Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 85

Episode Eighty Five : Ibrahim

Maimoon Book 1 Complete Hausa Novel 2,178 words 0 views Progress saved
Download Book

Happy Birthday Oluwaseun Ibrahim Adeniran. May you forever be happy. Kar ka chinye cake din kai kadai dai.
Ibrahim
Last thing da ya gani kafin motar sa ta fadi shine fuskar Moon, and she looks so scared. Sanda motar sa ta fadi babban tsoron sa shine ba mutuwa ba, tsoronsa shine kar wani abu ya sami Moon because of him. A lokacin daya dawo hankalinsa abinda ya fara tunawa shine Moon, Allah dai yasa babu abinda ya same ta, dan haka kalmar daya fara furtawa itace "Maimunatu" muryar mamansa yaji a kusa dashi tana yi masa magana, sannan kuma yaji shigowar wani namiji yana tattaba shi, mutumin ya bude idonsa ya haska masa wata karamar fitila, daga nan kuma ya koma bacci. Sai daya farka for the second time sannan ya fahimci kwanansa uku a asibiti unconscious, ga maman sa da little moon sun zo daga ibadan, amma ita maman sa abinda aka gaya mata shine accident yayi, ba ta san dalilin accident din ba, dan haka ya san bata da labarin ko Moon taji ciwo ko bata ji ba. Doctor ya saka ya kira Amina, wacce tun da ta kai shi asibiti kullum sai ta je ta duba shi, haka ma Daddy, doctor ya gaya wa Amina cewa ya farfado kuma yana nemanta, ba'afi awa daya da wayar ba sai gata tazo. Sosai ta nuna murnar ta daganin ya dawo hayyacinsa, ta ringa yiwa doctor din tambayoyi akan lafiyar Ibrahim din har sai da ta fahimci babu wani muhimmin concern dangane da lafiyar tasa, shi kam Ibrahim kallonta kawai yake yi yana murmushi, sai da doctor ya fita sannan yace "har haka aka damu dani dama ni ban sani ba?" Tace "no, ba damuwa nayi da kai ba. Naso ace ka balla spinal cord yadda ba zaka sake bin mata da miji ba" yace "yes you are right. Nasan banyi dai dai ba, komai yayi min ni na jawo wa kaina, I was just scared he would hurt Moon" tace "matarsa ce fa? In ma menene zaiyi mata ina ruwanka? Kuma ma Sultan will never hurt Moon. Yanzu gashi sanadiyyar abinda ya faru sunyi rigima, har ya kwanta a asibiti ma. She is pregnant fa. You ought to get over her by now" yace "I am over her. Abinda ya faru nima ban san ya akayi ya faru ba and am sorry na jawo problem a tsakanin su. Is she OK?" Tayi ajjiyar zuciya ta zauna a kujera tace "yes she is fine" yace "please can you go to her ki bata hakuri on my behalf? Ki basu hakuri ita da mijinta" ta bata fuska alamar bata son zuwa, ya marairaice murya, "please kinga bani da lafiya fa. Take little Moom with you in suka ganta sai sufi hakura". Har ran Amina bata so zuwa ba, ita a ganinta menene kuma na zuwa wani bada hakuri? Ai kamar kokarin tayar da magana ne kuma, aikin gama ya riga ya gama, daga Ibrahim har Sultan kowa jikinsa ya gaya masa shikenan magana ta wuce sai dai fatan a kiyayi gaba kuma. Amma sai ta yarda zata je din to put his mind at ease. Ta dauki little Moon suka tafi tare. Moon ta tare su sosai kuma taji dadin ganin takwararta amma kamar yadda Amina tayi tsammani sam ba ta ga alamar soyayyar Ibrahim a tare da Moon ba, sai care da mutunta juna, tace mata zata zo ta duba Ibrahim amma ita kan ta Aminan ta san fada kawai Moon tayi ba zuwan za tayi ba. Ga zasu taho Moon ta hada kaya da yawa ta bawa takwararta suka dawo asibiti gurin Ibrahim.
Suna shiga dakin suka tarar Ibrahim ya tashi zaune suna magana da mama, Amina ta durkusa ta gaishe da mama wacce ta amsa mata da fara'arta, daga nan mama ta fita ta basu guri suyi magana. Ba tare daya kalli Amina ba yace da little Moon "sweetheart menene wannan a leda kika samo haka?" Ta karaso gurinsa tana washe baki tace "namesake dina ce ta bani" ya karba yana dubawa "wow duk wannan naki ne ke kadai, bata baki komai ki kawo min ba?" Tace "ba abinda ta bani in kawo maka" yace "kuma bata ce tana gaishe ni ba?" Tace "eh bata fada ba" ya dauki yarinyar ya dora a cinyarsa, yana shafa kanta "sweetheart yau kinga namesake dinki ko? How do you find her?" Tace "she is beautiful and nice" yace "yes sweetheart she is the nicest person I have ever known". Amina ta ajiye ledar hannunta ta juya zata fita, sai a lokacin ya tuna tana gurin, yace "wait" bata juyo ba yace "Maimunatu Please" chak ta tsaya kafin ta karasa kofar, ta juyo a hankali tana kallonsa, a nutse ta fara magana "I am not Maimunatu, I am Amina" ya tsaya kawai yana kallonta dan shi bai ma san ya kirata da Maimunatu ba sai data fada. Ta kalli little moon akan cinyarsa tace "Moon je ki nuna wa Mama kayan da kika samo" da sauri yarinyar ta dauki ledar ta fita da gudu. Bayan ta rufe kofa sukayi shiru suna kallon juna, yace "am sorry, I didn't meant to hurt you, ban san ya akayi bakina ya kauce ba" tace "cut it. Dalilin da yasa ka tura mu gidan Moon kenan wato, because deep down you you still love her, duk abinda kake fada min cewa you are over her duk ba haka bane ba, kace baka san dalilin da yasa kabi su a baya ba amma ni nasan ka bi su ne saboda har yau baka hakura da ita ba. To bara in gaya maka wani abu, she is more than over you. Tun kafin tayi aure ta daina sonka ballantana yanzu. She is happily married. She is not coming back to you. The sooner you get this into your head the better for you. Am not maimunatu am Amina, duk da mun hada jini da ita hakan ba yana nufin feelings din mu da halayen mu daya ne ba. Duk da munyi kama da ita ba hakan yana nufin zan iya rikidewa in zama ita ba. I am my own person. I can't be a substitute for someone. You lost something a rayuwar ka, ka koma baya kayi tracing may be You will find it. I dan kuma baka samu abinda kayi loosing ba then I pity your soul" ta juya ta fita.
Ibrahim ya dafe kansa tare da cewa "ya salam" ya koma da baya ya kwanta akan gadon. "What is wrong with me dear God" duk abinda Amina ta fada gaskiya ne, sai da ta fada kuma sannan ya kara tabbatar da cewa gaskiya ne. He enjoys being with her only because in yana tare da ita sometimes yana jin kamar yana tare da maimunatu ne, amma kuma yasan ba maimunatun bace ba. Amma kuma mai take nugi da he lost something, tana nufin yayi loosing maimunatu? But ai that's obvious, to menene yayi loosing?. Gaba daya ji yayi ya kasa sukuni, duniyar duka tayi masa kunci, me yasa shi rayuwarsa take a haka ne? Sam ya kasa samun farinciki tun ranar da ya juya bayansa ya tafi yabar maimunatu a gidansu tana kuka, ba zai iya tuna ranar da yayi farin ciki ba, genuine farin ciki, ba kuma zai iya tuna ranar da wani yayi farin ciki domin sa ba. Hatta mahaifiyarsa kawai yasan hakuri take yi dashi amma bajin dadinsa take yi ba. What did he miss? Moon is over him ya sani amma shi why can't he get over har?
Satin sa daya aka sallame shi daga asibitin, cikin satin nan ya kara zama miserable, dan har 'yar karamar Moon ma tsoron sa take ji dan daga tayi wani abu kadan zai daka mata tsawa, daga asibitin mama cewa tayi ba zasu je gidan sa ba, yaje yaci kansa shi kadai, ta dauki jikarta su kayi tafiyarsu tasha suka hau mota suka koma ibadan. Shi kadai ya koma gidan sa inda yake zaune shi kadai, ya kira number din Amina yafi cikin charbi amma bata dauka ba, yasan in yaje gurinta ma ba fitowa zatayi ba kuma shi din ma yana tinanin mai zai ce mata in yaje din? Ranar daya koma gurin aikinsa sai da ya kori mutum biyar daga aiki, ya bawa wadansu query, gaba daya kowa ma haushi yake bashi, shi kanshi haushi yake bawa kansa. Rannan ya dawo daga office kawai yaki komawa gida, to in ya koma gidan ma me zaiyi a can? ya kama driving yana zagaya gari a hankali fresh air tana kada shi, ya fara tuno kalaman Amina, she said he lost something a rayuwarsa, she advice him to trace back his life yayi finding menene yayi missing. To in zaiyi tracing back ta ina zai fara? Kafin ya koma gida ya yanke shawarar he is taking the next plight to ibadan, tunda anan ne rayuwar sa ta fara, in ma yana da matsala anan ne zai samu solution.
Da sassafe jirgin su ya sauka a ibadan, ya dauki taxi ta kai shi unguwarsu. Ya sauka ya tsaya yana karewa gurin kallo, babu abinda ya chanja, ya kalli masallacin da a da babansa yake limanci, ya tuna da lokacin da suke zuwa masallacin tare da babansa, what has happened? Ya shiga gidan su da sallama, jakarsa rike a hannunsa, mamansa da take wanke kwanuka ta tsaya tana kallonshi da mamaki. Shi kuma gidan yake karewa kallo, babu abinda ya chanza sai tsufa da gidan ya kara yi da lalacewa. Ya tuna da uwar dukiyar da yake tarawa yake ajiye wa a banza, for what? Ya ajiye jakar hannunsa anan tsakar gidan ya nufi dakin da baba ya zauna kafin rasuwarsa, ya tura kofar ya shiga yana feeling kamar zai ganshi akan tsohuwar kujerar sa da alqurani a gabansa, alqurani? Ya shiga dakin sosai yana kallon tarin littattafan addini a jejjere kamar yadda suke kullum. Cikin littattafan nan babu wanda bai haddace from page to page ba. Ji yayi kansa yana juyawa, when was the last time daya bude alqurani ya karanta? When was the last time daya zauna yayi cikakken azkar? When was the last time daya yi istikara ya nemi zabin Allah a cikin rayuwarsa? How did he expect things to go right a rayuwarsa? Ya juya ya kalli mahaifiyarsa da take tsaye still tana kallonsa, ya sani cewa jin dadin rayuwar mutum duniya da lahira yana jingina a jikin how much yake kyautatawa iyayensa, amma shi baya kyautatawa tasa uwar, duba gidan da take ciki duba gidan da shi yake ciki a abuja. Amma ai da ba haka yake ba, da sanda bashi da komai amma dan albashinsa biyu yake rabawa ya kawo mata rabi, lokacin ma tana da miji ba yanzu ba da bata da kowa sai shi. Ya tuna da baban sa da yadda yayi making sacrifices dan yaga ya zama wani abu a duniya, duk kuwa da cewa bashi ya haife shi ba, a karshe ya dauki 'yarsa ya bashi aure, amma me yayi? Sai ya wulakantata, yaki yin biyayya ga iyayensa, ya take maganar su ya nuna musu basu isa dashi ba, har efi ta bar duniya bata ji dadin aurensa ba, ta yaya zaiyi tsammanin rayuwarsa zata tafi masa a dai dai? Ya dauki alqurani guda daya ya bude ya fara buda pages din yana jin wani feeling mai dadi a ransa, how did this happened? When? When did he lose himself? Sai yanzu ya gane maganar Amina, ba wani abu yayi loosing ba sai kansa, he lost himself the moment da yayi deciding yana son yayi kudi dan ya auri Moon, tun daga ranar he became slave to the idea of becoming rich for Moon. Duk da karyar da Amira tayi masa cewa Moon tayi aure amma ya kasa cire hop din cewa zata dawo gurinsa, kuma yana son sanda zata dawo ta tarar cewa he is richer than yadda tayi tsammani. Duk tsahon shekarun nan komai yayi dan ita yake yi ba dan kansa ba. Hatta kaya in ya saka sai yayi tunanin in ta ganshi yanzu what will she think? In tunaninsa ya gaya masa ba zata so kayan ba sai ya cire ya saka wadansu. He became so obsessed in preparing for her to come back to him that he lost himself along the way. Ya ajiye alquranin hannunsa. He found himself now. Everything is going to be alright now.
Mama ta karaso bakin kofar tana kallonsa tace da yarabanci "Seun lafiya kake kuwa? Yaushe kazo gari? Me kake yi a dakin nan?" Ya mike tsaye ya karasa gabanta ya zube a kan guiwoyinsa, yace "Mama dan Allah ki gafarta min. Nayi kuskure a baya, rayuwata gaba daya bata tafiya dai dai. Dan Allah mama ki yafe min kiyi min addu'ah ko Allah zai dube ni ya shiga rayuwata" Tace "my son, ni ban rike ka da komai ba, kullum addu'ah nake maka Allah ya dawo da kai kan hanya. Kuma Alhamdulillah tunda har kazo ka nemi gafara ta to na tabbatar ka fahimci kuskurenka. Allah yayi maka jagora"

MAIMOON
By
Maman Maama

Table of Contents

Chapters

99 chapters
  1. 1 Episode One : The Beginning of the Beginning
  2. 2 Episode Two: Meet my Family
  3. 3 Episode Three: Loved by All
  4. 4 Episode Four: Moon's Sister
  5. 5 Episode five: The Strangers
  6. 6 Episode six: The Challenge
  7. 7 Episode Seven: The Thin Tall Man
  8. 8 Episode Eight: The New Imam
  9. 9 Episode Nine: Give Me a Chance
  10. 10 Episode Ten: I Don't Know
  11. 11 Episode Eleven : The Protector
  12. 12 Episode Twelve : This is Me
  13. 13 Episode Thirteen : This is Me 2
  14. 14 Episode Fourteen : The Limit
  15. 15 Episode fifteen: blood is Thicker than Water.
  16. 16 Episode Sixteen : The Letter
  17. 17 Episode seventeen: Reply
  18. 18 Episode eighteen: what's Next?
  19. 19 Episode Nineteen: The Goodbye
  20. 20 Episode Twenty: The New Job
  21. 21 Episode Twenty one: Amira
  22. 22 Episode Twenty Two: Efisowa
  23. 23 Episode Twenty three: The Break up 💔
  24. 24 Episode Twenty Four: The Heartbreak 💔
  25. 25 Episode Twenty five: The Eclipse
  26. 26 Episode Twenty Six: A Step Further Away
  27. 27 Episode Twenty Eight : University of Oxford
  28. 28 Episode Twenty Nine: The Message
  29. 29 Episode Thirty : The Final Blow
  30. 30 Episode Thirty One: Let it go
  31. 31 Episode Thirty Two : Munnir
  32. 32 Episode Thirty Two : Mahdi
  33. 33 Episode Thirty Three: Zayed
  34. 34 Episode Thirty Four : Back to Square One
  35. 35 Episode Thirty Five : When Destiny Calls.
  36. 36 EpisodeThirtySix: Interesting
  37. 37 Episode Thirty Seven : The Dinner
  38. 38 Episode Thirty Eight : The Shadow
  39. 39 Episode Thirty Nine : The Shadow 2
  40. 40 Episode Forty :TheShadow 3
  41. 41 Episode Forty One : Born for This.
  42. 42 Episode Forty Two : Born for This
  43. 43 Episode Forty Three: America
  44. 44 Episode forty four : America 2
  45. 45 Episode Forty Five : The Rush
  46. 46 Episode Forty Six : The Repentance
  47. 47 Episode Forty Seven : Amir
  48. 48 Episode Forty Eight : Awkward
  49. 49 Episode Forty Nine : Ya Habeeb
  50. 50 Episode Fifty : Munir 2
  51. 51 Episode Fifty one : Mommy
  52. 52 Episode Fifty Two : The Journey
  53. 53 Episode Fifty Three : Daddy
  54. 54 Episode Fifty Four : Her Father's Daughter
  55. 55 Episode fifty five : Her Father's Daughter 2
  56. 56 Episode Fifty Six : What You Sow
  57. 57 Episode Fifty Seven : What You Sow 2
  58. 58 Episode Fifty Eight : I Missed You
  59. 59 Episode Fifty Eight : For You, Only You
  60. 60 Episode Sixty : The Prince
  61. 61 Episode Sixty One : Save the Date
  62. 62 Episode Sixty Two : The Manager
  63. 63 Episode Sixty Three : Amira 3
  64. 64 Episode Sixty Four : The Past and the Future
  65. 65 Episode Sixty Four : The Visitors
  66. 66 Episode Sixty Six : The Wedding
  67. 67 Episode Sixty Seven : The Wedding 2
  68. 68 Episode Sixty Eight : The Wedding Night
  69. 69 Episode Sixty Nine: The Wedding Night 2
  70. 70 Episode Seventy : The Wedding Night 3
  71. 71 Episode Seventy One : The Honeymoon
  72. 72 Episode Seventy Two : My Everything
  73. 73 Episode Seventy Three : His Father's Son
  74. 74 Episode Seventy Four : The Cook
  75. 75 Episode Seventy Five : The Emir
  76. 76 Episode Seventy Six : The Visitors
  77. 77 Episode Seventy Seven : Amina
  78. 78 Episode Seventy Eight : The Storm
  79. 79 Episode Seventy Nine : The Lightening and The Thunder
  80. 80 Episode Eighty : The Skeleton in The Closet
  81. 81 Episode Eighty one : The Skeleton in the Closet 2
  82. 82 Episode Eighty Two : The Light
  83. 83 Episode Eighty Three : The News
  84. 84 Episode Eighty Four : Little Love
  85. 85 Episode Eighty Five : Ibrahim
  86. 86 Episode Eighty Six : The Phone Call
  87. 87 Episode Eighty Seven : Riyadh
  88. 88 Episode Eighty eight :Khairat
  89. 89 Episode Eighty Nine : Khairat 2
  90. 90 Episode Ninety : His Mother's Son
  91. 91 Episode Ninety One : His Mother's Son 2
  92. 92 Episode Ninety Two and Three : Maldives 1 and 2
  93. 93 Episode Ninety Four : RIP
  94. 94 Episode Ninety Five : The Light
  95. 95 Episode Ninety Six : The New Bride
  96. 96 Episode Ninety Seven : The Real Prince
  97. 97 Episode Ninety Eight: My Baby
  98. 98 Episode Ninety Nine : New Little Love
  99. 99 Episode Hundred : Not The End.