Chapter 14
Chapter 14
kullum sai tayi fada da yara Yan uwanta inda Kuma kaf din yaran da take fadan dasu Suma ya'yan wasu ne da yawan su ma sun fita matsayi da daraja shiyasa ake Zama lafiya Amma Wanda izzatu ta Raina ajawalin su yanzu ne zata fito ta wanke mutum soso da sabulu in ma taga Kai ba kowa bane to yanzu zata sa akulle ka Lokacin da fulani ta shekara goma izzar ta ta fito fili duk wani wulakanci na izzatu fulani ta kwashe shi kaf har ma tacewa izzatu Bata iya ba inda Kuma tace waje take so akaita tayi karatu ai kuwa izzatu tasa Kabir ya sama Mata makaranta a America ta Kuma dage ta tafi inda acan ne Kuma ta Kara koyo izza da dagawa har da jijji da Kai har Allah da ikon shi ta kammala karatun ta dawo gida Inda Kuma can ummita eng AK ya so fiddata waje tayo karatu Amma ita ummita tace Bata son abinda zai rabata da abban ta tafi son kullum ta ganshi Yayi murmushi "to sai kinyi min alkawari Zakiyi karatu sosai don so nake kiyi karatu me zurfi...... "Nayi maka alkawari Abba in Sha Allah ba Zan baka kunya ba kuma sai kayi alfahari Dani", Hakan kuwa akayi itama tayi nata karatun anan cikin garin Abuja har ta Kare inda ita Kuma ta taso cikin nuna irin nata alkalin da ta tsotso Babu hayaniya sai tsantsar irin tarbiyar da ta samu ita da kowa sai mutunci da mutuntawa da Kuma sanyin hali inda shima eng ya soma shahara akan kwagiloli Kan na kamfuna da Kuma na gwamnati komai dai cikin rufin asiri Rayuwa Kuma na tafiya cikin godiya da Kuma wadata..................... [5/16, 9:33 PM] Aunty Fauzah Yar Amanah: *ZAN FASA KWAI* *NA* *HADIZA BARA'U GIDAN IKO* _Hakkin Mallakar na gidan iko ne_ *Page 22* *_____________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_____________________________________* [ ...........Mutane suka soma fusata da wannan wulakanci da humaira ke yi kowa Yana son ya wuce gida amma saboda iskanci ta saka kida ta ware Kara ta bar mutane da danno horn Wanda ya cika kunnuwan mutane inda gayen da tayi hakan domin shi ya Gane tayi hakan ne domin ta Kona ranshi ai kuwa Yan ta wagarshi dake bayan shi suka fito daga motar dake bayan shi katti ne majiya karfi da ita da motar sukayi Mata dibar Karan mahaukaciya suka aje gefe Sai jinta tayi an fizgi motar an kaita gefe inda ashar din da mutane ke ta dura mata Kan Bata musu lokaci da tayi ya Kara Bata haushi inda ta fito taga yadda bayani motar ya bandare saboda dibar Rashin albarka da akayi Mata motar da ko sati batayi da kawowa ba haushi ya isheta ga Kuma zagin da ake ta sheko Mata abinka da Yar gata haihuwar Asibiti sai kawai ta bare da kuka shabe shabe ganin Babu Wanda ya kula ta sai ma kallon banza da ake jifar ta dashi ya sa ta shigo motar ta taho inda taji gaba daya motar ta sauya saboda bandarewar da tayi haka ta iso gidan Yana kuka inda izzatu ta fito da sauri tana tambayar ta me ya faru? "Momy dubi yadda ya mayar min da mota wallahi ba zan yarda ba...... .... "Waye da wannan aikin? "Wani dan iska ne momy bayan yayi min Bari Kuma yasa Yan iska sukayi min haka da mota wallahi sai ya biyani...... "Muje ki nuna min shi don ubanshi ko waye uban shi sai na saka an daure min shi Bai San ke ko wacece bane? Hana suka SHIGA mota suka fice izzatu na ta zuba sababi har inda abib ya faru sai dai ko me kama dashi Basu gani inda izzatu ta SHIGA sababi da dai ta Gane harara cikin duhu take sai tace su koma gida kawai "Dan iska Allah ya kure shi da ya Kare Rayuwar shi gidan sarka matsiyacin banza bai San ke din zaune kike da kuturinki ba? Haka suka dawo fulani na kukan ita motar ta ya zatayi? Izzatu ta rungume ta tana Bata hakuri tana fada Mata Wai za a gyara Mata motar ta...... "Ni momy sai dai asauya min wata wallahi bana sonta bama Zan sake hawanta ba.......... "Sha kuruminki Yar lele za a sauya Miki ko jirgin sama kike so ubanki na da kudin siya Miki bare wata mota can da kudinta ba zasu wuce milyon goma ba Haka kuwa akayi Bata Kuma hawan motar ba sai da Kabir ya sauya Mata wata wadda tace tagani ana talla a aljazira ai kuwa akayi Mata oder ta soma burkar gari Wata Ranar asabar ta nufi park don ta huta bayan tayi order abinda take so ta shimfida darduma ta zauna tana chat awayarta har uku na maraice inda ta nade dardumar tayi nufin tafiya gida tana tsaye zata bude mota ta SHIGA taji saukar bawon ayaba afuskar ta Ta dago da sauri don taga daga inda ya fito sai kawai idonta ya hasko Mata gayen da yayi Mata wulakanci har hawa biyu Har ga Allah baiyi da niya ba asalima Bai San ya watso inda take ba Ta tafi afusace Kan ta sauke mishi lodi abin haushi kafin ta Isa har yaja motar yayi gaba abinshi Haka ta juyo tana kuka izzatu ta tarbeta tana tambayar ta "Momy sai na wulakanta gayen can me na yi mishi yake min haka? "Ba dai Wanda ya lalata Miki mota ba? Shine momy yau ma sai da ya watsa min bawon ayaba afuska....... "Wai Dan gidan uban waye ne? Dame yake takama? To koma uban waye ubanshi duk Ranar da ya sake na Kama shi ga hannu sai na saka an daure shi ya Kare Rayuwar shi a kurkuku. Nan ma haka izzatu tayi ta masifa har dai suka Gane ba mafita sai yazo hannu. Ciwo ya dawo wa dungo sabo gal inda wannan karon ta nufi Asibiti inda aka yi Mata awo aka gano matsalar ta Abin ya firgita likitan Amma ita dungon Bata firgita ba don tuni ta soma hasashen hakan Likitan ya dubeta cikin rudani da tashin hankali don Yana tausayin ta tun wancen zuwan da tayi yake tausaya Mata "Baba matsalar kwada ce tare dake Kuma mun duba munga saura guda daya Tak shin kin taba bada kodarki ga wani ne? Ta amsa da eh kwarai kuwa nasan anyi hakan...... "To baba sauran gudar da tayi saura tana da matsala don haka ana bukatar sake dasa Miki wata kafin wannan gudar ta tsaya da aikinta don ko za a dawo kanta sai anyi aikin dashen Ta dubeshi cikin zafin ciwo 'to yanzu kamar nawa ake bukata wurin aikin likita? Yawan kudin da ya ambato Mata ya kusa sakata faduwa inda ta tabbatar da lallai sai ta nemi daukin danta Kabir don wurin shi ne kawai zata iya samun wannan kudin don haka tacew likitan zata yi iyakar kokarin ta har ta samo kudin kome kenan zata dawo da haka sukayi sallama da likitan ta dawo gida Ta sanar da malam Ali abinda akace ta Kuma ce zataje Abuja wurin Kabir ta sanar dashi abinda kenan...... "Inaga ki Bari naje tunda Baki da lafiya dungo
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31