Chapter 18
Chapter 18
: MEERAH βπ γTHE ROYALTY LOVE β€πΉγ γ BOOK ________ 4 πβπ γ _______________________β‘β‘β‘β‘β‘β‘β‘β‘β‘β‘β‘β‘______________________ ο½ P A G E ________ 15 & 16 βππ₯ο½ dan jinkirtawa Diya ya yi kafin ya ce " tsinuwar macijiya ce a kan ahalin Abdoul Mujeeb , lokacin da mahaifin mu ya hau mulkin masarautar Ottoman ya yi kokarin kara fadada girman masarautar , akwai wani fili da ga bayan masarautar , kawai sai ya ce a sanyo shi cikin Daular , a yi sabin gineΒ² a cen , ashe wajen snake's nest ne , lokacin da ya samu labarin wajen gidan macizai ne kawai sai ya tura a kashe duk macizan , haka ko a ka yi , amma abun da ba su sani ba , sarauniyar macizan mayya ce , kafin ta mutu sai da ta tsinewa Ahalin Abdoul Mujeeb , duk yaran da zai haifa za su zo rabi maciji , rabi mutum , kuma haka a ka yi , ba Aymane kadai ba , duk yaran Abdoul Mujeeb mu na iya komawa wannan macijin da ka gani na koma yanzu , amma na Rouksar daban ne , dan duk lokacin da idanunta su ka koma na maciji a ka yi katari wani ya kalli cikin su , to sai ya koma status har sai ta yi mishi kiss sannan ya dawo dai'dai , shi ya sa ma mu ke kiran ta da Medusa , ina da shekara 17 na fara komawa wannan macijin , abun ya yi matukar ban tsoro , da na fadawa Daddy shi ne ya ke ban labarin yadda a ka yi na zama macijin , da na ji hakan kawai na ji na tsani masarautar , shi ya sa ma na daina zama cikin Saudiya baki daya , na koma UK da zama , idan na gaji na tafi DubaΓ― ko Jordan ko Asia , tsakanin wadanan gariruwan hudu na kammala karatu na , shi kuma Aymane nashi macijin daban ya ke shi ma , saboda shan jinin mutum ya ke , mutanan ma sai mata , ba yin da Daddy bai yi ba dan ganin Aymane ya daina shan jini amma ya kassa , har ya kai ya gogawa Rouksar shan jini , ba tare da sanin shi ba , ga shi kuma ya koyo yin tsafi , da ya ga abun ya fara gagara shi ne ya tura shi kassar Rouma wajen wani babban masanin tsafi dan ya cire wannan macijin da ke jikin Aymane , amma ya kassa asali ma tsafin shi sai karuwa ya yi , babu yadda ya iya ya sa mishi ido har ya girma a haka , ba zan maka karya ba , lokacin da Aymane ya yi kokarin kashe ka shekara bakwai baya , ina sane , saboda na zo wucewa na ji ya na maganar , dalilin da ya sa ma na shigo masarautar Saudiya a ranar dan na cece ka , amma ina shigar ta kai ne mutum na farko da na ci karo da shi , ba karamin sanyi na ji ba ganin ka a raye , shi ya sa ma na hakura na bi ka Nigeria , saboda ina tsoron Aymane ya cutar da kai idan ya samu labarin ka na raye , na san ka manta amma ni na sani , duk lokacin da ka je kai wa papi Ziyara a Daular Ottoman kai da Tesnim , sai Aymane ya yi kokarin kashe ka , amma bai taba yin nassara ba , akasin da a ka samu , duk lokacin da ka ke zuwa Daular ni ba na nan , shi ya sa ba ka san ko ni wanene ba ranar da mu ka hadu , tun lokacin da na sauke idanu saman Baby na san ta na da aljanu , na san kuma Malik ya shiga jikinta ya ce maka dole sai ka fara karaya tsafin Aymane sannan za ka iya kashe shi , ko kuma ka cire mishi kai , ni na san inda Aymane ya boye sihirin shi , amma ba zan iya fada maka ba , saboda a jikin RIANNA ya boye shi a ranar da a ka yi auren su , hakan na nufin sai ka kashe RIANNA , shi ya sa na ja bakina na yi shiru , bare kuma ba ni da tabbacin za ka yarda da ni , mistake daya a ka samu Aymane ya koma maciji a gaban ka , da ni ma ba zan fada maka ba saboda ya na daya da ga cikin abun da ba na son tunawa a cikin rayuwa , dalilin da ya sa ma na yi bincike a kan yadda zan cire macijin da ke jikina , kuma Alhamdoulilah ya na fita a hankali ta hanyar karatun kur'ani da sallar dare dan macijin ba ya son adini , da farko girman shi ya kai irin na Aymane , ka yi hakuri na boye maka wannan abun tsawon shekaru but i don't know how to explain you , i'm just afraid idan na fada maka ka ji ka tsane ni ba zan iya jure hakan ba , I'm so sorry " ya fadi na karshen kamar zai yi kuka sai da ya dan jinkirta kafin ya ci gaba da fadin " lokacin da a ce ka sha poison , lokaci guda na san da Rouksar ce , dan ita kadai ke da poison , ba rokon da ban yi mata ba a kan ta ba ni antidote , ka yi hakuri har alkawari na yi mata idan ka tashi za ka aure ta , amma fir ta ki , ta na cewa idan ta ba ni kashe ta zai yi , na tambaye ta wa amma ta kassa fada min saboda ya rufe bakin ta da tsafin shi , sa'ar mu guda aljanun Baby sun tashi , ba dan haka sai dai ka mutu dan antidote din poison din ta , yawunta ne that's why ma ka ga mahaifinmu bai wani damu da mutuwarta ba saboda ya san wacece ita , haka ma Aymane ya yi kokarin ya ja mishi birki lokacin da ya hau kujerar amma ya yi kokarin kashe shi , shi ya sa ya ja bakinshi ya yi shiru dan ba abun da zai iya yi , ka yi hakuri ahalina ya cutar da kai dayawa , please ka samu wani gurbin a zuciyar ka ka yahe min , na san ko na mutu ruhi na ba zai samu salama ba idan ban fada maka gaskiya ba " wata nanauyar ajiyar zuciya Malik ya sauke kafin ya mike tsaye , ya na kallon Diya da ya tsare shi da ido ya na hawaye a hankali ya tako gaban shi ya tsaya , sannan ya mika mishi hannu wani cool murmushi Diya ya saki kafin ya dago hannun shi a hankali ya daura saman na Malik kafin ya mike tsaye ya na mikewa tsaye Malik ya kai hannu ya goge mishi hawayen shi ya na fadin " ni wlh na zata wata babbar magana ce za ka min , kawai dan ka yi zaune ka min kuka ne , ko dadi ya yi maka yawa ne ? " " ta ya za ka min irin wannan maganar bayan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31