Chapter 34
Chapter 34
yake ce mata yayinda ita kuma yaci gaba da kiranta Babynsa.Surbajo godiya tadunga yiwa Al-ameen da Aisha abisa karar dasuka yimata. Rayuwa taci gaba da tafiya inda Ahalin yanzu Surbajo tagama university d'inta Amman Al-ameen yace bazatayi aykiba,bata musaba ta hak'ura,Aisha nakan nata karatun dan itama tuni takoma makaranta,Yaransu gwanin Sha'awa bame gane wannance Mamana acikinsu sabida duk kulawa d'aya suke basu. Al-ameen hankalinshi akwance na iyalanshi ma haka so da k'aunar dake tsakaninshi da Surbajo se son barka duk da yana b'oyewa gudun kar ran Aisha ya b'aci,amman son da yakewa Surbajo gagara misaline. ina labarin su Ruky? Ruky tunda suka bar gidan Aisha da wata uku tafara jin canje canje ajikinta dan haka ta nufi asibiti gwajin farko aka bata sakamakon HIV,yanke jiki tayi tafad'i sumammiya Gado aka bata a asibitin.Zuly nasamun labari tazo asibitin tagaida Ruky kamar abin arzik'i daga k'arshe se cewa tayi. " Wannan k'awance namu ina sonshi tunda gashi nayi nasarar saka miki ciwon danake d'auke dashi."daganan takwashe labarin komai tafad'a musu tana dariya, Maman Ruky shak'e Zuly tayi kamar zata kasheta tana yimata Allah ya isa,likitoci sunkasa kwaceta a hannunta dan haka suka kira police sukayi gaba da Zulyn. Ruky ko kuka take me tsanani tashiga barin wasiyya tace ma mamarta tanemarmata yafiyar Aisha tasan hakkintane yake bibiyarsu don Allah tayafemata,ranar Ruky bata sake kwanan duniyaba tace ga garinku bayan tayi kalmar shahada.Allahu akbar Allah nason masu tuba Allah kasadamu da rahamarka dan darajar Annabi da alqur'ani Ameen. Zuly ko kotu aka shigar da ita k'ara inda aka yanke mata d'aurin rai da rai agidan kaso,gamida horo me tsanani har iya k'arshen rayuwarta. Duniya kenan shiyasa akace abinda kashuka shi zaka girba Allah yasa mudace Ameen. Su Aisha dasuka sami labarin mutuwar Ruky har gida sukaje gaisuwa ananne mamar Ruky take sanar da Aishan sak'on Rukyn,kuka Aisha tasa tace, "Wlh nayafe mata duniya da lahira Allah yajik'anta yakyauta namu zuwan," godiya yan uwan Ruky sukai tayiwa Aishan. To Ruky Allah yajik'anki yasa kin huta ya yafemiki kurakuranki. Surbajo uwar biyu yanzu haka wani cikinne ajikin Surbajo tsoho yafi na Aisha girma scanning na farko aka shaida musu yan biyu ne duka mace da namiji,fad'in murna da farincikin da Al-ameen da Aisha sukayi page din yayi kad'an se fatan Allah ya sauketa Lfy. Tahaihu Lfy inda yaran suka ci sunan iyayen Al-ameen. So da k'auna agurin Al-ameen da Surbajo abin fatane ga kowacce mace agidan mijinta. *Godiya ga Allah subuhanahu wata'ala daya bani ikon kammala wannan littafi nawa me suna Surbajo.ya Allah kuskuran danayi kagafartamin wa'azin dake ciki gamu mata masu zafafa k'iyayyar kishiya Allah yasa mata sund'auki darasin, maza mata masoyana ako ina kuke afad'in duniya me surbajo na k'aunarku harcikin ranta Allah yabarmu damasu son mu ameen wandama baya sonmu Allah ka jarabceshi da sonmu,Allah yazaunar damu cikin aminci. Kubiyoni cikin sabon littafina mesuna CIN AMANA KO FANSA* NGD maman Yusuf love you all 💋💋💋 #complied by Princess Aysha Muhammad
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34