Chapter 3
Chapter 3
nace a karbo min?" Basu ji amsar da Amman ta bayar ba sai muryarsa da ta sake dagawo wajen kiran Aminu. "Aminu! Yana gidan nan?" "Na shiga uku.." Cewar Aminun, kuma Amina na kallon sanda Maryam ta murmusa a sallarta don daɗi. "Baba sannu da zuwa, wani abu ne ya faru ka dawo yanzu?" Ta tsinci muryarsa da yayi sauri ya tsugunna yana shafa kai ganin ya fito. "Ni da gidana don na dawo sai ka tambaye ni me nazo yi? Ina kayan da nace ka karbo min?" "To, to, bari aje a karbo." Ya fada kamar sai a lokacin yace 'je ka karbo din,' kuma bai jira ya sake cewa komai ba ya kama hannun Hafsa da ta gama shiryawa suka yi waje. Alhaji Sulaiman ya girgiza kansa kawai saboda takaici sannan ya kalli Amma dake tsaye a gefensa. "Hajiya Kilishi ce yanzun nan ta kira ni tace tana son ganina." Daga cikin ɗakin Amina zata rantse daga ita har Amman a lokaci guda suka yi murmushi. Hajiya Kilishi ƴaruwar Baba ce, mace ce mai kirki da son kyautatawa, ta taka muhimmiyar rawa a rayuwarsu ta kowanne fanni, tun kafin Mahaifinsu ya rasa arziƙinsa har bayan komai ya cakuɗe musu, don hatta kuɗin rubuta jarabawarta ta fita daga secondary ita ta tallafa aka biya, babban taimakon da tayi musu na kwanan nan shine lokacin da Maryam ta kamu da rashin lafiyar ciwon ciki, wanda daga ita har su kowa ya wahala kafin a gano cewar wani ƙari ne ke fito mata a gefen cikin kuma yayi girman da har sai an cire shi. A wannan lokacin komai nasu ya riga ya ƙare wajen jinya, don hatta abinci sai daga gidan wan Baban ake kawo musu kullum ko tukunya basa dorawa, ɗan abinda Baba ya samu da kuma na wajen Amman daga ƴan sana'o'in da take yi duk a asibitin suke karewa. Don haka a dole Baban ya shiga neman bashi ƙofa-ƙofa, ƴanuwansa suka hada masa iya abinda zasu iya amma ko kwata ba'a shafe na lissafin ba, Hajiya Kilishi ita taji labari a danginsu, ta kira Baban har gida ta bashi tallafin naira dubu ɗari uku, kuɗin aikin har da ɗoriya akai, tun daga wannan lokacin zuciyoyinsu suka kara girman darajarta a wajensu. Mijin ta wani babban mai kuɗi ne kuma sanannen mutum ne, itace matarsa ta biyu kuma ƴaƴan ta biyar dukkaninsu mata, amma ance saboda zaman amanar da suke yi da uwargidanta babban ɗanta ma a wajen Hajiya Kilishin ya tashi tun yana yaro ta yadda ba kowa ne ya san cewa ba itace ta haife shi ba, Baba yasha gaya musu cewar ko gidan yaje baya iya banbance ƴaƴan ta dana uwargidan. "Shinkafa da wake kuka yi? A zubo min dan Allah kafin yaron nan ya dawo." Muryan Baban ta katse tunanin Amina daidai lokacin da Maryam a gefenta ta idar daga sallah, ta sake kallonsa ta cikin labulen sanda da yake cewa. "Allah yasa Amina ta daka yajin nan nata mai daɗi." A lokaci guda murmushi ya suɓuce a fuskarta, sai kawai ta mike tana faɗin. "Akwai Baba, Bari in kawo maka." *** Royal Brompton Hospital. Sydney St, London SW3 6NP, United Kingdom. ...So I took your hand, back through lamp-lit streets, I knew, Everything led back to you So can you see the stars over Amsterdam? You're the song my heart is beating to... Waƙar a hankali take fitowa daga cikin labtop ɗin dake ajiye a wani ɗan ƙaramin tebur da kujerarsa dake can jikin dogon windon ɗakin, ɗakin asibiti ne da banda gadon mara lafiyar da kuma tarin computers ɗin gefe dake auna lafiyar wanda ke kwance, babu komai sai wata drawer daga can gefe wadda aka yi mata ado har da wasu ƴan fulawoyi, ɗakin a gyare yake tas yana kuma ƙamshi mai daɗi, ga room heater dake fitar da wani ɗumi mai daɗi sakamokon sanyin ƙanƙarar snow ɗin dake zuba daga waje. A hankali idanun mara lafiyar dake kwance akan gadon suka buɗe, kuma duk da lumshewar su girman su ya fito a lokaci guda, matashi ne mai siririyar fuska, yana da yalwar gashin kai da kuma na gira kamar yadda na idanunsa suke dogwaye ta yadda idan ka kalle shi zaka ga kamar baya iya buɗe idanun nasa ne sosai. Ya ɗago da hannunsa dake maƙale da allurar ruwan drip ɗin gefe, ya kalli hannun tsawon wasu sakanni kafin yasa ɗaya hannun nasa ya murza goshinsa alamun takaici, sannan a lokaci guda ya fizge drip ɗin daga jikinsa ya mike zaune, jini ya shiga fitowa daga inda allurar ta fita amma bai ko bi ta kai ba ya kalli rigar dake jikinsa, rigar asibitin ce wadda ake bawa kowanne mara lafiya. Ya shiga ƙarewa ɗakin kallo a hankali har zuwa kan drawer dake can gefe, a lokaci guda ƙwaƙwalwarsa ta tuna masa da jakar da Ishaq ya ajiye a ciki jiya don haka ya mike tsaye, jiri ya so ɗaukarsa amma ya dage ya tsaya akan ƙafafunsa sannan ya isa ga drawer. Ya buɗe ciki ya fito da wata baƙar jaka ya shiga fito da kayan ciki, ƙamshin turarensa na 'Dior Sauvage' shi ya tabbatar masa da cewar kayansa ne tun kafin ma ya gane su, kala biyu ne sai kuma wata ƙatuwar rigar sanyi wadda ke zuwa har gwiwa, bai yi tunanin komai ba ya shiga canjawa zuwa kayan, sai da yazo ɓalle maɓallan rigar saman sannan ya kula da jinin dake fita daga hannunsa. Don haka ya saka rigar asibitin da ya cire ya goge sannan ya ɗora daya rigar, ya kuma jawo rigar sanyin ya dora akai, bai ko ɗauke rigar asibitin dake kasa ba ya saita facing Cap ɗin da ya ɗauko a ciki daidai fuskarsa sannan ya nufi hanyar kofar ɗakin, ya san duka wayoyinsa basa nan kuma Ishaq bai bar tasa a gefen labtop ɗin ba don haka ya nufi ƙofar ya buɗe, dogon korido ne a wajen mai dauke da kofofin ɗakuna da kuma mutane dake ta wucewa ta cikinsa, ya tabbata babu ma'aikatan da suka san shi a cikin waɗanda ke wucewa don haka kansa tsaye ya bi ta cikin mutanen dake tafiya ya saje, yana mai nufar hanyar waje. Iskar dake kaɗawa a wajen mai tsananin sanyi ta ratsa fuskarsa sanda ya fito daga asibitin gabaɗaya, dare ne lokacin, ga fitulu a koina, na kan titi dana motoci, ga mutane birjik musamman na ƙafa sai faman wucewa suke. Haka ƙofar asibitin take a kullum, tun daga shekarun da ya fara zuwansa har yau. Sanyi ya shiga ratsa kunnuwan sa dake buɗe sannan a lokaci guda yaji wata irin yunwa ta mamaye shi, sai kawai ya saka tafin hannayensa duka biyu ya gefen fuskarsa lokacin da idonsa ya sauka akan sunan wani kanti daga can tsallake, kantin da yake yawan yin siyayya duk lokacin da yazo kasar. "24 dollors." (Dubu goma.) Baturen dake kan kantar ya faɗa a lokacin da ya gama lissafa abubuwan daya ɗebo. Ya kai hannunsa bayan aljihu kamar zai fito da wallet sai kuma ya dawo dashi, ya matso daidai jikin kantar yana kallon mutumin yace. "You know me right?" (Ka san ni ko?) Kallon da mutumin yake masa yasa ya cigaba da cewa. "I used to come
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73