Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 55

Episode fifty five : Her Father's Daughter 2

Maimoon Book 1 Complete Hausa Novel 3,040 words 0 views Progress saved
Download Book

Kowa a gurin sakin baki yayi yana kallon Sultan, hatta daddy rasa mai zaice masa yayi, ya jima yana kallon sa shi kuma Sultan ya sunkuyar da kansa kasa, a zuciyarsa yana wishing ina ma dai zai iya kuka, maybe in hawaye ya fito masa zai ji sanyi a zuciyarsa, wannan mutumin da yake tsaye a kansa is his only chance to happiness, idan yace yes to shi kam ya samu duk wani buri nasa na rayuwa, in yace no kuma tamkar a saka full stop ne a rayuwar sultan. Daddy ya sauke ajjiyar zuciya yace "wannan shine dalilin ka na shigo min gida ka tayar min da hayaniya? Wannan shine dalilinka na dukan securities dina?" Sultan ya kuma sunkuyar da kansa yana jin bugun zuciyarsa yana karuwa. Daddy yace "tambayarka nake yi fa?" Sultan ya dago kai ya kalli daddy da jajayen idanunsa yace "daddy ba zasu bar ni in ganka ba ne. And I must see you. Tun a England muka shirya da Moon za ta kawo ni gurinka, bamu samu dama ba, anan ma muka sake shirin zuwa ganin ka shima still bamu dace ba. This is the only way for me to see you" da mamaki daddy yace "ita moon dince ta amince maka kazo gurina ka nemi auren ta?" Sultan ya gyada kansa yace "yes daddy, kuma yanzu I don't even know where she is" daddy ya jinjina maganar a ransa, in dai har Moon ce ta turo shi gurinsa then she must have her reasons, maybe reasons dinta yana daga cikin dalilan da yasa mommy ta dauke ta. Ya juya ya kalli Walid a gefensa yace "Walid shigo dashi ciki" ya juya ya koma palo, walid ya bishi da kallon mamaki amma shi yasan bai isa yayi masa musu ba, yiwa iyaye musu baya daga cikin tarbiyyar da aka basu. Ya mika wa sultan hannu da niyar ya taimaka nasa ya tashi tsaye, sultan ya watsa masa harara ya mike a hankali yadda su biyu kadai zasu ji yace "zan dawo kanka ne" bai jira walid yayi masa jagora ba ya bi bayan daddy. Ya tarar palo babu kowa, da alama daddy sama ya hau, akan carpet ya zauna ya harde kafafunsa ya zabga tagumi. He is ready to wait to awa nawa ne, ko kwana nawa ne, indai har at last daddy zai saurare shi. Walid ya shigo ya samu guri can nesa da Sultan ya zauna, babu wanda yace wa kowa komai har daddy ya sauko, ya yi wanka ya chanza kaya sai kamshi yake, Sultan ya kalli kayan jikinsa, sun chukurkude saboda fadan da yayi da securities, babu abinda yake sai warin gumi, ya daga kafada bai damu ba.

Daddy ya zauna akan kujera yana studying Sultan. He is a perfect mixture of his father and mother. Fuskarsa sak ta Khairat sai dai kawai shi namiji ne ita mace, sai kuma duhun fata da ya fita saboda yayi mix da duhun fatar babansa, kirar jikinsa kuma sak na babansa lokacin yana age dinsa. Daddy yana hango su a idonsa suna wayo tare ko'ina a Oxford. What has gone wrong tsakanin su? Yayi gyaran murya yace "bismillah malan Abubakar, fara daga farko, a ina ka hadu da 'yata kuma menene a tsakanin ku?" Sultan ya danyi shiru yana controlling emotions dinsa sannan ya fara bada labari, komai sai da ya fada wa daddy, da boye boyen da suke yi saboda tana tsoron kawo shi gida, rayuwar su a England da America, amma duk bluntness din sultan bai bada labarin toilet experience dinsu ba, ya bada labarin plans din da suka ringa hadawa na zuwa ganin daddy amma ana samun sabani, ya bada labarin matsalar da suka samu akan project dinta da fushin da yayi ya tafi bar ita kuma ta bi Amir ya kaita gurin shi, ganin da munir yayi musu da zuwan Walid. Sai da ya gama kaf sannan yace "dan Allah daddy kar ka raba mu wallahi mutuwa zanyi, I have no body a duniyar nan sai ita" daddy ya kalle shi a nutse yace "you look like your mother" Sultan ya dago kansa da sauri ya kalli daddy yana tunanin anya kunnen sa ba karya yayi masa ba, sam babu wasa a fuskar daddy, ya sake cewa "kamar ku daya, sai dai ta fika fari, ta fika kuma hankali da nutsuwa" da rarrafe sultan ya karaso gaban daddy ya rike kafarsa yace "you know my mother?" Daddy ya gyara zama yana kallonsa yace "ba sosai ba, dan bamu taba magana da ita ba, amma na san ta kuma ina ganin ka nasan dan ta ne kai. Oxford sukayi karatu ita da babanka, lokacin yana kamar ka. Baban ka was exactly like you, he was a rogue also. A gang leader na 'ya'yan masu kudi" daddy yayi murmushi yana tuno rayuwarsu ta makaranta yacigaba da cewa "ni lokacin dan talakawa ne dan haka bana cikin su, ina dai hangen su suna yawo da motoci a cikin makaranta. He was so energetic, so stubborn like you. Duk sanda na ganshi a TV yanzu sai inyi ta mamakin yadda akayi ya koma haka" sultan ya saki baki yana mamaki, bai taba tsammanin cewa da akwai wani abu na halayya daya dangantashi da babansa ba. A hankali yace da daddy, "please tell me about my mother" daddy yace "kamar yadda na gaya maka, ban santa sosai ba, nasan dai sunanta khairat, and i always say, she is the most beautiful woman I have ever seen. She is full blood Arab. Tana da nutsuwa sosai, kuma daga ganin ta daga babban gida ta fito. They were so much in love ita da Sadiq. I remember always thinking they look odd, ita so fair shi kuma so dark, ita gentle shi stubborn, ita Arab shi Hausa. Amma duk 'ya'yan masu kudi. Muna gama PhD suka bar Oxford, ni kuma na zauna na kama lecturing a can. Ban taba dauka sun rabu ba. Shi yasa nayi mamaki da kace min baka san mamanka ba, and you said something about your father hating you. Ban gane me kake nufi ba. Why will your father hate you?" Sultan ya girgiza kansa yace "nima ban sani ba fa" nan ya fara bawa daddy labarin rayuwarsa tun sanda yayi wayo har zuwa haduwarsa da Moon. Duk abin ya daure wa daddy kai. He needs time to think about it. Sultan ji yayi kamar zai hadiye daddy, tunda yake babu wanda ya taba bashi labarin mahaifiyarsa, he only know her name shima kuma a birth certificate dinsa ya gani, yanzu yasan she is Arab, yayi murmushi, he always have a thing for Arabs, duk da ba wai iya larabcin yayi ba amma duk sanda yayi sai aji kamar a bakinsa aka rada shi ashe its in his blood. Ina ma dai one day zai ganta? Sai kuma ya cire maganar daga ransa, tunda har ta iya cire shi daga jikinta ta ajiye shi ta tafi without a second look to shima dan me zai nemeta. Suna tare da daddy har magrib sannan suka je masjid tare suka yi sallah daga nan daddy yace masa "kaje gida sultan, give Walid your number, I will think about maganar ka and I will call you" daga haka ya shige gida, Sultan yaji babu dadi, he don't want to go home, to menene a gidan ma in yaje? Shi da daddy zai barshi ma anan gidan zai zauna, it will make him feel closer to Moon and also to his Mom.

Tunda mommy taga Daddy ya shigo da Sultan palo ta hau sama ta shige bedroom din ta, this is exactly abinda yasa ta dauke moon, tasan halin daddy, he is soft hearted like moon, da mutum ya zauna ya tsara su ya nuna musu cewa shi abin tausayi ne shikenan. People are not to be trusted, especially people like sultan. Dan haka ta yanke shawarar ba zata gaya wa kowa inda Moon ta ke ba har sai daddy ya fahimci cewa Sultan is totally not to be trusted. A bangaren daddy kuwa bayan sun rabu da sultan ya hau samansa ya tarar da abinci sa a dining dinsa, an jera komai amma babu mommy a gurin, bata taba yi masa haka ba kullum tare suke cin abinci in dai yana gari dan haka abincin kadan yaci yaji ya koshi. Ya kira wayarta taki dauka, mata kenan, shi a ganinsa itace fa mai laifi, ita ta boye masa yarinya amma kuma itace mai yin fushi? Shi me yayi mata? Abu daya ya saka zai rabu da ita shine yasan babu yadda za'ayi tayi harming Moon dan haka kamar yadda tace she is safe ya yarda she is safe din. Maganganunsu da Sultan ya fara dawowa dasu baya yana bin su daya bayan daya, maganar farko daya kamata yayi looking into itace ta yadda Moon ta zabi Sultan har tace ya zo yaga babanta, yasan halin Moon kuma ya yadda da ita, in dai har tace ta zabi sultan than there is something about him da ta gani, something good. Ya shiga bedroom dinsa ya dauko laptop dinsa ya kunna, the first place da ake samun information ya shiga, internet, amma duk abinda ya gani akan Sultan are not good, but why will Moon choose him? Shi abinda ya gani ma zai iya cewa gwara Munir akan Sultan, ya girgiza kansa, hakkin ubane ya samo wa 'yarsa miji na gari, yes Sultan indai labarin daya bashi gaskiya ne to negligence ya jawo ya zama abinda ya zama, amma wannan ba zai saka shi kuma ya dauki 'yarsa ya bashi ba. Emails dinsa ya duba yaga sun taru, kwana biyun nan he was very busy baya samun duba mails dinsa. Ya tashi yaje yayi sallah isha ya dawo, daya bayan daya ya fara bin emails din yana karantawa, bai jima ba yazo kan nata, "please daddy look into this" ya duba date din ya ga ranar da tabi Sultan bar ne amma da safe, ya bude document din data yi attaching, it is an amazing write up akan sultan, ta fara da tarihinsa, almost duk labarin da sultan ya bashi sazu, tayi bayanin duk bad characters dinsa, so she knows duk mugayen halayensa amma ta zabe shi? Sai kuma ta fara wani bayanin da daddy bai gane ba, a totally different side of Sultan, tana bayanin wadansu halayen wanda babu wanda zaice sultan yana dasu, tana dauko kowanne mugun hali data fada a baya tana justifying abinda yasa ya zama haka, tayi bayani akan yadda yayi rayuwa a america da irin yawan mutanen da ya rike tun a lokacin da ya kamata shi kansa ace rike shi ake yi, she then mentioned the orphanages, anguwannin talakawa a Abuja da Sultan ya rike, he is a hero to them, mutanen da ya samarwa aiki, yaran da ya saka a makaranta, talakawan da yake ciyarwa kuma duk ba tare daya nemi ko da godiya ne daga gare su ba, tace "he told me that doing something good makes him feel good, and that's what he wants, not people's praises" a karshen rubutun kuma tace "I believe this character a good person, but this life conditions makes him look bad in his eyes and the eyes of other people, but deep inside him he is good, very good"

Daddy ya zama speechless, ya rasa tunanin me zaiyi, internet ya koma ya fara searching abubuwan data fada akan sultan amma bai ga ko daya ba, me hakan yake nufi? Amma yasan 'yarsa, she will not lie like this, especially not to him, amma me yasa babu wanda yasan sultan da wadannan halayen data lissafa sai ita kadai? Sai kuma yayi tunanin halin mutane, they only see what's on the surface, dan haka kallo daya zasu yi wa Sultan suyi tagging dinsa as a bad person shi kenan kuma, su kuma wadanda yake good to mutane ne da basu da say a cikin al'umma, dadin dadawa kuma shi kansa sultan din bai yarda cewa shi mutumin kirki bane kuma he is set on anything da zai bata wa babansa suna. Sai da kan daddy ya fara ciwo sannan ya tashi ya je ya kwanta, har yanzu mommy bata zo ba, ya yanke shawarar he is going to ignore her for now, har sai ya gama binciken sa akan sultan.

Washe gari sai 12 ya sauko saboda jiya bai yi wani baccin kirki ba. Kuma yau ma tunda ya tashi yake making phone calls na meeting din daya shirya, yana yin breakfast ya dauki Walid a mota suka fita. Farko court din da mommy ta shigar da kara ya fara zuwa yace an janye karar dama misunderstanding ne kuma an samu fahimta. Private investigators ya hada har mutum goma, task din su shine yana son sanin komai akan Sultan, komai, including labarin rabuwar iyayensa. Sun charging dinsa kudi da yawa amma money is nothing to daddy dan haka ya signing musu check, half now half kuma sai sun gama aikin. Exactly one week aka kawo masa report dinsa, ranar har gari ya waye bai runtsa ba, hatta school report din duk kanin makarantun da Sultan yayi sai da aka kawo wa daddy. Komai na Sultan sai da daddy ya sani har abubuwan da ita kanta Moon bata sani ba. Sanda ya karanta ainahin dalilin rabuwar iyayen Sultan sai da ya dafe kansa yace "ya Salaam" gari na wayewa ya kira Walid yace "ka kira Sultan kace ina son ganin sa da yamma"

A bangaren sultan kuwa tun da ya bar gurin daddy gida ya koma ya shiga part dinsa ya kori kowa ya rufe kofa, he misses Moon sosai, dama zai samu ko muryarta yaji da yaji dadi, amma babu abinda zai yi dole ya jira kamar yadda daddy yace masa, tunda yace he will call then he will call din tunda baiyi kama da karamin mutun ba. Matsalar daya ce shine bai san abinda zai gaya masa in ya kira shi din ba, it will either be the end of his life or the beginning of his life. Jiran kuma anan za'a samu matsala, jira bashi da dadi ballantana ga mutum mai zuciya irin ta sultan. Kwana daya kawai duk yabi ya tayar da hankalinsa, he badly want a drink amma yana tsoron kar yasha daddy kuma ya kira shi, ko kuma ace moon tazo, ya tuna rokon da tayi masa akan kar yasha, menene ma abinda tace masa yayi instead? Ce masa tayi ya karanta alqurani. Ya tashi a hankali ya bude drawer da yake zuba books dinsa, anan yake aje alquranin sa tun wanda kakansa ya bashi, yana yawan daukoshi ya karkade ya mayar ya ajiye, karantawar ne dai baya yi. Ya dauko ya dawo kan gado ya zauna ya bude page din farko ya karanta fatiha. Ita kadai ya karanta yaji wani dadi a ransa, ya tuno sanda yana yaro a gurin kakansa wani lokacin tare suke karatu saboda kullum kakansa yana ce masa yana son yaji yana karatu saboda yadda yake lankwasa harshensa irin na larabawa. Ya ajiye al'quranin ya shiga toilet ya yo alwala ya zo ya shimfida sallaya yayi sallah raka'a biyu, sai kawai ya samu kansa da yin addu'a, abinda da ba yayi, ya roki Allah ya kawo haske a cikin rayuwarsa duniya da lahira, ya kuma yiwa Moon addu'a Allah ya kare ta a duk inda take sannan kuma Allah ya sa allkhairi a al'amuran su baki daya, daga nan ya jawo alquraninsa duk surorin saman sun bace masa duk da cewa da ya iya amma rashin karantawa yasa duk sun zube, na kasan dai ya iya su sosai saboda kullum yana karantawa a sallah. Nutsuwar da ya samu sai yaji tafi wacce yake samu idan yasa giya, ji yake kamar wani assurance na cewa everything will be OK. Tun daga ranar ya samu abinyi, baya zuwa ko ina yana daki sai dai a kawo masa abincinsa nan, kullum sai Amir ya shigo ya duba shi su dan taba hira ya fita, sosai Amir yaji dadin changin abokin nasa dan bai dauka zai taba zama calm akan rabuwarsu da Moon ba, Sultan ya bawa Amir labarin duk yadda sukayi da daddy nan suka hadu zaman jiran kiran daddy. Sai da akayi kwana takwas sannan kiran ya shigo, lokacin amir yana game da wayar Sultan, wayar ta fara ringing amir yace "wow, is this who I think it is?" Sultan ya kalli screen din yaga 'Walid' da sauri ya warce wayar ya daga da sallama, ba tare da Walid ya amsa ba yace "Daddy says to come after Asr" daga nan a katse wayar. Sultan ya jima yana kallon wayar a hannunsa, duk jiran da yake yi kuma sai yaji gabansa yana faduwa. Ya gayawa Amir abinda walid yace, ya tashi ya fara neman kayan sakawa, sai yau yayi nadamar rashin dinka manyan kayan da bayayi, da sam bai damu da duk irin shigar da yake yi ba amma yau sai yaji yana son yayi shigar kirki, da kyar ya samu kaya wadanda basu kama jikin sa ba. Amir yace zai rakashi, nan sultan ya kora masa warning kar ya saka matsatstsun kaya kuma ya tabbatar baya warin sigari, baki kawai Amir ya saki yana kallon Sultan, he is really changing, yace "since when did you care wanne kayan na saka?" Sultan ya bata rai yace "just do as I say kuma ka tabbatar ka cire wannan sarkar in ba haka ba bazan tafi da kai ba"

Da yamma suka je gidan, a palon baki aka sauke su aka kawo musu drinks da snacks, sultan da baya barin abinci amma yau sai ya samu kansa da kasa cin komai, so yake kawai daddy yazo yaji abinda zai ce masa. Basu jima ba daddyn ya fito cikin shiga ta alfarma kamar kullum, yana shigowa suka mike tsaye duk har sai da ya zauna sannan suka zauna suma tare da gaishe sa, ya amsa ba yabo ba fallasa sannan ya kalli Amir yace "Amir ko?" Amir ya gyada kansa, haka kawai yaga daddyn yayi masa kwarjini. Shima daddy ya karanta labarinsa da duk abinda Sultan yayi masa. Ya jima yana kallon Sultan wanda ya sunkuyar da kansa yana jiran abinda zaice, can daddy ya bude baki yace "Sultan, zaka iya dawowa nan gidan ka zauna a gurina?"

Table of Contents

Chapters

99 chapters
  1. 1 Episode One : The Beginning of the Beginning
  2. 2 Episode Two: Meet my Family
  3. 3 Episode Three: Loved by All
  4. 4 Episode Four: Moon's Sister
  5. 5 Episode five: The Strangers
  6. 6 Episode six: The Challenge
  7. 7 Episode Seven: The Thin Tall Man
  8. 8 Episode Eight: The New Imam
  9. 9 Episode Nine: Give Me a Chance
  10. 10 Episode Ten: I Don't Know
  11. 11 Episode Eleven : The Protector
  12. 12 Episode Twelve : This is Me
  13. 13 Episode Thirteen : This is Me 2
  14. 14 Episode Fourteen : The Limit
  15. 15 Episode fifteen: blood is Thicker than Water.
  16. 16 Episode Sixteen : The Letter
  17. 17 Episode seventeen: Reply
  18. 18 Episode eighteen: what's Next?
  19. 19 Episode Nineteen: The Goodbye
  20. 20 Episode Twenty: The New Job
  21. 21 Episode Twenty one: Amira
  22. 22 Episode Twenty Two: Efisowa
  23. 23 Episode Twenty three: The Break up 💔
  24. 24 Episode Twenty Four: The Heartbreak 💔
  25. 25 Episode Twenty five: The Eclipse
  26. 26 Episode Twenty Six: A Step Further Away
  27. 27 Episode Twenty Eight : University of Oxford
  28. 28 Episode Twenty Nine: The Message
  29. 29 Episode Thirty : The Final Blow
  30. 30 Episode Thirty One: Let it go
  31. 31 Episode Thirty Two : Munnir
  32. 32 Episode Thirty Two : Mahdi
  33. 33 Episode Thirty Three: Zayed
  34. 34 Episode Thirty Four : Back to Square One
  35. 35 Episode Thirty Five : When Destiny Calls.
  36. 36 EpisodeThirtySix: Interesting
  37. 37 Episode Thirty Seven : The Dinner
  38. 38 Episode Thirty Eight : The Shadow
  39. 39 Episode Thirty Nine : The Shadow 2
  40. 40 Episode Forty :TheShadow 3
  41. 41 Episode Forty One : Born for This.
  42. 42 Episode Forty Two : Born for This
  43. 43 Episode Forty Three: America
  44. 44 Episode forty four : America 2
  45. 45 Episode Forty Five : The Rush
  46. 46 Episode Forty Six : The Repentance
  47. 47 Episode Forty Seven : Amir
  48. 48 Episode Forty Eight : Awkward
  49. 49 Episode Forty Nine : Ya Habeeb
  50. 50 Episode Fifty : Munir 2
  51. 51 Episode Fifty one : Mommy
  52. 52 Episode Fifty Two : The Journey
  53. 53 Episode Fifty Three : Daddy
  54. 54 Episode Fifty Four : Her Father's Daughter
  55. 55 Episode fifty five : Her Father's Daughter 2
  56. 56 Episode Fifty Six : What You Sow
  57. 57 Episode Fifty Seven : What You Sow 2
  58. 58 Episode Fifty Eight : I Missed You
  59. 59 Episode Fifty Eight : For You, Only You
  60. 60 Episode Sixty : The Prince
  61. 61 Episode Sixty One : Save the Date
  62. 62 Episode Sixty Two : The Manager
  63. 63 Episode Sixty Three : Amira 3
  64. 64 Episode Sixty Four : The Past and the Future
  65. 65 Episode Sixty Four : The Visitors
  66. 66 Episode Sixty Six : The Wedding
  67. 67 Episode Sixty Seven : The Wedding 2
  68. 68 Episode Sixty Eight : The Wedding Night
  69. 69 Episode Sixty Nine: The Wedding Night 2
  70. 70 Episode Seventy : The Wedding Night 3
  71. 71 Episode Seventy One : The Honeymoon
  72. 72 Episode Seventy Two : My Everything
  73. 73 Episode Seventy Three : His Father's Son
  74. 74 Episode Seventy Four : The Cook
  75. 75 Episode Seventy Five : The Emir
  76. 76 Episode Seventy Six : The Visitors
  77. 77 Episode Seventy Seven : Amina
  78. 78 Episode Seventy Eight : The Storm
  79. 79 Episode Seventy Nine : The Lightening and The Thunder
  80. 80 Episode Eighty : The Skeleton in The Closet
  81. 81 Episode Eighty one : The Skeleton in the Closet 2
  82. 82 Episode Eighty Two : The Light
  83. 83 Episode Eighty Three : The News
  84. 84 Episode Eighty Four : Little Love
  85. 85 Episode Eighty Five : Ibrahim
  86. 86 Episode Eighty Six : The Phone Call
  87. 87 Episode Eighty Seven : Riyadh
  88. 88 Episode Eighty eight :Khairat
  89. 89 Episode Eighty Nine : Khairat 2
  90. 90 Episode Ninety : His Mother's Son
  91. 91 Episode Ninety One : His Mother's Son 2
  92. 92 Episode Ninety Two and Three : Maldives 1 and 2
  93. 93 Episode Ninety Four : RIP
  94. 94 Episode Ninety Five : The Light
  95. 95 Episode Ninety Six : The New Bride
  96. 96 Episode Ninety Seven : The Real Prince
  97. 97 Episode Ninety Eight: My Baby
  98. 98 Episode Ninety Nine : New Little Love
  99. 99 Episode Hundred : Not The End.