Chapter 59
Episode Fifty Eight : For You, Only You
'Yan # teamibrahim ina jin duk abinda ake yi muku, believe me, i will surely reward your loyalty. Bature yace "he who laugh last.......
Washegari da sassafe Sultan ya kira ni yace min ya tafi office, yana da meeting very early, dan haka nima ban tashi da wuri ba, ina jin Mommy kusan shigowarta uku tana dubani, sai kusan karfe 12 na tashi, shima kuma yunwa ce ta tashe ni, nayi wanka na shirya cikin wasu riga da skirt english wears tunda duk kayana sunyi min yawa yanzu, nayi packing gashina a tsakiyar kai na sauko kasa, a kitchen na samu su Mommy already suna aikin abincin lunch, na gaishe da Mommy ta amsa tana kallon kayan da na saka, na jawo kujera na zauna nace "Ma'u ki kawo min taimako, yunwa na ke ji" da sauri Asma'u ta ajiye aikin da take yi ta fara hado min tea, na karba na fara sha sannan ta zubo min farfesun naman ragon da suka gama hadawa ta hado min da bread, na karba ina ci ina santi, Mommy tace "aikin kenan, amma in akace kiyi garki ba zaki yi ba sai dai a girka ciki, ni ban taba ganin macen da bata son girki ba sai ke Moon" Furaira ta karba "kuma gashi gwanin nata gwanin abinci ne ba" a tare muka watsa mata harara ni da Mommy, tayi sauri taja bakinta tayi shiru, can Mommy tace "ke furaira ya akayi kikasan saurayinta ne?" Furaira tace "nima Mommy wallahi a gurin 'yan waje nake ji, shi yake gaya musu" a raina nace "zai aikata" Asma'u tace "kar ki damu mai sunan daada, duk sanda akayi bikin ki gidan ki zan koma inyi ta dafa miki abinci ke da mijin ki" nan itama ta karbi nata rabon hararar daga Mommy" sai da na gama cin abinci na sannan Mommy tace "ku bata suyar friend rice din nan tayi" na fara yarfe hannu ina kallon Mommy kaman zanyi kuka "Mommy wallahi kone wa zanyi, ni kuba ni in yanka muku wani abu, ni zafin wutar ne bana so" asma'u ta biye min "dama wannan jikin naki haka babu tsoka ina zaki iya juya shinkafa? Bara dai in baki ki hada fruit salad" nan na kama murna na zauna dishen a kasa na nade kafa, maryam tace "so take fa ta gudu, ai tana zuwa kitchen zata ce a bata yanka, daga nan zata yanke hannu sai kuma ta tashi ta fita shikenan ba zaki kara ganin taba sai akan dining" duk suka saka dariya, na bata rai nace "ke Maryam har zaki nuna min aiki da wuka? Da likita fa kike magana" daga nan sai na fara basu labarin yaddda muke buda kan mutun mu bude kwakwalwarsa mu yi masa aiki sannan mu mayar mu rufe, ban ankara ba ina ta surutu sai gani nayi ana juye fruit salad din a bowl, har an gama hadawa, na dauko cup aka zuba min na koma gefe na fara sha ina cigaba da labari na. Tsayuwar mota muka ji a waje, Mommy ta kalleni tace "madam ki je ki chanza wadannan kayan na jikin ki, dan wannan tsageran yaron bashi da linzami a gidan nan, har kitchen din nan zai iya shigowa" nace "Mommy kaya na duk sunyi min yawa ne wallahi" tace "to sai ki saka wadanda suka fi wadannan girma ko kuma ki saka dogon hijab" nace "yes Mommy" har zata fita tace "kar ki yadda fa inzo dining in tarar dake da kayan nan sai ranki ya baci" da sauri na mike na riga ta hawa saman. Sai da nayi alwala na saka dogon hijab dina bayi sallah sannan na dan gyara fuskata na sauka kasa, ya Habeeb na tarar a palo, na zauna muka fara hira sai da ga Daddy, ya Walid da Sultan sun dawo, daga gani daga masjid suke. Ko kallon inda Sultan yake banyi ba na gaishe da Daddy, duk da ina jin idanuwansa a kaina. Daddy ya fara yi mana zancen convocation din mu da za'a yi next week, kuma duk tare za'ayi har dasu Faruk. Nan muka kama murna. Saukowar Mommy ce ta katse mana hayaniyar mu, gaba daya muka juya muna kallonta, tasha ado tun daga sama har kasa, tayi kyau sosai dan bazaka kalleta ba kace ta haife ni ma ballantana ya Walid daya doshi 30 years. Tana zuwa ta gaishe da Daddy, su kuma duk suka gaishe ta har Sultan, ta amsa ba tare da ta kalle shi ba, sannan tace "ga abinci nan a dining" ta mike ta tafi, muma duk muka bi bayanta. Muna zama na tashi na fara zubawa kowa abinci, sakara ce da miyar vegetables, fried rice da hadin salad sai farfesun naman rago, sai kuma fruit salad. Kowa farfesu na fara zuba masa sannan kuma sai in tambaye ka me kake so a cikin sakwara da shinkafa sai in zuba maka, amma da nazo kan Sultan ban tambaye shi ba na xuba masa fried rice da salad da yawa amma na ciccire tumatir din cikin salad din, duk abinda nake yi idon kowa akaina yake, ina gamawa yace min "thank you" ban amsa masa ba na koma na zauna. Ya Habeeb ne ya kasa shiru yace "shi Sultan mai yasa ba'a tambaye shi abinda yake so ba? Idan kuma ransa yafi son sakwarar kuma fa?" A hankali nace "baya cin sakwara ai" ya Walid yace "wow, yanzu kai zama kayi kai ta lissafa mata abincin da kake so da wanda baka so?" Daddy yayi gyaran murya duk kowa yayi shiru. Ina lura da Sultan gaba daya a takure yake, kuma nasan ganin Mommy a gurin ne. Daddy ya cigaba da maganar zuwan mu England ita kuma Mommy ta gaya mana cewa in munje zamu taho tare da Hafsat saboda tana son tazo ta haihu a gida, nan muka kara yin wata murnar. Sultan ne ya fara tashi yace wa Daddy zai koma office saboda ya baro aiki sosai a can. Yana tafiya su Daddy da yaya Walid suka fara maganar irin cigaban da company n Sultan yake samu, yaya Habeeb yace "yanzu fa a cikin 'yan watanni har ya fara zancen sayan building din kusa dashi zai kara wasu offices din ya kara expanding din gurin. He is a real hustler. Baya zama sam, baya kuma gajiya da aiki" ni da Mommy kawai jin su muke bamu ce komai ba. Sai da suka gama sannan Mommy tace da ya Habeeb "kai da kake ta celebrating success din wani kai ina taka success din? Tunda aka samar maka aikin nan ka fara ni banga ko hula ka saya wa kanka ba, baka da aiki sai kashewa 'yammata kudi ko? Ka san Allah Habeeb ka fita daga ido na in rufe, kana ganin walid ya sayi filin sa yana kokarin fara gini amma kai ko ajikinka sai ana maganar wani ka iya cewa 'he is a real hustler' bayan kai yanzu da zan duba account dinka babu wani abin kirki a ciki" yadda kokayi maganar ya Habeeb ne saka mu muka yi dariya ni da ya Walid, ta juyo tana hararar ya Walid tace "kai kuma ka iya taya wani murna cewa budurwarsa tasan abinda yake so da wanda baya so amma kai kaki yin budurwar ballantana ka gaya mata kai me kake so din, you are not getting any younger fa, ya kamata kai ma ka san me kake ciki tun kafin hajja ta juyo kanka ta samar maka mata" na rufe bakina ina dariya ganin yadda ya Walid ya bata fuska, ta juyo kaina tace "ke kuma a ina kika samu wannan wayar ta hannun ki?" Cikina ne ya bada kululu, na fara in ina, tace "shine ya baki ko?" Na gyada kai, tace "ce masa akayi ba zamu iya saya miki waya bane ba? Ko kuma ke ce kika roke shi?" Nayi sauri na girgiza kaina tace "to ki tabbatar kin mayar masa da wayarsa, phones din ki suna dakina kije ki dauka, kuma kar ki sake karbar komai nasa" nace "yes Mommy" Daddy yace "saura ni" duk mukayi dariya banda Mommy, yace "to duk kin hada min kan yara kin musu fada ai gwara ki hada dani kawai"
Haka rayuwa ta cigaba da tafiyar mana inda Sultan ya dage da aikinsa ni kuma na fara mayar da kiba ta. Kullum haka muke wuni makale a waya duk da cewa zai zo muyi lunch tare, dinner ma haka, kullum da daddare kuma muna tare a palon su ya Walid har sai Mommy ta kira ni ko kuma in su ya Habeeb sun kora ni gida. Ana gobe zamu tafi england aka dauko Amina daga 'yalleman. Tare duk muka tafi England a jirgin Daddy, a gidan Hafsat na sauka naga tayi nauyi sosai, Sultan ma ba kunya cewa yayi acan zai kwana, dole Zayed ya bude masa guest room din waje, ranar kusan raba dare mukayi hira, da zayed da sultan suka zauna hira har sai da muka gaji ni da Hafsat muka tafi muka kwanta muka barsu. Washegari da sassafe muka tashi muka fara shirin tafiya Oxford, wata tsadaddiyar doguwar riga Sultan ya aiko min da ita yace in saka, ai kuwa kamar an gwada ni dan das ta zauna a jiki na, Hafsat ta kalle ni ta tabe baki tace "to ba dole tayi miki dai dai ba tunda yasan size din komai, ni rashin kunyar ku har mamaki take bani, kun wani maze kamar babu abinda ya faru" na bata rai nace "kai Hafsat, ni kam da na sani ban gaya miki maganar nan ba, ni dashi har mun manta ma amma ke kin kasa mantawa, it is in the past, please move on" ta tabe baki tace "shine yace miki ya manta? An gaya miki duk wannan kallon naki da yake na banza ne? To gwara ma ki sani, bai manta ba, dan haka sai kibi a hankali dashi" ni dai ban kuma ce mata komai ba saboda bana so tayi spoiling mood dina for today. Na dora graduation gown akan doguwar rigar muka fita, sam na kasa hada ido da Sultan sai nake ganin kamar maganar da Hafsat ta fada gaskiya ne. Tun daga gidan Hafsat muka fara pictures, a dole na ware da Sultan muka yi ta pictures sannan muka tafi mkrt, muna zuwa suma 'yan gida suka zo nan guri ya hargitse muka tafi hall din taro, muna shiga muka tarar anyi displaying innovations na graduands, zanen Sultan na gani anyi enlarging dinsa a saka a wall din da take kallon mu, duk kan mu tsayawa mukayi muna kallon zanen, kowa yana cewa "kunga zanen sultan" "yayi kyau" "moon ke kika zana?" Ni dai duk ba wanda na bawa amsa, na juya na kalli sultan a gefe na naga ya saki baki yana kallon zanen, na kasa karanta expression dinsa, can ya juyo ya kalle ni yace "ke kika yi zanen nan?" Na kalle shi cikin ido nace "yes" ya kuma kallon zanen sannan ya sake juyowa yace "dama haka shape din kaina yake kamar mangaro?" Duk gurin kowa sai da yayi dariya nace "you are welcome, dan nasan thank you kake so ka ce" An gama taro lafiya duk muka karbi certificate din mu, I am now officially a neurologist and also a psychologist, Faruk da Amina ma duk sun karbi nasu, daga gurin taron gidan Hafsat muka zarce gaba daya inda Zayed da Hafsat suka shirya mana Walima. Washegari zamu koma Nigeria dan haka Hafsat already ta riga ta gama hada kayanta, Zayed sai bacin rai yake yi, ina jinsa yana gayawa sultan wai shi fa ba'a son ransa ba, kai Sultan maimakon ka bada hakuri sai cewa yayi "chafdi, ai kayi kokari ma, ni kam babu mai rabani da matata dan zata haihu" Hafsat tace "wato kar mu saka rai kenan ko?" Yace "gaskiya kam, kar ma ku saka rai ballantana in na hana kuji haushi"
Washegari muka dawo Nigeria. Motar mu tana shigowa gate na hango mutane cirko2 a tsatstsaye. Da sauri muma muka karasa gurin muka fito. Wata arniyar picanto fara tas an nada mata ribbon alamar gift ce, a jikin plate dinta an rubuta 'Her Royal Highness' ina gani nasan aikin waye wannan, nayi ta nemansa ko sama ko kasa bayanan, a saman motar an ajiye card, na dauka na karanta 'it will be my pleasure if you will let me teach you how to drive' lallai sultan rigima yake so ya debo min a gidan nan. Daddy yana ganin motar shima ya gane aikin waye yace da walid "ina sultan?" Ya Walid yace "a hanya ya sauka bai karaso gida ba" Daddy yace "call him" yana zuwa Daddy ya mika mishi key din motar yace "not now. In zaka koya mata mota akwai motoci a gidan nan ku dauki duk wacce kuke so" Sultan ya dan bata fuska Daddy yace in serious voice "I said NO" dole sultan ya karbi key dinsa. Inaji ina kallo aka saka motar a garage aka rufe.
A kasa aka gyara wa Hafsat daki saboda tace ba zata iya zirga2r hawa sama ba, nayi mamaki sosai yadda naga suna mu'amala da sultan, ta sake dashi sosai, Mommy ma naga yanzu tana dan kulashi kadan, har wani lokacin takan tambaye shi ya office ko kuma ta dan saka shi wani aiki. Shi kuma na lura yana jin nauyin ta sosai, dan in dai tana guri wata nutsuwa ta musamman yake yi. Kwanan mu biyar da dawowa rannan da safe bayan mun gama breakfast duk 'yan mazan sun tafi aiki sai ga Amira da mamanta sunzo, daga ganin fuskarta na san akwai matsala, a palo suka zauna tun kafin mu gaishe da mama ta fara fada "gata nan fatima na kawo miki ita maybe ke in kika yi mata magana zataji, Amira taki aure, na rasa me yake damun yarinyar nan, taki samarin ma ballantana har ta samu na aure. Ni na gaji, gwara in tattara in koma gida in yaso acan a samar mata miji a 'yan'uwanta" nan Mommy ta samu abinda take so, daga yiwa amira fada ta hada har dani tayi mana tas tace kuma tace ta bawa Amira 3 months in bata fitar da miji ba da kanta da kanta zata kaita kano gidansu a aura mata duk wanda yace yana so. Ni dai bance kala ba, maman Amira tace "wani shegen yaro ta hadu dashi ya hana ta kula kowa kuma shi yaki ya fito ayi maganar aure, na rasa yadda zan yi in raba ta dashi. Nan Mommy ta fara tambayar Amira wanda take so din ita sai ta aika a gaya masa idan bai shirya auren taba ya rabu da ita, tambayar duniyar nan Amira taki magana, duk fadan Mommy haka ta hakura ta kyale Amira. Muka tashi muka tafi dakin Hafsat muka zauna, nayi ta tambayar Amita problem din ta amma tace min ita babu abinda yake damunta tace " ita fa mama duk abinda take dauka ba haka bane ba, shi wanda take magana akansa fa ba saurayi na bane, a makaranta muka hadu, he is my friend kuma haka kawai sai inje in ce masa ya fito ya aure ni? Kullum threats dinta shine zata kaini kano dan tasan bana son can to ni ya zanyi? Idan miji bai zo ba ni zan auri kaina ne?" Sai naji tausayinta na rungume ta ina lallashinta, Hafsat ma ta bata hakuri, nan muka zauna hira na bata labarin duk abinda yake faruwa tsakani na da Sultan, na dauka zamuyi rigima akan maganar amma sai naga tayi murmushi tace "Allah ya sa hakan shi yafi alkhairi" gaba daya muka ce "ameen". Mama anan ta tafi tabar amira ta wuni a gurin mu tana bamu labarin aikin data samu a aso rock, da irin kudin fa take samu tana saving, yanzu basu da wani problem na matsalar kudi. Na danyi tunani nace " Amira ni kuwa ina ma zaki gwada Amir abokin Sultan, he is really nice...." Kafin in karasa ta katse ni "Allah ya sawake, ai kwantan nawa bai kai har haka ba, ke dai da kika ga zaki iya da sultan sai kije kiyi tayi" nayi dariya nace "idan kuma Allah yayi mijin ki ne fa?" Tace "ai Allah baya dora wa bawa abinda yasan ba zai iya ba" tare muka yi lunch da ita, Sultan yana ta tsokanar ta wai Amir yana gaisheta. Bayan la'asar ta shirya tafiya muka je zata yiwa Mommy sallama, nace "Mommy zan raka Amira gida" tace "to sai driver ya kai ku" na dan yi shiru nace "Mommy da Sultan ne yace zai kaimu" ta jima tana kallona ni kuma na sunkuyar da kai kasa sannan tace "a dawo lafiya" Na kira Sultan nace an bar mu gamu nan fitowa.
A motar sa muka same shi already yana jiran mu, na shiga gaba Amira ta shiga baya muka tafi, yace "Amira wai yaushe ne bikin kawar ki ne?" Tace "wacce fa?" Yace "wacce ki ka fi damuwa da ita" tace "sai ranar da ka shirya ranar za'ayi" yace "to ai ni already a shirye nake" ina jinsu na rabu dasu nasan neman magana yake yi, naga ya chanza hanya na tambaye shi yace "Amir zamu dauko" da sauri Amira tace "What? Please ku sauke ni in hau taxi, I can't tolerate that man" duk dariya muke mata tace "am serious wallahi, he is so annoying" muna yin packing ya bude ya shiga baya, yana ganin Amira a ciki ya ja tsaki yace "damn it, wannan yarinyar me take yi a motar nan?" Dariya muka sake yi, ni drama dinsu dariya take bani. Daga nan naga mun kuma yin wata hanyar daban, this time banyi magana ba Sultan yace "I want to show you something" Bance komai ba har naga yayi packing a gaban wani katon building duk muka fito na daga kaina naga an rubuta a saman ginin 'MOON CONSTRUCTION AGENCY" na kalle shi da mamaki yace "to ba kin ki gayamin sunan da kike so ba, shi yasa na saka sunan da na fi so" muka shiga gurin suna nuna mana ko'ina suna kuma yi mana bayanin komai,gurin ya tsaru sosai, I trust sultan in dai ta gurin tsari ne, aikin architecture yayi suiting dinsa sosai. Daga nan muka tafi gidan su Amira, a can mukayi magrib sannan muka fito muka kai amir gida shima. Finally daga ni sai shi, nace masa "thank you for the name" yace "I only hope it will shine as bright as you" nayi murmushi. Yace "wai har yanzu Mommy ba ta ce miki komai ba?" Nace "akan me fa?" Ya nuna kansa sannan ya nuna ni yana mischievous smile dinsa. Na gane me yake nufi, na dan bata rai nace "ni ban san akan me kake magana ba" yace "common, how much longer do I have to wait ne wai. Ni aure na ke so seriously" na rufe baki ina dariya nace "kai Sultan, baka jin kunyata kake cemin aure kake so?" Yace "ke din zanji kunya? Ke fa zan aura kuma sai inji kunyarki? Please ki dan tambayi Mommy mana kiji me ake ciki" nace "kai ma wasa kake, me zan ce mata? Mommy yaushe za'ayi min aure?" Yace "exactly" na girgiza kai nace "sai dai kai kaje ka tambayi Daddy" yace "OK, wato ke kina nufin ba kya son auren kenan?" Nace "wai what has come over you ne yau?" A lokacin muka shigo gida, yayi packing amma be kashe motar ba yace "ai na riga ma gaya miki me yake damuna, aure nake so, ai nayi kokari, ya kamata a bani medal ma. Kinga yanxu abinda za'ayi, irin in kuna magana da Mommy sai kike gaya mata ga abinda kike so ayi da bikin ki, zata dauki haske ai sai tayi wa Daddy magana" nace "wai ni na ce maka ina son aure? Kai da kake son auren ba sai ka fada ba?" Ya juyo yana facing fina yace "look into my eyes kice ba kya son aure na" na ki kallonsa, yasa hannu zai juyo fuskata na kara matsawa, yace "kin gani ko? You want it too" na girgiza kaina nace "I don't want anything" yace cikin murya kasa kasa "then look into my eyes and tell me you don't want me" da sauri na bude kofar motar na fita, shima ya bude ya fito ya sha gabana "au guduwa zaki yi ko?" Nace "kafi karfina yau. Yau mood dinka is not for me" yace yana kallon cikin idona "I have always been in this mood, for you, only you. Kawai hakuri nake, please do something. Ni fa idan ba'ayi mana aure kwanan nan ba to akwai rigima." Dariya nake son yi amma shi fuskarsa so serious, can ya fara devilish smile dinsa sannan yace "laugh all you want, baby girl, my time will come, then I will do the laughing and you will do the crying" bansan sanda na daina dariyar ba, da sauri na nayi hanyar gida, ina jinsa yana kira na amma ko waiwayowa banyi ba.
Table of Contents
Chapters
- 1 Episode One : The Beginning of the Beginning
- 2 Episode Two: Meet my Family
- 3 Episode Three: Loved by All
- 4 Episode Four: Moon's Sister
- 5 Episode five: The Strangers
- 6 Episode six: The Challenge
- 7 Episode Seven: The Thin Tall Man
- 8 Episode Eight: The New Imam
- 9 Episode Nine: Give Me a Chance
- 10 Episode Ten: I Don't Know
- 11 Episode Eleven : The Protector
- 12 Episode Twelve : This is Me
- 13 Episode Thirteen : This is Me 2
- 14 Episode Fourteen : The Limit
- 15 Episode fifteen: blood is Thicker than Water.
- 16 Episode Sixteen : The Letter
- 17 Episode seventeen: Reply
- 18 Episode eighteen: what's Next?
- 19 Episode Nineteen: The Goodbye
- 20 Episode Twenty: The New Job
- 21 Episode Twenty one: Amira
- 22 Episode Twenty Two: Efisowa
- 23 Episode Twenty three: The Break up 💔
- 24 Episode Twenty Four: The Heartbreak 💔
- 25 Episode Twenty five: The Eclipse
- 26 Episode Twenty Six: A Step Further Away
- 27 Episode Twenty Eight : University of Oxford
- 28 Episode Twenty Nine: The Message
- 29 Episode Thirty : The Final Blow
- 30 Episode Thirty One: Let it go
- 31 Episode Thirty Two : Munnir
- 32 Episode Thirty Two : Mahdi
- 33 Episode Thirty Three: Zayed
- 34 Episode Thirty Four : Back to Square One
- 35 Episode Thirty Five : When Destiny Calls.
- 36 EpisodeThirtySix: Interesting
- 37 Episode Thirty Seven : The Dinner
- 38 Episode Thirty Eight : The Shadow
- 39 Episode Thirty Nine : The Shadow 2
- 40 Episode Forty :TheShadow 3
- 41 Episode Forty One : Born for This.
- 42 Episode Forty Two : Born for This
- 43 Episode Forty Three: America
- 44 Episode forty four : America 2
- 45 Episode Forty Five : The Rush
- 46 Episode Forty Six : The Repentance
- 47 Episode Forty Seven : Amir
- 48 Episode Forty Eight : Awkward
- 49 Episode Forty Nine : Ya Habeeb
- 50 Episode Fifty : Munir 2
- 51 Episode Fifty one : Mommy
- 52 Episode Fifty Two : The Journey
- 53 Episode Fifty Three : Daddy
- 54 Episode Fifty Four : Her Father's Daughter
- 55 Episode fifty five : Her Father's Daughter 2
- 56 Episode Fifty Six : What You Sow
- 57 Episode Fifty Seven : What You Sow 2
- 58 Episode Fifty Eight : I Missed You
- 59 Episode Fifty Eight : For You, Only You
- 60 Episode Sixty : The Prince
- 61 Episode Sixty One : Save the Date
- 62 Episode Sixty Two : The Manager
- 63 Episode Sixty Three : Amira 3
- 64 Episode Sixty Four : The Past and the Future
- 65 Episode Sixty Four : The Visitors
- 66 Episode Sixty Six : The Wedding
- 67 Episode Sixty Seven : The Wedding 2
- 68 Episode Sixty Eight : The Wedding Night
- 69 Episode Sixty Nine: The Wedding Night 2
- 70 Episode Seventy : The Wedding Night 3
- 71 Episode Seventy One : The Honeymoon
- 72 Episode Seventy Two : My Everything
- 73 Episode Seventy Three : His Father's Son
- 74 Episode Seventy Four : The Cook
- 75 Episode Seventy Five : The Emir
- 76 Episode Seventy Six : The Visitors
- 77 Episode Seventy Seven : Amina
- 78 Episode Seventy Eight : The Storm
- 79 Episode Seventy Nine : The Lightening and The Thunder
- 80 Episode Eighty : The Skeleton in The Closet
- 81 Episode Eighty one : The Skeleton in the Closet 2
- 82 Episode Eighty Two : The Light
- 83 Episode Eighty Three : The News
- 84 Episode Eighty Four : Little Love
- 85 Episode Eighty Five : Ibrahim
- 86 Episode Eighty Six : The Phone Call
- 87 Episode Eighty Seven : Riyadh
- 88 Episode Eighty eight :Khairat
- 89 Episode Eighty Nine : Khairat 2
- 90 Episode Ninety : His Mother's Son
- 91 Episode Ninety One : His Mother's Son 2
- 92 Episode Ninety Two and Three : Maldives 1 and 2
- 93 Episode Ninety Four : RIP
- 94 Episode Ninety Five : The Light
- 95 Episode Ninety Six : The New Bride
- 96 Episode Ninety Seven : The Real Prince
- 97 Episode Ninety Eight: My Baby
- 98 Episode Ninety Nine : New Little Love
- 99 Episode Hundred : Not The End.