Chapter 32
Episode Thirty Two : Mahdi
Na jima a tsaye ina kallon kofar da ya rufe bayan ya fita, me wannan mutumin yake nufi ne? Ni wannan ko a kafa aka daura min shi ai na gwammata in dau wuka in datse kafar in huta. Na zauna akan kujera na dafe kaina da hannayena. Dear Ibrahim, is this our destiny? Sai kuma naji haushin kaina, why am I even thinking of Ibrahim now. Me yasa har yanzu na kasa cire shi daga raina? Shekara biyu kenan rabona dashi, shekara daya kuma da yin aurensa, maybe har sun haihu by now. Jiki ba karfi na tashi na shiga daki na kwanta kusa da Hafsat. Tun muna yara dama ni bana son munnir, sam bai yi mun ba, ballantana yanzu da ya kara habaka, I must be strong, I must pray hard, in nemi zabin Allah kuma nasan Allah ba zai zabar min munnir a matsayin miji na ba. Ina nan kwance inna ta shigo take cewa waye ya ajiye kudi a palo? Nace "mata munnir ne" ta ajiye akan dressing mirror sannan ta fara yi mana fadan mun kwanta da la'asar bayan munsan babu kyau.
A ranar da daddare har nayi bacci na fara jin hayaniya sama-sama, na farka sai naji a compound ake yi, na tashi da sauri na fita palo sai naga Hafsat a tsaye a bakin window tana lekawa, na karasa kusa da ita ina tambayar ta "lafiya" ta yi min alama da inyi shiru. Nan muka cigaba da leke tare. Hajja ce take balbalin fada "ai ba haka mukayi dashi ba, ce min yayi ba zasu tafi ba sai an daura aure, kuma yanzu kawai sai ace min wai gobe zasu wuce?" Baffa yace "kai muhammadu mai yasa kayi mata alkawarin da kasan ba zaka iya cikawa ba?" Daddy yace "baffa ni abinda nace shine, in har an samu fahimtar juna a tsakanin yaran to baza mu bar garin nan ba sai an daura aure, kuma ai daga zuwan manniru yau ba za ace har sun fahimci juna shida maimuna ba, abinda nake gani shine kar ayi gaggawar auren nan ya zama an bata zumunci maimakon a gyara shi, a bari idan yaran sun daidaita tsakanin su shikenan" hajja ta katse shi da cewa "yo yaushe zasu daidaita tsakanin su bayan zaka dauke yarinyar ku tafi? Ai in ma so ake su daidaita sai a bar yarinyar anan yadda zasuke ganin juna" kawu Aliyu yace "hajja rayinyar nan fa karatu take yi, ya za'ayi a raba ta da karatun ta? Daga manniru har maimuna 'ya'yan mu ne, ba za mu so mu tauye wa wani hakkinsa ba, tunda yarinyar nan tace bata son shi a rabu da ita, hajja zamani fa ya chanja, yanzu da da ba daya bane, idan da anyiwa yara aure ba tare da son ransu ba suna hakura yaran yanzu zasu zo su bata mana zumuncin mune. Maimuna yarinya ce mai hankali wallahi, Manniru ba shi da kunya sam, kuma ya girme mata nesa ba kusa ba, ni dai baffa ina ganin in akayi wannan hadin an tauyewa yarinyar nan hakkinta kuma zata iya ta kullace mu har abada" a raina nace "God bless uncle Aliyu, Allah ya baka abinda kake so duniya da lahira" na jingina kaina wanda already ya dau zafi a jikin Hafsat ina cigaba da sauraron mahawarar da zata iya chanza rayuwata gabadaya. Baffa naji ya fara magana "kai manniru kana son auren maimuna kace ko?" Nayi sauri na leqa window, munnir na gani a zaune a gefen hajja, murya kasa kasa yace "eh baffa" baffa yace "to shikenan, na baka damar ka cigaba da neman auren ta daga yau har zuwa ranar da zata gama karatun ta, idan kafin nan ta amince tana sonka shikenan" da sauri munnir yace "baffa shekara uku kenan fa nan gaba" tas, naji saukar mari daga hannun uncle Aliyu zuwa fuskar Munnir, inajin Hafsat tana dariya kasa2, nan uncle Aliyu ya rufe shi da fada "baffan kake musawa magana? Rashin kunyar taka takai har haka?" Baffa yace "rabu dashi Ali, idan ba zai jira ba ya nemo wata a aura masa, ni na gama magana" daga nan ya mike yayi hanyar part dinsa. Nan gurin ya hargitse kowa yana fadin albarkacin bakinsa, kuma daga dukkan alama fiye da rabin mutanen gurin basa bayan wannan hadin saboda duk suna yabon halayena tare da kushe da Allah wadaran halayen munnir, inna sam bata cewa komai, hajja kuwa sai kumfar baki take har da cewa duk sanda mukayi kwantai kar a kawo mata. Munnir kuwa tun daga inda nake nake hango yadda ya murtuke fuska yana bin kawunnan mu da mugun kallo.
Washe gari tun assuba muka fara wanka muna fitar da akwatinan mu, inna ta zo ta saka mu a gaba da nasiha "ku kyautata addinin ku, ku bi iyayenku, ku tsarkake zuciyar ku daga mugun nufi akan kowa, in kuka yi haka Allah ba zai munana rayuwar ku ba, kullum in za kuyi addu"a ku nemi zabin Allah, kar kuce 'Allah ka bani kaza ko Allah ka yi min kaza' gwara kuce 'Allah ka zaba min mafi alkhairi a duk al'amurana'. Ku yawaita karatun alqur'ani dan shi kariya ne, musamman ayatulkursiyu, ku mayar da ita tamkar babbar kawarku kullum ta kasance a bakin ku, in zaku kwanta bacci kuyi alwala, na tabbatar muku in kuka rike wannan duk wani mugun nufi na mutun, aljani ko shaidani ba zai same ku ba".
Kiri2 sanda mukaje yiwa Hajja sallama taki kulamu, haka muka taso muka fito, Hafsat tace a hankali "kinyi wa kanki" muna fita waje naga nuraddeen tare dasu ya Walid, muka gaishe su muka wuce. Na shiga gaba Hafsat ta zauna a baya tunda tare zasu zauna da mommy, ba tare da Amina zamu tafi ba, saita karasa hutunta anan zata same mu a Abuja, ya Walid ne zai tuka mu. Ina zama sai ga nuraddeen yazo yana tsokana ta "amaryar yayan mu" sai na samu kaina da daure fuskata, yayi dariya yace "congratulations though, naji yadda aka kare maganar jiya" nayi masa murmushi nace na gode, ya juya yace "gashi nan yazo sallama bara insan inda dare yayi min" sai da ya matsa sannan na hango munnir yana tahowa inda motar mu take, sai a lokacin nayi nadamar fito war mu da wuri, da munsani mun jira mommy dan nasan duk rashin kunyarsa ba zai yi a gaban mommy ba dan zata iya kwakkwada masa mari. Na yi sauri na dauko wani katon bakin glass na saka wanda ya kusa rufe rabin fuskata, yana karaso wa na daga glass din motar, ga mamakina sai naga ya zagayo ta side din driver, ya shigo ya rufe kofar, daga dukkan alama bai san da Hafsat a motar ba, na dauke kaina tamkar ban san ya shigo ba, murya can kasa yace "ba gaisuwa" nayi banza na rabu dashi, ya sake cewa "shine kika ce da kawu ambassador ba kya so na ko?" A zahirin gaskiya ni daddy bai tambayeni ba, asali ma bamu taba maganar dashi ba, nasan ya fadi haka ne saboda shima baya son wannan hadin. Ji yayi bani da niyyar cewa komai ya sake cewa "ina so ki sani, yanzu na fara sonki, kuma zan cigaba da bin wannan tsohon har sai ya amince da maganar nan dan ni yadda nake jinki bazan iya jiran 3 years ba" still no reply from me, na juya kaina ma ina kallon daya side din, kawai sai jin hannunsa nayi a fuskata yana kokarin juyo dani in kalle shi, Hafsat tana daga baya tace "hey, don't" a tsorace ya juya ya kalleta, duk da ban juya ba na tabbatar harararsa take yi, yace "hey, yaushe kika shigo?" Tace "tun kafin ka shigo, naji komai" yace "sa'ido fa babu kyau, musamman a harkar miji da mata" Hafsat tace "not even in your dreams". Suna cikin haka mommy ta fito, da sauri ya juyo gurina yana min blowing kiss tare da cewa "sai munyi waya" ya fice, a tare mukayi tsaki ni da Hafsat. Yana fita gurin mommy ya tafi ya durkusa yana gaisheta, Hafsat tace "chusa kai ba kwarjini" mommy ta amsa masa fuskarta a sake sannan ta karaso mota. Su daddy ma duk suka shiga motar su shida ya Habeeb da faruk, sai motar security a gaba, muka tafi.
Tun daga ranar har muka koma England kullum sai munnir ya kira ni a waya, na rasa a gurin wanda ya samu numberta, muna komawa England muka koma school.
Shakara daya tazo ta wuce muna ta karatu, har shekarar ta wuce babu Ibrahim babu labarinsa, munnir kuwa har yau yaki hakura duk da maimaita masa da nake yi kullum cewa bana son sa. Amira ma muna da contact da ita tana ci gaba da karatun ta a abuja. An tura mu clinicals, daddy ya saka aka tura mu asibiti daya da Hafsat amma ita tana bangaren gynecology ni ina neurology, Amina ma an samar mata admission ita da faruk sun fara karatu, yaya Walid ya gama, ya Habeeb kuma yana project dinsa.
Na koyi abubuwa da dama a asibitin nan, anan na kara sanin irin baiwar da Allah yayi wa bil adama, naga yadda ake bare kan mutun ayi masa aiki a kwakwalwa sannan a mayar a rufe, na koyi yadda ake yin hemisphecrotomy inda ake chire rabin kwakwalwar mutun a bar masa rabi kuma ya tashi lafiya lau. Na koyi abubuwa da yawa wadanda nake sa ran zan dawo Nigeria in yi.
A asibiti na hadu da Mahdi. Nasha ganinsa amma bamu taba magana ba saboda ba daga school daya muka zo ba dan haka ban sanshi ba. Rannan mun fito daga wata theatre ina zaune ina hutawa kawai sai naji anyi min sallama, na daga kaina sai na ganshi, na amsa masa cikin mamakin accent din hausa da naji a bakin sa. Fari ne tas, irin farin da har jaja yake yi kamar in ka taba jini zai fito, kirar jikinsa dai dai misali, komai nasa kamar shi yayi wa kansa, sam bai yi kama da hausawa ba. Ban gama mamaki ba sai ji nayi yace "sunana Mahdi Datti Sufyan, daga university of Michigan, ni dan garin kano ne, unguwar gwauron dutse. Naga kamar kema 'yar Nigeria ce ko?" Sai a lokacin hankali na ya dawo kaina, sannan na fahimci cewa na bude baki ina kallon sa, nayi sauri na rufe bakina nace "wait Datti Sufyan? The name sounds familiar" yayi dariyar data bayyana kyawawan jerarrun hakoransa yace "yah... My father is kind of famous in kano" ya zauna a kusa dani yace "baki gaya min sunan kiba amma" na sake tattaro hankali na nace "sunana Maimoon Muhammad Dikko, I am Nigerian also, I.." Ya katseni "ambassador MD?" Nace "kasanshi ne?" Yace "yeah..... Da akwai sanda baba yazo ya kaini embassy gurinsa, yace in ringa zuwa ina gaishe shi, amma kinsan halin students ban taba zuwa ba. So you are his daughter?" Na gyada kai ina murmushi, yace "nice to meet you Maimoon" nace "nice to meet you too Mahdi"
#ga masu complain cewa Moon bata da kamun kai, ina tuna mana cewa akwai mutane in reality da suke exactly kamarta wadanda sam basu iya bata rai ba, suna da faran faran da saurin sabo da mutane, yawancin su kuma suna da mugun kirki. Hakan ba yana nufin basu da kamun kai ba, kawai nature dinsu ce haka, kuma yawanci mutane suna son su. Fara'a ita take jawo mutane, su kuma mutane rahama ne#
Thank and I love you all.
Table of Contents
Chapters
- 1 Episode One : The Beginning of the Beginning
- 2 Episode Two: Meet my Family
- 3 Episode Three: Loved by All
- 4 Episode Four: Moon's Sister
- 5 Episode five: The Strangers
- 6 Episode six: The Challenge
- 7 Episode Seven: The Thin Tall Man
- 8 Episode Eight: The New Imam
- 9 Episode Nine: Give Me a Chance
- 10 Episode Ten: I Don't Know
- 11 Episode Eleven : The Protector
- 12 Episode Twelve : This is Me
- 13 Episode Thirteen : This is Me 2
- 14 Episode Fourteen : The Limit
- 15 Episode fifteen: blood is Thicker than Water.
- 16 Episode Sixteen : The Letter
- 17 Episode seventeen: Reply
- 18 Episode eighteen: what's Next?
- 19 Episode Nineteen: The Goodbye
- 20 Episode Twenty: The New Job
- 21 Episode Twenty one: Amira
- 22 Episode Twenty Two: Efisowa
- 23 Episode Twenty three: The Break up 💔
- 24 Episode Twenty Four: The Heartbreak 💔
- 25 Episode Twenty five: The Eclipse
- 26 Episode Twenty Six: A Step Further Away
- 27 Episode Twenty Eight : University of Oxford
- 28 Episode Twenty Nine: The Message
- 29 Episode Thirty : The Final Blow
- 30 Episode Thirty One: Let it go
- 31 Episode Thirty Two : Munnir
- 32 Episode Thirty Two : Mahdi
- 33 Episode Thirty Three: Zayed
- 34 Episode Thirty Four : Back to Square One
- 35 Episode Thirty Five : When Destiny Calls.
- 36 EpisodeThirtySix: Interesting
- 37 Episode Thirty Seven : The Dinner
- 38 Episode Thirty Eight : The Shadow
- 39 Episode Thirty Nine : The Shadow 2
- 40 Episode Forty :TheShadow 3
- 41 Episode Forty One : Born for This.
- 42 Episode Forty Two : Born for This
- 43 Episode Forty Three: America
- 44 Episode forty four : America 2
- 45 Episode Forty Five : The Rush
- 46 Episode Forty Six : The Repentance
- 47 Episode Forty Seven : Amir
- 48 Episode Forty Eight : Awkward
- 49 Episode Forty Nine : Ya Habeeb
- 50 Episode Fifty : Munir 2
- 51 Episode Fifty one : Mommy
- 52 Episode Fifty Two : The Journey
- 53 Episode Fifty Three : Daddy
- 54 Episode Fifty Four : Her Father's Daughter
- 55 Episode fifty five : Her Father's Daughter 2
- 56 Episode Fifty Six : What You Sow
- 57 Episode Fifty Seven : What You Sow 2
- 58 Episode Fifty Eight : I Missed You
- 59 Episode Fifty Eight : For You, Only You
- 60 Episode Sixty : The Prince
- 61 Episode Sixty One : Save the Date
- 62 Episode Sixty Two : The Manager
- 63 Episode Sixty Three : Amira 3
- 64 Episode Sixty Four : The Past and the Future
- 65 Episode Sixty Four : The Visitors
- 66 Episode Sixty Six : The Wedding
- 67 Episode Sixty Seven : The Wedding 2
- 68 Episode Sixty Eight : The Wedding Night
- 69 Episode Sixty Nine: The Wedding Night 2
- 70 Episode Seventy : The Wedding Night 3
- 71 Episode Seventy One : The Honeymoon
- 72 Episode Seventy Two : My Everything
- 73 Episode Seventy Three : His Father's Son
- 74 Episode Seventy Four : The Cook
- 75 Episode Seventy Five : The Emir
- 76 Episode Seventy Six : The Visitors
- 77 Episode Seventy Seven : Amina
- 78 Episode Seventy Eight : The Storm
- 79 Episode Seventy Nine : The Lightening and The Thunder
- 80 Episode Eighty : The Skeleton in The Closet
- 81 Episode Eighty one : The Skeleton in the Closet 2
- 82 Episode Eighty Two : The Light
- 83 Episode Eighty Three : The News
- 84 Episode Eighty Four : Little Love
- 85 Episode Eighty Five : Ibrahim
- 86 Episode Eighty Six : The Phone Call
- 87 Episode Eighty Seven : Riyadh
- 88 Episode Eighty eight :Khairat
- 89 Episode Eighty Nine : Khairat 2
- 90 Episode Ninety : His Mother's Son
- 91 Episode Ninety One : His Mother's Son 2
- 92 Episode Ninety Two and Three : Maldives 1 and 2
- 93 Episode Ninety Four : RIP
- 94 Episode Ninety Five : The Light
- 95 Episode Ninety Six : The New Bride
- 96 Episode Ninety Seven : The Real Prince
- 97 Episode Ninety Eight: My Baby
- 98 Episode Ninety Nine : New Little Love
- 99 Episode Hundred : Not The End.