Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 89

Episode Eighty Nine : Khairat 2

Maimoon Book 1 Complete Hausa Novel 1,872 words 0 views Progress saved
Download Book

Na taso na dawo kusa da ita na zauna nace "yes Ummee, we will. Nayi miki alkawarin Sultan zai zo gidan nan, kuma in yazo zaki yi mamakin sa, dan duk wannan zuciyar da wannan fushin na dan lokaci ne, haka yake, akwai saurin hawa kuma akwai saurin sauka, I assure you yana ganinki shikenan komai zai wuce, he is just not sure of yadda zaki karbe shi ne, duk wannan girman jikin da wannan kwarjinin a ido ne kawai, in side him he is the kindest man I have ever known, yana da tsananin tausayi da kuma kokarin kyautatawa mutane, ko da kuwa wadanda suka zalince shine bai damu ba, he said kyautatawa mutane makes him feel good shi yasa yake yi, ballantana ke da kika haife shi, kallo daya zaiyi miki and it will all be over, he will take you in his arms and cry on your shoulders, he will love you fiye da yadda kike tsammani, zai zamar miki 'da daya tamkar da dubu, he will feel Lucky to have you as his mother" sosai Maganganu na sun kwantar mata da hankali dan har murmushi na gani akan lips dinta, ta kama hannayena duka biyun tace "Maimunatu bansan me zance miki ba daga ke har iyayenki, you are really an angel a rayuwar dana, bani da bakin da zan gode miki sai dai in dawwama har karshen rayuwata ina yi miki addu'ar" na dora hannunta daya akan cikina tace "ubangiji Allah ya jagoranci rayuwarki, da duk kanin zuri'ar ki, ya baku kyakykyawar rayuwa fil duniya wal ahkhira, Allah ya daga garajarki da duk kanin ahlinki, Allah ya kade duk wani sharri dake cikin rayuwar ku ya tabbatar da alkhairi a duk al'amuranki, Allah yayi miki sakayya a bisa duk abinda kika yi a rayuwar sultan. Allah ya albarkaci zuri'arki yasa su zamo sanyin idaniya a gare mu baki daya. Allah kuma ya kara soyayya a tsakanin ki keda mijinki, ya dauwamar da zaman lafiya a tsakaninku, ya sa ku kasance tare har karshen yaruwar ku" duk abinda take fada ina cewa amin, kuma ina jin dadi har raina, sai da ta gama yi min addu'ar sannan ta jawo ni jikinta ta rungume tace "Nagode Maimunatu".
Kwana biyu bayan nan, ni gani nake yi ma kamar nafi sultan damuwa, komai nake yi hankali na yana kansa, da kaina nace Hafsat ta bani sim card dina amma taki, kullum sultan yana cikin kiran wayar Hafsat, tun yana yi mata masifa har ya koma bata hakuri yana lallashinta, ita kuma tace sai ta rama fadan da yayi mata, innaji suna waya sai in ji kamar in kwace wayar amma nasan muna yin magana da sultan zai kalallame ni yace in dawo Nigeria, I don't think I can resist him in inajin muryarsa. Little khairat ce ta zama babbar kawara, tana ta rarrafenta ko'ina har ta fara tsayawa, in tana gurina babu abinda yake kaita gurin Hafsat sai in zata ci abinci. Ummee kuwa sosai muka kara sabawa da ita. Kamar yadda tayi min alkawari haka ta zage wajan koyamin girki, irin abincin larabawa iri iri haka take koyamin, babu abinda take so irin in zauna inyi ta bata labarin sultan, wannan kullum shine abin hirar mu. Hotunan sa kuwa na waya ta ta gansu yafi a kirga. A wayar Hafsat na hada ta da Mommy suka gaisa, nan take suka kulla kawance. Mommy ta gaya min ta yaba da ita tun kafin ma ta ganta.
Ranar dana kwana biyar a Riyadh, muna dinner da daddare sai ga kiran sultan a wayar Hafsat. Ta nuna min screen din sannan ta daga. Sun danyi magana sannan tace min "yace in ba zaki karbi wayar ba in saka shi a speaker zai yi miki magana, na kalli Ummee naga alamun anticipation a fuskar ta, she has never heard her son's voice tun da suka rabu, na gyada wa Hafsat kai, ta saka wayar a speaker ta ajiye a kusa dani, naji muryarsa "Moon please listen to me, why are you punishing me for the crime I didn't commit? Ni laifin me nayi wai? Kina so zuciyata ta buga in mutu ko?" Na danyi murmushi, dadin baki yake so yayi min, ya cigaba da magana, "Love please, nasan kinaji na, kuma nasan me kike so, I promise you zanzo amma kinsan it will take time, dan Allah na wahala haka, kar kice ba zaki yi min magana ba sai nazo, I can't take it kin sani" Ummee ta taso ta dauki wayar da fitar daga hands free ta miko min, na karba na ajiye khairat da take bacci a kan cinya ta, na mike na fita veranda, ina jiyo Hafsat tana gyaran muryar tsokana amma ban kula taba, na saka wayar a kunne na nace "My Love" kamar ba zaiyi magana ba amma ina jiyo numfashinsa a hankali, sannan yace "why are you doing this?" Nace "I just want you to come and see your mother, shikenan" yace "you should have talk to me ai, ki gaya min ga abinda kike so, you know I can do anything for you love" nace "nayi maka maganar ai kaki yadda, babu yadda zanyi da kai ne" ya dan yi shiru sannan yace "you have no idea how damn good it feels to hear your voice" Nace "me too" yace "ba wani nan, da kin damu dani ai da baki kashe wayarki ba, you always say kina sona but nasan ko rabin wanda nake miki ba kya yimin" nace "kai ma kasan ba haka bane ba. Kawai dai we show our love ne in different ways ni da kai. Zuwa na garin nan da kashe wayata da nayi are all ways of showing you how much I love you. Sometimes you have to sacrifice something to get something better" yace "zaki yi min dadin baki ko?" Nayi dariya, nace "tun da nazo garin nan bana samun bacci me dadi saboda babu kai, ba karamin dauriya nayi ba these five days" yace "uhmmm, na ji ki dai amma ban yarda ba, kina can kina sharar baccin ki kin barni da rungumar pillow da mafarkai ko?" Nace "sorry" yayi ajjiyar zuciya yace "so, how is she?" Nace "come and see for yourself" yace "hmmm baza ki fada min ba kenan ko?" Nace "eh din. In kana son kasan ya take kazo da kanka ka ganta" yace "I will come ai, na gaya miki zanzo. Ina baby na kuma? Haka kawai kin raba ta da daddyn ta" nace "na gaya maka namiji ne fa ba mace ba, he is fine. Can you believe Ummee tana taba cikina ya fara motsi" yace "what? You mean she touched your tummy?" Nace "yes, she does, she is really nice Sultan" muka ci gaba da hira, sam ban san time yana ta tafiya ba, haka muke dama duk sanda muke tare da sultan ko a fili ko a waya ji muke yi kamar time ya tsaya. Sanda ba koma ciki na tarar har kowa ya kwanta, dan haka nima na shirya na kwanta, da safe Hafsat tazo ta cillo min sim card dina tace "bani wayata" na mika mata nima na kunna tawa.
Kwana na goma cif a Riyadh Sultan yazo, tun sanda yayo waya cewa zaizo gaba daya ummee ta tayar da hankalinta, ana gobe zuwansa kuwa sam bata yi bacci ba, daga baya ta tashi ta fara salloli tana rokon Allah for courage. Ni kam tausayinta nake ji har raina, ban san ya take ji a ranta ba. Twelve na rana jirgin su sultan zai sauka, abinciccikan da muka shirya masa nasan duk cinsa sai ya gaji ya bari, Hafsat tana dariya tace "Moon gwara ki tanadi maganin gudawa a kusa". Muna gama shirya komai na tafi daki nayi wanka, ina fitowa Ummee ta shigo ta kawo min wata doguwar riga pink mai ratsin blue a sides dinta, sai stones a gaban rigar, da viel shima blue. Tayi kyau sosai rigar. Na karba nayi mata godiya. Kwalliya na zauna na tsara sosai, na saka rigar naga tayi min bala'in kyau, na fito palo na bar ummee itama tana shiryawa itama. Lokacin dauko shi yana yi zayed yazo, nace su tafi kawai shi da Hafsat ni na jirashi a gida, Hafsat ta kalle ni tace "you are wicked" nayi dariya kawai. Nasan halin sultan, ba karamin aikinsa bane yana ganina a airport ya ce komawa zamuyi, ko kuma in babu jirgi yace mu kwana a hotel da safe mu koma, nayi wa ummee alkawarin zan kawo mata sultan har gida and am going to keep that promise. Su Hafsat suna tafiya sai ga Ummee ta fito, ta saka riga irin tawa sai dai tata blue ce da ratsin pink, tayi nadin veil mai kyau, ta zo ta zauna a kusa dani tayi irin zaman da tayi ranar da zanzo, at the edge of the seat da hannayenta a tsakanin cinyoyinta, muna nan zaune babu wanda yayi magana har muka ji karar bude gate, daganan muka ji tsayuwar mota da sound din bude mota da rufewa, naji ummee ta kama hannuna ta rike kam, na kasa kallon fuskarta, a hankali muka ji an bude sliding door din palon, idona na kafa a gurin, na ganshi ya shigo, bakin wando ne geans a jikinsa mai kauri, da farar shirt yayi stocking ya daura bakin belt, gashin kansa a tsatstsaye kamar wanda ya tashi daga bacci, nasan abinda yasa yayi wannan shigar, so yake ya nuna wa ummensa what he used to be. Idanuwansa a kanmu muma namu a kansa, ya saki jakar hannunsa ta fadi a kasa, ummee ta saki hannuna ta mike tsaye tana jujjuya hannunta, ya kalle ta for some seconds sannan ya dawo da idonsa kaina. Na mike tsaye nima, da sauri ya karaso inda muke, ban ankara ba kawai sai ji nayi ya jawo ni jikinsa ya rungume, na fara kokarin ture shi amma yaki ya sake ni, ya saka fuskar sa a wuyana, a hankali nace "sultan ummee fa tana kallon mu" yace "i know" Nace "go to her" ga mamaki na sai cewa yayi "kunyar ta nake ji" dariya na fara yi kasa kasa, ummee ta zagayo ta bayansa tana kallona tace "me yake cewa?" Ina dariya nace "wai kunyarki yake ji" ta danyi murmushi kwalla ta fara taruwa a idonta, ta dora hannunta a hargitsatstsen gashinsa tana shafawa tace a hankali "my little love" ai kuwa ya sake chusa kansa a wuyana yace "am not little" ta sake cewa "me yace?" Nace "wai he is not little" tayi dariya hawayenta suna karasa saukowa tace "to shikenan, ka koma big love yanzu" har yanzu ya kasa dago fuskarsa ya kalle ta, ni kam dariya kawai nake yi, ban taba ganin sultan yana jin kunyar wani ba sai yau, yace a hankali "yanzu sai tace zata fara pampering dina kuma" tace "ai har na hada maka bottle, yanzu zanje inyi warming in baka" ta dora kanta a bayansa hawayenta yana zuba a jikin rigarsa, ni kam dariya kamar cikina zai yi ciwo, lokaci daya kuma sai ya sake ni ya juya ya rungume ta, take ta saki kukanta gaba daya, na dan ja da baya ina kallon su ina jin dadi a raina, a hankali na sulale na bar musu palon.

Table of Contents

Chapters

99 chapters
  1. 1 Episode One : The Beginning of the Beginning
  2. 2 Episode Two: Meet my Family
  3. 3 Episode Three: Loved by All
  4. 4 Episode Four: Moon's Sister
  5. 5 Episode five: The Strangers
  6. 6 Episode six: The Challenge
  7. 7 Episode Seven: The Thin Tall Man
  8. 8 Episode Eight: The New Imam
  9. 9 Episode Nine: Give Me a Chance
  10. 10 Episode Ten: I Don't Know
  11. 11 Episode Eleven : The Protector
  12. 12 Episode Twelve : This is Me
  13. 13 Episode Thirteen : This is Me 2
  14. 14 Episode Fourteen : The Limit
  15. 15 Episode fifteen: blood is Thicker than Water.
  16. 16 Episode Sixteen : The Letter
  17. 17 Episode seventeen: Reply
  18. 18 Episode eighteen: what's Next?
  19. 19 Episode Nineteen: The Goodbye
  20. 20 Episode Twenty: The New Job
  21. 21 Episode Twenty one: Amira
  22. 22 Episode Twenty Two: Efisowa
  23. 23 Episode Twenty three: The Break up 💔
  24. 24 Episode Twenty Four: The Heartbreak 💔
  25. 25 Episode Twenty five: The Eclipse
  26. 26 Episode Twenty Six: A Step Further Away
  27. 27 Episode Twenty Eight : University of Oxford
  28. 28 Episode Twenty Nine: The Message
  29. 29 Episode Thirty : The Final Blow
  30. 30 Episode Thirty One: Let it go
  31. 31 Episode Thirty Two : Munnir
  32. 32 Episode Thirty Two : Mahdi
  33. 33 Episode Thirty Three: Zayed
  34. 34 Episode Thirty Four : Back to Square One
  35. 35 Episode Thirty Five : When Destiny Calls.
  36. 36 EpisodeThirtySix: Interesting
  37. 37 Episode Thirty Seven : The Dinner
  38. 38 Episode Thirty Eight : The Shadow
  39. 39 Episode Thirty Nine : The Shadow 2
  40. 40 Episode Forty :TheShadow 3
  41. 41 Episode Forty One : Born for This.
  42. 42 Episode Forty Two : Born for This
  43. 43 Episode Forty Three: America
  44. 44 Episode forty four : America 2
  45. 45 Episode Forty Five : The Rush
  46. 46 Episode Forty Six : The Repentance
  47. 47 Episode Forty Seven : Amir
  48. 48 Episode Forty Eight : Awkward
  49. 49 Episode Forty Nine : Ya Habeeb
  50. 50 Episode Fifty : Munir 2
  51. 51 Episode Fifty one : Mommy
  52. 52 Episode Fifty Two : The Journey
  53. 53 Episode Fifty Three : Daddy
  54. 54 Episode Fifty Four : Her Father's Daughter
  55. 55 Episode fifty five : Her Father's Daughter 2
  56. 56 Episode Fifty Six : What You Sow
  57. 57 Episode Fifty Seven : What You Sow 2
  58. 58 Episode Fifty Eight : I Missed You
  59. 59 Episode Fifty Eight : For You, Only You
  60. 60 Episode Sixty : The Prince
  61. 61 Episode Sixty One : Save the Date
  62. 62 Episode Sixty Two : The Manager
  63. 63 Episode Sixty Three : Amira 3
  64. 64 Episode Sixty Four : The Past and the Future
  65. 65 Episode Sixty Four : The Visitors
  66. 66 Episode Sixty Six : The Wedding
  67. 67 Episode Sixty Seven : The Wedding 2
  68. 68 Episode Sixty Eight : The Wedding Night
  69. 69 Episode Sixty Nine: The Wedding Night 2
  70. 70 Episode Seventy : The Wedding Night 3
  71. 71 Episode Seventy One : The Honeymoon
  72. 72 Episode Seventy Two : My Everything
  73. 73 Episode Seventy Three : His Father's Son
  74. 74 Episode Seventy Four : The Cook
  75. 75 Episode Seventy Five : The Emir
  76. 76 Episode Seventy Six : The Visitors
  77. 77 Episode Seventy Seven : Amina
  78. 78 Episode Seventy Eight : The Storm
  79. 79 Episode Seventy Nine : The Lightening and The Thunder
  80. 80 Episode Eighty : The Skeleton in The Closet
  81. 81 Episode Eighty one : The Skeleton in the Closet 2
  82. 82 Episode Eighty Two : The Light
  83. 83 Episode Eighty Three : The News
  84. 84 Episode Eighty Four : Little Love
  85. 85 Episode Eighty Five : Ibrahim
  86. 86 Episode Eighty Six : The Phone Call
  87. 87 Episode Eighty Seven : Riyadh
  88. 88 Episode Eighty eight :Khairat
  89. 89 Episode Eighty Nine : Khairat 2
  90. 90 Episode Ninety : His Mother's Son
  91. 91 Episode Ninety One : His Mother's Son 2
  92. 92 Episode Ninety Two and Three : Maldives 1 and 2
  93. 93 Episode Ninety Four : RIP
  94. 94 Episode Ninety Five : The Light
  95. 95 Episode Ninety Six : The New Bride
  96. 96 Episode Ninety Seven : The Real Prince
  97. 97 Episode Ninety Eight: My Baby
  98. 98 Episode Ninety Nine : New Little Love
  99. 99 Episode Hundred : Not The End.