Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 17

Chapter 17

Alheri Danko Ne Book 1 Complete Hausa Novel 1,222 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

shafata sai alokacin idonsa yagano masa gashin kanta mai tarin yawa nanfa yarude ya nemi nutsuwarsa ya rasa shi bai ma san ta inda zai fara ba, bakinta ya laluba yasaka cikin nashi yafara tsotsa duk yagama rudewa, wata yar na'ura yadanna abin mamaki sai kawai kujerar tabaje tazama kamar katifa, ahankali yafara fitar da numfashi, kirjinta yafara shafa wanda sukayi mutukar gigita shi, nan yafara fita daga hayyacinsa. [1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [9:59PM, 11/20/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 5⃣6⃣ Na UMMI A'ISHA Shinfidar da ita tafida yayi akan bajajjiyar kujerar yafara bata kiss ta kowanne sashe na jikinta tareda lasar lips dinta, hancinsa ya goga akan nata yadora hannunsa akan kirjinta yafara fincike botiran gabar rigar tata ai hanfa najin haka jikinta yafara rawa, acikin kunnenta yarada mata whats wrong? Idonta cikeda kwalla tace kabari pls, murmushi yayi ya lumshe idonsa dama duk wannan tsiwar taki ke matsoraciya ce? Kinga kuwa bazan bari ba sai nayi abinda nayi niyya, duk da cewa a tsorace take dashi amma sai ta fuske ta murguda masa baki tace kar Allah yasa kayi hakurin ai nasan duk abinka dai ba mutuwa zanyi ba, bakinta ya cafka yafara tsotsar harshenta yana shafar wuyanta har ya gangaro kan na fulaninta baiyi wata wata ba yazame hannun rigarta yafara kokarin tura hannunsa cikin kirjinta amma kuma sai rigarta da bra suka yimasa cikas, gashin kanta ya fara shinshina wanda yake ta faman kamshi mai dadi ahankali yafara lasar wuyanta kamar wani sabon maye sai da yagama jigata ta sannan yahakura yakama hannunta ya matse cikin nashi ya lashi lebenta muje kirakani unguwa mudawo. ALHERI DANKO NE❗ 5⃣7⃣ Na UMMI A'ISHA Gabanta ne yafara faduwa karfa yaje yayi min aika aika yanzu batare da na shirya ba, tafada aranta,zaune yatashi yafara gyara wuyan rigarshi yaja hannunta tashi ki gyara mutafi tashi tayi tanada gyalenta amma kuma duk gaban rigarta abude yake yacire mata botiran gaban rigar, ganin yana kallon kirjinta yasata janyo gyalen tarufe jikinta murmushi yayi acikin zuciyarsa yace zakiyi bayani yarinya, gyara kujerar yayi tadawo yadda take ya zuge glass din setinsa yadagawa su sarkin fada hannu sai gasu aguje sunzo ranka yadade, kushigo mutafi, jikinsu narawa suka shiga motar sarkin mota yaja suka fara tafiya, hannunta tafida yariko tareda matsawa jikinta sosai ahaka suka je kofar fada anan yace sarkin mota yayi packing, yana tsayawa yace ku karasa gida nizanje unguwa firfita sukayi daga motar shi kuma yadubeta madam fito kidawo gaba kin san ni ba driver bane, baki ta buntsira tabude tafito batare data kalleshi ba saboda nauyin hada ido dashi take ga wata kunyarsa dataji ta saukar mata kai gaskiya al'amarin nan akwai kunyafa, fitowa shima yayi yazauna a mazaunin driver yakunna motar yayi ribos yajuya kan motar, suna hawa kan titi yajiyo ya kalleta tadauke kanta takalli titi hannunta yakama yarike yayinda yake driving da dayan hannun, kaga yadda kacire min botiran jikin rigata ko, murmushi yadanyi eh saboda bana son kisake saka rigar ne, yanzu kiga yadda ta takurani ta hanani taba......... [8:53PM, 11/21/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 5⃣8⃣ Na A'ISHA (ummi) Kanta tadauke bata tanka masa ba, kinga wannan rigar bata kamace ki ba madam nahadaki da Allah kar ki kara saka rigar nan kinji? Shiru tayi masa sanin bazata amsa masa ba yasashi matsa dan yatsanta dakarfi wash! Tafada hadeda runtse idonta gaskiya ka iya mugunta,murmushi yayi zakiga mugunta yanzu bakiga komai ba sai ranar da kikaji nauyi na, nanma shiru tayi amma aranta tana cewa dama ai nasan da mugunta zaka yi min wlhi, daidai wani shopping plaza yayi packing yasaki hannunta yace ina zuwa, fita yayi yashiga wani babban boutique ya lodo mata arabian gown kala kala da after dress bakake masu kyau da tsada da turarurruka domin shi yana son kamshi sosai tana nan zaune ya shigo motar da babbar leda ya ajiye abaya yatashi motar,fita suka yi daga shopping plaza yace zakisha ice cream? Girgiza kai tayi nagode, hmmm to tunda bazaki sha ice cream ba nasan abinda kike son sha kuma zan baki ita dai hanfa bakinta gum bata ce masa komai ba har suka shiga school of nursing, lokacin an fara kiraye kirayen sallar magrib. ALHERI DANKO NE❗ 5⃣9⃣ Na UMMI A'ISHA Daidai bakin gate din hostel dinsu yayi packing yajiyo ya kalleta yana murza dan yatsan hannunta, madam ga kaya nan su nayarda kisaka ako da yaushe mutukar ba uniform zaki saka ba, kallonsa tayi fuskarta dauke da alamar tambaya wanne irin kaya? Idan kinje zaki gansu, bana son nasake ganinki da irin wannan rigar da kika saka yau, sannan wannan dan motsitsin hijabin da kike sakawa amaimakon sa na siyo miki wanda yafishi girma kinji? Naji tafada ahankali, hannunsa yasa yadago fuskarta lumshe idanuwanta tayi bata kalleshi ba ahankali yakai bakinsa kan nata yahada yafara tsotsa, abin da yabashi mamaki yau batayi gardama ba amma idonta arufe yake gam ganin haka yasashi niyyar tsokanarta yafara zuba mata yawunshi nanma bata yi masa irin najiya ba haka yakaraci neman maganarshi yagama sai da yaji an shiga masallaci sannan yacikata yace dauki kayanki, sai da safe hannu tasa tadauki ledar tace nagode ta bude kofar motar tafita tsayawa yayi yana kallonta har tashige hostel sannan yatashi motarsa yafita daga cikin makarantar. [9:20PM, 11/21/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE❗ 6⃣0⃣ Na UMMI A'ISHA Fita yayi daga cikin makarantar yanufi gida yana tafe yana tunanin abar kaunarsa hanfa. Koda yaje gida ma yana cikeda tunaninta acikin ransa, washe gari mai martaba ya aikesu kano shida faisal inda zasu kaiwa sarkin kano katin gayyatar bikin zumunta wanda aka saba gudanarwa bayan kowacce shekara uku domin yaukaka dangon zumuncin dayake tsakanin sarki da talakawansa. Basu dawo ba sai karfe 6 lokacin agajiye suke lis washe garima suka sake tafiya jihar jigawa inda suka rinka shiga gari gari suna kaiwa katin gayyata domin dama wannan biki da za ayi bikine na al'ada da aka saba gudanarwa sannan kuma jama'a daban daban ne suke halarttarsa, aranar da suka dawo daga jigawa ma bai samu ganinta ba sai dai yana yiwa zarah sulaiman waya yaji lafiyarta,sai da yayi sati 1 bai ganta ba saboda kullum akwai inda zasuje aranar da suka dawo daga darazau ne yace komai dare sai yaje yaganta, wurin 5:30 ya isa makarantar dama shi kadai ne yau bai tafi da fadawan nasa ba, yana shiga a kofar hall din daya saba ganinta ya hangota zaune da wasu maza daga can gaba kuma zarah ce zaune ita da wata, tsaki yayi yafara kiran zarah awaya, daga inda take tadaga hello yallabai,zarah yakike, lfy lau, kituro min matata gani ina kallonku murmushi tayi angama ranka ya dade, tashi zarah tayi taje inda hanfa take tace kije tafida nakiranki, yana ina? Gashi can acikin mota, tashi hanfa tayi ta nufi inda motarsa take gaba tabude tashiga tazauna ta dan kalleshi yana sanye da farar shadda wadda tasha dinkin sarauta kansa babu hula, kallonta shima ya tsaya yi tana sanye da riga da skirt na atamfa da dan madaidaicin farin hijab, wai ke ban hanaki zama acikin maza ba? Shiru tayi ba amsa, wlh idan kikayi wasa bazaki gama karatun nan ba sai da ciki ajikinki tunda gashi nan kayan da nace kirinka sakawa ma bakya

Table of Contents

Chapters

36 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});