Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 39

BOOK 3

Maradams Book 3 Complete Hausa Novel 5,406 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin  na kudi ne mai bukatar karantashi   byn na kammalashi zai  biya 1000 ta wannan  account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura  domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina  (Hausa bakwai ) a YouTube.

38

A kaikaice mami ta kallesa sannan tace “maganata ta tabbata kenan ?ATA ya bala’in tsurawa mami Ido yana kallonta fuskarsa d’auke da mamakinta yayinda kwakwaluwar sa ta shiga maimaita masa abinda ta fad’a yanzu “maganata ta tabbata kenan “.to me hakan yake nufi?” “adamcy!“ ta kira sunansa tare da riko tafin hannunsa cikin wani irin yanayi mai cike da tashin hankali da jin tsoron abinda take son fad’a ,shi kam kallonta ya cigaba dayi cike da rauni tare da yin kasa da murya yace “sweetheart ina jinki “da gaske adamcy son yarinyar nan kake tunda gashi kace zata zo? numfashi ya sauke yana cigaba da kallonta “itace fa ta matsa masa da batun tana son ganin maryama yanzu kuma ga abinda take fad’a “wai meyasa sweetheart take masa haka ne ?numfashi ya janyo da kyar ya fesar sannan ya motsa lip’s dinsa yana cewa “sweetheart nifa ban fahimceki ba?” ya qarasa maganar yana mai kawar da kanshi daga kallonta “adamcy nasan ka fahimceni sosai ba iya zargina ba ,hatta zuciyata ta aminta da son da kake ma yarinyar nan abida naso ya faru akan mar…” .“sweetheart abar maganar nan .”ta sake bud’e baki har ta soma magana ya juyo da sauri yace “dan Allah sweetheart karki sake cewa komai akan yarinyar nan ,itama maryama baza tazo ba shikenan “ya qarashe maganar cikin ‘bacin rai da rauni a fuskarshi ,ya rasa dalilin da yasa take masa haka idan ma son yarinyar yake me ye laifi aciki tunda shi ba yaro ne da zaa dinga masa irin haka?.”tace tana son gani yariya yace yaji sannan kuma ta shigo masa da batun wata maryam abinda ta rigada tasani ne ko maganarta baya son ana masa,wannan matsalar na cikin abinda yasa yake son ya auri maryama a boye sai bayan sun haihu sannan ya fad’a mata dan yasan kota amince ya auri maryama to fa kullum sai tayita masa mitar rashin kasancewarsu da wannan banzar maryam din ”.

“Me yasa?kuma saboda me za’a bari “?me yasa zaka d’auki zafi daga ‘yar wannan maganar har kace baza tazo ba ?”tayi masa tambayar ajere tana dubansa cikin tsananin tashin hankali duk da dai tafi son shi da maryam dinta amman kuma hakan bazai sa taki son abinda yake so ba dan arincikinsa shine nata “kayi shiru kana jina kayi magana mana,sarkin zuciya. “Kai dai ba’a ta’ba yin hirar arziki da kai batare da ka shigo da zafin zuciya ba ,kanshi ya juya tare da zare hannunsa cikin nata ya had’e waje d’aya ya fuskanci mahaifiyar tashi cikin sanyi yace “ba maganar zuciya bane kawai dai gani nayi rashin zuwan nata zai fi zuwanta samun kwanciyar hankali”amman dai kasan kana son yarinyar nan “inna lillahi ya furta yana runts ido “babu wani batun inna lillah gskyr dake cikin zuciyarka nake son nasani “dan girman Allah sweetheart ki bar maganar nan kuma maryama bazata zo ba dan nasan zuwanta ba zai kwantar miki da hankali ?
”girgiza masa kai tayi alamun a’a.”karka damu ka kawo min ita Ina son naga ka sake ajiye iyali a karo na biyu, zaka auri yariyar nan kuma anan kusa idan ma bazaka iya sheida mata kana sonta bane ni zan sheida mata da kaina karyata taki amincewa ,dan banga macen duniya da zaace mata ga miji kamar d’ana tayi rejecting ba gara ma ka natsu ka kawo min ita ni na sheida mata d’ana yana sonta tunda kai girman kan tsiya bazai barka ka iya sheida mata ba.”numfashi da ajiyar zuciya ya sauke atare still idanunshi na kallonta .mami ta jima zaune suna hira irinta d’a da mahaifiya sannan tai masa sallama ta sauko qasa ta shige bangarenta .”

Bayan fitar mami tashi yayi ya shiga bedroom dinsa ya qarasa inda system dinsa yake ya d’auka ya dawo kan bed dinshi ya kishingid’a akan gadonsa had’e da tokare hannunsa d’aya a gefen kungunsa sannan a hakan ya kunna system ya soma daddana keyboard din system dinsa yana amsa sakonin abokan kasuwancinsa yayinda bangaren maryama itama zaune take a tsakiyar gadonta ta rungume pillow a qirjinta tana tunanin abinda ya faru yau atsakaninsu sosai take tunanin abinda mr ATA yayi mata a yau din nan ,ahankali komai daya faru tsakaninsu yake zuwan mata daki daki har zuwa sanda ya kamo hannunta yace“tayi jump !”jump maryma” ya fad'a hankalinsa a matukar tashe yana sake hura hanci “wannan  shine best solution agareki ,shine kawai abinda zai kawo miki qarshen kuncin da kike ciki ,kuma shi zai kawo qarshen rayuwarki .”
”kina zubar da hawayenki a banza bayan Kinsan mutumin nan ya mutu baya raye "wani irin tsoro da matsanancin firgice taga ya bayyana akan  fuskarsa alokacin "oya jump!”har sanda ta soma kuka mai tsanani wanda ya zamo sanadiyyar kawar da tarin damuwarta wani irin naunayen ajiyar zuciya ta sauke mai qarfi tana cewa “duk rashin kirkinka da nake gani still kai din mutu min kirki ne ,ban ta’ba tunanin zaka zamo silar yayewar damuwata ba sai gashi acikin awanni ka zamo silar kawar da tarin damuwar da nayi shekara da shekaru ina dawainiya dasu.” “hakika kai din mai kyakkywar zuciya ne ,kawai da nice da wasu daga cikin mutane muke maka wani irin kallo ,duk da kana da wasu dabi’u marasa kyau amman dai kana da kyakkyawar zuciya .”ta furta a fili fuskarta bayyane da murmushin farinciki ta matse pillow dake makale a qirjinta tana cewa .”maryama tana godiya bisa qoqarin da kayi mata na gode sosai daka canza min rayuwa .”

ahankali mr ata ya d’auke kwayar idanunshi akan system zuwa wani bangare dabam tare da rufe system din gaba daya“ya d’aga kanshi sama kallon saman d’anki tunanin maryama yake yana jin kamar ya kirata “idan ka kirata kace mata me?”ai ita ya kamata ta kiraka no kai ya kamata call her and tell her how much you loves her dan idan ka bari wani ya sake sace zuciyar yarinyar nan zaka iya mutuwa for real you’re so much in love with her .”ya fad’a yana runts tsumammun idanunshi .a natse maryama ta sauko daga kan gado ta soma tafiya tana magana a fili muryarta cike da matsanancin farinciki “na gode sosai mr ata Allah saka maka da mafificin alkhairi.”
shima bangarensa mikewa yayi tsaye tare da yin shiru ya saka hannunwansa duka cikin aljihunsa
wondonsa yana magana a fili “lallai soyayya ya zautar da kamilar yarinya mai tsananin baseera da sanin kan aikinta yana matukar son furta mata cewar yana sonta amman soyayyar wannan mataccen da yake hangowa har yanzu acikin kwayar idanunta shine dalilin da yasa ya kasa fad’a mata ,hakazalika itama karon kanta shine dalilin da yasa ta kasa fahimtar inda ya dosa ina ma zata bashi damar daya d’an d’ana mata gard’in soyayyarsa.”amman zan yaki zuciyarta.
“ zan yi duk yadda zanyi na raba zuciyarta da tunanin kowa sai nawa ,zan dasa mata qaunata ta yadda zata kasa samun kwanciyar hankali sai tana tare dani.”cire hannuwansa yayi duka yaje ya bud’e wordrobe dinsa ya d’auko wani takarda ya rufe wordrobe din ya tsaya sosai rike da takardan yana kallo yana cigaba da tunanin maryama sosai yake jin tsananin soyayyarta na sake ratsa dukkanin sansar jikinsa kai kawo ya shiga yi acikin d’akin shi kad’ai yasan irin azabar da yake ji ajikinsa .”

Hotonsu maryama aunty abida ta tsaya tana kallo jikinta na wani irin rawa tmkr mazari “meye haka sultana? meke faruwa haka ?”mafarki nake ko kuwa gaske ne abinda nake gani adam ne rungume da wannan yarinyar ?shine aunty ai ba wannan bane karo na farko da suke lalatarsu a office sai dai wannan shine karo na farko da nayi qoqarin d’aukarsu batare saninsu ba bama fa AGC wannan abu ya faru ba d’aukar ta yayi taka nas suka bar kamfani zuwa ATA company .” “aikinsu fa kenan sai dai idan basu had’u da juna ba.” nan take gaban aunty abida yayi wani irin bugawa da qarfi tamkar wata matarsa “aunty da alamun yaya adam yana tsananin qaunar yarinyar nan “ai wannan ma ba abu ne mai yuwu ba sultana kinji yadda nake ji kuwa “ta mika mata wayar tana cewa” ai kallon wadan nan hotunan zai iya sa mutun yayi loosing temper dinsa .”wallahi aunty haka nake fama da wannan bakinciki kullum zuciyata kamar ta fashe ni nasan bazan ta’ba samun auren yaya adam ba kinsa zuciyata ta kamu da tsananin soyayyarsa .”ta qarasa mgnr tana dafe goshinta

“aunty kece kika dasa min soyayyarsa a zuciyata gashi nazo ina masa wani irin mahaukaci so da bazan iya rayuwa babu shi ba “sultana ta qarasa maganar cikin zafin rai “ki natsu sultana duk runtse duk wuya ina tare dake kuma zaki auresa sannan soyayyarsa da wannan yarinyar ba abu ne mai yuwuwa ba kamar ma ya lalace ya gama “me zaki iya yi aunty akai ?zanyi komai akai sultana “sultana ta matso kusa da auntynta tana cewa “aunty kibi komai a hankali karki yi bakin jini ki barni dashi “no no sultana gara ni nayi saboda kinsan halinsa bazai ta’ba d’aga miki qafa ba “yadda bazai ta’ba d’aga min qafa ba haka kema bazai d’aga miki ba amman da sannu ni zanyi maganinsa sai na watsa hotunan nan zuwa social media kowa ya san halin da yake ciki sai dai kafin nayi haka sai muyi da wajewa dashi zai aureni ko kuwa na yad’a idan ya amince fine idan kuma yayi taurin kai nima zan nuna masa kalar nawa taurin kai ta fad’a idanuwanta na kawo ruwan hawaye “.

“mai na rasa aunty da yaya adam bazai soni ba ?wallahi aunty ina tsananin son yaya adam yana da matukar mahimanci arayuwata ina mutuwar son shi amman shi ko kad’an baya qaunar sanyani acikin kwayar idanunshi .”mai yasa ya bawa maryama mahimanci haka arayuwarsa in takaita miki aunty a irin soyayyar da yakewa yarinyar nan baya iya juyata a office komai taga dama shi take yi kuma yana kallonta bai isa yayi magana ba amman kuma nasan duk yana yin haka ne saboda yana samun wani abu agurinta ka rasa ma sonta yake ko kuwa saduwa yake daita .?”ni babu ruwana sultana da ma koma menene a tsakaninsu ni dai ya barta kawai ya fuskanceki kema Kinsan dole kema kiyi closing dashi idan ya kama ki mallaka masa kanki ne duk kiyi domin dole ki zama suruka acikin gidansu dan bazan bari wata mace ta sake shigowa cikin rayuwar adam ba never .”sultana tayi shiru kawai tana duban yayarta dake tsaye cikin tsananin tashin hankali anya kuwa zata iya wannan kasadar mallaka masa kanta fa ta ina ma haka zata kasance a tsakaninsu mutunin da ko second biyar baya bata za dai ta tuntubesa akan aure idan yaki kuwa zata bashi mamaki .”

*****

Washegari

Ahankali maryama ta shigo cikin ma’akatan sanye cikin doguwar riga baka mai ratsin ash colour ajiki tayi rolling din kanta da mayafi ash yayinda qafafuwanta ke sanye da bakaken flat shoe haka jikinta wani irin sihirtaccen qamshi mai sanyi ne yake fitarwa,jikinta a sanyaye take tafiya makale da jakar aikinta sai dai kallo d’aya zaka mata ka fahimci yau din tana cikin farinciki .”a natse ta shiga lifter zuciyarta da kwayar idanunta cike da tsananin farinciki son d’aura kwayar idanunta akan mr ata kofar lifter na gama bud’ewa ta fito tare da mutane dayawa kowannensu ya d’auki hanyar office din da zashi .”kai tsaye hanyar office dinsu ta nufa a natse ta shiga fuskarta d’auke da murmushi
ta gaishe da abokan aikinta sannan ta cire jakarta ta ajiye akan table daidai saitin kujerarta sannan ahankali ta kai kwayar idanunta zuwa ga office din mr ATA ta hango kujerarsa empty da alamun bai zo ba tai shiru kawai tana cigaba da kallon office din kuma tana tunanin kalmomin da zatai amfanin dasu wajen gode masa domin ya cancaci tai masa godiya na mussaman amman gashi bai zo ba har yanzu babu mamaki yazo ya fita ne ? zuciyarta ta fad’a mata haka .”

ahankali ta tsuke qaramin bakinta kafin ahankali ta fito zuwa inda ta hango madam some zaune ta qaraso tana gaisheta “good morning ma ?”
”mornig maryama !”ta amsa mata tana dubanta da kulawa “amm ko mr ata yazo kuwa ?”no !bai zo ba amman dai zai zo yana kan hanya “okay maryama ta fad’a tare da juyawa ta koma office dinsu ta zauna zuciyarta na cigaba da tunaninsa haka fuskarta na cigaba da bayyana farincikinta.”
Ko cikakken minti shabiyar batai da zama ba qamshin daddaden turarensa ya soma karasowa inda suke ta juyo zuwa bayanta nan take kwayar idanunta suka sauka akanshi yana taku ahankali cike da izza da isa yayinda duk taku d’aya idan yayi sai zuciyar maryama ya buga da qarfin gaske sakamakon qamshin turarensa dake kusantota .”
ahankali ya shigo office dinsa na farko inda madam some take zaune hannunsa d’aya cikin aljihunsa ,yayinda jikinsa ke sanye da wani had’ad’den suit brown colour ,suma kanshi dana fuskarshi na kwance luf luf kamar ta yan india madam some na ganinsa ta mike tsaye da sauri cike da girmamawa tace “good morning sir ?.”
”morning ! ya amsa mata atakaice sannan ya nufi kofar shiga cikin office dinsa ya zauna yana juyi akan kujera .”

ahankali maryama ta mike ta nufi kofar office dinsa ta turo kofar ta shigo ta tsaya a gabansa tana gaishesa “good morning sir ?” a natse ya d’ago tsumammun idanunshi wad’an da suka wadatu da gashin ido dana gira ya zuba mata tare da yin shiru yana sauraronta itama shiru tai tana kallonsa tana wasa da yatsun hannunta ganin irin kallon da yake mata yasa babu shiri ta sunkuyar da kanta qasa ta cigaba da murza yatsun hannunta dake tsarke cikin juna ta sake d’agowa ahankali fuskarta d’auke da murmushi amman nan take murmushi ya d’auke a fuskarta sakamakon ganin fuskarsa a had’e tamkar yadda ya shigo ,kwatakwata fuskar nan babu alamun fara’a bare annuri akan fuskarsa ,dole tasa ta shanye dukkanin wani farinciki da take tattare dashi .”

shiru tayi tana zazzare idanu kusan mintuna shabiyar bai ce mata kala ba itama bata iya ce masa komai ba tana dai tsaye a gabansa tana kallonsa ya mike tsaye ya zagayo ya wuceta tsaye ya shige d’aya daga cikin dakun nan dake cikin office din .”qirjin maryama na wani irin dokawa ta juyo da sauri tabi shi da kallon mamaki tamkar bashi ne jiya ya dinga bata kulawa ba “karfa yayi tunanin wani abu akanta alhalin ita tazo ne dan yi masa godiyar taimakon da yayi mata ,yayinda sultana wacce idanunta ke kansu tai murmushin jin dadi yadda yayi mata wulakaci “kad’an ma kika gani dan dole yayi miki wulakanci tunda ya rigada ya gama more miki albarka jiki ,amman kuma sultana ki natsu da kyau zai iya zamowa pretending yayi dan kwayar idanunshi kad’ai idan kika kalla kinsan akwai zazzafar soyayyar yarinyar acikinsu sai dai ga dukkanin alamun bai sheida mata ba ,kamata yayi ki bari maryama tasan irin son da kike masa ta haka ne kawai zata janye jikinta daga nashi .”

Wani irin wahalallen numfashi maryama ta sauke ta soma magana da zuciyarta“ki sharesa kawai ba sai kin masa godiya ba ,no no hakan bazai yuwu ba ga mutumin daya tayaka jin pains dinka ,mutumin da yayi qoqarin cire maka damuwar dake cikin zuciyarka ai ko babu komai ya cancanci kayi masa godiya koda kuwa bazai amsa ba.jiki a sanyaye ta fito daga office dinsa zuwa nasu ta tsaya dan gabad’aya ta kasa samun natsuwa bare ta zauna tunanin abinda zata kawai take “to ni yanzu me zanyi ? ” me zanyi “?yauwa nasan me zanyi !ta furta a fili lokacin data furta hakan sai da kowa dake zaune acikin office din ya kalleta .”da sauri ta dauki jakarta ta fita daga office din inda sultana ta mike da sauri tabi bayanta tana son taga inda zata.”ganin ta fita daga maaikatar gabadaya yasa ta dawo .”

Maryama bata d’auki wani lokaci ba ta dawo still dai ta kasa samun natsuwa dan ko aikin da madam some ta ajiye mata bata bi ta kansu ba babban burinta tai masa godiya sultana ta kalleta a tsanake “meke cikin zuciyar maryama yau kamar tana son furta wani abu mai mahimanci ga yaya adam I most find what’s the matter maryma ta sake kallonsa alokacin daya fito yana waya “ni na rasa ma me zanyi gabad’aya yanayinsa yau ya bani tsoro ta fad’a a zuciya inda sultana tazo ta tsaya a kusa daita tana cewa “lafiyarki kuwa maryama “?“me kika gani ?maryama ta tambayeta fuskarta babu yabo babu fallasa “abubuwa dayawa na gani !” “sultana abubuwa dayawa kuma ?”maryama ta tambayeta, ta gyada mata kai alamun eh “amman kuma babu komai ai,” amman me yasa kika kasa zaune kika kasa tsaye kike ta zariya office din d’anuwana bayan nasan babu aikin daya baki ?”am babu komai sultana kawai dai Ina son na gode masa ne saboda ya taimakeni.” tayaya akayi ya taimakeki ki fad’a min dan ina son sani “?mr ata yayi min taimakon mai girman da wani dan adam ya kasa min a jiya na d’auki tswon lokacin ina cikin damuwa sakamakon mutuwar mijina amman a jiya yayi silar yaye min wannan damuwar ya taimakeni wajen dawo min da farincikina shiyasa nake son ganinsa na gode masa .”

murmushi sultana tayi tana cewa “wannan bashi ne asalin gaskiyar abinda ke ranki ba akwai wani abu dabam acikin zuciyarki da kika boye .”ta fad’a tana kallon tsakiyar idanun maryama “no sultana babu komai acikin raina bayan wannan karki manta mr ata matsayin mai gidana ne kawai dai godiya zan masa bayan haka wallahi babu komai acikin zuciyata “lallai ya tsaya amatsyain babu komai sultana ta fad’a mata hk cike da gargadi har maryama zatai magana sai kuma tayi shiru ta fasa cewa komai ta zaro takardar zanenta tana mamakin maganr sultana ”lallai ya tsaya amatsayin babu komai ta sake maimaitawa kanta maganar sultana na qarshe tana mata wani irin kallo mamaki to me take nufi daita ?.”

can bangaren mr ata kuwa kawo qarshen wayar da yake yayi da cewa “okay zan duba thank you sannan ya ajiye wayar ya maida tsumammun idanunshi zuwa ga glass din office dinsu maryama ,ya d’an kalleta yana jin wani irin magadisun sonta na shigarsa ,kafin ahankali ya mike yasa hannunsa d’aya cikin aljihunsa ya bud’e kofar ya fito yana cewa madam some “ina mukalan motocin da’aka kawo “?gasu anan sir !”okay biyoni dasu “okay sir ta bud’e doruwar data ajiye ta kwaso “kai tsaye office dinsu maryama ya shiga ya tsaya yana cewa “guy’s!gabad’ayansu suna ganinsa duk suka natsu suka tattara hankalinsu garesa cike da girmamawa madam some ta tsaya kusa dashi inda hankalin maryama da idanunta suke kanshi tana qare masa kallo tsab tare da nazarinsa tana son gano wani abu atattare dashi cikin tunanin da take ta soma jiyo sautin zazzakar muryarsa mai bugar da zuciya tare da sanya natsuwa a zuciya “some ki fara raba masu”. d’aya bayan d’aya some take mika masu keyn din motar benz new model “lokacin data kawo kan maryama yace “bani nata !”babu musu ta mika masa ya jefa cikin aljihunsa hakan bai damu maryama ba kamar yadda taga yanayinsa mutum kamar hawainiya kamar bashine jiya yay silar cire mata damuwa ba .”wannan shine kyautarku na presentation din da kuka gabatar “.nan take office din ya kaure da hayaniyar godiya ,yayi saurin dakatar dasu ta hanyar d’aga masu hannu “bana bukatar godiyarku sannan bana son ganin kowa yau din nan a office dina duk wanda yake da wata bukata ya samu some yana gama fad’ar haka ya juya ya fita inda maryama ta mike ta biyosa da sauri tana cewa “sir !”go back to your office …”

cak ta tsaya qafafuwnata na d’aukar rawa “me ke faruwa dashi ne yau ?” tayiwa kanta tambayar tana mai jin wani irin tashin hankali mai tsanani yana shigarta “bayansa ta cigaba da kallo har sanda ya qarasa shigewa office dinsa ya zauna jikinta a sanyaye ta dawo ta zauna inda sauran abokan aikinta ke cike da tsannain murna.”yusura ta matso kusa daita ta dafa kafadarta tana cewa “lafiya maryma meke faruwa mr ata ya bawa kowa kyautar mota amman ya hanaki ?”I don’t know yusura ban san meke faruwa ba bansan dalilinsa ba but is like sir his not in good mood today ki natsu sosai maryama kiyi tunani baki yi masa laifin komai ba dan bazai yuwu ace ya bawa kowa kyautar mota ya hanaki ba ?”tai shiru kawai tana tunanin mutumin da suka wuni dashi jiya kuma lafiya lafiya suka rabu dashi babu wata matsala kawai dai tafi tunanin miskilancinsa ne ya motsa. numfashi ta sauke da qarfi tana cewa” yusura kije kiyi abinda ke gabanki ni ban damu da kyautar motar da ya baku ba dan ko bai bani ba inada niyyar zan siya lokaci kawai nake jira ta qarasa maganar tana hura hanci tare da runtse idanunta tana mai jin zafin abinda yayi mata.”

Yana zaune rike da file yana dubawa maryama ta shigo office dinsa batare data tsaya neman izininsa ba ta tsaya a gabansa tare da goya hannunwanta duka abaya yayinda kwayar idanunta ke kansa muryarta a sanyaye tace “sir !”ya d’ago tsumammun idanunshi ya zuba mata sai data ji wani irin mummunar fad’uwar gaba sannan taji wani abu ya caki zuciyarta sai dai tayi qoqarin danne abinda taji a zuciya da sansar jikinta ta motsa lip’s dinta ahankali ta soma magana a natse “thank you for yesterday sir .”daman shine dalilin zuwana d’azu office dinka ba wani bane kawai ina son na gode maka ne bisa qoqarinka akaina domin ka dawo min da farincikina” shiru yayi kawai yana kallon kyakkyawar fuskarta da qaramin bakinta da burinsa a yanzu ya jisa cikin bakinsa yana sarrafasa tana gama fad’ar haka ta juya a natse ta nufi kofar fita batare datai masa maganar keyn motarta ba .”

ya ajiye file din hannunsa yana ya cigaba da kallon bayanta yaji kamar ana zarar ranshi ne a zaune da yake ,idanunshi na kanta har ta shiga office dinsu ta samu waje ta zauna ta soma aikinta batare da wata damuwa ba ,can bayan wasu mintuna duk abokan aikinta suka fita zuwa break ,office din ya saura ita kad’ai, ta mike a natse taje inda aka tanada masu ruwan zafi ta tara cup ta tsiyaya ruwan zafi ta had’a shayi ta soma sha ahankali tana lumshe idanunta ahankali mr ata ya tashi daga mazauninsa ya fito har zai karya kwana sai ya hango bayanta tsaye shiru bata ko motsi dan haka ya shiga office dinsu har lokacin tana tsaye hannunta rike da cup qamshin daddaden turarensa ne yasa ta juyo da sauri aiko taji tayi karo da mutu tsaye a gabanta da sauri ta d’ago shi din ta gani tsaye yana dubanta da tsumammun idanunshi gashi har ruwan tea ya d’an ta’ba masa gaban rigarsa a rikice ta soma cewa so..” sorry sir ban..”bansan kana tahowa ba.”

ya tsura mata ido kawai yana kallon yadda duk ta rikice tana faman furta masa “sorry sir “what happened maryama ?” ya sorry yaki qarewa haka ?”.maryama why are you so distracted ?” Sorry sir am ..” bai tsaya jin mai zata sake cewa ba ya fita ya koma office dinsa ya d’auki kwalin tissue ya ajiye akan table ya zari kwaya d’aya ya soma goge jikinsa.” oh Allah meke shirin faruwa dani ne yau ?” ta ajiye cup din hannunta da karfi akan table ta biyosa alokacin daya zauna yana goge saman takalmin qafarsa dan ruwan tea ya sauka akansu muryarta a sanyaye tace “kayi hakuri dan Allah ba da gangan nayi ba “is okay “.
ya fad’a yana lumshe ido .”Jin haka yasa ta juya tana mai jin sanyi aranta dan tafi son taji muryarsa da yanayinsa haka bata son ganinsa cikin fushi ko miskilanci domin hakan yana rikitata sosai if kar yayi wani tunani kamar yadda sultana tayi ai data bashi flowers din data siyo danshi ko hakan zai qara sanyaya zuciyarsa amman tasan halinsa bahagon mutun ne kuma gara ma da sultana tai mata gargadi dan shima haka zai fassara ta ,ta shigo office dinsu da niyyar ciro flower din da niyyar ta yar a shara sai dai taga wayam babu jakarta a inda ta ajiye babu alamunta ta sake dubawa taga babu, ina jakata yake kuma anan fa na ajiye jakata ?”ta fad’a tana duddubawa tana sake tambayar kanta, nan take ta rikice tana sake dubawa alokcin mr ata ya fito ya nufi qasa .”

tayi shiru kawai tana tunani inda jakarta ya shiga kafin ahankali ta jiyo sautin muryar sultana abayanta “kalli nan maryama !”maryama ta juyo da sauri tana kallonta, sultana ta nuna mata kan makeken table din mr ata jakarta dake makale da takada mai ruwan kasa data makala flower ta gani ajiye akai ,har ana iya hango flowers din dake ciki da sauri ta zaro ido waje tana cewa “mai yasa zaki min haka sultana ?”ai gode min ya kamata kiyi domin na saukaka miki “na sakaki ?me yasa zaki min haka “?no no !! yanzu me kike tunani idan mr ata ya gani ?”ta fad’a cikin tsannain tashin hankali gani nayi kina so kina jin tsoro har qarin taimako nayi miki ta yadda zaki samu shiga a wajensa ba dai bazakiji gargadin da na miki ba ai..”kafin sultana ta sake cewa wani abu da sauri maryama ta ra’ba ta gefenta ta nufi office din mr ata inda sultana ta tsaya tana kallon bayanta tana murmushin mugunta. “

cak maryama taja ta tsaya daga tafiyar saurin da take sakamakon jiyo qamshinsa datai ta d’an juyo ahankali shi din ne yana taku cikin yanyanayi na jin kai ,fuskar nan tashi a had’e ta gefenta ya ra’ba ya wuce yana satar kallonta hannu ta kai saman goshinta ta dafe tana kallonsa ta rasa meke mata dadi can tayi wani tunani dan haka ta matsa gaban kofar tace “sir may I coming ?”ya kalleta a natse daga inda yake yace “are you okay ?kayi hakuri ina distoping dinka over daman na manta jakar aikina ne ko zan iya shigowa na d’auka?” da hannunsa ya bata umarni ta shiga ahankali tamkar kazar da kwai ya fashewa aciki ta kai hannunta ta d’auki jakarta ganin idan ta tsaya tura flower din sosai cikin jakarta zai iya fahimtar wani abu tayi tunanin boye jakar abayanta alokacin da ya juyo da saurin idanunshi suka sauka akanta .”kallo daya yayi mata ya fahimci alamun rashin gaskiya atattare daita .”

Muryarsa a kasalance yace “me kike boyewa ? muryarta cike da in..ina tace “amm ..”umm no babu komai “show m your hands zaro idanunta tayi tana cewa “babu komai sir jakata ce”.uhm nasan jakarki ce but let me see .”gabad’aya maryama ta rikice tayi fuska kalar tausayi ta ciro jakar ta rike a hannunta tana nuna masa a tunaninta ganin jakar kawai zai yi ya barta ta wuce kawai sai taga ya kawo hannunsa zai kar’bi jakar.”ta sakar masa jikinta na rawa ,ya tsurawa jakar ido da takardar dake jikin jakar makale yana kallo yana jin wani irin zirrrr a gabdaya ilahirin sansar jikinsa yayinda qararrawar soyayya ta buga a zukansu .ahankali maryama tasa gefen mayafinta tana rufe fuskarta cike da jin tsananin kunya gabdaya a matukar tsorace take da irin kallon da yake mata yana wa flowers din hannunsa, ta sake kai hannunta daya ta rufe fuskarta saboda tsannain kunyar data kamata kallonta yayi yana cewa”. menene wannna .”?
”amm umm daman dan naga irin taimakon da ka min shine na siya d’an wannna abun dan na ba..”

“Meke damunki ?” menen ma’anar wannnan kuma “?sir kawai dai nayi amafani dashi ne dan nayi maka go….” maryama !”ya kira sunanta cikin wani irin salo yana dawowa gabana ya tsya yana tsura mata idanunshi kafin ahankali yace “kin fara sona ne ?”da sauri ta girgiza masa kanta jikinta na d’aukar rawa” ai ni yanzu babu wani maganr soyayya araina aikina da kulawa da rayuwar dan’uwana ne kawai agabana amman babu wata soyayya araina ina jin ma haka zan qarar da rayuwata babu soyayya bare au” shiiiii ya daura yatsana hannunsa akan lip’s dinta yana cigaba da kallonta “ki natsu da kyau maryama ki saurari zuciyarki kin kamu da son mr ata .”no no sir akan wani dalili zakace haka ?”me zai sa zuciyata ta min haka ?”bazan ta’ba yarda zuciyata tayi min haka ba, idan kuma dan flower din nan ne kayi wannan tunanin dan Allah ka daina zan iya maka rantsuwa da alqurani babu digon sonka araina ga wacce ke maseefar sonka can “.ta qarashe mgnr tana nuna masa kofar wajen office dinsa .”

numfashi ya sauke da qarfin yana jin wani irin zafi aransa bai san sanda yayi wulli da jakarta da flowers din ba yana jan tsaki ,tabi gurin da jakarta da flowers dinta ya sauka da kallo ranta yayi mugun baci akan abinda yayi ,nan take idanunta ya ciko da ruwan hawaye tana kallonsa yaja baya ya zauna akan kujera ya d’aura hannunsa daya akan table yana mai jin wani irin rad’ad’i a qirjinsa numfashi ma da kyar yake saukewa kafin ahankali ya nuna mata hanyar waje da hannunsa “get out !” ya fad’a a matukar tsawace babu mutsu ta nufi kofar fita har ta bude kofar sai dai ta kasa fita ta juyo tana kallonsa a tsanake bayan kamr minti biyar ta d’auke idanunta akanshi ta fita tana sauke numfashi sama sama .”

Wani murmushin farinciki ya bayyana akan fuskar sultana ashe ba abinda take tunanin bane acikin zuciyarsa taji dadin wannan wulakanci da sake yiwa maryama da banzar flower ta .zama maryama tayi tana tunanin abinda yasa reactions dinsa ya canza daga tace ba son shi take ba ?”wasu maganganunsa na jiya akan yaya sadam ne suka shiga dawo mata daki daki wani irin yrrrr taji a gabad’aya ilahirin jikinta alokacin data tuno yadda yasa hannunwansa duka  ya zagaye kugunta dashi jiya ya kai bakinsa daidai saitin kunnenta ya soma mata magana cikin wata irin   kasalalaliyar murya mai  cike da tausayawa "maryama duniya cike take da jarabawa kala kala amman idan kayi imani da Allah ,Allah yana tare da kai ,ki manta komai da duk abinda ya faru a tsakaninki da mutumin nan  zaki iya samun madadinsa koma wanda ya fishi arayuwarki ki sani da kice kika mutu da yanzu  yana tare da wata ko nadiya sun cigaba da rayuwarsu daga inda suka tsaya"ki  mantashi arayuwarki hakan shi zai bawa wani damar mallakarki ko baki damar mallakar wani ."wani irin numfashi ta sauke da qarfi tana cewa “na fara tunanin kamar mr ata sona yake idan ba haka ba mai zai sa daga nace dan me yasa zan so shi zai ji haushi ?kai kai maryama ba haka bane bazai ji dadi ba yana son yasan ko kin fara son shi ne sakamakon flower da yaji kince shi kika kawowa to me yasa yaji haushi“?

Yayinda mr ata ranshi ya cigaba da ‘baci juyi kawai yake yi akan kujera yana jin ciwo a cikin zuciyarsa ,ya mike ya bude fridge ya dauki roban ruwa mai sanyi ya dawo mazauninsa ya zauna sannan ya bude ya kai baki nan idanunshi ya sauka akan flowers da jakarta shiru yayi kawai yana kallon flower yana tunanin maganarta me yasa zuciyata zata min haka ?”bazan ta’ba yarda zuciyata tai min haka ba idan kuma dan flowers din nan ne kayi tunanin haka, ka daina zan iya maka rantsuwa da alqurani babu digon sonka araina ga wacce ke matsefar sonka can.”numfashi ya sauke da ajiyar zuciya atare sannan ya fara shan ruwa ,bai sauke ba sai daya shanye tass sannan yayi wurgi da gorar ya sake miikewa tsaye dan ya rasa meke masa dadi.”ahankali ya qaraso ya tsaya gaban jakarta yana kallo kafin ahankali ya duka flower da tace dan shi ta siya ya d’auka yana kallo sai kuma yaji kashi hamsin na damuwarsa ta kau ahankali ya dinga jin zuciyarsa na karkafa masa gwiwar ta fara son shi kuma nan kusa ko bai furta mata ba zata iya nuna masa ,ina ma son shi ta fara da bai san adadin dadin da zai ji ba yau ,ahankali ya bude yar saman suit dinsa ya tura flower yana jin wani irin maseefafen soyayyarta na shigarsa sai dai fuskar nan a had’e take ya d’ago kanshi yana kallonta ta cikin glas

Mmn sudais💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

Table of Contents

Chapters

50 chapters
  1. 1 BOOK 3
  2. 2 BOOK 3
  3. 3 BOOK 3
  4. 4 BOOK 3
  5. 5 BOOK 3
  6. 6 BOOK 3
  7. 7 BOOK 3
  8. 8 BOOK 3
  9. 9 BOOK 3
  10. 10 BOOK 3
  11. 11 BOOK 3
  12. 12 BOOK 3
  13. 13 BOOK 3
  14. 14 BOOK 3
  15. 15 BOOK 3
  16. 16 BOOK 3
  17. 17 BOOK 3
  18. 18 BOOK 3
  19. 19 BOOK 3
  20. 20 BOOK 3
  21. 21 BOOK 3
  22. 22 BOOK 3
  23. 23 BOOK 3
  24. 24 BOOK 3
  25. 25 BOOK 3
  26. 26 BOOK 3
  27. 27 BOOK 3
  28. 28 BOOK 3
  29. 29 BOOK 3
  30. 30 BOOK 3
  31. 31 BOOK 3
  32. 32 BOOK 3
  33. 33 BOOK 3
  34. 34 BOOK 3
  35. 35 BOOK 3
  36. 36 BOOK 3
  37. 37 BOOK 3
  38. 38 BOOK 3
  39. 39 BOOK 3
  40. 40 BOOK 3
  41. 41 BOOK 3
  42. 42 BOOK 3
  43. 43 BOOK 3
  44. 44 BOOK 3
  45. 45 BOOK 3
  46. 46 BOOK 3
  47. 47 BOOK 3
  48. 48 BOOK 3
  49. 49 BOOK 3
  50. 50 BOOK 3
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});