Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 4

Chapter 4

Mabaraciya Book 2 Complete Hausa Novel 1,182 words 0 views Progress saved
Download Book

na a waya ,nayi kuka har na gaji daga karshe dole na saduda domin danaki yarda da ita takaini gun wasu kattin maza kallon su kawai yana haifar maka da rudani tace" gani nan bata son su tausayimin ai inaganin haka babu shiri nace na amince da bukatun ta ,tunda ga lokacin haka take kwanciya nice nake komai ,gata macece mai yawan sha'awa ,tun ban saba ba har yazamana idan ma bata nemeni ba haka zanyita matar kafafu ,cikin lokaci se gashi nima na Kware sosai a harkar ,duk wacce ta dauko tana anfani da itane nadan lokaci daga bisani se ta rika hada kawayenta dasu suna bata kudi tana da matsanan cin kishi shiyasa indai har tafara bawa kawayenta ke to daga ranar bazata sake mu'amala dake ba ,tamayar dake business machine sedai suzo ta turaki abata kudi ,wani lokacin ma har maza irin manyan 'yan siyasa idan tana Neman wani Abu bata samu ba setayi musu shu'umanci tahanyar basu mata suna anfani dasu ni da kike gani tace bata taba zama da yarinya tadade da ita kamata ba ,a cewarta na Kware sosai a harkar yanzu ma so take nima ta yayeni domin mutane da yawa suna nuna suna bukata na ,amma taki basu fuska ,wannan shine labarina saboda haka nake baku shawara da kuma kuyi hakuri kawai kuyi biyayya dukan su rasa me zasuce sukayi lallai rashin imanin matar yawuce tunanin mai tunani ,dayar ce tayi karfin halin cewa "to ita batada aure ne? Murmushi binta tayi tace " ya sunanki ta tambayi yarinyar "sunana Maryam tabata amsa " to kisani tanada aure harda ma 'yaya yaranta 2 duka mata dayar tayi aure dayar ce yanzu ba'anan take karatu ba kuma duk abun Hajia mutane girmamata sukeyi domin tana da kirki ga jama'a ga yawan kyauta ,mijinta ba mazauni bane amma idan yana gari to takan kai masa xiyara duk da bawai yana gabanta bane . Tunda sukaji wannan labarin na Hajia se jikinsu yayi sanyi lallai basuda wani mahita da yawuce su mika wuya a gareta ,sedai zasu mika lamuransu ga Allah domin shine buwayayyen sarki sarkin da baya kwana kuma bayada fadawa shine Wanda ze tseratar dasu yakuma basu mafita "kunyi shiru maganar Binta ya katse musu tunani Murmushin takaici Maryam tayi tace " aunty muna kai kukan mu ga ubangiji ne ,Wanda muka kiyiwa Hajia biyaya saboda tsoron azabarsa sarkin da yaharamta zalunci a tsakanin mu ,yahane mu da alfahasha ,natabbata baze bar rayuwar mu ta tafi haka ba ,kifadamana tsarin Hajia zamuyi mata biyayya domin mu a yanzu kamar bayine a gareta ,se abunda takeso zamuyi Murmushi Binta tayi ,tabbas yarinyar tabata tausayi amma dai tasan ko ta halin yane dole yau da gobe wanann takawar da take nunawa zebar zuciyarta ,pointing din 'dayar tayi tace "ita wannan ko kurma ce har yanzu banji maganar ta ba " karki damu sunan ta Nusaiba itadin 'yar kanin babana ne itace yayata ,haka take bamai yawan magana ba ,na tabba ta yanzu halin da muke cikine yasake taba zuciyar ta Maryam tafada tana kallon Nusaiba " shikenan dai ni shawarar da zan Baku kawai kuyi abunda Hajia ke bukata ,yanzu zaku iya biyoni mutafi gunta domin tabbatar mata da aikinta ya kammala "Wai ke Ameerah se yaushe ne zaki cire damuwa da tunani cikin ranki ,I have staying almost 30 minuts ,but yuh don't even know ,let gone by gone yuh have to face ur future pls ,banajin dadin ganin yanda kike a cikin damuwar nan why? Fashewa Meerah tayi da kuka ,cikin murya irin na waanda yake cikin kunci tace " aunty have yuh see what i seen ?do yuh know how aunty Maryam did her life with that prostitute women ,she's destroyed her life all for my on life ,only me know how im feel Cikin sanyi jiki Aunty tace "who told yuh all this? jefa mata wani book dake hannun ta tayi tace " take it you will understand, kurawa littafin ido aunty tayi ,at the top up the cover book anrubuta ,its confidential ,mi'kawa Meerah tayi tace "me yasa kika karanta bayan Maryam batason kowa ya gani? " My heart tabata amsa , tareda kara fadin "na dade idanuna suna kallon wanann book din zuciyata nagayamin na duba amma danaga ,warning dinta se naji na ga gara saboda banaso ko bayan ranta ace nasaba wa umurinin ta ,ashe mafita ne zan samu yanzu kam nasamu hanyar da zan tunkari Saudah ,nasamu hanyar da zanbi nasamu kusanci da ita ashe da can duk hauka nakeyi ,a lokacin ma da nasamu ganinta ba lallai nayi nasara ba ,amma yanzu zan jure komai Zan yaudareta ta hanyar da take yaudarar iyayen yara sun yarda da ita ,xan zambaceta kamar yanda take zambatar mutane suna yimata kallon mutuniyar kirki ,tabbas ba yanzu yakamata na shiga gidanta ba ,aunty takira sunanta tare da kallonta ,cikeda mamakin Meerah tace " inajinki " kudi nake nema sedai bansan ta ina zan fara ba mafita 'dayace wadda zanyi anfani da ita ,badan raina yaso ba ,zankarya maganar yayata karo na biyu tabbas zanshiga gidan Alh Yusuf a matsayin mabaraciya ,daganan zannemi aikatau ,sedai matsalar 'dayace ta ina zan fara gidan da baabarin kowa ya shiga ,shiru tayi kamar mai tunanin wani Abu sekuma tafada 'dakinta da gudu, itadai aunty da kallon mamaki tabita ,tana nan tsaye a inda tabarta ,Ameerah tazo ta wuceta ,da sauri tafara kiranta tare da tambayar ina zata je amma ina ko waigowa batayi ba ..... $Mutum ze iya karantamin labarin amma following ne bazeyi ba ,to na haramta hakan don Allah idan kinsan bazakiyi following dina ba karki karanta wanann kawai na my followers ne Follow me on wattpad@damselfeedo #Rael@Bazamfaria *INTELLIGENT* *WRITER'S* *ASSOCIATION* ( *On* *word* *together* ) *MABARACIYA* *Story* *and* *writing* *By* *FIDDAUSI* *SANI* (damsel feedorh) 🅿️:7️⃣ ,,,,,,,,Har kofar gida aunty tabiyota sedai koda ta fito ko inuwar Meerah bata ganiba ,haka tadawo cikin gidan jiki babu kwari tare da addu'ah Allah yatsareta Meerah kam bata tsaya ko ina ba se gidan wata kawarta tafiya tayi sosai a kafa amma kasancewar kamar ba'a hayyacinta take ba shiyasa bata ji nisan ba ,abakin get din gidan ta tsaya tana karewa gidan kallo ,rayuwar ta tabaya ta tuna kafin iyayensu su rasu take taji wani kwallah ya zubo mata ,knocking tayi ,mai gadi ya leko "sannu baba dan Allah Fatima tana nan? Seda yakare mata kallo tukuna yace " ehhh amma waza'a ce mata tazo wurinta " kace mata Ameerah Almustapha ,koma yayi babu dadewa segashi ya dawo ya bude mata kofar ta shiga ,direct main house din ta nufa kasancewar tasaba zuwa gidan kafin rayuwa ta sauya mata ,tana shiga falon taji anyi hugging dinta so tight ko ba'a fada ba tasan Fatima ce ,dariya tayi tace "ashe baki manta da niba tafada tana Jan hannunta suka karasa kun kujerun falon. Zama sukayi cike da jin dadin ganin ta Fatima tace " nayi zaton shikenan bazan sake ganin ki a idona ba Meerah where all this have you been? " Labari ne mai tsawo kedai bani ruwa nasha tashi Fatima tayi tana fadin " yi hakuri murnar ganin ki ne ya mantar da ni ,juice ta doro tare da ruwa a tire agabanta ta

Table of Contents

Chapters

34 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34