Chapter 7
Chapter 7
abin fada ba, amma ya fi kowa jin ciwon abin a cikin ransa. Haka na ajiye takarduna, na sanya hannu domin tamaikawa mahaifina alokacin dama k'arfinsa yayi rauni. Rayuwa tayi mana tsanani domin mahaifina bashi da wani cikakken jarin da zamu juya mu kasa mu sayar, sai dai kullum idan mun fita shago mu zauna jiran masu kawo kwaskwarima, idan hakan ta samu kenan, domin watarana yanda muka fita haka zamu dawo babu ko kwabo cikin aljihunmu, gashi rayuwa tayi tsada kullum 'kara tsanani take. Ganin abinda zamu ci yana nema ya fi k'arfin bakinmu, yasa na fara shiga cikin kasuwani domin daukar dako, to anan ne na samu na tara kud'in da na sayi kayan gyaran babur da faci, sannan na nemi albarkar iyaye na, na fita bakin titi, domin gwada sa'a ta akan sana'ar ko Allah zai sa a dace. Cikin ikon Allah kuwa sai Ubangiji ya bani sa'a, kullum idan nayi sana'oi na, na kan tashi da kud'i masu kauri wanda zanyi awo da cefene a gidanmu sannan da safe na basu kudin karin kummalo. Iyaye na sunyi farin ciki sosai da wannan sana'a da nake, kullum cikin yi min fatan alheri suke, ita kuma Hajiya lokacin ta matsanta min lallai sai na fito da matar aure, duk yanda naso na fahimtar da ita abinda ke da akwai amma fafur! taki saurarata, ita dai tunda na samu sana'a to nayi aure. Ni kuma tunani a yanzu shine, shi aure sai mutum yana da kwakwarar sana'a! saboda yau da gobe gashi bani da muhalli uwa uba nauyin iyayena da 'kawanta Sadiya dake kaina Haka dai rayuwa ta cigaba da gurgurawa, yau da dadi gobe babu, cikin wannan yanayi ciwon ajali ya kwantar da mahaifinta! gabadaya ya daina fita yana gida a kwance sakamakon wani irin tari da ha-ki! da ya ci k'arfinsa, na d'auk'e shi na kai shi asibiti, a lokacin akayi masa gwaje-gwaje! amma cikin ikon Allah ba'a gane abinda ke damunsa ba, sai dai likita ya rubuta masa maganin da yake ganin zai taimaka masa. To koda naje gurin siyan maganin hankalina ya tashi sosai sakamakon yanda mai siyar da maganin ya fada min adadin kudin da zan biya domin a bani magungunan da likita ya rubuta a katin. Kudin dake aljihuna duka-duka dubu biyu ne, wanda ko guda daya ba zai siya ba, gashi likitan yace lallai a sayi magungunan duka domin suna da mutukar amfani. Jiki a sanyaye na koma gida da tunanin hanyar da zan bi gurin samun dubu ashirin da hudu wanda zan sayawa mahaifina magani, 'Yan uwansa ba su dashi, amma ya zama dole na je gurinsu, domin na sheda musu halin da ake ciki, saboda haka kai tsaye gurin sana'ar Malam Audu na nufa inda yake sana'ar faskare na icce. duk na sheda masa halin da ake ciki, na kuma nuna masa katin asibitin domin ya tabbatar. Sosai ya jajanta al'amarin, ya kuma tausayawa d'an uwansa halin da yake ciki, da karshe ya dauko dari uku ya bani tare da bani hakuri kan cewa shima bashi da kudi ga wahalhalu na iyali sunyi masa yawa. Kwata-kwata ban ji haushinsa ba, domin na san da gaske bashi dashi, d'an abinda ya ke samu bai taka kara ya karya ba, kuma dashi yake daukar nauyin iyalinsa. Gurin d'an autansu na nufa wanda muke kiransa da Baba Auta babu laifi shi yana d'an samu a kasuwa tunda harkar hatsi yake gidansa babu yunwa kuma sannan a cikinsu duk yafi su rufin asiri. Kallona yayi a lokacin dana gama yi masa bayani, ya girgiza kansa da fadin." Lallai Sani yana cikin jarrabawa, Allah ya ba shi lafiya" na amsa da "ameen" ina jin sanyi a zuciyata, domin duk a zato na zai taimaka mana, kawai sai ji nayi ya ce." To Saddiku kasan dai yanda rayuwa take, duk wanda ka ga yana nema to saboda iyalinsa yake, saboda haka zan taimaka daga abinda naga zan iya domin kuwa ba zan takurawa kaina ba." Yasa hannu cikik aljihu ya dauko kudi d'aure da kyaure ya zaro dubu daya ya miko min da fadin." Ga wannan a hada a saya masa maganin, Allah ya ba shi lafiya." Jikina a sanyaye na kar'ba da fadin." Allah yasa ka alheri ." Ya amsa da ''ameen" tare da shigewa cikin gidansa ya bar ni tsugune a gurin. To koda na shedawa Hajiya abinda ya faru, sai cewa tayi ai sunyi 'kokari ma a hakan, abinda yanzu wahala tayi wa kowa yawa, wa zaka je ka daura nauyinka" Sai na kasa fahimtar inda maganarta ta dosa, wato tana nufin ta goyi da bayan abinda sukayi kenan daidai ne a gurinta. girgiza kaina kawai nayi na tashi na bar gurin, zuciyata cike da jin ciwon rashin kulawar da take akan mahaifina kamar ba ita ce ta haife su duka ba. Wani abokina ne ya bani shawarar zuwa gidan redio domin na kai kuka na, cikin ikon Allah kuwa kwana biyu da zuwa na wani bawan Allah ya biya kudin maganin, sosai nayi farin ciki, addu'a kuwa munyi masa sosai dani da mahaifiyata da k'anwata Sadiya. Cikin ikon Allah yana fara shan maganin sai sauki ya fara samuwa, muna ta murna da godewa Ubangiji, sai dai kuma mune muke haukanmu ashe saukin na tafiya, daran alhamis ya rasu! da kalmar shahada a bakinsa. Mutuwar mahaifina ba zan ta'ba mancewa da ita a tarihin rayuwata ba." Shuru yayi, ya kasa cigaba da bata labarin. saboda yanda mutuwar ta dawo sabuwa, kukan zucci kawai yake, Lokacin ita kuma tausayinsa duk ya gama mamaye zuciyarta, sai ajiyar zuciya take saukewa tana sake shigewa jikinsa kukan da take dannewa ne ya su'bce! sai sautinsa ya ji a kunnensa! sosai take zubar da hawayen tausayinsa. Hankalinsa ne ya tashi ya dinga rarrashinta cewa tayi shuru saboda dare yayi sosai! sautin kukan zai iya fita, duk da cewa gurin da suke da tazara mai tsayi da cikin gidan. Ganin ta'ki ta daina kukan ne yasa ya d'auke ta kai tsaye d'aki ya nufa da ita a rungume a jikinsa yana cigaba da lallabata, kan kirjinsa ya kwantar da ita ya matseta tsam! da zai samu shima kukan zai yi domin komai ya dawo masa sabo. [1/12, 11:25 PM] Binta Umar Abbale: 71&72 "Ina gurin aiki sai ganin Sadiya nayi a kaina. Na san dama hakan zata faru, ko ga yanayin da naga yarinyar, idanuwanta sunyi jawur! da alama ta ci kuka ta 'koshi. na ce" Menene? nan take sheda min cewa gida babu lafiya na je ana nema na." hankalina na kan babur din da nake gyarawa, na ce "taje kawai gani nan zuwa." Koda na shiga gidan hayaniya hayaniya ce kawai take tashi. muryar Hajiya tafi ta kowa sai sababi take, ta inda take shiga ba tanan take fita ba. shigowata yasa suka saurara, Inna Samira ce 'kanwar mamana, suke musayar yawu da Hajiyan, yayin da mahaifiyartawa ke cikin d'aki tana zubar da hawaye, wannan shine abinda ya d'aga min hankali, kuma nayi nadamar abinda na aikata, wanda na san shine musabbabin tashin hankalin da yake afkuwa a gidan. " Ka shige ciki zanyi magana da kai." Hajiya ce ta bani wannan umarnin, ban yi mata jayayya ba, na bi bayanta. nan na gan su a zaune
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28