Chapter 26
Chapter 26
nayi naga sai dudduba rigar yake mussaman ma'ajiyar nonon dake jikinta kafin ma nayi magana na ji yana fad'in" Anya kuwa Wannan gurin be miki kad'an ba ?" Ya fad'a yana nuna min gidan nonon rigar. da saurin gaske na kawar da kaina kunya kamar na nutse a gurun. Abubuwan da yake kamar wani matashin saurayi! na lura shima kunya tayi masa 'karanci. Ya sake maimaita maganar. Na ce" Nima ban sani ba. Sai kawai na ji saukar hannunsa a :kirjina yana lalubawa! a gigice! na sauka daga gadon! ina harararsa! dama abinda yake bu'kata kenan! a ganinsa wannan ba harara bace kallon soyayya ne. Ido ya kashe yana bina da wani shu'umin kallo! duk sai na tsorata, kamar na bud'e dakin na fita, amma sai na daure, na zauna kan kujera gabana na cigaba da fad'uwa! babu shakka akwai babban al'amarin da zai faru a tsakaninmu. Kira ne ya shigo wayarsa na ji yana fad'in" Yaushe ka dawo babu labari?" Shiru na 'yan second biyu kafin ya ce." Allah ya kai mu lafiya idan ka shigo sai ku gaisa da amarya ta." Dariya naga yayi kafin ya ce." Ai babu wasa a tsakaninmu, wallahi da gaske nake nayi aure kimanin wata uku da suka wuce." Shiru yayi yana sauraransa kafin ya ce." To Idan ka zo zaka dai tabbatar da magana ta, Allah ya ba mu alheri." Kashe wayoyinsa yayi duka ya ajiye kan dirowa kafin ya kalle ni, babu wasa a fuskarsa ya ambaci sunana da sautin da zan ji maganarsa. Amsawa nayi nima ina kallonsa. Ya ce." Za mu yi sallah ta godiya ga Allah ko?" A sanyaye na d'aga kaina. Sai ya tashi ya nufi band'aki! ya bar ni a zaune ciki tararrabi da fad'uwar gaba! Alwala yayi ya fito nima na shiga nayi alwalar na fito na same shi ya shimfida mana babbar dadduma! Hijabi ya mi'ko min na kar'ba nasa a jikina, na tsaya a bayansa ya tayar da sallar. Raka'a biyu mu kayi, ya daga hannu sama, ya dinga kwararo addu'a har sai da na tausaya masa jin yana rok'on haihuwa da samun wadatacciyar nutsuwa da kwanciyar hankali a tare da ni, da kuma zuria masu albarka, muryarsa sai rawa take kamar zai fashe da kuka yake fad'in "Ubangiji Allah kasa nayi auran nan kenan! mutuwa ce zata raba ni da matata, ya rabbi ka bani zuria da yawa da ita, kasa na samu nutsuwa da ita, Wahidun ahadun! kayi min wannan arzi'kin don alfarmar Annabi Muhammadu S.A.W." Hawaye ne suka fara zuba a saman fuskata, gabad'aya tausayinsa ya gama kashe min jiki, ro'kon Allah yake akan ya samu zuri'a da ni, ya na kuma bukatar ya samu nutsuwa da ni, duk ni kad'ai! tabbas Allah yayi min tagomashi! kuma yayi min kyautar da ba kowace mace ba, domin samun nagartaccen namiji a wannan zamanin sai anyi dace. Bayan ya shafa addu'ar ya juyo yana kallo na, lokacin na kasa tsayar da kukan da na ke yi, hannuna ya ri'ke kafin ya ce." Menene?" zuciyata ta sake karyewa, hawayen suka cigaba da zuba, yasa hannu yana goge min, ya ce"Zubar hawayenki yana min zafi a cikin raina, yau babbar rana ce a gare ni, na had'a ki da girman ALLAH ki daina yi min asarar hawayen nan" Kallonsa nayi, naga yayi wani irin rama a gabana, kamar mai neman gafara sai rarrashina yake da kalamai kyawawa! na ce" In sha Allahu! zan zama farin cikin ka, ai ban za ci 'kaunata ta kai haka a cikin zuciyarka ba. Murmushi yayi wanda yake 'kara masa kyau! ya ce." Kin wuce haka a can cikin zuciyata, domin k'aunar da nake miki tayi nisa ta bi ilahirin jinin jikina gabad'aya idan babu ke rayuwata zata salwance, a kanki na san meye so! duk matan dana aura akwai dalili, amma ke ce ra'ayi na, buri na shine ki bani dukkanin kulawarki, kuma ki zauna lafiya da ni." Hannuna na ri'ke a karo na farko! ban ji nauyin had'a yatsuna da nasa ba, na ce" Zanyi 'kokari in sha Allahu." Murmushi kawai yake yana jifa na da wani irin kallo, wanda yasa nayi saurin sunkuyar da kaina kasa. To duk da ya ce a 'koshe yake sai da ya taya ni cin abincin, nima ba wani da yawa na ci ba saboda fargaba, kad'an na tsakura, na shiga bandaki nayi wanka tare da wanko bakina na fito, duk jikina babu 'kwari, domin ina jin tsoron abinda zai wanzu a tsakaninmu, yanayin kallon 'kurrulan da yake min, shi yake tabbatar min da cewa; da wuya yau wani abu bai faru ba. Rigar ya mi'ko min yana kashe min ido. Kasa 'karba nayi saboda kunya, na sa hijabi a jikina. Ya tashi ya je ya kashe fitilar dakin, da ya dawo ya zauna yana lalube na. Can gefe na matsa tsigar jikina sai tashi take. Sai da ya lalubo ni, ya rike hannuna sosai kafin ya fara kici-kicin cire min hijab, dama kuma daurin kirji ne a jikina. Kuka nasa masa ina ture shi, ni gabad'aya al'amarin banbarakwai nake jin sa. Bai damu da yanda nake kuka turje-turje ba, haka ya cire hijan din jikina ya ajiye ya kwantar da ni saman gado. Ni dai tun daga lokacin na shiga d'imuwa, domin kasa fahimtar kaina nayi, don jikina saki yayi tunda ya d'ora min nauyinsa, ban san ya akayi ba har ya gano abinda na fi muradi, nan naga ya mayar da hankalinsa a gurin, har ya samu kaina na dinga biye masa ina rawar jiki, sai dai kuma lokacin da mai afkuwa ta afku na raina kaina mutuka gaya! domin dai nan na gane cewa maza suna suka tara, dattijon 'karfi! ne dashi sosai! ya k'urewa duk wata fitina ta, kuka na dinga rizga tare da kokarin kwatar kaina daga hannunsa, a lokacin da shi kuma yake kan ganiya, ya hana ni k'atabus! jikina ya laushi sarrafa ni kawai yake ta kowace siga, yana yi tare da numfarfashi! [1/12, 11:30 PM] GARKUWAR MATA: 92&93 Ba zai iya tantance wane irin hali yake ciki ba sakamakon tarayyarsa da yarinyar. ita ce mace ta uku da wata mu'amula ta shiga tsakaninsu. amma ya bata lamba ta d'aya a cikin jerin matan da ya yi mu'amula irinta ta auratayya. babu shakka Ubangiji baya tarawa bawa damuwa! domin ko da ya halliceta cikin jerin masu rangwamin gata sai kuma ya wadata ta da ni'ima tare da sauran abubuwan da ba kowace mace ke da irin shi ba, shi dai ya tabbatar da cewa; yarinyar ta zarce duk matan da yayi tarayya da su don ya samu gamsuwa da ita sosai, babu wani abu da yayi saura a mararsa, sakayau! ya ke jinsa tare da wani irin nishad'i da bai ta'ba shigarsa ba, lallai dole ya godewa Allah bisa ni'imar da yayi masa gurin azurta shi da 'yar baiwa wacce take da tarin nagartattun abubuwa masu alfanu a gare shi. Da wannan tunane-tunanen bacci mai nauyi ya d'auke shi ya matse ta tsam-tsam! a jikinsa. Da gari ya waye kuwa duk hidimar da ya kamata na yi da kaina shi ya yi min, yanda yake nuna kulawarsa a kaina hakan ya faranta min raina mutuka! sosai nayi farin ciki da ya samu budurci na
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28