Chapter 8
Chapter 8
biyu da kwanauku wato ranar laraba da sassafe sai ga wata mota an kawo hannemakarantahaisam ya roki wani abokinsa safiyanu yaje cangidan uwarbiyu ya dauko hanne da kayanta ya kawotamakaranta. Haisam ya gama mata siyayyarta kakaf ko yaranattajiranmakarantar baza su fita kaya ba(provision)kayanmakarantarta (uniform)suma har kala kala bibiyuyayi matatakalma kuwa kala kala akwai kito, sandal , kambos fari dabaki tsadaddu, silifas dan madina har biyu, ya suyomata dawasu yan kanti riga da siket suma kala biyu. Yasuyo matajakar zuba kaya mai kyan gaske yar madaidaiciya wato (travelling bag)a ciki aka zubawa hanne kayansawarta, nata nada kuwa yana gidan uwar biyu, kayan tande tandedamakulashe kuwa abun baya lissafuwa kama daga biskit kalakala, alewa (chocolate)indomie, madara, milo,sugar ,complakes da dai sauransu ko gari babuballe wanikanzo irin na yan makaranta makilin da brushhadaddu, mayukan shafawa da sabulansu masu kamshi gamayukangashi cike a akwatin hanne hankar da kaya allahya taimaketasa kansilansu ya tashi kawo maya akwatin yakawo mata randimemiya, mai cin kaya da yawa.Hanne sanye take da kayan makaranta(uniform)kafar ta kumafarin kambos ne da farar safa an tufke kitson kantada waniribom mai kyau mai fulawa, duk wanda yaga hanne kwanakibiyu da suka wuce a yau dai bazai gane taba tayifari kyalkamar yar larabawa, ashe mai dangwali ya ba neda bakinkwalli suka cabe mata fuska tayi baki kirin. Safiyanu yazobakin offishin malamai ya tsaya da motarsa sannanya fitodaga ciki ya juya ya kalli hanne wacce ke zaune abaya tanakokawa da murfin kofa ta kasa budewa abunka fa bakauyiiya.Wannan ne karo na farko da hanne ta taba hawadon hakabata san ina zata ja kofa ta bude ba. Safiyanu yazagayo dasauri ya bude mata, ta fito yace'' to dauko jakar litattafan nakimana'' hanne tasa hannu ta jawo wata bakar jaka(schoolbag)tsadadda mai kyan gaske, yar madaidaiciyadaidaibayanta cike take da kitattafan rubutu da litattafan karatu(textbook)duk dai kamar yadda aka zano ajikintakardar babuwanda haisam bai siya mata ba ga biruka da fensirdamathematical set din su ya suya mata . Safiyanu ya nunawahanne yadda zaya rinka ratayawa a bayanta tarataya sukanufi cikin ofishin. Suna shiga suka iske wani malamibayansafiyanu ya mika masa hannu sun gaisa sai yayi masa bayaninabunda ke tafe dasu yace daliba ya kawo, sai yanuna masaofishin vice principal yace nan zasu shiga.sukayi sallama suka shiga suka iske viceprincipal yanaharhada wasu takardu a gabansa, bayan syn gaisasafiyanu yashaida masa cewa yarinya ya kawo yar aji daya cesabuwar zuwa sai ya nemi daya bashi takardar shaidar cewaita dalibarnan makarantar ce wato (joining instruction)daman haisam yabashi ya dauko ya mika masa ya duba yace''sunanta hanne habu imamu daga babban mutum ko ? Safiyanuyace ''eh,''vice principal din nan ya kurawa hanne ido yanakallozuciyarsa cike da mamaki ga yarinya kyakykyawakamar baturiya gashin kanta har baya amma duk dama antufkemata da ribon amma kuma sunnan kauyawagareta gata kumadaa kauye. Ya ce a ransa'' wata kila dai asalin garinsune babban mutum din amma daga birni take, can yanisa yace''babu komai,'' ya jawo wani littafin rasitai ya budeyace dasafiyanu'' sai ku bibbiya kudaden in baku rasitai dasauri don yanxu lokaacin assembly ne, don taje ta shiga cikindalibai ayida ita. Vice principal ya lissafawa safiyanu yawankudade dazai kawo safiyanu ya dauko ya bashi, shi kumayana rubuta rasitai har ya biya kudin komai ya ce '' sannan yafadi sunandakin da zata je, sannan zata je j.s.s. 1A ajin malamhaisamsunan ajin, yanzu ka kaita hall ayi assembly da ita,kayanta kuma a barsu a nan bakin staff room ana tashi tazozamu samaigadi da prefect din dakin suje ta bata gado.Safiyanu ya ce''to'' yayi godiya suka fito yana sake yiwa hannebayani akan abinda vice principal ya ce, yana kuma karalallashinta ganinyadda nan da nan ta canja hankalinta yayimummunan tashidaga shigar su ofishin vice principal duk kwalla tacika mata ido saura kiris ta fashe da kuka. Yace mata'' kar kiyikuka nanmakaranta ce karatu kawai za.a koya miki babumai zaginkiballe duka kinji. Gashi ajin malam haisam za,a kai kidon haka baki da matsala zai kula dake''suna tsaye a bakin baranda yana yi mata nasihasaiga viceprincipal ya fito daga ofishinsa zai tafi hall wajenassemblyyace'' ah har yanzu bata tafi assembly ba ai gara kuyi sallamata tafi,'' safiyanu yace '' aima shikenan mun gamadaman halldin zan tambaya don bamu ganshi ba,'' viceprincipal t harcikin hall din yashige da hanne a lokacin principal tana bayanihall din yayi tsit kowa yana sauraro. Amma dagashigowarhanne da vice principal sai kowa hankalinsa yakoma ga kallonhanne. Hanne ta zama yarinya ''yar dagwas 'yar karama maikyan gaske akwai dubbunan dalibai a makarantardaga jahohidaban daban amma babu mai kyawun hanne watokamarwata tauraruwa ce mai haske a cikin taurari. Sai sheki take danfarar fatarta hanci har baka, dan karamin baki,gazar gazargashin gira dana ido fatar jikinta luwai luwai irintayan hutuamma ita dai daga innallahi. Ga ido dara dara bata da kibakuma bata cika tsaho sosai ba gata dirarriya duk dadaikarama ce masassakin budurci bai fara sassakataba. Wasukitso ne yiri yiri aka yarfa mata kamar bada hannu aka yisuba. Hanne tayi kyau kwarai da gaske a cikinkayanmakarantar nan ga 'yar jakar litattafanta a baya.Babu wandazai kalli hanne bai sake juyowa ya kalli halittar ubangiji ba.Dalibai manyansu da yaransu babu wacce bata cedama nicewannan ba ko kuma ace 'yata ce a ransu ba. Hattahaisamwanda ke tsaye a bakin kofa bai gane hanne ba. Suka zo sukawuce ta gabansa ya bita da kallo sai dai a zuciyarsayaketambayar kansa da kansa ina nasan wannanyarinyar?Tabbasa na santa a wani waje, sai daga baya zuciya ta bashiamsar cewa wannan itace hanne habu kenan. Yayimatukarmamaki ganin yadda hanne ta koma haka a kwanabiyu,hanne ta tsorata ta kuma rikirkice ganin dubbunnan idanuwacaa a kanta, ta tsaya cak, ta kasa tafiya tana shirinfashewa dakuka.Vice principal yayi kiran wata prefect dake tsaye agefe yace tazo ta kaita layin 'yan j,s,s 1A. Tazo ta kamahannun hanne takaita layin ajinsu ana ci gaba da assembly kamaryadda sukasaba. Bayan principal ta gama jawabinta, viceprincipal ma ya fadi albarkacin bakinsa sai aka nemi sauranmalamai sucewani abu akan dokar makaranta. Bayan sun gamaaka yinatsonal pledge kowa ya kama gabansa, ya nufiajinsu. Hanne ta tsaya cak a inda take tsaye tana kallon dalibaikowa yanatafiya ajinsa ta rasa ina zata nufa. Haisam ya matsokusa da itaya ce'' hanne yaya kika tsaya bakya gani kowa yanufi ajinsu ke kika tsaya idan baki sani ba, ba sai ki tambaya ba.To nanmakaranta ce kowa ta kansa yake, gara ki rinkatambayar dukabinda baki sani ba, muje in nuna miki ajinnaku, hanne tace'' to'' ta bishi suka doshi bangaren da ajujuwa sukeyaci gaba dayi mata nasihohi akan kada ta sake ta zamawawuya, idan bahaka ba sai sauran dalibai su raina mata wayo tazama duk abunda bata sani ba ta tambaya musamman idanmalamiyana darasi idan bata ganeba tayi masa tambaya.Hanne nasauraro da alama kuma nasihohin suna shigarta.Haisam ya kalleta yayi dariya ya ce'' hanne ince kin zamacikakkiyardaliba babu wannan damarar? Hanne ta kyalkyaleda dariyahaisam yace'' to tunda kin zama yar birni 'yar bokomai aji to yanzu komai naki yzai koma na aji, kin san abundanake nufi?Hanne tace ''a'a'' yace to sunanki zai tashi dagaHANNE HABUIMAMU ZAI KOMA HANNAH ABUBAKAR IMAM.kowaya tambayeki sunanki kice..'' kafin ya fada cikin murnada farinciki tace '' hannah abubakar imam'' haisam yatuntsire dadariya yace harma kin rike sunan kenan? Hannetace eh hannah yafi dadi Allah'' a daidai wannan lokacisuka haubarandar ajin haisam ya wuce gaba ya shiga ajinhannah nabiye dashi a bayasuka
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31