Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 97

Episode Ninety Eight: My Baby

Maimoon Book 1 Complete Hausa Novel 3,284 words 0 views Progress saved
Download Book

Pre-eclampsia rare ciwo ne na masu tsohon ciki. Shine ciwon da yake saka mata convulsions (jijjiga) during labor. Alamominsa sune matsanancin hawan jini, kumburi, jiri, matsanancin ciwon kai, sensitivity to light, blurred visions etc. Matan da suke at risk of samun ciwon sune wadanda already suke da hawan jini kafin su samu ciki, wadanda mahaifiyar su ko sister din su ta taba yi, yara kanana da suka samu ciki da wuri ko kuma manya wadanda shekarun su suka ja sosai. In kina da ciki kuma kika ga kina da wadan nan alamomin dana lissafa a sama to kada ki yarda ki fara labor, it is very deadly, za'a iya rasaki ko babyn ko duk ku biyun, ko kuma ki samu wani mugun ciwon, wani lokacin har hauka ake haduwa dashi. In baiyi tsanani ba kuma cikin ki bai tsufa sosai ba, ana iya control dinsa, in yayi tsanani best solution shine ki tafi asibiti ayi miki aiki a cire babyn. Shikenan.
Na rintse idona ina lissafa condition dina, a take na yanke shawara. Na bude idon na sauke su akan sultan, a hankali nayi magana "sultan stop the car" ya dan kalle ni yaga am serious sai yasa signa yayi packing a gefen titi. Ya juyo gaba daya yana kallona "Moon menene? What do you need? Jikin ne?" Na danyi masa murmushi kadan nace "asibiti zaka kaini ba gida ba" ya dan tsorata kadan "is the baby coming?" Na girgiza masa kai, "asibiti zamuje, za suyi min aiki su fitar da babyn" a take naga tashin hankali a rubuce a fuskarsa, na rike hannunsa sosai nace "don't do this sultan please, I need your support and strength. Please don't freak out" ya dan nutsu kadan yace "me yasa kika ce zasu yi miki aiki? Kince kuma ba labor kike ba" nan nayi masa bayanin duk situation dina da risks din da naje facing. Sosai naga hankalinsa ya tashi, ya daki stirring wheel da hannunsa yace "damn it, I hate that Ibrahim" na bata rai nace "Ibrahim bai dora min ciwo ba Allah ne ya dora min. Ba akaina aka fara ba ba kuma akaina za'a gama ba. Tunda na samu ciki lafiya lau nake, ko mugun laulayi banyi ba, wadansu matan daga ranar da suka samu ciki ba zasu samu lafiya ba har sai sun haihu. Wadansu matan talauci ya saka ko abinci mai kyau basa samu a lokacin da suke da ciki, wadansu matan basa samun medical care, wadansu matan zasi hadu da ciwo irin nawa amma basu san menene ba kuma su zo su fara labor a haka, a karshe su samu matsala koma su mutu gaba daya. Amma ni na samu komai, komai da nake bukata na samu, abinda nake bukata a yanzu shine support dinka, together we will get through this" ya dan nutsu ya dakata yana kallona, na mayar da idona na rufe inajin kaina tamkar zai rabe gida biyu, ga wani jiri da nake ji duk da cewa a zaune nake. Naji hannun sultan yana shafa fuskata, na dan bude idona ina kallonsa, na rike hannunsa da yake kan fuskata nace cikin sanyin murya "I need you to be strong" ya hadiye wani abu a makogwaronsa yace "yanzu me zamuyi" nace "asibiti zamuje. Amma please bana son ka kira kowa, Mommy da ummee in suka zo zasu kara min pressure ne. We can do this alone. Everything is going to be alright" da hannu daya ya dauko wayarsa yayi dialing, na fahimci doctor na yake kira, yana dauka ya fara masa bayanin abinda nace masa da kuma symptoms dina, banji mai doctor din yace masa ba yace "alright, we are on our way" ya kashe, hannun na yana cikin nasa ya kunna motar yayi reverse muka dau hanyar hospital, na koma na kwanta na rufe idona. Sama sama naji shigowar mu asibitin, naji sultan yana gayawa doctor a waya cewa gamu mun iso, hannunsa daya a rike da nawa dayan kuma ya saka yana shafa fuskata, na dan bude ido da niyyar in kalleshi amma hasken fitulun cikin asibitin ya saka na mayar da idona na rufe ba tare dana kalle shi din ba, naji zuwan doctor gurin mu, ya kunna fitilar wayarsa ya haska ni, na kara runtse idona saboda bana son hasken, yace da sultan "gwara da Allah yasa kuka taho yanzu baku zauna kunce sai safe ba, she is in critical condition and we will have to take the baby out now" sultan yace "yes, haka tace". Doctor din ya tafi sai ga wasu nurses sun kawo gadon daukan marasa lafiya, sultan ya chika hannuna ya zagayo ya dora ni akan gadon aka tura ni zuwa cikin asibitin. Ko sau daya sultan bai cika hannuna ba har aka kaini dakin da za'a shiryani. Doctor ya kawo wa sultan takardu yayi signing, har zai fita sultan ya tsayar dashi ya fara magana muryarsa kamar wanda zaiyi kuka yace "doctor please, nasan kasan aikinka ba wai koya maka zanyi ba, but please if anything should arise, in kana ganin Moon zata iya samun wata matsala, please doctor just forget about the baby and save my wife. Gwara in rasa shi akan ace wani abu ya same ta" doctor ya dawo ya tsaya a gaban sultan ya dora hannunsa akan kafadar sa, fuskarsa da murmushi yace "Our Prince, insha Allah nayi maka alkawarin zan kawo maka matarka da dan ka lafiya lau, babu abinda zai same su duk su biyun" sultan ya danyi murmushin yake yace "thank you doctor" doctor yace "amma nima ina bukatar wani taimako daga gareka, akwai maganar da zamuyi ka biyo ni office yanzu" sultan ya dan juyo ya kalleni yace da doctor din "bazamu iya maganar anan ba? Cos I don't want to leave her alone" doctor yace "OK, sai muyi anan din" suka zauna akan kujera doctor ya fara magana yace "kaga dai halin da take ciki yanzu, dan haka dole ba zamuyi mata anaesthesia ba, muna bukatar control over her bp, in muka yi mata allurar bacci ba zamu samu wannan control din ba, we need to keep her awake through the entire operation. Da akwai aikin da ake yi na ido biyu, zamu kashe lower part of her body yadda ba zata ji zafin komai ba har mu gama. Taimakon da nake nema a gurinka shine ina so ka shiga operation room din a tare damu ka zauna a kusa da ita kana yi mata magana mai dadi wacce zata kwantar mata da hankali" sultan yayi saurin girgiza kansa yace "I can't watch" doctor yace "you won't. Zamu saka labule a saman cikin ta mu raba ta biyu, her upper part tana gurinka zaku ke maganar ku, her lower part yana gurin mu muna aikin mu, baza kusan ma muna yi ba sai in mun gama muyi muku magana. Just don't let her sleep" sultan ya gyada kai yace "OK. I can do that" doctor ya mike tsaye yace "and we will need blood, just in case" da sauri sultan yace "you can take mine" doctor yayi murmushi yace "in yayi matching da nata ba. Zamu gwada mu gani in yayi dai dai sau mu dauka, in baiyi dai dai ba kuma sai ka samo mana wasu 'yan'uwanka ko nata a gwada a cikinsu ko za'a samu". In less than one hour da zuwan mu asibitin har an shirya ni suma doctors din sun shirya, duk abinda suke ina jinsu amma bana cewa komai saboda magana ma kara min ciwo take, idona kuma a rufe saboda bana son haske. Sai da aka tura gadona cikin theatre room sannan nayi nadamar cewa da nayi kar a kira kowa, ji nayi babu abinda nake son gani irin Mommy na da Daddy na, kuka naji yana taho min, nayi sauri na mayar dashi dan nasan ina fara kuka zan kara wa kaina ciwo kuma sultan zai kara rikicewa, so far dai yayi abin kirki sai dai ko dai dai da second daya bai matsa daga kusa dani ba. Muna shiga suka yi min wata allura a tsakiyar bayana mai dan karen ciwo, amma tana shiga naji kamar an yanke min daga cikina zuwa kafafuwana, kamar ba'a jikina suke ba, na juya ina kallon sultan wanda idonsa ya kada yayi jawur nace "ka kira daddy ka gaya masa. At least they will pray for me" ya dauko wayarsa, na lura hannunsa har rawa yake, bai iya kiran Daddy ba sai text ya tura masa. Aka sauko da labule aka raba jikina biyu. Sai ya zamana kamar ba'a daki daya muke da doctors din ba, jikina ya bani sun fara aikin amma banji komai ba. Na kalli sultan daya kankame hannuna kamar za'a kwace ni, nace "naji kamar cewa akayi kayi min hira" ya danyi murmushi nervously yace "labarin me kike in baki" nace "anything. Kamar the best day of your life" yace "da akwai ranaku da yawa da zan iya kira da best days of my life. Kuma duk days din da akwai ki a ciki. Because you are my life. Rana ta farko ita ranar dana fara ganinki. It was the day that my life begun. Daga nan sai days din da muka yi spending a America, I will never forget those days. Daga nan sai ranar daurin auren mu and then our first night, you took away not only my body but also my soul. Then, ranar da Takawa ya kira ni da his little love and asked for my forgiveness. Sai ranar dana fara ganin Ummee na. Sai kuma ranakun mu a Maldives" yayi murmushi yace "seriously ban so muka dawo ba" nayi murmushi nima, yace "rana ta karshe a yanzu ita ce yau, ranar da zamu ga result of our love. Zamu raine shi together, mu bashi tarbiya da soyayya da kulawa, we will give him all the things that I missed in my childhood. He is going to grow up to be better than me saboda he have the best mother in the whole world" I was so lost a maganganun sultan har na manta ma aiki ake min, sai kawai kukan baby muka ji, muka yi murmushi a tare, doctor ya dan daga labulen yace da sultan "a miko maka shi ka rike?" Sultan yayi saurim girgiza kai yace "babu hannun da zan rike shi dashi, I won't let go of her hand. Sai dai ku ku rike shi a wajanku" doctor ya saki baki yana kallon sultan, shi kuwa ko a jikinsa, nace "doctor kawo min shi ni in rike shi" doctor yace "ke kina ji da kanki ina ke ina rike baby? Ka rike ta da hannu daya sai ka dau babyn da dayan hannun, shi yasa Allah yayi maka hannu biyu saboda kayi two things at the same time. Kuma idan yaron nan ya girma sai na gaya masa" ya koma sai gashi ya dawo da baby a cikin towel, har yanzu kuka yake ta tsanyara wa, sai kuma naga sultan ya cika ni ya tashi ya karbe shi, fuskarsa cike da farin ciki, na fara lissafin yanzu fa dinke ni akeyi sai kuma nayi sauri na kawar da wannan tunanin daga raina, sultan ya zauna ya juyo min da fuskar babyn yace "look Moon, he is perfect. Dake yake kama" na kalli babyn, ba dani yake kama ba, hancinsa da bakin sa irin na sultan, idonsa da kuma kalar fatarsa irin nawa ne. Na saka hannu na shafa kansa nace "Allah yayi maka albarka".
Sai da aka gama dinke ni tas, suka gwada bp dina suka ga cewa is almost stable sannan sukace zan iya yin bacci yanzu, suka yi min allurar bacci. Tun kafin a gama zare allurar nayi bacci. Sanda na farka a wani dakin daban na ganni, babu ciwon kan kuma gani na ma ya fara dawowa dai dai, sai azaba da naji a gurin da aka bude cikina, na dora hannuna a gurin naji kamar inyi ihu saboda zafi, na hango sultan a zaune akan sallaya, daga alama sallah ya idar, babu kowa a dakin sai shi kadai. A hankali nace "Sultan" ya juyo da sauri ya taso yazo gurina "Moon? Wani abu yana miki ciwo? Me kike so?" Na nuna masa gurin aikina yace "bara in kira doctor" nace "Mommy tazo?" Yace "suna can sun hada kai ita da Ummee suna kuka a waje" na danyi murmushin yake, kafin ya bar gurin wani baccin ya sake dauke ni. Farka wa ta ta biyu Mommy ce a zaune a kusa dani, idanuwanta sun kumbura kamar zasu fado kasa, fuskarta tayi jawur. Na jima ina kallonta bata san ma na farka ba. A hankali nace "Mommy ki daina kuka, ba mutuwa zanyi ba, the worst part is over. Allurar bacci ce kawai take dibana" ai kuwa kamar cewa nayi Mommy yi kuka, nan da nan hawaye ya fara zuba, ta rike hannuna "Moon na shiga uku, ina can ina wurin dinner ke kina asibiti ana bude cikinki. Why didn't you tell me?" Nace "am sorry mother" na kalli agogon dakin naga 4:30, amma kuma ga rana ina kallo ta taga, this means har gari ya waye yamma tayi kenan. Na duba naga drip a hannuna, shi yasa banji yunwa ba. Akwai sauran ciwon kan kadan amma ina gani tas yanzu. Kumburin ma ya ragu. Nace "Mommy ina Daddy?" Tace "dazu ya tafi, ya zo sau biyu yana ganin ki, sun hana shigowa ne saboda kar a tashe ki. Shima wancan rigimammen an fita dashi yana ta tsala kuka, daga ganin sa acici ne. Bara inje in karbo shi sai a gwada feeding disa ko zai sha" har takai bakin kofa sai ta juyo tace "Allah yasa Khairat ta bani, dan ta hana kowa, duk wanda zai ganshi sai dai ya kalle shi a hannunta" nayi murmushi, dama nasan abinda zai faru kenan. Ai kuwa Ummee bata bawa Mommy ba, sai gata da kanta ta taho dashi, ta zauna tana yi min sannu, ina so in sake ganin fuskarsa amma ta kudundune shi a jikinta, tace "kafin ince komai, tell me, idea din waye a cikin ku kuka taho asibiti ba tare da kun gaya wa kowa ba?" Nayi shiru bance komai ba, tace "you almost give us a heart attack. Mun dauka kuna gidan biki, du kuma sun dauka kun dawo gida" nace "we are sorry Ummee" ta shafa kaina tana murmushi tace "ya jikin ki? Menene yake miki ciwo yanzu?" Nace "babu komai" tace "gurin aikin fa?" Nace "yana yi kadan. Nasan zasu zo anjima suyi min allura" sai a lokacin ta miko min babyn, sai kuma naji inajin kunyarta naki karba, Mommy ce tazo ta dan daga ni kadan tasaka min pillows a baya na sannan ta karbi babyn ta dora min a kan kirjina, na saka hannu na tare shi dan kar ya sauka kan ciwo na, ni duk kunyar Ummee nake ji ita kuma taki ta gane ballantana ta fita. Mommy ta fahimci kunya nake ji tace "Khairat ko zaki zo muje mu gano masu gwajin jinin can ko an dace an samu wanda yayi?" Ba tare data kalle taba tace "jeki kawai Fatima, gwara in zauna a gurinta kar mu barta ita kadai" Mommy tayi ajjiyar zuciya ta daga kafada ta fita. Na rasa yadda zanyi gashi shi kuma har ya fara kusur kusur yana tabe baki zaiyi kuka, Ummee tace "what are you waiting for? Feed him gashi nan zaiyi kuka. Tun da yazo duniya baici komai ba sai dan dabino da zam zam da babansa ya bashi" ya na iya da raina, dole na gyara riga na bashi, ai kuwa da sauri ya karba kamar yasan menene, ya nutsu sosai yana sha, na kura masa ido ina kallo, I can't believe wannan perfect halittar daga jikina ta fito, Allahu Akbar shine abinda kawai zan iya fada. Na bashi ring finger dina ya rike da hannunsa, sai kawai naga ya bude ido yana kallona, nayi masa murmushi sai kace yasan me nakeyi. Ummee ta zagayo ta bayana ta lakuce masa hanci tace "like father like son" Sultan ne ya shigo ya tsaya daga bakin kofa yana kallon mu, fuskarsa filled with feelings, Ummee tayi masa alamr ya shigi da hannunta, ya karaso ya ajiye ledar hannunsa yana kallona yace "ya jikin?" Na sunkuyar da kai nace "da sauki" ya matso kusa da gadon yana kallon babyn yace "an samu abinda ake so kenan, za'a bar kunnen mu ya huta" sai da ya gama sha dan kansa ya cika sannan na gyra rigata, Ummee ta karbe shi ta saka shi a kafada yayi gyatsa sannan ta bawa sultan shi tace "zauna in yi muku pictures" ba musu ya zauna a gefen gadon ya jawo ni jikinsa da hannu daya, daya hannun kuma ya rike babyn a jikin mu, Ummee tayi mana pictures da yawa. Ya dauko ledar daya shigo da ita ya fito da fruits, ya dauko ayaba ya bare ya miko min yace "doctor yace zaki iya cin fruits" na karba na fara ci sai muka ji anyi knocking kofa, Ummee ta saka min mayafi aka turo kofar, mutane suka fara shigowa kamar va zasu kare ba. Hafsat tana kan gaba, da sauri tazo ta dauki babyn daga kan cinyata tana cewa "shine ka hanamu karasa bikin mu ko?" Hatta amare da angwayen jiya duk sunzo, a raina nace 'jiya na hana first nights da yawa' Amina tazo tana yimin sannu, Zainab da Fadila, saratu da Faiza, Huda da Aishan Amir duk suka zagaye ni, mazan kuma suka tafi suna gaisawa da Sultan. Ina kallon Ibrahim ya mika wa Sultan hannu amma yaki karba, sai ya wayance da bare min ayaba. Ana ta hayaniya ana daukan hotu a ba baby, Ummee kuwa sai cewa take a daina jagwalgwala shi kar yayi ciwon jiki. Ni kam sai kallon su nake ina jin dadi a raina. Daddy yayi sallama ya shigo, ji nayi kamar in tashi inje in rungume shi, bai kula kowa ba har masu gaishe shi ya taho gurina bakinsa har kunne, ya sunkuyo yayi kissing dina a goshi yace "well done my daughter. Barakallahu fi ki" ya zauna a kujera yace ku kawo min wannan ragon mazan daya kasa jure taron biki" akayi dariya gaba daya.
Aka mika masa shi ya karba yayi masa addu'ah sannan yace "Sultan wannan ai kayi wa Moon yawo" Sultan ya karasa kusa dashi ya leka fuskar babyn yace "wannan idon ba nawa bane Daddy, kuma daga dukkan alama sai yafi ni haske" duk akayi dariya, ya Habeeb yace "Sultan in surukai suna magana aka akan dan mutum baya amsawa" Sultan yace "Daddy ai ba suruki na bane" a raina nace 'koma waye yayi magana amsa zaka bashi'.
Doctor ya bude kofa ya shigo. Yana kallona yace "Maman baby an tashi kenan, at last" nayi murmushi na gaishe shi, ya zo dudduba ni ya bani magungunan da zansha, yayi min allura a hannu, yace "zamu sake miki allurar bacci in an jima, saboda kamata yayi ace kinyi 24hours kina hutawa" sannan ya dauko takarda yana kallon mazan gurin yace "ga result din tests din da akayi muku na jini. Abbakar Sadiq Abdallah, jininka bai yi dai dai ba" su ya walid har da yiwa sultan dariya ganin yadda ya bata rai. Doctor yace "Lawan Muhammad Dikko kaima naka baiyi ba, Habeeb muhammad dikko naka kaima baiyi ba, Faruk Muhammad dikko kaima zero" akayi musu dariya suma gaba daya "Abbas sadiq abdallah kaima baiyi ba, Abdullahi Abdallah kaima zero, Adeniran Ibrahim, congratulations, kai kayi winning, naka yayi matching, mun gwada kuma munga it's free of all blood transmitted diseases, in ka shirya sai muje mu diba" gaba daya aka juya ana kallon Ibrahim, shi kuma ya kalli sultan, sultan kuma ya kalleni, ni kuma na sunkuyar da kaina.

Table of Contents

Chapters

99 chapters
  1. 1 Episode One : The Beginning of the Beginning
  2. 2 Episode Two: Meet my Family
  3. 3 Episode Three: Loved by All
  4. 4 Episode Four: Moon's Sister
  5. 5 Episode five: The Strangers
  6. 6 Episode six: The Challenge
  7. 7 Episode Seven: The Thin Tall Man
  8. 8 Episode Eight: The New Imam
  9. 9 Episode Nine: Give Me a Chance
  10. 10 Episode Ten: I Don't Know
  11. 11 Episode Eleven : The Protector
  12. 12 Episode Twelve : This is Me
  13. 13 Episode Thirteen : This is Me 2
  14. 14 Episode Fourteen : The Limit
  15. 15 Episode fifteen: blood is Thicker than Water.
  16. 16 Episode Sixteen : The Letter
  17. 17 Episode seventeen: Reply
  18. 18 Episode eighteen: what's Next?
  19. 19 Episode Nineteen: The Goodbye
  20. 20 Episode Twenty: The New Job
  21. 21 Episode Twenty one: Amira
  22. 22 Episode Twenty Two: Efisowa
  23. 23 Episode Twenty three: The Break up 💔
  24. 24 Episode Twenty Four: The Heartbreak 💔
  25. 25 Episode Twenty five: The Eclipse
  26. 26 Episode Twenty Six: A Step Further Away
  27. 27 Episode Twenty Eight : University of Oxford
  28. 28 Episode Twenty Nine: The Message
  29. 29 Episode Thirty : The Final Blow
  30. 30 Episode Thirty One: Let it go
  31. 31 Episode Thirty Two : Munnir
  32. 32 Episode Thirty Two : Mahdi
  33. 33 Episode Thirty Three: Zayed
  34. 34 Episode Thirty Four : Back to Square One
  35. 35 Episode Thirty Five : When Destiny Calls.
  36. 36 EpisodeThirtySix: Interesting
  37. 37 Episode Thirty Seven : The Dinner
  38. 38 Episode Thirty Eight : The Shadow
  39. 39 Episode Thirty Nine : The Shadow 2
  40. 40 Episode Forty :TheShadow 3
  41. 41 Episode Forty One : Born for This.
  42. 42 Episode Forty Two : Born for This
  43. 43 Episode Forty Three: America
  44. 44 Episode forty four : America 2
  45. 45 Episode Forty Five : The Rush
  46. 46 Episode Forty Six : The Repentance
  47. 47 Episode Forty Seven : Amir
  48. 48 Episode Forty Eight : Awkward
  49. 49 Episode Forty Nine : Ya Habeeb
  50. 50 Episode Fifty : Munir 2
  51. 51 Episode Fifty one : Mommy
  52. 52 Episode Fifty Two : The Journey
  53. 53 Episode Fifty Three : Daddy
  54. 54 Episode Fifty Four : Her Father's Daughter
  55. 55 Episode fifty five : Her Father's Daughter 2
  56. 56 Episode Fifty Six : What You Sow
  57. 57 Episode Fifty Seven : What You Sow 2
  58. 58 Episode Fifty Eight : I Missed You
  59. 59 Episode Fifty Eight : For You, Only You
  60. 60 Episode Sixty : The Prince
  61. 61 Episode Sixty One : Save the Date
  62. 62 Episode Sixty Two : The Manager
  63. 63 Episode Sixty Three : Amira 3
  64. 64 Episode Sixty Four : The Past and the Future
  65. 65 Episode Sixty Four : The Visitors
  66. 66 Episode Sixty Six : The Wedding
  67. 67 Episode Sixty Seven : The Wedding 2
  68. 68 Episode Sixty Eight : The Wedding Night
  69. 69 Episode Sixty Nine: The Wedding Night 2
  70. 70 Episode Seventy : The Wedding Night 3
  71. 71 Episode Seventy One : The Honeymoon
  72. 72 Episode Seventy Two : My Everything
  73. 73 Episode Seventy Three : His Father's Son
  74. 74 Episode Seventy Four : The Cook
  75. 75 Episode Seventy Five : The Emir
  76. 76 Episode Seventy Six : The Visitors
  77. 77 Episode Seventy Seven : Amina
  78. 78 Episode Seventy Eight : The Storm
  79. 79 Episode Seventy Nine : The Lightening and The Thunder
  80. 80 Episode Eighty : The Skeleton in The Closet
  81. 81 Episode Eighty one : The Skeleton in the Closet 2
  82. 82 Episode Eighty Two : The Light
  83. 83 Episode Eighty Three : The News
  84. 84 Episode Eighty Four : Little Love
  85. 85 Episode Eighty Five : Ibrahim
  86. 86 Episode Eighty Six : The Phone Call
  87. 87 Episode Eighty Seven : Riyadh
  88. 88 Episode Eighty eight :Khairat
  89. 89 Episode Eighty Nine : Khairat 2
  90. 90 Episode Ninety : His Mother's Son
  91. 91 Episode Ninety One : His Mother's Son 2
  92. 92 Episode Ninety Two and Three : Maldives 1 and 2
  93. 93 Episode Ninety Four : RIP
  94. 94 Episode Ninety Five : The Light
  95. 95 Episode Ninety Six : The New Bride
  96. 96 Episode Ninety Seven : The Real Prince
  97. 97 Episode Ninety Eight: My Baby
  98. 98 Episode Ninety Nine : New Little Love
  99. 99 Episode Hundred : Not The End.