Chapter 10
CHAPTER 9
⚖HOME OF QUALITIE'S WRITER'S ASSOCIATION📚
Ammar bai daina neman Salmah kowane lungu da sakon na garin ba. Haka bai daina kiran wayar ta ba da koda yaushe ake ce masa kashe take. Har kawar ta Khadija bata samun ta a waya. Wannan lamarin ba karamin tayar masa da hankali yayi ba, bai san me zai yi ba ko a ina zai neme ta ba. Gashi gobe zai koma company, bai san ko zai iya aje hankalin sa yayi aikin ba.
Kafin yace zai aure ta, sai da ya fada mata shi bai damu da abinda tayi ba a baya, kuma har yanzu hakan yake tunani. Ya hadu da ita ya fara soyayya da ita, ta dalilin son da yake mata. Kara fadawa ma yayi sonta lokacin da ta bashi labarin rayuwar da tayi a baya. Eh tayi kura-kurai amma ta tuba ta daina, kuma Allah na son masu tuba.
Bai san ta yaya Mahaifiyar shi tayi wajen gano wannan sirrin da ya boye kasan zuciyar sa ba. Haka bai san ko Salmah zata yarda idan ya fada mata baida alaka da abinda mahaifiyar shi tayi mata, kuma zai yi iya kokarin sa ganin ya dawo da ita. Bai taba kaunar wata 'ya mace ba kamar yanda yake kaunar ta, kuma zai iya shiga mawuyacin hali idan ya rasa ta. Mahaifiyar sa, mahaifiyar sa ce ba yanda za'a yi ya iya saba mata, amma tana sa masa matsi ba kamar dan uwan sa ba. Shima yana son yin gidan kansa ya koma kamar Kamal, amma ba zai iya barin mahaifiyar su ita kadai ba. Mahaifin su mai yawan tafiye tafiye ne, ita kuwa Mommy ta daina aiki, kullum tana gida. Dama dama da cikin kannenta wata ta bata rikon 'yarta Anifa, wacce take yanzu tamkar kanwa uwa daya uba daya a gare su. Ba zai iya tafiya ya bar su su kadai ba a gidan. Wannan ne yasa ya tsaya amma yana ganin hakan kusa zuwa karshe.
Yanke shawarar neman taimakon yayan sa Kamal yayi, domin yana da hanyoyi da dama a wajen manyan mutane. Wata kila ya iya samo masa private detective da zai nemo masa inda take. Bai yarda da yan sanda ba, zasu bata masa lokaci ne daga karshe suce babu abinda zasu iya akan batan ta.
A cikin motar sa, kokarin kiran Kamal yake amma baya dauka. Bayan wasu yan mintuna sai gashi ya sake kiran shi.
“Hello..” Kamal ya fara magana.
“Hello bro ya kake? I really need you. Kana ina ne yanzu?”
“Ina gida, zaka zo ne?”
“Eh.” Ya bashi amsa kafin ya juya motar sa zuwa hanyar gidan Kamal.
Lokacin da Ammar ya karaso gidan, ya tarar da Kamal yana cikin painting wani zane.
“Salmah ta bata, na kasa samun ta a waya. Kuma na duba ko'ina ban ganta ba. Hankali na ya tashi. Bata kira ka ba?”
Ajiye brushes na zanen sa yayi, ya juyo yana fuskantar Ammar.
“Kaje gidan su ne? Ban sake ganin ta ba tun lokacin da kace na kai Zahara.” Cewar Kamal.
“Yaya Zarahan take? Ban je na ganta ba da duk wannan abun dake faruwa. Mom ta gano wasu abubuwa kan Salmah kuma hakan ba karamin tada kura yayi ba. Saboda hakan ne ta bata. Ni wallahi bansan abin yi ba.”
“Ka tambayi Khadija? Kaje gidan su? Ko kiran yan sanda muke yi?”
“Na duba ko ina na fada maka. Kuma bana son saka yan sanda a wannan lamarin. Na zo nan ne, ina son kayi min wani taimako.”
“Taimako? Zan iya taimaka maka wajen neman ta, amma bani da masaniya ko kadan akan inda take.”
“A'a ina son ka taimakamin wajen samun private detective.”
“Kana tunanin ta bace da gaske? Ba zamu iya jira na karin kwana daya ba? Ina da tabbacin tana son yin nesa da duk wannan ne, na wani lokaci, ina ganin ka daina daga hankalin ka haka. Rashin ganin ta yana da alaka da abinda ka fada min yanzu.”
“Wlh bro, ni ban san me zan yi ba yanzu.”
“Da farko, kayi kokarin samun nutsuwa. Mu karawa Salmah dan lokaci idan nan da zuwa gobe bata bayyana ba, sai mu sanar da yan sanda ko kuma mu nemi private detective.”
“Kana da gaskiya.” Cewar Ammar. “Ina ga nima zan nemi gida na koma, domin na fara gajiya da halin mom.”
“Ba zan shiga cikin lamarin ku ba. Kayi abinda kake ganin ya dace.” Cewar Kamal kafin ya juya ya cigaba da painting sa.
“Ni zan wuce gida, zan zo gobe na same ka idan na tashi ban samu labarin Salmah ba.” Ammar ya fada yana saka takalmin sa.
“Ok, amma ka kira kafin ka zo. Ina son zuwa wani wuri ne goben.”
“Ina zaka je?”
Ammar ya tambaye shi amma bai bashi amsa ba. Yanke shawarar ya tafi ya bar dan uwan nasa cikin duniyar shi mai cike da abin al'ajabi. Koda ya fito daga gidan Kamal , gida ya koma. Da nasanin dawowa gidan yayi, lokacin da mommy ta tarar da shi cikin daki taci kwalliya.
“My son ka dawo? Dazu nake tambayar Anifa take ce min ka fita tun da safe.” Cewar Mom tana mai zaunawa kusa da shi.
Tashi yayi daga kusa da ita, ya dauki computer shi.
“Ina cikin aiki ne Mom.. bana son a takura min.”
“Wane irin aiki? Tashi ka shirya muna da baki yau. Tun jiya nake son yi maka magana amma sai wani gudu na kake kamar wani karamin yaro. Ba wani lokaci mai yawa a gaban ka, je ka shirya kayi kwalliya kazo ka tarbi bakin mu.”
“Mom da alamu baki damu da damuwa ta ba. Baki ga halin da nake ciki ba? Salmah ita ce wacce nake son aure, amma jiya ta sanadin ki soyayyar mu da muka gina ta shekaru ta rushe. Idan har ba zaki iya goyon baya na ba kan abinda nake so, ina tunanin nima zan bar gidan nan kamar Kamal.”
“Oh, dan kawai na kori budurwar ka, shi ne kake son juya min baya? Kana tunanin zaka iya biya na duk wata dawainiya da na da kai? Na dauke ka a ciki na tsawon wata tara, na shayar da kai kuma na nuna maka kauna. Kai kuma da hakan zaka saka min? Yarinyar nan karuwa ce, kana tunanin idan ka aure ta, 'ya'yan ka zasu samu tarbiya mai kyau? Amma ba zaka fahimta yanzu ba, sai nan gaba idan ka samu 'ya'ya masu tarbiya zaka fahimci dalilin da yasa naki aminta da yarinyar nan.”
“Kina tunanin tarbiyar 'ya'ya ta danganta da halin mahaifiyar su ne? Muna ganin yanda mata na kwarai ke haihuwar fandararrin 'ya'ya, ko kuma malaman da ke haihuwar barayi da yan fashi. Salmah tayi kura-kurai a baya kuma ta tuba. Na rantse miki yanzu, yarinyar kirki ce, idan kika yi kokarin sanin ta da kyau zaki fahimci haka.”
“Zamu yi maganar nan daga baya, je kayi wanka ka shirya yanzu dai.”
“Ni yanzu bani da lokaci, kuma bani da bukatar tarbar bakin ki da murmushin munafunci. Bansan halin da Salmah take ciki ba a dalilin ki. Ki rabu da ni dan Allah, ki je ki ji da bakin ki ke daya.”
“Ka gani koh, dalilin yarinyar nan ka fara min rashin kunya, abinda baka taba yi ba a baya. Hakan yasa na fara tunanin bata barka haka ba.”
Mikewa Mom tayi, tace
“Bari ganin kana da kusan shekaru 33, ni mahaifiyar ka ce kuma inada iko a kanka, dan haka zaka tashi ka shirya ka same ni a falo. Ko kuma na nuna maka wani bangare na fushi na da baka san da shi ba.” Ta fada kafin ta fita daga dakin kamar yanda ta shigo.”
A BANGAREN HAFSAT
Mahaifiyar ta ta fada mata komai zai je daidai. Amma ita tafi kowa sanin waye Ammar. Ita ce mace ta karshe da zai so gani a duniyar nan kuma ya tabbatar mata da hakan haduwar su ta karshe. Ya fada mata ya gwammace mutuwa da ya aure ta. Hakan ya mata ciwo amma ita ma kanta bata bukatar auren shi. Su biyu basu taba zama a inuwa daya ba kuma bata tunanin yanzun wani abu zai sauya. Abinda yasa bata ce a'a ga auren nan ba, saboda tasan mahaifiyar ta da Hajiya Karima indai suka sa abu gaba sai sun cimma masa. Bata san me zaya biyo baya ba, amma tasan zaman su ba zai yi kyau ba. Ina ma zai yarda da auren, da kowannen su ya samu yancin sa. In yaso bayan wasu yan watanni sai su rabu, sai su cewa iyayen nasu basa jituwa ne... Kuma wani bangaren na ce mata, koda sunyi auren a irin plan din nan. Suna iya kashe junan su saboda kiyayya.
“Ke kuwa Hafsat ki dan yi kwalliya mana.” Cewar Mahaifiyar ta yayin da ta sako kafa cikin mota.
“Mom, na fa shirya, ba wani karin wata kwalliya da zan yi. Na tabbatar kawai batawa kan mu lokaci ne zamu yi.”
Cewar Hafsat kafin ta yiwa motar key.
“Je a hankali kar ki kashe ni nidai.”
Rage gudu Hafsat tayi, ta cigaba da tuki ba tare da tace wani abu ba.
“Amma Mom..”
Katse ta mahaifiyar ta tayi.
“Amma me? Ke kin fi kowa sanin dalilin da yasa zamu yi hakan. Kuma kema zaki iya amfani da wannan damar, Ammar namiji ne kyakyawa mai hankali da nutsuwa, kuma kema haka. Toh banga dalilin da zai sa ta ki daidaituwa tsakanin ku ba. Kinga daga karshe kowa zai fita da rabon shi.”
Koda tana son auren Ammar, zaman su ba zai yiwu ba. Ba zata so rayuwar da zata zauna da mijin da ba sonta yake ba dalilin abinda iyayen ta ke so. Koda hakan ta faru, zata nemi takardar saki daga baya. Bata yi tsufan da zata yi irin zaman auren nan ba, tasan zata samu miji da ta fito cikin sauki.
Sun iso gidan Alhaji Yusuf, cikin rabin awa. Hajiya Karima ce ta tarbe su, tasha kwalliya da murmushi a fuskar ta.
Bayan sun yi gaishe-gaishe, Hajiya Karima tayi musu iso cikin katon falon su, sannan tasa yan aiki suka kawo musu abinci iri-iri da abun sha.
“'Yata me yasa baki zuwa ganin mu? Nan ma ai gidan ku ne, ki dinga kawo mana ziyara mana.” Cewar Hajiya Karima tana mai zaunawa kusa da Hafsat.
“Ah, kar ki damu kawa ta, zata dinga zuwa ganin ku akai-akai. Bata samun lokaci ne saboda aiki, amma yanzu da zata zama yar gida, zata dinga samun lokacin zama da ku insha Allahu.” Cewar Mahaifiyar Hafsat.
“A'a na fahimta. Har Ammar baya da lokaci na, amma kar ku damu indai zaku kasance cikin farin ciki nima haka. Zaki iya zuwa ki ganshi yana sama in kina so. Nasan kun jima baku ga juna ba.”
Kallon mahaifiyar ta Hafsat tayi, da ita kuwa take jin tamkar ta daka tsalle dan murna. Tana tunanin wannan ce damar da zata kusanta Hafsat da Ammar, amma bata san wata hanyar da zai ci mutuncin Hafsat din bace aka bude masa.
Ok Hafsat tace tare da ajiye kofin jus din dake hannun ta sannan ta tambayi inda dakin nasa yake.
Kiran Anifa Hajiya Karima tayi, tace ta kai Hafsat dakin Ammar. Kallon Hafsat Anifa tayi sannan tace ta bi bayan ta. Sama suka nufa, ta kaita bakin kofar wani daki, cewa tayi ta tsaya a nan. Sannan ta konkwasa dakin sau biyu, kafin ta murda kofar ta shiga. Ta bar Hafsat tsaye bakin kofa tana jira.
Haushi ne ya kama Hafsat, wato dakin nasa kamar wani office dan zata ganshi sai ta jira an je an nemi izinin sa, ba zata iya jira nan ba kamar wata sakarya. Murda kofar ita ma tayi ta shiga. A kishingide yake da computer bisa gwiwan sa. Bai wani yi mamakin ganin ta ba, domin ko kallon ta bai yi ba. Ita kuwa Anifa kallon ta take na ganin bata jira tayi mata iso ba kamar yanda tace mata.
“Zaki iya tafiya Anifa, zan yi magana da shi.”
Amsawa Anifa tayi cen ciki, tare da juya zata fita, harda dan bangaje Hafsat tayi da ta bita da kallon mamaki. Hafsat na tunanin me ke damun yarinyar cen, domin bata taba yi mata irin haka ba.
“Me kike yi nan?” Cewar Ammar ba tare da ya daga kai ya kalle ta ba.
Dakin Hafsat tabi da kallo, da komai yaji tsari. Kafin tace
“Nazo ganin mijin da zan aura ne, irin tarbar da zaka yi min kenan?”
Sai a wannan karon ya dago ya kalle ta. Kafin ya mayar da kanshi jikin computer.
“Kwantar da hankalin ka, nazo nan ne saboda mahaifiyar ka ta gayyato mu.”
“Mahaifiya ta ta gayyato ku, so ki fitar min daga daki.”
“Ni kaina ban so zuwa wajen ka ba, mahaifiyar ka ce ta nemi da inzo in ganka.”
“Bai zama tilas sai kin shigo nan ba. Kina iya ki tsaya a corridor sai ki juya ki koma. Ina da ayyukan da zan yi yanzu. Dan haka kina iya tafiya.”
“Ba sai ka nuna muguntar ka ba a kaina. Nasan ba sona kake ba.”
“Baki san komai ba tinda har yanzu gaki a tsaye. Ki tafi, nan zan gane kin dauki darasin da kyau.”
“Bana son auren nan nima, idan mun hada kan mu zamu iya samun abinda muke so. Muna iya yin aure, sai mu rabu bayan wasu watanni. Iyayen mu zasu shafa mana lafiya.”
“Saboda irin wannan haukan ne bana son ki tsaya nan, ki wa girman Allah ki fita kuma kar ki sake dawowa.”
Kallon sa take ba tare da tayi wani abu ba. Tana jin tamkar ta rufe shi da duka amma bata iyawa.
“Tinda haka ne, zan tafi.”
“Da kin kyautawa kanki.” Ya fada yana cigaba da latsa keyboard na computer shi.
“Amma ka san wani abu, koda na tafi zaka samu labari na nan kusa. Ka sa wannan a ranka.”
Mikewa yayi da sauri daga kan gadon sa, ya kama hannun ta, ya jata da karfi zuwa bakin kofa. Ya tura ta waje sannan ya buga kofar da karfi.
Wannan shi ake kira cin mutunci na karshe. Kuma tayi alkawarin sai yayi nadamar yi mata hakan. Ko kuma ba sunan ta Hafsat Alhaji Abubakar ba.
-------------------------------------------------------------
[03/03 à 05:18] ASHTAR: AMRIYA
(Hatsabibiyar Aljana)
Love 💞 and Horror ☠️ story 📖
By Malik al-Ashtar 🖋
On wattpad : https://www.wattpad.com/story/270492485
Table of Contents
Chapters
- 1 Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
- 2 CHAPTER 1
- 3 CHAPTER 2
- 4 CHAPTER 3
- 5 CHAPTER 4
- 6 CHAPTER 5
- 7 CHAPTER 6
- 8 CHAPTER 7
- 9 CHAPTER 8
- 10 CHAPTER 9
- 11 CHAPTER 10
- 12 CHAPTER 11
- 13 CHAPTER 12
- 14 CHAPTER 13
- 15 CHAPTER 14
- 16 CHAPTER 16
- 17 CHAPTER 15
- 18 CHAPTER 17
- 19 CHAPTER 18
- 20 CHAPTER 19
- 21 CHAPTER 20
- 22 CHAPTER 21
- 23 CHAPTER 22
- 24 CHAPTER 24
- 25 CHAPTER 23
- 26 CHAPTER 25
- 27 CHAPTER 26
- 28 CHAPTER 27
- 29 CHAPTER 28
- 30 CHAPTER 29
- 31 CHAPTER 30
- 32 CHAPTER 31
- 33 CHAPTER 32
- 34 CHAPTER 33
- 35 CHAPTER 34
- 36 CHAPTER 35