Chapter 18
Chapter 18
yasake haskawa, gashin kanta ya kara tsawo sabidatayi wayon gyarashi ga mayukan gashi kala kalada haisam yake siya mata. Ranar wata social night da daddare ne haisam ya hango hanna, nusaiba darauda sun sha wandunan jeans da teasirt sun nufikatafaran kantin siyar da kayayyaki kala kala dakecikin makarantar. Suna tsaye suna siyayya saidariya suke suna tafi, cikin sanda ya karasa kantindon yaga me suke siya haka suna dariya. Wai ashe rigar nono zasu fara sawa 'yan kanana. To shine yakawo musu guda dai dai suke jin kunyar siyakyma. Hannah tace'' ni dai ba don kunce a siyobireziyar na dani ba da bazan siya ba, yanzu fa dolebazan dinga sakewa ba zan dinga gani kamar anaganin shatinsa ko hannuna yana fitowa ta riga kowa yana gani'' rauda tace'' caf aini da ganganzan dinga sakin hannun rigata don ta fito'' nusaibabata ce komai ba ashe ta hango uncle haisam abayansu a tsaye tana ta kifta musu ido basu ganiba. hannah tace'' ko da yake mun zama senior har 'yanj.s.s 1 ma naga wasu suna sawa fa, nusaiba zabi.Hannah na daddagawa, nusaiba tayi gyaran muryataga dai basu san uncle haisam na bayansu ba. Saitace '' ba ruwana ga yaa haisam nan yana kinku''.Haisam ya kyalkyale da dariya. Sai su duka suka juyo nan fa hannah ta wurgar data hannunta taruga a guje, nusaiba da rauda kuwa suka cusa tasua riga suma suka arce. Haisam yazo ya dauki waccehannah ta wurgar shi da mai kanti suka dingadariya. Haisam yace su hannah yan mata Haisam ya dada kyau sosai hankalinsa ya kwantaya zama mai kudi baya ga albashinsa accountmahaifinsa ya bude masa yana zuba masa ribar dasuka ci a kamfaninsu duk wata yake warewa'ya'yansa, ga hannah ba laifi ta girma wahalar datake sha a gida ta ragu abubuwa da yawa ta fara takawa iya abu da 'ya'yanta burki tana kwatarkanta dole wasu abubuwan suke raga mata. Donhaka kallo daya zaka yiwa haisam kasan dan gidanwani gawurtaccen mai kudi ne saboda suffarsa ta'ya'yan hutu ce, fari ne sol fatarsa mai haske, yanada dara daran ido da dogon hanci, mai yawan gashin?idon dana gira gazar gazar . Wani dan siriringemu ne ya zagaye dan madaidaicin bakinsa(kautar million)gashi dogo mai dan madaidaiciyarkiba. Haisam yana daya daga cikin irin da kowacce'ya mace take mafarkin samun irinshi. Gashi amakarantar yan mata masu ji da kudi da kyau ga gayu. Don haka kusan kullum haisam sai ya samiwasikun 'yan mata akan teburinsa a ofis dinsa sunjefa masa. Wai suna sonsa soyayya mai tsananikuwa sai kawai yayi dariya ya yaga ya zubr kodakuma ya hadu dasu bazai nuna musu yagasakonsu ba. Yan aji shida ne suka fi yi masa wasikun amma wasu 'yan aji biyar din suna rubutomasa shi gani yake suk suna duk hauka suke zasugaji su daina. Gasu kyawawa dasu amma bayaganin kyawun, 'ya'yan attajirai amma shi baidameshiba, shi dai kawai yazo ya cika burin da yakudira ya tafi. senior juwairiyya itace shugaban dalibai (headgirl) juwairiyya kyakykyawan gaske ce fara solharma akan ce suna kama da hannah. Gatamahaifinta wani babban manager ne a wani bankia lagos tana ji da gata da dukiya ga tsananin kokaritafi kowa kokari a shekararsu. Amma sai allah ya jarrabeta da tsananin son uncle haisam tun ba yauba gashi da yawa daga cikin malaman sun mato a sontaita bata son su ta fi son haisam. Ta aika masa dawasiku sunfi a kirga amma shiru ko alama haisambaya nuna mata na yaga wasikarta . Da ta gaji daaika masa da wasikun saita dinga aika masakawayenta baro baro suke tarar sa su gaya masa amsar daya basu cewa yayi duk yarinyar data saketarar sa da maganan juwairiyya saiya sabar mata.Don haka juwairiyya ta rasa yadda zata yi ta shawokan wanda take so . Ranar litinin da daddare an fitodaga (prep) juwairiyya ta sami kan wata baranda tazauna tana tunani don ita son haisam har ya fara dasa mata wani ciwo da yake damunta a zuciya hartake kasa karatu sosai gashi kuwa tafi duk yanmakarantar kokari, don haka nema aka nada tashugabar dalibai. Zaman da tayi wucewar haisamkawai take son ta gani sannan ta iya bacci. Salahanura itace babbar aminiyar juwairiyya tazi giftawa zata tafi ajinsu taga kawarta a zaune a baranda itakadai, taje wajen ta dade a tsaye a kanta juwairiyyabata sani ba. Ta dafata sannan tayi firgigi ta dago .Salaha nura ta zauna a kusa da juwairiyya tace''juwairiyya tunanin meye kike, ke kadai kowa yanaaji ? Juwairiyya ta nisa tace allah salaha inasan uncle maikayu sosai har kamar zan zautu'' salaha tatuntsire da dariya tace'' uncle haisam wai? Shegusunan da kuka saka masa kuma, to juwairiyya yayazamuyi kin rubuta a rubuce yaki kin aikemu yazazzagemu ko ke kika je da kanki ba zai yadda ba.Kwarjini yake mun ba zan iya tarar saba'' inji juwairiyya salaha tace'' to meye abun yi? Juwairiyyata zunguri salaha ta nuna mata haisam ne yatunkaro inda suke daga staff qurters ya karasoinda suke su duka suka gaisheshi cikin ladabi. Yace ''oh shugabar dalibaice da labour prefect ? Sukace mune si'' yace ''wato kun kora yara aji ku kunzo kun zauna kuna hira ko? Kamata yayi kufi kowakaratu yanzu tunda kune masu shirin yin waec daneco da jamb ko? suka amsa eh ba hira muke bawani muke jira'' juwairiyya ta marairaice muryatace'' amma na ganshi yanzu zamu tafi damanfatana in ganshi kawai ''haisam ya gane abunda take nufi sai kawai yayi sauri ya katseta ya ce'' idanzaku tafi gashi kuje j.s.s. 1a science class ku bawahannah abubakar imam. Ya mika mata wata leda adaure ya juya ya nufi ofishinsa ya shiga sannan yarufo kofar. Juwairiyya tace da salaha''kinga abunda nakegudu ko shariya ce da wannan mutumin ko fuskabaya bani da zan gaya masa abunda yake damuna.Salaha nura tace'' to wai ni na lura meye yaketsakanin uncle haisam da hannah abubakar imamne ? Kamar duk makarantar nan yafi kulata komai hannah zaka ji yana ambata kamar shi ya radamata sunan. Juwairiyya tace'' ance abokin wantane wai, kuma saboda rauda shitu kawar hannah itaai kanwarsa ce. Salaha nura tace'' to kanwarabokinsa ai zai iya sonta. Salaha ta karbi ledar da yabawa juwairiyya ta kwance sai suka ga magunguna na ruwa da kwaya ne , na zazzabidana tari ya saya mata. Salaha ta tabe baki tace.Lallai magunguna ya sayo mata tafi karfin ma tashana clinic din makaranta kenan'' juwairiyya tace'' zomuje nasan abunda zan hadawa yarinyar na''salaha ta taso suna tafe suna zancen suka nufi ajin su hannah. Juwairiyya tace'' ba uncle haisam yacekada wata ta kuskura ta kara kai masa sakona bato ni kuma hannar da yake ji da ita daga yau ita zandinga aike wajensa. Salaha tace'' kwarai kuwahaka za'a yi muga ko itama zai korota din'' tawundo juwairiyya ta leka tace'' ina hannah abubakar ? Yan ajin suka ce'' gata can a sit dinta akwance bata da lafiya'' tace ''ko ciwon ajalo take tataso ta zagayo tazo ina kiranta'' nusaiba ce tatasheta tace '' hannah kije senior juwairiyya nakiranki'' hannah ta daga ido dakyar tace'' bazan iyatashi ba bani da lafiya'' jikinta zafi kyau kamar wuta. Jijiyoyinta kanta sunyi rudu rudu don ciwonda yake yi mata. Juwairiyya ta daka mata tsawatace da hannah ta taso allah yasa asibiti ne a kantaba jinya ba. Nusaiba da rauda suka rirrikota sukatasheta tsaye. Juwairiyya ta daka musu
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31