Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 17

Chapter 17

Exiled Princess Book 4 Complete Hausa Novel 1,066 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

da Allah Nawfel komawa za ka yi , tun da komai ya wuce ka zauna cikin familyn ka mana " a hankali ya tako wajen sofar ya zauna geffen ta murya a sanyaye ya ce " momy , ba zan yi miki karya ba , these months that I spent there were the best of my entire life, I felt free, without any pressure, just her and me , na ji dadin zamana a cen fiye da komai , please kar ki ce za ki tsayar da ni , i promise duk bayan sallar Azumi za mu dinga dawowa mu yi babbar sallat a nan , just let me go please " shiru MALIKAT AL'UMU ta yi ta rasa abun da za ta ce mishi , ita ta na farin cikin komai zai dawo dai'dai , amma ya ce zai koma , zai sake barin su a hankali ta sauke ajiyar zuciya kafin ta ce " kujerar Malik kuma fa ? wa zai hau ta yanzu ? " " Diya " ya fada a takaice " ka sani Diya ba zai iya hawa kujerar nan ba , in da ma a ce Abdoul ne da zai iya hawa " " na sani momy , amma shi za a nada , dan na san Bayan shi babu wanda zai iya rike min ahalina , na san zai kula da masarautar nan kamar yadda ni zan kula da ita , na yarda da Diya fiye da rayuwata , ba dan shi ba da yanzu ban san inda zan tsinci kai na ba , ba dan shi ba da ba zan taba haduwa uncle bare har ya ba ni auren Cutie , duk wani abun al'heri da ya same ni cikin rayuwata shi ne sila , shi ya sa na yarda da shi fiye da rayuwata , he is my best and ONLY friend's , He is my Brother not my Cousin , dan haka ya na da ikon hawa kujerar Malik " wani dan karamin murmushi MALIKAT AL'UMU ta saki kafin ta ce " ka tabbatar shi ne abun da ka ke so ? " " na tabbatar momy " ya fada kai tsaye " shikenan , amma kar ka fadawa kowa maganar nan , har ranar nadin " " okay momy " ya fada ya na mikewa tsaye da sauri MALIKAT AL'UMU ta ce mishi " ina kuma za ka tafi ? " " ina son na ga babyna kafin mu tafi mosque lokacin sallat ya yi " da to kawai ta amsa , da ga haka ya sa kafa ya fice part din har ya nufi hanyar word room a ka fara kiran sallat , kawai sai ya juya ya nufi mosque dan ya yi sallat bayan sun yi sallat , Diya ya ja hannunshi ya nufi part din shi da shi , sai tambayar shi Malik ya ke me ya faru , ya sake shi amma ko sauraron shi Diya ba ya yi , su ka shiga part din shi sai da su ka shiga cikin dayar bedroom sannan ya saki hannunshi , ya meda kofar ya rufe , ya saka mata security Malik na ganin haka ya ce mishi " wai lafiya ka kawo ni nan , ina son na je na ga babys di na , ka wani kawo ni nan har da rufe kofa " cikin sanyin murya Diya ya ce mishi " please , ka tsaya akwai wata magana da na ke son mu yi " wani dan karamin tsaki Malik ya yi ya na fadin " magana ba za ka iya yi min ita ba a mosque sai ka kawo ni har nan ? , wlh ba ka da hankali , ban hanya na wuce " ya fada ya na nufar kofar dakin da sauri Diya ya riko hannunshi ya janyo shi bayan da karfi ya na fadin " please Nawfel , ka tsaya wlh maganar mai mahimanci ce , don girman Allah ka tsaya " ya fada ya na marairaice fuska wani dan karamin tsaki Malik ya yi ya na fadin " okay , ina jin ka , amma yi sauri " wani dan karamin murmushi Diya ya yi kafin ya gyada mishi kai a hankali ya lumshe idanunshi a fara motsa lips din shi kamar ya na karanto wani abu a hankali skin din shi ta fara sauya launi , ta koma wani launi shi ba green ba shi ba yellow ba , scales su ka fara fito mishi , nan take skin din shi ta koma irin ta maciji , a dubu dari Diya ya bude idanun shi dai'dai lokacin da ya koma wani babban maciji , amma yanayin jikin shi da tsawon shi duk dai'dai yanayin jikin shi Diya ne da tsayin shi , sai wutsiyarshi a baya ta na motsi " inallillahi wa'ina illaihi raji'un " Malik ya fada da karfi har ya na yin baya ya fadi , ya na zaro idanu ya na kallon macijin da Diya ya koma zuciyar shi na duka uku uku , ganin abun ya ke kamar a mafarki a hankali ya bude baki lips din shi har kerma su ke ya na fadin " Diya ! " ya furta lokaci guda ya na gama fadar haka ya ga A hankali skin din macijin nan ta sauyawa , sannu sannu har ya bace Diya ya dawo tsaye a hankali ya zauna a kassa ya yi irin zaman cin tuwo ya sunkuyar da kai murya a sanyaye ya ce " na je na kira ka mu tafi mosque dan lokacin sallat ya yi , amma ban gan ka ba a part din MALIKAT HOUDA , shi ne da na tambaya , a ka ce min ka na part din MALIKAT AL'UMU , na je part din zan shiga na jiyo Muryarka ku na magana da MALIKAT AL'UMU , na ji abun da ka fada mata , ka yi hakuri na boye maka wannan sirrin tsawan shekaru , just na rasa yadda zan iya fada maka ne , na san duk lokacin da ka san ya na ke ba za ka taba ci gaba da yarda da ni ba , that's why ya bunne abu na , amma bayan na ji abun da ka fadawa MALIKAT AL'UMU shi ne na yanke shawarar fada maka " " ya Salam " Malik ya fada cikin zuciyar shi , ka fin ya bude baki ya ce " kai , kai ma tsafi ka ke yi ? kamar Aymane ? " da sauri Diya ya dago kai , nan Malik ya ga hawayen da ya ke zubar wa da sauri ya ce mishi " No , ba na tsafi , duk zaman da mu ka yi da kai ka taba gani na na yi wani abu mai kama da tsafi ? " a hankali Malik ya girgiza mishi kai allamun a'a kafin ya ce " ta ya a ka yi ka ke zama wannan abun kai ma , kenan ka na sane da Aymane shi ma ya na zama hakan ? " ❤⚘ EXILED PRINCE ⚘❤ ( LOVE MEETS POWER ) 👑🔥 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) STORY & WRITTEN BY

Table of Contents

Chapters

31 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});