Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 91

Episode Ninety One : His Mother's Son 2

Maimoon Book 1 Complete Hausa Novel 3,823 words 0 views Progress saved
Download Book

Tace "to ni yanzu moon ta ina zan same shi?" Nace "How will I know ni da bana kasar ma" tace "Moon tsoronsa nakeji, tunda ya gane gaskiya bamu hadu ba, bansan wacce irin karba zai yi min ba" na danyi tunani a raina, tabbas Ibrahim yana jin haushin Amira sosai, dan haka ba lallai ne yasaurare ta ba in taje wajansa, Allah ma yasa karya faffalla mata mari. Sai kuma wata shawara ta fado min arai na, nace "abinda za'ayi Amira, kije gidan mu gurin Amina, ni zan kira ta in yi mata bayanin abinda nake so tayi, zata hada ki da Ibrahim kuyi magana, duk abinda ake ciki kuma sai muyi waya" ina gama yawa da amira na sake kiran Amina, ta dauka tace "what again?" Nace "ke dalla can ba maganar shi zanyi miki ba" sai nayi mata bayanin duk yadda mukayi da Amira, nace "yanzu taimako nake nema a gurinki, so nake ki hada su ta roke shi gafara, kema dan Allah sai ki tayata rokonshi" tace "kuma kika ce min ba maganarsa zakiyi min ba" nayi dariya nace "amma ai ba maganarsa dake nayi miki ba, maganar abinda ya faru tsakaninsa da amira nayi miki" ta danyi tsaki tace "ba lallai ne fa ya yafe matan ba, tunda har yanzu bai manta ki ba ba lallai ya yafewa wadda ta raba ku ba" nace "in kika hada su ne zaki tabbatar cewa ya manta dani yanzu, nayi miki alkawarin zaki sha mamaki, bazan miki alkawarin zai manta dani completely ba tunda nima ban manta dashi completely ba amma babu zancan soyayya, an wuce gurin, sai mutunta juna. Duk kanin mu, ni da ke, Ibrahim da Amira, duk mutane ne mu, muna making wrong decisions a rayuwar mu, muna sabawa Allah ma kansa ballantana mutum, amma in muka nemi gafarar Allah sai ya yafe mana, ya sake bamu chance saboda yana son mu chanza mu zama mutanen kirki, ti me yasa mu mutane ba zamu ke yafe wa junan mu ba? Me yasa zamu ke riko a ranmu bayan munsan cewa muma muna so in mun yiwa wani laifi ya yafe mana. Please Amina kiyi kokari kiga Ibrahim ya yafe wa Amira kema sai ki yafe masa ki sake bashi chance" ina kallon sultan ya shigo dakin da takardu a hannunsa ya tsaya yana kallona, Amina tace "shikenan, zanyi magana da Amirar in gani, I will see what I can do" muka ajiyar wayar. Sultan har yanzu yana tsaye yana kallona, am sure yaji ambaton sunan Ibrahim da nayi a waya, na tsaya ina jiran inga reaction dinsa, ya karaso inda nake yace "miss problem solver, kina nan amma kina solving problems din wadanda suke thousands miles away" naji dadi da ya fahimce ni, ya zauna a gefe na ya miko min takardun hannunsa yace "Ummee tayi miki maganar nan?" Na karbi takardun ina dubawa, da sauri na mike zaune sosai ina kara dubawa, na girgiza masa kai nace "bata yi min maganar ba, ta dai ce saboda kai ta fara kasuwancin ta, amma bata gaya min cewa sunan ka ne akan komai ba" dukkan takardun abinda Ummee ta mallaka ne, hatta takardun wannan gidan, da bank account dinta, da takardun dukkan contracts din data karba na shigo da kaya, duk sunan sultan ne a jiki. Na ajiye takardun ina kallonsa, yace "how do I tell her ni bana son kudinta?" Na girgiza kaina nace "mahaifiyar kace sultan, duk abinda ta baka ba faduwa tayi ba kuma kaima in ka karba ba faduwa kayi ba, karbar da zaka yi a ganina shine nuna godiyar ka gareta, inka mayar mata ka nuna mata baka so ba zata ji dadi ba, ka karba amma sai kace mata ka barta a matsayin care taker ta dukiyar taka, ta cigaba da kula da ita kamar yadda takeyi da" yace "to wannan uban cash din kuma da yake banki ya zanyi dashi?" Nace "kudi ne fa, you can do anything with it" ya jawo ni kan cinyarsa yace "ke a shawarar ki me kike ganin ya dace inyi dasu?" Na gyara kwanciyata a kan cinyarsa na danyi tunani kadan sannan nace "why not ka sake gina wata orphanage din, kuma ka bunkasa wacce kake da ita already, kace kana son gina musu makaranta da daukan malamai. Kaga idan kayi haka daga kai har ummee zaku samu lada har karshen rayuwar ku", yana murmushi yace "har ke da kika kawo shawarar" na mayar masa da murmushin nace "yes, har ni dana kawo shawarar". Washegari Ummee ta kaini gidan su zayed na wuni a can Umm zayed me kirki sosai gata wayayyiya, da sister dinsa zahra, na sake sosai dasu muna ta hira da zahra ina vata labarin England, wai tana son zuwa tayi karatu amma an hana ta a gida, muma cikin hira tace "amma kinfi sister dinki kirki, ita bata yiwa mutane magana" nayi dariya nace "ba haka bane ba, Hafsat tana da kirki sosai, kawai dai banbancin halayya ne a tsakanin mu, ni ina da surutu da saurin sabo da mutane ita kuma bata kula mutane sosai, amma in kika saba da ita zaki fahimci tana da kirki sosai. Abinda zakiyi ki lallaba a barki ki je England gurinsu ki dan kwana biyu, zakiyi mamakin kirkin Hafsat" sai magrib sultan yazo ya dauke ni muka koma gida. A hanya yake ce min "yaushe zamu koma Nigeria ne, Takawa yana ta waya wai ya kamata in taho haka nan" nima nayi missing gida sosai, amma nace masa "akwai rigima da ummee kenan" yace "sosai kuwa, dan yadda take ta plans dinta tunani take yi munzo garin nan kenan, ta manta ina aiki a can, besides Takawa ba zai taba barina in dawo nan da zama ba" a raina nace wasa kenan, dan nashi namiji guda daya kamar rai, his only heir, sultan yace "abinda za'ayi yanzu in munje gida, naga kunfi shiri da ita, ki tayar mata da maganar komawar mu Nigeria mu gani abinda zata ce, sai muyi mata bayanin ai ana ta nemana a office din mu sannan kema asibitin da kikayi booking zaki yi antenatal suna nemanki, mu ce mata amma zamu ke zuwa from time to time" na yarda da shawarar sultan dan haka muna dinner na fara maganar, dama sai da na gama jero adduoi sannan na fara magana, tunda na fara ta ajiye spoon din hannunta tana kallona, na duburburce na kasa karasawa, na kalli sultan amma sam yaki dago kansa ya kalleni, tace "yaushe kuka hada wannan plan din? A hanya ko kuma dazu a daki? You are not going anywhere. Me zakayi da aikin a can din? In aikin yi kake so sai ka nema anan ai. Ke kuma wanne antenatal zaki yi wanda ba zaki iya yi anan ba? You are a doctor, kinsan duk abinda kike ji kinsan kuma drugs din da zaki sha, ki rubuta masa sai ya siyo miki, sai menene kuma ake yi a antenatal din? Akwai kanin zayed shima doctor ne anan, ki shirya gobe sai muje ayi miki scanning" na kalli sultan na ga har yanzu baya kallona, nace a raina, wato zura ni kayi dama ka barni ni kadai ko? Ai kuwa muna komawa part din mu na fara sauke masa kwandon bala'i, "shine dazu kaki yin magana ko" yace "dama nasan ba zata yarda ba, I just want to confirm" nace "shine kayi using dina kayi confirmation din ko? I tot we are suppose to be a team" yace "we are a team. Yanzu ni bansan me zance wa Takawa ba idan ya sake kira, dazu daya kira cewa yayi da yasan zamu dade da kema ba zai barki ki taho ba ballantana har in biyo ki. Yanzu me zance masa?" Nace "oho, ni dai ba zaka sake yin using dina ba ehe, kawai dan ace ni ce marar kunya" ya jani muka zauna yana langwabar da kai, "hava love, ba using dinki nayi ba, kin san ina jin kunyar ummee ba zan iya yi mata musu ba shi yasa nayi shiru. Ina son komawa Nigeria amma kuma bana son inyi hurting ummee" na danyi tunani sai kuma nayi murmushi nace "then tell Takawa the truth, ka gaya masa ummee tace ba zamu dawo ba anan zamu cigaba da rayuwa har illa masha Allah" ya dan yi shiru sai kuma ya fara dariya, yace "that means war" nace "then let them have the war, mu sai mu zama 'yan kallo" ya manna min kiss yace "that's why I love you more every day".
Washe gari muka je scanning. Dani da Sultan da Ummee. Private clinic ne na Ahmad kanin zayed, kusan sa'an sultan ne dan haka muna zuwa suka kama hira, yana da fara'ar sosai da wasa kamar zayed. Tare muka shiga dakin scanning din gaba daya, ya fara min tambayoyi ina amsawa yana tsokana ta, ummee tayi masa bayanin cewa nima doctor ce, yace "shi kenan ma kinga abin yazo da sauki, duk bayanan da zan miki kin sani, sai dai kawai mu duba muga lafiyar babyn shikenan" nace "doctor we don't want to know the sex of the baby" da sauri sultan yace "when did we decide on that?" na harare shi, ummee tayi dariya, nace "kullum yana cewa mace ce ni kuma ina cewa namiji ne, so I tot mu barshi kawai in an haihu magani" sultan yace "no, ban yarda ba, dan kinsan ke zaki yi loosing shi yasa kika ce haka" Ahmad yace "ai ya danganta da kwanciyar babyn, idan babyn ya kwanta yadda zamuga sex din shi kenan in kuma ba haka ba sai mu bari daga baya mu sake dubawa" ni dai na bata rai, dan nasan in aka ga macece sultan in ya saka ni a gaba da tsokana har sai nayi kuka. Ummee taga na bata rai tace "abinda za'a yi, in kaga sex din kar ka fada musu, ni zaka fada wa, ni zanyi deciding me za'ayi dashi" sultan ya fara kunkunin ummee tafi sona a kansa. Doctor Ahmad har da juya screen din dan kar in gani, sam bai daga min riga ta ba, ta cikin rigar ya saka handle din ya kama jujjuya shi akan cikin yana yiwa ummee da sultan bayanin komai, sultan sai washe baki yake yi. Sun fi minti talatin suna kallo, sultan wai bai gaji da gani ba, sai da doctor yace "kai da za'a haifa maka a baka a hannunka ba sai kayi ta kalla ba?" Ya rubuta result ya bamu, ya rubuta wani ya bawa ummee. Alhamdulillah komai normal yake tafiya. Daga nan muka koma gida. Washegari doctor Ahmad ya kira sultan wai yana son muje gidan sa mu wuni a can, yana son ya hada ni da matar sa. Matarsa mai kirki sosai, Firdausi, zamuyi kusan sa'anni ni da ita, sai dai ita har tayi 'ya'ya biyu, Amra da Afra, su sultan suka fita suka barmu tare, tare muka hada lunch tana ta yaba methods of cooking dina, bata san cewa da zero nake ba daga baya na koya, muna gama shirya table su sultan suka dawo muka yi lunch tare, nace da doctor Ahmad, "da fatan dai baka gaya masa ba" yace "ai nayi wa ummee alkawari, duk wanda yake so ya sani sai dai ya tambaye ta" nan muka zauna hira akan banbancin al'adun mu da nasu, da yadda zamani yake chanza both al'adun mu da nasu. Ummee ce ta kira ni a waya tace mu dawo gida haka nan, na duba agogo naga 4:30, nayi mamaki cewa da tayi mu dawo da wuri bayan hira tana dadi, Ahmad yace bara su biyo mu kawai dama sun jima basu je gidan ummee sun gaishe ta ba. Muna yin packing na lura da motoci da yawa a gidan, ni dai ina mamaki na kalli sultan ya daga min kafada alamar shima bai sani ba, a palon farko muka ga al rataye balloons pink and blue, a kofar shiga palo na biyu an yi decoration an rubuta 'Welcome to the Gender Reveal Party' mamaki ne ya kamamu, dama Ummee party ta shirya mana? Muna shiga kuwa aka dau tafi da sowa, da 'yan'uwan sultan nan kusan duk wanda yake gari yazo, na kalli Ahmad naga yana mana dariya, wato dashi aka hada baki shi yasa ya gayyace mu gidan sa. Ni dai ba zan iya cewa ga abinda ya faru ba, they are all talking at the same time kuma mostly larabci suke yi, ni dai naga an jamu ni da sultan gefe, aka hada hannayen mu aka daure da pink and blue ribbons, sai kuma naga an turo wani table da katon cake akai, fari tas cake din kamar snow, aka kawo gabanmu aka ajiye, aka kawo mana 'yar karamar wuka fara aka saka mana a hannayen da aka daure, ina kallon zahra tana recording da wayarta, suka fara chanting 'cut the cake, cut the cake' sultan ya kalleni yace "are you ready?" Na juya na kalli ummee, ta gyada min kai, na kalli sultan nace "yes" nan aka dauki tafi da sowa, suna chanting "pink means girl, blue means boy" wato in muka yanka cikin cake din muka ga pink to girl ce, in kuma muka ga blue to boy ne, na kalli sultan naga sai zuba murmushi yake, dadi ya ishe shi, gani ga ummeensa ga 'yan uwansa duka kuma muna sonsa, ga kuma cikin jikina, dan haka bai damu ba ko mace ce ko namiji ba, nima sai naji ban damu ba, fatana Allah ya bani mai albarka. Muka dauki wukar a tare muka yanka cake din, tun kafin mu karasa yanka wa na ga blue, muna gama yankawa kuma aka dauki ihun "it is a boy" ni dai dariya kawai nake yi, na kalli sultan naga shima dariyar yake yi, ya kalle ni yace "Congratulations My Love, you won" yayi kissing dina a cheeks sannan yayi min a goshi, sai kuma ya rungume ni a jikinsa ya rada min "I Love You" a cikin kunne na, nima nace masa "I love you more".
Nigeria
Ibrahim;
Satinsa biyu a Ibadan ya dawo abuja, a zaman da yayi a ibadan ya kuma kulla dangantakarsa da ubangiji kuma ya kara kulla wa da mama da sauran 'yan uwansa, dan takanas ya fita yawon zumunci, kusan duk 'yan uwansa da suke ibadan, barim mama da baba da kuma babansa mahaifi babu gurin wadanda baije ba, kuma duk inda yaje sai ya kai musu goma ta arziki. Yana dawowa Abuja kuwa ya karawa employees dinsa albashi, wadanda ya kora ya kira su suka dawo bakin aikin su. Shi kansa yaji chanji a jikinsa, dan yanzu fresh yake jin kansa, zuciyarsa da take a kuntace a da yanzu tas yake jinta. Ya nemi masu aikin construction suka zo sukayi masa renovating gidansa aka kara dakuna, aka fitar wa da mama part dinta, da nashi part din shi da Amina, daga baya kuma akayi dan karamin BQ saboda kannensa maza. Har furnitures sai da ya zuba da komai sannan ya koma ibadan, nan fa mama ta saka rigima ita ba zata koma gidan sa ba, sai da ya hada da gaya wa 'yan'uwanta da yasan tana jin maganar su sannan ta yarda ta biyo shi, ita da maimunatu da kannen Ibrahim maza su biyo, matan dama duk sunyi aure suna gidajen mazajen su, mazan kuma an gama secondary school amma babu halin shiga jami'a, 'yar collage din ma ta gagare su. Ai kuwa suna ganin gidan da zasu zauna yanzu sai murna, wahala ta kare dadi yazo kuma, suna zuwa ya nema musu admission a university of Abuja, Allah ya so lokacin sabon dauka ne kuma yana da hanya tunda yana da kudi, dan haka basu samu matsala ba suka samu, maimunatu kuma ya nema mata makaranta me kyau sosai ya saka ta, yayi hiring 'yan aiki saboda kula da gida, baya son mama ta ringa aiki da kanta, amma duk da haka tace a bar mata girki zata ke yi musu da kanta tunda bata saba da zaman banza ba. Ya saka mata DSTV a dakinta saboda in babu kowa ta ringa debe mata kewa. Maimunatu kuwa a part dinsa ya ware mata daki, ya cika mata shi da dukiya duk abinda yasan little girl zata bukata sai da ya saka mata, amma ita duk wannan bai dame ta ba, ita babban burinta shine ta ganshi tare da ita, dan sam kin zama tayi a dakinta sai nashi dakin ta dawo, tare suke kwana ta makalkale shi kamar zai gudu, har ransa yake jin tausayinta, bata san mahaifiyarta ba shi kuma mahaifin nata yayi watsi da ita yana chasing dead dreams dinsa, rannan yana shiryata zai kaita makaranta tace "Daddy please don't take us back to ibadan" ya durkusa a gabanta yana shafa gefen fuskarta yace "I promise you I won't". Dadin gidan yake ji sosai yanzu, amma da har baya so ya dawo gida saboda zaman kadaicin da yake ciki, yanzu kuwa kullum cikin nishadi yake da dariya, bashi da wani sauran problem sai Amina. Sam Amina taki kulashi, tun ranar nan har yau taki daukan wayarsa, yaje gidan yafi sau a kirga amma taku fitowa, direct take cewa a gaya masa ba zata zo ba, yayi messages din ban hakurin har kalamansa sun kare, kullum yana ganinta online a WhatsApp amma maganar duniyar nan in yayi mata ba zata bashi amsa ba, kuma tana karantawa yana gani. Gashi kuma wani irin sabon sonta ne yake kara shigar sa, ita kuma kamar da gayya kullum sai ta chanza DP dinta, sai yayi saving yayi ta kallo, sam yanzu ya daina kanin fuskar moon a fuskarta, har mamaki yake yi ya akayi da yake ganin suna kama, they are totally different, kowacce is special in her own way. Daga baya ya yanke shawarar zai biyo mata ta sama, dan haka yaje gidan ya binciki ranar da zai samu Daddy, ranar kuwa yaje ya aika akayi masa sallama dashi, Daddy ya gane shi dan haka yayi masa iso har palon bakinsa yana tambayarsa ya saukin jiki, Ibrahim kan har ya manta ma da yayi wata jinya, shi yanzu jinyar zuciyarsa ce a gabansa. Nan ya yiwa Daddy bayanin abinda yake tafe dashi, Daddy yayi murna sosai amma kuma sai ya tambashi ko Aminan ce tace masa yazo? Nan fa Ibrahim ya fara shafa kai, daddy yace kar ya damu zai yi magana da Aminar yaji menene amsarta, duk abinda ake ciki zai saka walid ya kira shi a waya ya gaya masa. Ibrahim ya riga yasan amsar da Amina zata bayar dan haka sanda walid ya kira shi ya gaya masa abinda tace bai yi mamaki ba, amma Daddy yace a gaya masa ya cigaba da nemanta, inta chanza ra'ayi shikenan, in bata chanza ba kuma sai dai yayi hakuri dan ba za'a yi mata dole ba. Nan Ibrahim ya kara kaimi gurin rarrashi da ba da hakuri amma shiru kamar an shuka dusa, kuma har a zuciyarsa bai taba tunanin ya hakura ba saboda yana ji a ransa cewa itace matarsa. Ranar wata Friday kawai yana zaune a office sai yaga message, har sai da ya mitstsika idonsa dan yana ganin kamar yaudarar sa idon yake yi, Amina, ya bude ya fara karantawa "if you can, come over tomorrow, someone wants to meet you" da sauri yayi reply, "of cause I can, And I really hope that someone is you". Saturday yana yin sallar la'asar ya cewa mama zai dan fita ya dawo, sai gidan su Amina, suka gaisa da baba habu dan yanzu sun fara sabawa dashi, ya shiga yayi packing ya kira ta a waya, bata dauka ba har ta katse, sai kuma gata ta fito, ta kira wani yaron gidan tayi masa magana sannan ta koma ciki, yaron yazo yayi masa iso zuwa palon su yaya Walid, ya shiga ya zauna yana karewa haduwar gurin kallo, sam yanzu dukiyar gidan bata tsorata shi saboda yasan karamcin jama'ar gidan. Yaji motsi a bakin kofa, yayi sauti ya juya, Amina ce a tsaye da dogon hijab a jikinta tayi sallama ta karaso ciki, murna kamar ta kashe Ibrahim, gani yake kamar bai taba ganin macen da hijab yayi wa kyau irin amina ba. Ya mike yana amsa sallamar ta, sai kuma yaji wata sallamar daban, ya kalli bakin kofar, nan take annurin fuskarsa ya kau, ko a mafarki baya fatan ganin wannan fuskar, me take yi anan, ta karaso palon kamar wadda kwai ya fashewa a ciki, ya kalli Amina da sauri yace "what is she doing here?" Amina ta yamutsa fuska tace "dama ita ce mai son ganin naka bani ba" Amira ta karaso ta durkusa a gaban Ibrahim, da sauri ya matsa yace "tashi daga kusa dani kar kisa inyi amai" Amina taji wani takaici ya kama ta, ta rike kugu zata zazzaga masa masifa kuma sai ta dakata tana so taga yadda zasu kare kafin ta yanke hukunci, Amira ta fara magana muryarta na rawa "Ibrahim dan Allah ka yafe min. Nasan na munanawa rayuwarka, wallahi sharrin shaidan ne da son zuciya suka kaini ga aikata haka, dan Allah ka yafemin, ni yanzu yafiyar ka ita kadai nake bukata, ka yafemin ko na samu Allah ya yafemin ko rayuwata zata yi kyau" ya kalle ta ya dauke kai, sai kuma ya kalli Amina, ba dan abinda Amirar tayi ba da bai hadu da Amina har yayi mata wannan son da yake yi mata yanzu ba, ya tuna da little Maimunatun sa, ba dan abinda Amira tayi ba da ba'a haife ta ba, ya kuma tunawa da cikin dake jikin Moon, dan Sultan, shima badan Amira ta raba shi da Moon ba da ba za'a haifeshi ba. Babu wanda ya isa ya raya ko ya kashe sai Allah, kamar yadda babu wanda ya isa ya wuce kaddarar sa. Ya kalli Amira yaga yadda take kuka daga dukkan alamu va karamar nadama tayi ba, ya dauke kansa yace "na yafe miki, Allah ya yafe mana baki daya" ba Amira kadai ba, hatta Amina sai da tayi mamakin saurin yafiyar da yayi wa Amira, ya kuma kallon Amirar da take durkushe har yanzu a gabansa yace "tashi ki tafi, na yafe miki nace" da sauri ta mike tana kallon Amina sai kuma ta fita, ya dawo da kansa kallon Amina yace "I now have the most precious jewel in the world, why will I be unhappy?" Murmushi taji ya subuce mata, sai kuma ta sake bata rai, ya karaso kusa da ita yace "ko nima sai na durkusa a kasan ne?" Ta juya kamar zata fita sai ta tsaya ta juyo tace masa "ka dawo ku sake magana da Daddy, wannan karon da izini na". Dadi kamar ya kashe Ibrahim, sai kuma wani tsoron Allah ya kama shi. Haka fa Allah yake kallon mu idan munyi masa laifi mun roke shi gafara, sai ta duba yaga cewa mu din masu gafara ne ga 'yan'uwan mu? Kafin ya yafe masa ko akasin haka. Wannan ma wani darasin ne.

Table of Contents

Chapters

99 chapters
  1. 1 Episode One : The Beginning of the Beginning
  2. 2 Episode Two: Meet my Family
  3. 3 Episode Three: Loved by All
  4. 4 Episode Four: Moon's Sister
  5. 5 Episode five: The Strangers
  6. 6 Episode six: The Challenge
  7. 7 Episode Seven: The Thin Tall Man
  8. 8 Episode Eight: The New Imam
  9. 9 Episode Nine: Give Me a Chance
  10. 10 Episode Ten: I Don't Know
  11. 11 Episode Eleven : The Protector
  12. 12 Episode Twelve : This is Me
  13. 13 Episode Thirteen : This is Me 2
  14. 14 Episode Fourteen : The Limit
  15. 15 Episode fifteen: blood is Thicker than Water.
  16. 16 Episode Sixteen : The Letter
  17. 17 Episode seventeen: Reply
  18. 18 Episode eighteen: what's Next?
  19. 19 Episode Nineteen: The Goodbye
  20. 20 Episode Twenty: The New Job
  21. 21 Episode Twenty one: Amira
  22. 22 Episode Twenty Two: Efisowa
  23. 23 Episode Twenty three: The Break up 💔
  24. 24 Episode Twenty Four: The Heartbreak 💔
  25. 25 Episode Twenty five: The Eclipse
  26. 26 Episode Twenty Six: A Step Further Away
  27. 27 Episode Twenty Eight : University of Oxford
  28. 28 Episode Twenty Nine: The Message
  29. 29 Episode Thirty : The Final Blow
  30. 30 Episode Thirty One: Let it go
  31. 31 Episode Thirty Two : Munnir
  32. 32 Episode Thirty Two : Mahdi
  33. 33 Episode Thirty Three: Zayed
  34. 34 Episode Thirty Four : Back to Square One
  35. 35 Episode Thirty Five : When Destiny Calls.
  36. 36 EpisodeThirtySix: Interesting
  37. 37 Episode Thirty Seven : The Dinner
  38. 38 Episode Thirty Eight : The Shadow
  39. 39 Episode Thirty Nine : The Shadow 2
  40. 40 Episode Forty :TheShadow 3
  41. 41 Episode Forty One : Born for This.
  42. 42 Episode Forty Two : Born for This
  43. 43 Episode Forty Three: America
  44. 44 Episode forty four : America 2
  45. 45 Episode Forty Five : The Rush
  46. 46 Episode Forty Six : The Repentance
  47. 47 Episode Forty Seven : Amir
  48. 48 Episode Forty Eight : Awkward
  49. 49 Episode Forty Nine : Ya Habeeb
  50. 50 Episode Fifty : Munir 2
  51. 51 Episode Fifty one : Mommy
  52. 52 Episode Fifty Two : The Journey
  53. 53 Episode Fifty Three : Daddy
  54. 54 Episode Fifty Four : Her Father's Daughter
  55. 55 Episode fifty five : Her Father's Daughter 2
  56. 56 Episode Fifty Six : What You Sow
  57. 57 Episode Fifty Seven : What You Sow 2
  58. 58 Episode Fifty Eight : I Missed You
  59. 59 Episode Fifty Eight : For You, Only You
  60. 60 Episode Sixty : The Prince
  61. 61 Episode Sixty One : Save the Date
  62. 62 Episode Sixty Two : The Manager
  63. 63 Episode Sixty Three : Amira 3
  64. 64 Episode Sixty Four : The Past and the Future
  65. 65 Episode Sixty Four : The Visitors
  66. 66 Episode Sixty Six : The Wedding
  67. 67 Episode Sixty Seven : The Wedding 2
  68. 68 Episode Sixty Eight : The Wedding Night
  69. 69 Episode Sixty Nine: The Wedding Night 2
  70. 70 Episode Seventy : The Wedding Night 3
  71. 71 Episode Seventy One : The Honeymoon
  72. 72 Episode Seventy Two : My Everything
  73. 73 Episode Seventy Three : His Father's Son
  74. 74 Episode Seventy Four : The Cook
  75. 75 Episode Seventy Five : The Emir
  76. 76 Episode Seventy Six : The Visitors
  77. 77 Episode Seventy Seven : Amina
  78. 78 Episode Seventy Eight : The Storm
  79. 79 Episode Seventy Nine : The Lightening and The Thunder
  80. 80 Episode Eighty : The Skeleton in The Closet
  81. 81 Episode Eighty one : The Skeleton in the Closet 2
  82. 82 Episode Eighty Two : The Light
  83. 83 Episode Eighty Three : The News
  84. 84 Episode Eighty Four : Little Love
  85. 85 Episode Eighty Five : Ibrahim
  86. 86 Episode Eighty Six : The Phone Call
  87. 87 Episode Eighty Seven : Riyadh
  88. 88 Episode Eighty eight :Khairat
  89. 89 Episode Eighty Nine : Khairat 2
  90. 90 Episode Ninety : His Mother's Son
  91. 91 Episode Ninety One : His Mother's Son 2
  92. 92 Episode Ninety Two and Three : Maldives 1 and 2
  93. 93 Episode Ninety Four : RIP
  94. 94 Episode Ninety Five : The Light
  95. 95 Episode Ninety Six : The New Bride
  96. 96 Episode Ninety Seven : The Real Prince
  97. 97 Episode Ninety Eight: My Baby
  98. 98 Episode Ninety Nine : New Little Love
  99. 99 Episode Hundred : Not The End.