Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 11

CHAPTER 10

Amriya Hatsabibiyar Aljana Book 1 Complete Hausa Novel 2,185 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

⚖HOME OF QUALITIE'S WRITER'S ASSOCIATION📚

A BANGAREN SU ZAHARA

Tafiya suke a hankali cikin duhun dare, baka jin motsin komai. Zahara ji take duk wani taku da take yi, tamkar yana tafiya da duk wani kuzarin ta ne. Mama ta rike mata hannu, amma duk haka tana jin tsoro yana kamata a hankali. Bukatar kin zuwa na kara shigar ta. Shuru da hayakin dake tashi wanda bata san ko na meye ba a cikin makabartar na ƙara sa taji kamar ta falla da gudu. Kokowa take da duk wani sassa na jikin ta, dan kar ta kalli wuraren, ta saddar da kanta ƙasa. Ita kuwa Mama na bin tsohon a baya dan kar ya ɓace musu. Zahara tasan itama Mama cikin tsoro take amma bata son nunawa ne.

Tsoro Zahara take ji da kuma da nasanin zuwa. Nadamar kin bin shawarar Abba take yi. Haka kawai sun biyo wani tsoho dan yace musu yanada mafita akan matsalar ta ba tare sun san ko waye shi ba. Mama tace ta yarda da shi dan alamun sa na nuna mutumin kirki ne. Sai dai ko me Zahara zata ce ko zata yi lokaci ya ƙure...

Mama ce ta tsaya daga tafiyar da suke yi sakamakon shima tsoho ya tsaya. Juyowa tayi ta cewa Zahara ta karaso.

“Yi hakuri ki kara daurewa.” Cewar Mama. “Saurin yin abinda yace, saurin ganin kin rabu da wannan abun da ke jikin ki. Kin ji?” Mama ta sake faɗa.

Gyaɗa kai Zahara tayi sannan ta ƙaraso inda Mama take. Tafiya suke wannan karon da dan saurin su ganin sun cimma inda tsohon yake tsaye yana jiran su. Bayan sun ƙaraso wajen sa, ya kama hannun Zahara. Kallon ta yayi a tsanake kafin ya juya ya kalli Mama, sannan ya saki hannun ta ya ɗora hannayen sa biyu bisa kafaɗun ta da iya ƙarfin sa dan zaunar da ita. Ita kuwa Zahara kokarin tashi tsaye take amma tsohon yaki bata dama. Sannan ya cewa Mama ta ɗan koma gefe dan ya samu yin aikin sa. Mama kallon Zahara tayi da kokarin nuna mata komai zai je daidai, amma ita Zahara wannan bai ishe ta ba a yanda take cike da tsoro.

Rufe idanu Zahara tayi lokacin da tsohon ya shiga kewayar ta. Bata san kewaya ta sau nawa yayi ba, amma tasan yanada yawa. A duk lokacin da ya kewaya ta sai taji tamkar tana shakewa. Tsohon yace ta zauna bisa gwiwan ta, amma gajiyar da take ji ba zata barta ba. Ita babu abinda take so yanzu face ta bar wurin nan da sauri.

“Mama...ni.. gida..nake son..tafiya..” Zahara ta samu nasarar haɗa kalmomin nan, amma Mama bata ce komai ba. Shi kuwa kamar yana jira ta faɗi hakan, ya dakata daga abinda yake.

“Zan kira Amriya zuwa cikin jikin ki. Dan haka ba wani abu bane idan baki iya tuna komai ba.”

Da Zahara yake amma ita ba lallai bane taji abinda yace. Domin duk a gajiye take, ga kuma bukatar barin wurin da take da.

“Ayyarubo ramataniya sasiban..”
Tsoho ya shiga maimaita wannan kalmomin ba ƙaƙƙautawa a bayan Zahara. Ya shiga zuba mata wani abu a kai, ita kuwa ta daga kanta domin samun yin cikakken numfashi. Wasu ruwan ya sake fiddowa ya watsa mata wanda wannan karon suka sanyata amai bayan wasu yan mintuna. Zahara taji tamkar zata amayo da hanjin ta. Bata gani sosai amma abinda ya fito daga cikin bakin ta baki ne sosai fiye da gawayi. Wani azababben ciwo ne ya sanyaye mata jiki ta faɗi kasa kamar wani yasa ƙarfi ya ture ta. Ta kasa magana ko motsi. Fatar idanun ta a hankali ta fara yi mata nauyi. Ta kasa controlling jikin ta.

Mama kuwa tsoro duk ya kamata, jikin ta ya shiga rawa ganin ƴarta kwance a kasa. Tambayoyi suka fara yawo cikin kanta. Anya kuwa tayi abinda ya dace? Toh in fa mijin ta yayi gaskiya? Yanke shawarar korar tunanin tayi, tabi abinda zuciyar ta ke fada mata na son taimakon ƴarta. Addu'a kawai take yayin da shi kuma tsoho Malam Shehu ke warkar da ƴarta.

Shuru wajen yayi. Malam Shehu bai daina kewaya Zahara ba, kafin shima ya dagata. Numfashin Mama da kadawar iskar bishiyun maƙabartar kawai ake ji da ya bada yanayin nan tamkar a cikin horror film. Mama kallon tsohon tayi, taga alamar kamar murmushi a fuskar sa. Tana shirin ta tambaye shi dalili, ƴarta dake kwance bata motsi ta tashi da karfi tana gurnani tamkar karen zangai.

“Me kuma nake yi anan? Me kuma kake nema gare ni?”

Zahara ta tambaya amma tsohon yasan ba ita bace Amriya ce.

Mama baya tayi kamar zata fadi ganin idanun Zahara sun koma bakikirin. Duk tsikar jikin ta ta tashi, tsoro ya ƙara jigar ta ganin kusan siffar ƴarta duk ta canja.

“Me ka aikata min mugun tsoho, ka kunce ni. K cewa wannan munafukan su sake ni in tafi!” Zahara ko ince Amriya ta cewa Mama da take a rude ta kasa gane komai, domin bayan ita, Zahara da Malam Shehu bata ga kowa ba a wurin.

“Ba kina tunanin kin fimu ƙarfi ba. Sai ki nuna mana mu gani.” Cewar Malam Shehu.

Wata mahaukaciyar dariya Amriya tayi kafin tace
“Ni da kai mun san zan iya kai maka farmaki idan ina so a kuma inda nake so. Ba kamar kai ba, ni ba matsoraciya bace, ba zan nemi ɗaruruwan aljanu ba kafin na kama ka. Ni kaɗai na na ishe ka.”

“Ke fah? Baki jin kunyar yiwa bil'adama biyayya? Na ɗauka wayon ki yafi haka.”

“Idan baku sake ni ba, na rantse muku sai kunyi da nasani!!” Ta faɗa tana kubce-kubce da iya ƙarfin ta, amma ta kasa tashi daga durƙushen da take, hannayen ta a bayan ta.

“Ya isa haka Amriya. Zamu kai ki wajen mahaifin ki.”

Da jin haka Amriya tayi shuru, ta nutsu.

“Kada ka sa mahaifi na cikin wannan zancen.” Ta faɗa cikin siga mai sanyi da barazana.

“Zamu kai ki ko kina so ko bakya so.” Tsoho ya bata amsa.

“Ok, me kake so? Zan baka ko me kake so. Kana son duka dukiyar duniyar nan? Zan iya mayar da kai mutumin da yafi kowa kuɗi a duniyar nan. Ko karfin iko kake so? Zan iya maka ko me kake so yanzu yanzun nan. Kawai ka faɗa min abinda kake bukata yanzu muyi magana a nutse. Ka shafa min lafiya, kuma ka daina saka mahaifi na a ciki.”

“Oh yanzu zaki bada haɗin kai kenan? Bana son komai cikin abinda kika zayyana. Ina son ganin an hukunta ki kan abubuwan da kika aikata.”

“Oh duk kana wannan haushin ne, saboda ƴar ɓarnar da nayi kauyen ku? Come on nasan kafi haka, mu manta da komai.”

“Hakan sauki gare shi a wajen ki, dan baki da wanda kike so da gaskiya...”

“ƘARYA KAKE!” Cewar Amriya cike da karaji, har da yayi silar barbajewar gashin Zahara kan fuskar ta. Duk wannan laifin ku ne, kun raba ni da abinda nafi ƙauna a duniyar nan. Duk ku ne silar duk abinda ya faru da ku. Ku ne halittu marasa tausayi a doron ƙasa, amma bansan ta yaya kuka zama wanda Allah yafi ƙauna ba. Kun cutar da ni, alhali ni kawai rayuwa nake son yi da shi.”

Mama tuni an fara baro ta a baya, bata gane abinda Amriya ke faɗa. Tambayar kanta take, me wannan mutanen suka aikata mata da har ta zama haka.

Hausa novel

“Kece kika so yin abinda aka hana, duk sai da muka gargaɗe ki amma baki ji ba.”

“Ka yarda da ni, in har ina raye sai na kashe duk wata mace da naci karo da ita kan hanya ta. Sai na sanya ku cikin kunci kamar yanda kuka sanya ni. Kana tunanin na gama da mutanen ƙauyen Na'iya ne? Duk abinda nayi musu soman taɓi ne.”

“Kafin nan zamu kai ki wajen mahaifin ki. Shi zai daidaita miki zama.” Cewar Malam Shehu yana mai kara kusanto inda take.”

“Kuyi duk abinda ma zaku yi...!”

“Ki faɗi duk abinda zaki faɗa Amriya, amma nasan mahaifin ki ne kaɗai zai yi maganin ki domin shi kaɗai kike tsoro.”

“Kuyi ko me zaku yi, tun ranar da mahaifi na ya kore ni tare da jefa min wannan alkaba'in nima na manta da shi.”

“Ah kenan ba shaci faɗi bane? da gaske ba zaki iya shiga jikin namiji ba?”

“Hakan ba zai hana ni na wargaza su yanda suka cancanta ba. Idan ka shafa min lafiya, zan baka labarin duk abinda ya faru kuma zaka gane abokan ka aljanu ƙarya suka yi maka kan labari na.”

“Bana bukatar ji, domin kowa yasan labarin.”

“Kayi kwance kan ƙaryar da aljanu da kuma munafukan bil'adaman nan suke yaɗawa ne? Ka bani mamaki. Na ɗauka kai abokin gaba ne wanda ya kai. Ashe nayi kuskure.” Cewar Amriya.

Malam Shehu ida ƙarasowa inda Zahara take yayi, sannan ya damki gashin kanta amma Amriya ce taji zafi. Duk hakan yana faruwa ne kan idanun Mama ne da bata kuskura ko kalma ɗaya na abinda suke cewa ba. A kiɗime take sosai ganin abinda ke faruwa kan idanun ta. Irin wannan abubuwan tana ganin su kaɗai a cikin TV da fina-finai ne, a da bata yarda ba amma yanzu taga zahiri...

“Koma dai meye zaki fita daga jikin yarinyar nan da son ranki ko ta karfi.”

“Labari na da ya faru lokacin da kana ɗan ƙanƙanin ka, shine zaka ce min kasan komai. Wai a wa kake ɗaukar kanka ne?” Cewar Amriya tana dariya.

Haushi ne ya kama Malam Shehu. Ba tun yau ba yasan Amriya ta rena shi. Kuma hakan ne take yi idan tana son hassala shi. Amma ba zai barta ta tsira ba wannan karon. Cigaba yayi da aikin fitar da ita daga jikin Zahara.

“Ayyarubo ramataniya sasiban kuki kinaka kuna kiban...”

Ya cigaba da faɗin kalaman nan yana kewaya ta. Amriya da da farko ta nutsu, ta shiga ihun wahala tana murkususu. Ihun mai ƙarfi ta yanda har yasa Mama ta toshe kunnuwan ta da iya ƙarfin ta.

“Zan kashe ka, ka daina...banzan tsoho kawai..” Amriya ke cewa da iya wahalar ta.

Shi kuwa tsoho ya cigaba da faɗar kalaman sa.

“KAYI SHURU, KAYI SHURU...zan fita...zan fita.”

“Zaki fita?” Malam Shehu ya tambaye ta yana cigaba da zuba mata ruwan dake cikin kwalbar hannun sa.

“Eh, zan fita amma ba zan bika wajen mahaifi na ba.”

“Ayyarubo ramataniya sasiban kuki kinaka kuna kiban...”
Malam Shehu ya cigaba da faɗa, yana kewayar ta.

“A'A. A'A ZAN FITA, ZAN FITA AMMA BA ZAN JE WAJEN MAHAIFI NA BA... IDAN NAJE ZAI KASHE NI...ZAN RASA DUK ƘARFI NA.. KUMA BA ZAN TAƁA YAFE MAKA BA. ZAN ƊAUKI FANSA TA GA DANGIN KA DA KUMA ABOKAN KA ALJANU.”

“Barazana kike min?” Malam Shehu ya tambaye ta.

“Gargaɗin ka kawai nake.” Amriya ta faɗa tana haki kamar wacce taci uban gudu.

“Wannan yarinyar bata yi miki komai ba, baki da yancin shiga jikin ta. Har ki gallazawa rayuwar ta.”

“Ka min shuru, ka yi abinda ya shafe ka. Na shiga jikin ta saboda tana burge ni. Ina yin abinda raina yake so ne.” Cewar Amriya.

“Ayyarubo ramataniya sasiban kuki kinaka kuna kiban..”

“Na faɗa zan fita...”

“Ayyarubo ramataniya sasiban kuki kinaka kuna kiban...Ayyarubo ramataniya sasiban kuki kinaka kuna kiban, Ayyarubo ramataniya sasiban kuki kinaka kuna kiba,Ayyarubo ramataniya sasiban kuki kinaka kuna kiba..!”

Ihu Amriya ta saka na wahala, tana kuka ba ƙaƙƙautawa. Mama tambayar kanta take, meye ma'anar wannan kalmomin kuma me yasa suke cutar da aljanar.

“Ya isa, zan fita wannan karon...Zan fita.” Ta faɗa cikin kuka. “Kawai ka faɗawa aljanun ka da su rabu da ni. Ka ce musu su daina taɓa ni.”

“Zasu sake ki, idan mun je kan babban dutsen ƙauyen Na'iya wajen mahaifin ki.”

“Toh kace musu su sassauta ɗaurin da suka yi min. Dan zafi nake ji.”

“Zasu yi idan kika fita daga jikin yarinyar nan.”

Shuru tayi na kamar mintuna goma, kamar tana bacci. Malam Shehu bai ce komai ba, yana jira. Ita kuwa Mama tunani take ko dagaske zata fita daga jikin Zahara ganin irin taurin kan dake gare ta...

Murƙususun wahala Zahara ta shiga yi, tana fizge-fizge na tsawon wasu yan mintuna kafin ta faɗi kwance.

Juyawa Malam Shehu gun Mama da hankalin ta yake a tashe. Cikin sigar tabbaci yace mata. Komai yazo karshe. Ta fita daga jikin ta.

Kusa da jakar shi ya tafi, ya buɗa ya ɗauko wata laya. Yaje inda Zahara take kwance bata motsi, ya ɗaura mata a hannun dama.

“Ko me zata yi kar ta yarda ta cire wannan layar. Zan je na mayar da Amriya wajen baban ta, amma bansan me zai faru ba daga nan. Zamu iya dawowa, amma da wannan layar, ba zata ƙara shiga jikin ƴarki ba.” Cewar Malam Shehu kafin ya juya.

“Kuje muje...!” Ya faɗa cikin ɗaga sauti kafin wani iska ya ɗauke shi suyi sama su ɓace.

---------------------------------------------
See you next chapter Insha Allahu🤞
[03/03 à 05:18] ASHTAR: AMRIYA
(Hatsabibiyar Aljana)

Love 💞 and Horror ☠️ story 📖

By Malik al-Ashtar 🖋

On wattpad : https://www.wattpad.com/story/270492485

Table of Contents

Chapters

36 chapters
  1. 1 Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
  2. 2 CHAPTER 1
  3. 3 CHAPTER 2
  4. 4 CHAPTER 3
  5. 5 CHAPTER 4
  6. 6 CHAPTER 5
  7. 7 CHAPTER 6
  8. 8 CHAPTER 7
  9. 9 CHAPTER 8
  10. 10 CHAPTER 9
  11. 11 CHAPTER 10
  12. 12 CHAPTER 11
  13. 13 CHAPTER 12
  14. 14 CHAPTER 13
  15. 15 CHAPTER 14
  16. 16 CHAPTER 16
  17. 17 CHAPTER 15
  18. 18 CHAPTER 17
  19. 19 CHAPTER 18
  20. 20 CHAPTER 19
  21. 21 CHAPTER 20
  22. 22 CHAPTER 21
  23. 23 CHAPTER 22
  24. 24 CHAPTER 24
  25. 25 CHAPTER 23
  26. 26 CHAPTER 25
  27. 27 CHAPTER 26
  28. 28 CHAPTER 27
  29. 29 CHAPTER 28
  30. 30 CHAPTER 29
  31. 31 CHAPTER 30
  32. 32 CHAPTER 31
  33. 33 CHAPTER 32
  34. 34 CHAPTER 33
  35. 35 CHAPTER 34
  36. 36 CHAPTER 35
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});