Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 33

Episode Thirty Three: Zayed

Maimoon Book 1 Complete Hausa Novel 2,174 words 0 views Progress saved
Download Book

Tun daga ranar mahdi ya zama best friend dina, in har ina cikin asibiti to muna tare dashi, rannan muna zaune dashi nace "dan Allah Mahdi in tambayeka" ya cire glasses dinsa yana kallona yace "ina jinki" nace "dan Allah da gaske kai bahaushe ne? I mean biologically?" Straight yace min "no, babana adopting dina yayi" da sauri nace "yes!! I knew it" dariya yayi sosai har yana buga kafa sannan yace "wasa fa nake miki, serious ni bahaushe ne, why do you doubt it?" Sai naji kunya kuma nace "kawai dai ba kayi kama da hausawa ba" yayi shiru sannan yace "my mother was shuwa arab, ni kadai ta haifa Allah yayi mata rasuwa, so.... I am different duk a family, wannan shi yasa na taho kasar waje karatu, I want to feel like I belong, a gida kullum kamar alien nake ji na a cikin siblings dina" na sunkuyar da kaina inajin ba dadi, ace ka zama kamar bare a cikin 'yan'uwanka babu dadi, nace "am sorry about your mom, am sorry I asked you" yayi murmushi yace "chill, ba komai, it is better that you know".

Har gida na kai Mahdi ya gaishe da daddy, take daddy ya gane shi kuma yayi masa fada akan baya zuwa yana gaishe shi. Karatun mu muke yi sosai gar muka gama first year din mu a clinical, sanda muka je hutu gida kamar za'a chinye mu danyu, babu shiri daddy ya sako mu a jirgi muka dawo England. Munir da ya ganni kamar zai yi hauka, lallai ai shi baffa yayi masa alkawarin aure na. Inna da daada ma yanzu sun fara mita, a cewarsu ya kamata by now ace muna da tsayayyun samarin da muna gama makaranta sai aure. Four years kenan rabona da Ibrahim, tabbas har yanzu ina jinsa a raina amma sosai na rage tunaninsa. Sometimes na kan yi lissafin ko me yake yi yanzu? Sai kuma in yi sauri in kawar da tunanin saboda bana son in dawo wa da kaina aiki baya. Sai da muka shiga final year din clinical sannan na fara fahimtar cewa Mahdi is gradually falling in love with me. Yawan kira na a waya, kullum da weekend yana hanyar embassy gurina, ga yawan compliment, duk kayan da na saka sai yace nayi kyau, ko kuma yayi ta kallona a sace in mun hada ido ya yi sauri a dauke kai. He is really a nice guy and I really don't want to hurt him, amma sam ni bana jin sonsa a raina, I like him, but I don't love him.

Rannan muna daki da Hafsat da Amina, sai Amina ta dau waya ta tana ganin pictures kawai sai taga hotona da Mahdi. Tace "wow, moon wannan gayen fa?, gaskiya ya hadu ba karya" nace "wa kenan?" Ta juyo min screen din naga Mahdi nace "ohh, he is my friend, sunan sa Mahdi" tace "wait, don't tell me bahaushe ne" nace "dan kano ma kuwa, kanon ma cikin badala" ta bude baki tana kallona da mamaki sannan ta sake kallonsa, sai kuma tayi murmushi tace "something is really cooking here, wannan din za ki ce min wani friend din ki? Mu dai a fada mana ba sai tayi tsami ba" nayi dariya nace "am serious, we are just friends" tace "then something is definitely wrong with you, anya kuwa kina da lafiya, anya kuwa female hormones estrogen and progesterone suna aiki a jikin ki kuwa?" Nayi dariya kawai na share maganar ta, amma kuwa maganar ta tsaya min a rai, ba maganar Mahdi ba, maza in general, sam bani da interest a kan su, sam bana jin wani feeling idan naga wani namiji me kyau ko kuma in muna tare da wani namiji ballantana Mahdi wanda jinsa nake kamar Hafsa. Na tuna sanda muna tare da Ibrahim yadda nake jin attraction a tsakanin mu, why is it now gone? Yanzu dana kara girma ma ya kamata ace libido na ya karu amma it's like I have none. Na zauna ina lissafo Mahdi, komai bashi is perfect, sai kawai naji a raina ina comparing dinsa da Ibrahim. Mahdi is far more handsome than Ibrahim, more educated, more richer, his family is well known, kuma a kyawun dabi'a ma ban taba kama Mahdi da hali marar kyau ba, dan tunda muke bai taba taba ni ba. Amma why is it that in na tuna shi bana jin komai amma in na tuna Ibrahim nake jin pang a zuciyata, why must love be so cruel? Da haka na yanke shawarar cewa i must do something about Mahdi tun kafin inyi hurting dinsa.

Rannan yazo gida gurina kawai sai nace masa "ni kuwa Mahdi baka taba fada min wacce irin mata kake son aure ba" kamar wanda na sosa masa inda yake yi masa kaikayi nan ya fara lissafo min duk siffofi na da halaye na yana murmushi, yace duk sune abinda yake bukata a gurin matarsa. Ji nayi kamar hawaye zai zubomin dan na tabbatar da cewa she is head over heal in love with me. Sai da ya gama tsarinsa sannan yace "ke kuma fa" na kakalo murmushi nace "OK, inason namiji baki, kakkarfa, mai ilmi, mai addini.. " ya katseni yace "baki kuma? Why?" Na sake yin wani murmushin nace "tun ina yarinya haka kawai sai nake ganin kamar dark color is for men and fair color is for women, to har girma na sai ya kasance I am more attracted to darker men then fair men" murmushin fuskarsa naga yana subucewa, nayi sauri nace da alamar mamaki "oh God am so sorry Mahdi, you are very handsome the way you are, it's just my short coming and it's not as if you are in love with me, right? Na tambayeshi zuciyata na bugawa, ya sunkuyar da kansa kasa sannan ya girgiza kai yace "you are right, i just find it weird cewa ba kya son maza farare" ya hadiye wani abu a makogwaronsa yace "bara in tafi, see you tomorrow " bayan ya tafi na jima a gurin a zaune, I hated hurting him amma it's better this way, na dafe kaina nace "ohh Ibrahim, what have you done to me? Kai kana can kayi auren ka ni kuma I can't even have a boyfriend"

Tun daga ranar muka koma 'yar wasan buya da Mahdi, duk sai naji na takura saboda ban saba da haka ba.
Cikin 'yan kwanaki naga Hafsat ta fara zama mysterious, nasan da abinda take boyewa amma na kyale ta nace in tayi tsami maji. Rannan kuwa na dawo daga asibiti kawai sai na hango ta a mota ita da wani, can nesa da gate din gidan mu, na saka driver ya sauke ni a gate, ni ma yau sai na gwada mata sa'do irin wanda take yi wa mutane. Ina karasa wa kuwa na tabbatar ita din ce da wani, harara ta watso min, na dauke ido na daga kanta na kalli wanda suke tare, ai bansan sanda na bude ido, baki, hanci kai har da kunne ina kallonsa ba. Dariya yake yimin wholeheartedly sannan yace "so, the beautiful one is here" Hafsat tace min da fulatanci "to rufe bakin haka" na mayar da bakina kuwa na rufe, nace mata nima da fulatanci "kamar balarabe nake gani?" Bata bani amsa ba ta shareni. Tabbas sanda nace duk saurayin da Hafsat tace tana so to azo a ganshi da gaske nake, amma sam banyi tsammanin irin wannan ba. Balarabe ne, kuma daga ganin shi full blood balarabe ne, ga gayu da cikar kamala irin na larabawa, zai kai around thirty something years. Fuskarsa cike da kyau da annuri irinna larabawa. Yasa hannu ya bude min kofar baya yace cikin kyakykyawan turancin sa "shigo, waje akwai zafi sosai" ba musu na zagaya na zauna. Ina zama yace "my name is Zayed, and i am going to be your brother in law insha Allah" na ce excitedly "Ameen, sunana... " ya katse ni "Maimunatu, ana ce miki Moon, shekara daya Hafsat ta baki and you are her only sister... " nan yayi ta bani labari akaina har abubuwan da nake so da wanda bana so, nace " ya akayi ka sani?" Ya kalli Hafsat yace "kullum sai anyi min hirar ki, Moon this, Moon that, kullum maganar kenan, inama zan samu asoni kamar yadda ake sanki" Hafsat ta dafe kanta tace "ohh God, am out of here" na bude motar sannan tace min, "to parrot, in kin gama surutun ki shigo gida" ko kallon sa bata yi ba ta rufe kofar ta kama hanyar gida. Tana tafiya nima na fito, amma maimakon inyi hanyar gida nima sai na zagayo na dawo seat din gaba in da ta tashi na zauna, nan muka kama hira dashi, na fahimci shima yana da surutu da tsokana. Ya gaya min cewa shi mutumin saudi arabia ne, aiki ne ya kawo shi England, shine director na pediatric department na asibitin da muke clinical, wato ogan Hafsat ne, be taba aure ba saboda be taba ganin wacce tayi masa completely ba sai akan Hafsat. Nan nima nace masa "kasan kuwa Hafsat bata taba saurayi ba, ko da kuwa saurayin wasa ne" yace "really?, please bani labarin ta? Nan na gyara zama na fara kwararo masa labarin Hafsat tun muna yara, muna nan har aka kira sallar magrib, sam bai gaji da hirar ba nima kuma ban gaji ba, a karshe nace masa "the bottom line is, she is very annoying but she is the best sister that I could ever ask for"

Tun daga ranar kullum Zayed yazo sai ya neme ni munyi hira, tun Hafsat tana tashi in nazo har ta hakura take zama. Na fahimci cewa suna matukar san junan su kuma ni a idona sunyi bala'in dacewa. Zayed yayi min a matsayin brother in law.

Muna kokarin gama clinical din mu ne rannan da weekend naga Hafsat kamar hankalinta a tashe, nayi niyyar in rabu da ita sai kuma dai na kasa, na tambayeta, har ta shareni sai kuma ta dawo kusa dani ta zauna. Tace "Zayed ne zai zo ya gaishe da daddy yau" nan da nan na washe baki na da murna nace "Allah?, to kuma menene abin bata ran ke da zakiyi murna" tace "I am scared moon, gani nake kamar za'a samu matsala, and I really love Zayed you know" sosai na gane yadda take ji saboda nima na taba kasancewa a irin exact position din ta, nan na shiga lallabata ina cewa "daddy ba zai taba kin someone like Zayed ba". Wajen yamma yazo, Hafsat kasa fita tayi dan gabaki daya jikin ta karkarwa yake yi. Sai ni na fita na shigo dashi main palo sannan naje na gayawa daddy yayi bako a palo, sai da daddyn ya fito sannan na tashi na dawo daki, akan sallaya na tarar da Hafsat tana ta faman jan charbi, har dariya taso ta bani amma na dake, kawai na tuno ranar da Ibrahim yazo gidan mu a Abuja yadda securities suka ringa maltreating dinsa, Zayed kuwa yanzu yana zuwa har wani bashi guri suke yi suna gaishe shi, a raina nace rayuwa kenan, if you have money you have everything. Muna nan zaman jiran sakamako ni har na fara bacci naji Hafsat tana kiran sunana, na tashi na hango ta akusa da window, nima naje na leka, Zayed, daddy da ya Walid muka hango suna tafiya hanyar gate, daga ganin yadda suke cikin nishadi kasan an samu nasara, Zayed bakinsa har kunne. Hafsat ta rungume ni itama tana murna, kawai sak naji kwalla a idona. Inama Ibrahim ne muma hakan ta kasance damu. Su daddy basu jima da dawowa cikin gida ba ya kirani a waya yace muzo ni da Hafsat. Hafsat duk kunya ta ishe ta. Muna zuwa kuwa kowa ya fara tsokanarta wai ta dauko balarabe dan take yin aikin Hajji da umra a free. Sai da akayi shiru sannan daddy yace " Hafsat naga sakon ki, kuma ni dai a ra'ayina ni da mommyn ki munyi na'am da zabin ki. Amma na gaya masa in kun gama wannan session din zamu je Nigeria sai ya saka time ya turo magabatan sa sune 'yalleman su gaida baffa da kawunnan ki, su zasu bada auren ki bani ba, suma kuma ina saran insha Allah ba za'a samu matsala dasu ba. Allah ya sanya alkhairi" gaba daya muka ce "Ameen" ya Walid ya kalleni yace "saura ke" nayi sauri na sunkuyar da kaina. Daddy yace "eh Maimunatu saura ke. Ya kuke ciki ne da wannan farin yaron dan Datti Sufyan?" Nayi sauri na dago kaina nace cikin in ina "ba.. ba komai daddy" yace "bangane babu komai ba, dama ba saurayin ki bane?" Na girgiza kaina, yace " to maimunatu, kinsan dai akwai maganar Munnir har yanzu, kuma ni Allah ya sani bana son hadin ku da munnir, amma babu yadda zanyi indai har baki fito da miji ba kafin nan kafin ku kammala karatunku" Mommy tayi ajiyar zuciya tace "ni na rasa gane kan Moon wallahi, kamar wadda take gudun samarin, who would have thought Hafsat zata riga Moon samun miji

Table of Contents

Chapters

99 chapters
  1. 1 Episode One : The Beginning of the Beginning
  2. 2 Episode Two: Meet my Family
  3. 3 Episode Three: Loved by All
  4. 4 Episode Four: Moon's Sister
  5. 5 Episode five: The Strangers
  6. 6 Episode six: The Challenge
  7. 7 Episode Seven: The Thin Tall Man
  8. 8 Episode Eight: The New Imam
  9. 9 Episode Nine: Give Me a Chance
  10. 10 Episode Ten: I Don't Know
  11. 11 Episode Eleven : The Protector
  12. 12 Episode Twelve : This is Me
  13. 13 Episode Thirteen : This is Me 2
  14. 14 Episode Fourteen : The Limit
  15. 15 Episode fifteen: blood is Thicker than Water.
  16. 16 Episode Sixteen : The Letter
  17. 17 Episode seventeen: Reply
  18. 18 Episode eighteen: what's Next?
  19. 19 Episode Nineteen: The Goodbye
  20. 20 Episode Twenty: The New Job
  21. 21 Episode Twenty one: Amira
  22. 22 Episode Twenty Two: Efisowa
  23. 23 Episode Twenty three: The Break up 💔
  24. 24 Episode Twenty Four: The Heartbreak 💔
  25. 25 Episode Twenty five: The Eclipse
  26. 26 Episode Twenty Six: A Step Further Away
  27. 27 Episode Twenty Eight : University of Oxford
  28. 28 Episode Twenty Nine: The Message
  29. 29 Episode Thirty : The Final Blow
  30. 30 Episode Thirty One: Let it go
  31. 31 Episode Thirty Two : Munnir
  32. 32 Episode Thirty Two : Mahdi
  33. 33 Episode Thirty Three: Zayed
  34. 34 Episode Thirty Four : Back to Square One
  35. 35 Episode Thirty Five : When Destiny Calls.
  36. 36 EpisodeThirtySix: Interesting
  37. 37 Episode Thirty Seven : The Dinner
  38. 38 Episode Thirty Eight : The Shadow
  39. 39 Episode Thirty Nine : The Shadow 2
  40. 40 Episode Forty :TheShadow 3
  41. 41 Episode Forty One : Born for This.
  42. 42 Episode Forty Two : Born for This
  43. 43 Episode Forty Three: America
  44. 44 Episode forty four : America 2
  45. 45 Episode Forty Five : The Rush
  46. 46 Episode Forty Six : The Repentance
  47. 47 Episode Forty Seven : Amir
  48. 48 Episode Forty Eight : Awkward
  49. 49 Episode Forty Nine : Ya Habeeb
  50. 50 Episode Fifty : Munir 2
  51. 51 Episode Fifty one : Mommy
  52. 52 Episode Fifty Two : The Journey
  53. 53 Episode Fifty Three : Daddy
  54. 54 Episode Fifty Four : Her Father's Daughter
  55. 55 Episode fifty five : Her Father's Daughter 2
  56. 56 Episode Fifty Six : What You Sow
  57. 57 Episode Fifty Seven : What You Sow 2
  58. 58 Episode Fifty Eight : I Missed You
  59. 59 Episode Fifty Eight : For You, Only You
  60. 60 Episode Sixty : The Prince
  61. 61 Episode Sixty One : Save the Date
  62. 62 Episode Sixty Two : The Manager
  63. 63 Episode Sixty Three : Amira 3
  64. 64 Episode Sixty Four : The Past and the Future
  65. 65 Episode Sixty Four : The Visitors
  66. 66 Episode Sixty Six : The Wedding
  67. 67 Episode Sixty Seven : The Wedding 2
  68. 68 Episode Sixty Eight : The Wedding Night
  69. 69 Episode Sixty Nine: The Wedding Night 2
  70. 70 Episode Seventy : The Wedding Night 3
  71. 71 Episode Seventy One : The Honeymoon
  72. 72 Episode Seventy Two : My Everything
  73. 73 Episode Seventy Three : His Father's Son
  74. 74 Episode Seventy Four : The Cook
  75. 75 Episode Seventy Five : The Emir
  76. 76 Episode Seventy Six : The Visitors
  77. 77 Episode Seventy Seven : Amina
  78. 78 Episode Seventy Eight : The Storm
  79. 79 Episode Seventy Nine : The Lightening and The Thunder
  80. 80 Episode Eighty : The Skeleton in The Closet
  81. 81 Episode Eighty one : The Skeleton in the Closet 2
  82. 82 Episode Eighty Two : The Light
  83. 83 Episode Eighty Three : The News
  84. 84 Episode Eighty Four : Little Love
  85. 85 Episode Eighty Five : Ibrahim
  86. 86 Episode Eighty Six : The Phone Call
  87. 87 Episode Eighty Seven : Riyadh
  88. 88 Episode Eighty eight :Khairat
  89. 89 Episode Eighty Nine : Khairat 2
  90. 90 Episode Ninety : His Mother's Son
  91. 91 Episode Ninety One : His Mother's Son 2
  92. 92 Episode Ninety Two and Three : Maldives 1 and 2
  93. 93 Episode Ninety Four : RIP
  94. 94 Episode Ninety Five : The Light
  95. 95 Episode Ninety Six : The New Bride
  96. 96 Episode Ninety Seven : The Real Prince
  97. 97 Episode Ninety Eight: My Baby
  98. 98 Episode Ninety Nine : New Little Love
  99. 99 Episode Hundred : Not The End.