Chapter 11
Chapter 11
sallama sosai ardo yadunga kara bashi hkr abisa tsautsayin dayafaru sallama yamasa yanufi gurin motarshi kamar anjefota yahango surbajo tafito daga gidan dauke da tulu Zata dibar ruwa tsayawa yayi harta karaso ko kallonshi batayiba Tana kokarin wuceshi Dan ita yanzu tsoronshi takeji kiran sunanta yayi arude tajuyo Dan tunda take babu Wanda yataba kiranta da sunanta taji dadin sunan kamarshi tsayawa tayi ainda take ba gaisuwa yatambaya kayi hkr ina kwana murmushi yayi sannan yaamsa da Lfy yakara da ina Zaki ruwa zan debo tabashi amsa muje inrage miki hanya yafadi sannan yajuya yashige motarshi bude mata gaban motar yayi tsayawa tayi kamar da karta shiga sekuma ta tuno bindinga dagudu taje tashige yarufe kofar yatada motor suka tafi afuwan akwai tafiya agabana maassalam maman yusuf 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *SURBAJO* 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 Zahra Muhammad mahmud *page 21-22* Tafe suke yana janta da hira har suka iso bakin rafin yana parking Ta bude motar tafice Tanufi rafin ko sallama bata masa ba Murmushi yayi sannan yace halin surbajo se ita shima bedamu ba yaja motarshi yawuce yana fita agarin wayarshi tafara ringing abokinshine Usman bayan sungaisa yace yanemi wayar alameen din besamuba ko Lfy Dariya yayi sannan yabashi labarin abinda yafaru tsakaninshi da surbajo dariya shima Usman din yayi yace shege mutumina wlh dukanku kunburgeni kunyi dede Allah de yanuna mana ranar bikinnan Hakade suka Dan jima suna hira daga baya sukayi sallama Alameen gidansu yasauka yaci abinci anan abba yake shaidamishi sati mezuwa zasuje nemarmasa auran surbajo .sosai alameen yanuna jin dadinsa dajin zancan godiya yamusu sosai sannan yanufi gidanshi fuskarsa dauke da faraa Koda isarsa Kai tsaye cikin gidan yanufa bayan yagama gaisawa da masu tsaron Lafiyarsa Yana shiga falon Aisha ta taso afusace ta kama kwalar rigarsa tarike sannan tace daga ina Kake kuma agurin wacce shegiyar ka kwana batare daka sanar daniba tafadi cike da rashin kunya ran alameen tuni yafara zafi jin takira surbajo da shegiya Dagowa yayi yace sakeni inwuce Aisha banason rigima yanzu shewa tayi sannan tace ay Wlh inkaga nasakeka kafadamin gurin wacce ka kwana ko anfadamaka bansan taketakenka ba ay Tunda kafara zama bunsuru nagane to Wlh baka isaba bade agidannanba Tass yadauketa da Mari kamin tawatsake yasake Kai mata wani daga bisani yarufeta da duka ihu take Tana neman agaji seda yamata dukan dashi kanshi besan iya adadinsaba sannan yakyaleta tuni tajima da sumewa Ko ajikinshi ya dauko ruwa yasheka mata tafarko sannan yabata amsa dacewa Aisha Tunda nake bantaba ganin jaka kamarkiba dakikiya kawai mahaukaciya Wai kindauka tsaron ki nakeji to Wlh ko daya tausayinki nakeji amma Tunda kin nunamin kedin dabba ce Wlh sena baki mamaki kuma dakikace daga ina nake daga gidan matar dazan Aura nake kisama ranki Wlh aure zanyi nanda sati guda kuma it doesn't matter to me kome nene ze faru yafaru banza tinkiya kawai ko kigyara halinki ko kada ki gyara damuwarkine ko tablet nahana haihuwa dakike sha keze cutar baniba Danni wuyarta nayi auran ya ingijeta tafadi akan tiles sannan yawuce yabarta da faasshen jiki se kuka takeyi ******** Surbajo Tunda alameen yatafi kullum da tunaninsa take kwana take tashi sosai take kewarsa sakamakon so da kaunarsa dasuka addabi zuciyarta tabbas yanzu tana sonshi dari bisa dari zuwa yanzu sunfara samun sabani da jae ganin yanzu batashi takeyiba shiyasa yaja baya shima da ita duk da yanasonta amma baze jure tadunga shareshiba su daddy sunje nemama alameen auranta inda ardo yay matukar murna da afkuwar hakan badan komaiba sedamutuncin iyayensa kamar yadda alammeen yafadawa mahaifinsa daga baya cewa shima bayason bikin yawuce sati guda tokoda suka sanar da ardo bemusamusuba aka tsaida ranar auran sati mezuwa bayan an tambayi surbajo shin kotana sonshi ta amsa da eh tanasonshi Ayimin afuwa nayi tafiyane maman yusuf 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 *SURBAJO* 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀 Zahra Muhammad mahmud *page 23-24* Acikin satin aka soma shirye shiryen biki dan ranar asabar zaa daura auren Aisha Data fuskanci dagaske aure alameen zeyi hankalinta vakaramin tashi yayiba Dan haka tanufi kawayenta subata shawara Koda isarta gidansu zuly kuka tasa mata tace kawata nashiga uku alameen aure zeyi Dan Allah kitaimakeni narasa abinyi Wani dadine yarufe zuly Dan Dama sun jima suna jiran wannan ranar Amman afili kukan tasa itama suka rungume juna dakyar sukayi shuru zuly tace wannan tashin hankali dame yay Kama wallahi bazamu zuba ido muna kalloba semun dauki mataki ki kwantar da hankalinki Gobe in Allah ya kaimu zamuje gidan wani malaminmu yaiya ayki sosai zeshare miki hawayenki sosai Aisha tayi murna da shawarar aminiyartata Dan bata bar gidanba se dare Alameen murna yake sosai Badan komaiba sedan auren cartoon dinshi dazeyi Usman dariya kawai yakeyi dazaran yaji alameen yakira surbajo da cartoon Dan yana da tabbacin alameen dinne zekoma cartoon din Shiri suke sosai musamman gidansu alameen Dan sunfi kowa murna da auren da alameen zeyi Dubai mommy taje tahadowa surbajo kayan lefe da kayan daki sabida sunce ardo base yayiwa surbajo kayan dakiba su zasuyi Dakuna biyu dake falon kasa nagidan alameen aka shiryawa surbajo kayanta aka kulle dakin yayinda kayan lefenta aka ajiye gidan su alameen sabida ardo yace a ajiyemata acan ********** jae dayasamu labarin surbajo aure zatayi har gida yaje yasameta koda tazo jae rufe idonsa yayi ya zazzagamata masifa har yana cewa auran kwadayi zatayi kuma insha allahu se an sakota kuka surbajo tasa Tana rokonsa ya yafemata Dan tasan bata kyauta mishiba amma bata da iko da zuciyarta takamu da son alameen me tsanani Wanda tanajin bazata iya rabuwa dashiba kuma ita badan kudinsa takesonsaba sedan Allah Jae shima kukan yakeyi Dan kukan surbajo yadagamasa hankali cikin kuka yace ya yafemata Allah kuma yabasu zaman Lafiya da mijinta daganan yawuce yatafi yabarta Tana Ta kuka alameen shida Usman suka dauko hanyar makarfi Dan sunason ganawa da Amarya suji shirye shiryenta da isarsu ardo yasaukesu a dakin saukar baki yasa aka kawo musu fura da nono me kyau sosai Usman yasha furar sabanin alameen dashi ba cimarshi bace seda suka Dan jima dazuwa sannan aka turo surbajo wacce ta yafo mayafi tarufe fuskarta sabida jin kunya sallama tayi tashigo dakin tasami guri tazauna daga nesa dasu dakyar ta iya gaishesu suka amsa cike da barkwanci Usman yace amaryarmu kunyarmu kuma kike Yi haka Ko fuskar bazaki budeba Ay surbajo jitayi wata kunyar tasake kamata Dan haka Kara Rufe idonta tayi Tana murmushi daga cikin mayafinnata hakade Usman yay tajanta da hira amma takasa bashi amsa sabida kunya mikewa Usman yayi yafice daga dakin Dan yabasu guri su tattauna shuru ne yabiyo bayan fitar Usman jin shurun yayi yawa ne yasa surbajo zaton sun fitane daga dakin ne dukansu yaye rufar datayi tayi carab idonta yasauka akan na alameen da tun tuni ita yake kallo dasauri tamaida rufar matsowa alameen yayi gab da ita har jikinsu na gogar juna lullubin ya bude surbajo kankame hannunta tayi a kirjinta sabida batason yakalleta murmushi yayi Dan yafahimci me take boyewa hannuwanta yakamo yaruke anasa sannan yabita da ido yana karewa halittarta kallo ba laifi duk da kankantar shekarun surbajo hakan be hanata mallakar duk wani Abu da yamace ke daukar hankalin da namiji dashiba surbajo duk Ta takura da irin kallon da alameen yake mata kokarin kwace hannunta takeyi amma takasa cikin siririyar muryarta tace kado Don Allah kasakarmin hannuna
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34