Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 26

Chapter 26

Farar Wuta Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

a jikin burner, a lokacin kuma Samirah ta shigo riƙe da katon tray ɗin dake shaƙe da kayan abincin da ita kadai ta san me ta dafa. Ta ajiye su daga kasa kujerar da ta san nan ne wajen zaman Baffan sannan ta juya. "Bana jin zan fito sai gobe kuma, kar ki daɗe a waje." "To Mami." Cewar Samiran tana saurin fita, sai dai tana isa bakin kofar Hajiya Kilishin ta sake kiranta. "Da gaske nake miki magana, kar ki wuce goma a wajen mutanen nan." Kuma duk da ta amsa ɗin sai da taga yadda ranta ya ɗan ɓaci kafin ta fita. Dole ne ma ta ƙara dagewa wajen kokarin fara ɓanbare tarin abubuwa daga jikinsu, don komai ya kusa ƙarewa, wannan rayuwar ba dahir ɗinsu bace. Fitar ta ke da wuya kuwa taji muryoyi daga wajen suna bin layin gaishe da Baffan da ta hango hasken fitilar motarsa da direba ya sauke shi ta labulen falon. Sai ta taho wajen kofar don ta bude, so take ya fara yin tozali da ita da kuma kwalliyarta kafin wani abu ma na ɗakin. Sai dai kafin ta ƙarasa ɗin wayar hannunta tayi ƙara, ya kalli lambar dake kiran ke shigowa kafin ta dauka, Kuma abin da muryar cikin wayar ta faɗa tun kafin ta kai ga cewa komai, shi yayi sanadin da zuciyarta ta doka a cikin ƙirjinta sannan wayar ta zame daga cikin hannayenta ta faɗi kasa ta tarwatse! *** Hasken safiyar ya shigo ta tsakanin fararen labulen ɗakin yana ratsowa har ciki zuwa kan gadon da shima komai a jikinsa fari ne, Rukayya ta motsa a cikin baccinta tana ƙara binne kanta a cikin filon amma tasirin wasu dogwayen yatsu dake shiga cikin gashinta suka hana baccin nata cigaba. "J dan Allah mana.." Muryarta ta fito a can kasan numfashinta. Jawad ɗin dake tsugunne a gaban gadon sanye da singlet fara ƙal da kuma wandon gogaggiyar shaddar daya sanya bayan ya fito daga wanka ya sake motsa yatsun nasa cikin gashinta yana matso da fuskarsa kusa da ita. "Na gaya miki ina da meeting by 10 a Abuja, ko so kike in tafi in barki anan?" Bata bude idanunta ba tace. "And what time is it now? (Kuma yanzu karfe nawa?) "Eight tana dab da ƙarasawa, kamar yadda zuciyata take dab da shirin fashewa akanki." Bata san lokacin da tayi dariya ba sannan ta bude idonta akansa. "Sai yaushe zaka dawo?" "Sai nayi kwanakin da kika yi Paris." Ta juya idanunta tana jin yadda yatsun nasa ke ƙara shiga cikin gashinta. "Ka san bani da matsala ko zaka ninka kwanakin ne." Ya gyada kansa a hankali. "Na sani Barbie, na san ni zan haukace..." Sai kuma yayi shiru yana kallon kyawawan idanunta yayin da itama tayi shirun tana sauraren yadda sautin numfashinsa ke fitowa akan fuskarta. "You never know what I went through da bakya nan Rukayya, zan iya tsayawa a gaban ko waye in faɗa miki ke daban ce." Ta lumshe idanuwan nata tana murmushi, tana da tarin hujjojin da zata yarda cewar dukkan maganganun Jawad akanta gaskiya ne, yana ƙaunarta ne da gaske, sai dai maganganun basa taba ƙarasawa har cikin zuciyarta don bata so ya tsallake huruminsa, tafi so ya tsaya a iya matsayin da tsananin kulawarsa gare ta da kuma matsayinsa na ɗan gidan minister da mahaifiyarta ke kwaɗayi yasa ta bashi kawai. Amma akwai wajajen da duk yadda ta kai ga jin sa a zuciyarsa bai isa ya tsallaka ba, Ma'aruf ne kadai mai wannan ikon akanta. Ta tuna da text ɗin da ta tura masa a jiya ta nambar da aka tabbatar mata tasa ce, wani text layi guda kawai da ta tattara dukkan fatanta a cikinsa tana fatan ya zama silar niyya da kuma ƙudirin da ta gama tsarawa a cikin kanta har ma tayi masa ado da ƙarin wasu kyawawan abubuwan da zuciyar tata ke so. 'M'aruf, Hameeda ta tambaye ka...' Kuma sai bayan da ta tura ne sannan bangaren ƙwaƙwalwar tata mai hankali ya shiga jero mata kuskure tare da wautar ta, yana gaya mata kamar ba haka ne daidai ba, yana hasko mata tarin yarjejeniyar data yarda da ita a cikin doguwar takardar nan, lokacin da ta yarda tasa hannu akan komai yayin da zuciyarta ke cike da ɗokin rayuwa mai kyau a gaba kamar yadda mahaifiyarta tace, yana gaya mata cewa saboda ta sami saɓanin tunaninta hakan baya nufin cewa ta shirya fuskantar duk waɗannan sharaɗan? "Jibi zan dawo, ki gaya min zan ƙara samunki dan Allah." Muryar Jawad ta jawo ta daga tunanin yayin da yake ƙoƙarin ƙara matsowa. Sai kawai tayi murmushi sannan a lokaci guda ta shammace shi, ta ture shi ta miƙe tsaye tana dariya, yayi ƙoƙarin kamo ta amma ta kauce saboda haka shi ya faɗa kan gadon inda ta taso. "Zo." Ya faɗa daga kwancen yana kallonta, ta matse kafaɗarta ɗaya. "Zanje in shirya ne kar kayi missing flight dinka." "Wani abu zan gaya miki." Ta ƙara matse kafaɗarta. "Ka barshi sai na fito." Da haka ta shige banɗakin tana murmushi yayin da Jawad ya dafe kansa da duka hannayen sa biyu yana jin wani abu kamar taraddadi akan abinda ke shirin faruwa. Allah ya sani da gaske yana sonta, irin son da bai san adadinsa ba kuma bai san lokacin da ya shige shi ba, abinda ya sani kawai shine a matan da yayi mu'amala dasu a rayuwarsa Rukayya daban ce, komai nata daban ne ta yadda tun daga lokacin da ya santa, sanda suka haɗu a airport zuciyarsa ke bin ta kamar raƙumi da akala. Shi yasa a yanzu da iyayensa ke damunsa da maganar aure ya ture duk wani kokwanton zuciyarsa ya tsayar da abu guda, don ya tabbata idan yayi saɓanin hakan zai zama kamar an bar baya ba zani ne. Saboda haka a lokacin da ta fito take tsaye a gaban mudubi tana shiryawa, sai ya ture komai ya jawo ƙwarin gwiwarsa ya isa kusa da ita ya tsaya daga bayanta. Ta ƙifta masa idonta ɗaya tana murmushi ta cikin mudubin kafin ya kira sunanta. "Ruƙayya.." Sai ta juyo ta kalle shi amma yasa hannayensa ya komar da ita gabaɗaya, tana kallonsa ta cikin mudubin shima yana kallonta lokacin da da ya buɗe baki yace. "Ina so zan aure ki." Ga mamakinsa sai kawai ta kalle shi na wasu sakanni ta cikin mudubin sannan ta ƙyalƙyale da dariya. "Me kace?" Ya haɗiye wani abu mai zurfi a maƙogwaronsa kafin ya saka hannayensa ya sake juyo da ita yana kallon fuskarsa. "Wallahi da gaske nake, ina so zan aure ki Rukayya, ki bani dama ko a weekend ɗin nan zan turo iyayena, saboda na fahimci cewa I can't live without you. (Ba zan iya rayuwa ba sai da ke)" A lokaci guda ta shiga girgiza kanta yayin da duk wannan rahar ke barin fuskarta, kamar tana karkade ta ne tare da girgizawar kan nata. "Ba muyi wannan alkawarin ba Jawad, saboda haka don me yasa zaka yi tunaninsa, ofcourse kana burge ni saboda wasu abubuwa a gefe, amma bana sonka, na daɗe ina gaya maka hakan, zuciyata ba taka bace." Tana kallon yadda dukkan wani ƙwarin gwiwar da ya tashi dashi a safiyar ke zagwanyewa daga

Table of Contents

Chapters

73 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});