Suna sonka Sultan, kawai dai basa nuna maka ne, amma deep down suna sonka sosai, maybe more than yadda nake son ka ma" ya sakeni yana kallon fuskata yace "don't say that, in kina son kwantar min da hankali na say something else amma ba wannan ba, cos nasan basa sona, tun kafin in san menene so nasan basa sona. They hate me and I don't know why, wannan shi yafi komai bata min rai, why do they hate me so?" Bance masa komai ba saboda bansan me zance masa din ba. Ya zauna akan kujera ya zaunar dani a kusa dashi yace "tunda ya fara wannan maganar ba zai bar ta ba har sai yaga ya raba mu, I know him, zan shirya mana barin kasar nan, shine kadai hanyar da zamu bi mu tsira daga gare shi" na girgiza kaina nace "Sultan barin kasa ba shine mafita ba, iyayen mu ne, we are nothing without them and we can't runaway from them. Mafita shine mu zauna muyi facing din su mu yi duk abinda suka ce mu bar duk abinda suka hana mu. In mukayi haka to Takawa will have no reason da zai sa ya takura mana ko yayi tunanin raba mu. Amma in dai muka ce zamuyi retaliating ko kuma zamu bar kasar to anan ne zamu bashi damar yi mana duk abinda yake so" ya girgiza kansa yace "baki san halinsa ba, he will not stop, baya bukatar reasons, in dai yana son yayi min abu to tabbas zai yi min ne ko nayi laifi ko banyi laifi ba, ballantana yanzu yana ganin yana da dalili a hannunsa. Yanzu nasan Daddy zai kira ya nuna masa picture dinki da bindiga ya kuma gaya masa cewa nace nine na baki. The next thing you will know Daddy zai zo yace ki fito ku tafi an gama auren kenan" nace "then you don't really know Daddy. Daddy ba zai taba yanke hukunci ba tare da bincike ba, ni kuma in ya tambaye ni zan san yadda nayi nayi masa bayani yadda zai gane, kuma nasan zai gane din ma. Yanzu abinda nake so muyi magana akai shine; wa kake tunanin ya kaiwa Takawa pictures din nan?" Wani murmushin takaici yayi yace "tunani? Am sure it is Abbas, ba yau ya fara ba ai, but this will be the last time da zai shiga harkata, dan wallahi sai jikin sa ya gaya masa. He shouldn't have touch you" yadda ransa yake a bace na tabbatar idan ya kama Abbas sai dai wani bashi ba. Na kama hannunsa ina shafa gashin hannun a hankali nace "wannan shine exactly abinda Abbas yake so kayi, so yake ka taba shi yadda Takawa zai sake samun karin dalilin raba ka dani. He got your weak point, me. Yasan cewa you will react exactly like this, yasan cewa in Takawa yayi maka magana zakace zaka dauke ni mubar musu kasar, yasan kuma Takawa zai ce ba zaka tafi dani ba. Ya lissafa cewa duk abinda ya faru shine mai riba, in ka tafi kabar kasar dani shikenan he got rid if you, in kuma bamu tafi ba zaku yi ta rigima da Takawa shima nan shine da riba" He seems calmer now, yana sauraro na sosai, yayi ajjiyar zuciya yace "yanzu mai kike ganin zamuyi?" Nace "kar mu bawa Abbas abinda yake nema. Kar muce zamu je ko'ina. Kuma kar kace zaka dauki fansa akan Abbas, just let him be, duk abinda zai yi kar ka kula shi. Sai kuma muyi taka tsantsan, kar mu yarda muyi wani abinda muka sam Takawa baya so. You already got your job, ka cigaba da abin ka, duk sanda kake bukatar fatherly care ko wata shawara, go to Daddy. The last and the most important thing shine mu dage da addu'ah. I believe Allah yana tare damu kuma yana ganin duk abinda yake faruwa kuma ba zai taba barin mu ba as long as muma bamu barsa ba. Yadda ba zamu bar Allah ba kuma shine ta hanyar ibada da addu'a. Kuma ka saka a ranka cewa I will never leave you, Ever. Duk ma wani abinda zai faru, we will face it together" na dago hannunsa na kai baki na nayi kissing, nace a hankali "I love you" ga mamaki na sai naga yayi murmushi, genuine murmushi, yace "I love you too".
A ranar Asma'u tazo, da gudu naje na rungume ta ina murna, itama murnar take yi, tace " me sunan daada in dai girki kike so ki koya to ki tabbatar kin samu, dan bazan bar gidan nan ba sai na tabbatar babu wani abincin da baki iya ba" na nuna mata kitchen ta shiga tayi surveying ta fito ta fara lissafamin abubuwan da babu ina rubutawa, muna gama wa na bata kudi isassu nace taje ta siyo, shatar taxi ta dauko daga kasuwar saboda yawan kayan da ta siyo, ni dai ina ta mamakin wai duk wadannan kayan a ciki za'a zuba su. A ranar tare mukayi lunch da ita da sauran yara na, banyi aikin ba ina dai zaune ina kallon su suna tayi amma asma'u tana yi min bayanin komai da suke yi da dalilin da yasa suke yin komai. Har aka gama aka shirya table, for the first time yau anyi abinci a gidana, duk da cewa bani nayi ba amma naji dadi, nayi feeling cewa nayi gaining wani abu. Sam na manta ma da Takawa da Abbas and their problems. Sultan ma naga ya saki ransa. Da yamma muka fita muka tafi orphanage gurin surprise party din mu, a hanya muka tsara muka saya musu gifts, kowa sai da muka sai masa toy, mata baby dolls maza bindiga, yan kananan kuma mota, shigar mu cikin yaran ya kara saka wa muka manta da komai. Sunyi organizing abin sosai, harda drama da sport suka yi mana, aka kawo mana cake muka yanka sannan na zauna na yayyanka na bisu na bawa kowa a baki. Nan take naji yaran sun kwanta min a raina, na sake sosai a cikin su mukayi ta wasa, sultan har mamaki na yake yi saboda ganin bamu da yara a gidan mu. Bamu dawo gida ba sai bayan magrib, muna zuwa dama a gajiye muke, dan da kyar muka ci abinci, na fara shirin wanka kenan aka zo aka ce min wai nayi ba'ki, na kalli agogo naga 8:30, nace "wadanne irin ba'ki ne kuma yanzu?" Yarinyar tace min "Hajiya ce, tare da wadansu mata" wata irin faduwa naji gabana yayi, a daki na nake, sultan ya tafi nasa. Nace yarinyar ta shigo dasu palo na tace musu ina zuwa, fasa wankan nayi sauri na zura doguwar bakar riga nayi rolling veil na fesa turare na fito. Su uku ne na tarar a zaune suna karewa palon kallo, Hajiya, sai wata mata kusan sa'arta sai kuma khulsum. Na tattaro murmushi na shimfida a fuskata na karasa gurin su, na tarar already an kawo musu drinks da snacks da fruits, na durkusa na fara gaishe da Hajiya sannan na gaishe da daya matar dana lura suna kama, suka amsa min duk da fara'a a fuskarsu. Na juya na kalli khulsum nace "nayi fushi, sai yau zaki zo gidan nan" ba tare data mayar min murmushina ba tace "abubuwa ne suka yi min yawa. Kuma yanzu ba gashi nazo ba" Hajiya tace "dazu kuma nace ki tsaya sai da na fito na tarar ba kya nan" na sunkuyar da kaina bance komai ba, ta cigaba "ko da yake nasan ba laifin ki bane, yaron nawa ne sai a hankali, amma ace kwana nawa da bikin nan bai kai ki kin gaishe mu ba, sai da Takawa ya kira ku da kansa, sannan kuma ace kunje din ma bamu samu mun gaisa ba. Shi yasa na taho yanzu da kaina ni inzo mu gaisa din, in ga dakinki kuma in saka muku albarka" daya matar dana fahimci kamar 'yar uwartace tace "to yanzu 'ya'yan zamani ne sai a hankali, dan da ka haifa ma yaya ka kare dashi ballantana dan da yake ganin ba kai ka haife shi ba. Ke dai kawai Allah ya saka miki da alkhairi na abinda kike yi masa, dan ko uwar data haife shi iyakacin abinda zata yi masa kenan" Hajiya tace "Ameen dai" ta juyo gurina "ina yake ne? Kar dai kice daga gama biki har ya cigaba da yawon daren nasa? Wannan yaro na rasa yadda zanyi in raba shi da wannan yawon daren. Kullum ya fita hankali na a tashe yake saboda bansan me yake aikatawa a wajen ba" ban katse taba sai da na bari takai aya sannan nace "yana daki" suka kalle ni sannan suka kalli junansu sannan Hajiya tace "to kirawo shi mu gaisa" na tashi na tafi part din sultan. Ya fito daga wanka yana shafa mai, na shiga da sallama, ya juyo yana kallona, ya kalli kayan jiki na yace "why are you all dress up sai kace fita zakiyi" nace "we have guests" ya kalli agogo yace "su waye?" Nace "Hajiya" take yanayin fuskarsa ya chanza, ya ajiye tiraren hannunsa yace "me suka zo yi?" Na karaso na dauki tiraren ina fesa masa nace "zuwa sukayi mu gaisa suga gidan mu si saka mana albarka" yace "bull shit" na shiga closet na dauko masa wata doguwar riga na taimaka masa ya saka, sannan nace "please sultan, don't give them abinda sukazo nema. Kaje kawai ka gaishe su sai kayi dawowarka daki". Da kyar na samu ya biyo ni hannunsa cikin nawa, muna shiga palon duk suka juyo suna kallon mu, nima kallon nasu nake daya bayan daya ina studying din kowannen su. Khulsum kallo daya tayi mana ta dauke kai, she obviously still loves sultan and is jealous, matar da suke tare da hajiya ta danyi blushing alamar taji kunyar ganin hannuna ha sultan ya rike, Hajiya kuma gaba daya hakoranta a waje tana murmushi, tace "yaron kirki, da fatan bamu tashe ka daga bacci ba" yayi kamar bazai amsa ba sai kuma yace "ban kwanta ba ai dama" ya zauna a kasa na zauna a gefensa, yace "barkan ku da yamma" suka amsa su biyi a tare, bai kalli inda khulsun take ba, Hajiya ta fara masa jawabin abinda ya kawo su, ni kuma nayi using wannan opportunity din na fara studying dinta, she looks so calm and happy on the outside, duk wanda ya ganta zai dauka duniya babu wanda take so sama da sultan, but inside she is full with hatred, she is boiling witj bakin cikin ganin mu tare da sultan, a lokacin na kara fahimtar komai. Hajiya may not be responsible for rabuwar iyayen sultan, amma ta tsane shi, tsana ta sosai, she may not be dalilin daya raba sultan da mahaifinsa in da first place but tana da hannu wajan kara huruwar wutar al'amarin. She succeeded so far, amma yanzu na shigo cikin rayiwar sultan kuma sam bata jin dadin changes din da sultan yake samu, tana kallona a matsayin wacce tazo zata tarwatsa mata plans dinta. Tasan ba zata samu nasara akan sultan ba sai ta raba shi dani, and she plans on doing that. Sai kawai na samu kaina ina murmushi, nayi studying psychology ne saboda haushin yaudarar da nake tunanin Ibrahim yayi min, amma sai gashi ilimin nawa ba akan Ibrahim yake min amfani ba akan Sultan ne. Allah mai tsara lamarin sa yadda yaso kuma a lokacin da yaso. Na dawo da hankalina kan maganar da take cewa naji har yanzu fada take yi mana akan mu zauna lafiya mu bawa marada kunya. Tana gamaws daya matar itama tayi nata, daga ni har sultan babu wanda yace musu komai. Suna gamawa sultan ya mike yayi musu sallama ya koma part dinsa. Bayan ya tafi matar da suka zo tare ta kalli khulsum tace "me yasa baki gaishe shi ba? Ba mun gaya miki cewa maganar nan ta wuce ba? Ya kamata ki manta da komai ku cigaba da zumuncin ku" gaba na ne ya fadi saboda nasan wata maganar suke son fada min kuma daga dukkan alama ba zata yi min dadi ba, ban dago kaina ba ballantana in nemi ba'asin me take nufi da maganar ta. Jin bance komai ba sai ta cigaba da cewa "Maimunatu gwara kiji daga bakin mu kar wani ya gaya miki kiga kamar mun boye miki. Tun khulsum tana yarinya karama sultan yake son ta, babu yadda baiyi ba abashi aurenta iyayen mu suka ki saboda a ganin su babu uban da zai yarda ya hada 'yarshi aure da yaro irin sultan. Hajiya babu yadda batayi ba akan iyayen mu su yarda da auren amma suka ki. Bakin cikin abin ne ya saka shi ya fara shaye shaye. Daga baya da yaga da gaske ake ba za'a aura masa ita ba shine yayi kokarin bata mata rayiwarta, Allah ya taimake ta bai ci nasara ba" kallonta kawai nake yi ina tunanin how can someone, mai shekaru kamarta, lie like that? Murmushi na tattaro na dora akan fuskata nace "na sani, ya gaya min komai daya faru tsakanin su, and I still love him".
N

Table of Contents

Chapters

99 chapters
  1. 1 Episode One : The Beginning of the Beginning
  2. 2 Episode Two: Meet my Family
  3. 3 Episode Three: Loved by All
  4. 4 Episode Four: Moon's Sister
  5. 5 Episode five: The Strangers
  6. 6 Episode six: The Challenge
  7. 7 Episode Seven: The Thin Tall Man
  8. 8 Episode Eight: The New Imam
  9. 9 Episode Nine: Give Me a Chance
  10. 10 Episode Ten: I Don't Know
  11. 11 Episode Eleven : The Protector
  12. 12 Episode Twelve : This is Me
  13. 13 Episode Thirteen : This is Me 2
  14. 14 Episode Fourteen : The Limit
  15. 15 Episode fifteen: blood is Thicker than Water.
  16. 16 Episode Sixteen : The Letter
  17. 17 Episode seventeen: Reply
  18. 18 Episode eighteen: what's Next?
  19. 19 Episode Nineteen: The Goodbye
  20. 20 Episode Twenty: The New Job
  21. 21 Episode Twenty one: Amira
  22. 22 Episode Twenty Two: Efisowa
  23. 23 Episode Twenty three: The Break up 💔
  24. 24 Episode Twenty Four: The Heartbreak 💔
  25. 25 Episode Twenty five: The Eclipse
  26. 26 Episode Twenty Six: A Step Further Away
  27. 27 Episode Twenty Eight : University of Oxford
  28. 28 Episode Twenty Nine: The Message
  29. 29 Episode Thirty : The Final Blow
  30. 30 Episode Thirty One: Let it go
  31. 31 Episode Thirty Two : Munnir
  32. 32 Episode Thirty Two : Mahdi
  33. 33 Episode Thirty Three: Zayed
  34. 34 Episode Thirty Four : Back to Square One
  35. 35 Episode Thirty Five : When Destiny Calls.
  36. 36 EpisodeThirtySix: Interesting
  37. 37 Episode Thirty Seven : The Dinner
  38. 38 Episode Thirty Eight : The Shadow
  39. 39 Episode Thirty Nine : The Shadow 2
  40. 40 Episode Forty :TheShadow 3
  41. 41 Episode Forty One : Born for This.
  42. 42 Episode Forty Two : Born for This
  43. 43 Episode Forty Three: America
  44. 44 Episode forty four : America 2
  45. 45 Episode Forty Five : The Rush
  46. 46 Episode Forty Six : The Repentance
  47. 47 Episode Forty Seven : Amir
  48. 48 Episode Forty Eight : Awkward
  49. 49 Episode Forty Nine : Ya Habeeb
  50. 50 Episode Fifty : Munir 2
  51. 51 Episode Fifty one : Mommy
  52. 52 Episode Fifty Two : The Journey
  53. 53 Episode Fifty Three : Daddy
  54. 54 Episode Fifty Four : Her Father's Daughter
  55. 55 Episode fifty five : Her Father's Daughter 2
  56. 56 Episode Fifty Six : What You Sow
  57. 57 Episode Fifty Seven : What You Sow 2
  58. 58 Episode Fifty Eight : I Missed You
  59. 59 Episode Fifty Eight : For You, Only You
  60. 60 Episode Sixty : The Prince
  61. 61 Episode Sixty One : Save the Date
  62. 62 Episode Sixty Two : The Manager
  63. 63 Episode Sixty Three : Amira 3
  64. 64 Episode Sixty Four : The Past and the Future
  65. 65 Episode Sixty Four : The Visitors
  66. 66 Episode Sixty Six : The Wedding
  67. 67 Episode Sixty Seven : The Wedding 2
  68. 68 Episode Sixty Eight : The Wedding Night
  69. 69 Episode Sixty Nine: The Wedding Night 2
  70. 70 Episode Seventy : The Wedding Night 3
  71. 71 Episode Seventy One : The Honeymoon
  72. 72 Episode Seventy Two : My Everything
  73. 73 Episode Seventy Three : His Father's Son
  74. 74 Episode Seventy Four : The Cook
  75. 75 Episode Seventy Five : The Emir
  76. 76 Episode Seventy Six : The Visitors
  77. 77 Episode Seventy Seven : Amina
  78. 78 Episode Seventy Eight : The Storm
  79. 79 Episode Seventy Nine : The Lightening and The Thunder
  80. 80 Episode Eighty : The Skeleton in The Closet
  81. 81 Episode Eighty one : The Skeleton in the Closet 2
  82. 82 Episode Eighty Two : The Light
  83. 83 Episode Eighty Three : The News
  84. 84 Episode Eighty Four : Little Love
  85. 85 Episode Eighty Five : Ibrahim
  86. 86 Episode Eighty Six : The Phone Call
  87. 87 Episode Eighty Seven : Riyadh
  88. 88 Episode Eighty eight :Khairat
  89. 89 Episode Eighty Nine : Khairat 2
  90. 90 Episode Ninety : His Mother's Son
  91. 91 Episode Ninety One : His Mother's Son 2
  92. 92 Episode Ninety Two and Three : Maldives 1 and 2
  93. 93 Episode Ninety Four : RIP
  94. 94 Episode Ninety Five : The Light
  95. 95 Episode Ninety Six : The New Bride
  96. 96 Episode Ninety Seven : The Real Prince
  97. 97 Episode Ninety Eight: My Baby
  98. 98 Episode Ninety Nine : New Little Love
  99. 99 Episode Hundred : Not The End.