Chapter 78
Episode Seventy Eight : The Storm
Bayan Wata Uku
Rayuwa tana tafiyar mana sosai cikin jin dadi. Dan ni kam a bangare na bani da problem. Su Hajiya tun ranar da suka zo na kora musu bayani basu sake dawowa ba, su fa'iza su na dan zuwa kadan kuma sam ban taba daure musu fuska ba. Amira ma ta dawo twice, mu kan danyi hira kadan amma sam ba kasa sake wa da ita kamar da, mun koma kamar strangers. Kullum kuma in tazo bata da zance sai na aure, ta gaji da zaman gida yanzu aure take so dan yanzu kullum suna cikin samun sabani da mamanta. A bangaren Sultan kuma tunda ya koma aiki ya zama busy, dan kullum sai dai akai masa lunch dinsa office, sai bayan la'asar yake dawowa, amma kuma in ya dawo din in ba dole ba baya fita ko kofar gida sai dai in zashi masjid, kullum company sa kara habaka yake yi, dan yanzu da kansa yake karbar kwangilar gine gine yana yi, na government ko kuma na private mutane. Sultan ya rike addini sosai dan har mamaki yake bani yanzu, karatun qur'ani kam kullum sai yayi safe da yamma, wani lokacin na yamman muyi tare. Ni kuma babu abinda nake yi a gida sai koyon girki, dan a yanzu Asma'u tafara bari na ina yin abincin da kaina, sai dai ta dan ci gyarana kadan, a raina nakan ce 'ashe ma abin babu wahala, kawai sa kai ne' tun daga kan main dishes, snacks, drinks babu abinda asma'u bata koya min, tace so take yi in na fara yi wa Sultan girki duk abincin da yaci idan ba nawa bane ya ji ci salam. Duk abinda kuwa na dafa ko sultan baya nan sai na ajiye masa na bashi yayi tasting, Sultan kam ko abin bai yi dadi ba cewa yake yi yayi dadi duk da nasan wani lokacin alkunya kawai yake yi min. Soyayya tsakanin mu kuwa kullum karuwa take yi, ni da na dauka da anyi na dokin aure shikenan amma ashe ba haka abin yake ba, stamina din Sultan har mamaki take bani, dole na na yawo jakar magungunan daada na cigaba da amfani dasu. Mun je gida ranar da Daddy ya dawo daga England, tunda akayi biki na sai ranar naje gida, da gudu naje na rungume Mommy, ita kam kallo na kawai take yi dan gaba daya na chanja, nayi kiba na kara chika, fata ta har wani yellow take yi saboda haske. Sau da yawa in kawayena suka zo sukan tsokane ni suce ko ciki ne dani, amma ni nasan bani da komai, dan cikin wata ukun nan ko tsallaken period ban taba yi ba. Ranar a gida Sultan ya barni na wuni. A lokacin ne Amina take bani labarin yadda suka kare da Ibrahim, naji dadi duk da dai tace min yace bayason jin labarin sultan, kawai shi fatansa in am OK shikenan, nan take min complaint cewa he is becoming a little bit touchy, nayi dariya nace "then it is going more than I expected" ta bata rai tace "ya zaki ce haka, ina gaya miki cewa yana yawan tabani kuma kice min kina murna?" Nace "yi hakuri Amina ta, abinda nake so ki gane shine, Ibrahim was born and raised in yaroba land, they are Muslims and then they are yarobas, su a gurinsu it is nothing dan saurayi ya rike hannun budurwarsa" ta harare ni tace "waye yace miki saurayi na ne? We are just friends" Nace "OK let me rephrase my statement, su a gurinsu it is nothing dan aboki ya rike hannun abokiyarsa" yadda na fadi kalmar abokiyar ya saka mukayi dariya gaba daya, nace "nasan ki fa Amina, kuma nasan tun ranar da kika fara ganin sa kika zo kina santinsa" ta tabe baki tace "lokacin ai bansan waye shi a gurinki ba" nace "he is nothing a gurina yanzu, not even my friend, but he will soon be my brother in-law" tace "in ya daina taba ni ba" nace "ai ke zaki hana shi, next time ya rike miki hannu ki bata rai ki ce kar ya kuma ba kya so, daga ranar ba zai kara ba". Sai dare Sultan yazo daukana. Kamar ba zan fito ba saboda duk su yaya Walid suna gida ana ta hira da dariya, a nan na fara matsar kwalla wai ni dan Allah sultan ya barni in kwana sai gobe na koma, ni kaina da nake fada nasan it is impossible, dan in dai zan kwana a gida to tabbas sultan zai biyo ni mu kwana tare. Mommy ce ta rakani har mota amma ita ma kamar ba zata barni in tafi ba, muna jan mota na dora hannu aka na rusa kuka wai ni ya mayar dani gidan mu. Gefen titi ya samu yayi packing sai da ya tsotse hawayen fuskar tas sannan ya dashi motar muka tafi kuma yace in dai na sake wani kukan abinda yafi haka zai yi min ba ruwansa da cewa a titi muke. Na san zai iya aikatawa dan haka nayi shiru da baki na. Muna zuwa gida sai da ya tabbatar ya mantar dani 'yan gidan mu sannan ya rabu dani.
Ranar wata Friday muna zaune palo da asma'u da baba gaji da wasu daga 'yammata na, baba gaji tana ta bamu labaran abin dariya muna ta darawa without a care in the world, ina yi amma ina kallon agogo, nasan sultan yana hanya by now, ai kuwa ba'a jima ba sai ga shi ya shigo. Yana shigowa duk suka nutsu, haka nan sultan yake da wannan kwarjinin, duk inda ya shiga sai kaga mutane suna shakkarsa ko da kuwa bai yi musu magana ba. Ya zauna a kujera, duk suka gaishe shi sannan suka fita, nayi masa sannu da zuwa, ya amsa a hankali yana jingina kansa a bayan kujerar, na tashi na dauko masa pineapple drink din dana hada dazu, na kawo na zuba masa a cup na mika masa, bai karba ba ya zauna yana kallona, nasan me yake nufi nayi murmushi na zauna a cinyarsa na dafa kafadar sa da hannu daya daya hannun kuma na dauki cup din drink din na fara bashi a baki, sai da ya shanye cup din tas sannan ya dauke kansa, na karo masa wani na sake bashi, wannan karon a hannunsa ya karba yace "let me guess, ki kika hada wannan drink din" na washe baki nayi fari da ido nace "you guess right, this drink was made by yours truly, Asma'u bata ma san nayi ba" yace "wow, wannan matar fa so kike ki fi asma'u iya girki, kuma it is like duk abinda kikayi yana da wani unique taste na musamman" naji dadi sosai nace "thank you Darling" ya juya wuyansa, kashin wuyan yayi kara alamar gajiya, nace "you are overworking yourself honey, ya kamata ka ke rage aikin nan kana hutawa fa" ya kwantar da kansa a kirjina yace "I know, shi yasa nake shirya mana tafiya zuwa Maldives, karshen watan nan in sha Allahu" na tashi tsaye na fara tsallen murna yana ta yi mini dariya, sai da na gama murna ta na zagayo bayansa na saka hannayena biyu akan kafadarsa na fara yi masa tausa, he feels so tense, a hankali nake matsa masa kafadunsa zuwa wuyansa, yayi ajjiyar zuciya yace "God, that feels so good" na cigaba dayi masa tausar har sai da naga yayi relaxing sannan na daina na zagayo gabansa naga kamar wani abu yana damunsa, nayi kneel down a gabansa na dora hannayena akan cinyarsa nace "me ya faru ne a office din yau? Ya dan saki ransa yana murmushi yace "why did I marry a psychologist?" Nace "because you are lucky" ya shafa fuskata yace "you are damn right I am" kamar ba zai cigaba da magana ba kuma sai yace "uncle galadima ne yazo office dina dazu. Dama tun dadewa yake cewa zai kawo min ziyara. To yau yazo muka zagaya dashi yaga gurin sannan aka zauna akayi addu'ah" yayi shiru, nace "then what's the problem?" Yace "kafin ya tafi ya kirani gefe yake ce min yana son in ringa zuwa fada ana zama tare dani, wai I belong there, a kusa da Takawa. Ni kuma na gaya masa NO, I am happy now, I have you, I have my job, bani da wani problem. He still insisted wai inje inyi tunani akai" na dan jinjina maganar a raina kafin nace "to yanzu wacce shawara ka yanke?" Yace "my answer is still no. Yanzu ina zaune lafiya Takawa ya dauke idonsa daga kaina, maybe ma ya manta da existence dina, amma ina zuwa kusa dashi shikenan na zama nama, ba lallai ne ma ya barni in shiga ba, zai yi disgracing dina ne a gaban mutane kuma ni na jawowa kai na. Besides, ina shiga gurin people will think kamar I want the throne" dariya na fara yi a hankali, ya tsaya yana kallona fuskarsa da mamaki, yace "menene abin dariya kuma?" Nace "since when did Sultan care about me mutane suke tunani akan sa?" Shima dariyar ya fara yi a hankali ina taya shi, sannan yace "na chanza da yawa ko?" Na mike na koma na zauna a cinyarsa ina shafa fuskarsa nace "yes ka chanza my Darling, and I am so proud of you. Amma yanzu ka ajiye Takawa a gefe, ka ajiye abinda mutane zasu ce a gefe, tell me what you really want" ya jima yana kallon gefe yana tunani sannan ya juyo yana kallona yace "lokacin da ina yaro, lokacin kakana yana da rai, there is nothing I want more than the throne. Kullum abinda yake gayamin shine the throne is mine, kullum idan yana zaune a fada zai saka ni in zauna a gabansa, telling me to learn, saying that one day I will rule. Wannan yana daya daga cikin abinda yasa na zama so furious lokacin da babana ya daina zuwa fada dani, a lokacin ina tunanin sarauta is what I was born for dan haka karbarta kamar an cire min purpose na rayuwata ne, amma as I grow up, musamman bayan haduwa ta da ke, na fahimci cewa there is more to rayuwata than sarauta, and now I don't want it, har cikin zuciyata" tun daya fara maganar nake kallonsa kuma na fahimci har cikin zuciyarsa abinda yake fada haka ne. Nace "tunda haka kake so then that's exactly abinda zaka yi. Amma ni ina ganin no matter how much kake so kayi ditching sarauta it is in your blood. In kana ganin zaka iya why not kake zuwa once a week, kamar on Fridays, just ka gaishe shi da sauran mutanen gurin ka fito, Amir zai iya kula da companyn ka a lokacin. At least kaga galadima ba zai ga kamar ka ki daukan shawarar sa ba" ya danyi murmushi yace "in dai hakan shine abinda my Queen tace to hakan zanyi. But not Amir, sai dai in sami wani, Amir hasn't been himself lately" naji babu dadi nace "why? Me ya faru dashi?" Yace "akan wata yarinya ne da yake nema. Sunanta Aisha, 'yar maiduguri ce, tazo bikin cousin dinta garin nan suka hadu suka fara soyayya, bayan ta koma gida har maiduguri yake zuwa gurinta, wajan shekarar su daya kenan tare. To yanzu sai iyayenta suka ce ta fito da miji ita kuma tace shi take so, aka aiko wa aunty din ta tanan garin akan ta bincika waye shi, the first thing da tayi finding out shine babu wanda yasan iyayensa, a kofar orphanage aka tsince shi ko cibiyarsa ba'a yanke ba. Suna jin haka suka aiko masa cewa kar ya sake zuwa gurin 'yarsu, su ba zasu bada 'yarsu ga wanda bashi da asali ba. And that break him down, bai taba nuna damuwarsa ga rashin iyayensa ba sai yanzu, lokuta da yawa yana mayar da maganar kamar wasa amma yanzu he is devastated, it hurts me that there is nothing I can do for him" naji kamar zanyi kuka, naji tausayin Amir sosai, how can some parents be so cruel, ki haifi da da kanki sannan ki je ki jefar dashi? Shi yaron menene laifinsa? Shi yace ki haife shi? Ana samu kuma har da masu kashewa, wadansu su jefa a toilet, ni dai a ganina wannan shine extreme of cruelty. Allah ya shirya mu baki daya.
Nace "but da na dauka yana son Amira ne ai, har na fara tunanin idan abin yazo zan yiwa Daddy magana ya shigar masa tunda akwai sanayya abin zai zo da sauki" Sultan yace "gaskiya bai taba yi min maganar Amira ba, kullum ina tsokanarsa akanta saboda inji ta bakinsa amma bai taba cewa komai ba, wannan Aishan dai ita ce a gabansa" nace "Allah sarki Amir, Allah ya kawo masa mafita" yace "Ameen".
Tun daga lokacin Sultan ya fara zuwa fada duk ranar Fridays, ranar farko da zai je haka na zauna nayi ta addu'ar Allah ya dora shi akan mahaifinsa kar ya wulakanta shi a cikin mutane, dan nasan zuciyar Sultan, in dai Takawa ya kore shi to kuwa ba zai sake zuwa ba, tunda yanzun ma ba wai a son ransa yaje ba. Cikin ikon Allah kuwa babu abinda ya faru, sai dai kamar kullum da ya gaishe shi bai amsa ba, Sultan bai nuna ya damu ba ya gaishe da sauran mutane ya dan zauna for one hour sannan ya tashi yayi tafiyar sa. Kiri kiri ya hango bacin rai a fuskar Abbas amma bai kula shi ba, sai ya nuna kamar bai san yana yi ba. Ranar ina zaune ina jiran sultan ya dawo daga office sai ga sako daga Abbas, alkyabba da rawani, wai a bawa sultan inji shi a ce masa in dai yana son zaman fada he should dress like dan fada, nasan tsokanar fada ne, dan haka na nuna wa dan aiken kamar Sultan yana dakin sa, na shiga na fito na dawo masa da kayan nace sultan yace a gaya wa Abbas ya gode sosai, amma ya riga yayo order nasa kayan daga saudiyya, idan sun iso ma har shi zai aikowa, tunda dai hakkin yaya ne ya jagoranci gida ya kuma kula da kannensa. Ni nasan na kunna wuta a zuciyar Abbas ranar nan, Sultan yana zuwa na bashi labarin abinda ya faru, muka yi ta dariya tare dashi na kuma cigaba da rokon sa akan dan Allah duk abinda Abbas zai yi masa kar ya kula shi, dariya kawai sultan yayi bai ce komai ba.
A kwana a tashi na fahimci shigar ciki a jikina, sam babu laulayi dan ko sau daya ban taba amai ba ko zazzabi, lokacin period dina yana zuwa naga bata zo ba dan haka na tabbatar da zargina, Sultan kam da yaga babu period shi murnar sa ta daban yake yi dan kwata kwata banga alamar yayi linking abin da ciki ba. Babu laulayi a ciki na sai dan karen kwadayi, kullum ina kitchen, in soya wancan inci, in gasa wannan inci, in tafasa wannan inci. Tunda sultan baya wuni a gida dan haka sam bai san me nake yi ba, da daddare kuwa yawo nake masa in gudu daga dakinsa in tafi kitchen in ci abinda zanci in dawo. Ina ta tunanin yadda zan yi in gaya masa, duk da bamu taba yin zancen haihuwa dashi ba amma nasan yadda yake son 'ya'yansa na orphanage dan haka nasan Allah ne kadai yasan irin son da zai yiwa nasa dan ko 'yar.
Ranar wata Wednesday tun da safe nake son chocolate, sauran wadda nake da ita a gida na shanye amma kamar tayar min da kwadayi ta kuma yi, sultan yana dawo wa daga office na saka shi a gaba sai ya kaini mall na sayo chocolate, da kyar na barshi yayi wanka ya dan huta, ana yin sallar magrib na dauko bakar after dress na dora akan riga da zanin jikina, nayi rolling viel na dauki key din mota na tsaya ina kallon Sultan, ya langwabe kai yace "please Love, ki bari muci abinci mana" na girgiza kai nace "in mun dawo ma ci, yanzu fa zamu je mu dawo, ko 30 minutes ba za muyi ba. Yayi ajjiyar zuciya ya mike yace " amma ki sani, ina binki bashi, in mun dawo zan karba" a raina nace 'oho dai, ko ka kaini ko baka kaini ba dama nasan sai ka karba din'. Muna fita nace "sahad zamu je" ya dan bata rai yace "why? Kin san bana son zuwa sahad, it is too crowded" nace "naga yafi kusa ne ai, kuma ba wani special abu zan saya ba kawai chocolate ne" ya daga kafada yace "OK, bara muje can din".
Ibrahim
Tun da safe yace da Amina zai zo gurinta da yamma, dan haka yana tashi daga office gida ya tafi yayi wanka ya shirya, yana yin sallar magrib ya fito ya dau hanyar gidan su, yana shan kwanar gidan ya hango ta tana tahowa bakin titi, bakar after dress ce a jikin ta, tayi rolling mayafin rigar, kamar kullum duk sanda ya ganta sai gabansa ya fadi saboda gani yake kamar Moon ce sai ta matso kusa sai yaga ba ita bace. Yayi slowing down ya barta ta karaso inda yake sannan ya sauke glass dinsa yace "ina zuwa ne haka?" Ta dan tsorata kadan, yayi dariya ita kuma ta bata rai "tun dazu kace min zaka zo ina ta jiranka shiru" ya hada hannuwansa biyu yace "am very sorry, ban tashi da wuri bane ba kuma naga it is already late, shine na tsaya na jira bayan magrib sannan na taho. But ina zaki je kuma?" Ta dan kara bata rai tace "Mommy ce ta aike ni sahad, kuma drivers din duk basa nan" yace "to ga wani drivern yazo, common in" ba musu ta zagaya ta shiga suka tafi. A hanya yace mata "but why sahad? Ba zaki zo gurina kiyi siyayyar ba?" Tayi dariya tace "are you jealous?" Yace "of cause I am" tace "let me tell you why. Shi sahad tsohon guri ne, akwai wasu specific abubuwan da ba'a samu a wani gurin, misali sababbin guri irin naka, sai acan. Dan haka Mommy ta fada min exactly abinda take so bata son substitute, dan haka gwara inje can din direct nasan zan samu" yace "OK, zan kaiki sahad ne kawai saboda inyi proving cewa you are wrong, babu abinda suka fi mu dashi, sai abubuwan da muka fi su dashi ma" tace "OK, we will see". Suna shiga cikin sahad motar su Moon tayi packing suma suka fito duka shiga, amma kowa da side din daya nufa. Ya dauko mata basket suka fara zagaye tare tana duna list din Mommy, ya karbi list din ya duba yayi tsaki yace "babu abinda bani dashi anan wallahi" ta karbi basket din tace "ka ga in kasan zaka dame ni da mita yi tafiyar ka wani gurin, in na gama sai in neme ka" da kamar ba zai tafi ba kuma sai ya tuna cewa a matsayinsa na dan kasuwa ya shigo gurin abokin competition dinsa gwara yayi using chance din ya zagaya yaga abinda suke dashi wanda shi bashi dashi, dan haka ya sakar mata basket din yace "OK, call me when you are done". Ya tafi yana zagaya gurin, har ya fama zagayensa bata kira shi ba, yayi tsaki, su dai mata in suka shiga kasuwa sai ka rasa me sukeyi, shi kuma bai ga abinda wannan gurin yafi nasa ba. Ya juya ya koma ya fara neman ta, ko bata gama bama fita zasuyi, ko me take so suje gurin sa ta dauka.
Moon
Muna shiga direct gurin sweets na tafi, na dauki basket na mika wa sultan ya rike min, na fara chocolate verities iri daban daban ina zubawa a basket din, Sultan kawai kallona yake yi da mamaki yace "wai yaushe kika zama shazumamu ne ban sani ba? Duk wannan chocolate din me zaki yi da ita? A matsayin ki na doctor ai kinsan illar zaki ga lafiyar ki ko?" Na juyo na murguda masa baki na juya na cigaba da abinda nake yi, yace "ni ko? Zaki yi bayani ne in mun koma gida?" Mun jima ina ta diban alawa, in dau wannan in ajiye in koma baya in dauko wata, Sultan ya gaji, kuma ina sane nake kara delaying din mu, a raina ina cewa 'bani kadai zan sha wahalar cikin nan ba kai ma sai kasha' duk kuwa da cewa har yau bai san da cikin ba. Ya ajiye basket din yace "bara in zagaya wajan perfumes, da akwai wani turare da nake ne ma ban sani ba ko zan samu anan" nasan babu wani turare da yake nema, ya gaji ne so yake in ce masa ai na gama mu tafi, na juyo nace masa "OK" ya saki baki da mamaki yana kallona yace "kin yarda in barki anan ke kadai" nace "I am 23 years old, ba zan bata ba" ya juya ya tafi, har yakai karshen lane din ya juyo, nayi masa alamar bye2 ya girgiza kansa ya sha kwana. Na juya ina dariya, a raina ina tunanin maybe tonight in gaya masa labarin cikin nan, I can't wait to see his reaction. Nayi murmushi na cigaba da kwasar sweets dina.
Kamar daga sama naji an kama hannuna an fara jana da sauri, "let's go, babu wani abinda ba zaki samu ba a gurina, menene anan din wanda ni bani dashi?" Duk da banga fuskar wanda ya rike ni ba amma muryar sa ta saka na gane shi, hakan kuma ya saka ni wata irin faduwar gaban da har sai da naji daci a bakina, wani amai naji yana neman taso min, nayi kokarin kwace hannuna amma bai sake ni ba kuma bai kalle ni ba, cikin muryar fada amma kuma cikin rada saboda bana son inyi calling attention din mutane zuwa garemu nace "what are you doing?" Yayi sauri ya sake ni, lokacin har mun kai karshen lane din, a razane yake kallona, hakan ya tabbatar min ba wai yana sane ya aikata abin da yayi ba, murya kasa kasa shima yace "Maimunatu what are you doing here? Am very sorry na dauka Amina ce, tare muka zo da ita kuma itama bakar riga ta saka. Am very sorry" nace "am here with my husband, go away bana son ya gan mu tare" ya dan bata fuska yace "you look scared, why are you scared of your husband, is he mistreating you" by then gaba daya hankali na ya tashi, na juyo da sauri na matsa daga inda yake amma sai ya kuma zagayo wa gaba na, fuskarsa fal da concern, yace "Maimunatu please tell me if you are not OK" numfashi na ne gaba daya naji yana neman daukewa, Sultan na hango a farkon lane din a tsaye, da kwalbar turare a hannun sa, tun daga inda nake na hango jijiyoyi sun fito rado rado a goshinsa, farin idonsa ya kada yayi jajawur light brown din ciki kuma yayi bakikkirin, mara ta ce ta daure kamar zan yi fitsari, a hankali na furta "innalillahi wa inna ilaihir rajiun".
Winter is really coming
Table of Contents
Chapters
- 1 Episode One : The Beginning of the Beginning
- 2 Episode Two: Meet my Family
- 3 Episode Three: Loved by All
- 4 Episode Four: Moon's Sister
- 5 Episode five: The Strangers
- 6 Episode six: The Challenge
- 7 Episode Seven: The Thin Tall Man
- 8 Episode Eight: The New Imam
- 9 Episode Nine: Give Me a Chance
- 10 Episode Ten: I Don't Know
- 11 Episode Eleven : The Protector
- 12 Episode Twelve : This is Me
- 13 Episode Thirteen : This is Me 2
- 14 Episode Fourteen : The Limit
- 15 Episode fifteen: blood is Thicker than Water.
- 16 Episode Sixteen : The Letter
- 17 Episode seventeen: Reply
- 18 Episode eighteen: what's Next?
- 19 Episode Nineteen: The Goodbye
- 20 Episode Twenty: The New Job
- 21 Episode Twenty one: Amira
- 22 Episode Twenty Two: Efisowa
- 23 Episode Twenty three: The Break up 💔
- 24 Episode Twenty Four: The Heartbreak 💔
- 25 Episode Twenty five: The Eclipse
- 26 Episode Twenty Six: A Step Further Away
- 27 Episode Twenty Eight : University of Oxford
- 28 Episode Twenty Nine: The Message
- 29 Episode Thirty : The Final Blow
- 30 Episode Thirty One: Let it go
- 31 Episode Thirty Two : Munnir
- 32 Episode Thirty Two : Mahdi
- 33 Episode Thirty Three: Zayed
- 34 Episode Thirty Four : Back to Square One
- 35 Episode Thirty Five : When Destiny Calls.
- 36 EpisodeThirtySix: Interesting
- 37 Episode Thirty Seven : The Dinner
- 38 Episode Thirty Eight : The Shadow
- 39 Episode Thirty Nine : The Shadow 2
- 40 Episode Forty :TheShadow 3
- 41 Episode Forty One : Born for This.
- 42 Episode Forty Two : Born for This
- 43 Episode Forty Three: America
- 44 Episode forty four : America 2
- 45 Episode Forty Five : The Rush
- 46 Episode Forty Six : The Repentance
- 47 Episode Forty Seven : Amir
- 48 Episode Forty Eight : Awkward
- 49 Episode Forty Nine : Ya Habeeb
- 50 Episode Fifty : Munir 2
- 51 Episode Fifty one : Mommy
- 52 Episode Fifty Two : The Journey
- 53 Episode Fifty Three : Daddy
- 54 Episode Fifty Four : Her Father's Daughter
- 55 Episode fifty five : Her Father's Daughter 2
- 56 Episode Fifty Six : What You Sow
- 57 Episode Fifty Seven : What You Sow 2
- 58 Episode Fifty Eight : I Missed You
- 59 Episode Fifty Eight : For You, Only You
- 60 Episode Sixty : The Prince
- 61 Episode Sixty One : Save the Date
- 62 Episode Sixty Two : The Manager
- 63 Episode Sixty Three : Amira 3
- 64 Episode Sixty Four : The Past and the Future
- 65 Episode Sixty Four : The Visitors
- 66 Episode Sixty Six : The Wedding
- 67 Episode Sixty Seven : The Wedding 2
- 68 Episode Sixty Eight : The Wedding Night
- 69 Episode Sixty Nine: The Wedding Night 2
- 70 Episode Seventy : The Wedding Night 3
- 71 Episode Seventy One : The Honeymoon
- 72 Episode Seventy Two : My Everything
- 73 Episode Seventy Three : His Father's Son
- 74 Episode Seventy Four : The Cook
- 75 Episode Seventy Five : The Emir
- 76 Episode Seventy Six : The Visitors
- 77 Episode Seventy Seven : Amina
- 78 Episode Seventy Eight : The Storm
- 79 Episode Seventy Nine : The Lightening and The Thunder
- 80 Episode Eighty : The Skeleton in The Closet
- 81 Episode Eighty one : The Skeleton in the Closet 2
- 82 Episode Eighty Two : The Light
- 83 Episode Eighty Three : The News
- 84 Episode Eighty Four : Little Love
- 85 Episode Eighty Five : Ibrahim
- 86 Episode Eighty Six : The Phone Call
- 87 Episode Eighty Seven : Riyadh
- 88 Episode Eighty eight :Khairat
- 89 Episode Eighty Nine : Khairat 2
- 90 Episode Ninety : His Mother's Son
- 91 Episode Ninety One : His Mother's Son 2
- 92 Episode Ninety Two and Three : Maldives 1 and 2
- 93 Episode Ninety Four : RIP
- 94 Episode Ninety Five : The Light
- 95 Episode Ninety Six : The New Bride
- 96 Episode Ninety Seven : The Real Prince
- 97 Episode Ninety Eight: My Baby
- 98 Episode Ninety Nine : New Little Love
- 99 Episode Hundred : Not The End.