Chapter 19
Chapter 19
gwada Mata kamar zoben abban su Ta Dade tana juya zoben A hannun ta to Amma me zai kawo zoben Abba a dakinta kuma kasan gadon ta? Dauke shi tayi ta boyeshi cikin kayan ta taci gaba da aikin ta da zummar in anjima zata tambayi abban Ina zoben shi in nashin ne to in ba nashi bane ta samu taci Gaba da harkokin ta ******************* Abdul ahad Dane ga alh bilya bello Yaya ga tahseenah ba laifi yaro ne Mai hankali ga son Yan uwa , akwai soyayya da shaquwa sosai a tsakanin su Abokinshi d"aya muheeb' class mate din shi ne sai dai ba unguwar su d"aya ba kokarin su yazo daya shiyasa suka kulla abota Mai karfi ***************** Cikin d'an kankanin lokaci umayma ta fand'are ta gagari kowa watarana ma bata kwana gida sageer Kam ya maida ta kamar matar shi gefe guda Kuma hankalin fateema kwance Dan bokansu ya samo mata Kan sageer son ta yake kamar ya mutu burin ta ya cika umayma ta lalace dan Yanzun ma sun raba jaha Dan sageer ya rqbasu a cewarshi kada umayma ta b'ata mishi fateemar shi Sai dai duk wannan abun da ake fateema tasan dai umayma ta watse amma bata san suna tare da sageer ba itama umaymar batasan cewa sageer Yana tare da fateema ba har anfara zancen aure Ba" Iyayen ta sun daka sun zaga sunyi fada kai har da rarrashi an had'a Mata Amma abun sai du'a'I Mahaifin ta har ciwo ya kwanta'Sabida baqinciki gidansu yasha kwana a bude sabida ita Kwatsam bata an Kare ba sai ga ciki ya bullo Mata ajikin ta Wai Allah ranar taga tashin hankali" ranar domin ranar da cikin ya bayyana a gidan su ranar baban ta ya tsine mata ya kuma koreta haka ya dinga wullo mata kayan ta Yana kuka yana zagin ta haka yadinga dukan ta yana jefa mata duk kqlmar da taxo bakin shi a lokacin ne jikinta ya fara sanyi taji wata nadama ta fara shiigar ta" Wata zuciyar ce ta kuma ingiza ta ta kakkabe jikinta ta tsinci abinda take buqata cikin kayan ta ta qara gaba Yan unguwar su na ta tsine mata da kalamai marasa dadi Mahaifiyar ta kuwa duk wannan budirin da ake tana can a some ana kwara mata ruwa Cikin qunar zuciya da baqinciki yazo shigowa gidan bayan tafiar umayma yana share kwalla kafarshi d"aya ta shigo ciki ya yanke jiki ya fad'i a take a gun bakin shi ya karkace Gefen fuskar shi ya kumbure wasu mutane ne da duk abinda ya faru a gaban idon su har shigowar shi cikin gidan da fad"uwar da yayi da sauri sukazo suka kamashi suka kaishi cikin sitting room dinshi ana ta mishi fita Ta d'anyi y'ar tafia kad'an ta Kira wani sabon dadiron ta tamishi kwatan cen inda take yazo ya dauke ta Suka Kara Gaba wata irin iskar yanci take ji Tana shigar ta __________________ Abincin dare suke ci kamar yanda suka saba sunaci suna y'ar fira jefi jefi a hankali ta ke kallon yatsun abban tabbas wannan zoben zoben abban ne dan zobuna uku ne a yatsun shi amma bari ta tambayeshi taji dai...... Comment Share 08038541511 [1/25, 9:18 AM] Zahrahbukar: *KARSHEN DUNIYA* _kalubalenku Iyaye_ *na* *Zahrabukar* *exquisite WRITTERS forum* *masu himma tuni sun fara subscription kui maza ku hanzarta fa kar ayi baku Tafiyar Mai tsawo ce Akwai rikita rikita da bankade bankade cin amana daukar fansa Mai zafi yaudara zamba cikin aminci kawata matso kusa da yan kudinki kalilan ki kwashi garabasar wannan daddad'an labarin* Normal group #300 VIP #500 special #600 _duk tsarin da kike bukatarku zaki samu Akwai banbanci yawan posting a kowacce rana akan kowanne tsari_ ki biya yan sulallan ki ta wannan account number din *6035968908 keystone bank umma yusif* Sai ki Turomin shaidar biya akan wannan number din 08038541511 *23* D'an dago kanta tayi a hankali ta Kalli Abban tace "wai Nikam Abba ina wannan zoben? Wanna duk yafisu kyau wallahi Kuma naga ka cire shi" ta karasa maganar Tana dubanshi ido cikin ido cikin daburcewa ya Ke kallonta ya matsayin kusa kwarewa da lomar chips din da yakai bakinshi, domin shima ya nemi zoben bai ganshi sai daga baya ya yi tunanin qilan fa a ranar da ya haike wa tahseenah ya fad'i a dakinta domin yana hannun shi har yaje dakin, Cikin sauri ya d"ago kai Yana in Ina yace "zo zobe na Kuma? Gaskia nima neman shi nake Ko kin ganshi ne?" Ta kula tsaf da yanayin da ya shiga sai ta basar tace " ah ah abba bangan shi ba zoben yana da kyau ne naga kamar kadaina sa shi ne bayan Kuma duk yafi sauran kyau" "Ah ah Ina tunanin dai kilan ya fad'i" "haba dai ya za ace zobe ya fad'I daga hannun ka baka da labari kilan dai ka fidda shi ka manta inda ka ajje shi" Cewar umma Abdul yace "Allah abba zoben na da kyau dama in tsince shi" Dariyar yake yayi yace "Ina zaka ganshi Nima neman shi nake" Azeema zatai magna yace "Kai kowa yayi shiru yaci gaba da cin abincin shi" ******************* Tafia Mai d'an tsayi sukayi sannan ya tsaida motar yace "kinyi shiru tunda muka baro unguwar ku Baki ce komai ba Ina muka nufa? Ga jikin ki duk alamun duka me ke faruwa ne?" Murmushie ta saki tace "ba damuwar ka bace bani da zabi muje kawaii Amma Fara kaini asibityn ko chemists a dan yo mun treating din ciwukan sai muje restaurant muyi take away sai muje duk in da ranka ya maka" ta kwanta jikin sit din motar Tana lumshe idanu wani irin yanayi na kewa da bakinciki Ke kokowa acikin ranta Tana kokarin Yaki da kewar domin itace zata Hana ta rawar gaban hantsi batajin cewa Akwai abinda zaisa ta Kuma tunawa da sunan unguwarsu ma bare gidansu daga Yau tashafe komai da yadangaci tarihinta zata kafu zata kafa kanta komai rintsi tada motar yayi suka tafi ********************** A gajiye ya shigo gidan da sallama hannun shi rike da baqar laida Amsa sallamar tayi ta karbi ledar Takai kitchen Ruwan wanka takai mishi ta zuba ruwan alwala a buta sannan ta shiga dakin ta mishi Sannu da zuwa sannan tasanar mishi GA ruwan wanka cen Ta iske har ya hunce ya na Shirin fitowa ma tare suka fito Bai kaiga shiga bandakin ba sukaji sallama Da sauri ya fad'a ciki Jin muryar mahaifiyar shi gashi da gashi sai boxer's Tabarma humayda ta shimfida mata ta zauna tana ta faman Harare Harare cikin girmama wa ta duka ta gaida ta A d'age ta amsa sannan tace "ina shi isashshen yake tunsafe bai leka mu ba har magriba ta kawo jiki to ni na biyo Shi Yana Nan ya nanike miki duk wani neman da tattalin shi Akan ki yake juyeshi ke ba haihuwa kike ba sai dai aci a kasayar" Zata ci gaba kenan ya fito Dan duk abinda take fad'a Yana jin ta yanda take daga mutual har sauri yake ya fito Dan yasan humaydar nacan a Duke tana kuka Dan haka ke faruwa duk sanda babar tazo gidan duk abinda zata fad'a Bata d'aga Kai ta kalle ta ko ta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27