Chapter 4
Chapter 4
amma ko dauka bayayi, baice dashi komaiba, ya mike tsaye sannan yace "shikenan zanyi shawara akai tashi kaje kaci abinci, saina dawo zamuyi magana" bai jira me zai furtaba daddy yafice yabar dakin, sai a lokacin faisal yaji sanyina zuciyarsa, sannan ya mike tsaye.. soyayyar rumaisa itace a cikin kowanne bugun zuciyarsa a koda Yaushe. .. *_Waye faisal_* Faisal d'a daya tilo a gurin mahaifinsa Alhj nura(wato daddy)Yataso cikin gata da azriki, iyayensa suna matukar sonso domin shine kadai d'ansu daya tsaya a duniya, sun haifi wasu yaran kusan hudu amma duk sun rasu, faisal ne kad'ai yatsaya, Hakan yasa suka dauki son duniya suka daura masa, sun bashi tarbiya akan tsarin addinin musulunci.. Mahaifiyar faisal haj cima yar asalin mali ce, alhj nura kuwa dan 9ia ne, aikine yakaisa mali acen kuma yagano haj cima yanemo aureta kuma aka bashi, bayan andaura aurene yadawo da ita 9ja, Faisal farine amma ba iri farin nan sosaiba yanada tsayi daidai misali, yanada gwarjini sosai a gurin wadda baisaba dashiba, sannan kuma yanada fara 'a, Wata rana yaje karbar sako a gurin mahaifin rumaisa a lokacin yaganta kuma yaji yana sonta kuma yanaso takasance matarsa, bayan yakarbi sakon yadawo gidane yasanar da daddy cewa shifa yaga matar aure gidan amininsa, bakaramin jindadi daddy yayiba, domin ya kosa faisal yayi aure, Washe garin ranar tunda safe daddy yaje yasanar da mahaifin rumaisa cewa d'ansa yaga 'yarsa ynaso, abban rumaisa yajidadi sosai tun a gurin yace yabayar da ita ga Faisal kuma tana kare karatu za a daura musu aure, Daddy yayi godiya sannan yadawo gida yasanar da faisal cewa anbashi rumaisa, bakaramin jindadi faisal yayiba, yayiwa daddy godiya sosaii, A daren Ranar da faisal yafara zuwa gurin rumaisa babu abinda yaganewaa domin taki sake masa fuska, kuma taki yi masa magana, Shine daya dawo gida yasanar da iyayensa yadda sukayi da rumaisa, daddy ya tsorota sosai dominshi bayason dansa ya aure wacca bata sonsa, domin yasan illar auren dole Washe gari daddy yaje gidan abban rumaisa domin yaji gaskiyar lamari shin rumaisa nasaon yaronsa ko bata sonsa, Bayan yakarasa gidan a bakin kofar falon yajiyo hargowar abba yana yiwa rumaisa fada akan acewa dole saitaso faisal kuda kuwa ranta zaifitane, Hankalin daddy yatashi makura, baijira abba yazo yasamesaba yayi saurin dawowa gida yasanar da faisal komai dayaji tare da bashi shawarar cewa yadaina tunanin rumaisa a ransa domin shi bazai barshi ya aure wacca bata sonsa ba, Momyn faisal ma tabiyewa daddy akan itama bata yarda ya aure wacce bata sonsa ba.. _Wannan kenan_ **** **** *** Yajima a tsaye kafin yakarasa toilet yayi wanka sannan yafito ya kammala shirinsa yakarasa falo yagaida momynsa kafin yafara breakfast... **** ***** *** A harabar wani dankararen gida yaja parking ma'aiktan gidan sukawo kansa da gudu suka bude masa kofar motarsa, yafito cike da kasaita wani farin dattijone fuskarsa amurtuke, alamun tsufa sun bayya a fuskarsa makura, Farar shadda ce a jikin dakuma babban riga ga hula fara hakama takalmi farare, sai wata yar gajeruwar sanda dake rike a hannunsa, A hankali ya kalli ma aikatan yace "where is my son" daya daga ma'aikatan ya sunkuyar dakai domin sunsan halinsa ba a maganani dashi ana kallonsa "alhj wlh tun jiya daya shiga cikin dakinsa bai sake fitowaba kuma yahanawa kowa shiga cikin dakinsa, yanzu haka abincinsa na nan a kichin, sai kira yakeyi yace a akawo masa kayan maye" Farin dattijon yace "what!! Yakara kalon ma'aikatan ya rafka musu tsawa"kuna aikinme, meye amfaninku a gidan, dabazaku kirani kusanar daniba, wlh duk wani abu yasami d'ana saina kasheku baki daya, yana ina yanzu" Muryar ma'aikacin tasoma rawa domin ganin yadda ya tambayesa a hnakli yake cewa "yana ciki " Baijira yakara maganaba ya yanufi cikin gidann.... Facebook page:- Abdul-mr, smiles novel's Website:_www.abduljega.blogspot.com [10/20, 10:39 PM] +234 905 395 7618: _Title:-_ *MAJNOON*😴 _The mad man_ _Author_:- *MR, SMILES*😃 17 and 18 Via *OHW* _A love story_💝 Rumaisa ta kwanta saman gadon duk jikinta ciwo, fatarta harta kunbura , idonta sun fito bulla2, Tunanin ummanta kawai take, tasan da ace yau ummata nan da bazata bari ayi mata wannan dukanba, sai a lokacin tasamu tayi kuka, Sosai takeyin kuka, bata ankarabba bacci yadauketa, zuciyartaa cike da bakin cikin halin datake ciki, Abba kuwa daki yakoma yayi wanka yagyara jikinsa domi duk yayi gumi a kan dukan dayaiwa rumaisa, Sannan yafita police station yanufa yafadawa yan sanda cewa yanaso akama majnoon, sukam sukace bazasu kama mahaukaciba, haka yayita musu magiya amma sukace sufa bazasu iyaba, Dolensa ya hakura yabar station din amma zuciyarsa takasa hakura akan abinda majnoon yamasa, kawai yayanke shawara aransa zaisa 'yan daba su narkawa majnoon dukan tsiya cikin dare... haka kuwa ya ajiye a ransa.. Sai 4 na yamma rumaisa tafarka, jikinta duk yayi tsami da kyar ta iya tashi taje tayi wanka d ruwan dumi, koda zataji saukin ciwon dake damunta, bayan tagama wanka tayi alwala sannan tafito, tadan shafa mai,, sannan takarasa bikin drower tadauko hijab, komai datakeji ba kama jiki, a hakan tayi salloli biyu azahar da la'assar, bayan taggama taci abinci, sannan taka dawowa saman gado ta kwanta, A hakadai ta yuni bawani kuzari a jikinta. Misalin karfe 9 nadare rumaisa kwance a tsakiyar gadonta, sanye take da rigar bacci,tunani kawai take tana hawaye, dukta fita hayyacinta, a yuni daya dukta soma ramewa, Majnoon dinta take gani a duk lokacin data rufe idonta, hawaye fal a idonta, ummata ta tuna sai kuka, kuka tasomayi sosai cikin kukan take fadan "haba umma meyasa zaki tafi kibarni, meyasa nakasa binki, umma na nisan nan kusa zanzo gareki cikin yan kwanakinnan domin nagaji da duniyarna... ummana zan mutu...." takarasa maganr tana kuka abin tausayi Allah sarki rumaisa, tayi rashin mahaifiyarta tun tana tanada shekara 12, tun daga lokacin da mahifiyarta ta rasu bata kara samun farin cikiba sai lokacin da ta hadu da majnoon, to gashi shima ana kokarin rabasu, Haka dai taci kukanta mai isarta har dare yafara nisa sannan tayi adu'ar bacci tabi lafiyar gado, har bayan bacci yafada daukarta tatuna bata rufe kofar dakintaba, Taso ta tashi amma saita kasa, hakura kawai tayi tashiga sharar baccinta... Karfe 2:00am nadare mutun biyu cikin baka ken kaya suka dirko ta ginan gidan su rumaisa a hankali suka karasa cikin falon bakowa hakan yabasu damar shigewa dakin rumaisa kai tsaye, kwance suka sameta saman gado tana bacci, Dayan yakarasa inda take yafitar da wata porda ya zuba mata a hanci, kadan tayi kara saikuma takomaba bacci haka suka daukotaa suka fice da ita daga gidan babu wadda yasani, _Washe gari_ Misalin karfe 8:30 nasafe abba yayi shirinsa zai fita aiki, amma yaji shiru yayi dubin rumaisa tafito zuwa skull amma sai yaji shiru, tashi yayi yanufi dakinta, yaduba bata ciki, sunanta yashiga kira a tunaninsa kotana cikin toilet hakan ma yaji shiru, tiolet din yanufa ya bude yaduba bata ciki fitowa waje yayi zuciyarsa cike da sake2 kala2, yadaisan rumaisa bazata guduba, yafi zargi saceta akayi, da karfi ya kalawa umma kira, dasauri ta kara gurinsa "gani alhj lafiya kuwa " Ina rumaisa " itace kalamar daya fara fada fuskarsa a murtuke Umma ta kallesa da mamaki tace " ni ina zansan inda rumaisa take rabona da ita tun jiya dadare " Cikin fushi abba
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37