Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 19

Chapter 19

Deejamah Book 1 Complete Hausa Novel 1,289 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

wajen karatun sa, a gefe daya Kuma Daddy ya turo magabatan sa wajen fake magabatan Shakeerah an tsayar da magana nan da two weeks za'a daura Aure. Daddy yaso ayi event sai dai Shakeerah tace ita Sam bataso bada itaba,kudi yaturomata 10million akan tayi siyayya kuma ta hada ma kanta lefe. Komai shiya siya hatta da kayan daki,domin a dangin Shakeerah bb Wanda yasan da maganar daga Ammi sai fulani Shiyasa bb wani shirye-shirye da ake gudanar wa ta bangaren ta sai dai a gidan hjy harirah. Ana saura sati guda biki 'yan uwan Daddy suka kawo kayan lefe ciki kuwa harda car key,abun ya birge kowa akwati dozin uku gaskiya Daddy yatara dukiyan haram Allah ya kiyashe mu. Ranar wata laraba da daddare Daddy na bacci yaji zoben hannun sa yafara rawa,alamun anason mgn dashi,bude ido yayi, nan kuwa zoben yayi haske sosai sai ga wani mutumi ya bayya na a gaban sa da jajayen kaya,mummuna sosai sai wani baki gashi bb alamun imani a fuskan sa, cikin tsawa yace"Lallai Sani kana nan kana bacci muko muna cikin matsala babba. A firgice Daddy yace"Oga Patrick tuba nakeyi........tsawa ya dakama Daddy"kayimun shiru kaje zaka auro Mana masifa da bala'i a binciken da mukayi wannan yarinyar annoba ce a cikin mu meyasa zaka Aure ta? Cikin Daddy na shaking yace"A'ah oga Shakeerah Bata da matsala kafin na Aure ta sai da nayi bincike kuma an tabbatar mun da Babu abinda zai faru kamar yanda sauran suka faru. "Alhj Sani kanaja da magana nane?da binciken da akamaka da Wanda mukayi wannene gaskiya? Shiru Daddy yayi. Mr Patrick yace"Oh nagane ka Saboda kaga nabaka karamin shugaban kungiya shine kakeso kayi abinda kaga dama?to Bari kaji Muddin ka Aure yarinyar nan aka samu matsala to kayi kuka da kanka badamu ba. Yana gama fadar haka yabace battt,tsaki Daddy yaja yace"kilama kunyi bincike ne kunka da alkhairi shine kukeson rabani da ita,aini da Shakeerah sai dai mutuwa,Yana gama fadar haka ya juya ya cigaba da baccin sa. Shakeerah dasu khadee Suma ta bangaren su sun dage da addu'ah sosai akan Allah yabasu nasara akan Daddy,haka ta bangaren Ammi,fulani da Ummi ma ba'a barsu a Baya ba,a kwana a tashi biki ya kasance saura kwana hudu,Babu wani gyara da Shakeerah taje yi domin ita ba Aure zataje yiba. Hjy sameera hankalinta yatashi Jin Daddy zai Kara Aure tunda ake mata kishiyoyi bata taba Jin irin wani mugun kishi ba sai akan wannan da za'akawo mata,gaban ta na tsanan ta faduwa matuka ta rasa dalilin hakan. Kwatsam su Shakeerah na school chairman din department dinsu yakira su Kan cewa antafi yajin aiki,ba karamin Jin dadi sukayi ba shikenan faduwa tazo dai-dai da zama,Ranar Asabar kuwa aka daura Auren Shakeerah da Daddy duk da Babu taro Amma Sai da Daddy ya turo abokan sa,unguwan du hjy harirah yayi makil da manyan Mutane,ana gama daurin Aure Daddy ya dauki Amaryan shi,dama tunkafin yazo Shakeerah taje sunyi sallama da su Ammi da fulani,sosai suka sake bata shawarwari da ja mata kunne Akan kada ta kuskura ta yarda da Daddy. Irin kukan rabuwar nan da'akeyi Sam Shakeerah batayi ba sukuwa su khadee da fauzy Sunyi kuka kamar ransu zai fita,a dalilin kewar Shakeerah ita kuwa cemusu take suyi hakuri tana nan dawowa soon. Sosai 'yan uwan Daddy suka tarbeta d farin ciki da kauna tunda family house dinsu suka kaita,Bayan sallar isha'i suka dauketa suka kaita gidanta,direct part din hjy Sameera suka nufa da ita,domin Amarya ma tana can. Sun samu hjy Sameera akan kujera tayi daurin kirji ture kaga tsiya Sai karkada kafafuwa take tana taunar chwengum. Sun aje Shakeerah 'yan uwan Daddy zasu gabatar da ita hjy Sameera ta dakatar dasu,kunga kutashi kutafi wannan abun da zaku fada ba yau nasaba jinsa ba don haka nariga na haddace ku ajeta ku tafi,duk da cewa 'yan uwan tane suma,mikewa sukayi suka fita batare dasun tanka ba,don sun San halinta ba kirki tacika ba. Tsaki Hjy sameera taja tace"kekuma munafuka Sai ki bude mana face din naki domin kuwa muba siyan sa zamuyi ba. Daddy ne yayi gyaran murya tare da shigowa,sannu da zuwa Aunty Amarya tamai,batare da ya kalleta ba ya amsa. Bude taro yayi da addu'ah sannan yafara magana kamar haka"Amarya Ina Miki maraba da shigowa gidan ki,Allah yasa kin shigo da kafar dama,pls inaso ki bude face din ki don 'yan uwan ki su ganki kigansu,toh Shakeerah tafada tare da yaye mayafin da ke kanta a hankali. Duk cikan su suka mike tare da tsalle, Hjy sameera tace"haba haba no wonder,dama nasan za'a rina tunda naga tazo gidan nan nasan tuggu aka shirya maka,Yaya tarasu shine aka baka kanwa ka Aura?lallai ne.ita kuwa Aunty Amarya nuna ta take tayi tace"Amma ke maciyiyar Amana ce,daga zuwan ki rannan shine har kintafi da zuciyar shi wajen malaman garin ku?lallai. Ture Aunty Amarya Hjy sameera tayi gefe ta matso har gaban Shakeerah tace"lallai yaro baisan wuta ba sai ya taka,yayarki ma bataci galaba akaina ba wajen kishi balle ke 'yar tatsitsiyar ki dake,wallahi tundaga gobe kifara irgawa cewa kinkawo kanki gidan wahala,domin Babu ke babu samun farin ciki a gidan nan. Tana gama fadar haka ta fice,shidai Daddy shiru yayi Yana tunanin yanda zai yi ya shawo kan matsalar,tsaki Aunty Amarya tayi ta dube Shakeerah tace"munafuka........ Daddy ne yadaga hannu zai mari Aunty Amarya cikin Sauri Shakeerah tarike hannunn shi tace"haba papi na kada kaga lefinta kishi ne yakawo haka,kishin na naka,sannan akan me zaka dake?ita mai danyar jini ma tayi kishi Ina ga wacce tsufa yazomata ta Fadi maganganu na rashin da'a baka hukunta taba sai wannan. Shiru Daddy yayi tare da wucewa fuuuuu ya nufi wani part daban da alamu shine na Shakeerah,duban juna Shakeerah da Aunty Amarya sukayi suka kece da dariya, Aunty Amarya tace"gaskiya Shakeerah plan dinki yana kyau,yanzu mutashi a part din nan kafin tsohuwar nan tadawo tamana rashin M. Tabe baki Shakeerah tayi suka nufi part dinta,zage-zage Aunty Amarya take cikin pretend ta wuce part dinta.tsayawa Shakeerah tayi a kofar Falon batare da tashiga ba, Saboda talura Hjy sameera na leken ta ta window,don haka sai tayi kamar batasan inda zatashiga ba.Wayar ta ne yafara ringing cikin sauri tadauka ganin Daddy ne,hade rai tayi kamar yana gabanta batare da tayi magana ba,a hankali yace"Amarya ta kina Ina? A zafafe tace"gani a waje cikin tantagar yan sanyi Babu Wanda yabani muhalli. Wat? Daddy yafada tare da mikewa,fitowa yayi yasamu Shakeerah duke ta hada Kai da gwiwa,kwalkwal tayi da Ido cikin Sauri Daddy yakariso yadaga ta yace"Ayya Darling afwan,aina zata kina biye dani dazu dana fita shiyasa. Turo baki Shakeerah tayi tace"Bakaine kana fushi damu ba?Shiyasa ban biyo ka ba,rungume ta yayi yace"Sorry Darling kinji zo muje nakaiki part dina. "A'ah ni kawai ka nuna mun part dina na shiga nibazani naka ba,no kizo muje nawa yanzu ina wani Abu ne a cikin nan. Wani irin kallo Shakeerah tamai tace" ban Isa inga abun bane papi? Daddy rudewa yayi yace"Haba Darling kin Isa har kin wuce zo muje part dina inyaso mayi maganar da zamuyi,hannunta yakama itama Kuma Sai waigen part din nata takeyi,part din tabbas yatsaru iya tsaruwa ya hadu iya haduwa, bedroom din shi yawuce da ita sannan yace gashinan zuwa tashiga toilet ta watsa

Table of Contents

Chapters

30 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});