Chapter 27
Chapter 27
tasaka a ranta se ta fara ramewa a tsaitsaye ,wata rana Bilkisu tazo gidan ,taga halin da Ammi ke ciki haka ta tayita bata hakuri tare da nuna mata cewar ,a koda yaushe itama Allah ze iya bata nata wani rabon nesa yake kuma ze iya kasancewa rabon Sauda ne a saman nata ,yanzu ta sanadin haka se taga nata rabon yazo ,haka dai tayi ta rarrashin ta kasancewar zata girme mata a shekaru kuma gaskiya tanason Ammi sosai ,ki ragewa kanki wannan zaman kadaicin duk lokacin da kike cikin kaɗaici ki rungumi Alkur'ani,ya zame miki abokin hira ,na tabbata zaki samu farin ciki " haka dai tayita rarrashin ta ,har seda ta ɗan rage mata damuwa ,sosai Ammi taji daɗin zuwan Bilkisu a gidan Bayan wata tara Saudah ta haifi yarta ,wacce ta ci suna Khadijah ,du da ba haka ta so ba dan ta so ne ta fara haihuwar namiji ,amma dai a hakan ma ta gode dan taga yadda Alh Yusuf keta rawar jiki da samun yar yarta , dan har kyautar kujerar Hajji yayi mata itada dangin ta, komai dai zece Khadija ,,haka suka fara renon ta cikin gata da soyayya ,har yarinya ta yi wayo ,wata rana Bilkisu tazo gidan ,tare da duka yaranta , Mu'aisam shine Babba, se me binsa Ruƙayya da Hafsah itace karama tun daga bakin get suke jiyo hayaniya cikin gidan , da sauri suka karasa ciki ,Saudah suka isko ,se tijara takeyiwa Ammi ga Abba a tsaye yana kallon su yakasa cewa komai ,a cikin kalamanta ne suka fahimci abinda ke faruwa " Alh Yusuf ne yashigo da Khadija bangaren Ammi ,shine da ta shigo ta samu Khadija a hannun Ammi tana ta tsala kuka ,shine take warning akan duk abinda yasamu yarta bazata barwa Allah ba se tayi kara akan me ma ze kawo wa juya yarta salon bakinci yasa ta cutar da ita idan haihuwa banza ne ta haifi nata mana ,ga Alh tsaye amma bece komai ba se Ammi da keta risgar kuka ,a fusace Bilkisu tace " ke Saudah ya isheki haka ,ke kika bawa kanki haihuwar ne da kike tunkaho idan Allah ya gadama itama wannan yar da yabaki se ya amshe abunshi dan ba dan kinfi kowa a wurin sa bane yabaki ita " ai ko wannan fatan mutuwar da Umma tayiwa yarta se takara hauka se zage zage take " ai bansan kema kina bakinci da hakan bane se yanzu to dan Allah idan bata mutu ba ke kixo ki kashe ta se kuma ta fashe da kuka " Alh ka gani ko bansan me nayiwa wannan yar uwar taka ba sam bata ƙaunata gashi yanzu har tanayiwa yata fatan mutuwa to wlh duk abinda ya sameta bazan yarda ba ,cikin fushi Umma ta kira sunan Ammi , Zainabu" ɗagowa tayi da rinannnun idon ta ta dubeta dan bazata iya amsawa ba ,duba nan kigani wa'yannan duka yaƴanane da Allah yabani ,su uku kizaɓi wanda kikeso a ciki wlh na baki har abada ,kuma babu wanda ya isa ya canja hakan ,koda zuwa gaba Allah yabaki naki kuwa ,Allah sarki se Ammi ta sake fashe wa da kuwa ,tace " da gaske kikeyi zaki bani Mu'aisam? Shi kike so? Itama Umma ta tambayeta " daga mata kai Ammi tayi ,dan haka Umma ta kama hannun Mu'aisam takaishi har jikin Ammi tace " daga yau yazama danki ,nabaki shi har gaban abada ,kizo ki ɗauki kayan sa " tana gama faɗa ta kada kan yan matan ta tayi gaba batare da ko kallon ɗan uwan nata ta yi ba Tun da ga wannan lokacin Mu'aisam ya dawo hannun Ammi wanda shine yafara kiranta da sunan Ammina sosai take son sa a zuciyarta bata taɓa jin ba ita ce ta haife sa ba ,duk wata kulawa da gata tana bashi lokacin shekarar sa 9 a duniya ,se Ammi ta nemi kunci rashin haihuwa ta rasa a xuciyar ta , dan duk wata irin soyayya da jin ƙai da ake samu a tsakanin uwa da da ta sameshi a tsakanin ta da Mu'aisam ,wannan kyautar da Aka yiwa Ammi sosai ta taɓa Saudah dan ita ba haka ta so ba ,taso ne kullum ta tabbata a cikin kunci. Shekarar khadija 5 da haihuwa amma shiru kakeji babu wani labari a wurin Saudah aiko se ta tayar da rigima wai Ammi ce tayi mata asiri dan ganin ita bata haihuwa ,shine ta hana ita ma ta haihu ,haka ta tsarawa Alh ƙarya da gaskiya wai har cikin baccin ta take ganin Ammi tazo mata ,shikuma ya yarda ,haka ya samu Ammi cikin fushi yace " wannan abun da kikayi ai ba Sauda kikayi wa ba nine kikeyiwa baƙin cikin kar na samu ƙaruwa saboda ɓaƙin halinki " rasa inda kalaman sa suka dosa ne yasaka ta tambayar " Alh me yake faruwa kuma? Ehhh dole zaki tambaya tunda ke baki haihu ba kuma na auro wacce take haihuwa ,shine kike bimin ta bayan ka tanga ,kuma wlh bazan lamunci haka ba idan ma wani abun kikayi dan kar Saudah ta sake haihuwa to ki kwance ahto " yana gama faɗar hakan yafita rai bace,wannan ranar kam Ammi tayi kukan da bata taɓa yin sa ba , Mu'aisam shima haka ya zauna yana tayata kukan dan a lokacin yanada 15 years ,saboda haka duk wani rashin a dalcin da ake yiwa Amminsa yasani, shiyasa sam baya sararawa Saudah dan ko gaishe ta bayayi ,ita dinma banda harara babu abinda ke haɗa ta dashi ,se wani lokacin takance shege ɗan cin dukiya ai inasane ba'a banza uwarka tayi kyautar ka ba ,dubarane takawo ka ne domin kaci arziƙi karage musu ɗawainiya "arziƙi kowa ma zaman cin sa yake yi kema shi kika gani kika biyo" ire-iren amsar da yake bata kenan duk sadda xatayi masa gori dan shi sam baya shakkar ta ,ga haushin ta da yakeji ko yaushe gida cike da mata ƴan uwanta kamar yadda take faɗa. Tun daga lokacin Abba ya canja Ammi sam baya kulata dan jin haushin abinda yake tunanin tayi masa ,cikin ikon Allah se ga wani cikin Hajia Sauda ta samu ,aiko duk se ta maida hankalin ta akan fafutikar son haihuwar namiji , sedai Allah bayada dole da ta tashi haihuwa se ta sake haihuwar macen ,taci suna Rufaidah ,tayi bakin ciki sosai dukda yarinyar kyakkawa ce hakan ne ya ɗan dallashe mata zafin rashin haihuwar Namijin ,watan Rufaidah 7 a duniya Allah yabawa Ammi ciki , sedai ita kanta bata san dashi ba ,har se da ciki yakai 5 months,dan da farko tana period dinta har yakai 3 months shiyasa ma bata gane komai ba se kwanakin nan da taɗan farajin sauyi da kuma motsi a cikin ta ,a tunanin ta ko macijin cikine saboda haka ta shirya taje asibiti sedai gwajin farko aka gano tana ɗauke da ciki ,ai lokacin da likitan ya faɗa mata faɗuwa tayi tana sujjada ga ubangiji ,dan ta san shine majiɓincin al'amuran ta ,kuma shine ya ji tausayin ta ,bata dawo gida ba seda tayi scaning aka tabbatar mata da watan cikin 5 a jikin ta daganan gidan Umma ta wuce ,tun a bakin get take kwalawa Umma kira " a firgice ta fito
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34