Chapter 22
Chapter 22
ce , da ga haka ya ci gaba da tafiyar shi har ya iso part din MALIKAT HOUDA bakin shi da sallama ya shigo parlourn MALIKAT HOUDA , nan ya tardo ta zaune tare da MALIKAT AL'UMU da mama da Nesrine , MALIKAT AL'UMU na rike da Nailah , MALIKAT HOUDA kuma ta na rike da Junior ( 🤣🤣🤣✌ gaskiya sai dai mu kira shi da Junior dan ni mutum guda na bawa wannan sunnan wato MALIK NAWFEL HICHAM BIN JAABAR , MY NUMBER ONE 🤣✌ ) MALIKAT INAS kuma ta na rike da Nayel bai ce musu komai ba ya nufi corridor ya shige , kai tsaye bedroom din da Inaya ke ciki ya nufa dan dama ita ya zo nema ya na shiga ya gan ta konce tsakiyar gado , ta dunkule waje guda , idanunta na bude da sauri ya nufi gadon dan a nashi tunanin wani abu ya same ta , ya na isa ya zauna a baki ya na fadin " my Cutie , me ya faru ? ciwo ki ke ? " a hankali ta dawo da kallon ta gare shi , ta saki wani dan karamin murmushi ta ce " yanzu fa na tashi da ga barci , ko one minute ba a yi ba da na bude ido " a hankali ya sauke ajiyar zuciya kafin ya ce " to me ya faru ? ko wani abu ki ke so ? fada min zan je na kawo miki " girgiza mishi kai ta yi ta na fadin " yaya Zayd ba na bukatar komai a yanzu , kawai ina son na huta , jikina duk a mace ya ke " a hankali ya sunkuyar da kai ya manna mata kiss saman forehead ya na fadin " okay my Cutie , konta ki huta , dama na zo na fada miki ran Friday za mu tafi Makkah , da ga nan mu koma gidanmu na US " wani dan karamin murmushi ta saki murya a sanyaye ta ce " da gaske yaya Zayd , za mu tafi Makkah ? " gyada mata kai ya yi a hankali ya na cewa " har Madina sai mun biya , da ga nan mu tafi Dubaï mu yi shopping sannan mu komawar US " har ta saki wani dan murmushi sai ta marairaice fuska ta na fadin " baby , please tell me , baby nawa na haifa ? don Allah ka fada min , wlh hankalina duk ya ki konciya , da na lumshe idanu sai na dinga jiyo Muryar shi " wata yar karamar ajiyar zuciya ya sauke , a sanyaye ya ce mata " Cutie , me ki ke so na ce miki yanzu ? " a hankali ta mike zaune , ta jingina bayanta a jikin forehead din gadon , ta riko hannunshi ta na fadin " ka fada min gaskiya mana , zan fi jin dadin ka fada min gaskiya ko me zai faru hakan zai sa na ji sanyi a zuciya ta , ko dai babyn bai zo da rai ba ? " ta fada ta na dan marairaice fuska sai da ya dauki lokaci kafin ya ce mata " i'm sorry my Cutie , na yi tunanin in na boye miki hakan ba za ki ji zafin rashin ba , amma gaskiya ne Triplets mu ka samu , sai dai namijin na biyu bai zo da rai ba , I'm sorry " wata nanauyar ajiyar zuciya ta sauke kafin ta lumshe idanunta , ta fara zubar da hawaye da sauri ya fara goge hawayen ya na fadin " kin gani ko , shi ya sa na ki fada miki , ga shi yanzu ki na kuka " a hankali ta girgiza mishi kai ta na fadin " ba komai baby , Allah zai ba mu wani , ko ba komai yanzu zan daina wannan tunanin , amma please ina son na ga Nayab , ina so na ga in ya na kama da Nayel din mu " ta kai karshen ta na ware idanunta a sanyaye girgiza mata kai ya yi a hankali kafin ya ce " i'm sorry my Cutie , amma tun ranar a ka yi jana'izar shi , bayan ni da doctor da nurse biyu sai mama ba wanda ya san wannan maganar , ko je dan kin matsa ne na fada miki , ki yi hakuri don Allah " a hankali ta sakin mishi kuka ta na fadin " yanzu ka hana ni ganin babyna , why za ka yi haka , da ka bar ni na gan shi mana " " i'm sorry my Cutie , wlh ban yi hakan dan na cutar da ke , please ki daina kukan nan wlh b....... " bai kai karshen maganar shi ba kawai ya ga ta koma Aswad lokaci guda ta na daga mishi da karfi ta ce " ka daina ce min na yi shiru , babyna ne ba nata ba , why za ka ce a yi jana'izar shi ba tare da na gan shi ba " ta fada har wani sama gashin ta ya yi kamar a na hura shi da iska ba karamar razana Malik ya yi ba , har sai da ya mike tsaye ya na karanto kalmar shahada wasu yawu ma su daci ya hadiye kafin ya ce " please my Cutie, calm down , please , i'm sorry " ya na gama fadar haka kawai ya ga ta saki kuka , wasu bakaken hawaye na zubo mata , ta na fadin " ka kawo min babyna na gan shi , ka kawo min shi na gani " ta fada a sanyaye kafin ta lumshe idanunta a hankali , nan take jelar gashinta ta zubo saman shoulder din ta wata nanauyar ajiyar zuciya ta sauke kafin ta ware idanunta a hankali shi ma nanauyar ajiyar zuciya ya sauke ganin idanunta sun dawo dai'dai a hankali ya zube saman guyiwowinshi ya riko kunnuwan shi , ya na fadin " i'm so sorry my Cutie , just na yi tunanin in na boye miki hakan ba za ki ji zafin mutuwar Nayab ba , ban yi tunanin hakan zai cutar da ke ba , i'm sorry , please forgive me , please " ( in na gane wani abu 🤔🤔🤔 Nayel shi ya dauko Abyad , Nayab kuma ya dauko Aswad , yanzu da babu Nayab Aswad za ta koma jikin Nailah1 ko kuwa ? ) wani dan karamin murmushi ta sakin mishi kafin ta mika mishi hannu a hankali ya mike tsaye ya riko hannunta , ya zauna bakin gadon " babu komai , na gode baby , na san duk abun da ka yi ka yi shi because you love me , kuma ba ka son abun da zai cutar da ni , ko ba komai na so na ga Nayab , amma tunda kai ka gan shi , ni ma kamar na gan shi ne , so it's okay now " ta kai karshen ta na sakin mishi wani dan karamin murmushi murmushi shi ma ya sakin mata kafin ya kai hannu ya fara goge mata bakaken hawayen Aswad ya na fadin " kin sani , ya na kama
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31