Chapter 86
Episode Eighty Six : The Phone Call
Bayan sati daya da dawowar mu daga asibiti, Sultan ya fara saukowa daga emotional height din da ya hau, ya fara accepting Takawa a hankali. A nasa bangaraen kuwa, Takawa kullum sai yazo part din mu, tun ina jin nauyinsa ina baya baya dashi har na saba na fara yi masa surutu in yazo, dan haka duk sanda yazo nice abokiyar hirar sa Sultan bin mu kawai yake yi da kallo, daga baya sai Takawa ya mayar da zuwa gurin mu da daddare al'ada, kullum anan yake cin abincin dare a palon sultan, sai tanzu nake kara jin dadin koyon girkin da nayi, duk da dai har yanzu asma'u tana nan amma hannu bibbiyu yafi sauri. Kullum Takawa bashi da labarin bawa Sultan sai na khairat, Sultan kam sai yayi shiru ya rabu dashi baya tanka masa. Nayi nayi da Sultan ya gaya masa cewa mun sami labarin ta amma yaki. Shi har yanzu fushi yake yi da ita, yace in ta ki neman mijinta saboda taji haushin ya sake ta to shi kuma fa? Ina laifinsa a ciki.
Wata ranar friday da daddare, Takawa yazo kamar yadda ya saba, ni kuma ina ta faman hidimar jera musu abinci akam carpet, sai ga Amir nan ma yazo, ya gaishe da Takawa, suka gaisa da Sultan ni kuma na gaishe shi. Sultan yana ta tsokanar sa suna dariya kamar yadda ya saba, sai Takawa yace "Sultan baka da kunya, Amir fa uba ne a gurinka" Sultan ya bata fuska yace "Uba kuma?" Takawa yace "eh. Mahaifina ne yayi adopting dinsa, dan haka legally kani na ne, hakan ya saka ya zama uba a gurinka" dani da Amir mukayi ta dariya, Amir har da rike ciki, Sultan ya bata fuska yace "wallahi ba'a isa ba" Takawa yace "daga yau baba Amir zaka ke ce masa. Amir duk ranar da bai ce maka baba ba kazo ka gaya min" Amir harda yiwa sultan gwalo, sannan yayi mana sallama ya fita, ina tayi masa mitar yaki tsayawa yaci abinci. Yana fiya na dauko yankakken apple na kawo gaban Takawa ya dauka ya fara ci yana min godiya, idonsa akan sultan yace "me Amir yake ciki ne?" Sultan yace "as far as I know bashi da problem. Amir is the must cheerful man I have ever known, kullum cikin farin ciki yake, sam bai dauki duniya da zafi ba ko kuma wai ya saka wa kansa damuwa akan neman asalinsa. Matsalar da yake fuskanta daya ce, akan neman auren da yake yi, iyayen yarinyar da yake nema sun hana shi aurenta, wannan shi yasa kwanan baya naga ya tayar da hankalinsa amma yanzu ya fara dawowa normal duk da dai har yanzu ba wai rabuwa yayi da yarinyar ba" Takawa yace "wacece yarinyar?" Sultan ya gaya masa sunan mahaifinta wanda yake malami ne a maiguduri, Takawa yace "ka gaya wa Amir, ya gayawa yarinyar ta gaya wa iyayenta, ni zanje har maiduguri in nema masa auren ta, nine waliyinsa" nan take sultan ya washe baki yana dariya, sai ince wannan shine karo na farko da naga sultan yayi wa mahaifinsa dariya, nima kaina sai da naji dadi, Amir deserves more than that, saboda duk wahalar da sultan ya sha a rayuwa tare suka shata, shima ya kamata ace ya samu farin ciki. Amma kuma can kasan zuciyata ina tausayawa kawata Amira, Amir din ma data dan samu gashi ya gudu ya barta zaiyi aurensa, amma kuma banji haushin Amir ba tunda bai taba furtawa yace yana son ta ba ballantana ace ya yaudare ta. Amma duk da haka sai dana yiwa Sultan maganar bayan Takawa ya tafi, kamar bai jini ba daga farko sai kuma yace "why do you care about her ne wai? Ina ruwanki da ita? She is not loyal" nace "she was not loyal. Amma hakan ba wai yana nufin bata yi learning lessons din ta ba. Everyone deserves a chance at redemption" ya sake dauke kai, na saka hannu na juyo fuskarsa gurina nace "pleeeassse" ya kara bata fuska "to wai ke me kike so ayi mata ne? Shi Amir ga wacce yake so, so kike ince masa Amir ka fasa auren wacce kake so ka auri wacce Moon take so?" Nace "ba haka nake nufi ba honey, kasan yadda Amir suke da Amira, na tabbatar ba za'a rasa sonta a cikin zuciyarsa ba kawai dai wancan son ne ya danne wannan. Kuma shi na miji ai mijin mace hudu ne ko?" Yana kallona kuma sai ya fara murmushi yace "ki sani, in dai akayi auren nan sai na gayawa Aisha ke kika ce ayi mata kishiya tun kafin a aure ta" nayi dariya nace "a'a kar ka hada ni da kawata, in dai har akayi auren to dama an rubuta cewa matar sa ce, bani na saka ba, shi aure ai rai ne dashi, ba'a creating dinsa ba kuma a destroying dinsa, sai dai a zama sila".
Washegari weekend, Sultan yana gida tun safe yana zuba mulki, duk yabi ya addabeni kamar zanyi masa kuka, dama kwana biyun nan kamar wanda ake kara tunzurashi a kaina, ni kuma yanzu ga kasala da take damuna da bacci, ko da yaushe a gajiye nake jina duk da ba wani aikin kirki nake yi ba, dan gyaran part din sultan ma mostly yanzu shi yake yin kayansa indai har yana gida sai dai in baya nan. Da kyar na samu na kwaci kaina daga gurinsa nace zan je kitchen muyi girki da asma'u, ina fitowa ko kallon hanyar kitchen din banyi ba na tafi part dina na shiga na rufe kofa harda saka key, duk da nasan cewa a banza nake yi in dai har sultan ne sai ya shigo sai dai in baiyi niyya ba. In kwanciya a gado ko minti daya banyi ba nayi bacci. Ina cikin baccin naji ana min tafiyar tsutsa a kafa ta, na janye kafar aka sake biyo ni, na tashi zaune da kyar nake bude idona dan bacci, na ga sultan a zaune a tsakiyar gadon yana kallona, yace "girkin kenan ko?" Kamar zanyi kuka nace "bacci nake ji Sultan dan Allah ka rabu dani" shima ya kwaikwayi muryata, "weekend ne fa yau. Weekdays ina damunki ne? Wanda ba'ayi da rana ranar aiki shi nake fanshewa da weekend" bai ankara ba kawai saiji yayi na fashe masa da kuka, ya saki baki yana kallona, na fara cewa "wayyo Mommy ki zo ki taimake ni Sultan zai kashe ni" dariya ya fara yi yana kallona ina ta kuka na, sai daya bari nayi mai isa ta sannan yace "kinsan da Mommy zata ganki yanzu me zatace?" Na girgiza kaina ina share hawayena, yace "cewa zatayi 'ke kika ce kina so, da baki ce kina so ba da ba'a baki shi ba'" na watsa masa harara nace "na fasa sonka ai yanzu, bacci nake so" na yunkura zan sauka daga kan gadon ya jawo ni ya dawo dani ya kwantar, yayi min rumfa da jikinsa yace "ba wani abu zanyi miki ba fa kike ta wannan gudun, wani cikin zanyi miki, kinga sai ki haifa min twins" na fara dariya nace "kai wa yace maka haka ake yin twins din?" Ya saka hannu cikin riga ta yace "haka ake yi mana, in aka yi ciki sai a sake yin wani sai a haifi guda biyu" na lumshe ido ina jin abinda hannunsa yake min nace "gaskiya sultan bacci kake yi a biology classes dinka na secondary school" na bude ido ina kallonsa yana min murmushin mugunta ganin yadda jikina ya fara saki, Sultan ya riga ya gane lagona, duk wani guje guje na da waye, he just need to put his hands on me shikenan magana ta kare. Sai da ya tabbatar he got me right where he wants me sannan ya fara raba jikinsa da nawa a hankali still da murmushi akan fuskarsa, naga cewa da gaske tashi yake son yi ai kuwa na saka hannu biyu na jawo shi na dawo dashi na hade bakinmu, ina jinsa yana dariya a cikin kirjinsa, a raina nace 'wallahi sai na rama, kayi da 'yar halak'.
Anan daki na yayi wanka, sai naga ya saka kaya kamar mai shirin fita, nace "fita zaka yi ne?" Yace "ba nisa zanyi ba, cikin gida zanje gurin Takawa" naji dadi sosai nace "naji dadi sosai da zaka je gurinsa, shima kuma zaiji dadi" ya zauna a bakin gado yana kallona ina goge ruwa a kaina, na gane magana yake so muyi dan haka na karaso na zauna kusa dashi, yace "ina so muyi magana dashi ne akan Abbas. Ya dage lallai sai ya kore shi daga gidan nan. Ni kuma ina ganin rashin kyautawar hakan, shi Abbas ba laifinsa bane ba, bashi ya zabi yadda haihuwarsa zata kasance ba, ba kuma shi ya zabi yadda za'a raine shi ba, bai kamata ace zai yi paying for his parents crime ba" na saka hannu ina kara kwantar da kwantaccen gashin kansa nace "me kake so ayi yanzu?" Yace "so nake yi Takawa ya kira shi su zauna ya gaya masa gaskiyar lamari da kansa cikin sigar lallami da lumana, ya kuma barshi ya cigaba da zama a gidan nan ya kuma cigaba da zuwa fada, babu wanda zai san abinda ya faru sai mu kadai. Kinga in akayi haka sunan family din da suke ta fighting for zai zama ba'a bata shi ba, kowa zai samu abinda yake so. Masu kirari suna yiwa sarki kirari da uban masu uba uban marasa uba, to gwara ya fara zama uban marasa uban akan Abbas" tunda ya fara maganar kallonsa kawai nake yi, a raina nace 'masha Allah' sai daya gama sannan nace "hakan shine dai dai mijina, am very proud of you. Cikar imanin mutum shine ya so wa dan'uwansa abinfa yake so wa kansa, kasan zafin rashin iyaye shi yasa kake kula iyakacin karfinka kaga babu wanda ya dandana wannan zafin, ko da kuwa mutumin da ya aikata maka sharri ne, cikar mutum shine ya rama mugunta da alkhairi. Allah ba zai taba barinka ta tabe ba sultan" nayi masa kiss a gefen bakinsa, yace "wow" ya juyo sosai ya nuna min bakin ya kashe min ido, na makale kafada ina dariya. Nace "ni kuma ga tawa shawarar; idan kun gama settling wannan maganar, ina ganin ka mayar da Abbas makaranta, yadda zai samu future mai kyau nan gaba, ya koma makaranta ko first degree ya samu ya kammala, in ma ba zai yi aiki ba ya ajiye takardun. Kuma komawarsa makaranta zata saka ya dauke hankalinsa daga kan sarauta yasan cewa yana da opportunities a rayuwa beyond his imagination" sultan ya daga kafada yace "OK, I can see what I can do. Amma in yace baya so kinsan bazan dauke shi aka in kaishi ba"
Washegari suka zauna akan maganar. Abbas did not take maganar lightly kuma ni na fahimce shi, maganar da ciwo. Da kyar Sultan ya shawo kansa dan cewa yayi sai yaga bayan Hajiya, Hajiya kam tayi kuka da idonta, ranar Abbas a gidan mu ya kwana part din baki maza. Bayan sultan ya dawo daga gurinsa ya same ni zaune da hijab ga key din mota a hannuna, ya tsaya rike da labule yana kallona, na langwabar da kai gefe, yace "yau kuma me babyn take so?" Nace "Namiji ne fa ba mace ba. Vanilla flavoured ice cream yake so. Sannan da sponge cake ya sha cream da yawa. Sai kuma tsire mai kuli kuli" dariya yayi sosai ya karaso ya karbi key din ya miko min hannunsa yace "you got it". Muna tafiya a mota muna shan ice cream din mu wayar sultan tayi kara, ya dauka, daga gaisuwar da yake nasan Takawa ne, yaje ya tarar bama nan, budar bakin sultan sai cewa yayi "mun tafi shan ice cream, baby ne yake rigima yace shi ice cream zai sha" na bude baki ina kallonsa, duk inda kake tunanin rashin kunyar sultan ta wuce nan, yace "what? He deserves to know da wuri saboda ya fara siyan pampers".
A cikin satin Takawa yaje maiduguri nemarwa Amir auren Aishan sa, ai kuwa iyayenta jiki na karkarwa suka ce sun bayar. Tare da sultan suka tafi. A bauchi suka sauka sannan suka hau motoci zuwa maidugurin, suka kuma dawowa bauchi igan sarki suka yi taro sannan suka dawo Abuja. Tun a hanya sultan yayi min waya wai ya gaji, shi ya dade rabon dayayi irin wannn gajiyar. Yana dawowa kuwa da kyar na samu yaci abinci duk kuwa da soyayyar sultan da abinci. Dakinsa ya wuce yana tafiya yana hada hanya saboda bacci. Ina kallonsa ina dariya a raina. Allah ya nuna min ranar da zan rama abinda sultan yake yi min a gidan nan, yau zai gane shayi ma ruwa ne, zai ji yadda nake ji idan ya hanani bacci. Dakina na tafi nima naje na tsalala wanka, na shafe jikina da turaruka da mayuka irin duk wanda sultan yake so, na dauko wata rigar bacci na da tun da nazo gidan ban taba saka taba saboda kallonta ma kadai in nayi kunya nake ji, na saka, na dauko jan jambaki da nasan yana ruda sultan na shafa a lips dina, na zura hijab a raina ina cewa sultan yau ka kade har ganyenka. Ina shiga dakin na ganshi ya bararraje akan gado daga shi sai three quarter wando, ya kure ACn dakin kamar ka shiga freezer, na taba jikin sa naji sanyi kalau, naje na rage ACn na dawo ina kallonsa, a hankali na hau kan gadon na fara shafa fuskarsa, "sultan? Sultan?" Amma sultan shiru kamar gawa, nayi masa chakulkuli a kafa irin yadda yake min amma bai san ina yi ba, a raina nace aikuwa sai ka tashi yau. Na shiga toilet na dauko cotton bud, nazo na fara sosa masa kunne a hankali, yayi juyi ya janyo pillow ya dora akan sa. Haushi kamar ya kashe ni amma naki hakura, na fara shafashi duk inda nasan yana so amma maimakon ya farka sai jikin sane yake farkawar. Naji tsoro na daina. Na koma kiran sunan sa da dan karfi, sai a lokacin yayi juyi ya dauke pillow daga kansa, na kara volume din kirana, ya dan bude idonsa da suka yi ja sosai saboda bacci ya kalleni kamar zaiyi kuka, nace "pay back time" ya kwabe fuska ya gane me nake nufi yace "dan Allah Moon ba yau ba. Ki bari wata rana kya ramar, you have no idea irin baccin da nakeji yau" nace "nima lokacin da kake tashina you had no idea irin baccin da nake ji" bai ce min komai ba ya juya baya ya ja bargo, na tsallaka ta samansa na yaye bargon ina dariya, hankali na ya kwanta, ko a haka na barshi nima na rama. Ya dago yana kallona ina dariya, a hankali naga baccin idonsa yana washewa lust yana replacing baccin, idonsa akan rigar dake jikina, nayi sauri na daina dariyar nace "shikenan ma babu wani abu na hakura kwanta kayi baccinka" ya dago yana kallon fuskata yanayinsa yana chanzawa, yana min rikitaccen kallo yace "no thank you, na fasa baccin kuma, I got something sweeter than bacci" da sauri na ja da baya, yau na kunto wa kaina ruwa kuma bani da lema, ai kam kafin in sauka ya kamo ni yana kare min kallo, na fara bashi hakuri "kaga ka gaji da yawa, dan Allah ka kwanta kayi baccinka kawai, kaga gobe zakaje office kar kazo ka makara" yayi dariya yace "a da kenan, yanxu na chanza shawara" ya kawo bakinsa dai dai kunnena yace "tunda har kika tambayeni bashin da kike bina, dole ki karba".
Nasha kama Sultan yana kallon picture din Ummee a waya ta, sai nazo kuma sai ya basar yayi kamar wani abin yake yi daban, shi a dole wai bai damu da ita ba. Ni kuma da naga haka sai ba saka hoton nata a screen saver dina, yana dauka ya gani ya juyo yana kallona da alamar tambaya, na daga masa kafada nace "for easy viewing" ya ajiye wayar yayi tafiyar sa irin baya son maganar nan. A bangaren Hafsat kuwa har suka gama zaman su a Riyadh Ummee bata fada mata wata maganar da zata dangantata da Nigeria ba ko kuma da Sultan. Rannan kawai sai ga Hafsat ta kirani tace zasu koma Riyadh Abban Zayed baya jin dadi zasu je su duba shi. Kuma tayi min alkawarin insha Allah wannan karon zata samo labari ko da kuwa a gurin Ummeen zayed ne. Kwana uku bayan nan muna zaune da Asmau tana yi min kitso sai ga wayar Hafsat na dauka ina addu'ar Allah yasa labari mai dadi ne, tace "Moon she talked to me" nace "how managed? Ya kika yi mata?" Tace "zama nayi ina ta bata labarin Nigeria da Abuja, na kuma bata labarin Mommyn mu da yadda take son mu bata son rabuwa damu ko kadan. Irin heart to heart talk din nan. Daganan kawai sai tace min ai itama tana da da, kuma tana sonsa fiye da komai a duniya, tana nan kuma tana jiran ranar da zai zo gurinta. All these years zaman jiran yazo gurinta take yi, all these dukiyar da take tarawa, shi take ajiyewa dan tasan komai daran dadewa zai zo gurinta" nayi shiru inajin hawaye yana taruwa a idona, tace "yanzu kina ganin in gaya mata nasan shi ko kuma me kike so in ce mata" na danyi tunani kadan sannan na tsarawa Hafsat duk abinda nake so ta gayawa Ummee. A ranar da daddare muna zaune a palon Sultan, ina kwance akan kujera ina game a wayarsa shi kuma kan study table dinsa yana zane, sai ga kiran Hafsat a waya ta, sai da na jera adduoi sannan na dauka, na daga murya yadda zan calling attention din sultan nayi mata sallama, tace min da fulatanci "na gaya mata duk yadda kika ce" ina jin haka na saka waya ta a hands free, Hafsat ta koma turanci "Maimunatu this is zayed aunt, she wants to talk to you about her son" ina kallon sultan ya ajiye pencil din hannunsa, nima sai da na hadiye yawu saboda bakina naji ya bushe, ina jin Hafsat tana bata wayar tana mata bayanin ga sister din tata, naji muryarta ta larabawa tace "As Salaam-o-Alaikum" na amsa mata murya ta na rawa, idona akan na sultan wanda ya juyo yana kallona, ta fara magana da turancin ta mai accent din larabawa "Am sorry to disturb you. What is your name?" Nace "Maimunatu" tace "Nice name you get, I always wanted to name my daughter that, but I didn't get a daughter I got a son. I talked to your sister about him she said she didn't know him, but she said you might. His name is Sultan, he is a Prince in Abuja. Very handsome and very strong. I only want to know how he is doing" sai da na tattaro dukkan jarumtata sannan na iya magana, still idanuna a cikin na sultan wadanda suka chanja kala, nace "I don't only know him, he is my husband, Ummee"
MAIMOON
By
Maman Maama
Table of Contents
Chapters
- 1 Episode One : The Beginning of the Beginning
- 2 Episode Two: Meet my Family
- 3 Episode Three: Loved by All
- 4 Episode Four: Moon's Sister
- 5 Episode five: The Strangers
- 6 Episode six: The Challenge
- 7 Episode Seven: The Thin Tall Man
- 8 Episode Eight: The New Imam
- 9 Episode Nine: Give Me a Chance
- 10 Episode Ten: I Don't Know
- 11 Episode Eleven : The Protector
- 12 Episode Twelve : This is Me
- 13 Episode Thirteen : This is Me 2
- 14 Episode Fourteen : The Limit
- 15 Episode fifteen: blood is Thicker than Water.
- 16 Episode Sixteen : The Letter
- 17 Episode seventeen: Reply
- 18 Episode eighteen: what's Next?
- 19 Episode Nineteen: The Goodbye
- 20 Episode Twenty: The New Job
- 21 Episode Twenty one: Amira
- 22 Episode Twenty Two: Efisowa
- 23 Episode Twenty three: The Break up 💔
- 24 Episode Twenty Four: The Heartbreak 💔
- 25 Episode Twenty five: The Eclipse
- 26 Episode Twenty Six: A Step Further Away
- 27 Episode Twenty Eight : University of Oxford
- 28 Episode Twenty Nine: The Message
- 29 Episode Thirty : The Final Blow
- 30 Episode Thirty One: Let it go
- 31 Episode Thirty Two : Munnir
- 32 Episode Thirty Two : Mahdi
- 33 Episode Thirty Three: Zayed
- 34 Episode Thirty Four : Back to Square One
- 35 Episode Thirty Five : When Destiny Calls.
- 36 EpisodeThirtySix: Interesting
- 37 Episode Thirty Seven : The Dinner
- 38 Episode Thirty Eight : The Shadow
- 39 Episode Thirty Nine : The Shadow 2
- 40 Episode Forty :TheShadow 3
- 41 Episode Forty One : Born for This.
- 42 Episode Forty Two : Born for This
- 43 Episode Forty Three: America
- 44 Episode forty four : America 2
- 45 Episode Forty Five : The Rush
- 46 Episode Forty Six : The Repentance
- 47 Episode Forty Seven : Amir
- 48 Episode Forty Eight : Awkward
- 49 Episode Forty Nine : Ya Habeeb
- 50 Episode Fifty : Munir 2
- 51 Episode Fifty one : Mommy
- 52 Episode Fifty Two : The Journey
- 53 Episode Fifty Three : Daddy
- 54 Episode Fifty Four : Her Father's Daughter
- 55 Episode fifty five : Her Father's Daughter 2
- 56 Episode Fifty Six : What You Sow
- 57 Episode Fifty Seven : What You Sow 2
- 58 Episode Fifty Eight : I Missed You
- 59 Episode Fifty Eight : For You, Only You
- 60 Episode Sixty : The Prince
- 61 Episode Sixty One : Save the Date
- 62 Episode Sixty Two : The Manager
- 63 Episode Sixty Three : Amira 3
- 64 Episode Sixty Four : The Past and the Future
- 65 Episode Sixty Four : The Visitors
- 66 Episode Sixty Six : The Wedding
- 67 Episode Sixty Seven : The Wedding 2
- 68 Episode Sixty Eight : The Wedding Night
- 69 Episode Sixty Nine: The Wedding Night 2
- 70 Episode Seventy : The Wedding Night 3
- 71 Episode Seventy One : The Honeymoon
- 72 Episode Seventy Two : My Everything
- 73 Episode Seventy Three : His Father's Son
- 74 Episode Seventy Four : The Cook
- 75 Episode Seventy Five : The Emir
- 76 Episode Seventy Six : The Visitors
- 77 Episode Seventy Seven : Amina
- 78 Episode Seventy Eight : The Storm
- 79 Episode Seventy Nine : The Lightening and The Thunder
- 80 Episode Eighty : The Skeleton in The Closet
- 81 Episode Eighty one : The Skeleton in the Closet 2
- 82 Episode Eighty Two : The Light
- 83 Episode Eighty Three : The News
- 84 Episode Eighty Four : Little Love
- 85 Episode Eighty Five : Ibrahim
- 86 Episode Eighty Six : The Phone Call
- 87 Episode Eighty Seven : Riyadh
- 88 Episode Eighty eight :Khairat
- 89 Episode Eighty Nine : Khairat 2
- 90 Episode Ninety : His Mother's Son
- 91 Episode Ninety One : His Mother's Son 2
- 92 Episode Ninety Two and Three : Maldives 1 and 2
- 93 Episode Ninety Four : RIP
- 94 Episode Ninety Five : The Light
- 95 Episode Ninety Six : The New Bride
- 96 Episode Ninety Seven : The Real Prince
- 97 Episode Ninety Eight: My Baby
- 98 Episode Ninety Nine : New Little Love
- 99 Episode Hundred : Not The End.