Chapter 1
ADON DAWA
.
BABI NA DAYA
.
Rana ta fadi daf da magaruba dogayen motoci kirar j5 har guda bakwai ne suka shigo jahar Maiduguri daga kasar daura, dauke da fasinjoji dari uku da hamsin manya da yara, mata da maxa. Tafiya yankin axaba, hakika matafiyan cikin motocinnan a gajiye suke kallo daya xaka yi musu ka fahimci haka. A layin suke firfitowa daga cikin motocin yayin da duk wanda ya fito sai ya yi mika ya yi hamma saboda yinin da suka yi cur a hanya suna tafiya.
Kaltum ‘yar kimanin shekaru goma sha biyar tana daya daga cikin matafiyan cikin motar nan. A galabaice take a sanadiyar amaye-amayen da ta dinga yi a mota, baya ga matseta da aka yi a lungu kafafuwanta sun kumbura sumtum kamar mai cikin watan haihuwa.
A tsaye take a gefe tana jiran kakrta ta fito daga bayan bishiyar da ta kewaya don rage tumbinta daya cika da fitsari itama ta bata buta ta kewaya. Sai ta ji muryar wasu samari guda biyu suna Magana a bayanta suna Magana dogo da gajere, dogon saurayin ne ya tambayi gajeren. Ya ce “wadannan fa daga ina suke kuma ina xa su je riki-riki da kaya kamar masu gudun hijira!”
Gajeren ya bashi amsa y ace “ ‘yan gudn hijira ne ma ba kamar ‘yan gudun hijira ba. Daga nan ma gaba xasu kara har xuwa sudan xa su tafi a mota, daga sudan kuma su haura ruwa su shiga saudiya. Haka kawai mutanenmu suke wahalar da kansu saboda kwadayi, yanxu wadannan da ka gansu wahala ce xata kashe rabin su a hanya.”
Kaltum ta waiwayo da sauri ta dube su hankalinta ya kara tashi yayin da suka yi ido hudu da kyakkyawar fuskarta wacce ta basu matukar sha’awar dubanta ba kakkautawa. Dogon ya sake tambayar abokin sa gajeren, y ace, “kai, kalli wata kyakkyawar yarinya. Ba dai itama sudan din xa ta je ba!”
Gajeren ya amsa masa da cewa “sudan xata je mana, baka ganta a cikin suba!
A banxa xa a wargaxa mata rayuwarta duk kyakkyawar halittar nan tata a wulakance xa ka gansu a sudan ko makka idan sun samu ma sun haye kenan., rashin tawakkali ne kawai irin namu na ‘yan Nigeria, ba xasu iya hakuri da talaucinsu ba sai sun je kwadayi.”
Kaltum ta sukuyar da kanta kasa yayinda hawaye ya fara bulbulowa daga idanunta tana tausayin kanta tana tausayin rayuwarta. Ganin hawayen da take yi ne samarin biyu suka karaso wajenda take tsaye, suka yi mata sallama sannan suka fara tambayarta sunanta, daga inda ta fito da kuma inda ta nufa!
Babu amsa se kuka take yi kawai da suka ga halamar bata da niyar Magana sai suka fara bata shawara. Gajeren cikinsu y ace, “ ni dai a matsayi na na musulmi dan uwanki shawarar da xan iya baki shine kada ki sake ki tarki wannan tafiyar shiga makka ta sudan a matsayinki na yarinya budurwa gara ki xauna a kasarku gaban ‘yan uwanki koda ace baki da iyaye saboda bala’in dake tattare da irin wannan harkar.”
Muryar kakarta goggo fatu ta jiyo a bayanta ta kwalla kiran sunanta gami da jan dogon salati harda ihu da dora hannu a ka.
Tace, “na shiga uku, kaltum me xan gani! Me nake jiyowa ana fada miki! Ina kika samo wadannan ‘yan iskan da har suke so su baki shawara ki bujire ki fasa tafiya!”
Kan ka ce kwabo kaltum ta fara rawar jiki saboda tsoro da firgici gami da gigicewa duk suka far mata a lokaci guda. Ta fara bayani cikin rawar murya “gwaggo ban san suba wucewa suke suka xo yi suka ganni tsaye, ba xuga ni suke yi ba.”
Goggo fattu ta cije baki ta dunkule hannu ta duma mata dundu a baya gami da wurga mata butar dake hannunta a kafarta. Kaltum ta yi tsalle ta ruga da gudu gefe ta tsuguna tana kuka. Hankalin samarin ya tashi suka fara yiwa goggo bayani cewar ba laifin kaltum ba ne, suma bada niyyar xuga ta suka xo yi ba wucewa kawai suka xo yi suka ganta tsaye. Goggo ta koma kansu ta rufe su da fada tana musu korar kare wai su tafi su bata waje kafin ta farfasa musu kai. Magana daya suka fada mata wacce ta kashe mata jiki.
Suka ce “ke tsohuwa, ki ji tsoron Allah ki san xa ki mutu, Allah xai tambaye ki dalilin da ya sa kike wahalar da yarinyar nan xa ki kai ta makka ki jefa ta a wata matsananciyar rayuwa kin rabo tada iyayenta. Kuma idan ki ka yi wasa sai mun je mun hada kida hukumar NAPTIC da take da alhakin kwatarwa yara hakkin su daman suna neman irin ku masu wahalar da yara musamman ‘ya’ya mata. Kina ganin yarinyar nan ko bata fada ba kowa ya san bata son tafiyar nan dole aka yi mata saboda tsoro gashi a gabanmu mun ga irin dukan da ki ke yi mata da xagi.”
Tsohuwa ta gaggauta barin wajen da sauri gami da fixgar hannun kaltum suka kutsa cikin jama’arsu ma’ana ‘yan tawagar su ta matafiya domin ta tsorota da abinda samarin suka fada mata. Hakika sun yi gaskiya kaltum bata son tafiyar nan tilas aka yi mata.
A wannan wajen su kaltum suka yi alwala suka yi sallolin da ake bin su Axahar, La’asar, Magaruba da Isha’i. kowa ya bude jakarsa ya dauko guxirinsa yana ci, wasu buredi da miya, wasu suka jika garin kwaki da sukari da gyada wasu kuwa fura ce wacce aka murtuke da nono aka shanya ta bushe suka jika da ruwa suka xuba sukari suke sha.
Misalin karfe takwas na dare suka sake duruwa a cikin motocinsu suka ci gaba da tafiya. Kai tsaye garin gamborin gala suka nufa, basu isa ba saida tsakar dare anan suka yada xango. Garin barebari ne amman akwai wasu yaren daban daban, a bayan gari akwai wasu tsofaffin gidajen kasa anan ake sauke su daman an yi su don sauke matafiya irin su, kuma daga nan garin motocin da suka kawo su suka juya xa’a sake musu motocin da xasu ci gaba da tafiya dasu.
A gambori aka wagarar dasu dakunan mata daban na maxa daban, amma a daki daya ana xuba mutane fiye da goma sha biyar, kar ku dauka daki ne mai gado da leda da labule a’a babu ko daya, ciccirarun tabarmi ne na kaba kawannensu sai yayi matashi da kullin kayansa ko jakar kayansa.
tafiya se da suka share sati biyu cur a gambori, jagorin tafiyar su, wato (agents) suna ta yi musu karairayi kala kala su ce yau xa’a tafi gobe xa’a tafi, wasu da yawa sun kusa cinye guxurinsu don haka suka fara sayen abinci da dan kudaden da suka boyo. Saboda gashi ba’a yi rabin tafiya ba ko Nigeria ba’a bari ba guxurin ya kusa karewa. Mutane biyu ne suka riga mu gidan gaskiya a cikin matafiyan tsoho daya da yarinya matashiya daman tun a hanya basu da lafiya anan aka sallace su aka binne, ‘yan uwansu suka sha kuka.
Matafiya sai mita suke yiwa agents babu ranar da yawa daga cikinsu basu yi kuka ba saboda wahala. Daga inda suke xuwa cikin gari yana da nisa haka suke faman tafiya kafin su je su siyo abunda xa su ci ko debo rowan da xasu yi wanka da wanki. Kowa ta kansa yake, babu babba ba yaro, babu mace babu na miji, babu mai taimako ko tausayin dan uwansa. Akwai mata masu ciki da yawa wasu karamin ciki wasu kuwa tsohon ciki ne, wasu masu goyo amma dole kowacce ta fita ta yi doguwar tafiya sannan ta nemo abinda xa ta ci, ta debo rowan da xata yi wanka da wanki.
A ranar da suka cika sati biyu aka kawo musu katuwar motar nan da aka yi ta musamman don daukar kaya wato tirela. A bayan motar aka dura su gaba dayansu su da kayansu kamar wasu shanu. Bayan haka aka jibga masu buhuhunan gyada da ridi wadanda xa’a sayar a sudan har buhu dari duk a bayan motar. A cunkushe suke a tattakure kafada a marmatse babu wanda xai iya mike kafarsa, da yawan su basu sami waje ba a bayan motar sai a saman mota aka loda su.
Kwalta ta kare don haka cikin kasa (sahara) ake tafiya, tafiya suke yi a mota amma a wahale suke tamkar da kafarsu suke tafiya sun jigata don haka rayukansu kowannensu a bace yake, babu abinda yake tashi a cikin motar sai kyara da bakaken Magana a jima kadan ka ji fada ya tashi ana sursurfawa ashar gunduwa gunduwa. Wannan tace waccan ta matseta sai wannan yace wancan ya shure shi aikin kenan.
Bayan sun yini suna tafiya suka isa kusuri, a dawa aka sauke su a nan ma saida suka yi kwanaki biyu. Sai dai kowannensu ya shimfida xaninsa ya yi filo da kullin kayansa. Babu famfo ko rijiya a kusa don haka jarkokin ruwa agents suke kawo musu jarkoki hudu a tartarfawa kowa a kwanonsa ya sha ya jika gari, alwala kuwa sai taimama babu batun wanka.
Daga kusiri sai suka nifi chadi (N’DJAMENA), basu yi niyyar kwana a N’djamena ba amma dole suka kwana a sanadiyyar ruwan da ya dates hanyarsu ta wucewa. Rowan daga cikin dutse yake bulbulowa ya dates hanyar wucewa dole motoci suka dakata har saida rowan ya tsaya, ruwa ya kafe hanya ta bude amma se da shirin tafiya ya wargaje dole suka sauke kayansu daga cikin mota a sanadiyar wasun su guxirin su ya kusa karewa sai sun nemi kudi sannan a ci gaba da tafiya. Nan fa matansu da maxajensu suka baxama cikin gari neman kudi sune dako, wankau faskare da dai sauransu. Satinsu uku a Ndjamena sannan suka kama hanya, a boda kuma ake sake duba takardarsu wato anan ake duba passport da visa sannan su wuce.
Daga N’djamena sai suka shiga Abbashe nan ma a bayan gari suka yada xango cikin rubabbun gidan katako, tabbas basu yi niyyar wuce kwana daya ba a Abbashe amma hakan bai yiwu ba a sanadiyar nakuda ta wata mace ke yi, yini guda ana abu daya da kyar aka samu dan da yake cikinta ya fito, ya fito da rai amma bayan awanni ya rasu.
A ka’idar garin duk wanda ya mutu sai an sanarwa da maigari ya rubuta takarda an nunawa hukumar da abunda ya shafa sannan xa’a yarda a binne gawa. Don haka hankali ya tashi ana tunanin yadda xa’ayi doguwar tafiya xuwa cikin gari, sannan a yi ta dogon bayani kafin su yarda a binne yaron. Daga karshe aka yi shawara a nannade gawar jaririn a kunshe a tsumma sai a sami mutum daya ya xagaya dawa ya binne gawar jaririn. Haka kuwa aka yi aka binne cikin dare. A daren kuma Allah Ya yiwa mai jegon rasuwa itama daman tunda ta haihu bata da lafiya.
Nan fa hankalin kowa ya tashi ‘yan uwanta sai suka yi ta kuka suna kururuwa. Da yawa daga cikinsu kaltum suma suka yi ta kuka duk da basu santa ba, haduwar motace kawai sai dai don tausayin rai da tausayawa kansu da kansu. Dakin da kaltum take shine dakin da aka yi mutuwar don haka a xaune suka kwana tangarai ko gyangyadi basu iya yi ba. Kaltum na lungu jikinta sai tsuma yake, hawaye ke kwaranya saboda tunda take bata taba ganin gawa ba,. Ta ji dama ace itace ta rasu kamar yadda wannan baiwar Allah ta rasu. Tana tunanin yadda rayuwa xa ta kasance mata nan gaba.
Da gari yawaye direban da jagorannin tafiyar (agents) suka hadu suka tafi wajen maigari ,dan gari ne ya jagorance su cikin yarensu mai suna wadai dan rakiyar ya yiwa sarki bayani cewar wadannan baki ne suka xo daga Nigeria xasu wuce sudan, suka yada xango a wajen gari sai Allah Ya yiwa mace daya rasuwa suna so su binne ta a nan. Sarki ya yi amanna ya basu takarda suka je suka nunawa masu jiran makabarta, sannan aka yarda suka binne ta bayan suna sallace ta kamar yadda ake yiwa kowane musulmi.
A ranar suka sake kama hanya suka ci gaba da tafiya, yini guda cur a mota har dare ba tsayawa saida kyar direban ya yarda ya tsaya a wani gari da ake kira Adre suka yi sallah suka ci guxurinsu garin kwaki ne dai, sannan suka ci gaba da tafiya. A xaune suke tangarai, se gyangyadi kowa ke yi a xaune. Gargada ce a dukkan hanyar a sanadiyar rashin kwalta, idan mota tadaka tsalle sai ka ga mutum ya yi sama ya dawo ya xauna dabas, idan aka yi rashin sa’a wanda ke xaune sai ya dawo sama dororo a jikin mutane matsi ya hana direwa a xauna daidai sai dai idan motar ta sake daka tsalle adan ka yi sa’a sai ka sami wajen xama wani kuma ya xama derere shi ba xaune ba kuma ba tsugunne ba, shi ba a kasa ba shi ba a sama ba.
Sai cikin dare suka isa jinene bayan sun yi sallolinsu suka haba garin kwaki da busashiyar gurasa sai suka ci gaba da tafiya, kwana daya da yini daya da yini daya guda cur suka yi a hanya suka isa wani gari da ake kira mukwar. Bayan sun huta a mukwar sai suka ci gaba da tafiya babu abun da yake kan hanyar nan sai namun daji, xuma caba caba ga ‘yan fashi. Basu tsaya a ko ina ba sai da dajin majawara.
Dajin majawara daji ne wanda yake shiru, tsit ko kukan tsuntsu babu balle gidajen bil’adama. Daga nan kowa dakatawa babu mahalukin da xai iya tsallakewa a sanadiyar tsantsar hadarin da ke tattare da ci gaba da tafiya. Dole ne duk motar da ta xo dajin majara sai ta ja ta tsaya a doka har sai motoci saba’in sun cika sannan sojoji su xo su tsallakar dasu saboda mugaye, kasurguman ‘yan fashin da suke fashi a hanyar. Don haka said a ‘yan tawagar su kaltum suka yi kwanaki uku a nan suna jiran motoci saba’in su cika sannan a hayar dasu.
A ranar da suka cika motoci saba’in sannan aka shirya ci gaba da tafiya a lokacin da xa su tafi da yamma wani dankareren maciji ya sari daya daga cikin ‘yan twagar su kaltum, kan ka ce kwabo mutumin ya sassankare kumfa na xubowa daga bakinsa. Jama’a suka bi macijin da jifa amma tuni ya sulale ya shige dawa basu kashe shi ba, daga karshe mutumin ya mutu a wajen, a nan aka binne shi suka shiga motocinsu suka fara tafiya. Amma a kowace mota said a sojoji bibbiyu suka shiga suna harba bindiga sama har sai an wuce mugayen daxuka da barayin suke. Tun da yamman da suke tafe ba tsaya ba har se da gari yawaye, sannan sojojin suka sassauka daga motocin da suka rako suka shiga motocinsu suka juya. Sannan su kuma matafiya suka ci gaba da tafiyarsu.
Tafiyar kwana biyu suka yi ba kakkautawa sannan suka shiga kartum tutu babban birnin sudan. Sun kwana daya a kartum, a wajen garin akwai dakunan katako da aka yi musamman don kwanan matafiya. Da suka waye a nan sannan suka ci gaba da tafiyar, kwana guda cur suka yi a hanya sannan suka isa kartum bahari sai suka nufi bur sudan nan ne inda ruwan daya hada sudan da makka ,ruwanne ya hade da ruwan maliya. Daga bur sudan kuma tafiyar mota ta kare don haka masu mota suka sauke su su da jifgin kayansu suka juya.
Daki ne na guntayen katakwaye joni joni, rufin dakin ma duk hudaddun katakwaye ne baya da katakon nan babu ko kwayar dakunan sai wanda ya ci sa’a ne xai tarar da kwalaye a shimfide a dakin. Ga duhu a sanadiyar rashin fitila gashi tsakar dare suka iso don haka babu wata wata kwanciyar kowa yake so ya yi. Aka ware dakunan mata da na maxa daban, amma a kowane daki mutane ashirin ne xuwa ashirin da biyar duk da haka wasu a xube suke a tsakar gida wasu maxan kuma a xube a kofar gida. Su dai fatansu su kwantar da hakarkarinsu su mike a sanadiyar kagewar da bayansu ya yi saboda kwana da yinin da suke yi a xaune a mota a tattakure.
Misalin karfe daya na dare suka isa bur suban a gajiye suke don haka idanuwansu a rufe suke burin kowanensu ya sami inda xai yada hakarkarinsa. A guje suke rububin hayewa kan wasu tudu da suka iske a cikin dakunnan katakon cikin rashin sani basu san kabarurrukan suka kwanta yayin da wadanda basu sami hawa ba suka bi layi suka doddora kansu a kan kabarurrukan.
Kaltum da kakarta sun yi sa’a sun sami daki, a cikin dakin ma kaltum ta yi sa’ar samun hayewa kan tudun dake tsakiyar dakin. Dan tudun maidan tsawo ne da fadi daidai kwanciyar mutum daya don haka da ta shimfida xaninta aka ta yi filo da dan karamin bacco dake dauke da kayanta sai ta yada kai xata kwanta. Kakar tace ta daka mata tsawa tace “kaltum, kina da hankali kuwa! Ina kasa cikin kasa turmus ke ki sami mulmulallen tudu ki kwanta harda shimfida xani ki yi filo da jakar kayanki ni babu ko daya, to ki sauko kasa cikin kasar ki kwanta nixan haye tudun.”
Kaltum na karkarwar jiki don tsoro ta sauko da sauri, goggo fatu ta haye tudu harda juya baya ta yi kwanciyarta, kaltum ta mike a kasa cikin yashi ta kwanta, burinta ta kwanta da hakarkarinta ma kawai ta huta gajiya. Nan ma manyan mata suka dinga yi mata carin masifa wai sai ta matsa lungu ta babbake musu fili. Ba ta tankawa kowa ba ta takure a lungu ta yi shiru.
Bayan da kowa ya gama cuku-cukun kwanciya sai kowa ya yi shiru ya rufe ido kafin kiftawar ido barci mai dadi ya kwashe su, kan ka ce kwabo minshari ne iri iri ke tashi tun daga kofar gida xuwa tsakar gida har cikin dakuna kai ka ce busa sarewa ake ko kuma goga gurmi ake yi saboda tsabar gajiyar dake jikinsu.
Kaltum na runtsa idanunta barci mai dadi ya kwashe ta amma fa bata kai minti talatin ba ta ji ta yi wata mummunar firgita, ta xabura ta bude ido a xaune dabas ta tsinci kanta. Duhu kirin dakin ko tafin hannunka ba ka iya gani, ta duba gabas da yamma kudu da arewa sai taga kamar wani mutum dogo da fararen kaya a tsaye a bakin kofa yana tunkaro ta, nan da nan ta kwanta ta kudundune, jikinta na rawa tana makyarkyata ta fara addu’a kafin ta karasa wannan sai ta kama waccan addu’ar.
Irin wannan raxanar ceta afkawa goggo fattu wacce ta haye kan tudu. Gara ma kaltum akan goggo fattu saboda ita har girgixata aka dinga yi kai ka ce wani ne ya danketa yake wujijjigata. Ta galabaita sosai tun tana salati a cikin mayafi harta fara salati da karfi sai ta fara kwalla kiran sunan kaltum da duk wacce ta san sunanta a dakin. Can kaltum ta yi karfin hali tana cikin mayafinta tace “goggo, menene!”
Goggo tace “kaltum, xo ki sauke ni daga kan tudun nan shake ni ake yi ana girgixa ni kamar xa’a kifa da ni cikin kasa na kasa motsa jiki na.
To pa!!! ko me nene ya kawowa su goggo fattu gaisuwa, ban sani ba, se ku biyo mu dan jin yadda xata kaya.
.
To da patan littapin ya muku?
Kamar yadda na pada pls koda kalma daya ce ayi kokarin rubutawa kapin a pita... 🙏
.
Typing : Sadin Maa.
Post : Dan Aunty .👩ADON DAWA 2
.
Hankalin kaltum ya tashi yayin da tsoron da take ji ya sake karuwa ta bude ido a hankali ta waiga inda ta ke ganin farin abun nan sai taga babu kowa, ta tashi xaune a tsoroce duhu ne dai dumdum babu abunda take gani. Ihu dai kakarta ke rusawa har yanxu don haka kaltum ta bi inda sautin muryar ke fitowa tana lalube, can ta riko hannun goggo fatu kamar shokin din wuta haka kaltum ta ji a jikin hannun goggo. Ta yi karfin hali ta fisgo ta rim tsohuwa ta rikito kasa sannan ta ji salama.
“ihu waiyo kaina”. In ji shatu, matar da ke kwance a kusa da tudun ta dora kanta a kusa da goggo fattu. Kanka ce kwabo daki ya rikice da kace nace ashe kowace idonta biyu ashe tsoron ne ya hana su Magana tun daxu. Yadda barci ya gagari idanuwan kaltum da kakarta haka barci ya gagari sauran, matsalar ma iri daya ce ji suke tamkar an saka musu wayar lantarki, aka dinga wujijjiga su ana hajijiya dasu.
A waje daya suka taru suka cunkushe suka xauna saboda tsananin tsoro. Masu salati na yi, masu kuka suna yi, haka masu jawo Allah Ya isa na yiwa agents din da suka kawo su wannan daki duk da ma basu san a makabarta suke kwance ba har garin Allah Ya waye tangarai, sannan kowa ya fito tsakar gida, suma ‘yan sauran dakunan suka yi nasu bayanin cewar suma fa basu iya yin barci ba saboda tsoro, amma duk da haka da yawansu sun yi barcin su basu hadu da wannan matsala ba, basu ma san abunda ke faruwa ba.
Ana cikin wannan hali na jimami kungiyar Madigan tafiyar su (agents) suka shigo daga cikin gari suke inda suka kwana. Goggo ta ja agent dinsu cikin dakinsu ta nuna masa wannan gado nata wato dan tudun data haye xata yi barci aka dinga wujijjiga ta. Sai ya yi ajiyar xuciya, ya yi shiru can ya dago ya dubeta.
Ya ce “ai duk wani tudu da kika gani kama daga kofar gida xuwa tsakar gida har cikin kowannen daki to kabaruruka ne, domin nan tsohuwar makabarta ce”
Suna jin kabari sai kowace ta daka tsalle tayi gefe yayin da salati da koke koke ya barke.
Goggo fatu t ace “ka cuceni musa agent da baka sanar mana batun jiya cewar akwai kabari a cikin dakunan nan ba, da ban haye kai na kwanta ba. Daman ina ni ina kwana akan kabari da raina, ai dole in ji ba dadi. Amma ba laifin kowa ba ne sai shegiyar yarinyar nan kaltum ita ta jawo min, har nayi kwanciya a kasa na hango tat a liliye ta haye xata kwanta na sauko da ita na haye. Da bata hau ba ina xan yi tunanin hawa nima!”
Ta jawo kaltum tana ta duka kamar kullum yadda ta saba yi mata dukan tsiya dakyar mutane suka kwace ta. Kaltum ta yi kuka har ta godewa Allah ta rasa yadda xata yi da rayuwarta. Tabbas guxirin wasu ya dade da karewa, wasu ke taimakon wasu su dan samusu dan abinda xa su afa a bakin su don kada su mutu amma badan koshi ba. Irin wannan matsala ta fatara ce ta far ma kaltum da kakarta babu sauran garin rogo haka babu furar da xasu jika su sha.
Nan dai wasu agents su ka sissiyo gayan gurasa suka rarraba musu, ruwan sha ma na siyarwa ne masu sayar da ruwa akan jakuna ne suka kawo musu kudi aka sissiya musu aka tattarfawa kowa ya jika makoshinsa. Tundaga wannan lokacin dayawan su suka kwashi aljannu, fuf sai kaga an buge daya ta fadi fuk a kasa in anjima sai a buge wata. Kaltum na daya daga cikin wadanda suka gamu da irin wannan larura, furgita take yi tana xabura kamar xata arta da gudu sai a cafko ta a danne.
Bayan xuwansu da kwana uku da yamma jirgin ruwan da xasu shiga ya iso, daga kofar gidansu suke hango shi a cikin ruwa saboda girma gareshi sosai tamkar gida ne mai benaye hawa hawa.
Sai suke jiyo wani kara ‘tu tut u tu’ jirgin na yi kamar an kunna inji mai kara, da suka tambaya, me yasa injin din ke kara kada ya tafi ya barsu, sai masana suka sanar musu cewar ba tafiya xai yi ba kwana biyu xai yi a kunne ana wasa manyan manyan wukaken wadanda ke sakale a karkashin jirgin, amfaninsu saboda su dinga yanyanka manya manyan kifayen da ke cikin ruwa wadanda xa su iya tuntsirar da jirgin.
Sai da inji wasa wukaken nan yayi kwana biyu yana wasa su sannan aka kashe. Daga bisani aka umurci fasinjojin kowannen su ya kinkimo jakar kayansa ya taho bakin teku don tantancesu xuwa saudiya.
Kallo daya xaka yiwa fuskokin su ka tabbatar da labarin xuciyoyinsu ko ba komai dai xa su je suga ka’aba su yi addu’a baya ga albarkar dake cikin makka. Ba’a yunwa, ba’a kishirwa ballantana rasa mahalli mai kyau, duk tsiya dai a makka ba xa kai su cikin makabarta ba a kwantar das u, don haka sun fi son su tafi maimakon su yi xama a nan duk dab a su san wane irin kaskanci xa su tarar ba a makka.
Kaltum na dauke da jakunkuna biyu a hannayenta, nata da na kakarta har suka isa a bakin teku a inda su ka iska dogon layi mata da maxa a cakude kowa ta kansa yake, fargaba da harbuwar xuciyoyin jama’a ke faman tashi a wajen, musamman da jami’an bincike suka fara ware wadanda bisar su bata yi kyau ba, bisar bogi kenan. Duk wanda passport dinsa da bisa suka yi dai dai sai ya sungumi jakarsa ya shige jirgi yana murna, duk wanda kuwa tasa ta bogice sai ka ga an ce ya koma gefe ya tsaya.
Da aka xo kan goggo fattu aka duba passport dinta da bisa sai suka ga komai ya yi daidai don haka aka ceta nuna kayanta xa’a saka mata a jirgi ta nuna jakunkunansu nata dana kaltum ma aikaci daya ya dauka ya loda a karkashin jirgi ita kuma aka umurce ta da ta shiga jirgin.
An shafe fiye da mintuna goma sha biyar a kan passport da visa , kaltum ana bincike bincike yayin da dogon larabci ya balle tsakanin ma’aikatan da agents dinta musa daga karshe suka gaskata visar kaltum ta bogice, baya ga passport din wani aka lika hotonta, don haka suka turata gefe. Haka itama kawar kakarta da take bayan kaltum mairo matsalar visar bogece ta far mata don haka aka tura ta gefen su kaltum, itama ta dauki kuka ta je ta tsaya ita da jikarta rakiya.
Goggo fattu na cikin jirgi a xaune shiru shiru kaltum da kawarta mairo basu shigo ba don haka ta fara tambayar wadanda suke shigowa.
“ina kaltum! Ina mairo da rakiya!”
Aka sanar mata kaltum da mairo an ware su gefe saboda rashin visa mai kyau, don haka basu tafiya. Goggo fattu ta yiwa ma’aikata magiya su taimaka mata su barta ta fito daga jirgin ta xo ta iske su kaltum xata yi musu Magana, da kyar suka bar tata fito ta taho da sauri in da suke tsaye a gefe. Kaltum na ganin kakarta sai ta fashe da kuka ta rike ta, tana cewa”goggo fattu xa ki tafi ki barni anan ban san kowa ba, ban san inda xan je ba!”
Goggo fatu ta girgixa kai t ace “babu yadda xan yi, ba laifina bane, laifin agent ne, ni dai na bashi kudin komai don haka ga ku ga agent ku rike shi, shi xai san yadda xai yi da kawo ku.”
Ta juya ta dubi mairo kawarta tace “mairo ga kaltum nan amana a hannunki”
Kuka ya hana kaltum da mairo Magana, jikin goggo fattu yayi sanyi da alama ta tausaya musu ta juya ta koma cikin jirgi yayin da kaltum ta fasa kuka mai tafe da tsananin takaici. A haka har aka gama duba kowa masu shigewa suka shige, mutane arba’in da takwas ne kadai aka rage a kasa ,talatin mata, goma sha takwas maxa, suna ji suna gani aka rufe jirgin sannan suka daina kallon sa.
Sai su sai sauran agents din da basu tafi ba, nan fa kowa ya rike rigar agent dinsa yana hayagaga. Suka tabure akan basu yarda ba a tafi a bar su, wannan ai ha’inci ne bayan suma kudi suka biya yadda wadancan suka biya. Bayani dai daya ne agents suke yi musu shine suyi hakuri su kwantar da hankalinsu xa’a je a gyaro musu nan da kwanaki biyu xa su tafi suma. Akan wannan sharadi ne su kaltum suka hakura suka saki rigarsu da suka cukuikuiye suka rike.
Da agents suka samu aka sake su sai suka sulmiye suka gudu, yayin dasu kaltum suka koma cikin dakunan su suka xaxxauna suna jiran tsammani.
Babban tashin hankaln da kaltum ta shiga shine gaggo fattu ta tafi da jakar kayanta sannan bata bata ko sisi ba, dan sauran kudin guxurinsu kacokan yana aljihunta ta tafi dasu don haka kaltum daga ita sai kayan jikinta.
Riga da xani da dankwali ne na atamfa nichem koriya saidan yalolon mayafinta baki da sidadden silifas wanda ya fara hujewa a sanadiyar wahalar da suka sha a hanya.
Yanxu mutane tara ne a dakin su kaltum, iya mairo da jikarta rukayya ‘yar kimanin shekaru goma sha biyu, sai amina, jidda’u, huwaila suma ‘yan mata ne iyayensu sun haye sun barsu shekarunsu basu wuce tsakanin goma sha hudu xuwa sha shida ba, gaba dayansu daga garin kwalfau suke a janhuriyar niger. Sai kuma hajara baxawara ce shekarunta ashirin da biyar ‘ya’yanta uku suka rabu da mijinta ta xubar dasu ta xo niman kudi ita kuma er garin matamaye a jamhuruyar niger. Sauran biyun kuma manyan mata ne maimuna daga xangon daura sai madina daga kaxaure dukkaninsu tsakanin shekara talatin da uku ne xuwa talatin da biyar, suma sunyi aure aure sun hayayyafa sannan suka ballo suka fito neman salamar rayuwar saboda al’amura sun tsananta a gare su. Sauran dakunan ma haka suka karkasa kansu wasu su goma, wasu su biyar, wasu su bakwai suka xauna suna xaman jiran agents.
Hakika kaskanci da wulakancin dasu iya mairo suke yiwa kaltum a dakin abun ya kaxanta a sanadiyar bata da guxuri, sukan bata dan abun da xata kai makoshinta amma bai taka kara ya karya ba, haka idan suka sayi ruwan sha mukurwa daya kacal suke bata ta jika makoshinta da alama yunwa da kishirwa sun fara cin jikinta a galabaice take baya ga datti da kura da suka addabi jikinta tamkar tababbiya xaka ganta, hawaye kadai ke yawan wanke kurar fuskarta. Tana manne a lungu a takure babu eh babu a’a, ga tsananin tsangwama da carin da rakiya , jidda’u, da amina da huwaila ke yawan yi mata saboda sun ga bata ramawa tsananin hakuri da tsoron da take ji. Mace dayace ke raga mata a dakin itace ke tausaya mata, mai hana yawan tsangwamar da ake yi mata itace madina, wani lokaci su ji maganar madina su bari wani lokqci su ki bari, itama ta sami rabon nata na rashin kunyar su.
Madina ceke xubawa kaltum dan abinci a murfin kwano idan sun xo cin abincin, amma sauran saisu juye mata baya idan sun tausaya mata ne suke yafito mata lauma daya su bata a hannu ta karba da sauri tana godiya da murna sannan ta ci ta lashe hannu.
Tafi tafi suka cika sati guda cur agents suna yi musu karairaye daga wannan satin basu sake ganin agant ko daya ba dukkansu sun sulale sun gudu Nigeria sun barsu anan a yashe babu tafiya babu alamarta . don haka suka tabbatarwa da kansu sun shiga tsaka mai wuya su basu je saudiya ba su basu ba’a dawo dasu Nigeria ba saboda haka hankalinsu ya kara tashi matuka babu wanda baya kuka matansu da maxansu, yara da manya. Daga nan suka sakawa a ransu nan ne garinsu na dun dun dun, xama ne xa su yi shi marar iyaka, sun fitar da xaman tsammanin yau ko gabe xa su bar sudan, don haka suka fara tunanin abunyi, ta ina xasu fara neman abunda xasu ci gaba da rayuwarsu.
Yadda suka sami tarihi daga wajen hausawa maxauna garin cewa babu wata sana’a da xasu iya yi anan su samu kudin da xasu iya rike kansu in dai ba bara ba sai kamun kifi a kogi wato ‘su’. Don haka barace ta kama su dole su xama almajiran karfi da yaji.
Hankalin dukkanninsu ya yi matukar tashi da suka ji Kalmar “bara” sun yi nadamar barin kauyukansu da kasarsu suka taho sudan. Haka su ka yi kuka mai tsanani da suka ji tarihin cewar dukkanin hausawan dasu ke gani a garin suma irin wannan abun daya same su shi ya faru dasu tun suna goye iyayensu suka xo suka yada xango anan da ximmar tafiya saudiya, su basu tafi ba sannan ba a komar dasu Nigeria ba. Iyayensu suka mutu suka bar yaran a xube suna walagigi har suka girma basu san danginsu ba suma har suna aure aure suna hayayyafa a junansu. Don haka ana basu tabbacin ba lallai ba ne su haye saudiya kuma ba lalle ba ne su koma Nigeria har abada.
BABI NA BIYU
Yan asalin garin bur sudan wasu ne da ake kira jange, akasarinsu ko ma ince dukkaninsu bakake ne wulik wulik masu tsananin tsawo da bakar fata wacce hakoransu ne kadai fari a jikinsu hatta kwayar idonsu jajaye ne ba fari ba,. Ba musulmai ba ne, don haka basu da tausayi ko kadan babu abunda suka sani sai fadace fadace, yanxu nan sai kaga fada ya tashi a junansu ko da wasu kabila daban saisu dauko wuka su soka ko su fardewa mutum ciki.
Fada na tashi xa ka ga sun fasa kwalba sun sokawa mutum don haka suka xama abun tsoro, abun kiyayewa da taka tsan tsan suna Gadara suna yiwa baki abunda suka ga dama saboda garinsu ne babu mai hana su. Ga su yawancin su shanmashune ma’ana ‘yan shaye shaye ne baya ga bin mata da suke yi, su danne su a lungu. Don haka hatsarin xaman su kaltum agarin nan ya karu.
Gidajensu ko ma in ce dan karamin kauyensu yana bayan gidan su kaltum, da akwai yar tafiya maidan nisa kasancewar gidan su kaltum su kadai ne a unguwar daga su sai ruwa a gabansu, gefensu na hagu bola ce babba, gefensu na dama makabarta ce katuwa wacce ta bullo har cikin gidansu. Bayansu kuma gidan karuwai ne da ‘yan shaye shaye. Duk ranar laraba jami’an tsaro na kawo surname suna cafke karuwai suna sakawa a mota suna tafiya dasu dan haka su kaltum basa tausayin xuwa ko bita wajen don kada kamen ya shafe su. Idan aka kama su hukunta su ake yi sosai sannan a dauresu a kurkuku.
Baya da garin jange sai kuma garin ADON DAWA suma kauyensu na gefen kauyen ‘yan jange. Sunan Adon Dawa ya samo asali ne daga wajen hausawan da suke xaune a nan, sun saka musu suna Adon Dawa saboda su wata kabila ce a cikin dawa suke xaune. Sun yi kama da bararoji, suma yarensu daban ba larabci ba ne, haka ba yaren jange ba ne, yaransu daban ne amman suna jin larabci. Akasarin su ba musulmai ba ne, amma suna da musulmai da yawa a cikin su. Arnan cikin su a shekara sau daya suke canja kayan jikinsu matansu da maxansu, yaransu da manyansu sai shekara ta xagayo. Suna da kyau sosai sun fi jange duk da suma yawancin su bakake ne amma suna da dogon hanci da gashi mai laushi ga tsawo.
Suna da kudi sosai amma kudinsu bana ci ba ne, saboda suna shiga manyan burane su gina tsala tsalan gidaje masu kyau na xamani da kudin su saisu xuba ‘yan haya sannan su dawo dawa suyi gidan katako su xagaye da kaya su xauna a ciki. Babu wani abu da xa’a iya dagawa a gidan a sayar dashi naira dubu daya, babu gado, babu katifa balle kujeru. Sai daisu xagaye dakunan su da tobe wato lafaya sai gadon karfe wanda aka yi tsakiyar da igiya babu xancen katifa akai sai tsummukarai. Yawancin kayansu bakaken yadi ne maxa su dinka ‘yar shara da wando iya kwairi, su hada da bakin rawani. Mata kuwa rigace shimi da xani da katon mayafi ko lafaya saisu yane jikinsu.
Baya da ginin gidajen da suke yi a burane su xuba ‘yan haya suna da sana’o’I kala kala, wasu suna da shanu don haka suna samun madara saisu xuba madara a doguwar buta maidan karamin baki ta tasa ce amma an yi mata kira kamar ta tulu, sai suyi ta jijjigawa har sai ya xama nono sannan su dora butocin akan jakuna su shiga gari su siyar, wasu kuwa a kasuwa suke sayar da dabino, namijin goro ko hatsi.
Su na da kasuwansu a tsakiyar kauyensu mai suna jim arab, ko da yaushe suna siye da siyarwa musamman da yamma. Yawancin abunda xaka ga ana yi a cikin kasuwar shine caca, kungiya kungiya sai kaga suna caca, suna yi suna shewa, ana ihu, suna ta shan taba da jabna.
Jabna, wani shayi ne da suke sha a dan kankanin kofi. ‘ya’yan jabna kanana ne koraye, saisu soya shi ya xama baki sannan a daka yayi laushi sai a kwarara ruwan xafi a xuba dan sikari ko a shah aka. Idan ka sha jabna xaka ji tamkar ka kurma ihu saboda bauri da daci gashi baki kirin sai daisu da suka saba sha ya xame musu tamkar naman kaxa ko soyayyen kwai don dadinsa da suke ji. Sun xamarda shi tamkar abincin su don da yawan su suna sallama abincin shi kadai suke sha saisu kora da taba shi yasa dukannin su suke sirara mararsa kiba sai tsawo tsigigi. Yini suke suna dafa jabna akan garwashi a cikin ‘yar buta suna xubawa a ‘yan kofuna suna sha iyakacin jin dadin rayuwar su kenan duk da tarin dukiyar da Allah Ya basu basa ci a cikin su ko su saka a jikin suba.
Daga nan kuwa tafiya ce mai yawa xuwa babban garin wato sudan bahari, inda suke da gine ginen siminti da benaye manya manya, titian da tsala tsalan motoci, manyan shaguna da wuraren cin abinci masu kayau, ga kasuwanni manya manya. A nan kasuwar hausawa take mai suna hajarar ases, anan xa ka ga hausawa burjik sai ka rantse a kano kake , matansu da kuma maxansu da kuma yarans. Mata na sayar da abincin hausawa iri iri, irinsu tuwo, kunu,koko,kosai, shinkafa da miya da salad. Maxa kuwa wasu suna yin kaho irin wanda ake kafa kahuhuna a bayan mutum a tattaro gurbataccen jinni sai a dan tsatstsaga a xuke gurbatacen jinni. Wasu na yin aski, wasu na sayar da magungunan gargajiya. Sunan kudin da suke kashewa ‘sudan jine’ misali kamar naira dayanmu saisu kuma su ce wahid jine.
.
AlhamduLillah,
gida yana kan parpadowa, naga mutane da dama sun bada gudumowa wajen comments da likes.
Naga sunan koma kuma nima na danbara masa like....
Godia ta musallam gare ku duka...
Ga wanda basu samu damar yin commnts ba, dan Allah yau a daure ayi koda kalma daya ce,
kowa da tasa uzurin, ban san mai yake hana ku ba, to idan baza asamu damar commnts ba pls a daure ayi like ko share kapin a pita, yazama kowa ya bada tasa gudumowar.
Ku tuna idan babu ku babu mu,
idan bakwa nan babu admin din da zai iya post, kuma haka idan babu mu babu mai karatu a cikin gidan nan,
ina kara rokon ku da kowa ya bada tasa gudumowar pls....
Sai kun jini dauke da wani sabon shirin..
Sai na gan ku....
.
Typing : Sadin Maa.
Post : Dan Aunty.❤ADON DAWA 3
BABI NA UKU
A lokacin dasu kaltum suka cika sati uku a bur sudan dole tasa suka fito neman abunda xa su kai bakinsu, mata da maxa, yara da manya kowa ya ja xugarsu suka shiga gari.
Tawagar ‘yan mata su biyar kaltum, rakiya, huwaila, jidda’u da amina suka fankama garin ADON DAWA don yin bara. Suka kuwa ci sa’a suka samo kudi da yawa wanda xai ishesu su ci abincin yinin yau. Kalmar da suke ambata itace “karama fisabilillahi” sai kaga an miko musu kudi. Su kan basu wahid jine wato kamar naira daya kenan, wasu se su basu hamsin jine ficika kenan idan kuwa suka ci sa’a sai a rana daya saisu hada maitan jine daga nan saisu wuce cikin gari maka makan wajen sayar da abinci (restaurant)su sayo abunda suke so, kamar su kisra wato sinasir ko su sayi esha wato gurasa, wani lokaci saisu hada da ful. Ful wake ne manya manya sai a dafa shi ba gishiri ana ci da gurasa. Idan suka samo kudin bara da yawa saisu sayi baitil mandi shima dafaffiyar shinkafa ce fara sai a kwarara madara akai, a yanka tumatiri da albasa, a yanka karas da kabeji, sannan a dora gasashshiyar kaxa a barbada dan gishiri sannan a ci.
Daga dukkan alamu yunwar da ke addabar su ta fara sauki har sun sami karfin da suke iya debo bokitai da manyan darukan ruwa akansu, su niki tafiya mai nisa sannan su samo ruwan da xa suyi amfani dashi wajen wamka, wanki da wanke-wanke. Ta cikin makabarta suke bi sannan su isa gabar kogin da suke debo ruwan.
Ruwan baya shawuwa saboda jajawur ne mai dandanon gishiri.
Jikin kaltum yakan yi sanyi har takan fashe da kuka idan taga yadda ake binne mutane a makabarta. Saboda sahara ce don haka suke yin dogon rami mai xurfi sosai, wanda mai hakawar sai ya shige ciki sosai yayi xurfi.sai an daina hango shi sannan ya miko hannunsa a kamo shi waje dan ba xai iya fitowa ba. Sannan saisu taru su saka gawa, sannan su jera bululluka a maimakon itace saboda yashi ne itatuwa ba xa su tsaya ba. Allahu Akbar!
Allah Ya sa mu cika da imani, Y a jikan musulman da suka riga mu gidan gaskiya.
Ameen.
A yau kaltum bata bisu bara ba saboda tana son ta wanke kayan jikinta kwaya daya kacal, yayi dakun dakun har gefen xanin ya yage don haka ta yanke shawarar sai kowa ya tafi bara sannan ta rufe gida ta cire kayan ta wanke ta xauna ta jira ya bushe sai ta yi wanka ta saka. Da ta tabbatar mata da maxa sun fita daman tun da sassafe ta debo ruwan wankinta, sai ta tsinci guntayen sabulai ta harhade ta ajiye. Suna ficewa sai ta rufe kofar ta fara wanke riga da dankwali da mayafin ta shanya ta koma gefe ta takure tana jiran su bushe.
Ta duba gabas da yamma, kudu da arewa na gidan sai tace a ranta “yanxu fa a makabarta muke rayuwa alhalin muna raye.”
Ta sake duban katon tudun kabarin da yake gefenta ta mika hannu a hankali ta shafa tace, “ko mace ce ko na miji ne a cikin kabarinnan Allah Shi ya barwa KanSa sani. Allah Ya jkansu da gafara.”
Ta ji hawaye yana sirnanowa daga idanuwanta don tausayin kanta da irin matsananciyar rayuwar da take ciki. Ta tuno gwaggo fattu wacce ta kawo ta nan ta ajiye ta ita kuma ta haye ta yi tafiyarta makka tana can tana jin dadin rayuwarta.
Babban tashin hankalin shi ne iyayenta basu san halin da take ciki ba don su a tunanisu tana saudiya kuma tasan mugun halin gwaggo fattu ba xata yi waya ba ko ta aika wasika ta fada musu gaskiya ba sai dai ta bar su a haka, suma kuma iyayen nata ba waya gare su ba balle su san lambarta ta makka su buga mata su tambayi halin da take ciki. Kaltum ta fi jin haushin iyayenta su da suka yarda suka yarda suka bayar da ita aka taho da ita don basa tausayinta. Ta ji ta tsani kowa a duniya kamar yadda kowa baya sonta, sai ta fashe da kuka mai tsananin ta kifa kai a jikin katakon dakin su. Kuka take yi haikan amma tana fada cikin daga muryar ta “inna lillahi wa inna ilaihi raji’un”
Tsananin bugun da ake yiwa kofar gidan ne ya sata tsagaita da kukan da take yi, ta kasa kunne tana sauraro sannan ta gaskata wani ne yake buga kofa. Sai ta mike tsaye ta yi wuri wuri tana tunanin yadda xata yi. Shawara take yi shin ta je a haka da daurin kirji ta bude kofar, sai dai ai bata sani ba mace ce ko na miji! Idan namiji ne ba xata iya tsayawa da daurin kirji a gabansa ba musamman yadda maxan suke ‘yan iska ko wanka ka ke yi idan baka kula ba saisu yi ta liken ki. Haka idan ki ka yi sake a daki kina barci baki killace jikinki ba sai dai ki ga suna ta xirga xirga ta kofar dakinku suna kallonki a dole wucewa bandaki su ke yi, ko suyi ta leke ta hudar katakon musamman dakin su kaltum da yake kunshe da ‘yan mata.
Ta ji sautin bugun kofar ya kara tsamari don haka ta yayimi jikakkiyar rigarta ta saka ta jawo jikakken mayafinta ta sharba a kanta ta goge idonta saboda hawayen da yayi mata kawanya. Ta isa da sauri bakin kofar ba tare da ta tambaya ba ko waye ta ja sakata ta bude game da wangale kofar. Jikinta na rawa ta dubi wacce ke bakin kofar sai taga madina ce tayi sauri ta duka a tsorace.
Ta ce “sannu da xuwa, yi hakuri ban xo na bude miki kofa da wuri ba ina kokarin saka rigata ne.” madina tayi murmushi t ace”lah ai ba komai kaltum.”
Kaltum ta mika hannu xata kar bi himilin daurin kayan dake kanta sannan ga leda a hannunta. Madina tace “bar shi kaltum, ba komai ba sai kin taya ni ba ai na xo gida mu shiga ciki.”
Kaltum ta dawo tsakar gida inda ta cire jikakkiyar rigarta da mayafinta ta mayar kan igiya ta shanya. Madina kuwa ta wuce cikin dakinsu kai tsaye ta xarce kan kwalin shinfidar ta da jakar kayanta a gefe ta ajiye himilin tsummakaron da ta samo. Ta fito tsakar gida inda kaltum ta daga ido da sauri ta dubeta sai suka yiwa juna murmushi a lokacin guda. Kaltum ta mayar da kai kasa don kunya da girmamawa. Madina tace “kaltum me yasa yau baki fita bara ba!”
Kaltum ta dan yi murmushi tace “kayana ne suka yi datti nake so na wanke sai sun bushe sannan in fita.”
Madina tace “ me yasa sai sun bushe xaki tafi, ki wanke ki shanya sai ki saka wasu kayan ki tafi ki nemo abunda xaki ci, yaushe xa’a ce tun safe baki karya ba har rana tayi yanxu kina jira sai kaya sun bushe!”
Kaltum ta langwabar da kai gefe tace, “ai bani da wasu kayan, kayan jikina ne kadai nake da su, kakata ta tafi da kayana hade da nata ta haye tana cikin wadanda suka tafi makka.” Hawaye ya sarnano daga idanuwan kaltum.
Madina ta tambayeta cike da mamaki tace “au iya mairo ba kakarki bace daman!”
Kaltum tace “kawar kakata ce, garinsu daya tare muka taho dasu, rakiya ce jikarta.”
Tsawon mintina biyar madina tayi tana kallon kaltum saboda tsananin tausayin ta da ya lullube mata xuciya, ta rasa kalma guda daya da xata iya furta mata. Tana tausayin kanta da kanta, amma ta fi tausayin kaltum yarinya karama ba uwa ba uba, ba dangin iya balle na abba a kasar da bata taso ba.
Kaltum ma ta yi shiru kanta a sunkuye a kasa sai kwalla data cika mata ido ta rasa abunda yake damunta saboda kuncin rayuwa.
Madina ta yi ajiyar xuciya ta share hawayen daya cika mata ido, sai ta shiga cikin daki inda ta kwance daurin tsummakaron data shigo dasu ta fara daddagawa tana warewa. Kala biyu riga da siket ta debo ta fito ta mikawa kaltum, kamar an xare mata laka haka ta mika hannu ta karba. Ta kurawa madina ido tana sauraron abunda xata fada, madina ta juya xata shiga daki sai kaltum tace,” wanke miki xanyi!” sai dai babu sabulu, nima guntayen sabulai na tsintsinto a bandaki na yi nawa wankin.”
Madina ta waiwayo ta dubeta sai tayi murmushi t ace “a wanke suke, baki nayi kyauta ki saka nima yanxu nan aka bani su sadaka a garin ‘yan Adon dawa.”
Farin ciki ne bayyane hade da mamaki suka halacci fuskar kaltum ta yi murmushin da har saida wushiryarta ta bayyana yayin da gafen kumatunta ya loba wato (dimple) ta dago da fararen idanuwanta dara dara ta dubi madina ta fada cike da annashuwa.
“anty kin bani kyauta in saka!”
Madina ta yi dariya tace “na baki kyauta kaltum, me ye sa kike mamaki!”
Kaltum, ta sunkuyar da kai kasa ta yi godiya sannan ta fara warwarewa tana duddubawa farin ciki fal a xuciyar ta. Kafin madina ta fito daga daki kaltum ta saka riga da siket cas da ita kuwa kamar dan ita aka saya daidai jikinta sun yi matukar yi mata kyau. Madina ta fito daga daki dauke da wata bakar leda a hannunta tana duban kaltum sai suka yiwa juna murmushi a lokacin guda. Madina ta yaba da yadda kayan ya karbe ta, sannan ta samu inuwa ta xauna a kasa ba tare da ta nemi wani abu ta shinfida ba. Kaltum ta jefa xanin da ta kunce a cikin bokitin data adana sauran kunfar data wanke riga da mayafinta ta fara sabawa . madina ta kwance leda sai ga kisra da ful.
Madina ta dubi kaltum tace “xo mu ci abinci yarinya”
Wannan kalma ta bawa kaltum matukar mamaki wanda har yasa ta dago da sauri ta dubeta har na tsawon ‘yan dakiku masu yawa ta kasa Magana, can ta yi murmushi.
Ta ce “na koshi, nagode.| madina tace, “me kika ci da xaki ce kin koshi.! Ki saki jikinki da ni ki xo mu ci ai xai ishe mu daman dayawa na siyo in ci yanxu sauran inci daddare ba komai, Allah de bani wanda dan ci daddaren.” Tsananin yunwa ce daman ta addabi cikin kaltum banda kugi babu abinda cikinta yake yi saboda ya fafake babu komai tun a bincin jiya da rana bata sake samun abunda xata sakawa hanjinta ba. Ta ajiye wankin ta goge hannayenta ajikin siket din dake jikinta ta karaso a hankali inda madina ke xaune, cikin kunya da nutsuwa ta xauna yayinda hannunta ya dau rawa a lokacin da take kokarin gutsurar gurasar madina ta dubeta, sannan ta tambayeta cike da mamaki.
Ta ce “kaltum lafiya, meke damunki, ya naga kina karkarwa kuma duk kin tsangwami kanki! Haba kaltum ki saki jikinki ai ba wani abu bane duk wanda ya taimaki wani shima Allah xai taimake shi.” Kaltum ta sunkuyar da kai kasa ta fada cikin sanyin jiki.
Ta ce, “ina mamaki ne saboda tun a mota kowa ta kansa yake babu mai taimakon wani ko dai dai da mukurwar ruwa ne sai naga kin bani sutura kyauta sannan kin siyo abinci kince in xo in ci shine na keta mamaki.”
Madina ta yi murmushin karfin hali ta dafa kafadar kaltum tace “yarinya ba haka bane duk masu yin haka jahilai ne, babu yadda xa'ayi musulmai su hadu a waje daya su ce babu wanda xai taimaki dan uwansa musulmi. Babu mai imani ga duk musulmin daba xai so wadan uwansa abunda ya sowa kansa ba.
Ko a lahira aikinmu ba xai kaimu shiga aljanna ba sai dai alfarma albarkacin masu albarka. Kaltum, ki cire wannan mugun tunani a ranki, ki dauka a xuciyarki duk runtsi duk talaucin da kike ciki komai kankartar abu xaki taimakawa wanda ki ka fi ko da babu mai taimaka miki domin Annabi Muhammad (S.A.W) y ace “hannun da yake mikawa shine a sama, ya fi hannun da yake karba shine a kasa.”
Babu wanda kaltum take yi sai gyada kai hakika tana gamsuwa da abunda madina take fada mata. Suka ci, suka koshi suka kora da ruwa sannan kaltum ta yi godiya ta tashi ta je ta ci gaba da wankinta, ta dauraye ta shanya. Dai dai lokacin iya mairo da tawagarta suka shigo, a jigace suke saboda tsananin yawon bara da suka yini suna yi da alama kuwa kwalliya ta biya kudin sabulu saboda kowaccensu hannunta dumu dumu da ledoji. Cikin fara’a kaltum ta tare su gani da yi musu sannu da xuwa. A tunaninsu kwadayin abunda suka samo take don haka kowa ya tsuke fuska babu wanda ya amsa gaisuwarta sai ma dai kauce mata suke yi suna kewaye ta suka nufi daki.
Iya mairo ce ta tsaya tace mata “sannu isashshiya ‘yar gata wacce bata iya wahala ba, kowa ya fita nema ke kina kwance a gida wa xai nemo ya baki a wannan marrar da nafsi nafsi babu mai taimakon wani, keta wanki ma kike yi. Waye ya baki aron Kaya ko kin fara tsayawa sai kinga ba kowa ki bude jakunkunan mutane ki daukar musu kaya! To kada ki sace kayan wani a kama ki kice kin sanni ko kice ni kakarki ce.
Rakiya ma ta leko daga daki ta tsoma baki tace “tun shigowata nake kallonta daga gani kayan nan na wani ta sato saboda bai yi kama dana bola ba kuma bata fita bara yau ba. Tun da safe ta debo ruwan wanki bata kara fita ba.” Sai sauran ma suka tsoma baki babu wacce bata yi mata cari ba a cikinsu.
Kaltum tadago da sauri ta dubi madina yayin da madina ta yi mata nuni da hannu alamar ta yi shiru kada tace komai. Kaltum ta sunkuyar da kanta kasa sai wani kuka na takaici ya kece mata marar kakkautawa. Ta koma gefe ta tsugunna tamkar almajirarsu yayin da kowaccensu ta shiga daki ta baje ledar abincita suka ci. Wasu shinkafa ce da miya, wasu baital mandi, wasu taliya, wata macaroni. Abun mamaki sai suka dinga yiwa madina tayi wai ta xo su ci. ta ce ta gode a koshe take amma babu wacce ta tuntubi kaltum.
Wani kululun takaici ya tsayawa kaltum a wuya ta fara tuhumar kanta tana tambayar xuciyarta wane irin mugun hali nake yiwa mutane haka suka tsane ni! Me nake yi wanda kowa baya sona aka tsane ni!”
Sai tayi xunbur ta mike ta shiga daki wajen shinfidar kwalinta ta dauko robar cin abincinta, yayin da kowacce ta dinga kare abincinta wasu ma suka fara daure ledar abincinsu a tunaninsu rokarsu xata ta yi, ta dube su duba irin na takaici ta langwabar da kai ta matse hawaye sai ta fice, ta yayimi gyalenta ba tare da ta yiwa kowa Magana ba har madina da take xaune a tsakar gida a wajen da suka ci abinci har yanxu bata tashi ba.
Fitarta kofar gida keda wuya sai ta tsaya cak ta dubi gabas da yamma, kudu da arewa babu abinda take gani sai tulun bola da kabarurruka yayin da gabanta kuwa katon kogi take hangowa yana ambaliya. Ta ji a ranta tamkar ta fada kogin nan ruwa ya hadiyeta ta mutu ta huta da bakin cikin rayuwa sai kuma ta tuna da wa’axin da aka yi musu a makarantar islamiyya cewar duk wanda ya kashe kansa ya mutu a kafuri. Ta juya ta dubi kabarurrukan da ke gabanta sai tayi sha’awar dama ace ita ce a ciki a mace ta mutu an binne ta. Ta ji a ranta rayuwar wadannan bayin Allah da suka mutu ta fi mata irin rayuwar da take yi a duniya jin dadi da kwanciyar hankali.
Kamar daga sama ta ji Magana a bayanta, ta waiga da sauri saida suka hada ido da madina.
Ta ce “kaltum ina xaki je!”
Kaltum ta saki fuskarta ta yi murmushin karfin hali. Ta ce “xan je bara.”
Madina tace ki kula da kanki, shawarar da xan baki itace kada ki je garin jange saboda kin ga ke yarinya ce akasarinsu kuma ‘yan iska ne gara ki je garin Adon dawa tunda su na da musulmai xa su fi tausaya miki. Hadari ne ma ki dinga tafiya ke kadai ba’a tawaga ba saboda irinku suke so ‘yan mata ba kamar mu ba manya ba damuwa.
Kaltum ta gyada kai tace “to anty bari in je garin Adon dawan.” Ta juya ta tafi yayin da madina ta dade a tsaye tana kallonta har saida ta kure ta daina hango ta sannan ta girgixa kai don tsananin tausayin kaltum ta shiga gida.
Kaltum tafiya take amma fa har yanxu bata fasa kuka ba harta iske gidajen Adon dawa. Ta fara shiga gida daya bayan daya, Kalmar da take ambata itace “karama fi sabilillahi”
Da alama yau bata fito da sa’a ba daga inda ake kyaleta ta yi ta bara ta gaji ta tafi da kanta sai inda ake yi mata korar kare. Ta yanke shawarar tunda yamma tayi yanxu duk maxan suna kasuwa bari ta je can ko Allah xai sa ta dace. Kaltum ta kama hanyar jim arab, nan ta iske dandaxon maxa kungiya kungiya suna sha’aninsu wasu suna caca, wasu kuwa suna hira suna shan jabna, yayinda wasu suke saye da sayarwasu. Kaltum na fara bara sai ta ci sa’a duk rumfar da tayi bara sai a miko mata sadakar wahid jine wato kamar kandala, farin ciki ya lullube xuciyar kaltum don ada ta shiga wani mawuyancin hali tana tunanin yadda xata yi in har bata samu ko kwabo ba idan ta je gida xasu kusa cinyeta da baki bayan wulakancin kala kala.
Ta ci gaba da bara harta karkashin wata inuwa inda dandaxon samari ne xalla, sun shinfida katuwar tabarma suna ta shan jabna suna caca. Sun kaisu goma sha biyu dukkanninsu shekarunsu basu wuce ashirin da biyar xuwa ashirin da bakwai ba. Shewa da ihu kawai suke yi da alama basu da matsala a rayuwa. gasu a kauye, a cikin gidajen katako da katangar kaya yayin da suturar jikinsu bakin yadi ne mai layi layin fari wacce suke dinka ‘yar shara da wando iyaka guiwa amma koda yaushe sai kaga suna farin ciki ko me yasa. Kaltum take xayyanowa aranta sannan ta bawa kanta amsa “tabbas dole suyi farin ciki a rayuwarsu saboda suna tare da iyayen su, a garinsu, kuma ga dukiyoyinsu” ta katse tunanin da take yi da ta ji suna tambayarta “lafiya, me kike nema a wajenmu!”
Tayi firgigit t ace “karama fi sabilillahi.” Kalma daya ta ji wani daga cikinsu ya fada a cikin yarensu sai taga dukkaninsu sun waiwayo sun kalleta a lokaci guda. Ta yi sauri ta sunkuyar da kanta kasa, da tadago taga har yanxu suna kallonta, sai ta sa gefen gyalenta ta rufe da fuskarta. Daga karshe ta yanke shawarar gaggauta barin wajen tun kafin su iskance ta.
Cikin harshen larabci daya daga cikinsu yace ta xo, kasancewar tana jin larabci sosai tun tana karama sai ta juyo ta dawo wajensu a nutse cikin ladabi amma fa duba daya xaka yi mata ka tabbatar a tsorace take. Ya dubeta sama da kasa duba irin na kurulla yayi dariya ya shafa baki don haka kaltum ta fara fuskantar manufar kiranta da yayi, sai ta fara ja da baya.
To pa, ko ya data kasance tsakanin kaltum da en samarinnan!
Sai ku biyo mu dan jin yadda xata kaya..
.
Typing : Sadin Maa.
Post : Dan Aunty. 👫️ADON DAWA 4
Ya fada cikin shagobe “ke me kyau, yaya sunanki!”
Ta na mkyarkyata tace “kaltum”
Su dukka suka maimaita sunan “kaltum” a lokaci guda suka ci gaba da dubanta suna kwada kyawunta, suna mamakin kyawunta don basu xata akwai masu kyau a cikin bakin almajiran nan ba saboda sun dauke su wulakanttatun bayi.
Daya daga cikin su ya dubi shugaban tawagar mai suna Mambela wanda har yanxu bai ce komi ba sai duban kaltum yake yi kasa kasa.
Cikin yarensu yake Magana yace “ranka ya dade shugabana mambela kai ka dace da kyakkawar halittar nan, du da de ba niman mata kake ba, lallai tana da kyau kuma ta hadu. Ya kamata a mika maka ita cikin shagon nan kawai in ka gama sai ka bata alif jine (dubu daya) ka ga sai tayi sati tana cin abinci, gobe xa ka ga ta dawo da kanta.”
Duk da cewar a cikin yarensu ya yi Magana bata ji duk abubuwanda yake fada ba amma ta fuskanci abunda yake fada, don haka sai ta juya da sauri ta fara tafiya. Mambela yace “tabbas yarinyar na ta dace da ni don haka ku dauko min ita, ku shigar min da ita cikin shagon nan.” Ba tare da bata lokaci ba kartai hudu suka bi ta da gudu suka damkota cak suka daga ta kamar kaxa suka nufo inda mambela ke xaune. Tuni robar bararta da yan kudaden data samu suka waste a kasa, ta kurma ihu kai kace rai ake xare mata.
Cikin kuka tace “inna lillahi wa’inna ilaihi raji’un. Laa ilaha illa anta subhana inni kuntu minaxxawalimin.”
Mambela yace su ajiyeta kasa a gabansa yayin da ta xabura da gudu sai ya damki hannunta ya fada cike da damuwa cikin harshen larabci.
Ya ce”kaltum bkya son kudi ne! bakya son mambela dan sarki, mai kudi da dukiya!”
Ta fada cikin firgicewa da kuka mai tsanani .
“eh, bana so.”
Ya yi murmushi cikin mulki da kasaita y ace “amma ni na ji ina sonki, so mai dinbin yawa kuwa. Yaya xa’a yi ken an!”
Abokansa suka fada cikin fusata “ka bamu ixini mu shigar maka da ita ciki kawai, ka gama da ita mu ma idan ka gama ka bamu sauran, tunda bata da gata a kasar nan waye xai tsaya mata.”
Mambela ya mike tsaye cak yana duban kaltum dake tsugunne a gabansa har yanxu kuka take, gardawan kacokan sun xagayeta babu hudar da xata samu ta arce . mambela ya dade a tsaye yana dubanta daga shi sai mahaliccinsa ya san abunda yake aiyanawa a ransa. Can ya dago ya dubi yaransa daya bayan daya sai yayi murmushi da kyakkyawar fuskar nan tasa, sannan ya yi musu nuni da hannu ko bai furta ba su sun fahimci abunda yake nufi nan da nan suka fara aiwatar da abunda ya umurcesu dasu yi domin ba’a yiwa mambela musu a garin.
Kartai uku ne suka damko ta suna kokarin shiga da ita shago. Ta kurma ihu ta ci gaba da kiran “inna lillahi wa’inna ilaihi raji’un.”
Muryar wani tsoho ne suka ji a bayansu ya fada cikin yarensu, daga dukkan alamu ransa a bace yake, y ace “haba mambela ko sauran ba musulmai ba ne ai kai musulmi ne, ko kunyi niyyar cutar da yarinyar nan albarkacin sunan Allah da take ambata ya kamata ku kyaleta.”
Suka ajiye ta yayin da ta balla da gudu ta je bayan tsohon ta labe, karkarwa kawai take yi. Gyalenta ya dawo wiyanta, kanta babu dankawali sai burtintin kitson da ya tuttuje wanda ya cika da yashi a sanadiyar rashin siminti balle katifa a dakinsu. Tsohon ya juya ya dubi kaltum yayi mata yarensa, sai ta girgixa kai ta yi masa larabci. Ta ce, “bana jin yarenka, larabci nake ji kadai” ya fada cikin harshen larabci “yi hakuri yarinya, daura dankwalinki, goge hawayenki ki tafi gidanku. Ki daina shigowa kasuwa bara wajen maxa ki dinga bararki a cikin gidajen mata ya fi miki alkhairi a matsayinki na yarinya mace budurwa kuma kyakkyawa.”
Ta gyada kai t ace “ nagode, ba xan sake xuwa ba. Baba karaka ni gidanmu tsoro nake ji kada su bini su sake tare ni a hanya.”
Ya ce to muje in raka ki.
Jikinta na karkarwa, hawaye yana kwaranya ta shige gaba tsohon na biye da ita a baya har suka yi nisa.
Mambela ya cije baki ya gyada kai ya dubi abokinsa.
Ya ce “xan jinyata tsohonna idan be daina shiga shirgata ba. Yanxu haka shima idan suka raba daji yaga ba kowa xai iya yi mata lalata, shine mu ya hana mu. Xamu hadu da kaltum wata rana wallahi ba xan hakura da ita ba duk ihunta.”
Abokansa suka ci gaba da xuga shi suna bashi kwarin guiwar gami da daukar masa alkawarin idonsu idon kaltum xa su kamo masa ita.
Har kofar gidansu kaltum tshon nan ya raka ta da gudu ta fada cikin gida ba tare da tayi msa godiya ba saboda a firgice take don tsananin tsoron da ta ke ciki.
Kaltum ta dawo gida da magaruba, kallo daya xaka yi mata ka tabbatar hankalinta a tshe yake ko Magana aka yi mata sai ka ga ta xabura. Babu irin tambayar da ba’a yi mata ba amma amsa daya ta gagara sai hawaye da take xubarwa. Daga ita sai Ubangijinta suka san abunda ya faru amma bata fadawa kowa ba.
Madina ceta ja hannunta tsakargida, suka shafe tsawon sa’a guda tana lallashinta tana bata baki da dubaru iri iri akan ta fadi abunda yake damunta amma kaltum ta ki cewa uffan, sai girgixa kai kawai take yi alamar babu komai. Karshen maganar madina t ace “babu yadda xa’ayi kice babu komi amma kuma kina kuka.”
Ta bata ruwa a buta tace ta yi alwala, ta yi sallah, ta yi addu’a ko me nene ma Allah Ya sawake mata.
Karkarwa hannu kaltum yake yi data dauki buta ta xagaya ban daki, ta fito tana alwala jkinta na rawa, kukan dai bata fasa ba har yanxu. Tana sallah tana sheshekar kuka a bayyane, hankalin madina ya tashi amma sai ta ji haushin kaltum ya kama ta saboda ta ki fada mata matsalarta. Su kuwa su huwaila banda xagi da dungure mata kai babu abunda suke yi suna cewa watakila satar kayan jikinta tayi masu kayan suka doke ta.
Rakiya tace “watakila gidan wasu ta shiga ta satar musu abinci tunda da yunwa ta fita tun jiya bata ci abinci ba.”
Amina t ace, “ko kuma xagin wasu ta yi suka kikkifa mata mari don bata da kunya.”
Iya mairo t ace, “ku kyale ta mana karta fadi abunda yake faruwa tunda bakin hali ne da ita babu mai jin cikinta.”
Kaltum na kudundune a kan kwalinta cikin mayafinta sai kuka take yayin da jikinta yak eta karkarwa. Har kowa y agama cuku cukun kwanciya, aka hure acibal bal wato fitilar da ake cika kwalba da kanaxir ayi lagwani da tsumma.
Duhu ya bayyana a cikin dakin, yayin da gari yayi shiru alamar dare ya tsala, kowane bawa ya kwanta hakarkarinsa kamar yadda masu iya Magana suke cewa dare mahutar bawa. Wannan dare kuwa ya xamarwa kaltum daren jan aiki babba maimakon ta huta sai ma ta tashi tsaye.
Misalign karfe daya na dare kaltum tayi firgigit ta mike tsaye a firgice gami da kwalla ihu mai tsanani tana fadin “wayyo Allah na, ku taimakeni gasu mambela nan xasu kamani.”
Ta tattaka sauran matan dake kwance a tsakiyar dakin burinta kawai ta fice waje da gudu. Gaba daya ‘yan dakin suka tashi a gigice suna riketa, tana bankarewa tana xubar das u sai da ta fita tsakar gida da gudu tana ihu tana fadin.
“su mambela ne xasu kamani, gasu nan xasu kashe ni.”
Madina da jidda’u ne suka bita da gudu suka damko ta suka shigo da ita daki sannan ta dan lafa ko minti biyar ba’ayi bat a sake kwalla ihu ta fice ta gudu. Wannan karon harda iya mairo a masu bin ta da gudu suka cafko ta. Ba ‘yan dakin su kadai ba gaba daya ‘yan sauran dakunan gidan babu wanda ihun kaltum da dawainiyar masu rike ta bai tasa daga barci ba. Kowa ya fito ido luhu luhu saboda barci suna tambayar “me ke damunta!”
“ba mu sani ba.” Amsar da su madina ke bayarwa ken an. Su duka suka kewaye kaltum suna tambaya,
“waye mambela, mutum ko aljan!”
Babu amsa, makyarkyata kawai take yi tana kuka, madina ce mai ilimn kur’ani ita ke tofa mata addu’o’I sannan kaltum tadan lafa harta fara gyangyadi, sannan ta sake firgita ta mike tsaye tana kokarin rugawa da gudu suka damko ta, suka xaunar da ita har yanxu fada take.
“ga mambela nan da abokansa xasu kamani.”
Su dukka sun tausaya mata, kowannensu mata da maxa sai addu’o’I suke tofa mata har saida ta lafa sannan suka koma dakunansu. Wsau suka kwanta amma wasu suna tsaye akanta har saida gari yawaye tangarai sannan kaltum ta sami barci. Sai kowa ya shiga neman ruwan alwala da sauransu.
Kaltum barci take yi haikan mai nauyi wanda bata iya jin duk wani motsi da surutan da ake yi akanta, bata bude ido ba sai karfe biyu na rana. Ta tashi xaune firgigit ta dubi sama da kasa, gefen hagu da damanta sai taga babu kowa sai ita. Ta dinga kokarin tuno komai. Kanta ne yake tsananin ciwo dan haka ta shafe awa guda a xaune ta rasa abunda yake mata dadi. Can ta daure ta yunkura xata tashi sai ta koma jabar ta xauna, ta sake cije baki ta rike katakon ginin dakin ta yunkura da karfi sannan ta mike tsaye. Ta fara tafiya a hankali yayin da kafarta ke xugi a sanadiyar bubbugewar da ta dinga yi jiya. Hakika duk ilahirin jikinta ciwo yake yi musamman kafadar ta saboda ciccibar da abokan mambela da ‘yan dakinsu suka dinga yi wajen jawo ta.
Ta fito tsakar gida ta tsaya ta dubi kowacce kusurwa babu kowa sai ita kadai, ta sake ci gaba da tafiya har saida ta fito kofar gida sannan ta sulale ta xauna a gefen wani kabari ta xura masa ido tana kallo. Sai hawaye ya fara sirnanowa daga idanuwanta, ta fashe da kuka mai tsanani ta fara Magana ita kadai tamkar tababbiya.
Ta ce “a ina nake! Ni wacece! Wa nake da shi a duniya! Me na ke yi a duniya!”
Sai kwakwalwarta ta tuno mata mambela da abokansa a lokacin da suke kokarin ciccibarta xasu shiga da ita wannan shagon, sai ta rushe da kuka. Ta ce “inna lillahi wa’inna ilahi raji’un. Yaya xan yi da rayuwata! Kowa ya tsane ni, kowa baya sona, kowa yana hantara ta, ga kishirwa ga yunwa. Allah Ka dau raina a saka ni a cikin kabari in kwanta in huta in daina ganin kowa, kowa ya daina ganina balle wani ya ji haushina.”
Ta sa hannu ta shafa kabarin ta fada cikin kuka ta tambaya tace “waye a cikin kabarin nan, mace ko namiji! Ina so in xama kamar ku, in mutu kamar yadda kuka mutu. In daina motsi kamar yadda kuka daina, in daina tafiya kamar yadda ku ka daina, in daina bara balle su mambela su kamani.” Yayin da kuka ya ci karfinta ta kasa ci gaba da Magana.
Muryar mai sayar da ruwa ne ya katse ta, ta dago idanuwanta da sauri ta dube shi, sai a lokacin ta tuno tsananin kishirwar da take matukar addabarta. Ta fada cikin wata marainiyar murya “saga dagiga moya hilwa wala murra!” ma’ana mai ruwa tsaya ruwan dadi ne ko na xartsine!
Mai sayar da ruwa ya tsayar da jakunansa ya dubeta yayi murmushi y ace “muya hilwa” ma’ana ruwan dadi ne.”
Ta ci gaba da Magana cikin harshen larabci tace “ka sauke min jarka daya.”
Ya sauko daga kan keken jakinsa da farin ciki yana godiya ya na fadin”Allah Ya yi miki albarka yarinya, kin taimakeni da xaki sayi ruwana yau ko digon ruwa ban siyar ba ban samu ko kwabon da xan yi cefane ba.
Maganar da yayi ya ambaci kudi shi yasa ta tuno dan silillikan data samu jiya da yamma. Sai ta yi sauri ta laluba jikin siket dinta, ta ji ba komai, sai ta tuno ashe sun xube a lokacin da ake ciccibar ta a kasuwa daga kudin har robar bara sun xube. Sai ta ji hankalinta ya tashi ta shiga tunanin abunda xata fada masa. Ya katse tunanin da ta ke yi ya tambaya, “a ina xan juye miki ruwan!”
Sai ta yi firgigit ta dube shi sannan ta sunkuyar da kai kasa, ta sosa keya, ta fada cikin gargadar murya “baba ka yi hakuri ba ni da kudi, ashe kudin ya xube jiya a jim arab. Ko xaka bani kofi daya in sha sadaka saboda Allah kishirwa nake ji.”
Tsoho ya tsuke fuska ya ciccibi jakar ruwansa ya mayar kan jakunansa yah aye, ya kada su suka tafi. Kaltum ta bishi da kallo har yayi nisa ta daina hango shi sai ta sulale ta kwanta a kasa domin a halin yanxu ta kasa kukan ma karfinta yakare. Can ta ji wata mryar kamar daga sama ana Magana cikin harshen larabci yace.
“yarinya, tashi ki karbi ruwa ki sha Allah Ya taimake ni yadda na taimake ki jikata.”
Ta daga ido da sauri sai taga mai sayar da ruwa ne ya dawo . ta tashi xaune da sauri yayin da farin ciki ya lulube mata xuciya, ya sauko daga kan keken jakunansa y ace.
“a ina xan juye miki jarka daya!”
Ta tashi da sauri ta shiga gida ta dauko bokiti ta kawo masa, ya tuttule mata jarka guda har saida bokitin ya cika taf da ruwan dadi. Ruwan da mutu daya baya iya siya a cikinsu sai daisu hada kudi su saya su uku ko su hudu su yini suna sha, ko alwala basa iya yi dashi sai dai su je kogi su dauko ruwan xartsi su yi alwala, wanka da wanki.
Kaltum ta dube shi ta fada cikin lallausar murya “baba, Allah Y dube ka kamar yadda ka dube ni, Allah Ya kawo maka ciniki ka samu na cefane kamar yadda ka taimake ni.”
“amen jikata” Kalmar da yake fada mata ke nan har ya hau keken jakunansa ya tafi yana daga mata hannu itama tana daga masa.
Ta tsugunna ta kafa kai a cikin bokitin ta sha ruwan nan tamkar rakumar da ta bude tankin cikinta. Ta dago ta yiwa Allah hamdala, ta sake kafa kai ta sha, ta sha, harta gaji sannan ta mike ta samu karfin ciccibar bokitin ta shiga dashi cikin gida, bayan ta kama ruwa sai ta shiga yin alwala ta shiga daki tayi sallolin axahar da la’asar domin har la’asar tayi. Tana idarwa amai ya kece mata a wajen da take xaune saida ta amayar da gaba daya ruwan da ta sha. Idonta ya yi jawur ya dinga xubar da hawaye saboda wahala sai a nan ta tabbatar yunwa ceke damunta ta fara tunanin ta inda xata samu abinci ta ci. Motsin shigowar mutanen gidan ne ta xaburar da ita ta yi sauri ta tula kasa akan aman ta rufe sannan ta fito tsakar gida da sauri sai taga ba ‘yan dakinsu ba ne.
Su na ganinta suka fara tambayarta yaya jikinta ta amsa da sauki. Duk da ta shiga rudani bata fahimci sannun da suke yi mata ba . tana tambayar kanta da kanta.’daman ba ni da lafiya! To ciwon me nayi da har ‘yan wasu dakin suke yi min sannu!”
Ta tambayi xaibu ko taga su iya mairo! Xaibu t ace ta bar su a gari ‘yan jange suna wankau, wasu daga cikin ‘yan matan kuma suna wajen sayen abinci suna saya. Kaltum ta yi shiru tana tunanin a ranta tana tababtarwa kanta kanta cewar ko yunwa xai kashe ta ba xasu bata loma daya ba, gara ma madina xata iya bata abinci ta ci amma da kunya jiya ta bata yau ma ta jira sai ta bata.
Xaibu ta katse tunaninta t ace “baki fita bara ba ne yau!”
Kaltum ta gyada kai tace “ban je bara ba saidaI yanxu xan tafi. Ko xaki bani aron robarki in tafi bara tawa ta bata jiya.”
Xaibu ta shiga ta dauko mata roba, a cikin robar da gutsurin gursa. Farin cikin ya lullube xuciyar kaltum, ta karba ta duka ta yi godiya ta yagi gayan gurasa ba tare da tagama taunawa bata hadiye tamkar mayunwancin xakin da yasa mu danyen nama. Fitowar ta keda wuya sai ta sake cin karo da tsohon nan mai sayar da ruwa akan jakunnan sa, ya dubeta yayi murmushi.
Ya ce “jikata, ki godewa Allah, ki yiwa Allah gadiya domin ke ‘yar baiwa ce, ki yi min addu’a ko Allah xai amsa min bukatuna.”
Kaltum ta yi kasake tana dubansa duba irin na rashin fahimta, ya lura da hakan sai ya ci gaba da cewa “na taimake ki daxu, ki kayi min addu’a kuma Allah Ya amsa miki. Ina barin wajenki na samu mai siyan ruwana ya saye dukka ya bani kudina, a yanxu haka jira na yake in je in debo masa wani ruwan in kawo musu xasu juye suba ni kudina. Na manta rabon da in sayar da jarkokin ruwa na duka har sau biyu lokaci guda. Yaya sunan ki!”
Ta yi murmushi ta amsa masa da “kaltum” ya dau waka yana cewa “kaltum ‘yar baiwa, kaltum ‘yar albarka.”
Ya wuce yana rera waka yayin da ta bishi da kallo fuskarta cike da murmushi. Ta fara xaiyano mutanen da suka fara sonta a rayuwa. madina, mai ruwa sai kuma xaibu wacce ta bata gurasa yanxu.
Muryar ‘yan dakinsu ta jiyo haya haya suna tafe suna tayar da kura tamkar dokunan da suke sukuwa. Kallo daya ta yi musu ta sunkuyar da kai kasa don tasan xaginta xasu yi, ta yi mamakin da ta ji su dukka suna yi mata sannu, yaya jiki! Ta amsa musu “da sauki.”
Iya mairo t ace “xaki iya xuwa bara, Amma ki yi sauri ki dawo kar ki kai magaruba don kar kiyi gamo irin na jiya.”
To pa, anya kaltum tana sane da halin da ta shiga jiya kuwa!
Meye dalilinta na shiga wannan halin!
Domin jin amsa, se ku biyu mu…
.
Typing : Sadin Maa.
Post : Dan Aunty 👫👨ADON DAWA 5
.
Kaltum ta tambaya a bayyane “gamo, wane irin gamo!”
Rakiya t ace “kin fi kowa sani ki ke tambayar mutane.”
Suka wuce suka shige cikin gida suka bar ta a nan tsaye tana tambayar kanta abunda suke nufi.
“shin me ya faru da ni jiya har ake ta min sannu!”
Ta nufi garin jange sai ta juya ta kama hanya garin Adon dawa, can ta ja burki ta tsaya cak data tuno abunda su mambela suka yi mata a kasuwa jiya ta yarda robar barar a kasa ta toshe kunne ta tsugunna ta kudundune jikinta kamar wacce xata nutse a cikin kasa. Wani hannu ta ji ya dafa bayanta, sannan ta ji wata murya mai laushi ta ambaci sunanta, kaltum ta dago a firgice sai taga madina ce.
Ta tashe ta tsaye, ta tambaye ta lafiya! Me take yi a tsugunne a nan! Amsa ta gagari bakin kaltum, madina ta yi shiru ta fara tunanin “anya kuwa kaltum bata yi gamo da aljannu ba a garin nan!”
Kaltum tace “bara xanje.” Ta tsugunna ta dauki robarta ta juya tana tafiya madina ta kwalla mata kira, kaltum ta waiwayo ta kalleta. Madina t ace “kin tabbata xaki iya xuwa bara yau! Domin baki da lafiya.”
Kaltum ta gyada kai t ace “xan iya xuwa” madina ta bita da kallo har said a ta yi nisa sannan ta juya ta shiga gida.
Garin jange kaltum ta je, daga dukkan alamu sun fara gajiya da barar nan ta su. Tun da safe su iya mairo suke abu daya, bayan wanki da wanke wanke da suka yi musu don haka basu da sauran wani aiki da xa’a yi musu kuma. Sai dai ta hadu da wani tsohon banxa wanda ya nemi ya kaimata cafka ta daka tsalle ta fito daga gidansa, har kofar gida ya biyota wai in ta yarda dashi xai bata kudin abinci. Don haka tunda ta juya ta fara sauri bata tsaya a ko’ina ba sai garin Adon dawa. Ta yi bara a gida daya bata samu ba, a gida na biyu sai ta ci sa’a ta samu shinkafa gaya ko gishiri babu aka cika mata robarta. Farin ciki tamkar anyi mata albishir da gidan aljanna, a kofar gidan ta durkushe ta dinga ci tamkar ta hada da yatsunta saboda yunwa, dadin gayar shinkafar da ta ke ci take yi kai ka ce da miyar kaji take hadawa. Shakewa take yi saboda rashin maiko ga babu ruwa a kusa.
Ta kusa cinyewa sai taga wata kwababbiyar kafa a gabanta wacce ta yi kama da kafar samudawan da. Ta dago ido da sauri sai taga wani sarkacecen saurayi dogo baki faffada a tsaye akanta da bakaken kaya. Saboda firgici sai shinkafar dake cike a bakinta ta fara xubowa yayin da laumar da ta debo a hannunta ta waste kasa saboda makyarkyata tana tunanin a inda ta taba ganin wannan halittar.
Bata jin yaren da yake yi mata sai dai ta yi kara mai tsanani ta tambaye shi da larabci me yake so a wajenta! Me tayi masa! Ya girgixa kai cikin harshen larabci y ace “ba ki yi min komai ba sai dai uban gidana yake neman amincewar ki.”
Ta tambaya a gigice “waye uban gidan naka!”
Yayi murmushi yace “mambela.”
Sannan yayi mata nuni da hannunsa, ta juya a hankali ta dubi inda ya nuna mata mambela da tawagarsa ta hango a tsaye suna dubanta. A inda taji wani mummunar faduwar gaba wacce ta fi wacce ta hadu da ita da farko. Kalmar “inna lillahi wa’inna ilaihi ra ji’un” ta ambata yayin da ta xura cikin gidan da aka bata sadaka da gudu. Cikin harshen larabci ta ke cewa “ku taimakeni mambela ne xai kama ni.”
Daga dukkan alamu ta tsorata matan gidan kasancewar duk saida suka xabura suka mike wasu kuwa har sun runtuma cikin daki da gudu. Da suka fahimci abunda take fadi sai wasu suka hau xaginta suna tankadar keyarta waje, wasu kuma daga cikinsu suka tausaya mata suka jawo ta cikin gidan.
Karkarwa take tana fadin “ni musulma ce, ku taimake ni ku biye ni xasu kashe ni.”
Hayaniya ta tashi tsakanin matan gidan su biyar uku suka ce kaltum sai ta fice ta bar musu gida saboda kada fushin mambela ya shafe su dan tsoransa ake yi agarin. Mabela yaro ne dan gata gaba da baya iyayensa masu arxiki ne, kakanninsa masu sarauta ne, yaro ne kwalli daya tak a wajen uwa da uba kuma shine kadai jika a wajen kakanninsa don haka ba’a saka shi, ba’a hana shi.
Daya daga cikin matan biyu da suke so su taimaki kaltum tayi fushi ta shige daki da taga hayaniyar ta yi yawa, fushi ta shige daki da taga hayaniyar ta yi yawa, yayin da dayar tace xata fita ta roki mambela ya kyale kaltum kada ya taba ta, amma in har mambela bai yarda ba sai ya taba kaltum to tabbas ba xata bar yarinyar nan ta fita ba sai dai in a cikin dare mambela ya sakawa gidan wuta.
Daga karshe dai aka fi karfin ta matayen nan uku suka turo kaltum kofar gida suka datse kofar gidansu, ta yi ta buga kokarin bankare kofar da karfi ta shiga tana ihu ba a bude mata ba, ta juya baya ta dubi inda su mambella suke tsaye, hakika har yanxu suna kallon gudun ruwanta se rada suke yiwa junansu, suna shawarta yadda xasu bullo mata. Ta kwalla ihu ta fashe da kuka ta sake kama katangar gidan ta kaya ta wujijjiga yayin da dukka hannayenta suka huhhuje jinni ya dinga xuba, can se taga matar da take son taimakon ta wacce aka hana ta boyeta ta a jikin Katanga ta dubi kaltum tana hawaye itama, cikin harshen larabci.
Ta ce “yarinya ki yi shiru ki kwantar da hankalinki xan taimake ki, amma sai kema kin taimaki kanki.”
Kaltum ta tsagaita da kukan ta dubi matar daga duk alamu bata fahimci abunda matar take nufi ba. Matar ta mika mata wani dan karfe karami dogo mai kama da axurfa. Kaltum ta karba ta jujjuya da alama bata san abun ba.
Matar ta sharce hawaye t ace “ki danna gefe ki gani.”
Kaltum ta danna, tana dannawa sai ga wata wuka kakkaifa ta fito fit. Hannun kaltum ya hau karkarwa ta fada a gigice “wuka ce.”
Matar t ace “sake dannan gefen.”
Kaltum ta sake dannawa sai tsinin kan wukar ya sake komawa ciki ta dawo ‘yar karama kamar da. Bakin kaltum na karkarwa ta tambiyi matar t ace “me xan yi da ita!”
Matar t ace “ki kwaci kanki da ita, duk wanda xai cuce ki ki kare kanki da ita, ki kashe duk wanda yake kokarin ya kashe ki, ki yanka duk wanda yake son ya yanka ki kafin ya yanka ki.”
Kaltum ta damke wukarta a hannu ta runtuma da gudu ta nufi hanyar garinsu, babban tashin hankali sai taga gardawan nan a guje suna biye da ita. Ba tare da bata lokaci ba suka damko ta tamkar kaxa haka ta ji sun cilla ta gefe, sai gata a kasa wanwar ta fadi ta yi ruf da ciki yayin da gardawa shida suka xagaye ta. Ta daka tsalle ta tashi tsaye da sauri ta kudindine jikinta da gyalenta tana kuka. Ta na cewa “me na muku, me ku ke so da ni!”
Se yanxu mambella ya karaso gareta, yana tafe yana takama tafiya ta kasaita ya tsaya a gabanta. Ya yi murmushi y ace “ke mai kyau, ya ki ke wahalar da ni ne don ina son ki! Ba kida labarin mambela a garin nan, baki da labarin ina da kudin da xan iyan siyanki keda iyayenki idan ma kina dasu! kar ki manta kasarmu ce nan, arxiki ku ka xo ci. Wuce mu je wancan gidan kafin na illata ki.” Ya nuna mata wani gida da hannu. Kaltum ta girgixa kai ta fada cikin kakkausar murya t ace “ba xan je ba, babu inda xan je sai dai ku kashe ni.”
Sauran suka kufula suka nufo ta a fusace xasu cafke ta sai ta daka tsalle gefe da sauri ta matsa gefen wukar dake hannunta kan kace kwabo wata kakkaifar wuka mai kyalli ta fito. Sai su dukka suka tsaya cak suna kallonta. Ta daga hannunta dai dai sangalin hannunta ta sa wukar nan ta keta da karfi, nan da nan wani sharbabben yanka ya bayyana mai tafe da jinni jawur ya fara gudana a kasa. Mambela ya raxana ya runtse ido saboda jinin day a gani yana xuba, sauran kuwa suka dakka tsalle gefe.
Ta ce duk wanda ya matso kusa da ni sai na yanka shi kamar yadda na yanka hannuna. Kun gani da idonku yadda na yanka hannuna jinni yana tsartuwa to ku tabbata xan iya yanka ku har lahira. Ku rabu da ni, ba ruwana da ku.”
Mambela ya kira sunayensu daya bayan daya, y ace ku xo mu tafi ku rabu da ita xamu hadu da ita wata rana.”
Sai suka juya suka tafi suka bar ta a wajen a tsaye, suna tafe mambela na waiwayanta har saida suka daina hangota. Tasa wukar ta yanki gefen gyalenta ta daure hannunta wajen yankan duk da haka hannun bai daina xubo da jinni ba, sai xuba yake ba kakkautawa. Ta danna gefen wukar tsinin ya koma ciki ta bude rigar ta, ta saka wukar a ciki ta juya ta tafi gida, kuka take yi a hanya tamkar ranta xai fita.
Tun daga kofar gida maxa suka fahimci jinni ke xuba daga hannunta, tambayata suke yi amma bata amsa ba ta shige cikin gida kai tsaye. Jama’ar da ke cikin gida suka taru akan kaltum suna tambayarta “lafuya, a ina ta yanke jinni yake xuba haka! Ta wuce daki da gudu ta fada kan kwalinta ta rike hannu jinni ne ke gudana, kuka take yi tun karfi saboda tsanani xugi radadin da yake yi mata babu wanda bai shigo ya tambayi kaltum ba amma bata amsa ba har bakinsu ya gaji da tambaya yawun bakinsu tamkar xai kare.
Jidda’u ta dubi iya mairo t ace “wai ni wannan kaltum din mutum ce, ko dai ba mutum b ace aljana ce! Ni fa na rasa kanta tsakanin jiya dayau.” Rakiya t ace “iskanci ne take ji das hi kala kala gara mu koreta daga dakinmu, idan aka bibiya ma sata take yi ake dukanta.”
Huwaila t ace tabbas biri yayi kama da mutum saboda kayan da yake jikinta ma na sata ne ai bata da Kaya ko daya.”
Aibu t ace “ba wannan ba ma, ina roba ta da kika karba xaki je bara daxu ba dai kin batar min ba nima kamar yadda kika batar da taki!”
Malam lawan y ace “ku yi mata a hankali mana jiri ne fa yake daukarta ku kalli idanuwanta bibbiyu take ganin mu, gashi asibiti sai an kasha kudi da sai a goyata a kaita.”
Madina ta tashi da sauri ta je ta bude jakar kayan aikinta sai ta dauko wata ‘yar karamar jakar hannu ta umurci jama’ar da suka baibaye kaltum das u marmatsa sannan ta umurci huwaila ta rike mata acibalbal ta haska mata. Koya yayi cirko cirko yana kallon madina suna son suga abunda take shirin yi. Ta bude jakar sai ga kayan asibiti burjik kamar su spirit, panadol, gestid, iodine da shan-shan bali. Ta yi mata allura a gefen ciwon don tsayar da jinin da yake xuba kan kace kwabo jinni ya tsaya, sanna ta fara xarga xare da allura tana daurewa. Ta dinke hannun nan tsaf, xafi ya addabi kaltum babu abunda take yi sai runtse ido hawaye na ta kwaranya, madina ta saka mata plasta ta like, sanna ta bata panadol ta sha ta kwantar da ita ta lullubeta da xani. Jama’a suka dinga mamaki suna tambayar madina ashe dama ita likita ce! Ta yi murmushi kawai domin babu amsar da xata iya basu, kowa ya waste ya shiga dakinsa. Ba’a hana mutane Magana da bakinsu musamman mata, sharrace sharrace iri iri da kage-kage akan kaltum suna fassara sanadiyar jin ciwonta sun fi dangatawa da watakila sata ta yi aka yanka mata hannu amma jama’a da yawa musamman madina sun musanta hakan don sun yaba da hankalin kaltum cewar ba xa ta yi haka ba. Allah Shi Ya barwa kanSa sani daga karshe suka gaji da Magana sannan kowa ya kwanta.
Tsakar dare misalin karfe biyu kaltum ta runtuma da gudu tana ihu fadi take “wayyo Allah na ga sunan xa su kamani mambela da abokanan sa ne”
Dole kowa ya tashi a firgice aka riketa, yau ma kamar jiya a tsaye aka kwana ana yi mata addu’a, kowa ya dinda tofa mata duk addu’ar day a iya wanda ma bai iya ba yana tofa mata yawun bakinsa.
(irin su o’o ken an, ni kuma na yi dariya……. Na ce dai ayi hankali, kar a topa min yawu ……..)
Da gari yaw aye tangarai kaltum ta sami barci yayin da hannunta wajen yankan ya kumbura sumtum saboda bibbigewar data dinga yi wajen ficewa da gudu. Kaltum abun tausayi har hawaye madina take yi don tausayinta.
Har axahar bata farka ba bata ma san har kowa ya fita ya barta ba har said a suka daddawo daga bara sannan ta bude ido. Madina ta gani ta riko hannunta ta tashe ta xaune ta girgixa ta, t ace “kaltum dube idonki tashi ki ci abinci kiyi sallah.”
Sai ta ji tamkar a mafarki ta manta rabon da ace mata ta tashi ta ci abinci kyauta ba tare da ta je nemo wa ba. Ta mike a hankali ta shiga bandaki ta rage faitsarin day a cika mata mara, tana fitowa tadaura alwala, a daddafe ta yi sallar da ake binta. Tana idarwa madina ta miko mata leda a cike da taliya dafaffiya da miya don haka kaltum bata yi wata-wata ba ta dinga xabga lauma.
Harara irir iri hade da tabe baki kawai sauran ‘yan dakin suke yi mata, wani abunda ya sake basu haushi ma shine hatta ruwan da xata sha saida madina ta kawo mata gabanta. Haushi ya sake karuwa a xukatansu sai suka shiga habaice habaice da jan dogon tsaki harda tsartar da yawu. Madina ta yiwa kaltum nuni da hannu ta yi shiru kada ta daga ido ta kallesu. Daga dukkan alamu kiyayyar da ake nunawa kaltum ta fara shafar madina saboda ita bata biye musu a dinga kyarar kaltum.
Iya mairo ta dubi madina ta tabe baki t ace “madina yarinyar nan kaltum fa ba’a wajenki kakarta ta dankata ba, haka baki san tsakaninmu ba har ki ke kokarin raba mu da ita. Kina son ki sangartar da ita alhali ba gata kike yi mata ba, cutar ta ki ke yi saboda yau idan aka ce kin gaji kin daina nemo mata abunda xata ci ita kuma bata iya nema ba yaya ki ke tunanin xata yi! Sai dai ta fara daukar na wasu.”
Madina ta yi murmushin karfin hali t ace, “iya mairo a ganina kaltum yar uwata ce a musulunce tunda dukkan mu musulmai ne kuma ban hana kaltum fita bara ba idan tana da lafiya yanxu ma dan bata da lafiya ne yasa na nemo mata abinci ko da ace haka kawai na nemo na bata taimako ne saboda kaltum yarinya ce xan iya kiranta marainiya tunda bata da uwa da uba a nan.”
Maimuna ta hasala ta katse madina t ace “in xancen yarinta xaki yi ai rakiya it ace karama a dakin nan, ita da take tare da kakarta ma wannan gatan bai sa ta nade kafa t ace aljannu sun taba tab a.” sais u dukka suka hau kunfar baki ana tsuye madina da kaltum. Amsa daya madina bata sake mayar musu bat a yi musu shiru ma’ana shiru ma Magana ce inji masu iya Magana.
Cikin dare kaltum ta sake firgicewa tana ihu da guje guje ana riko ta, madina addu’a kawai take ta tofa mata sannan can ta lafa. Duk da ‘yan dakin basa so su katse barcinsu akan kaltum dole kowacce ta tashi, idan kaltum ta fara ihu da guje guje ba xasu iya kwanta hakarkarinsu ba har sai sanda kaltum ta samu barci sannan kowacce xata rintsa.
Yau ma madina ta hana kaltum fita bara t ace ta xauna xata je ta samo mata abunda xata ci. Kaltum ta nuna xata iya xuwa bara saboda gudun xagin da ‘yan dakin ke yi mata, madina t ace ta yi xamanta ita xata nemo mata.
Kafin axahar madina ta dawo dauke da abinci mai yawa, ta yi sa’a aka ciko mata kwanonta da abinci mai xafi sadaka, suka hadu suka ci suka koshi su biyu. Kaltum ta yiwa Allah godiya ta yiwa madina godiya.
Kwanci tashi said a kaltum ta shafe sati guda cur a gida bata fita bara ba sai dai madina ta nemo mata har said a ciwon hannunta ya kame ya fara warkewa. A ranar da kaltum xata fara fita bara madina t ace da ita “kaltum ki bi kawayenki ku tafi bara tare kada su ce na raba ku tunda ada tare ku ke xuwa. Kin ga ni ban cika yawon bara ba ina da gidaje biyu da nake aiki a garin jange, ina yi musu wanki ko dahuwar abinci, in yiwa yaransu wanka sannan su bani ladan kudi ko abinci dafaffe ba xasu yarda mu je tare ba suna biyan mutane biyu ba.”
Kaltum ta ji gaban ta ya yanke ya fadi tana fargabar yadda xata kasance a cikin su huwaila. Hakika xa su yi mata korar kare don suna jin haushinta matuka. Kaltum tana tsaye a kofar gida tana jiran fitowar su iya mairo don madina harta yi gaba. Suna fitowa suka kalleta suka bar ta anan a tsaye, said a ta bari sun yi nisa sannan ta fara bin su a baya idan sun waiwayo sun kalleta sai ta tsaya cak har suka tabbatar su take bi amma fa tsoransu take ji matuka.
Hankalinta ya tashi da taga sun nufi jim arab kasuwar adon dawa sai ta fara jan burki tana kokarin tsayawa. Tana tsaye daga nesa ta ki karasowa cikin kasuwar tana hangen su suna bin rumfa suna bara da lama suna samu don taga ana ta miko musu kudi ko dabino. Sai ta fara tahowa a hankali amma tana ta addu’a kada Allah Ya hada tad a su mambela.
Ta iske wani tsoho mai sayar da namijin goro a runfarsa, sai ta yi bara, ya tsakuro namijin goro guda hudu ya miko mata, ta sa hannu a sanyaye ta karba yayinda suka hada ido da tsohon sai suka shaida juna. Wannan tsohon ne day a kwace ta daga hannunsu mambela. Sai yayi mata duba irin na tausayawa y ace “yarinya baki daina shigowa kasuwar nan ba ko kamr yadda na shawarce ki, sai yan iskan yaran nan sun sake far miki ko!”
Ta xubo hawaye ta fada cikin wata siririyar murya “baba, yunwa nake ji dole ta sani nake fitowa.” Sai yayi shiru da alama yana tausaya mata, sannan ya dauko kamsa jine ya bata hakika kudin nan ya isheta ta sayi abinci ta ci ta koshi a yau don haka sai ta yi murmushin jin dadi, ta durkusa ta yi godiya ta karba. Ta juya xata tafi kamar daga sama ta ji muryar rakiya ta kwalla kiran sunanta, ta waiga da sauri sai ta hango su a kofar wata rumfa suna tsaye carko carko dukkansu. Sai ta nufi inda suke tsaye xuciyarta cike da mamaki da kuma fargabar ko me nene dalilin kiran da suke yi mata. Jikin ta na rawa ta isa gare su.
Rakiya t ace xo ki yiwa wannan mutumin larabci tundaxu yake so ya bamu kudi sai larabci yake yi mana mu kuwa bama ji.
Kaltum ta cusa kai cikin rumfar dan ta jiyo musu abunda yak e cewa sai ta hada ido da mambela. Yayi murmushi ya fada cikin harshen larabci yace, “sannu da xuwa yake abar kaunata a ko da yaushe, ce musu nayi su kawo min ke xan basu metan jine (dari biyu) ke kuma idan kin amince da nixan baki alif jine(dubu daya) ya ishe ki ki ci abincin wata guda idan yak are in kara miki.
Kaltum ta tuntsura ta fadi kasa saboda fargaba ta mike a guje ta falfala da gudu kai ka ce gudun fanfalake take yi saboda tamkar kafarta xata tabo keyarta. Mamaki ya kama su iya mairo suka rasa abinda ya fada mata su dai sun gay a mayar da kudinsa aljihu sannan yayi musu korar kare.
.
Subhan Allah.
Allah Ya raba mu da kunci na rayuwa ko wacce iri ce..
Aamiin...
.
.
Typing : Sadin Maa.
Posting : Dan Aunty.ADON DAWA 6
BABI NA HUDU
Gari yaw aye hantsi ya keto, yayin da fataken gidan nan suka dinga baxama neman abunda xasu kai bakin salati. Kaltum a xaune take a tsakar gida cikin hantsiba sunkuye a kasa da alama rashin lafiya a jikinta. Mutanen gidan mata da maxa suka yi ta tsayawa a kanta suna tambayarta shin lafiyarta kalau ko jikin ne! sai ta girgixa kai t ace das u lafiyarta kalau, ba tare da tad ago ido ta kallesu ba. Hajara c eta fito daga cikin dakinsu ta tsaya akan kaltum ta dade a tsaye tana harar ta. Kaltum tad ago ido a hankali ta dubi wacce ke tsaye a kanta, kallon da hajara tayi mata na wulakanci shi yasa ta gane bada alkhairi take nemanta ba don haka sai ta mayar da kanta kasa ta sunkuyar.
Hajara ta girgixa kugu t ace “kaltum, na rasa robata da gurasa aciki wacce na ajiye jiya da daddare a wajen shinfidarki.”
Kaltum ta girgixa kai t ace “ba ni na dauka ba.” Hajara ta fusata t ace, “wane shegen ne xai dauka idan ba ke ba! Ko kin dauka bamu da labarin sace sacen da ki ke yi a gari!”
Kaltum tad ago da sauri ta dubi hajara hakika ko ba’a fada ba kaltum taji haushin maganar amma sai ta maida kanta kasa ta sunkuyar. Iya mairo da jikarta rakiya suka fito suka dubi kaltum suka ce “yauma ba xa ki je bara ba, sai kowa ya tafi bara an bar miki gidan sannan ki lalube mana ‘yan abubuwanda mka ajiye ko!”
Huwaila t ace ai ba lefin kowa bane laifin madina ce da ta shagwabata, sai ta je tayi aikatau hard a jido ruwa a biya ta amma ta je ta siyo musu abinci ta kawo su ci tare shiyasa ma bata fita bara sai taga dama. Taci ta koshi dare yayi ta dinga ihun karya tana hana mu barci.” Amina ta fito daga daki t ace “idan gari yaw aye saita kwanta tayi ta barci har yamma mu kuma mu fita nema mu yini muna yawo lokacinda ya kamata mu kwanta sai ta hana mu barci, gaskiya a raba man daki dan yanxu ma ciwon kai na ke yi saboda rashin barci.”
Hawaye ya dinga xuba shaf shaf shaf daga idanuwan kaltum. Madina c eta fito daga wanka sanye take da hijabi sa daurin kirji ta karasoi da sauri inda suke t ace “haba ku kuwa bayin Allah me kaltum tayi muku a rayuwa da kuka takura mata haka! Xagin safe daban na rana daban dan kun ga bata magan, ku kira ta barauniya, ku kira ta ‘yar iska, ku ce mata munafuka. Da me xa ta ji, ciwon dake addabarta! Baku ganin da xaxxabi take kwana kullum saboda raunin da ke jikinta! Ku tuna fa ku musulmai na Allah Yan a son kaltum tunda Shine Ya halicce ta. Baku ganin hakkinta da ku ke dauka xai iya kaiku wuta, shirun nan da take yi tsananin hakuri ne, hakurin da take yi bata rmawa xai iya sawa Allah Ya yi mata sakayya da KanSa.”
Maimuna ta katse ta , tace “madina dan Allah kiyi mana shiru ke ba kya ganin laifin kaltum, ke c ma mai xuga ta har wata rukiyya kike mata wai ita mai aljannu, mu dai gaskiya tana hana mu barci mun gaji.”
Madina ta ji hawaye yan surnano mata daga idanuwanta dan takaici, ta share hawaye ta dubi maimuna t ace “haba maimuna ban taba xata ba wannan maganar xata fito daga bakinki a matsayinki na babba. Shekarunki talatin da biyar kin haifi kaltum hard a ma wadanda suka girmi kaltum. Kinsan ciwon haihuwa, kin san dadin ‘ya’ya dan kusan kullum kina kuka idan kika tuna ‘ya’yanki da kika baro, ban dauka xaki ki tausayawa ‘ya’yan wasu baa she xaki biyewa rakiya, huwaila, amina ‘yan matan da basu taba haihuwa ba!
Ke ma hajara ba yarinya bace tunda kin kusa haihuwar kaltum shekarunki ashirin dad a biyar ‘yayanki uku. Ba kwa tunanin abunda ka yiwa ‘yar wani sai an yiwa naku! Iya mairo kin ci amana tunda yarinyar nan ke aka dankawa amanarta da tun kakarta bata tafi ba sai ki fada mata baki karba ba, amma kika karba ki ka xo kina banbanta tad a jikarki. Ko ba komai kece wacce kuka fito gari daya ko albarkacin sanin asalinta da ki kayi bai kamata kiji ana kiranta barauniya ba kiyi shiru.”
Kan kace kwabo hayaniya ya hargitse tsakanin madina das u dukansu. Harda masu dammara xa’ayi dambe. ‘yan sauran dakunan suka fito maxa da mata suna bada hakuri, da yake duk fita xasu yi daman sun shirya dan haka aka tura su maimuna waje ita kuma madina aka tura ta cikin daki, sannan kunnuwansu suka huta da hayaniya. Kaltum tana xaune har yanxu kantga a sunkuye yake a kasa.
Madina ta dade a daki bata fito ba sai shehshshekar kukanta ka ke jiyowa daga cikin dakin da alama kuka ta ke yi. Sai da ta tabbatar ba kowa a gidan sais u biyu sannan ta fito tsakar gida a fusace ta dubi kaltum. Ta kira sunan kaltum, sai tad ago a gigice hankalinta a tashe ta dubi madina ta amsa kiran da tayi mata.
Madina t ace “ki kula da abunda xan fada miki, ki fahimci a inda kike da kuma abunda kike ciki. Ki sani xaman nan da mukeyi xama ne na kowa yayi ta kansa.” Kaltum ta ci gaba da kallonta sokoko da alama bata fahimci abinda take fada mata ba.
Madina ta ci gaba da cewa “ban hana ki yin hakuri bad an Allah Yana tare da mai hakuri, yana dad a kyau yin hakuri, amma ina baki shawara ki tashi haikan ki kwatarwa kanki hakkinki na ‘ya dank e ba baiwa b ace. Saboda me xaki xama sakarya a cikin al’umma, ki xama juji wacce ake xuba mata shara da aka yayimo daga ko ina! Yara da manya kowa kaltum yake tsangwama bakya katabus sai kuka, to ina mai baki shawara ki nutsu kisan abunda kike yi.”
Hawayen kaltum k eta ambaliyar xubarwa shiyasa madina ta kasa ci gaba da magan sai itama ta fara hawayen.
Madina ta share hawaye da gefen hijabinta t ace “kaltum Allah Yayi miki xurfin ciki wanda duk irin tambayar da xa’ayi miki baxa ki fadi halin da kike ciki ba,
Abubuwa da dama sun faffaru wanda ya kamata ace kin samu mutum daya kin fada masa amma kin ki. To ki sani wannan kunshe kunshen da kike yi a xuciyar ki ba komai xai jawo miki ba sai ciwon xuciya ko hawan jinni. Kina yarinya karama xa’aji tuf kin fadi xuciyar kit a fashe.
Gara ki dinga amayar da abunda yake damunki, wacce kika san xata rufa miki asiri ki shawarce ta tunda kin rabu da iyayenki da ‘yan uwanki dole ki samu wasu su xamar miki abokan rayuwa da aminci.”
Har yanxu kalma daya bata fita daga bakin kaltum ba, hawaye kawai take yi kanta a sunkuye a kasa.
Madina ta rike kugu ta fada cikin fushi da kunar xuciya t ace “kaltum, waye mambela!”
Wannan karon a gigice kaltum tad ago ta dubi madina duba mai tafe da tsantsar mamaki gami da faduwar gaba. Madina ta sake maimaita tambayarta, nhar yanxu ba amsa daga bakin kaltum tambaya ta uku da madina xa tayi bada baki ta yi mata ba, wani wani xabgaggen mari ta kifa mata mari wanda said a kaltum ta kwanta kasa ta rike kunci yayin data fahse da kuka mai tsanani.
Madina ta fisgo hannunta ta xaunar da ita ta rike kunnenta na hagu da karfi har said a kaltum tayi kara. Madina t ace “waye mambela! Ko kuma wacece mambela idan mace ce! A ina take! Me yake faruwa a tsakaninku!”
Kaltum tana mai matukar mamaki inda madina ta ji sunan mambela, sai ta shiga tunanin waye yake labewa har ya san abubuwan da suka faru tsakaninta da mambela, domin ita bta san abubuwanda take yi a cikin dare ba, bata san tana fita da gudu ana rike tab a har take ambatar gasu mambela nan xasu kasha ni har kowa ya ji.
Madina ta tunkude ta gami da rankwashin goshinta t ace “to yau rabuwarmu ta xo ni da ke, yau ne rana ta karshe dana nuna na sanki, nasan sunanki a rayuwata, kema kuma koda wasa kada ki sake nuna wa kin taba ganina a rayuwarki. Hanyarki daban, tawa daban bari ma sauran ‘yan dakin su xo su kore ki daga dakinmu baxan hana sub a saboda na fahimci xama da irinku hatsari ne, xaki iya kasha mutum ba’a sani ba saboda xurfin cikinki yayi yawa, bana xama da masu hali irin naki. Ashe su iya mairo sun fin gaskiya har nake dukan kirji nake fada a kanki, babu ruwana dake har abada haka ko xaki fice waje da gudu da tsakar dare ba xan kamo ki ban a daina sai dai in kin tafi a rasa ki, ki koma can wajen mambela ko mutum ne ko aljani ne, ko matattune oho. Na daina damun kaina a kanki, na daina tausayinki, na daina shigar miki fada, duk abunda mutane xa suyi miki ido ne nawa.”
Madina ta shige daki a fusace ta ratayo Jakarta kamar mai shirin fita unguwa ta fito ta iske kaltum a durkushe a bakin kofar dakin tana kuka mai tafe da ruri idanuwanta sun yi jawur kallo daya madina tayi mata ta Harare ta, ta dauke kai tana kokarin kewayeta ta fice sai kaltum ta rike kafarta.
Ta ce “aunty madina, kiyi hakuri ki yafe min abinda nayi miki.”
Madina ta tsaya cak t ace “ai ni baki min laifi ba, shawara na baki baki dauka ba. Tambaya nayi miki baki amsa bad an haka xama dake ba xai yiwu ba, bana xama da masu bakin hali da xurfin ciki. Na kasa gane ko ke wa cece, ko ina kika dosa, ko wane hali kike ciki! Dan haka na rabu da ke kaltum kamar yadda na rabu da ‘ya’yan ciki na a Nigeria. Kinsan kuwa tunda na rabu da ‘yayan ciki nab a xai yi wahala in rabu da ke ba wacce na hadu dake a hanya a kwanan nan. Ni haka nake al’amurana xaman yarda na ke yi da mutum, da xarar babu yarda to bana kara yin ko second daya xan matsa daga wajensa. Kaltum, ko baki bar dakin nan ba hakika nix an bar miki dakin a tunanina ada na dauka ke mutuniyar arxiki ce, ashe bah aka ki ke bad an haka na daina tausayinki ki je ki karata.”
Madina na rufe bakinta sai ta fisge kafarta daga hannun kaltum ta juya a fusace xata fice, cikin kuka mai tsanani kaltum ta sake wawuro xanin madina ta riketa kam tana cewa ki taimakeni anty madina karki rabu dani ba ni da kowa sai ke a kasar nan, na yi alkawari xan fada miki komai.”
Madina ta ji sanyi a ranta sai ta juyo, ta daga kaltum tsaye ta karkade mata yashinda yayi mata bududu a jiki. Ta dawo da ita inuwa ta xauna yayin da itama ta samu waje ta xauna. Madina ta san har ga Allah tana kaunar kaltum a ranta tamkar jinin jikinta, tana tausayin rayuwarta dan haka ta kudiri niyyar taimaka mata ba xata iya rabuwa da ita ba. Ta yi furucin rabuwa da ita dan ta tsorota ta, tana tsananin son ta ji tarihin rayuwar kaltum da asalinta da abubuwan da suke faruwa da ita suke damunta. Tana so taji ta ina kaltum ta samo kyakkyawar halittar ta wacce kyawunta ya xama abun kwatantawa da sha’awa, sannan a ina ta samo sunanda take kira idan ta firgita wato, mambela! A ina kaltum ta samo ilimin addini dana xamani haka! Don ta iya larabci tamkar jakar makka. Haka ta iya turanci tamkar karamar jakar London, shin ‘yar gidan masu hali ce ko ‘yar gidan yak u bay ice! Tana da iyaye ko kuwa marainiya ce! Meye ya raba tad a kasarsu ta taho sudan! Shin ita kuwa a matsayinta na yarinya karama meye damuwartada hart a yadda xa ta yi hijira dan ta samu salama! Anya goggo fatu kuwa kakarta c eta jinni, amma take axabtar da ita hart a iya tafiyar tat a bar ta bata damu ba duk da yadda aka san soyayya da shakuwar dake tsakaninta da kakarta!
Amsoshin tambayoyinta suna nan tafe a bakin kaltum, kamar yadda ta ji kaltum ta soma bata labarinta kamar haka, wanda ke kunshe da duk amsoshin tambayarta kakaf.
BABI NA BIYAR.
Kaltum ta tsaya tunanin ta inda xata soma labarinta, domin du duniya bata taba ba kowa labarin rayuwarta ba.
Madina ta katseta t ace, “ina sauraron ki fada min meye damuwarki!”
LABARIN KALTUM
Ta ce “suna na kaltume, sunan mahaifina saleh mahaifiyata kuma safiya sunanta ana kiranta da sofi.
Mahaifiyata ‘yar asalin wani gari ce da ake kira da IBONKOMO a cikin kasar Cameroon, mahaifina kuwa dan asalin xangon daura ne. mahaifiyata ta tashi a marainiya ba uwa ba uba sai ita sai kanwarta daya mai suna joda iyayensu suka mutu suka barsu, kawunsu yayan mahaifiyarsu mai suna jalo shi ya rike su har suka girma a bisa amana, ya aurar das u ga wanda suke so ba tare da takura ba.
Mahaifina shima maraya ne tun bayan da aka yaye shi mahaifiyar sat a rasu ta bar shi a hannun matar babansa ita GOGGO FATTU.
Goggo fatu c eta rike baba na tun yana da shekara biyu har rana irin ta yau ko tsinke ta ajiye baya tsallakawa saboda tsananin biyayya da tsoronta da yake. Daman ita bata taba haihuwa ba a duniya, mahaifina shi kadai ne aka Haifa a gidan su don haka bas hi da abokin shawara sai goggo fattu ko mahaifinsa bai isa ba.
Hakika tarihi ya nuna mahaifina ya sha wahala, axaba da makircin goggo fattu tun yana yaro har yau bai huta ba. Mahaifina ma kenan bai isa ba balle matarsa balle kuma ni ‘yarsa karan kada miya don haka kacokan dinmu sai abinda t ace xamu yi, sai yadda tayi da mu.
Madina ta gyara xama ta dubi kaltum t ace “na ji asalinki. Amma ta yaya saleh da sofi suka hadu ita da take Cameroon shi yana xangon daura!”
Kaltum tayi murmushi t ace “mahaifina ne ya je garinsu sofi yawon fatauci, tun yana yaro yake bin mahaifinsa suke xuwa tare har yake xuwa shi kadai daya gane hanya, suna shiga da kayanmu na nan gida Nigeria can su sayar sannan su kawo na can su shigo das hi ta a haka suka hadu. Aure kamar xai yiwu kamar ba xai yi wu ba, Allah Yasa ya yiyu aka yin ammadukka bangarorin biyu ba’a son ransu ba a bangarensa da bangarenta.
A bangaren su sofi suna ganin hatsari ne su dauki ‘yarsu su bawa bako wanda ba’a san asalinsa ba, haka suma danginsa suke ganin duk ‘yan matan das u ke xangon dauura ya rasa wacce xai aura sai ya fita wata kasar sannan xai yi aure. Karfin addu’arsu su masoyan da tsananin rabon haihuwa daya rantse sai aka yarda aka daura auren. Amma fad a farko dangin sofi basu yarda ya taho da ita ba sai dai ya kama haya a can ya ajiye ta, yana xuwa yana dawowa said a ta shekara sannan suka yaba da hankalinsa na ladabi, amana da rikon gaskiya. sannan aka sami wadanda suka san asalinsa ‘yan xangon daura amma maxauna garin su sofi sun yi gidaje, sun yi aure, sun hayayyafa sannan aka bari ya taho da ita. ‘yan uwanta suka rako ta har xangon daura suka ga mahallinta da ‘yan uwansa sannan suka tafi suka bar ta a lokacin tana dauke da karamin cikina.”
Madina ta nisa t ace “to naji yadda iyayenki suka hadu har suka yi aure. Da babanki ki ka yi kama ko da mamarki!”
Tambayar madina ta bawa kaltum dariya, sai ta kyalkyale da dariya sannan t ace, “da mama na nayi kama sak babu inda na baro ta, idan kika ganta kika ganni idan baki lura ba sai ki kira tad a sunana ko ki kirani da sunanta saboda bat a da kiba kma ba tsufa ba. Kamar yadda na fada miki fulanin Cameroon ne danginta kyawawa ne masu tsananin farar fata sai ka dauka larabawa ne, gashinsu har baya. Banyi kama da mahaifi nab a kwata kwata saboda shi baki ne, amman kanne na biyu sun yi kama das hi sak”
Madina tayi murmushi t ace “yaya xaman sofi ya kasance a xangon daura!”
Kaltum tayi murmushi t ace “gidan kasa da katangar xana gadon mahaifi na ke nan anan aka kai sofi, tana xaune a daki daya, goggo fattu a daki daya don a shekarar da aka yi auren baba na mahaifinsa ya rasu. Don haka goggo fattu ta sami filin casa sofi da saleh, sai yadda take so xa’a yi, sai abinda t ace xa suyi. Babu wahalar da sofi bata sha ba, ga cikin fari a wajen yarinya ‘yar shekara goma sha hudu, har ciki ya tsufa kuma ta hana a kai ta garinsu ta haihu. Da watan haihuwarta ya kama kawu jalo ya aiko da matarsa Asta da ‘yarsa Ladi su xo su dauko safi ta haihu a gida amma goggo fattu tayi musu dadin baki luf luf wai sofi ‘yar t ace tamkar wacce ta Haifa a cikinta don haka su bar ta a wajenta xata kula da ita sosai. A haka suka hakura suka tafi suka bar ta suna ta yabon kirkin goggo fattu, ita kuwa sofi tsoro ya hana ta fada musu gaskiya.
A cikin dare nakuda ta tashi sofi daga barci sai ita sai saleh, tashin farko daman dakin goggo fattu saleh ya nufa da gudu ya buga mata kofa ya sanar mata cewar sofi tana nakuda. Ta xage shi tsaf wai bashi da kunya meye abin gigicewa har ya fada da bakinsa matarsa tana nakuda. Ya sunkuyar da kai kasa yana bata hakuri, ta umurce shi day a fice daga gidan kada ya dawo sai gobe da safe.
Yana fita ta rufe kofar gidan sannan ta leka dakin sofi ta isketa a tsugunne ita kadai tana murkususu, tana ganin goggo fattu sai ta fashe da kuka ta hau kiran sunanta, amma goggo fattu ta tabe baki t ace “ki bar kiran sunana ma don ba xan shigo inyi ta fama da ke har gari yaw aye ba, haihuwar da bata da tabbas xata fito ko ba xata fito yanxu ba.”
Ta juya ta koma dakin ta tayi kwanciyar tat a bar ta a wannan halin. Allah cikin ikon Sa ta haihu ita kadai, jaririya ta fito fuk akan tabarma gtana tsala kuka haka mabiya ma ta fito . sofi ta rasa yadda xata yi da ni sai ta sami leda ta kwashe mabiyar da jaririyar ta rufe a leda fuskata ce kadai a bud eta dora ni akan gado ta xauna a gefena tana ta kuka har gari yaw aye tangarai sannan goggo fattu ta shigo dakin ta iske halin da muke ciki. Jaririya a kunshe a leda ga cibiya nan ba’a yanke ba a jikin mahaifar sai jini jage jage. Duk idanuwana, hanci na da kunnuwana duk busashshen jini ne.
Ta dau dogon salati ta dinga dimawa sofi duka a baya tana kiranta munafuka so take ta ja mata xagi a gari a c eta kasheta ta kasha jaririyar. Wai me yasa da haihuwa ta xo bata kwalla mata kira ba ko ta xo ta kira tad a kanta ba, xata xo ta kunshe ‘ya a leda ba’a yanke mahaifa ba alhali mahaifa shanye jini take.
Tayi tax age xagenta tana borin kunya sannan ta yanke cibiya, tayi ma ‘yar wanka ta gyara mai jegon sannan ta bude gida mahaifina ya shigo ya iskemu tsaf.
Haka danginsu su kayi tayi mata sannu da kokari yadda ta karbi haihuwar sofi tamkar ‘yar cikinta don sun iske mai jego sumul da jaririyarta kalau.
Bayan an yi suna aka saka min Ummu Kaltum sunana da goggo fattu ta xabar musu kenan wai sunan mahaifiyarta ne, basu isa su saka sunan mahaifansu bad a suka rasu tuntini. Sai dangin sofi suka xo suka dage xasu tafi da ita da kyar goggo fattu ta bari suka tafi da ita, mahaifina ya fi son haka daman. Bata dawo ba said a nayi wata uku nayi kwari sannan muka dawo xangon daura tun daga lokacin na fara shiga halin da nake har yanxu yak e bibiyata a rayuwata.”
Tab ashe haka wasu suke da busashshen imani!!!
Allah Ka sanya mu pi karpin xukatan mu, sannan Ka dada kare mu daga sharrin miyagu.
Se a saurara nan gaba domin jin yadda ta kasance.
Typing : Sadin Maa.
Posting : Dan Aunty.ADON DAWA 7
.
.
“kamar yaya halinda kike ciki har yanxu yake bibiyarki!”madina ta tambaya cikin rudani kaltum ta xubo da hawayenn daya cika mata ido tace “goggo fattu ta hana mahaifina ya dauke ni balle yayi min wasa ko ya rungume ni mu shaku. Ko kallona yayi sai ta dauki dogon salati kai kace mutum ya kashe. Ta ce wannan ai rashin kunya ne don haka kwata kwata baya kusanta ta. Haka mahaifiyata bayan nono da xata bani babu sauran soyayyar uwa da ‘yarta, idan kuwa ta cika daukana da tattalina sai xagi da Allah wadai take yi mata kala kala. Komai aka yi da ni, sai goggo fattu tace rashin kunya ne.
Wata rana har kuka goggo fattu ta ke saka musu, ta ce dan bata da haihuwa,a haka iyayena suka kyaleni, sai yanda goggo fattu ta yi da ni.kar ki dauka kulawar take bani, sai ta ajiye ni a dakinta in ta kuka, sai taga dama sannan tace sofi ta dauke nita bani nono. Har aka yaye ni na bar dakin mahaifana xuwa dakin goggo fattu, ba komai kuma take min ba sai duka da rankwashi musamman idan nayi fitsarin kwance, aka ce komai sanyin asuba xata kore ni waje tsirara bayan ta xane ni.
A lokacin karayar arxikii ta far wa baba na bashi da cin yau bare na gobe sai ya nemi shawara xai sayar da kiwonsa da mahaifinsa ya bar masa gado, akuyoyi da yawa da gonaki xai yi jari, sai ta ki amincewa t ace bakin ciki yake yi don ta xuba nata kiwon a cikin nasa shine yake so ya tona mata asiri a garin ace daman duk tulin akuyoyin nan ba nata ba ne don tayi karya t ace duk nata ne. muka dade cikin rashi da fatara da yunwa har Allah Yasa kawu Isiya kanin mahaifin babana ne yayi masa hanya ya samu aikin gadi a kano,ya tafi kano amma ya bar iyalansa a xangon daura.”
Madina ta gyara xama ta gyada kai ta ce “lallai yanxu xa’a fara labari. Daga nan yaya aka yi? ”
Kaltun ta girgixa kai ta ci gaba da Magana cikin marainiya murya ta ce “duk karshen wata yake xuwa ya kawo mana kudi albashinsa don mu ci abinci amma yana tafiya xata juya akalar kudin tayi sha’anin gabanta dasu .kuli –kuli guda uku shine bincin mu na rana, tuwon dawa da miyar kuka lami ko wace babu shine abincin dare, dumamensa sine abincinmu na safe.Duk muka rame muka lalace ita kuwa har tsire da kaxa take ci acikin shinkafa muna kallonta.
Da mahaifina yaga alamar mun rame sai ya dinga tambayar mahaifiyata ko lafiya muke rame wa?
Ta boye masa don itama irin halinta kenan ba xa ta yi Magana ba ko abu xai kashe ta, sai a makwabta aka fada masa duk abunda yake faruwa damu. Ya samu goggo fattu yace yana so ya tafi kano da sofi itama ta samu aikin wanke-wanke da shara duk wata xasu dinga hado mata albashinsu duka suna kawo mana ni da ita. Tuni ta amince sofi tabi mijinta suka tafi kano suka barni cikin wahala Kaman ta kashe ni tsunma ma ya fi ni nauyi, ga ciwuka kala-kala kullum.
Mahaifina bai fasa xuwa ba, duk wata xai shiga mota ya xo xango daura ya kawo kudin albashinsa fiye da rabi. Ina ganinsa sai in hau murna ina kiran “ga baba, ga baba.” Amma sai ya ture ni gefe in fadi kasa, ya dauke kansa baya kallon in da nake saboda kada goggo fattu t ace yayi rashen kunya.
Ina shekara uku yunwa da ciwon kyanda suka sa ni a gaba na rame sai kashi da fata, ido yayi min xuru –xuru kamar mai ciwon kanjamau sai ka kirga kashushuwan dake kirjina. Sai in suma sau biyar a rana wanar ba xan rayu ba sai ta ji tsoro kar in mutu a hannunta don haka sai ta nemi kawu isiya ya kawo mu har gidan da mahaifina yake gadi, suka ci sa’a kuwa a boy’s kuarter gidan suke xaune da mahaifiyata.
Ta hau fada hard a kumfar baki tana cewa sun gudo kano sun xo sun kwanta sun bar ta da wahala tana fama da ‘yarsu ko barchi bata yi, don haka ga ‘yar sunan su rike kayansu. Ta jankwabar dani da kayana ta juya ta tafiyarta, suna binta suna rokonta ta xo ta huta ta ci abinci, tace ba xata dawo ba dole ta tilastawa kawu isiya dole ya taso suka hau mota suka koma xangon daura.”
Madina ta girgixa kai t ace “daman haka halin goggo fattu yake! Ni fa na yi mamakin ace kaka ce take tsangwamar jikarta haka yadda naga tana kyararki a mota.”
Kaltum ta surnano da hawaye ta cika mata ido ta ci gaba da cewa “mai gidan da muke gidansa sunanasa Alh Adnan Mahbub, shi da matarsa Salaha sai ‘dan su daya Mashkur. Mashkur sa’ana ne shima a lokacin shekarunsa uku kamar yadda shekaruna uku cur a duniya. Alh Adnan yana da arxiki mai yawa duk da matashi ne a lokacin, aurensa ne na fari kuma haihuwarsa c eta fari bai wuce shekaru talatin ba aduniya, matarsa kuwa baxata wuce shekaru ashirin da uku ba don da haka kusan sun girmi iyayena ma. Suna xaune a kataferen gidan, kerarre mai girman gaske yayin da mu kuma muke xaune a boys quarters in gidan.
Alh Adanan na ganin halinda nake ciki na rashin lafiya sai ya ji hankalinsa ya tashi ya umurci direban saya dauke mu ya kai mu asibiti ni da mahaifana. Ya ce ayi duk abinda ya kamata ayi xai biya ko nawa ne. asibitin nasarawa aka kai ni a lokacin shine asibitin da yake tashe sai dan wane da wane. Likita na ganin yanayin jikina sai ya bamu gado muka kwanta aka dinga kara min ruwa da allurai. Allah cikin ikon Sa kafin sati guda na murmure, shi yasa aka ce kowace cuta da maganinta. Na samu sauki har na fara tashi xaune ina surutu kuma komai aka bani ina ci. Kusan kullum Alh Adnan da matarsa salaha suna xuwa su gaishe ni a asibitin bayan kayan dadi na marmari da abinci iri-iri da suke yini suna aiko direba yana kawo mana asibiti.”
Madina tace “gaskiya wadannan iyayen gidan naku suna da kiriki.”
Kaltum tayi murmushi tace “suna da matukar kirki shi da matarsa dukka. Bayan an sallamo mu mun dawo gida sai muka ci gaba da rayuwarmu a gidan, ina matukar jin dadin gidan saboda na samu walwala ba’a dukana, babu yunwa, ba babu hantara.
Makaranta mai tsadar gaske aka sani.
Madina tace “Allah kenan, haka yake ikonSa.”
Kaltum tayi murmushi tace “na tsinci kaina mai farin ciki matuka sai dai matsala daya data addabe ni itace bana samun kulawar iyayena. Ba kulawar rashin wanka da wanki ba ne, kuma ba matsalar abinci ba ne, basa hira da ni, haka basa saurarona, ko na matso kusa dasu saisu matsa saboda wancen ra’ayin da goggo fattu ta cusa musu.”
Madina tace “ban fahimci basa sauraronki ba, kamar yaya? ”
Kaltum t ace “kunyata su ke ji saboda ni ‘yar farice don haka na xama tamkar mujiya a tsakiyarsu sai kallo da ido. Ina matsowa kusa dasu saisu ture ni ko su tashi daga wajen, idan na taho musu da hira saisu gwale ni ba xasu saurareni ba. Idan xan yini ina kuka babu wanda xai lallashe ni a cikin su. Har ‘yan gidan suka fara fuskantar hakan, Alh Adnan ya dinga yiwa mahaifana nasiha yana nuna masa wannan kunyar da yake yiwa ‘yar fari ba’abun burgewa ba ne illa jahilci da cutar kai.
Akwai wata ranar asabar ba xan taba mantawa ba da sassafe misalin karfe takwas, a lokacin ana tsananin sanyi. Ni da mushkur muka fito bakin get wajen da babana yake xaune yana jin dumi da itace, yayin daya rufa da burgujejen bargo. Yana ganinmu ya tabbatar sulalowa mukayi muka fito ba tare da sanin iyayenmu mata ba, saboda ko rigar sanyi babu a jikinmu, ba hula, ba takalmi daga ni sai yar yaloluwar singileti da pant, haka mushkur daga shi sai karamar jallabiya ba dogon wando. Ana tsananin hunturu, mai tafe da haxo, da iska mai kura don haka hanci da ido sai xuba suke yi, yayin da duk ilahirin tsikar jikinmu ta tattashi.
Babana na ganinmu sai ya kira mushkur ya dauke shi akan cinyar sa ya rungume, ya lullube shi da bargo, yayin daya juyar dashi saitin garwashi suka yi ta jin dumi, suka juya min baya. Ina xaune akan benci a bayansu ina ta makerketa ban isa in kutsa cikin bargon ba saboda nasan hantara ta xai yi ya kore ni.
A cikin wannan hali Alh Adanan ya fito ya iske mu, sai ya ji ransa ya baci yayi ta yiwa mahaifina fada yana cewa shi fa ba burge shi yake yi ba in har xai bar ‘yar sa ta cikin sa a wulakance ya tallafi dan wani. In har iyayena basu shaku da ni ba to ina xansa raina, ya kwatanta wannan abunda suke yi da suna ADON DAWA wato gida bai wadata ba an wadata waje ma’ana ya wulakanta ‘yarsa ya tallafi bare.
Alh Adnan ya dauke ni ya rungume ni ya shiga da ni cikin falonsa ya dauki bargonsa ya lullube ni yayin daya kunna min room heater jin dumi ta lantarki. Yana lallashi na, ya bani biskit da alewa, har said a ya tabbatar hantsi yayi, sanyin safiya ya lafa sannan y ace in je gida ayi min wanka a saka min kayan sanyi. Haka shima mushkur yake samun wannan gata daga wajen mahaifana har goyon sa mama na keyi amma ni ban isa matsowa kusa da ita ba.
Dan haka na kasance ako da yaushe ina hanyar bangaren daddyn mushkur. Ina tashi daga barci wani lokacin ko karyawa bana yi sai in yi wuf nagudu wajensa, sai dai idan ban ci sa’a ba nayi karo da maman mushkur sai ta kora ni gida, idan kuwa tana kicin ko ban daki tuni na isa gare shi a falonsa ko akan gadonsa, yana gani na sai ya rungume ni ko daga ni sama cimak, ya wujijjiga ni in yi ta dariya.
Musamman saboda ni yake ajiye katan katan din alewa da biskit da kananan kwalayen lemuna. Ko da yaushe ka ganni ina ciye ciye, baya ga karatun boko dana arabiya da yake koya min. ya na sona saboda ina son karatu, kuma ina son in koya.
Ko da yaushe ina tambayarsa abun da ban gane ba haka duk abun daya koya min duk daren dadewa ya tambaye ni sai na fada masa bana mantawa, in da ya kara sona kenan.
Sabanin dansa wanda ya tsani karatu don haka ma basa shiri da uban. Gashi ina da tsananin wayo kamar ba ‘yar fari ba, ga ladabi da biyayya, na iya hira tatsuniya kala-kala da labarum nake bashi yayi ta dariya ya na tuntsurewa da dariya tamkar yana hira a cikin abokansa.
Amma fa bana labarin da kowa saishi kadai, idan baya nan sai ka rantse ni doluwa ce don bana Magana, sai kallo da ido a gidanmu saboda bana hira da iyayena. Don haka duk sanda daddy yayi tafiya kwana biyu sai kowa ya gane bana jin dadin rayuwata. Jikina sai yayi sanyi, in kaura bakin get ina duban hanya musamman idan na ji karar mota sai in xankada da gudu in leka, idan naga bashi ba ne sai raina ya baci ko kuma in fashe da kuka. Idan kuwa na ci sa’a shi din ne sai in yi ta tsalle da ihu don murna yayin da nake fara xaxxago masa labaru iri-iri dana tattara ina jira ya xo in fada masa.”
Kaltum tayi shiru tana matse hawaye, yayin da madina ta tsura mata ido tana yi mata kallon tausayi.
Madina ta nisa tace “ikon Allah idan da ranka babu abunda baxa ka jiba. yaya kuka kasance? ”
Kaltum ta gigixa kai tayi dan murmushi ta ci gaba da cewa “daddy shine tamkar uwata, ubana, kuma abokina. Shi kadai yake goge min hawaye a idona saboda a kasance koda yaushe ina cikin kuka a sanadiyar kyarar da mahaifana da kuma mamar mushkur ke yi min, tatsane ni saboda taga mijinta yana tarairayarta fiye da dansu na cikinsu.”
Madina ta girgixa kanta t ace “Allah sarki duniya, abun al’ajabi baya karewa ban tabajin irin wannan kauyenci ba. Daga kanki ba’a kara haihuwa ba a gidan ku? Mushkur ma ba’a hqifa masa kanne ba? ”
Kaltum tace “an haifawa mushkur kanne biyu amma dukkansu ba’a haifesu da rai ba, saura kiris mamarsa ta rasa ranta a garin haihuwarsu. Saboda duk a juye ake fitar mata dasu ta hanyar tiyata ma’ana kan jaririn ne suke komawa kirjinta, kafafuwan a kasa sai anyi tiyata ake fitar mata kuma a mace don haka nema aka juyar da mahaifarta baxata sake haihuwa ba. Ni kuwa mahaifiyata ta haifi namiji mai bina ya rasu bayan an yi suna, sai ta dade bata haihu ba sai daga baya ne haihuwar ta bude, kusan duk shekara sai ta haihu, a yanxu haka kannena bakwai na baro mata da maxa.”
Madina t ace “suma kannen naki suna jin kunyarsu basa kula su kamar yadda suke yi miki!” kaltum ta girgixa kai tace “iyayena suna son su, suna wasa dasu, suna hira dasu ba kamar yadda suke yi min ba har tsayawa nake ina kallonsu ina mamakin ashe mama da baba sun iya yiwa da wasa da lallashi.
Duk wani abu da ake bukata na makaranta sai na jira daddy ya xo sannan in fada masa, ya bani in kai makaranta idan kuwa baya gari ko baya kasar sai dai idan kashe ni xa’a yi a makaranta don duka amma babu wanda nake iya tara in fadawa sai daddy.
Ina shekara takwas nagama nursery har na shiga primary, ina primary 3 a lokacin ne karshen karatuna ya xo.”
“kamar yaya karshen karatunki ya xo? ”
madina ta tambaya cike da damuwa.
Kaltum t ace “eh, a lokacin ne goggo fattu ta aiko tana son ganin mahaifina, yana rawar jiki ya tafi kiranta a can garin mu xangon daura. Ta sanar masa abun da take bukata daga gare shi, gashi baya iya yi mata musu. Nan danan ya amsa mata ba tare da yayi kokonto ba saboda tsoro.”
Madina ta gyara xama t ace “me take bukata a gare shi!”
Kaltum ta cije baki tayi murmushin karfin hali t ace “ce masa tayi ya amince ta sayar da gadonsa da mahaifinsa ya bar masa sannan da tabkekiyar gonarsa dake garin sandamu, wacce mahaifiyarsa ta mutu ta bar masa, sannan da dinbin awakinsa xata biya kudin jirgi ni da ita mu tafi makka neman kudi. Idan muka je xa mu samo dukiya mai yawa , sai ta biya shi linkin ba linkin in kudin gonarsa.”
Madina tace “ya yarda a cire ki daga makaranta ku tafi maka? ”
kaltum t ace “a take ya yarda, haka mahaifiyata ma bata hana ba a sanda ya sanar mata. Ko da wasa babu wanda ya fada min shirye-shiryensu, ni dai nasan ankai ni gidan daukar hoto an yi min kananan hotuna, goggo fattu ta xo ta kwana biyu a gidan mu, sai kuma ranar da naga mahaifiyata ta xuba min kayana a dan buhu, goggo fattu tace in taho mu tafi.”
Madina tace “daddy ya sani bai hana a tafi da ke ba? ”
Kaltum ta girgixa kai tace ‘sai da suka ga daddy baya na sannan suka tarki tafiyar, koda wasu basu shawarce shi ba, matarsa ma bata sani ba.
Na tsinci kai na a cikin jirgi, sannan na tsinci kai na a cikin birnin makka.
Madina t ace ‘ki ce kin taba xuwa makka ba wannan ne xuwanki na farko ba? ”
Kaltum t ace”na dade a makka a can na koyi larabci, yanxu haka lungu-lungu da sako-sako na sani a cikin garin makka, haka da ace na samu xuwa xaki yi mamakin irin mutanen da xa ki ga sun sanni duk da na girma nasan xasu shaida ni saboda kammanina basu canxa ba.”
Madina tace”yaya xamanku da goggo fattu ya kasance a maka?
Amma dai bata wahalar dake ba tunda kin girma ba kamar sanda ta yeye ki ba, ga ku kuma a kasa mai tsarki, gashi komai a wadace ba’a wahalar abinci”
Kaltum tayi jugum can ta nisa t ace “uhum wahala ma daya kenan, ai ba xai yiwu in iya xayyana ta gaba daya ba saboda axabar tayi yawa.
Wahalar da na saha ina ‘yar jaririya ai karama ce saboda tsana bansan komai ba, a wannan lokacin kuwa nasan “eh” nasan a’a, na san ace in yi abu in yi, ace in bari in bari.
Da farko dai mun ci sa’a mun sami gidan haya a unguwar ‘yan kasa wato a unguwar masfala, a gidan wata balarabiya mai suna hajiya isra, hajja isra ruwa biyu ce mahaifiyarta baka, mahaifinta balaraben makka ne dan haka gadimiya ce. Hajja isra tana da ‘ya daya mai suna ahlan. Ahlan sa’ata ce, mahaifin ahlan ya rasu ya bar musu gida sama da kasa. Suna xaune a sama, mu kuma muna haya a kasa mu kadai ne.
Hajja isra tana da kirki matuka,tana sona sosai musamman yadda taga mun shaku da ‘yarta Ahlan, har ana cewa muna kama kasancewar Ahlan tayi kama da mahaifiyarta ba suyi kama da larabawa ba sak nima kuma gani fara sol mai gashi sai nake kama dasu. Ta kan yiwa goggo fattu wasa t ace “yadda fuskar nan taki take baka kirin idan askarawa (yan sanda) suka ganki da kaltum ki ka ce jikarki ce sai sun kama ki, suce karya ki ke ‘yar larabawa kika sato. Saboda baku yi kama ba kwata-kwata, gara ki dinga saka nikaf da safar hannu da ta kafa idan xaku fita tare.
In da xaki tabbatar hajja isra na sona sai ta siyawa ‘yarta ruguna ko sarka da ‘yankunne na gwal, biyu take saya iri daya ni da Ahlan musamman a lokacin sallah. Haka abinci, komai ta dafa sai ta aiko min sai dai kash aiken baya xuwa gare ni saboda goggo fattu karbewa take yi bata bani. Da takardar Ahlan ta ‘yan kasa hajja isra ta saka ni a makarantarsu Ahlan, muke xuwa tare duk da ba’a koyar da boko larabci xalla ake yi sai karatun qur’ani ta tahfix ce. Na koyi larabci, na koyi karatun qur’ani sosai, nasan baki, hadisai da daman na haddace su kuma xan iya fassarawa, haka fikihu, tafsir, sira da sauransu. Muna xuwa makaranta da sassafe misalign karfe takwas xuwa karfe goma sha daya muke tasowa. Muna tashi daga makaranta idan na shiga gida na ajiye jakar makaranta sai in karbi kudi a wajen goggo fattu in tafi sarar kaya sannan in je in sayar.”
Madina tace “ban fahimce ki ba. Ke kadai din ne xaki iya xuwa ki sari kaya da kanki? ”
Kaltum tace “ni nake xuwa in saro kaya, kar k ice tafiyar ba nisa, ko a mota tafiya ce mai nisa daga masfala xuwa shara Mansur masallacin mai cixo. Sai na niki tafiya kamar raina xai fita in saro kaya masu yawa sannan in doro kayan a kaina in nufi harami in da xan baxa a bakin hanya ina sayarwa. Idan na sayar sai in koma shara Mansur masallacin mai cixo in sake saro kaya in koma harami in sayar, har sai dare yayi bayan sallar isha’I sannan nake komawa gida sai na tabbatar kudin ya lunku sau biyu. Ma’ana idan riyad dari biyar ta bani sai ya xama riyad dubu biyu, ranar da ban yi ciniki ba ne xan kai mata ruyad dubu daya da ‘yan kai.”....
.
Gida fa ya fara shiru, mai yasa aka rage comments?
Ko littafin ya fara isan mutane ne?
Typing : Sadin Maa.
Posting : Dan Aunty.ADON DAWA 8
.
Madina tace “amma tana farin ciki da cinikin da kika yi mata bata kyarar ki ko? ”
Kaltum ta tabe baki ta ce “ko a lokacin xahma ma’ana lokacin da baki suke nan an fi yin ciniki wato lokacin Umara da Hajji idan ta bani riyad dubu daya in yi sari, daga safe xuwa dare sai nayi mata riyad dubu biyar xuwa dubu shida amma bata godewa kuma se ta dake ni kullum.”
Madina tace “to cnikin nawa take so kiyi mata? ”
Kaltum t ace “duka na take yi kullum ba sai nayi laifi ba, ba kuma dan ban yi ciniki ba. Yadda na lura doka ce wacce ta wajaba a kaina kullum sai ta xane ni ko da laifi ko ba laifi. Daman ina dawowa take ce min in cire kayana a bakin kofar shigowa daga ni sai dan wando, sannan in karaso gaban ta in durkusa, in mika mata cinikin dana yi. Sai ta kirga ta soka a aljihunta sannan ta xaro wayar rediyo ta fara sharara min a duk ilahirin jikina, laifin da take cewa nayi shine ban dawo da wuri ba ko kuma sharar da nayi da wanke-wanken da nayi da asuba kafin in tafi makaranta bai fita ba. In yi ta kuka da ihu ina mata magiya tayi hakuri ba xan sake ba. Har sai hajja isra ta jiyo ta xo ta kwace ni sannan take kyaleni, amma tun sanda ta yiwa hajja isra targade a yatsa garin kwata ta hajja isra ta daina saukowa ta kwace ni ki san larabawa da tsoro. Sai dai ki ji tana cewa “fattu kiji tsoron Allah, ki kiyaye ranar da hakkin yarinyar nan xai tabaye ki.” Amma goggo fattu bata ji, gobe ma xatayi min wanda yafi na yau.”
Kaltum ta fashe da kuka, yayin da madina ma taji hawaye ba kakkautawa yana xubo mata suka dauki lokaci mai tsawo babu wanda yake Magana don takaici. Can kaltum ta ci gaba da Magana cikin kuka take cewa “bulalar roba irin ta jona rediyo nan sai ta farfashe a bayana, yayin da karfen cikin wayar ke shiga cikin naman jikina ya nutse, jinni yayi ta fita. Idan wayar ta fatattake ta kare sai ta bani kudi in je in siyo wata a kanti da kaina, in kawo mata. Idan itama ta kare sai ta sake aikena in siyo wata.”
Kaltum ta juyowa da madina bayanta, yayin data daga rigarta sai ga shatin bulala xabga-xabga reras a jere a bayanta da wuyanta.
Madina ta shashshafa bayan yayin data gyada kai tace “kwarai kuwa wannan tabon duka ne. Allah sai Ya kama matar nan da hakkin yarinyar karama wacce bata jiba bata gani ba. Ta rabo ki da iyayenki ta xo ta axabtar da ke.”
Kaltum t ace “idan bayana ya farfashe yana jinni sai ta kaini bandaki ta daure hannuna da wuyana da kafata a jikin famfo kamar yadda na gaya miki sani take in cire kayana daga ni sai dan wando, sai ta dauko farin omo ta gurxa min a baya na a wajen ciwon sai kaji ya dau xugi yana tafasa, yana kumfa sai ciwo ya kakkame, sai jinin ya tsaya.”
Madina tace “ta daure ki a bandaki fa kika ce, kamar wata dabba?
Ko dabbace xatayi mata haka? ”
Kaltum t ace “na sha kwana a bandaki ina rawar sanyi har gari ya waye sannan ta jibgo min abinci t ace sai na cinye. Shinkafa himilin guda da kaxa dankwaleliya tace sai na cinye tas, inyi ta turawa badon ina jin dadin abincin ba saboda bana cin abinci sosai na saba in yini ina talla baci basha don haka nama daina son cin abincin kwata kwata.
Idan nace mata ya isheni sai ta kwada min mari tace sai na cinye duka, in yi ta ci har wani lokacin in amayar da duk abunda na ci, sai ta sani in kwashe aman in gauraya da abincin tace in cinye abincin da aman dole nake cakudawa in ci gaba da ci.”
Madina ta tsartar da yawu gefe,
(NI KUMA DAN ANTY, HAR SE DA NA KOMA YIN AMAI , YANXU MA AKAN AMAN NAKE OOOOOOOOO…….)
Ta dau dogon salati. Ta ce “kaltum kin sha wuya, kai wannan abu da me yayi kama?
Ke kuwa me kika yiwa wannan tsohuwar take wahalar da ke haka da alama don bata taba haihuwa bane take miki haka, da ta san xafin haihuwa da ta rage wani abu duk muguntarta.”
(NI KUMA NA CE, “BA WANI DAMAN MUGUNTAR A JININTA YAKE, WASU BABU HAIHUWA KUMA SUNA DA TAUSAYAWA DAN UWA. ALLAH MA YA TSARE MU DA IRIN WANNAN RASHIN IMANI. AMEEN)
Kaltum ta matse hawayenta tace “duk unguwar sun san ina shan wahala duk da basu san wata axabar da nake sha a cikin gida ba, amma suna ganin irin wahalar da nake wajen daguwar tafiya in saro kaya sannan in je in sayar, in koma in sake sarowa duk da kafa, saboda tsabar daukar kaya a kaina sai da kaina yayi tolo gashin wajen ya kade ya gurguje saboda wahala.
Akwai wani yaro saurayi a makwabtanmu mai suna Anwar. Bakar fata ne amma haifaffan Saudi ne yana tausaya min matuka y ace duk sanda xan je sari in je in karbi kudin motar xuwa da na dawowa in daina tafiya da kafa. Haka kuwa aka yi duk sanda na fito daga gida xan je in kwankwasa kofar gidansu ya fito ya bani riyal biyu, riyal daya na xuwa daya na dawowa. Sai in je in shiga doguwar bus a kai ni har kofar kantin sari, in saro kaya himili guda in sake hawa mota in tafi harami in sayar. Abunka da yarinta idan na sayar xan sake komawa in saro wasu bana shiga mota sai in tafi a kafata tunda Anwar bai bqni wanda xan sake komawa ba tsoro kuma ya hana in dauka a kudinta, gani nake kamar xata gane.
Wata rana da axumi na fito daga gida karfe shida da rabi na safe, gari ma bai karasa wayewa ba saboda akwai baki a garin don haka ana cin xahma. Anwar ya bani kudin mota na tafi na hau doguwar mota mai beni hawa biyu, sama da kasa don haka sai na samu lungu na shige a can sama.kan ka ce kwabo barci ya dauke ni kasancewar axaune a bandaki na kwana, tsirara ga tsananin sanyi dan haka ban samu nayi barci ba har asuba sannan ta kwance ni ta turoni sari ko karyawa banyi ba, anyi mana hutu saboda axumi a lokacin.
Ina wannan barci har aka wuce dani inda xan sauka ban sani ba. Da barci yayi barci saina sulale na mike a karkashin kujera na kwanta sosai na lulluba da gyalena. Ban tashi farkawa ba said a wata mata ta tashe ni ta ce in tashi masu mota dasu kai motar wajen parkin, sun gama aikin ranar. Sannan nayi firgigit na biyo bayanta muka sakko tare da ita. Ina tafe ina laluba kudina a cikin jaka dana daure a tsantsata, hakika kudina yana nan riyad dubu daya.
Ina fitowa sai na ganni a wata unguwa da ake kira shara sittin, sai ban damu ba saboda tafiyar da xan yi xuwa sharu Mansur babu nisa sosai don haka na tabbatar barci kadan nayi don ba’a wuce dani da yawa ba. Na duba sararin samaniya hakika har yanxu rana bata futo ba yayin da na duba agogon dake daure a hannuna karfe bakwai daidai. Sai farin ciki ya kama ni tunda na san karfe shida da rabi na fito daga gida mintuna talatin kadai nayi a hanya. Na dinga tafiya ina sauri kamar xan ci daka sai dai wani abu daya daure min kai sai naga du kana rufe kantina kuma kowa na haramar tafiya masallaci ko’ina sai kiraye-kirayen sallah ake yi. Sai nake ganin jama’a da dama suna cin dabino, wasu na shan shayi a cikin kantina ko a cikin motocin su, gashi axumi ne kuma asuba ta wuce an gama sawur. Na tambayi xuciyata me yasa suke karya axumin su?
Tambayoyi kala-kala na dinga yiwa kaina har na isa kantin sari. Mutum daya na iske yana alwala a bakin kantin. Cikin harshen larabci ya amsa min y ace “ba’adis salat”ma’ana, sai an idar da sallah xasu bude kantin. Na dube shi duba na rashin fahimta n ace “ba kuyi sallar asuba da wuri ba ne? ”
ya yi dariya yace sallar magariba xa mu yi ba dai asuba ba. Ko dan bakya axumi shi yasa baki damu a sha ruwa da wuri ba ko?
Sai gabana ya yanke ya fadi, nan da nan na rikice. Na ga wata mata ta xo wucewa jikina yana karkarwa n ace mata “karfe nawa yanxu? ” ta duba agogon dake daure a hannunta t ace “karfe bakwai.” Na tambaye ta “bakwai na safe ko bakwai na dare? ” itama sai tayi dariya sannan t ace “bakwai na dare ne. ba ki ga ana shan ruwa ba? ”
Sai na sulale na tsuguna ina ta salati, ina kuka hakika yau na shiga uku ban san abunda xan je in gayawa goggo fattu ba, ga dare yayi gashi ban juya mata kudinta ba. Ta yaya xan iya mayar da riyad dubu daya ya xam riyad dubu biyar ko dubu shida, daga magaruba xuwa dayan dare? Sai da su kayi sallar isha’I aka yi asham sannan suka bude kantina nan da nan na shiga na saro safar kala kala, da doxin doxin din carbina. Na fito na shiga mota na nufi harami kuka kawai nake yi jikina yana rawa, duk Alhajin da na gani sai in bishi, bakake da farar fata hawaye na xuba ina cewa ku siya kaya na don Allah idan ban sayar ba duka na xa’ayi a gida. Da yawa saisu tausaya min su saya ko basu yi niyya ba, wasu kuma saisu bani kudi sadaka, wasu kuma su fisge rigarsu su wuce subar ni. Kan ka ce kwabo na siyar na ruga da gudu na je na kara saro waqsu, na sake dawowa harami na sayar.
Akwai wasu kawayena ‘yan indiya da muka saba dasu a wajen talla, suma dasu ka ga ina kuka sai suka tausaya min suka sarar min da kayansu dukka a yadda suka saro na dora riba na sayar. A lokacin dasha dayan dare yayi jama’a sun fara tafiya masaukinsu suna barin harami sai mu ma masu talla suka fara neman hanyar gida. Ina tafe ina kirga kudin cinikin da na yi, saura kadan ya cika riyal dubu uku, sai na dinga kuka ina addu’a yayin da hankalina ya kada yayi gida ina tunanin abunda xan tarar don cinikin yau ba yawa. A titi na tunkaro wata mota wacce ta karkato xa ta tsaya (parking) gwuiwata ce ta daki gaban mota. Kan kace kwabo kwabrina ya fahse jinni yakece, na fasa ihu na daka tsalle gefe na tsuguna.
Hankalin direban ya tashi ya fito da gudu a gigice saboda yasan hukuncin kade mutum a kasar, ko ba’a ji ciwo ba balle a ce har an ji ciwo har jinni yana xuba. Larabci yake yi min, tambaya yake yana cewa wai me yasa nake tafiya kaina a kasa, bana lura da motocin kan hanya duk da horn dinda yake yi amma ban jiba? gashi nan na ja ya buge ni xan janyo masa wahala. Sai yaga ina ta bashi hakuri burina in tafi in bar wajen ban damu da ciwon da na ji ba. ya kira ni na xo, sai ya dunkulo kudi masu yawa ya bani yace in tafi chemist in sayi magani.
Na karba kudin ina murna, na wuce ina godiya sai na hada da kudin cinikina ya xama riyad dubu biyar harda doriya. Nan fa na ji hankalina ya kwanta na tsaya a fanfo na wanke jinin sannan na shiga gida. Na isketa a kufule tana jirana da bulalarta a hannu, kallo daya tayi min na gane manufarta. Sai na fara cire abayata na xama tik daga ni sai wando. Ina karkarwa na xo na durkusa na mika mata ciniki, ta karba ta kirga. Sai ta Harare ni ta ce “ina kika je aka ganki a mota daxu da magariba bayan ni ban baki kudin mota ba? ”
Sai na ji xuciyata ta harba tabbas wani ko wata sun ganni har an fada mata. Sai na shiga dogon tunani ina neman hanyar da xan kare kaina. Ta daka min tsawa t ace “Halima kawata ta ganki kina saukowa daga mota ina ki ka je? ”
Sai wata fasaha ta fado min nace askarawa ne suka kamani, suka tafi dani da kyar suka sake ni suka sake ni. Ta fixgi kunnena ta murda da karfi t ace duk sanda na sake na bari askari ya kara kamani to Nigeria xa’a mayar dani, ina xuwa Nigeria kuma daga filin jirgi xa’a yanka ni saboda yankan kai ake yi a Nigeria. Sannan ta kunnawa risho wuta yayi ja sosai sannan t ace in dauki risho din yana ci da wuta in xo in wuce ta gabanta yayin da take shauda min bulala idan na bari risho din ya fadi ko yayi karkacewa to dukan ya xube. “sai kaltum ta fashe da kuka mai tsanani.
Madina ma kukan take, ta dafa kafadar kaltum tana lallashinta tana bata baki. Tsawon lokaci kaltum bata daina kuka ba, saida kyar ta ci gaba da Magana. Ta ci gaba da cewa “tun ina kukan idan tana dukana har na daina kuka, tun ina ihu har na daina ihu, wannan abu kuwa yana bata haushi matuka ta fi so ta dake ni in yi kuka da hawaye sannan ta ji dadi don haka take dukana kamar xata fitar min da rai ni kuwa bana iya kukan.
Da wahala ta yi wahala sai nake fita in da Askarawa suke kame don su kamani amma basa kamani, sai daga baya na gane ashe basa kama masu talla sai masu bara don haka ina ganinsu sai in wurgar da kayan tallar nayi wuf na fada cikin masu bara. Naci sa’a kuwa rannan aka kamani aka kaimu sijin wato kurkukun da ake ajiye wa'anda aka kama ma’ana wa’anda basu da takardar ixinin xama.”
Madina tace “yaya rayuwar kita kasance a sin?
Kuma yaya goggo fattu ta yi data ji an kama ki? ”
Kaltum t ace “ai babu wanda ya san an kamani sai dai idan ta ji shiru ban dawo ba ta shiga tunani, musamman idan ta ji labarin an yi kame a harami. Bata cika damuwa ba saboda tasan riga kafin da ta yi min, ta riga ta tsorata ni da xuwa Nigeria . tace idan na yarda aka kawo ni Nigeria yanka ni xa’a yi a filin girgi, ni kuwa na yarda na dauka da gaske take yankan ake yi din. Su kuma askarawa baxa su yarda su kai yaro kasarsu ba shi kadai sai an hada da iyayensa. Don haka saisu tambayemu muna da iyaye a nan Saudi ya? Sai mu ce a’a saboda idan muka ce eh, to xa’a aka mu gaba a kaimu wajen iyayen namu.
To a haka da suka gaji da tambayar iyayen mu muka ce babu suka fitar da mu suka kaimu harami, amman ranar jikina se da ya gaya min, domin irin abunda ta saba min na cin xali, shi ta min. sauran da muke siya da siyrwa da su ba’a dukansu ko basu sayar da kayan su duka ba, basa damuwa saisu mayar gida gobe su xo su sayar amma banda ni, yi nake kamar raina xe fita sai na siyar ninkin baninki du da haka kuma ban tsira ba. Kaltum ta rushe da kuka.
Madina ta girgixa kai yayin data kurawa kaltum ido tana duban ta xuciyarta cike da tausayi akan tausayin da take ke ji a da. Can kaltum ta dago da luhu luhun idanuwanta ta kalli madina idanuwansu yayi musu jajawur ta ci gaba da cewa “da wuya tayi wuya shekara ta xagayo na fara wayo ina tunanin mafita sai naga babu wata mafita wacce ta wuce in koma sijin in xauna shine kadai salamata. Saboda a sijin akwai bangaren yara xalla a inda ake bamu duk wani abun dadi da ko a gidanmu ba ma ci. Shinkafa da dakwaleliyar kaji ga taliya, macaroni, lemo iri iri, nono (laban), madara, xuma da gurasa, kankana, da sauransu.
Watarana na ji labarin ana kame a wata unguwa tuni na xubar da kayan talla na nufi wajen, na sami fili na xauna ina bara. Da nayi sa’a sai suka gano ni suka kuwa xo cafke ni suka yi, suka tafi da ni sijin. Na shafe wata biyu cif a sijin, ina walwalata tare da sauran yara har akayi karamar sallah muna can, suka bamu kayan sallah kala bibbiyu.”
Madina tace “atamfa ko leshi? ”
Kaltum ta yi dariya t ace “larabawa ai basa saka atamfa ko leshi, dogayen riguna ne da dankwalayen su sai riga da siket ko wandaduna jeans wanda xamu saka daga ciki sannan mu dora da abaya daga sama, muci, mu sha, mu yi wasa, babu duka, babu xagi, sai dai muna leka wata ‘yar huda muna ganin bangaren karuwai da aka kamo su ake duka.”
Madina t ace “kullum sai ayi ta xane su? ”
Kaltum t ace “a’a, duk sanda aka kama karuwa sai a sakata a wani daki wanda aka sakale bulala sako sako, bulalen an jona su da na’urar lantarki. Ana saka karuwa sai a fito a barta a ciki sannan a kunna na’urar, makunnar na waje. Kan ka ce kobo bulalen nan sun hau aikinsu na duka ciki da waje, duk tsallanta haka ko kwanciya tayi sai dukan ya sameta, abunka da na’ura mai kwakwalwa daga sanda bulala tamanin ta cika sai injin ya mutu da kansa ma’ana bulala tamanin hukuncin xina, ana kiran dakin XANXANA.”
(YA ALLAH KA TSARE MU DAGA AIKATA TA, DA MU DA EN UWAN MU MUSULMAI BAKI DAYA AMEEN.)
Madina ta yi tagumi t ace “ikon Allah, kaji kasar da ake shari’a ake hukunta masu xina ba kamar kasarmu ba Nigeria wanda a wani bangaren ma xina ta xama fassion. Yaya ake yi da karuwa, idan an gama dukan ta? Nasan mafi yawancin su ‘yan Nigeria ne ko? ”
Kaltum ta girgixa kai t ace “cikin ikon Allah kuwa ban taba ganin an kamo bakake ba, sai irin kananan mutanen nan wato ‘yan Asia kamar Indonesian, malesian ko indiyawa. Idan an gama dukan daya sai a fito da ita a shiga da wata kuma, suyi ta kuka suna ta ihu daga nan suma sai akwashe su kowacce a kai ta kasarta bayan an bata mata passport dinta.”
Madina t ace “to yaya aka yi dake a sijin, tun daba xaki taba yarda ki nuna gidanku ba? ”
Kaltum t ace “tsoro kala kala ya hana in nuna, na daya ina storon in kaisu wajen goggo fattu a kamo ta nasan na lahira sai ya fini jin dadi, haka ina tsoron dira a filin jirgin Nigeria t ace xa’a yanka ni don haka na ki fada ina da iyaye. Suka gaji da ajiyarmu suka kai mu bakin harami suka ajiye mu, saura yara suna ta murna sun xo gida ni ina bakin ciki an raba ni da sijin, in da ba’a dukana, ba’a daure ni, bana talla.
Hakika ta gana min axaba irir iri, bata xuba min kalanxir ta kona niba, amma ta kyarta min ashana ta daddana min hannayena da kafafuwa na bayan duka. Ta shaida min cewar ai ta ji labarin har wajen kame nake xuwa da kaina don tsan ba’a kama masu talla sai masu bara.
Haka ake tayi kullum sai wahala da axabtarwa har na cika shekara sha biyu a duniya wato shekarrunmu hudu da rabi a makka. Na gaji da duka sai na sake xuwa wajen masu kame suka kama ni karo na uku kenan. Wannan karon kuwa na hadu da wasu yara sa’annina wanda suma irin matsalata ke gare su. Muka yanke shawara mu nuna iyayenmu a kamo su akai mu kasarmu ko xamu huta da wahalar duka. Na sanar musu cewar kakata goggo fattu tace yanka mutane ake a filin jirgin Nigeria, suka ce karya ne tsorata ni kawai goggo fattu keyi. Don haka ana tambayarmu muna da iyaye mu uku muka ce “eh muna da iyaye.” Sauran da suka ce basu da iyaye aka dawo dasu bakin harami aka xube su. Mu kuwa da muka ce muna da iyaye kowacce aka hada ta da Askarawa bibbiyu da mota don ta nuna gidansu. Tiryan tiryan na kaisu gidanmu, ashe labari ya kai kunnen goggo fattu tun kafin mu karaso kofar gidan cewar an ganni da Askari. Tabbas waya aka doka mata, don haka ta shige cikin tankin ruwa anan suka xaliko ta aka kwaso mu da kayanmu kwacokam. Hajja isra da ‘yarta Ahlan na kuka muma muna kukan rabuwa dasu, aka tafi damu sijin ammam ba na da bane, wannan sijin din na masu tafiya ne don haka yara da manya a hade suke.
Tun a sijin goggo fattu ta fara dukana, xagi ba adadi ko abinci na karbo sai ta kwace tace ba xan ci ba. Kwananmu uku ban ci abincin kirki ba, lauma daya ko biyu sai ta faki idon ma’aikatan ta fusge abincin ko ta ci ko ta xubar. A rana ta hudu aka kwashe mu, aka kai mu jidda airport daga nan sai aka saka mu a jirgin da xai kawo mu Nigeria yayin da farin ciki ya lullube min xuciyata su goggo fattu kuwa suka dau kuka da kururuwa kai ka ce lahira xa’a kaisu da ransu. Bana farin ciki don xan je in ga iyayena ko kadan ban tuno su, farin cikina daya ne xanga daddy, xanga mashkur dansa abokin wasa na to daga nan sai kannena guda biyu a lokacin na baro Amani da Yasmin, saida na dawo naga mamana ta sake haihuwar ‘ya’ya biyu Mohammad da Ishak.”
Madina ta tambaya “ya kuka kasance da goggo fattu a Nigeria? ”
Kaltum ta sharce hawaye tayi murmushin karfin hali tace “goggo fattu ta shaidawa iyayena abunda na jawo mata, cewa da gangan nake xuwa wajen masu kame har suka kama ni, na nuna ta. Duk da irin himilin kudin dana nemo mata har tsawon shekara hudu da rabi amma sai ta boyeta ce bamu samo komai ba don haka kudin gonakin babana da dabbobinsa da ta siyar sun mula ba xata biya ba. Ta ce wai bana tsinana mata komai a can sai kwanciya, yara kanan suna neman kudi wadanda ma basu kai ni girma ba.
Babana yayi shiru yasan halinta amma sai ya biye mata yayi ta xagina kuma ya bata hakuri, sai dai duk wanda ya kalli jikina yasan shatin duka ne a ko ina. Wuyana, dantsen hannayena, tsintsiyar hannayena duk sun dashe, sun yi jawur saboda dauri abunka da fara don a lokacin na fi haka fari sosai.
Haka daddy yana ganina ya tambaya yace “kaltum meye ya faru da wuyanki da ma duk jikin ki?
amman wannan shacin duka ne. wa yaketa dukanki haka? ”
wannan amsa ta gagare ni, balle iyayena sai ita goggo fattu take bayani tace “ai bata jin Magana a garin tsalle tsallenta take karkarcewa.” Ai idan mafadin Magana wawa ne, majiyanta ba wawa ba ne. sai dai su kyaleta a haka amma basu yarda da bayananta ba kowa yasan shatin duka ne. duk ilahirin kayan da kika sani wadanda hajja isra take saya min da gwalagwale sarka da ‘yan kunne da xobuna du ta kwashe babu wanda ta bani. Hatta da wando (fant) idan na saka sai ta kira ni daki tasa na cire ta ce wai ba nawa ba ne nata ne. kaya kadan ta bar min ta hada da himilin dilolinta tasa a mota aka kaita xangon daura, bayan ta shafe wata guda cur a gidanmu. Banda ‘yan tsummakaron data hada iyayena da kannena wato gumama babu abunda ta basu shine tsarabar su.”
Madina t ace “amma wannan matar makira ce bata tsoron Allah. Yanxu ina xata kai hakkin dukiyar mahaifin ki data danne ta gado? Yaya rayuwarki ta kasance kuma a kano tare da iyayen ki? ”
Kaltum t ace “kamar yadda muka saba sai kunyar da iyaye na suke ji ta karu, rashin kulawar ta dadu, dakina daban na kannena daban.
Aikina kuma wanke wanke da shara da yiwa kanne na wanka, aikina yi na ke, ba se an saka niba saboda na saba da aiki har bana son xama. Mama kuma ita ke dafa abinci safe rana da dare.”
Madina t ace “ba a cikin gidan su mashkur take dafa abinci ba har kuma ku samu, ko an raba girki saboda kun yi yawa yanxu? ”
Kaltum t ace “ai a lokacin su mashkur sun tashi daga kano sun koma Abuja daddy yayi arxiki ya ninka na da, sun wuce xama a irin wannan gidan yanxu. Gidansu na Abuja tamkar aljannar duniya, ga motoci kala kala.”
Madina t ace sai suka bar muku babban gidan kuka bar boys quarters? ”
(Wash , hannuna, se na ji kawar da su karye sabida typing gaskiya na gaji, masu so ga littapi nan suma suyi.)
.
Lol... Sadin Maa ina xamu iya wannan aikin naki?
Inbanda addu'a da patan alkhairi ai babu abunda xamu iya biyan ki da shi.
Allah Ya saka miki da alkhairi Ya biya miki bukatun ki na alkhairi baki daya..
Aamiin Yaa Rabb 🙏.
.
Typing : Sadin Maa.
Posting : Dan Aunty.ADON DAWA 9
.
TRUE LIFE STORY
.
Kaltum t ace “idan ta daddy ne ba damuwa xai iya barmu mu shiga mu xauna amma matarsa anty salaha bata da kirki baxa ta yarda ba. Sai wata ‘yar uwarta tsohuwa mai suna Iya Altine itace take xaune a cikin gidan, tana sharewa tana goge goge don kada a bar gidan ya lalace saboda suna dadewa basu xo hutu ba. Daddy dai yafi xuwa akai akai ba kamar mashkur da mamansa ba, sai sallah ko bikin ‘yan uwa da yake su dukkansu ‘yan kano ne. mu dai muna xaune a boys quarters sai ma rashin dadi daya karu, saboda a yanxu basa gidan bare mamana ta dafa musu abinci su ci har mu ma mu samu mu ci, mu ke cefanen mu, mu auno abinci, sannan mu dafa don haka daga masara sai gero, shinkafa jifa jifa muke iya saye. Ga uwa uba duk gonakin da ake nomawa mahaifina kakaf goggo fattu ta sayar, bama samun ko kwayar masara daya daga gona sai dai mu auna daga albashinsa, sai ‘yar kyautar da daddy yake yi masa akai akai idan yaxo. Tunda ta abunda xa’a ci ake, babu wanda yayi tunanin a saka ni a makaranta. Da kanwar mahaifiyata ta xo wato goggo joda daga garinsu Cameron sai na bi ta muka tafi can na xauna. Hakika na ji dadin xama a kasar kuma na sake, ina walwala acikin dangin mahaifiyata suna sona sosai. Duk da kauye ne, talakawa, Fulani ne amma komai ya wadata. Ga abinci iri iri, ga ruwan fanfo, ga wutar lantarki.
Duk wasu labaru da tarihin rayuwata, da ta iyaye na, da yadda suka hadu aka yi auran, da yadda xamana ya kasance a hannun goggo fattu ina yarinya duk goggo joda ta fada min, badan ita ba da ba xan san komai ba saboda da mahaifana basa hira da ni. Amma mahaifiyata tana hira da kanwarta tana fada mata komai. Naja baki na gum na rufe ban fada musu irin axabar da goggo fattu ta gana min a saudiya ba. Sai dai duk sanda na cire rigata xanyi wanka kowa ya kalli bayana sai ya tambaya ni “wannan shatin meye.” Kuma har rana irin ta yau ina kwaikwalo robar wayar da ta shige min jikin nama na.
Wata na uku cur a Cameron sai kwatsam naga babana da direban daddy a mota sun xo daukana wai daddy ne ya turo su, su xo su tafi da ni kano an samarmin makarantar sakandire, rabi boko rabi Arabic ce. Bada sona ba na baro Cameron na dawo kano don bana jin dadin gidan mu musamman dasu daddy suka kaura Abuja ga tsananin rashin abinci.
Na iske daddy a kano, ya kira ni, sannan ya kira babana, mama ta muka xauna a gabansa a kasa kan kafet.
Ya fara bayani yace “nayi matukar bakin ciki dana dawo daga tafiya aka ce an cire kaltum daga makaranta an tafi da ita saudiya neman kudi. Naji tamkar in fasa ihu saboda takaicin yadda kuka tauyewa yarinyar nan hakki, ku ka tauye mata rayuwa gashi dai yanxu ta dawo ba dammar a mayar da ita aji uku na primary saboda ta girma, in da Allah Ya rufa asiri ta shiga makaranta a can, tasan qur’ani, tasan baki xataa iya karanta larabci aduk inda ta gani haka duk abunda aka fada mata da larabci xata ji shine naga ya dace asamar mata sakandire wacce ta hada Arabic da boko sai kwakwalwarta ta tafi daidai saboda har yanxu ta iya karatu da rubutun boko don haka ta je ta gurgura ta tsinci abunda xata tsinta.”
Daga karshe ya roke su Allah da Annabi su barni inyi karatu kada su sake cire ni su ce xa’a kaini Makka ko xancen aure. Ni kuma yayi min fada da na mayar da hankali nayi karatu musamman a bangaren boko shine wanda ban iya ba sosai. Muka yi masa alkawarin xamu bi duk abunda ya fada mana.
Makarantu uku na shiga, makarantar boko da safe, ta Islamiyya da yamma sai kuma ta dare karatun hadisi ake da tauhidi. Nayi bakin jini a waje ‘yan makaranta saboda na fisu kokari, nice karama a ajin manya cikin xabga xabgan ‘yan mata, suma na fi su kokarin domin kullum ni nake karatu da larabci malami yana fassara musu. Duk in da aka bude daga cikin kowanne littafi sai kiga na iya saboda an dade da koya min a Makka. Hakan ya jawo min farin jinni a wajen malamai kacokan suna so na, wasu ma daga cikinsu so irin na soyayya suke nuna min. yayin da hakan ya jawo min tsananin bakin jinni a wajen dalibai kacokam sun tsane ni, ba ni da ta kamammiyar kawa guda daya saboda ana tsoran kada bakin jinina ya shafe su.
Kullum idan aka tashi daga makarantun nan da nake xuwa guda uku, sai dalibai sun tare ni sun ja min kunne akan kada in sake dagewa wajen yin karatu tiryen tiryen bayan su basu iya ba, malamai su dinga yi musu kallon dakikai. Wasu kuwa saisu tare ni su dake ni akan samarinsu da suke ji kishin-kishin yanxu ni suke so alhali ni ban san hawa ba ban san sauka ba. Ba na saurayi, ban taba yi ba saboda da wadannan dalilai duk sanda garin Allah yawaye sai na ji gabana yana faduwa ina fargabar tafiya makaranta saboda a makarantar boko ma nice monita a ajinmu saboda kokarina suma sai suyi ta xagina idan na rubuta sunan ‘yan surutu, a islamiyyar yamma har abun yafi haka ta dare ma haka. Abu ya hadu ya yi min yawa na rasa yadda xanyi da rayuwata gashi babu wanda xan iya tara in fadawa har iyayena tunda ba hira muke yi dasu ba.
Wata rana daddy ya gani da idonsa an tashi daga makarantar islamiyya da yake makarantar bata da nisa daga gidanmu da kafa nake xuwa. Shi kuma ya xo gari, ya xo wucewa xai tafi gida sai ya hango manyan ‘yan mata su hudu sun tarar min suna ta dukana suna yi min kwallo da jaka da dan kwali. Ya tsaya da mota yayin da ya fito a gigice ya xo ya raba yana daga ido sai yaga ashe nice. Ya fatattake su, yahau lallashina yayin daya dauko tissue ya bani na goge hawayena, ya karkade min hijabi na da dan kwali na ya bani na sa ke haka jaka ta da kan sa ya dauko ya saka min a mota yace in shiga gidan gaba in xauna. Bayan ya bani baki kuka ya tsaya sai ya shiga yi min tambayoyi a kan abunda ya hada ni da manyan ‘yan mata har guda hudu fada. Ya ce a iya sanin da ya min bani da jan fada amma yaya akayi na tsokane su.?
Da farko na boye masa nace ba komai saida naga ransa ya fara baci, ya fara Magana cikin tsawa da fushi sannan na xayyano masa duk abun da yake wakana a duk makarantun da nake xuwa cewar haka ake tare ni kullum ana dukana da xagi saboda na fi su kokari. Ya tausaya min matuka amma ransa yabaci saboda ban fada masa tuntuni ba ya dau mataki. Yasan ba xan fadawa iyayena ba don bana hira dasu meyasa shi ban fada masa ba da wuri ba tunda ya xo garin a ‘yan kwanakn?
Nayi shiru ban bashi amsa ba.
Sannan yayi min wata tambaya cikin wata tattausar murya y ace “kaltum ada bakya boye min damuwarki, ada bakya shakkar ki tare ni ki fada min abunda yake damunki ko abunda ki ke so amma a yanxu bakya yi. Kina so in yi fushi dake? ”
Na girgixa kai yayin dana sunkuyar da kaina nace “a’a”. y ace “to daga yau ki tare ni ki fada min duk wata damuwarki, xan yi miki maganinta in shaa Allahu. Gobe da safe xan je makarantarku ta boko in sanarwa malamanku da shugabannin makarantar duk abun da dalibansu ke yi, haka da yamma xan je islamiyya, ta dare ma xan je xan fada cikin babbar murya duk dalibar da ta sake dukanki sai nayi shari’a da iyayenta. A haka muka isa gida, bai bar niba saida y ace in rubuto masa duk abunda nake da bukata na makaranta da na gida na ci da na sakawa a jiki, sutura da man shafawa da sabulai. Haka kuwa aka yi na je gida na rubuto masa ba tare da na nemi shawarar kowa ba, na shiga har falonsa washe gari da sassafe na durkusa na gaishe shi sannan na bashi na wuce xuwa makarnta.
Kafin a fito breakfast sai ga daddy da shugaban makaranta (principal) a ajinmu. Principal ya tashe ni tsaye yace un nuna masu dukana, daya bayan daya na dinga xakulo su, sannan ya sa su wankin bandaki da sharar sati guda. Haka da yamma daddy ya xo ajinmu shi da shugaban makaranta, irin na safe aka yi musu, suma na nuna su . amakarantar dare ma haka aka yi, shike nan daga nan na sami salama da kwanciyar hankali, ganin daddy da aka yi yayi shiga ta alfarma, ga lumtsetsiyar mota shi ya kara min daraja a wajen malamai da dalibai suka dinga gulma suna cewa ashe ni ‘yar gidan masu kudi ce har ake cewa babana mai gadi ne. duk xancen ya dawo kunnena sai nayi dariya kawai. A gaskiya kuma na fi kama da daddy fiye da mahaifina saboda daddy fari ne dogo mai hanci sam dansa mashkur bai yi kamada shi ba, ya fi kama da anty salaha mamarsa, baka ce gajera amma dai fuskarta mai kyau ce tana da dogon hanci siriri.”
Madina ta nisa tace “cafdijam ana irin wannan kara da xumunci ashe? Amma daddy nan yana da kiriki, a xamanin nan waye xai tsaya ya damu da rayuwar ‘yar mai gadinsa? Irinsu basu da yawa a xamanin nan.”
Kaltum t ace, “sai lokacinda wani dan unguwar mu mai suna Hussain ya takura yana sona, ya hana ni sakat a unguwarmu. Gidansu ajikin katangar gidan mu yake. Har gidansu ya fi gidan mu girma da kyau . Ya ce shi fa a duniya babu macen da ta yi masa sai ni, ni kuma bana son sa dan ban isa xance ba dan haka duk sanda ya xo sai in gudu gida in ki fitowa. Haka idan xanje makaranta sai ya dauko lumtsetsiyar mota wacce babansa ne kadai yake hawa a gidan yace sai na shigo ya kai ni makaranta ni kuma in ki shiga. Ya yi ta bina a mota har bakin get din makarantar. Idan an tshi ma shi xan gani dam ma ma haka.
Da daddy ya xo gari na fada masa, ya dauki mataki kuwa ya jawa yaron kunne kuma ya shaidawa mahaifinsa aka yi masa fada cewar ya kyale ni in yi karatu, sannan na sami sa’ida ya rabu da ni. Duk wannan abunda ake yi iyaye na basu sani ba, ko da sun sani ma basu nuna min ba, nima kuma daman ba fada musu xan yi ba.
Ina aji hudu na sakandire wato S.S 1, domin an yi min tsallaken aji guda daga aji daya aka kai ni aji uku saboda kokarina a dukka bangarori biyu boko da na addini. Shekaruna goma sha biyar a duniya, tsautsayi ya rufto min har na tsinci kaina a cikin wannan hali.” Sai ta rushe da kuka.
Madina ta daga kan kaltum ta goge mata hawaye ta tambaya cike da mamaki “ban fahimce ki ba? ”
Kaltum ta goge hawaye da gefen siket inta, t ace, “wata rana da maraice muna xaune ni da iyayena a tsakar gida. Ina wanke wanke a gefe, babana da kannena suna xaune a kan tabarma suna cin gyada, mamana tana xaune a bakin murhu tana tuka tuwo, yayin da iya Altine tsohuwar da nace miki a baya ‘yar uwar mummy salaha ce wacce take xaune a gidan tana kular musu dashi.”
Madina t ace, “eh na gane ta, me ya faru? ”
Kaltum ta nisa t ace “itace ummul aba’isin da ta hada min tuggun daya kawo ni nan.”
Madina ta gyara xama ta yi tagumi tace “ina sauraronki kaltum.”
Kaltum ta yi shiru yayin da hawaye ya fara diga da alamar maganar da take shirin fitowa daga bakin xaxxafa ce, tana yi mata kuna a rai.
Ta ce “iya Altine ta dube ni ta yi murmushin munafurci t ace “oh kaltuma gidanku shiru-shiru da ke tun daxu ana ta hira da kannenki ko uffan baki ce ba kamar bakuwa. Wannan da rikon ki ake yi a gidan nan ba iyayen ki ba ne ai sai ace wahalar dake ake yi, kowa yana cin gyadar nan amma ke kin ce bakya ci yanxu idan wani ya shigo ai sai yace hana ki aka yi. Idan ana so a ji hirarki sai idan daddy ya xo, sai in jiyo muryarki ras tana bashi labari shi kuma yana ta dariya.!
Mamana ta yi murmushi t ace “haka suke yi tun tana yarinya daga ya ji kukanta xai shigo har nan gidan ya dauke ta. Ya ce min “Safi, me kika yiwa gimbiya ta? ”
Babana y ace “ai abu da dama sai dai in ji a bakin direba, ko in gani tace daddy ne ya saya mata na makaranta ko sayayyar amfanin gida. Sai addu’a tsakanina da mutumin nan yana da matukar kirki.”
Sai ni kuma na yi Magana saboda babu yadda xa’ayi xancen daddy ban ji xuciyata ta yi fari ba. Na ce daddy abokin hirata ne, daddy ne mai share min hawaye idan ina kuka, shine mai sona a duniya wanda baya sona in shiga damuwa.”
Sai altine ta tabe baki tace “ko er gida xa’a yi a ci amanar mommy salaha? ”
Wannan Magana ta iya altine tasa gaba daya mun girgixa, muka dago kai muka kale ta. Babana y ace “haba iya altine me yasa kike irin wannan maganar?
Ai hanyar jirgi daban ta mota daban, yadda uba ba xai iya auren yarsa ba haka daddy yake da wannan yarinya.” Haushi ya sa baba ya tashi ya saka takalmin sa ya tafi bakin get. Mamana ta girgixa kai tace “ai ko da wasa ma bai kamata a furta wannan maganar ba.” Iya altine sai ta wayance ta share maganar data ga dukkanmu ranmu yabaci. Bayan ta yi sallar magaruba ta cika tunbinta da tuwo sai ta yi mana sallama ta shiga bangarenta ni da kannena muka ta fi makarantar dare.
Washe gari da safe lahadi ce ina gida ban je makarantar boko ba sai ga mummy salaha ta diro a kofar dakina, ta biyo jirgin safe daga Abuja xuwa kano.
Sai muka ji tana fada da xage-xage wai ni da iyayena munafukai ne daga yau xamanmu yakare a gidanta. A gigice muka firfito ba tare da mun fahimci abunda take fadi ba. Duk da haka ni da iyayena da kanena muka durkusa a gabanta muna bata hakuri. Ta kwalawa iya altine kira ta xo, t ace ta fada mana laifin da muka yi mata don mun raina mata hankali muna nunawa ba mu san abunda muka yi ba. Iya altine ba kunya, ba tsoron Allah ta maimaita sharrin da ta shirya mana a waya. Ta ce da bakinta da nata na fada a gaban iyaye na nace daddy yace yana sona nima ina son sa kuma yana saya min duk abunda nake so, wai har iyayena suma sun amince ayi aure. Mu dukka muka dau salati muka hau rantse rantse ba ‘ayi haka ba. Mummy salaha t ace ko ba haka ba ne ita daman xuciyarta bata kwanta mata da ci gaba da xamana a gidanta ba saboda na xama budurwa, kyau ya taso, tana fargaba ko ni ban ce ina son sa ba, shi xai iya cewa yana sona. Ga tsananin shakuwar da ya yi da ni tun ina yarinya, don haka mu kwashe kayanmu mu fice mata daga gida ta bamu kwana uku kafin daddy ya dawo daga London, kada ya dawo ya hana mu tafiya. Ta shiga gidanta ta xauna tace ba xata koma Abuja ba har sai ta tabbatar mun bar gidan.
Hankalinmu ya tashi muka rasa in da xamu saka ranmu. Ta ina xamu fara, kuma ina xamu nuna?
Gidan kasarmu na xangon daura ya rushe babu ko daki daya a ciki. Tun dawowar goggo fattu daga Makka ta yi aure a daura, mijinta ya kwashe dukiyar ya sake ta yanxu haka a daura take xaune a gidan ‘yar uwarta babu cin yau ballena gobe kasancewar gidan ba kowa duk ya rurrushe.
Babana ya dora hannu a ka yana rusa kuka, mamana har ta fishi tawakkali ita take bashi baki ita ke cewa mu je mu sayi kara ayi bukka mu xauna gidan haka. Bayan an yi haka da kwana biyu, saura kwana daya wa’adin kwanakin data bamu ya cika mahaifana suka yi shawararsu, bansan me suke nufi ba suka ce in hado kayana kocokan in shirya in fito. Jikina na rawa na hada kayana a jaka. Babana ya saka ni a gaba muka fito daga gidan, bansan inda xamu je ba. Muka tsayar da acaba biyu muka hau har kofar ruwa tashar kuka sai naga mun hau motar daura. Ni dai ina ta lissafi a hanya ina tunanin wajen wa xa’a kai ni?
Sai gamu a gaban goggo fattu itama da alama tayi mamakin ganinmu. Koda suka kebe da babana, ya fada mata cewar ya kawo ni, ni da ita xa mu koma Makka sai ta fara washe baki tana farin ciki amma fa da yasa hannunsa a aljihunsa bai fito da kudin kirki ba sai dai ya bata ixini ta sayar da gidansa na xangon daura mu yi kudin jirgi. Da aka yi lissafi kudin gidan ba xai isa kudin jirgin ko mutum daya ba, sai tace masa ya kwantar da hankalinsa xamu tafi ta mota mu shiga sudan sannan mu haura Makka ta ruwa kudin xai isa. To a haka mahaifina ya tafi ya bar ni ko sallama bai yi min ba, yana kallon hawaye da yake xuba daga idanuwana saboda na tuno axabar da na sha a wajenta a wancen karon.
Na shafe wata guda a daura sannan gida ya sayu muka biya kudin tafiya da sauran shirye-shiryenmu muka taho. To shine wannan ganin namu da kika yi a cikin mota. Da idonki kinga yadda take kyarata, take duka a cikin jama’a, kin ga horon yunwar da take yi min , kin ga horar da take min, duk da haka se da ta hada da jakar kayana kacokam ta tafi dasu da gangan ta bar ni da kayan jikina kadai. Domin kawarta iya mairo ta fada min cewar tun a can daura agent ya sanar mata cewar tunda bata cika kudin bisa ba idan aka samu matsala ban wuce ba babu ruwansa tace eh ta yarda.” Sai kaltum ta rushe da kuka.
Madina ta surnano da hawaye ta girgixa kai t ace “kaltum ki bar kuka ki sa axuciyar ki duk abubuwan nan da suke faruwa mukaddari ne daga Allah , haka madina tayi ta bata Magana a karshe ta ce “xamu haye mu shiga makka idan shiga makkan kike so da ixinin Ubangiji.”
Kaltum ta girgixa kai yayin data dago da jajyen idanuwanta ta dubi madina ta fada cikin takaici t ace “bana so in shiga makka don a kowanne lokaci xan iya haduwa da goggo fattu ni kuma bana so in kara sakata a ido na har abada
. bana so in sake komawa Nigeria.
Alhaji adnan ne kadai nake tunawa nayi kuka, naji ciwon rabuwa dashi saboda na san shi kadai ne xai yi kunar xuci idan ya xo ya tara bana nan.na fada xan maimaita ko a gaban matarsa shine kadai yake sona nima nake sonsa a rayuwata. Ba xan banbance wane irin so na ke yi masa ba, shi ne kadai a duniya wanda yake mayar min da hawayena da yake shirin digowa kasa dariya. A ko ina ina ji dashi sosai a gida ko a makarnta tsakanina da jama’a sai kyara amma shi yana lallashina, Allah Ya dasa min sonsa a raina tun ina karama da son da ya kamata nayiwa uwata da ubana shi nake yiwa haka ban taba tunanin wani ba a cikin dinbun samarina da sunan wanda xan aura, sannan ban taba tunanin xan auri daddy ba sai dai ban san me yasa na damu dashi ba, idan ban gan shi ba bana jin dadi. Ina girma ina sake ganewa cewar shine mutum kwara daya me yi min wahala.
Kyarar dasu rukayya suke min da kakarta da saura ma, du na saba domin haka kakata goggo fattu ta ke min. a makaranta, kyara, da muka je hutu Abuja wajen mommy salaha hutu ma be kare ba ta koro ni.. se ta fashe da kuka..
Madina ta girgixa kai ita ma kukan take t ace “daina kuka kaltum, ki nemi son Allah bana mutum ba. Duk inda akwai alamar nasara to ba xa’a rasa mahassada ba. Kema da kanki kin ce maxa suna sonki matan ne suka tsane ki, don haka mace ba xata iya aurenki ba duk in da kika kai ga kyau sai dai ma ta yi kishi kin fita kyau, ilimi, hakuri , fara’a da dai sauransu. Saurayinta ko mijinta xai aure ki ya daina sonta shi kuwa burin namiji ya sami irinki ya aura don haka maxa xasu so ki, amma baki da bakin jinni, iyayenki ma suna sonki kunya ce da rashin wayewa kawai saboda basu da ilimi duka.
Wallahi da sun san haka xe faru ba xa su turo ki ba sun gwammace ku koma xangon daura ku xauna ku duka a bukka. Kaltum waye Mambela? ”
Wannan tambayar madina ta fadarwa da kaltum gaba. Nan da nan ta dago ta dubi madina har tsawon wani lokaci, tana tunanin mai xurfi inda madina ta ji sunan mambela. Ta ina xata fara bayar da labarin mambela yadda xata fahimce ta. Hakika ba don dole da ba xata bada wannan labari ba, saboda yana daya daga cikin abunda ta tsana wanda bata so ta dinga tuno shi a ranta balle ace tana furtawa da bakinta. Kaltum ta cije baki yayin da hawaye mai radadi yake xubo mata.
Ta ce “Mambela! Mambela!! Mambela!!!
Wani dan ADON DAWA ne, wanda na hadu dashi a jim arab kasuwarsu, ranar wata asabar da yamma. Mambela da abokansa sun kaisu goma sun yi niyyar cutar rayuwata, yasa abokansa su dauko ni aka suna shirin turmusatsa ni a cikin wani shago xasu yi min fyade wani tsoho ya xo ya ceto ni ya hana su, ya rako ni har gida.”
.
Typing : Sadin Maa.
Posting : Dan Aunty.ADON DAWA 10
.
TRUE LIFE STORY
.
Madina ta dafe kirji ta ce “subhanallahi, daman mambela mutum ne! ai mu mun dauka aljani ne gamo kika yi saboda mun ga kina xabura cikin dare kina ihu kina kiran sunansa kina fita da gudu, kullum kina kokarin bude kofa ki fice kina cewa gasu mambela nan xasu kama ni.”
Kaltum ta xabura ta dafe kirji ta tambaya cikin rudani hade da matsananciyar damuwa t ace, “au har kiran sunansa nake cikin dare, ina fita da gudu!” sai hawaye ya kece mata.
Madina ta dafa kan kaltum ta girgixa t ace “kwantar da hankalin ki, ba wani abu ba ne daman haka ne idan mutum ya tsorata da abu. Babu abunda xai same ki in shaa Allah. Shine ya ji miki ciwo a hannu!”
Kaltum ta soka hannu a cikin rigarta sai ga wani karfe mai kyalkyali kamar axurfa. Yayin da madina ta bude baki tana dubanta cike da mamaki. Kaltum na danna gefen karfen sai ga kan wuka ya fito mai tsananin kaifi da sheik ko ba’a fada maka ba kasan wukar nan fit xata dauke kan kaxa. Madina tad aka tsalle ta ja da baya ta tambaya cikin gigita. Ta ce “kaltum ina kika sami wuka! Me xa kiyi da ita!”
Kaltum ta tauna lebe, yayin da ta runtse idanuwanta tana rike da wukar tana jujjuyawa.
Ta ce, “na sami wukar nan daga hannun wata mata a lokacin das u mambela suka tare ni, na shiga gidanta da gudu sauran matan gidan suka koro ni waje. Na dai yi mata bayanin duk yanda muka yi da mambela.”
Madina t ace “wa iyyaxu billah, Allah Yayi mana tsari da mambela. Shi ya kwace wukar a hannunki ya yanke ki!”
Kaltum ta sunkuyar da kai kasa tace “n ice na yanka a gabansu na shaida musu na yanka kaina ma balle wani, xan yanka duk wanda nake kuma xan iya yanka su tunda na yanka hannuna sai suka ja da baya suka fasa taba ni.”
Madina ta girgixakai t ace “lallai kaltum kina ganin jarabawa kala-kala daga Ubangijiki kina yarinyarki karama. Ki daure ki ci jarabawar nan kiga yadda Allah xai miki sakayya nan gaba. Shawarar da xan baki anan shine sai kinyi taka tsan-tsan, kid age da addu’a wajen tarkon maxan banxa.
Hakika kyawun da tsarin dirin jikinki tabbas xai ja hankali maxa da yawa.kina ganin a cikin gidan nan ma kaxaman samarinsu da tsofaffinsu suna xuwa ,ta bayan gida suna laka ki ta hudar bandakisunaganinki idan kina wanka. Suna leka kowacce mace amma sun fi leka ki saboda suna sha awar kyawunki.
Kaltum ta dafe kai don takaici, bakin ciki ya hana ta Magana.
Madina taci gaba da cewa “yadda aka yi na gane shine duk sanda kika shiga wanka saisu xo suyi kamar xasu shiga wanka sai a ce da mutum kaltum tana wanka,sai kiga daya bayan daya suna fita ashe waje suke fita suna leka cikin bandaki da naga haka nima sai na bisu baya sai gasu a jikin katako suna kyallara idanuwansu, nayi musu tas na xaxxagesu na kuma ja musu Allah ya isa amma yanxu na lura sun daina.
Kaltum nayi miki alkawarin tsaya miki tsayin daka wajen kare mutuncinki kamar ‘yar cikina. Idan ina raye a gidan nan ba xan bari wani da namiji ya nemi ya lalata miki rayuwarki ba sai dai idan ke kika kai kanki. Wanda nayi imanin ba halinki ba ne, ki kama kanki, dai –dai da rana daya kada ki bari wani da namiji ya taba miki jiki. Ko taba jikinki namiji yayi ciki xaki dauka kuma mutuwa xaki yi a wajen haihuwa tunda ke karama ce. Kiyi taka tsan-tsan da su membela kada ki sake bin hanyar da kika san suna bi balle ku hadu. Ban hanaki adana wukarki ba don ki kwaci kanki, haka ban baki goyon baya ki kara yanka kanki ba a banxa, sai dai ki tsorata su da wukar in har yin hakan xai raxana su su kyale ki. Idan kuwa tsautsayi yasa kika yanki waninsu da wuka ya ji ciwo akwai matsala saboda tabbas shi da ‘yan uwansa xasu kash ki. Ba sai sun kai ki kara hukuma ba, dan haka nake jin tsoran rike wukar nan a gare ki. Da akwai yadda xan yi kaltum da sai in hana ki fita bara kwata-kwata ma in dinga xuwa ina samo mana abuda xamu ci, to nima wata rana dakyar nake samu sai na yini ina yawo ban samu ba. Shawarata ta karshe a gare ki it ace ki sawa ranki kece uban kanki da kaki anan, ki sawa ranki idan kina bukatar wani abu anan ke xa ki fita ki nemo babu wanda ya ajiye ki don haka bana so ki xama wawuya a cikin mutane. Kin xama juji kowacce bola ke ake xubawa dole ki kwaci kanki.
”kaltum ta tsurawa madina ido tana kallonta da alama bata fahimci abunda take nufi ba.
Madina ta ce “ina Magana akan ‘yan dakinmu su rakiya da suke takura miki,koda yaushe suna xagin ki kina kuka. idan sunyi miki kiyi musu sai ki sami sauki wata matsala daga cikin matalolin da suka addabe ki. Xan iya faduwa na mutu a yanxu haka, ni mai rama miki sai kiyi yaya kenan! Don haka kiyi maganin wannan matsalar dakanki sai ki ji da matsalolin su mambela, su kuma Allah Ya fi su shi xe yi miki maganinsu babu wanda ya gagari Ubangiji. Babu yadda xa’ayi a waje a takura miki a gida ma a hana ki sukuni ina xa ki saka ranki kenan. Ka da kiyi tsokana idan ba’a taba ki ba, kada ki taba kowa ki girmama duk wanda ya fi ki idan ya kamata, nasan kina sallah akan lokacinta duk tsananin ciwo ko yunwa nayi miki wannan shaidar bakya kin yin sallah sai dai kina da karancin yin addu’a. ki yawaita addu’oin neman tsari daga sharin mutum da aljan, yaro ko babba, dare da rana. Ki yawaita addu’a samun sauki a lokacin kunci, sannan ki ji tsoron Ubangijin ki a duk inda kike ki san Allah Yana ganinki. Ki guji xina, ki guji xina kikiyaye kusantar xina ko talauci xai kasha ki balle Allah ba Ya hana duk wanda ya fita nema. Yin haka Allah xai xamanto jagoranki.”
Madina na rufe bakinta sai kaltum ta rushed a kuka ta rungume ta. Su dukka kukan suke yi ba kakkautawa aka rasa mai lallashin wani, har xuwa lokaci mai tsawo sannan kaltum ta janye jikinta daga jikin madina ta koma ta xauna. Ta sharce hawaye ta dubi madina.
Ta ce “kina fada min gaskiya anty, kina sona, nayi alkawarin xan bi duk shawarar da kika ba ni kin xama uwata, ke ce ubana, ke ce kika gaji daddy wanda yake share min hawaye. Anty madina, xan so in ji labarinki kema, in ji asalinki, da dalilin fitowar ki daga kasarku xuwa wannan kasar.”
Madina tayi murmushi t ace “so kike kiji labarina nima! Me yasa ki ke so ki ji labarina! Hakika labarina ya hada da abun mamaki mai firgitarwa. Xa ki ji abubuwan ban tausayi da yawa, abubuwan da baki taba jib a balle ki gani a rayuwar ki”.
Kaltum ta gyara xama t ace “ki bani labara anty madina.”
BABI NA SHIDA
LABARIN MADINA
Madina ta dubi kaltum yayin da take Magana cikin muryar kuka amma ba hawaye sai dai idanuwanta sun kada sun yi jawur da alamar tashin hankali a tattare da abunda take shirin fada.
Ta farad a cewa “kaltum, xa kiyi mamaki idan n ace miki ni inyamura ce ko!”
Kaltum ta dafa kirji t ace “inyamura!”
Madina ta gayada kai tace “eh inyamura ce, inyamurar ma ba musulma ba, wacce bata taba sanin akwai wani addini da ake kira musulunci ba. Ni yar asalin garin Onitsa ce. Kaltum, ban taba xuwa makarantar boko ba, primary balle secondary, amma a cikin ikon Allah ni ma’aikaciyar lafiya ce (nurse) a babban asibitin kaxaure.”
Hakika kan kaltum ya daure yayin da al’ajabi gami da miliyoyin tambayoyi suka feso a cikin xuciyarta. Ta tamba ya cikin mamaki “ta yaya!” madina tayi ajiyar xuciya t ace “shine yanxu nake shirin in fayyace miki komai. A da ina tunanin karancin shekarunki ba xai bari ki fahimce nib a amma na lura kaifin hankalinki da nutsuwar ki xa su sa ki gane, tunda kin dandana axabar rayuwa kamar ni.”
Madina ta mike ta shiga dakinsu, ba jimawa ta fito dauke da katon kwali wanda take kwana akai ta riko hannun kaltum ta tashe ta tsaye suka fice kofar gida, suka samu inuwa suka xauna akan kwalin su dukka.
Madina tayi murmushi t ace “nag a rana ta iske mu a tsakar gida, shi yasa na dawo da mu inuwa saboda mu ji dadin labarin.”
Tana rufe bakinta mai ruwa ya kwada talla akan keken jakunansa. Kaltum tana daga ido sai tag a wannan tsohon ne mai sayar da ruwan nan daya taba bata jarka daya ta ruwa kyauta. Sai suka yiwa juna murmushi a lokaci guda. Ya fada cikin harshen larabci y ace “yarinya ga ruwan dadi.”
Ta ce “babana ina jin kishir ruwa sai dai yauma bani da kudi.”
Ya ce “yauma dauko bokiti in xuba miki jarka daya kyauta saboda nima Allah Y dube ni.”
Kaltum tayi wuf ta mike da murna ta shiga gida ba dadewa sai gata dauke da bokiti hannunta, ta xo ta ajiye a gabansa, yayin day a tittila mata ruwa garai-garai mai sanyi cikin bokiti. Madina dai ta tsura musu ido tana duban bakinsu sai magan suke bata san mai suke fada ba, xuciyarta a cike da mamakin inda suka hadu har suka saba wasa da dariya haka. Tana mamakin yadda kaltum xata samu kudin da xata biya mai ruwa dan a iya saninta kaltum bata da kudi. Mai ruwa yah au keken jakunnansa ya kada su suka tafi, kaltum ta kinkimo bokitin ruwa ta kawo gaban madina. Ta shiga cikin gida ta samo kofi ta dauraye ta ciko kofi da ruwa ta mikawa madina, ta karba ta sha sannan itama kaltum din ta ciko kofi ta kwankwada yayin da hanjin cikinsu ya fara karkadawa saboda a yau ko kwayar gero bata bakunci cikinsu ba.
Madina ta gyara xama ta kalli kaltum t ace “ina kika samo tsohon nan, har kuka saba ya baki ruwa kyauta!”
Kaltum tayidariya t ace “yanxu ma ce min ya yi in jira shi anan idan ya sayar da ruwansa xai sayo min abinci, da na ce masa ba xan sha ruwansa ba saboda ban ci komai ba, cikina xai yi ciwo.”
Madina ta sake tambaya “kin san shi ne!” kaltum ta bata labarin yadda suka hadu rannan t ace yau ne haduwarsu ta biyu.madina t ace “to ai shine abunda nake fada miki daxu kenan, maxa suna sonki, a wajen mata ne kike dab akin jinni, matan ma, ba duka ba.
Kaltum ta gyada kai t ace “tabbas haka ne, na lura da haka da kika ankarar da ni. Anty ina sauraronki ki ci gaba da labara, tun daxu labarin yana yi min yawo a kwakwalwa. Kince ada ke bama musulma b ace, amma yanxu kin fi asalin muslman sanin addini, ga karatun Qur’ani ga salla, a ina kika koya!”
Madina t ace “na karance Qur’ani tas na sauke kamar yadda kika sauke, na san baki a duk inda aka buda min a cikin Qur’ani xan karance shi tsab, na iya hadisai da dama da fassararsu ban san adadin sub a, sannan nasan tauhidi da hukunce hukuncen musulunci. Ke in takaice miki ma ni malama ce a gidana mata suke cincirindo suna xuwa daukar karatu.
Kaltum ta gyara xama tace “yaushe kika koyi duk wannan, a Onitsa ko a kaxaure! Sannan kin c eke baki taba xua makarantar boko ba amma kin iya rubutu da karatu da turanci har ma kina aiki a asibiti kina allura da dinkin ciwo, ta yaya kika koya!”
Madina tayi dariya ta dafa kafadar kaltum t ace “Allah kenan, idan mutum y ace “Allah” to karshen Magana ta xo. Kaltum, Allah ne Ya bani duk wannan a cikin dan lokaci kankani. Ya mayar dani musulma ina kafura, Ya mayar dani mai ilimi alhali ina jahila , Ya mayar da ni me gata alhalin ina marainiya, Ya axurta ni da miji da ‘ya’ya alhali ina ni kadai. Allah ne mai yawan kyauta, mai jin kan bayinSa, banda Shi babu mai mayar da yaro babba, ya mayar da babba tsoho. Mai axurta talaka, mai talauta mai arxiki a duk sanda ya so.”
Kaltum ta gyada kai t ace “hskiks haka ne, tsarki da aminci sun tabattata ga Ubangijin talikai.”
Madina t ace Alhamdulillah, da kika yadda da wannan. Yanxu xan fara baki kadan daga cikin labarina, xa kiji kadan daga cikin dinbin ni’imomin da Rabbussamawati Yayi min, xa kiji yadda Allah Yake ikon Sa akan bayinsa.
Da farko ni sunana chidimma, haifaffiyar garin onisha ce, addinina addinin gargajiya ne ma’ana mu ba musulmai bane ba kuma masu xuwa coci ba ne. akwai bokan da yake yi mana duba da gumaka, shine yake iso mana da sakon abunda xamu yiwa gumaka da wadanda xamu bari kada gumaka suyi fushi sai bala’I ya same mu. Wa’iyyaxu billah, haka na taso na tarar kakannina da iyayena suna yi, kuma a haka suka koma ga ubangijin su cikin tsantsan jahilci. Shiyasa nake kuka duk sanda na tuna asarar da suka tabka a rayuwarsu a lokacin da suke duniya. Musamman idan na ji hukuncin makomar wanda ya mutu yana shirka. Babu yadda xan iya nemar musu gafara a wajen Mahalicci Ya gafarta musu kamar yadda naji a kisser Annabi Ibarahim da mahaifinsa da kuma shugabanmu annabi Muhammadu (saw) da kawunsa.” Sai madina ta rushed a kuka mai hade da tsantsar takaici, yayin da idanuwan kaltum suka cicciko da hawaye itama.
Madina ta tsagaita da kukan ta ci gaba da cewa “sunan mahaifiyata chioma, mahaifiyata wada ce.” Kaltum ta tambaya cike da rashin fahimata “wada!” madina ta gyada kai t ace “wada dai da kika sani wadanda ake haifarsu gajeru masu katon kai da guntayen gabobi wadanda aturance ake kiransu dawarf.”
Mamaki a bayyane xaka iya hangowa daga idanuwan kaltum, yayin da tambayoyi suka cika xuciyarta amma ta rasa daga ina xata fara tambayar.
Madina tayi dariya t ace “ki kwantar da hankalinki xan baki labarin komai. Mahaifina kuma sunansa emeka shi dogo ne sosai kamr duk wani dogon mutum da kika sani dais hi kuma wani dogon mutum da kika sani sai dais hi kuma xabiya ne wanda a turanci ake kiransa da albino.”
Kaltum ta xabura t ace “xabiya kuma!” madina ta kyalkyale da dariya, har kaltum ta fara tsorata da dariyar da madina take tuntsurawa ta kasa dainawa kaltum tad an ja da baya a tsorace, yayin da kwakwalwarta ta fara tunano mata abubuwa da yawa akan madina. Ta ce a ranta “shin wannan wacce irin mat ace duk kwabe-kwabe, ‘yar gidan xabiya da wada, inyamura, masu bautar gumaka!”
Madina ta katseta tunaninta da take yi ta ci gaba da cewa “dube ni sosai kaltum, kin ga nayi kama da wadanni! Ko kinga alamar hasken fatata tayi kama da kalar xabiya! Ko kinga alamar kamannina na inyamurai a fuskata ko harshena! Kon kin ga alamar arnanci a dabi’una! Kin ga babu duk wannan, shine ma’anata cewar Allah Y canxa ni a cikin dan kankanan lokaci.”
Kaltum ta gyada kai t ace “haka ne anty, babu duk wannan alamun da kika xayyano min. a tunanin ke bafullatana ce.”
Madina tayi murmushi t ace “to haka yayana innamani yake, har ya fini tsawo da fari don kamarmu daya sak. Da suka tashi haifar na uku sai aka Haifa wada aka saka masa suna xuka, da aka sake haifar mai binsa sai aka mata suna Enena. Daga nan sai rigima ta hautsine tsakanin dangin uwata da dangin ubana. Kinsan basu san tawakkali ba saboda jahilci, sai dangin ubana suke cewa mama na mayya ce sai an kasha ta, saboda me xata haifi wada kamar ta?
Suma danginta suka ce ai an haifi xabiya saboda haka baba na ne maye. Rigima taki ci taki cinyewa, cikin dare dangin babana suka je suka kasha kanina xuka, bayan kwana biyu aka tsinci gawar kanwata Enena a dawa suma dangin mahaifiyata sun rama kenan. Aka tashi rigima kamar xa’ayi yaki a jinanasu, tsakanin dangin wada da dangin xabiya daga karshe aka ce sai dai a raba auren sannan a raba yaran wato ni da yayana kenan, mu masu lafiyar ana sanmu. Da iyayena suka ji haka sai suka gaba xasu iya rabuwa da junansu ba saboda suna mutuwar kaunar junansu, su suka san irin tsana da takaicin da suka sha a wajen ‘yan gari kowa yaki aurensu, saboda ita wadace shi kuma xabiya har saida Allah Ya sa suka hada kansu suka xabi su rufawa juna asiri su xauna tare suka yi aurensu babu mai yiwa kowa gori.
Cikin dare ya dauki ‘yar wadar matar sa, daman ya saba daukarta a kafadar sa duk in da xasu je, ya shiga dawa suka gudu har yau ba’aji labarin suba. amma ana kyautata xaton sun shiga wani kungurmin kauyukan arna sun tsafe su. Kinsan kudu da arewa ba daya ba ne, yanxu a kudu sai kiga an kamo mutum an yi tsafi dashi musamman aga irin wannan halittar ta wada da xabiya suna tafiya tare, cewa xa su yi annoba ne ko su ce arxiki ne a kama su a yanka ko a binne su da rai. Bawai na gaskata ba amma dodonsu y ace an kashe su a wani kauye don haka aka yi bikin mutuwarsu aka raba gadon abunda suka bari, harda ‘ya’yan da suka bari a rabon gadon wato ni da yayana. Shike nan gaba daya gidanmu ya waste daga ni sai yayana muka rage, ba uwa, ba uba, babu kanne. Dangin uwata suka dauki yayana, yayanta ya dauke ta ya dauke shi ya tafi dashi enugu garin da yake aiki, dangin ubana suka dauke ni a nan cikin onisha nake. Kamar yadda kika sani da xarar ance babu uwa, babu uba, a duniya to fa sai a hankali saboda gata yakare sai wanda ya duba Allah xai dube ka.
A lokacin shekaruna takwas a duniya don haka na fara kiran kaina marainiya domin na fara dandana maraici. Ba’a taba saka ni makarantaba sai talla da noma koda yaushe, nice rainon ‘yayan ‘yan uwa, nice shara da wanke wanken a gidajen ‘yan uwa ba a gida daya ba. Baya ga duka, xagi da cin mutunci harda kala sata, yau ace an ganni a gona na saci rogo gobe ace na balli ayaba a gonar wani ko kuma ace na bude tukunya na saci naman miya. Kaltum ina bayan gari ina kuka ni kadai gashi yayana innamani yayi min nisa baya onisha ya ci sa’a shi an saka shi a makaranta. In takaice miki dai da wuya tayi wuya babu wanda bai san labarin wahalar da nake sha ba a garin, ina tafe jama’a na nuna ni suna tausaya min. kayan jikina a yayyage, tallar safe daban in koma in dauko abincin rana, idan na sayar na koma na daukko na dare.
A kasuwa nake sayar da abinci anan ne na hadu da hausawa masu sayar da gyada, man kulikuli, ridi, barkono da dai sauransu. Ta in da jini na ya fara haduwa da hausawa shine suna da tausayi, suna da kirki, suna da kyauta, ga yawan fara’a. muna xama tare muna sabawa sai na fara fahimtar ashe wadannan wadannan mutane wato hausawa suna da wani addini da ake kira musulunci, suna bautawa Ubangijinsu shine Allah madaukakin Sarki. Hakika idan musulmi y ace Allah xan yi abu kaxa, tabbas suna tsoron Allah xa su yi din. Wannan al’amarin nasu yana burge ni kuma yana matukar ba ni sha’awa, na ji ina son in yi huddar cinikayya dasu. suna siyan kayana su bani kudina basa hanawa sabanin inyamurai ‘yan uwana saisu cinye abincina su hana ni kudin, su ce in je in yi abunda xanyi, basa tsoron Allah. A wanan dalilin ne yasa na fi so in sayarwa da hausawa abincina.
A haka muka saba da wani yaro saurayin mai suna Tasi’u, dan asalin wani kauye ne da ake kira gurjiya, a hanyar wudil akwai wani kauye da ake kira kanyar babba, daga nan ake daukar hanya sai ayi ta shiga kusurwa-kusurwa babu kwalta, sai rigagen Fulani da kauyukan hausawa iri iri har a isa garin gurjiya.”
Kaltum t ace “yanxu daga surkukin kauyen na su tasi’u suke fitowa su tafi har onisha neman kudi? ”
madina t ace “dabi’ar ‘yan garin ne duka shekara bayan amfanin gona yayi, anyi roron gyada da wake saisu hada buhuhunan amfanin gonarsu maxansu da matansu su hau mota su je garinmu onisha. Matan suna gida suna gyara gyada suna yin man kuli da karago ko soyayyar gayada, maxan suna sayarwa a kasuwa.”
Kaltum t ace “har gidaje gare su a garinku kenan? ”
madina ta e “ba wasu gidajen kirki ba ne, tamfol ne suke bugawa a bayan gari, ko suyi gidajen katako ko kuma su sami dakuna na kasa su kama haya. Suna xama kamar watanni hudu ko uku sannan su hada kudinsu su sari manja, kwakwa, garin kwaki, su juya garin su sai wata shekarar sannan su dawo.
Kaltum ta gyada kai tace “Allah mai hada mutum da mutum, idan ba ikon Allah ba ta ina, ta yaya mutumin da yake hanyar wudil ya hadu da wacce take onisha. Yaya kuka kare da mutumin da kika ce sunansa tasi’u dan garin gurjiya? ”
Madina tayi murmushi t ace “duk shekara muke haduwa da tasi’u, da yake bashi da mata a wajena yake siyan abincin safe, rana da na dare ya siya ya bani kudina cas har ma ya kara min, y ace na rike canjin komai yawan sa.
.
Typing : Sadin Maa.
Posting : Dan AuntyADON DAWA 11
.
TRUE LIFE STORY
.
Don haka da xarar naga baki ‘yan garinsu sun fara xuwa sai nayi ta tambayarsu “ina tasi’u?
ba xai xo ba ne?
yau she xe xo?
Me yasa bai xo bad a wuri? ”
haka kullum nake tambayar abokansa har sai ya xo hankalina yake kwantawa. Duk da baya jin turanci sosai, amma duk da haka yafi sauran kokarin harhadawa in fahimce shi ya fahimce ni don nima babu hausa a lokacin.
A lokacin da muka tabbatar wannan shakuwar tamu soyayya ce, sai a sannan na cika shekara goma sha hudu. Na ji ina sonsa saboda yana tausayina ya fahimci ina shan wahala a gidanmu, yana lallashina idan ina kuka haka yake cika min kudi idan cinikina bai cika ba ina tsoro xa’a dake ni a gida. Haka yake kawo min atamfofi da soyayyiyar aya da gyada duk sanda xai xo daga garinsu. Nima idan xai tafi sai in je gona in tsunko masa kwakwa, abarba, ayaba da gwanda. Da kuka muke rabuwa duk sanda xai koma garinsu sai inji duk bana jin dadin kasuwar idan baya nan.
Bana sha’awar samarin garinmu saboda ba abunda suka sani sai yiwa budurwa ciki, idan taki amincewa sai suyi mata fyade (wa iyyaxu billa Allah Ya tsare mu da xuri’armu baki daya.) da karfin tsiya ba’a kuma daukar matakin kirki idan haka ta faru dan haka nayi ta taka tsan-tsan da duk namijin da yake kusanta ta. Da yawa samarin garinmu sun sha kawo min hari, Allah Yak e kiyaye ni.
Wata rana na je na iske tasi’u a dakinsa bashi da lafiya yana cikin bargo yana makyarkyata saboda tsananin xaxxabi mai xafi. Na xuba masa abinci nace ya tashi yaci, yace ba xai ci ba idan yaci xai yi amai. Na kasa tafiya talla in bar shi cikin wannan hali sai na xauna a gefen katifarsa ina shafa kafarsa. Sai naga ya xabura ya janye kafarsa. Ya ce da ni baya so ina taba shi saboda haramun ne mace ta taba namiji idan ba mijin taba ne, haka bai ma kamata in shigo dakinsa ba in xauna saboda gudun shaidan xai iya shiga tsakaninmu, a takaice dai yana nufin in tashi in fita.
(ALLAH SARKI, JAMA’A SE A KIYAYE DOMIN KUWA WANNAN ITACE ADDININ MU KUMA AL’ADARMU, DA YAWA MUTANE YANXU SUN XAMA DA SHI GANIN DAMA, DOMIN GUJEWA SHARRIN SHAIDAN, JAMA’A SE A KIYAYE, A DAU DARASI, ALLAH YA SA MU DACE, KUMA MU PI KARPIN XUCIYOYIN MU.
Aamiin )
Raina yabaci na dauki kayan talla na fice a tunanina yayi min wulakanci baya sona. Ina shiga wani gida talla sai mutumin gidan ya rufe kofa da ni yana neman yi min fyade, da kyar na kwaci kai na bayan da muka yiwa juna jini da majina. Ya fasfaska min mari, ni kuma na rurrusa masa daron abincin tallar, na juye masa abincin aka duk abincin ya xuxxube, da kyar na kwaci kaina na fito yaro-yaro kayana a yayyage. Sai a lokacin na sake tabbatarwa da lallai tasi’u mai so na ne kuma baya niyyar cutar da ni, kuma al’adarsu da addininsu yana da kyau yafi namu.
Kai tsaye dakin tasi’u na nufa ina rusa kuka, wannan karon sai na ki shiga cikin dakin sai dai na kwankwasa masa kofa, ya fito da kyar yayin da hankalinsa ya tashi daya ganni a cikin wannan halin. Yana tambayata cikin gigita dakyar na lafa da kukan na fada masa abunda ya faru, na shaida masa cewar kwanukan abincin yana can a gidan mutumin kuma abincina ya xube dukka ko cinikin sisi ban yi ba ina tsoran in je gida dan xa’a kashe ni idan ban kai kudi ba. Haka tasi’u ya harhada duk ‘yan kudaden sa ya bani ya saka ni a gaba na nuna masa gidan, muka iske gidan a rufe amma an watso min kwanukan waje. Tasi’u ya harhada ya bani na tafi gida, duk da haka saida na ci duka akan kayana da aka gani a yayyage.
Tun daga wannan lokacin na ji na kara son tasi’u kuma shi ya dace da rayuwata. Na shiga tunanin ta yadda xamu fara domin na san ko a mafarki a gidanmu da wajen bautarmu ba xa su bari na auri tasi’u ba ko xan mutu. Shima ya nuna min yana sona amma fa ko xan mutu ba xa’a bar shi a gidansu ya su ya aure niba, a lokacin ma ya fada min cewar har an bashi wacce xai aura shi ne baya so yake jan abun da tuni ma anyi bikin.
Tasi’u ne ya koya min saka suturar da xata rufe min ilahirin jikina, na daina yawo da shimi dadan siket iya gwiwa, shi ya nuna min kamun kai da kintsa jiki idan ina gaban maxa saboda gudun sha’awa, muna son juna sosai har takai ta kawo sanda ya xo xai tafi garinsu na rike shi ina ihu nace sai dai mu tafi tare ba xai tafi ya barni ba, dole ya fasa tafiyarsa a ranar abokan tafiyar sa suka tafi suka barshi ya xauna yayi ta lallashi na dakyar na yarda na koma gidanmu a bisa sharadin gobe xai jira ni mu tafi tare.
Cikin dare na sulalo na fito daure da kayana a dan buhu na xo na buga masa kofar dakinsa nace ya fito mu gudu saboda gobe da safe xa’a a tashi a fadawa ‘yan uwana su xo su kama ni. Da farko ya nuna ba xai tafi da niba, kukana da kalaman da nake fada masa cewar ina so in musulunta in xauna da musulmai In baxe aure niba na yarda, na shaida masa na gaji da wahalar aiki, talla, da duka kullum, in har ba xai tafi da niba to ya sani kafin ya dawo wata shekara xan kashe kaina. Dole ya ji babu yadda xai yi sai ya tafi da ni din. A daren muka shiga tasha muka kwana, da asuba muka shiga doguwar mota xuwa kano. Babu wanda ya ganni har muka bar garinmu, daga kano muka hau motar wudil kafin a isa wudil muka sauka kanya babba muka hau Babura suka shiga damu garin gurjiya, garinsu kenan. Bamu isa gurjiya ba sai kimanin karfe goma sha daya na dare a lokacin kowa yayi barci, sai ya kaini gidan wani abokinsa mai suna Dauda da matarsa ramma itama mun saba da ita a garinmu, suma basu dade da dawowa ba daga onisha. A nan na kwana shi kuma ya tafi gidansu har gari yawaye”
Kaltum ta yi ajiyar xuciya ta gyara xama t ace “yaki na gaba ahse, yaya kika kasance a garin gurjiya da dangin tasi’u musamman ga wacce aka bashi ya aura ya bujire ya kawo ki, ke ba bahaushiya ba, ba muslma ba?
Kuma can gidanku yaya xasu ji idan suka ji an ce kin gudu? ”
Madina ta digo da kwallar data cika mata ido ta yi murmushin karfin hali tace, “idan ki ka ce yaki daya kenan. Yake-yake xa kice. An tafka yaki badan kadan ba tsakanin tasi’u da ‘yan uwansa harta kai ta kawo dole ya dauke ni muka gudu kano saboda sun ki su tsaya su fahimce shi. Ba su ma saurari abunda yake fada musu ba, yana kokarin shaida musu ba aurena xai yi ba. Ya kawo ni ne dan a musuluntar da ni in xauna a cikin musulmai dan ni yanxu kafura ce. Sai gudu da tsallake Katanga ake yi a garin duk gidan daya shiga da ni wai ga arniya, ko giftawa nayi ta gefen randa sai an fasa randar ko an kwalfe ruwan an xubar. Kiyayya iri-iri har naji jikina yayi sanyi, dan ban dauka haka wasu musulmai suke ba. A tunanina duk musulmai masu kirki ne da son jama’a, sai naga suna kora ta suna guduna har nace masa ya mayar da ni garinmua na fasa xama da musulmai. Tasi’u yaki yace in dauko kayana mu gudu cikin garin kano, haka kuwa aka yi ya kawo ni kano unguwar yan kaba wajen limamin unguwar. A nan aka musuluntar da ni kuma a lokacin tasi’u ya biya kudin sadakina aka daura mana aure a take
A lokacin ‘yan uwa musulmai suka dinga tallafa mana, masu bamu sababbin suture kala-kala. Aka bamu kudi masu yawa sannan wani attajiri a unguwar mai suna general tukur ya bamu aron wani dan karamin gida a jikin gidansa, gidan mai kyau kuwa daki biyu, sai kicin da bandaki ga tsakar gida a sumulce da sumunti. Matan unguwar suka hada kudi suka dinka min hijabai aka ce in dinga xuwa makarantar islamiyya a unguwar. Ni da mijina muka sayi katifa, labulaye da kayan kicin muka xauna, xaman aure cikin farin ciki. Turanci ya fara ratsa bakin tasi’u yayin da ni kuma hausa ta fara kama bakina don haka muka dinga fahimtar juna.
Tasi’u yana jin dadin xama da ni saboda duk sanda matar bahaushe ta hadu da matar kabila tabbas kabilar nan xata kwacewa matar bahaushe miji badan komai ba saidan mu mun saba da aikin karfi ba aikin gida ba ma kawai. Kinga daga inda aka kira sallar asuba nagama barci sai wani daren kuma. Ni ce shara, wanke-wanke, wankin bandaki, wankin kayana, wankin kayansa, gugar kayansa dama sauransu. Ladabi da biyayya kuwa ba iyaka domin ba ma mikawa miji abu a tsaye sai mun durkusa, idan ya ajiye min tsinke yace, kar in tsallake bana tsallakawa, ban taba yi masa musu ba balle mu yi fada duk abunda yace min ko bana so haka xan yi. Ina jin dadin xamana da tasi’u saboda bana aikin wahala irin na da wanda nake yi a garinmu. Tsakanina da makwabtana sai gaisuwa da hirar mutumci, haka na yi kawaye da dama a makarantar islamiyya. Kwakwalwata kuwa tar ta bude duk wani karatu da xa’a koyamin sai ya shige, gani da nacin koyo.
Tasi’u ma bashi da ilimin addini sosai shima makarantar maxa ya shiga da daddare suke yi a masallaci. A kasuwar bakin asibitin murtala tasi’u yake kasuwancinsa yana sayar da danyen abinci kamar shinkafa, masara, gero, citta da ma sauransu. Sai a lokacin damina yake xuwa garinsu ya noma gonar gadonsa domin babansa ya dade da rasuwa mahaifiyarsa ce kawai sai ‘yan uwa jibgi guda mata da maxa. Tun mahaifiyarsa na kin amsa gaisuwarsa har dai ta huce ta fara amsawa, ta huce amma koda wasa baya marmarin kai ni garin, nima bana marmarin xuwa garinmu. Shima tasi’u bai sake waiwayar onisha ba sai dai labari ya kai kunnen ‘yan uwana cewar ina tare da tasi’u a kano. Da sun yi shawarar su xo su tafi da ni, sai bokansu yace a kyale ni xan dawo da kaina, akwai tsibbun da xai yi xan dawo da kaina. Amma fa karya yake domin addu’ata tafi tasu karfi.
Na dade ban samu haihuwa ba don haka na dinga kokarin neman ilimi ta dukka bangarorin biyu Qur’ani da boko.”
Kaltum ta tambaya cike da mamaki tace “ta yaya kika shiga makarantar boko alhali kina matar aure kuma ko primary baki yi ba?
To, mu hadu a #LITTAFI kashi na biyu, domin jin cigaban labari.
Taku me son ku da kuma son nishadantar da ku har kullum .
Sadin Maa...
Kunji ta pa?
Wai mai son ku? 😏
To ai nima dan Aunty dan aikenta ina son ku duka baki daya.
Allah Ya sa mu dace.
Aamiin
.
Yawwa AlhamduLillah, gida ya parpado daga parin da ya shiga, mutane sun para dawowa,
Ada ana samun masu karatu bayan anyi post sama da 4k xuwa 6k, akwai post din da naga masu karatu sama da 10k, sai yanzu kuma da gidan yayi shiru dakyar ake samun 1k, daga 700 xuwa 800 ake tsayuwa,
To AlhamduLillah mutane sun bada hadin kai wajen comments, likes da share har yau naga mutane sama da 3k sun karanta littapin, Allah Ya saka muku da alkhairi.
Aamiin.
Naji dadi matukar gaske, ha ila yau muna mai kara janyo hankalin wanda basa yi a taimaka ana yi ko da like da share ne idan baka so agan ka, amma mun pi son comments din da share, ta haka ne xai kara jawo hankalin mutane su kara shigowa gidan.
.
Sadin Maa Allah Ya saka miki da alkhairi da wannan na mijin kokarin da kike magana,
Aamiin.
.
Yawwa, xamu tapi hutun kwana biyu kamar yadda wani ya sanar dani wai an gaji da karatu.
koya kuka ce?
😊 😊
.
Abbas Abdulkadir Hada Hada (Dan Aunty)ADON DAWA LITTAFI NA 2 (P 12)
.
TRUE LIFE STORY
.
Madina t ace “da kyau, na ji dadin tambayarki, wannan yana nuna min kina fahimtar labarin da nake fada miki. Da farko dai ban taba xuwa makaranta ba kamr yadda na fada a baya amma duk yaran gidanmu ‘yan boko ne don haka tun ina karama na koyi A B C D har xuwa xed sannan na iya 123 har xuwa dubunnai, xan iya kirgawa kuma na iya rubutawa. Sannan nasan yadda ake rubuta sunan abubuwa da yawa kamar su hen, cup, ball da dai sauransu. Dalilin da yasa ba xan wahala a boko ba saboda na iya turanci duk da turancin ba turanci ba ne sak (broken English) ne amma muna jin mai kyan din, duk abun da ka fada min da turanci xan ji kuma xan mayar. Don haka satifiket din primary na je aka yi min a dakata special primary school.
A makwabtan mu wato gidan attajirin nan daya bamu aron gida wato general tukur . akwai wata budurwa ‘yarsa mai suna sumayya tukur. Sumayya sa’ata ce shekarunmu goma sha takwas har ta gama secondary, ajinmu daya a islamiyya. General tukur mahaifin sumayya babban soja ne, mai arxiki ne, gawurtaccen dan boko ne, gidansa rayuwar turai ake yi tsantsa. Yana da ilimi matarsa hajiya hafsa cikakkiyar lauya ce har ma tana koyarwa a jami’ar bayero ta kano, don haka su sumayya da kannenta ‘yan gata ne basu san talauci ba balle wahalar rayuwa.
Sumayya tukur itace babba a gidan kuma itace kadai mace, duk kannenta maxa ne har guda hudu. Mai bin ta sunansa tukur tukur ana kiransa da abba shekarunsa goma sha uku a lokacin, kinga kenan sumayya ta girme masa da shekarunsa goma sha daya, sai Hassan da hussain ‘yan auta shekarunsu bakwai bakwai. Tabbas mun shaku da ‘yan gidan duk unguwar ana mamakin ni da mijina kadai muke wadaka a gidan, mu shiga gidan mu fita a duk lokacin da muke so, haka suma yaran suke safa da marwa a gidana koda yaushe. Duk da sojojin da suke gadinsu suna hana kowa shiga gidan amma ni basa hana ni saboda hajiya hafsa tukur ta ce kada su hana ni shiga komai dare. Maigidana ma duk sanda ya bukaci ganin general tukur kai tsaye yake shiga ayi masa iso, ya shiga ya gan shi ya taimaka masa da duk abunda yake nema.
Allah ne gatanmu, general tukur da iyalansa sune gatanmu. Barrister hafsa itace uwar dakina itace tamkar uwata a kano tunda bani da kowa a kano. Ita take ba ni shawara, ita take fada min gaskiya idan na kuskure. Abubuwa da yawa idan ta sayawa ‘yarta sumayya nima sai ta saya da ni musamman dinkunan sutura ko bata yi mana iri daya ba tana kwatantawa nima tayi min. yawanci duk abunda suka dafa xata sa masu aikinta su xuba su kawo min. nima kuma ina iya kokarina wajen xage karfina in tsaftace mata gida ko tana nan ko bata nan xan hau sama bangarenta ko bangaren mijinta in tsaftace shi tsaf,
(TAB!!! NI SADIN MAA ME TYPING NA CE “SAM, BANNA YARDA WATA TA GYARA MIN DAKIN MIJI EHE. DAN ANTY ME POSTING, KO KUWA DA KA YARDA WATA TA GYARA DAKIN KA BAYAN MATAR KA? )
( tab 🤔, ai ni Sadin Maa ko er aikin ma baxan yarda da ita ba, idan kawai naga aikin xai yi wa mata ta yawa sai na karo wata ta biyu ta xo a taimaki juna 😊)
Har bata so masu aikinta suyi mata gayarn daki idan ba niba, bata ganin dai-dai saboda na fi su iyawa. Haka take aikawa in xo in yi mata wankin bandaki ko goge gogen kura, ko dahuwar abinci kala-kala irin na garinmu musamman dakan sakwara.
Daga in da na fara sha’awar boko sai yadda naga ana rugurguxa turanci, ana xaxxankada rubutu a gidan ni ban iya ba sosai. Kullum mummy hafsa t ace min “madina dama ace kin yi boko da kyawunki ya kara futowa, haka da kin fi xama ‘yar gayu da gogewa.” Sai na ji na fara tunanin ta ina xan fara karatun boko dan haka na sauke girman kai na xauna xaman dirshen da biro da littafina, kawata sumayya take koya min idan bata nan kaninta tukur (abba) yake koya min idan na iske mummy hafsa a gida bata je aiki ba itama sai ta koya min, kan ka ce kwabo na fara gane me nene boko, ko ina gida na abba yana shigowa ya koya min ni kuma ina nacewa ina tilawa har cikin dare. Tasi’u mijina baya hana ni duk abunda nake so shima dai bai yi boko ba amma bashi da niyyar koya kuma bai hana ni inje in koya ba. To kin ji yadda na koyi boko daga wajen makwabtana don karfin hali ma harda biology da chemistry sumayya take koya min da yake science tayi.
Ina da shekaru goma sha tara a duniya na haifi dana na fari, aka saka masa suna Abdul malik, na yaye shi kenan na haifi kaninsa Abdul hakim. ‘ya’yana biyu kenan tamkar ‘yan tagwaye kamarsu daya sak. Farare sol da ni suka yi kama basu dauko kamannin mahaifinsu ba. Sumayya kuwa karatun likita take yi a B U K yayin da kaninta abba ya kusa kammala secondary, shima dai ya dage yaketa koya min karatu, ni dole sai na koyi boko nima. Yana matukar burge su, su duka har daddy su ya fada ya sake maimatawa cewa shi kuwa in har xan dage in koyi karatu in nemo makaranta duk tsadar ta xai biya min. sumayya da abba kaninta suka shiga tunanin ta in da xan fara karatu a makaranta.”
Da muka nemi shawarar mummy hafsa wacce makaranta ya kamata in shiga , gani harda ‘ya’ya, sai t ace tunda ina da kokari har ma na fi wata wacce ta gama secondary sanin karatu, to inje in yi register a wata private school wacce ake yin lesson a duk lokacin da jarabawar WAEC ta karato wacce ake koyar da darussan da akayi a SS3, ana amsa past question papers na WAEC.daddy ya biya min nayi register WAEC sannan nake ta xuwa daukar darasi har na tsawon watanni uku kafin ranar jarabawar.
Na xana jarabawar WAEC na sami credit shida aka bani certificate da testimonial, kamar yadda na fada miki daman na sami certificate da testimonial na primary school tutuni.
Kaltum tayi dariya t ace “’rabo ne wannan, ba kiyi boko ba amma kin xama ‘yar boko dole.”
Madina t ace “sa kai ance ya fi bauta ciwo in ji masu iya Magana. Naci ne da son karatun na saka a xuciyata sai kuma kwarin gwiwa da na samu daga masu koya min, musamman abba yana mutukar karfafa min gwiwa.
Haka xa kiji yana cewa sister madina xa ki iya karatu ki dage.
To ko jikina yayi sanyi na daina koyo sai yasa in dauko littafi in ci gaba. Da yake abba yana matukar jin turanci ya taimaka min wajen gane abunda yake koya min, haka irin tsadaddiyar makarantar da suke yi mai kayu ita ta kara musu sanin abubuwa da yawa suma suka koya min, ga lesson teachers dinsu ko wane subject suna da malaminsa.
A bamgaren addini kuwa idan ban koya musu ba, su ba xasu koya min ba, islamiyyarmu daya dasu haka malamin da yake koya musu a gida nima ina shiga ya koya min , bikin saukar mu tare aka yi mana da muka sauke Qur’ani mu uku, ni sumayya da abba babu abunda suka bambata ni.
Abu kamar wasa sakamakon jarabawar WAEC dina ta fito, ina da credit shida da pass uku haka ya taimaka min na shiga school of hygine inda na karanci aikin jinya. To kinji yadda na xama ma’aikaciyar asitbiti kenan shi yasa na iya dinke miki ciwo, na iya allura da bada magunguna.
Kaltum tace “na ji duk wannan sai dai na damu in ji dalilin da yasa ki ka rabu da mijinki da ‘ya’yanki ki ka taho nan alhalin kina cikin rayuwar jin dadi da kwanciyar hankali. Mijinki mai sonki, ‘ya’yanki a hannunki kina kula dasu ga makwabtanki masu son ki suna taimakonki. Ba dai mai gidanki ba ne ya rasu, ‘yan uwansa suka debe ‘ya’yanku suka kore ki?
Madina tayi murmushi sai ga hawaye yana ta sirnanowa daga idanuwanta. Hankalin kaltum ya tashi ta shiga yiwa madina tambayoyi “me yasa kike kuka?
Ma ya faru da tasi’u? ”
Madina ta rushe da kuka tana Magana cikin kuka mai tsanani t ace “kaltum, dole ne inyi kuka dole ne in ji ciwon abunda ya faru da ni har bakin cikin abun ya fito dani xuwa nan.
Kaltum ta tambaya “anty me nene ya far? ”
Madina ta sharce hawaye da gefen hijabinta t ace “na kammala school of hygien nakarbi certificate dina yayi kyau cinye dukka. Haka sumayya ta xama cikakkiyar likita ta auri abokin karatunta shima likita dan gidan shahararren masu kudi ne sunansa dr basher, gidansu na korau road. Kaninta abba kuma ya yi nisa da karatunsa na lauyer a BUK har yaje law school .
Ni kuma har na sake haihuwa na haifi ‘ya mace mai suna shahida, yarinyar nan duk ta fi mu kyau duk da itama ta yi jawur da ita mai hanci dadan karamin baki, mahaifinta ya fi sonta haka su sumayya da mahaifiyarta suke son shahida, musamman abba ko da yaushe yana yi mata siyayya ya dauketa a mota ya xaxxagaya da ita. Alhamdulilla duk da tasi’u bai yarda inyi aiki ba amma na yi karatun na ajiye kwalin shi kuma harkar kasuwancinsa ta bunkasa dan saida ya sayi gidan da muke ciki na genersl tukur, duk da yayi masa rangwame sosai amma ya biya fiye da rabin kudin gidan na xahiri, har ma ya kara da wani fili da yake bayanmu ya hade yakere mana gidnmu ba laifi dai irin na rufin asiri ga ‘yar motarmu a gareji. ‘ya’yana suna karatu a makaranta me kyau don haka hankalina a kwance in ci mai kyau ga sababbin kayan daki dana falo duk tasi’u ya canxa min, sutura sai dai in bawa talakawa jace.
Sumayya na taimaka min da kayan sawa kal-kala haka ma duk sanda na je ko ta xo tana ba ni, haka abba kaninta aminina ne sosai, duk wata damuwata ko ta yarana idan na fada masa xai yi min komai yawan kudin. da yake mahaifinsu yana wadata su da kudi mai yawa. Ni da ‘yayana shar damu, bana tunanin wani abu wanda xai batamin raina in ba tunanin dan uwana ba innamani, sai takaicin rashin sanin addinin musulunci da iyaye na suka mutu cikin rashin sani da jahilci bana marmarin daidai da rana daya in leka garinmu. Amma dangin mijina sun huce dani suna xuwa nima ina xuwa sai daga baya ne ma surukata ta rasu.
Abu na farko da tasi’u ya fara shine bayan ya wadata mu ni da ‘yayana sai ya tarki Karin aure don daman na lura da yanayin gini da yayi (MAXA……….) na xaman mata biyu ne ban yi masa Magana ba sai na xuba masa ido har sanda ya gama xagayensa ya sanar min xai kara aure. Dole ne in jiba dadi amma ban isa in nuna masa ba saboda tsoronsa da nake ji, ban isa yana fada ina fada ba sai dai nayi kukan xuci sannan nayi kukana a daki na lallashi kaina saboda ban ga inda na ragi tasi’u ba da har xai yi sha’awar kara aure, nayi addu’a Allah Yasa ya auro min ta gari wacce xamu xauna lafiya.
Allah cikin ikon Sa aka auro min kishiya mai suna sa’ada ‘yar cikin garin kano ce sai dai kash bata kaunata bata kaunar ‘ya’yana, bata so a xauna lafiya. Duk da bana kula ta muyi fada amma duk shiru na sai tayi abunda sai na yi Magana. Tasi’u har mamaki yake bani, bamu taba fada da sa’ada ba tasi’u yabi bayana koda yaushe nice marar gaskiya itace mai gaskiya kullum ina ta hakuri ko sumayya bana fadawa haka ban taba fadawa mahaifiyar sumayya ba halin da nake ciki ba sai dai sun kula ina ta rama, walwalata ta ragu kamar ina cikin damuwa, ko sun tambaye ni sai in ce babu komai.
Abu yayi taci gaba kullum wulakanci karuwa yake, tasi’u da matarsa suna yi min abunda suka ga dama bana iya ramawa harta kai ta kawo tasi’u ya fadawa sa’ada asalina da yadda muka hadu. Sai na ji yarinya kullum tana yasar min da habaici tana cewa da ba’asan asalin balbela ba da sai tace madina ne sunanta na asali kuma madina ne garinsu.
Na san madina sunana ne amma kuma madina garin ne baxan kulata ba sai taga kamar dai ita kadai take rawarta take kidanta bani da lokacinta don haka ta tare ni kiri-kiri ta goranta min cewar ni arniya ce inyamura, shegiya ce marar uba, na biyo saurayi kano na musulunta. Ko a mafarki yadda nake da tasi’u ban xaci xai kwance min xani a kasuwa ba komin dadin xama komin duk dadin xance da amaryarsa ba, amsa daya na bata shine nace “nagode Allah da har na gane na dawo hanyar gaskiya na musulunta har na xo nafi ta ilimin sanin Ubangiji ita da take takama asalinta musulma ce, n ace tayi asara tunda aka haife ta a musulma ta girma a musulma amma bata iya karatun sallah ba har yanxu, kuma kar kice nayi mata sharri da gaske nake, jahila ce bata iya ba din.”
Kaltum tayi dariya ta yi tafi hade da shewa harda buga kafa kasa tace, “kin burge ni anty, amma abun da kika fada mata yayi mata ciwo ko? ”
Madina t ace “lallai kuwa abun ya kona mata rai sosai harma ta fini damuwa, ta dauki kuka ta shiga daki ta dauko gyalenta ta fice ta tafi gidnsu kinsan me tace?
Kaltum tace “a’a”.
Madina tace, “gayyar ‘yan uwanta ta dauko min mata da maxa suka iske ni har falo suka xage ni harda yayarta daya da take kokarin dukana aka rirriketa sannan suka fita daga gidan da kyar, suna kira na da arniya.”
Madina ta fashe da kuka ta ci gaba da Magana cikin kuka t ace “sa’ada ta bi ‘yan uwanta suka koma gidan su, tasi’u ya dawo daga kasuwa da rana, na kawo masa abinci ya fara ci sai ya tambaye ni ina sa’ada yaga dakinta a rufe? Na c eta tafi unguwa amma ina tunanin gidansu ta je. Nan da nan ya buga mata waya, sai ta fara fada masa cewar xamansu yakare tunda matarsa take xaginta. Kinsan fasa cin abincin nan yayi, ya mike jiki na rawa ya figi mota sai gidansu, a can ita da iyayenta suka shiryo masa karya da gaskiya, ya dauko matarsa suka shigo gida bai tambayeni me ya faru ba sai duka da saki daya yayi min.
Ya kure ni cikin dare ina kuka, yarana suna kuka, na tafi na barsu. Dana fita ban san inda xani ba don ba inda nake dashi wanda yafi makwabtan mu amma ba xan iya shiga in fada musu duk abunda ya faru ba saboda ban taba fada musu matsalata ba tsakanina da mijina sai xaman lafiya nake nuna musu. Hak basu taba sanin asalina ba duk da dai sun san daga inda na fito da yadda aka musuluntar da ni a unguwar basu san kundin tarihina ba.
Don haka sai na tafi gwammaja gidan wata aminiyata hajiya hadixa na yi mata karya n ace mijina ya tafi da yaran garinsu sai ni kadai a gida kuma gyaran bandaki ake yi min shiyasa na rufe dakina na xo inyi mata kwana biyu, tayi mamakin amma tayi murna.
Mami hafsa kuwa yarana ne suka kai mata labari suna kuka suka shaida mata an saki mamarsu, hankalinta a tashe ta aika akira tasi’u ta tambaye abunda ya hada mu. Ya xauna ya shirya mata karaye da nasa dana matarsa data shirya masa, idan ki ka ji abubuwanda yake cewa a kaina sai ki rantse ban taba yi masa abu daya na kirki ba a iya xamana dashi na shekara da shekaru. Yana gama bayanansa, mommy hafsa t ace “karya kake yiwa madina wannan halaye ba halinta ba ne kuma ko Qur’ani xan dafa baxa tayi haka ba.”
Ta bashi shawarar ya tashi ya nemo ni don idan ya rasa ni ya rasa mace ta gari har abada. Babu inda shi da ita basu jejje nema nab a, inda suke tunanin ina xuwa basu same nib a, sai gani kwatsam da yamma na dawo da kaina saboda na rasa inda xanje ma, sai na yanke shawarar in dawo gidana in ba tasi’u da matarsa hakuri in xauna da yarana. Tasi’u na gani na kafin in ce wani abu yace in shiga dakina ya mayar da ni. Ni da ‘yaya na muka yi ta murna.
Mommy hafsa ta aiko in je tana nemana na je, na iske ta a xaune a falonta sai ta fara jero min tambayoyi akan me tasi’u da matarsa suke min?
Na boye mata nace “babu komai”
Data takura da tambaya sai taga na rushe d a kuka kawai, ta girgixa kai.
Ta ce “madina ke ‘yar aljanna ce ki je ki xauna a gidanki, ki cigaba da hakuri Allah xai jagorance ki.”
Na tashi na tafi gida ba tare dana fada mata komai ba. Haka sumayya ta xo ta dinga tambaya ta abunda ke faruwa sai dai in yi kuka bana iya fada. Abba kaninta ma har falona ya shigo yayi iya kokarinsa wajen bugun cikina don ya ji halin da nake ciki a matsayinsa na lawyer ya bi duk wata hanya da dabaru na jin labari shima daya takura min sai nayi ta kuka ba shiri ya fice ya kyale ni.
Na dauki tasi’u tamkar rabin jikina na nunawa jama’a tasi’u shine rayuwata ina jin kunyar ace ya watsa min kasa a ido, kunya nake ji ace baya sona yanxu wata yake so.”
Madina ta shrce hawaye t ace “sai na shiga taka tsan-tsan don kada in batawa sa’ada rai ta fadawa tasi’u shima ransa y abaci, sai na xama tamkar baiwarta a gidan komai ni nake yi mata musamman data haihu nake kula da yaron ita tana can a nade a dakin miji domin ni bani da kwanxa, akwai lokacinda tasi’u yayi wata biyar bai kirani dakinsa ba balle ya shigo dakina sa’ada ce kadai matarsa a gida. Namiji kenan idan kika kalli sa’ada kika kale ni sai ki rasa dalilinsa na son sa’ada, shi da yake da mace kamata a matsayinki na mace ba namiji ba ma sai kice me xai yi da sa’ada baka kirin, xololuwa mai kama da tabarya ko dan kyawun fuska ma bata dashi amma it ace mace ni kuma bora.”
Madina ta rushe da kuka yayin da kaltum take tayata. Madina ta daga idanuwanta ta dubi sama.
Ta ce “Allah kana ganin halindana shiga ada da wanda na ke ciki yanxu. Kaltum ba xaki gane wasu abubuwa da nake fada miki ba saboda baki yi aure ba, baki san rayuwar aure ba, haka gidanku ba mata biyu ba ne balle kisan ma nene kishi da kishiya.”
Ni da ‘yayana mun xama tamkar bayi, ni ban huta ba suma basu sake a gidan ubansu ba. Kaltum, bari in takaice miki tasi’u saida ya sake sakina akan yarinyar nan sa’ada, shi kuma akan abinci ne. ranar girkinta ya bata naira dubu biyu tayi cefanen rana dana dare. Sai ya tafi kasuwa, ita kuma a ranar xata je gidan suna dan haka ta kwada mana gayan tuwo na jiya da mai da yaji tace abincin ranarmu ne ni da ‘ya’yana ta shirya tayi tafiyar ta. Saboda muna jin yunwa haka muka ci nace suyi hakuri xata xo ta dafa mana da dare. Da ta dawo da daddare sai ta shigo da kwano dauke da alala dauri uku ashe mijinta ta daukowa abincin darensa mu banda mu kuma ko sisi bani dashi balle in siya mana abinci ko in yi cefane in dafa mana mu ci ga uwa-uba ina gudun bacin rai dan haka ko farar shinkafa ban dafa mana ba.
Mijinta ya dawo suka shiga daki suna ci suna hira suna shewa har karfe goma na dare. Abdul malik yana xaune a daki yana min juye juyen ulcer sa na kokarin tashi saboda yunwa haka shahida ma kukan yunwa take yi. Na tashi na nufi dakin tasi’u, bayan na yi musu sallama suka bani ixinin shiga, na shiga sannan na durkusa na gaishe shi. Na ce dan Allah ya bani naira dari daya in siyawa yara biredi yunwa muke ji. Ya tambaye ni cike da mamaki y ace ba’ayi abinci bane?
Na ce ai gidan suna sa’ada ta je shiyasa bata yi girki ba.
Sai sa’ada ta hau fada da gatsine gatsine tana min rashin kunya wai ina yawan hada mata gulma, dan haka in fita daga idonta ta rufe. Ya ce in tashi inje dakina yana xuwa yanxu. Na tashi na fice xuciyata na tsananin kuna da radadin bacin rai, sai naji jiri ya dauke ni ina kokarin faduwa a kofar dakin nan da nan na sulale na xauna saboda na san idan na ci gaba da tafiya faduwa xanyi hawan jinni ne dani ya hadu da yunwa. Sai na ji yana ce mata “karki damu kishi ne yake damun madina saboda taga na fi son ki shiyasa take so ta hada mu, kin san rabon da wani abu ya hada ni da ita an doshi wata takwas bana ma kusantar ta.” Sa’ada tayi shewa ta tafa hannu tayi girgixa taji dadi.
Sai na tuno soyayyarmu da tasi’u a da, na tuna yadda na xama haka a wajensa sai na rushe da kuka in tashi ma tsaye ya gagare ni saboda jikina ya mutu. Sai gasu sun fito sai suka yi cikibis da ni a bakin kofa, ya dube ni a sheleke.
Ya ce “kukan me kike yi?
Bana son munafunci ba ni n ace ki je dakinki ki jira niba meye abin xama a nan? ”
Na share hwaye n ace “tasi’u me nayi maka a duniya ka tsanani?
Me nake yi maka yanxu wanda a da bana yi maka yanxu, dan in sani in daina. Tasi’u yanxu baka tausayina ashe, baka nadamar abinda kake yi min ashe?
Na ji kana fada mata baka sona shi yasa baka kula ni ya dace ka fadawa kishiyata haka alhalin ina yi mata boye-boye bana bari ta fahimci halin da nake ciki. Ka daina yi min haka tasi’u nima matarka ce, ni mai sonka ce, har abada ba xan fasa sonka ba kome xaka yi min. tasi’u na yafe maka, tsakani na da kai sai addu’a ta alkhairi domin bana so Allah Y tashe ka da shanyayyen bari jiki ranar gobe kiyama saboda rashin adalci a tsakanin matanka don ana xalunta ta.”
Da alama jikinsa yayi sanyi da farko, saida sa’ada ta kama shi da fada ta inda ta shiga bata nan take fita ba, t ace wai ya tsaya yana kallona bayan labe nake yi musu kullum daman ta sha ganina ina yi musu labe ina jiyo duk abunda suke fada. Tasi’u ya kama ni da fada akan me yasa nake yi musu lae?
Na ce ba labe nake yi musu ba, jiri ne ya dauke ni na ji xan fadi sai na xauna a kofar daki. Sai ya shiga daki y rubuto min takardar saki daya, kinga ya xama saki biyu kenan yayi min.
Na karbi takardar na dauki gyalena na fita ban yiwa ‘ya’yana bayani ba. Ina fita nahau acaba na tafi korau road gidan sumayya kawata na iske tana call a asibiti sai mai gidanta dr basher da yaransu biyu mami da Khalid sunan mommy hafsa da daddy tukur ne aka saka musu, sai a wajensa na karbi kudi na biya dan acaban daya kawo ni. Na ce masa bani da lafiya ne na xo ta duba ni, ina tunanin jinina ne yahau. Ya dauko abun auna jinni ya auna, yana auna ni kuwa sai ya girgice ya kwashe ni a motarsa ya kai ni asibitin su, da yake sun bude asibiti nasu na kansu shi da matarsa a lamido cresent.
Allah sarki madina ko me ya sameta oho.
Se a biyo mu dan jin yadda data kasance.
.
Maza wasu da sanin su wasu ba da sanin su ba, abun da mata yasa suka tsani kishia kenan, inda maza zasu na adalci tsakanin matan su da mata sun so kishia sun dauke ta abokiyar xama, shi yasa ni dan aunty bana ganin laipin mata akan rashin son kishia, kuma duk wata matsalar dake kai kawo cikin gida tsakanin mata na miji shine ummul kaba'isin sa, dan duk na mijin da bai budewa mace kopar iskanci ba a cikin gida bata isa tayi ba, idan ta para ya dakatar da ita ya nuna mata duk matan sane su ai baza ta sake ba, amma akwai wanda ake musu pin karpi da asiri basu san su nayi ba.
Nuna banbanci tsakanin su shine babban abun dake haipar da rashin zaman lapia.
.
Allah Ya tsare mu da mata marassa imani, Ya azurta mu da salihai na gari, kuma matan Allah Ya albarkace ku da maza je na gari Ya kare ku da muguwar kishia Ya hada ku da ta gari.
Aamiin Yaa Rabb 🙏
.
Typing : Sadin Maa
Posting : Dan Aunty.ADON DAWA2 (P 13)
.
Sumayya tukur ta bani gado na kwanta ta ci gaba da kula da ni, ta fara shawarar neman number tasi ‘u a waya xata shaida masa halin da nake ciki sai na hana ta, nace ko mami hafsa bata san na xo ba kuma bana so ta sani. Na dauko takardar saki na nuna mata, ta yi matukar raxana hadi da gigita tayi ta salati sannan ta ci gaba da bani hakuri tana gargadina da cire son tasi’ u raina kada ya kashe ni a banxa.
Saida na shafe kwanaki biyar a asibiti, sai da suka tabbatar nayi ras sannan muka koma gidanta na xauna bana sakewa a giban ina ganin kamar ina takura musu gobia- gobia da ni na wuce xaman gaban wasu. Sai na yanke shawarar in koma gidana in xauna tunda ban san kowa ba sai Tasi’ u. sumayya ta hana ni ta ce sai dai ta kira mami Hafsa a sanar mata halin da nake ciki sai ta xo ta dauke ni ta mayar da ni maimakon ace da kaina na koma don yin haka xai sake kawo raini da gore-gore a wajen kishiya .
Haka aka yi, mami hafsa da kanta ta dauko ni daga gidan sumayya ta shiga da ni har falon tasi’ u muka iske shi a xaune shi da matarsa. Ta yi masa fada sosai hade da gargadi da wa ‘axi mai ratsa jiki akan ya ji tsoron Allah saboda idan bai yi wasa ba hakkina xai kai shi wuta
Sai sa’da ta hau botsare-botsare tana kokarin yiwa mami hafsa fitsara wai an kori mutum ba xuciya dan naci an dawo da ita. To ita baxa ta xauna da niba in har xan dawo in xauna in ci gaba da xama a gidan ni kadai ita xata wuce, a take ta dauki gyalenta ta fice tabar ‘ya’yanta guda biyu kanana, wannan lokacin tasi’u bai bi bayanta ba washe gari ya aika mata da takardar ta ya sake ta saki daya. Ai kuwa wannan saki ya girgixa ta, yayi musu ciwo ita da danginta gaba daya.
Sa’ada ta shiga damuwa dan bata taba xaton xai iya ya mata haka ba saboda yadda taga yana tattalinta kamar gwal. Tana takama da asiri, asirinta ba xai bari a saketa ba, dan abinda ta dogara dashi kenan.
Kaltum t ace “wannan rayuwa akwai wahala sai ki kayi xamanki ke kadai a gidan, hankalinki a kwance ko? ”
Madina tace “na sami sauki dai kadan saboda tasi’u kwata –kwata ya canxa, hankalinsa baya wajena baya raga min, baya sona, ya xama mutum mai mako ko abincin wadatacce baya bamu ni da ‘ya’yana ga kananan ‘ya’yan sa’ada da nake rikewa. Daga nan ma ya sake sabon aure, ni din ce dai ba xa xauna da ni kadai ba.
Ya auro wata baxawara ta girme ni tama gama haife haifenta a wasu gidajen bama a gida daya ba. Sunanta hajiya talatuwa, ita ma jahila ce ba arabi ba boko, gata katuwar gaske ce xama da kyar tashi da kyar, fuskarta a cike da tsage suffer mata ‘yan duniya dai, itama dai na rasa gane mai ya gani a jikinta, har gara sa’ada da yarinta a jikinta.
Itama ta shigo da nata salon iskancin, shima bai isa ba balle ni da ‘ya’yana a haka muka shekara ana ta tafkawa. Bana kula ta sai dai addu’a ni ke Allah Y daidaita mu amma abu yaci tura. Sai ma wata masifar ya kara lalubowa wai xai dawo da sa’ada gidan don haka yasa na kwashe kujeruna na cusa su a daki daya. Ya toshe ya hade mata da falonsa, su duka suna da daki bibbiyu ni kuwa daya jal amma ban damu ba, ina ta hakuri ina ta addu’a Allah Ya ganar dashi, duka da haka bana nadamar aurensa da na yi saboda idan na tuna daga inda na fito da yadda nake a da, na ci riba dana samu na musulunta kuma ga ‘ya’yana nan hausawa musulmai sun sami ilimin dana boko yadda ya kamata.
Amma duk nacin nan nawa saida dole na fita a sanda yayi min saki uku, tasi’u ya yi min karya wai dukkanmu ukun mu tafi gidajen mu ya gaji da rigima ya miko min takardar saki. Ya ce min suma sauran ya basu takardar saki. Suka hau shirye shiryensu a jaka suka fice ashe dana tafi sun dawo gidan ni din ce dai yake so ya saki shine suka hada baki aka kore ni.
Tun sakin yana bani tsoro har ya daina, saboda nasan Allah Shi ne gatan bawa. Tasi’u bai isa yayi min arxiki ba, bai isa ya yaye min maraici da talauci ba, xuciyata ta kyankyashe tunda yayi min saki biyu ban yi masa komai ba sai na sadakar nasa a raina xai karasa ukun daman. Sannan na ji bana sonsa saboda yana cusguna min na xabi gara in xauna lafiya da in cusa takaicin da namiji a raina ya janyo min ciwo a banxa, ba kula ni xai yi ba hankalinsa na wajen matansa in ji da hawan jinin da na hadu dashi akan sa’ada. Na shirya kayan sawata tsab a jakuna da akwatina, ‘ya’yana suka taya ni diba na shiga gidan general tukur domin sune uwata, su ne ubana bani da inda xanje.
Wannan rana itace ranar farko dana xaunar dasu duka na basu labarina naci sa’a kuwa duk suna gida. Daddy da mami hafsa, sumayya da mjinta sun xo su ma haka abba ya xo gida daga inda yake bautar kasa. Kannensa na gida. Ga ‘ya’yana nan gaba daya su ukun suna tare da ni, na fayyace musu tarihin rayuwata tun daga ranar da aka haifeni har ranar da tasi’u ya sake ni saki uku.
Hankalin dukkanninsu ya tashi matuka babu wanda bai xubar min da hawaye ba musamman ‘yayana sun gigita da suka ji tarihina koda wasa basu taba sani ba. Don su a tunaninsu mami hafsat ‘yan uwana ne na jini saboda yadda suka taso suka ga yadda muke yi dasu.”
Kaltum tace “a lokacin ‘yayanki sun yi wayo kenan har sun san ciwon Magana? !”
madina tace “shekara guda ken an da yin abun ba’a dade ba sosai ba, sun girma mana har sun girme ki yanxu. Abdul malik, shekarunsa goma sha bakwai yana kokarin shiga jami’a, Abdul hakim ne yake dab da kammala secondary shekarunsa goma sha shida, shahida ce take primary ita kuma shekarunta goma a duniya, su dukka sun yi hankali sun san komai.
Daga karshe nayi musu ban kwana nace xan koma garinmu. Su duka suka hana ni, shawara daya suka tsayar shine in yi xamana a gidan general tukur ga dakuna nan birjik in xaba in darje duk inda yayi min, ko in kaura bangaren sumayya tunda tayi aure babu kowa har yanxu. Falo ne kato da daki mai dauke da bandaki, ga dining area, nace bana so in xame musu wahala tunda na girma ba xan ji dadin irin wannan xama ba.xan fi son daddy ya taimaka ya samar min aiki a asibiti in kaura can gara in yi nisa da tasi’u domin bana so mu dinga haduwa dashi ko da matansa idan ina ganinsu fami ne babba a xuciyata don xan dinga tuna abubuwan da suka yi min a rayuwata. Sannan idan ina kusa xasu dinga batawa ‘ya’yana don in ji haushi amma idan bana unguwar koma bana garin xan fi jin dadi da sakewa, hankalina xai fi kwanciya.
Suka gamsu da bayanina, daddy ya bani goyon baya akan bukatuna sai dai yace bai san kowa ba a bangaren health a kano amma a jigawa yana da abokai a bangaren health, nan da nan na amsa masa ina so a jigawar na ma fi son haka, ya karbi takarduna yace in saurare shi. Tsawon watanni biyu cur ina xaman jiran aiki amma tamkar a daure nake Allah-Allah nake in samu aiki in bar unguwar. Kinga kuwa abunda nake gudu saida ya afku, tasi’u ya hana ‘ya’yana xuwa wajena duk san da suka shigo sai an fada masa ya dake su musammam karamar ba xata iya daurewa ba sai ta shigo sai dai ya kashe ta. Haka suma kishiyoyi na ina samun sakonnin bakaken maganganunsu musamman daga sa’ada. Sannan na kan jiyo muryar tasi’u daga dakin da nake shima babban bacin rai ne domin na tsane shi bana son ganinsa.
Aka kira ni interbiew a dutse na ji nayi, abunka da hanya ba’a dade ba aka bani offer an dauke ni aiki sai dai kaxaure suka tura ni. Naji dadi nan da nan na hada kayana daddy yasa direbansa ya kaini kafin in tafi mami hafsa ta dauki lokaci mai tsawo tana yi min nasiha cewar in kama kaina in rike mutuncina idan na samu miji in yi aure in cire son tasi’u a raina, na ci sa’a na samu gida a staff querters din asibitin, daki biyu da tsakar gida ga kicin da ban daki.
Hakika na ji dadin aikina ina xaune da abokan aikina mata da maxa lafiya. Dan albashi na yana isata in ci abinci, in dinka ‘yar sutura har in kunshe in kawowa yarana wani kudin ko su shigo mota idan babansu baya gari su xo su karba. Na ci gaba da kama kai na ina rike addinina yadda ya kamata ina cikin walwala fiye da a gidan tasi’u. labari ya iske kunnen makiyana cewar na samu aiki har na murmure na yi kyau sai haushi ya ishe su, suna hassada dama ban samu ba sun fi so kullum in shiga wahala da wulakanci amma Allah Ya fi su.”
Kaltum tayi dariya tace “na ji dadin labarin nan naki matuka da na ji karshen ki alkhairi ne. Allah Ya dube ki ya rufa miki asiri musamman da kika yi tawakkali kika cire son tasi’u a xuciyar ki. Ta amma me yasa kika bar aikinki kika taho nan bayan aikin yafi tahowa ki? ”
Madina ta yi ‘yar dariyar karfin hali ta cije leben kasa tace “kaltum, kema kin san in har babu matsalar da tafi karfina, ba xan baro aikina in taho ba. Gagarumar matsala ce ta fado min wacce har tafi matsalolin da na hadu dasu a baya. Tsanani yayi tsanani wanda har mami hafsat da daddy tukur da sumayya kawata masoyana wa anda bani da kamar su a duniya suka kini suka kira nida MAYYA. In takaice miki hatta da ‘ya’yana dana Haifa a cikina saida suka ki ni suka guje ni, suka ce ni ba uwarsu b ace. Kaltum tun daga ranar da Abdul malik ya furta min haka, na jawo hannun Abdul hakim ya fisge yace min bana sonki mama, nace to ba ni da amfani a duniya, rayuwata ta xo karshe gara in shiga duniya kawai xai fi ye min sauki.” Sai madina ta rushe da kuka.
Kaltum ta ji hankalinta ya tashi, tuni ta shiga surkukin tunani ta tambaya cikin damuwa “anty, me yasa haka?
Me kika yi musu haka ko asiri aka yi miki kowa ya tsaneki ? ”
Madina ta goge hawayen ta ta yi dan murmushi t ace “ba asiri ba ne kaltum kaddara ce kawai ta hau kaina sai dai in xama me godewa Allah a duk halin da na tsinci kaina. Xaki ji dalili kema idan kika ji dalilinsu baxa ki xarge suba, watakila ma k ice sunyi daidai da suka yi min haka amma nima ba laifina ba ne an yanke min hukunci bisa rashin sani.”
Madina na rufe bakinta sai ga baba tsoho mai sayar da ruwa ya dawo akan jakunansa, ya ja ya tasaya a gabansu kaltum, daya dubeta sai yayi dariya.
Cikin harshen larabci yace “’yar baiwa dawowa nayi in cika alkawarin dana dauka , dana ce idan na sayar xan siyo miki gurasa da xuma gashi na kawo miki. Na sayar da ruwan dukka har xan koma in karo wani.”
Kaltum ta tashi da murna taje ta durkusa ta karba tana godiya ya wuce ya tafi. Ta xo ta ajiye a gaban madina tana mai fassara mata abunda suka fada cikin harshen larabci.
Madina tayiwa tsohon nan addu’a suna ci suna yabonsa har suka cika tunbinsu, saboda gurasar mai yawa ce, badan suna jin yunwa ba da ba xasu iya cinyewa duka ba, suka kora da ruwa.
Madina tace “muje muyi sallah na lura axahar tayi sai mu dawo mu ci gaba da labari . Kaltum, labarina akwai abin al’ajabi nan gaba, ai ba ki ji komai bama a baya.”
Kaltum t ace “tabbas na shiga wani hali na xumudin son in ji wannan labarin, kaina gaba daya ya daure tamkar an yi min dabaibayi.”
Suka shiga gida da ruwansu don suyi alwala suyi sallah, saida suka idar da sallah sukayi nafiloli da addu’o’insu sanna suka dawo wajensu na da wato kofar gida suka xauna yayin da wata iska mai dadi take kada su baya ga tumbinsu daya dau lodi, don haka mai sauraro, da mai bayar da labari suka sami nutsuwa labarin ya fara tafiya yadda ya kamata.
Kaltum ta dubi madina ta fada cikin kaguwa tace “anty ci gaba ina sauraron ki.”
Madina ta nisa tace “watanni shida da fara aiki a asibitin kaxaure yayin da shekarata talatin da uku a duniya. Tukur tukur wato Abba kanin kawata Dr sumayya tukur, ya kawo min xiyara har kaxaure wajen aikina da misalin karfe tara na safiyar wata littinin. Yaro matashi a tseleliyar motar da mahaifinsa ya saya masa a satin saboda farin cikin kammala bautar kasarsa da yayi ya xama cikakken lauyer.
Banyi mamaki ba da naga Abba a kaxaure a daidai wannan lokacin, kuma ban yi mamakin ganin tsaleliyar motar nan tasa ba saboda nasan mahaifinsa xai iya bashi wacce ta fita ma saboda general tukur mutum ne mai son ‘ya’yansa da yawa. Sai na dauka Abba ya xo don ya nuna min sabuwar motarsa ne, ban yi mamaki ba idan haka ne saboda Abba mutumi na ne sosai, abokin labarina ne a yi wasa ayi dariya ayi shewa saboda ni mai yawan Magana ce da xolaya.
Abokan aikina har guda biyu suka shigo office dina suna shaida min cewar nayi bako a waje yace daga kano yake sunan sa Abba tukur, sai nace su ce masa ya shigo amma Abban na tsaye a bakin baranda bai shigo ba. Na aika masinjanmu har sau biyu yace masa ya shigo amma Abba bai shigo ciki ba, ni kuma ina ta faman aiki ina shigar da sunayen da sakamakon wadanda muka yiwa gwajin hawan jinni da ciwon suga cikin wani file. Kafin su xo su karbi sakamakon su. Dole tasa na ajiye biron na fito da kaina, ina ta murnar ganinsa ina ta hayaniya ni kadai. Haja ina ta shafa mota ina doguwar addu’a ni kadai Abba na tsaye kikam bai ce da ni komai ba.
Ya xura hannu a aljihun wandon yayin da yayi shar a cikin suit dinsa baka da farar shirt a ciki mai dogon hannu, wuyansa makale da nektie, sai wani bakin takalmi kafa ciki sai sheki ya keyi. Abba ya yi kiba, ya murmure yayin da kalar fatarsa mai hasken duhu (chocolate colour) ta sake haskakawa, dogon hancinsa da habarsa wato (quarter million) sai abun salla baki a goshinsa ya dinga walkiya babu musu kana ganinsa ko ba’a fada maka ba kaga cikakken lauyer ko likita.
Na dube shi tsab sai na kwashe da dariya nace “barrister Abba, nutsuwa ceta xo maka ne, saboda an girma aka daina Magana sai sunkuyar da kai kasa?
Ni yayarka ce fa na san tsarkin kashinka, ni kuma xaka jawa aji?
Wuce cikin office ka taya ni aiki, idan na gama sai mu je gidana ka ci wani abu.”
Na wuce gaba Abba yana biye da ni har cikin office dinmu. Mu biyu ne a offishin kowacce da kujerarta sai na ci sa’a a ranar dayar bata xo aiki ba sai ni kadai. Na jawo masa daya kujerar kusa da ni nace ya xauna, ya xauna a hankali. Idan Abba ya dube ni sau daya sai ya sunkuyar da kai kasa da sauri wanda ada baya yi min haka. Ya gaishe ni cikin siririyar murya mai tafe da tsantsar ladabi da biyayya. Na amsa masa a sanyaye, sai na gyara xama a hankali ina fuskantarsa na dube shi na tambaya cikin fargaba. Na ce “Abba lafiya?
Waye bashi da lafiya ko kuma waye ya rasu, ‘yayana ne ko? ”
ya girgixa kai yace “babu wanda ya rasu kowa lafiyarsa kalau.” Na xungure shi na yi dariyar farin ciki nace “shegantakar banxa, wai meye haka ko yunwa kake ji in je in sayo maka abinci? ”
ya sake girgixa kai a sanyaye alama baya ci.
Na ce “to yanxu xaka warware dole idan na saka ka aiki, karbi biron nan ka fara shigar min da sunayen nan cikin file din nan.” Abun mamaki sai ya karbi biron hannunsa ya hau karkarwa ya kasa rubutun, ina daga nesa na jiyo bugun xuciyar sa ke yi saboda tashin hankalin da yake ciki. Na mike tsaye da sauri na fashe da kuka na tambaye shi cikin kakkausar murya Abba, ka fada min abunda yake faruwa kafin xuciyata ta buga, kasan ina da ciwon xuciya da hawan jini idan ba so kake na mutu ba, ka fada min abunda yake faruwa. Ni musulma ce Abba na san kaddar na yarda da ita kuma ‘ya’yana ne suka mutu ko?
Ko kuwa mami ce ko daddy? ”
Shima sai ya fara hawaye yace wallahi babu wanda ya rasu, xauna in fada miki abunda yake tafe da ni.”
Na xauna da sauri jikina na rawa na xura masa ido hawayena yaki ya tsaya, amma sai naga yahau kame kame, yayin da yana Magana numfashinsa ya na kokarin tafiya gaba daya saboda fargaba. Bana jin abunda yake fadi, sai na tabbatar Abba bashi da lafiya yau har maganarsa na hardewa baya ga bugun da kirjinsa ke yi tamkar xuciyar sa xata fito sarari in ganta. Na dora hannuna a kirjinsa na dafe yayin dana dafa kansa na fara tambayarsa ina ne yake masa ciwo?
Sai na ji ya ja dogon numfashi yayi ajiyar xuciya da karfi tamkar ransa xai fice. Na figa da gudu xanje in kira likita, sai naji ya jawo hannuna ya dakatar da ni yace “lafiyata kalau sister madina, dawo ki xauna xa muyi wata magan.”
Na dauka abin gwada jini na auna dantsensa, hakika jininsa yahau kadan. Na ce “Abba me yake damunka kai kuwa a duniya da har ka hadu da hawan jin kana karamin ka?
Abba me kake nema ka rasa a duniya daya wanda ya dameka a xuciyar ka?
Kada ka kashe kanka a banxa ka tashi iyayenka tsaye bayan iyayenka gaba daya burinsu da tanadin su akan ka, ka gama karatunaka kai na miji ne babban namiji, ka dube ni mana ka dubi irin matsananciyar rayuwar da nake ciki amma na yi hakuri da tawakkali.”
Sai ya sirnano da hawaye yace “ai kuwa sun kusa su rasa ni, shine ma abunda na xo in bayyana miki. Sister madina, ajalina ya xo tabbas na kusa mutuwa.”
Sai na fashe da kuka na dauki dogon salati, shima kukan yake. Na ce “Abba me nene matasalarka inyi maka maganinta in har xan iya? ”
Ya girgixa kai ya yi murmushi yace “ba xaki iya ba sister madina, abu daya nasan xaki iya taya ni dashi shine addu’a, itama sai bayan na mutu xaki tabbatar abun nan da nake fada miki bada wasa nake yi ba. Ba ni ne na jawowa kaina ciwon da gangan ba, sister madina na dade da kamuwa da ciwon nan a kalla xai yi wata shida ina fama da abu daya ni kadai amma daidai da rana daya ban taba samun sassauci ba sai dai ma karuwa da ciwon yake yi. Na rasa yadda xan yi har na tsani kaina da kaina kafin jama’ar gari su ji su tsane ni suma.” Sai kuka ya ci karfinsa, ya rushe da kuka me tsanani..
Ni kuka, shi kuka. Na tambaya cikin kuka “kai kuwa Abba wannan wane irin ciwo ne?
me yayi xafi haka ka fada mini ko mene ne irin ciwon ne, na yi alkawarin xanyi iyaka kokarina wajen taimaka maka, xan yarda da abunda xaka fada min ko da ace duniya gaba daya xasu karyata ka. Me yake damunka kanina ka fada min, Abba ciwon kanjamau ka dauko? ”
Sai yayi murmushi yace “kanin ki? Anya kuwa yau xaki bi bayan kanin nan naki kuwa, alhali ya bi baudaddiyar gada mai Burma wa?
Ke ceta farko da xaki fara karyata kaninnan naki a yau koda ace duniya gaba daya xasu gaskata shi. Ciwon kanjamau sassaukan ciwo ne tunda yana da maganin da xa’a sha a xauna lafiya a ci gaba da rayuwa cikin kwnciyar hankali.”
Sai na fara tsorota da jin irin wannan sababbin lafaxai daga bakin dan uwana Abba. Na koma jikin kujera na jingina na langwabe kai ina dubansa, na ji alamar jini na ya fara hawa.
Ya ga alamar na damu sosai sai ya shiga lallashina yana bani hakuri. Na fada cikin sanyayyar murya nace “Abba bana bukatar hakurinka, laifin me kayi min da xa ka bani hakuri?
Sai dai ina mamakin wannan al’amari naka, idan wasa ne ka daina. Wannan watan September ne ba april ba balle kayi min April full na kasa gane manufarka. Ka xo ne kawai don ka tayar min da hankali tunda baka tausayi na yanxu, bayan kasan tashin hankalin da nake ciki na rabu da mijina, na rabu da ‘’ya’’yana, ba ni da kowa sai Allah , sai kuma ku da iyayenku.” Na fashe da kuka.
Ya girgixa kai yace “ba April full ba ne ba, ba ma irin wannan wasan dake sistr madina. Ki gafarce ni akan abunda nake shirin fada miki domin nasan ba xai yi miki dadi ba ko kadan.”
Sai na ji xuciyata ta sake harbawa na shiga tunanin abunda xai fito daga bakinsa marar dadi da yadda kunnuwana xasu xukowa kwakwalwata. ‘ficik’ na jiyo wata kakkausar mummunar kalamai sun fito daga bakinsa xuwa kunnuwata yayin da xuciyata ta harxuka, kaina ya sara, kan kace kwabo gumi ya keto min, tsigar jikina ya mike tamkar an kwara min ruwan kankara a lokacin hunturu, na ji kamar na shake shi ya mutu, nima idan ya so a kashe ni, har na gwammace mutuwata da wannan mumunar kalaman daya fada min.
‘wukit’ na bude dara-daran iduwannan nawa na dube shi yayin da nasa dara-daran idanuwan suka tsugunna kasa da sauri. Na fada cikin fushi n ace “Abba ban jiba, maimaita min abunda ka fada.”
To pa, ko wace irin mummunar kalma Abba ya padi, bamu sani ba, nima se dubawa nake na kasa sanin me ya padi mata....
.
Kai Sadin Maa da iya datse labari kike..
Allah Ya kai mu goben muji me ya sanar da ita...
.
Typing : Sadin Maa.
Posting : Dan Aunty.ADON DAWA 2 ( P 14)
.
TRUE LIFE STORY
.
Me Abba ya padi ne?
Tabbas kunnuwana ba suyi min karya ba Kalaman daxu ce ya maimaita min itace “SISTER MADINA ALLAH YA DORA MIN CUTAR SONKI.”
Na ce “Abba kamar so na ji ta fi fito daga bakinka ixuwa gare ni kunu wata?
Ashe xaka iya duban sumayya ka ce kana sonta so iri na soyayya? ”
Sai ya durkushe a kasa yana neman gafrata, yayinda yake nuna min kuskure yayi ba haka yake so ya fada min ba, kubcewa Kalmar tayi.
Na fuskanci xai raina min hankali don haka na mike a fusace na nuna masa hanyar waje, ma’ana ya tashi ya fita daga office dina. Simi-simi ya mike yana tuntube ya fice, na yi kukan takaici har na gaji a wannan rana. Na ji na tsani Abba har na fi tsanar kai na, ina tunanin Abba yana yi min kallon ‘yar iska don ba ni da miji kuma bani da kudi don haka xai xo ya sauke tashen balagarsa akaina. Na tunano tonan sililin da xa’ayi min idan har maganar na ta fito fili, mutuncina xai xube a idon mutane. A yi min mummunar fahimta da fassara ace yara nake bi kanana sa’annin kanne na ko ‘yayana.
Maganr nan ta dame ni sosai a raina, kwana biyu bana xuwa office ina gida ina xulumi ni kadai babu wacce xan iya fadawa. Abun mamaki sai ga Abba na turo min sakonnin soyayya ta waya, yana bayyana min mummunar halin da yake ciki a sanadiyar rashin amincewata.
Bana bashi amsa sai dai in yi kuka in goge sai takai ta kawo ya daina turo sakonnin saboda bana bashi amsa ya fara kiran lambar. Watarana da daddare misalin karfe goma da rabi ya kira ni, a wannan lokacin ne na fara amsa wayarsa don da rejecting nake yi sai a lokacin na samu daman amayar da duk abundake xuciyata. Na ja masa kunne nace Abba, saboda talauci da rashin gata da rashin asali mai kyau ne har na xama haka a wajen ka?
Ko rashin miji da rashin kudi shine kake tunanin xan xubar da girmana da mutuncina in yi lalata da kai?
Ko dan a gidanku ne ake taimakona shike nan na xama wulakantacciyar baiwa wacce xaka iya daukarta wajen biyan bukatar ka ta banxa? ”
Sai ya rafka salati yayin daya hau rantse-rantse cewar ba haka ba ne. ya shiga yi min bayani wallahi shima ya tsinci kansa ne a cikin wannan hali wanda da farko bai yarda ba sai da abu ya ci tura bayan yayi addu’a da kansa haka yasa abokansa sun taya shi akan Allah Ya yaye masa amma abu sai karuwa yake yi shine ya yanke shawarar bayyana min ko xan taya shi addu’a daman yasan ko da wasa ba xan amince ba.
Na sake jin na tsane shi fiye da da, na shaida masa koda har abada babu wani namiji a doron kasa saishi to wallahi gara in koma ga mahliccina banyi soyayya ba da na yi soyayya dashi. Na fatattake shi na ja masa kunnuwa koda wasa kada ya sake kirana ko ya turo min sako balle ya tako ya xo kaxaure. Nima har abada na daina xuwa gidansu.
Sai na ji ya fashe da kuka yana fadin inna lillahi wa’inna ilaihi raji’un, na murtsuke wayar gaba daya na kashe. Sai da aka yi sati guda sannan na kunna abun mamaki sai ga sakonninsa ba adadi. Hakuri dai yake bani, lallashina yake in saurare shi, wai ya kasa daina sona.
[TAB “SO” BALA’I YA ALLAH KA MANA BAIWAR WANDA XUCIYAR MU TA XABA DA DUKKAN KHAIRI, amen]
(Aamiin thumma Aamiin Sadin Maa)
Wanna al’amari na Abba ya fara tsorata ni sai na shiga tsayuwar dare ina mai neman tsari daga sharrin Abba. Hankalina ya tashi dana ji kiran wayar yayarsa sumayya ta dinga damuna da tambaya wai me yasa bana xuwa week end yanxu sunga na dade ban je ba. Na lura dai bata san abunda yake faruwa ba, haka daga mami hafsa ta kira ni sai kirjina ya harba sai idan naji ba wannan ba ne dalilin kiranta sannan in ji sanyi a xuciyata, ina ta faman yi musu karairaye cewa aiki ne ya yi min yawa amma xan xo.
Wani week end sai ga Abba har cikin gidana ya shigo ya iske ni kadai a xaune atsakar gida, ya yi baki sosai kuma ya rame. Yana shigowa sai ya tsugunna ya gaishe ni, ban amsa ba, sai ya koma gefe ya tsugunna rabe har abin tausayi.
Ban kula shi ba, na tashi na ci gaba da aikace aikace na na tsakar gida, almajiri na ya shigo na mika masa tsintsiya xai yi min shara sai Abba yayi xuruf ya dauki tsintsiyar ya fara shara. Cikin fushi na Harare shi na daka masa tsawa nace ya ajiye min tsintsiyata bana son shararsa, ya ajiye da sauri ya koma gefe ya tsugunna. Almajirin yakare shara sai na dauko kayan miya nace ya gyara min ya kai markade, sai Abba ya taso da sauri yahau tsinke hancin tattasai. Ko kallonsa ban yi ba don na fuskanci takalo abunda xan fara yi masa Magana yake yi. Ya ja alamajiri suka tafi markade a inji.
Takaici ya sana rushe da kuka ni kadai a tsakar gida, na rasa abunda yake yi min dadi suka dawo suka iske ni ina kuka Abba ya xo ya durkusa a gabana yana furta min kalaman sanyaya rai dan hankalina ya kwanta amma sai suka xame min tamkar wuta yake hura min a xuciyata. Na hasala na mike tsaye na dakawa almajiri na tsawa nace ya fice min daga gida, ya fice da gudu saboda yaga yadda raina ya baci kada in kai masa mari duk da yasan bai yi min laifin komai ba. Yayin da na juya na dubi Abba a durkushe a gabana na sake jin haushinsa da tsantsar tsanar sa suka hadu, na fashe da kuka mai tsanani.
Na ce “Abba, idan sha’awa ce ke damunka me xaka yi da tsohuwa er shekaru talatin da uku kana saurayin dan shekara ashirin da takwas?
Me xaka yi da ni wacce na tsufa na gama haife-haifena, wacce ba ni da sauran amfani na wanda har shi kansa mijina yaga bani da amfani ya sake ni, yakore ni, yace baya sona. Me xaka yi da sauran alhali ga sababbin ‘yan mata can a gari wadanda ido rufe irinka suke nema. Na yaye hijabinda yake jikina daga ni sai siket da t-shirt ko eaner wears ban sa ba. Na ce me kake sha’awa a jiki na?
Idan sha’awata ka ke yi mushiga daki in har daga yau xaka rabu da ni in huta.”
Sai Abba ya sa hannu ya rufe idanunsa da sauri yaki dubana, ya girgixa kai ya fada cikin tashin hankali da damuwa y ace “wallahi sister ba wannan ba ne manufata, ban taba sha’awarki ba kuma da xaki yarda ki aure ni ki gindaya min sharadin kada in dangwali hanuna a jikin ki, har karshen rayuwar mu to xan amince, don ni ke nake so kawai.”
Hankalina ya gushe yayin da haushi ya ishe ni, na rufe ido na na yi ta cusa masa ashar babu kakkautawa. Na ce ya tashi ya bar min gida kafin na dauko tabarya in fasa masa kai. Ya tashi sadan sadan ya kama hanyar waje saida ya kai bakin kofa, ya waiwayo ya dube ni yana hawaye yace “madina idan na mutu kece ajalina, nagode da duk abubuwanda kika yi min, ki yafe min, ki yafe min nima ba haka na soba.” Sai ya fice ya bar ni a nan a tsaye kamar gunki.
Bayan sati biyu da faruwar wannan al’amarin a bisa takurawar mami hafsa da sumayya akan na xo week end dan na dade ban je ba, dole tasa na ebo ‘yan kayana kala biyu na taho gidansu Abba. Abba na fara iskewa a falo yana xaune sai gumi yake yi shi kadai duk da AC dake kunne a falo, kallo daya xaka yi masa ka tabbatar yana cikin matsananciyar rayuwa. yana ganina sai ya xabura ya gyara xama sai dai kash ya kasa hada ido da ni, ni nake yi masa duba irin na tsantsanr tsana da jan kunne ma’ana niba sa’arka bace.
Na wuce shi ba tare da na yi masa Magana ba na isa kofar dakin mahaifiyarsa na kwankwasa mata kofa gami da yi mata sallama.
Kasancewar tasan ina tafe nan ta dau muryarta t ace “madina ki shigo mana.” Na shiga muka gaisa, na tambaya duk ‘ya’yanta sai ban tambayi Abba ba, tace “mutuminki ma Abba ya dawo daga bautar kasa. Bai je ya nuna miki motarsa ba? ”
da xata lura da ni a lokacin da xata ga yadda na raxana yayin da a gigice n ace “be je ba.”
Sai ta dan gatsine fuska tace “Abban ma kamar wanda aka yiwa jifa a kudu nan daya je wajen bautar kasa, daya dawo duk ya susuce kamar bashi ba, baya son shiga mutane haka nan baya walwala da kyar sai da lallashi yake dan cin abinci. Sai daddy ya dauko mai aski da gyaran fuska, sai kaga ya tara kasunba yumu-yumu yana muxurai kamar wani bunsuru, kai gaskiya Abba ba lafiya ba. Shiga dakinsa ki ganshi ko ke da yake mutuniyarsa ce xai yi miki bayani.”
Sai na ji gabana ya yanke ya fadi tabbas al’amarin Abba ya fara bani tsoro ya wuce xolaya kamar yadda nake tunani. Kan kace kwabo hankalina ya tashi na shiga xulumi, abu daya nake tsoro kada Abba ya sake ya furta musu damuwarsa, yana furtawa kuwa mutuncin dake tsakaninmu dasu ya rabu har abada saboda ba abu ne mai yuwa ba, a dukka bangarorin biyu ko da’ace su xasu yarda niba xan yarda da yaron da na girma ba koda wanda ma ban sani ba ne, balle Abba yaron da na sani, na san yarintar sa. Baxan iya ba har abada, da in yi soyayya da Abba gara Allah ya dauki raina shi ma na fada masa haka. A haka na share xancen xuwa dakin Abba, na yi saurin xakulo hira kala-kala daga nan ma ‘yayana suka shigo muka hau murnar ganin juna daga karshe suka rako ni har wajen motoci direba ya kaini gidan sumayya.
Ina xuwa gidan sumayya muna hira sai da ta maimaita min abunda mahaifiyarta ta fada min akan Abba cewar ko an jefe shi ne a wajen bautar kasa, saboda ya susuce. Itama tana so na tambaye shi cikin dabara kasancewar sun san mutumi na ne, na amsa mata amma badan xan yi ba. A daddafe na yi kwana biyu a gidan su Abba, na je ranar juma’a da yamma na koma kaxaure ranar lahadi da yamma.
Naga yarana na basu abin da suke bukata, shima Amma mun harhadu a falon gidan musamman da safe idan zamu karya sai dai baya iya yi min Magana nice ke faman washe masa baki ina yi masa wasa a dole saboda a gaban iyayensa ne kada su gane akwai wata ‘yar takaddama a tsakanin mu na sulalo na dawo kaxaure da xummar a wata shida ma ba xan je kano ba, ai dai na yi tunda na je.
Haka kuwa aka yi na dade ban je kano ba sun yi min xancen xuwa week end sai na fake da aiki yayi min yawa. Kusan watanni uku ban ga Abba ba, ban ji kiransa ba a waya sai hankalina ya kwanta na dauka ya hakura da ni. Wata rana da daddare ana tafka ruwan sama kamar da bakin kwarya. Na rufe gidana tun kafin magaruba, ina dakina akan salla na idar da sallar isha’I ina wuridi da addu’o’I kala kala ina fadar bukatuna, saboda Allah Yana amsa addu’a a lokacin da ruwan sama yake sauka. Na ji yo da gaske ana buga min kofa sai jikina ya dau rawa, kwallawa nake yi ina tambaya “waye? ” shiru ba amsa, sake bugun kofar ake yi da karfi na wawuri lema na fito tsakar gida na tsaya, can dai na isa bakin kofa na yi Magana “waye? Waye? ”
shiru sai bugun da ya karu. La’ilaha illa Anta subhanaKa inni kuntu minaxxwalimina” na yi ta karantawa sannan na bude kofar jikina na rawa.
Dogon namiji sanye da shadda taxarce koriya da hula na gani a tsaye yaro-yaro yana digar ruwa ya jike sharaf. Ban gane ko waye ba na tambaya cikin firgici “bawan Allah wa kake nema ne, ko kayi batan kai ne? ”
sai yace “ke nake nema.” Na jima a tsaye ina dubansa saboda duhu ba wuta ban gane ko waye ba ne amma ni xuciyata bata bani mutumin nan xai cuce niba saboda nayi addu’a Allah xai kiyaye ni. Sai na ji ya bani tausayi saboda yana tsaye har yanxu a cikin ruwa, yana dukansa. Na sa Allah daya a raina ko daya xo da niyyar cutar da ni Allah xai kare ni sai na matsa ya shigo xauren. Ban de rufe kofar ba muka iso falo a inda na kunna fitila sai ga Abba duban farko na gane shi sai na ji tamkar an hura min wuta a xuciyata dan haushi.
Na fada a hasale “Abba, baka rabu da niba ko? Sai ya fada cike da tabbaci “ba xan iya rabuwa da ke ba, har sai ranar da na rabu da raina.” Sai a lokacin na tabbatar na hadu da alakakai, na hadu da masifar rayuwa.
Na ce “ni kuwa gara a raba ni da raina da in yi soyayya da kai.” Sai kuma ya rushe da kuka harda dora hannu a kai, yana tambaya ta waishi a duniyar nan me yayi min haka nake yi masa wannan wulakancn?
Wai me yasa na tsane shi alhalin yana so na?
sai naga ya dafe kirji da alama xuciyar sa ke yi masa ciwo, yaro yana kokarin kakkafe min xai fadi ya mutu.
Nan da nan na fara lallashinsa ina cewa ya kwantar da hankalinsa na amince. Wannan Kalmar na fitowa daga bakina sai naga Abba ya lafa, ya koma ya xauna ya mike kafa a tsakiyar falon. Da yake babu kujeru a falon leda ce da labule kawai, ni ma na samu lungu na xauna muka yi jugum kamar a gidan makoki. Idan ya dago ido ya dube ni sai yayi murmushi ya sunkuyar da kai kasa da alama yau farin ciki ya same shi kasan cewar na amsa masa . ni kuwa tuni takaici ya dame ni.
Fiye da awa guda muna xaune a cikin wannan yanayi, sai na dube shi na ce “ruwan sama ya tsaya sai ka tafi gida ko? ” ya juyo ya dube ni yace “a ina xan hau motar kano? ” na fusata na harare shi na ce “da ta ina ka biyo ka xo? ”
sai ya dukar da kai kasa cikin ladabi yace “nagode xan tafi saida safe.” Ya mike ya fara tafiya, ban amsa masa ba na saka shi a gaba muka fita har kofar gida. Na waiwaiga ban ga motar daya xo da ita ba, ashe da gaske bada mota ya xo ba a motar haya ya xo. Ina lekensa ya nufi hanyar get xai tafi tasha ga nisa, gashi garin tsit babu ‘yan Babura, ga tsananin iska da sanyi, ga kayan jikinsa a jike sharkaf. Yana ta rawar dari ya tafi yayin da ni kuma na ji ko a jikina bai dameni ba shiya dorawa kansa wahala, na jawo kofata na rufe na shiga daki na kwanta. Ina ta sake sake a raina, idan na fara saka soyayyata da Abba sai na yi maxa na warware baxan iya soyayya da kanina ba sai dai duk mu rasa rayukan mu ni dashi gaba daya.
Wayata ceta hau kara na xabura na duba Abba ne, sai na yi sauri na katse dan ba xan amsa ba , ya ci gaba da kira, ina ta rejecting. Sai ya turo rubutaccen sako yana shaida min ya isa gida lafiya. Na tabe baki nace “ina ruwana, ni na aike ka.” Yaron nan bai iya barci ba haka har cikin dare bai daina turo sakonni ba, har saida nayi masa reply, sannan ya runtsa. Ka da ki dauka wata Kalmar soyayya na rubuta masa kalma daya na rubuta itace. “ok” sannan ya kyale ni na runtsa.
Kaltum na rike haba ta afka cikin mamaki tace “cafdijam, haka soyayya take daman ko a fim din indiya ban taba ganin irin wannan soyayya ba.”
Madina ta yi dariya tace “so ya wuce haka ma kaltum, ai ke yarinya ce karama baxa ki sani ba sai dai nan gaba. Ke in takaice miki duk wannan halin da Abba ya shiga ban fada miki komai ba ma saboda kwakwalwarki karama ce ba xaki fahimta ba, kadan nake takaice miki, kuma duk wannan rigimar da aka yi ba’ayi komai ba. Bala’I na gaba sai kin tausayawa Abba, ko makiyinsa xai tausaya masa idan ya ga halin da yake ciki.
Hakika daga baya na tabbatar bada gangan yake yi ba da gaske Allah Ya saukar masa da jarabawar sona wacce ta xame masa matsala a dukkanin lamarinsa. Na fuskanci shi kansa baya son nacin da yake yi min yana iya kokarinsa wajen danne son da ture shi amma abu ya ci tura, ko baya so xuciyarsa xata tursasa shi sai yayi min waya idan ban amsa ba sai ya taso ya xo ya ganni. Bayan na amsa gaisuwarsa bana kara kallonsa balle na kara yi masa Magana, a gidana ko a office, da daddare ko da rana ya kara ci xamansa ya karaci xamansa ya kara ci satar kallona in yi kamar bansan yana yiba, daga karshe sai yayi min sallama ya tashi ya tafi idan ya dame ni da waya in amsa in ce masa “menene? ” sai yace ya kira ya gaishe ni ne.in ce “nagode”. In kashe wayata, idan ya fara turo sakon daya danganci soyayya sai na ja masa kunne cewar ya daina niba sa arsa ba.
Sai gashi rannan a gidana shi da wani amininsa mai suna mukaddam. Na san mukaddam sosai abokinsa ne tun suna sakadire suna shigowa gidana, tare ma suka yi jami ‘a shima lauya ne.bayan sungaishe ni sai mukaddam ya kai-kai –ce xai tsara ni cewar abokinsa ya shaida masa komai game da halin da muke ciki, wai in daure in kula shi ba hargetse na daga musu hankali gaba dayansu, na xage su tsaf na kore su daga gidana. Na ce da mukaddam ya fadawa abba kada ya sake nemana ko a waya balle a ido biyu, jikinsu na rawa suka tafi.
Abba yayi ta kuka ya dinga turo sakonnin bada hakuri kala-kala a waya, na ce duk halin da xai shiga ya shiga baxan cuci kaina ba na aikata abunda xai dame niba.
Wata rana da yamma ina cikin garin kaxaure ni da abokan aikina nurses muna bikin wata abokiyar aikin mu. Sai wata kawata da muke xaune tare tace “wayar ki na ringing tun daxu fa.”
Na yi sauri na bude jakata na dauko wayar sai naga 30 missed calls. Sai na ji gabana ya yanke ya fadi na fara dubawa sai naga missed calls din Abba 19 ne 6 kuma na mukaddam abokinsa, 5 kuma wata bakuwar lamba ce. Na fito gefe saboda kidan da ake yi a wajen da kuma hayaniya, ina kokarin kiran lambar da ban sani ba amma ban damu da in kira Abba ba balle mukaddam na san dai abu daya ne, shine su yi min magiyar soyayya ni kuma ba xan yi ba, kuma bana yi. Na kira number na ji number busy ana amfani da layin, ba’a jima ba sai naga lambar tana kara kirana na yi sauri na dauka sai na ji muryar wani inyamuri yana Magana cikin harshen turanci.
Ya ce dani “madina ce? ” na amsa cike da mamaki “eh, madina ce.” Ya ce “to gamu a kofar gidanki, kofarki a rufe.” Na tambaya cike da mamaki “waye kai? Lafiya? ” ya fada cike da damuwa “madam, ki yi sauri ki xo, emergency ne muna tare da marar lafiya ne yana neman taimakon gaggawa.” Na fada cikin mamaki marar lafiya a gidana kuma? Me xan yi masa ni da ba likita ba, kuma ko ni likita ce gidana ya kamata akawo shi ba asibiti ba?
Sai na ji mutumin ya hargitse yana Magana a fusace y ace “ina Magana ne akan mai gidanki daya yi hadari a hanyarsa ta xuwa onisha, gashi nan rai a hannun Allah be san ma a inda yake ba, jini ne ke xuba.”
Na ji gaba daya tunani naya hautsine na rasa me yake fada, kafin in ce wani abu ya kara da cewa “muna nan a kofar gidanki ki xo idan baki xo ba nan da mintina goma sha biyar xamu ajiye miki shi a kasa mu tafi da motar asibiti ce na roka aka kawo mu tun daga onisha dan kawai na ceci ransa ya na gama fada ya kashe waya.”
Kaltum ta dafe kirji t ace inna lillahi wa inna ilaihi ra ji’una, waye wannan marar lafiyar ko dan uwanki ne daga onaca? ”
Madina ta share hawaye t ace “xaki ji ko waye, ki ci gaba da saurarena. Mutumin na kashe wayarsa sai ga lambar mukaddam ta shigo na yi sauri na amsa jikina na rawa. Sai na ji y ace “sister madina wai me yake faruwa ne da Abba? Na ji ana ta kirana da lambar sa idan na dauka sai na ji muryar wasu inyamurai daga karshe ma naji wayar a kasha.”
Na ce “nima ban sani ba, amma ka je gidan su ka duba shi ka gani.”
Sai mukaddam yace “ai Abba baya gida tun da asuba na kaishi tasha yahau doguwar motar xuwa onisha.”
Sai na dora hannu a ka, n ace “inna lillahi wa inna ilaihi raji’una. Mukaddam me Abba xai yi a onisha? ”
Sai y ace “babu yadda ban yi ba kada ya je y ace sai ya je wajen ‘yan uwanki su bashi kwatancen inda xai samu yayanki innamani a enugu, yana ganin idan ya nemo miki yayanki uwa daya uba daya wanda shine kadai dan uwanki wanda rashin sanin inda yake yana damunki to yana ganin xaki dan tausaya masa ki aure shi ki tabbatar da gaske yake sonki da aure. Abba yace kada na fada wa kowa a gidansu baya so ki ji.”
Ai ko rufe bakinsa bai yi bana katse wayar na rusa ihu na yi bakin titi da gudu, saura kiris mota ta kade ni na tsayar da mai babur nahaye da sauri, kawayena da gudu suna kirana tuni mai babur ya figa da ni, ce masa nake kara gudu malam yi sauri bamu tsaya a ko ina ba sai kofar gidana, a inda na hango motar asibiti da marar lafiya a kwance abaya tamkar gawa sai wadansu maxa guda uku. Na karasa gare su ina karkarwa suka bude min bayan motar na leka dakyar na gane Abba daga kafarsa na shaida shi amma babu mai gane fuskarsa saboda ta yi kaca kaca da raunuka. Kunnensa ma an manne shi dan saura kiris ya fadi dan haka fuskar ta kunbure sumtum an nade da bandeji fari, bashi da riga se dan gajeren wando saboda dorin karayar da aka yi masa a hannun hagu da kafar dama kara bibbiyu sai kafadarsa wani katon rauni ne, an like shi da bandeji, sanna duka ilahirin jikinsa babu inda babu rauni jini jage jage, a jikin shinfidarsa farare gasu nan a gefansa a yayyage jawur da jinni tamkar an tsoma su a bokitin jinni a ka tsame su suna ta diga.
Na tsala ihu na gigice ina tambayarsu me ya faru das hi? Ya aka yi haka ta faru, yaya xan yi in kwaci kaina idan Abba ya mutu a dalilina?
Tambayarda na rirrike su nake yi kenan a gigice suka shiga lallashina suna shaida min babu lokacin batawa saboda marar lafiyan nan yana neman taimakon gaggawa a inda suke nuna min suna neman kudin su da suka karkashe wajen kaishi asibiti da xuba mai wajen kawo shi tun daga can har nan. Yayin da gabana ya fadi saboda na san bani da kudi, kudin da ke jakata bai wuce duu biyu ba saboda bikin nan duk na kashe kudaden kakaf.
Na tambayae su cikin kuka me yasa basu kaishi gidan suba suka kawo shinan? Sai suka ce min ai sanda yayi hatsarin yana Magana shine ya fadi sunanki yace matarsa ce, yana so mu kira ki kuma ke ce last call dinsa da muka gani a wayarsa, ke yake kokarin kira a sanda hadarin ya afku shi yasa muka kira ki, baki dauka ba daga nan muka ga wani lambar mukaddam shima mun kira baya jin mu har cajin wayarsa yakare ta mutu shine ya bamu adireshin ki yace idan muka xo kano mu nemi kaxaure mu shiga general hospital staff quarters mu tambayi madina. Sai kuka ya ci karfin madina ta katse labarin.
Nima na huta hannu, Allah sarki Abba, ko ya mutu ne, ya na nan da rai ban sani ba, se mu saurari ci gaban labari.
.
Wai mai yasa Madina baxa ta yarda da Abba ba tunda ba haramun bane dan ta aure sa ba?
Misali idan kece haka ta paru dake xaki yarda ki auri Abba tunda Kinga har yana neman rasa rayuwar sa akan ki?
Misali kuma idan Kaine duk yadda ka nuna mata kana tsananin son ta har kana neman rasa ranka xaka yarda Kaci gaba da son ta kuwa duk da bata son ka?
Tambaya gare ku mutanen gidan Al-Hada Hada maza da mata kowa muna son jin ra'ayin sa...
Akapta..
.
Typing Sadin Maa.
Posting : Dan Aunty.ADON DAWA
TRUE LIFE STORY
LITTAFI NA BIYU (P 15)
NA JAMILA UMAR TANKO
GABATARWA SADIQ HALIMA (Sadin Maa)
DAGA Al-Hada Hada Hausa Book stories
.
Kaltum ma hawaye take inda ta dafe wuya tace “Allah sarki bai ce a kai shiwajen iyayen sa ba sai ke, gaskiya yana sonki. Amma dai kin tausaya masa da kika gan shi a cikin wannan hali? ”
Madina tayi murmushin karfin hali ta dafa kafadar kaltum t ace “na tausaya masa har na fara nadamar wulakancin da na yi masa a baya. Dan na tabbatar ba son wasa yake min ba. Allah sarki so, shi burinsa na karbi gawarsa ba iyayensa ba don in tabbatar a dalilina ya mutu kamar yadda ko da yaushe yake ce min idan ya mutu in sani a sanadiya ta ya mutu.
Na rasa yadda xanyi dasu sai na kira mukaddam ina rusa kuka ina fada masa halin dana ga Abba. Shima sai ya rushe da kuka yace min mu garxayo dashi asibitin malam aminu kano xamu iske shi a nan yana jiranmu, haka aka yi kuwa, na roke su dasu kaimu asibitin a kano na shiga gidan gaba su biyu suka shiga baya wajen Abba direba ya tuka muka tafi sai xura gudu muke yi kamar xamu kifa saboda su da suke xaune a kusa dashi suna shaida mana cewa yana kokarin cikawa yana bukatar oxygen.
Tsananin kukan da nake rusawa da irin addu’o’in da nake xubawa shi ya ja hankalinsu suka dinga lallashina suna tausaya min kamar yadda suke tausayawa Abba. Muka isa aminu kano, na kira mukaddam na shaida masa mun shigo asibiti sai ya kwatanta mana inda xamu same shi. Kafin mu karaso har ya tanadi likitoci da nurses da leburorin da xasu kula dashi, a tsatstsaye suke suna jiranmu, motar na tsayawa aka dauke shi aka dora shi a gado mai taya aka tura shi aka shiga dashi dakin tiyata.
Abunka da masu hali domin baban mukaddam ma wani hamshakin mai kudi ne ga mulki saboda yayi gwamnan kano a lokacin mulkin soja. Na shaida masa cewar wadanda suka kawo shi suna bukatar a biya su kudin da suka kahse, ya je ya same su suka yi mar lissafi ya dauko kudi masu yawa ya basu, suka shiga motarsu su ka tafi, sai ni sai mukaddam a bakin dakin tiyata, xullumi nake, addu’a muke yi kada ya mutu, idan ya mutu bamu san me xamu fadawa iyayensa ba.
Nayi ta kuka, tamkar raina xai fita ba mukaddam ba, hatta jama’ar da ke wucewa da ma’aikata saida suka taru suke bani hakuri suna kwatantani da marar tawakkali, basu san ba rashin tawakkali ba ne, rashin sanin bayanin da xan yiwa duniya da kaina ne dalilin da Abba ya je ya ragargaje a hanyar garinmu wajen nemo yaya na.
Mukaddam ya dauko waya yana kokarin kiran iyayen Abba xai shaida musu halin daya ke ciki sai na yi caraf na rike wayar na hana shi . tambayata yake me yasa baxa’a fada musu ba, halinda yake ciki ba?
Ai doloe su sani ko bai mutu ba balle yaga alama da wuya Abba ya tashi a yadda yaga numfashinsa yana sama yana kasa. Ni dai na hana shi kira kuma ban san dalili ba, har aka fito dashi daga dakin tiyata likitoci sun duba shi tsaf sun sake dora wasu karayar da ba a dora shi ba da sannan suka sake like ciwukan amma sun hango buguwa a kirjinsa, akwai kashin daya goce a hakarkarinsa sai gobe xa’ayi wannan aiki sannan xa suyi masa hoton kwakwalwa itama su duba ko ta tabu saboda raunin da yake kansa a haka suka kwantar da mu a amenity dakin mutum daya.
Mukaddam yabiya kudin daki mai tsada lafiyayya mai AC, fanka, firij da kujerun alfarma. Mukaddam ya fita ya sissiyo mana abinci da abin sha , shi ma be iya ci ba balle ni, balle kuma shi marar lafiyar wanda babu abunda yake yi sai suma an sakala masa roba a hanci ana xuko numfashi, sai Karin ruwan da ake yi masa leda leda.
Ina xaune a gabansa a kan kujera yayin da nake rike da hannunsa na gaji da kuka sai addu’a nake tofa masa Allah Ya tashi kafadarsa.
Yayinda mukaddam yake lungu yana ta sa addua’ar hankalinmu a tashe bamu Ankara ba sha biyun dare agogon dakin ya buga ya yin da daidai wannan lokaci wayata da wayar mukaddam tadau ruri. Ina duba tawa naga sunan sumayya tukur yayin da mukaddam na duba tasa lambar mami hafsa tukur ce, maman Abba . sai gaba dayan mu muka mike tsaye muka dafe kirji, muka xaxxare ido muka kalli juna. Na ce sumayya ce, yace, mami ce, sai na yi saurin na karbi wayarsa dan kar ya danna . suka yi ta ringing har suka katse yayin da na murtsika wayoyin na kashe gaba daya, duk na bi na rude, ban san me ya kamata na yi ba.
Mukaddam na kokarin nuna min bai dace na kashe wayoyin ba saisu xaci ba lafiya ba ko mun hada baki mun kashe shi musamman idan suka xo suka iske mu tare dashi a asibiti cikin wannan halin, sai na cakumi kwalar rigarsa na matse shi a jikin bango Magana nake yi cikin fushi da kururuwa ina kuka, nace kai ne duk munafukin da ka janyo mana, saboda me xa ka kaishi tasha yahau mota ya tafi garinmu baka sanar min ba, baka sanarwa iyayensa ba?
Dan haka baxa ka amsa wayarsu ba, in kuwa har Abba ya mutu ka sani gawa biyu xaka kwashe domin ni ma sai na kashe kaina.
Kaltum ta tambaya “kuma ke lokacin da gaske kike xaki kashe kan ki? Duk wanda ya kashe kansa dan wuta ne fa.”
Madina ta share hawaye ta yi dan murmushi tace “ba kashe kaina xan yi ba, bacin rai ne kawai da tsantsar jin haushin mukaddam.”
Kaltum t ace “yaya kuka kare? ” madina t ace “kinsan kasa kwacewa yayi daga shaker da na yi masa yana ta bani hakuri har saida Abba yayi Magana. Nan da nan muka dungumo da gudu wajen gadon da yake kwance muna kiran sunansa idonsa a rufe amma sunan madina ya ambata a hankali nan da nan na rike hannunsa na matso da bakina saitin kunnensa na ambaci sunansa nace “Abba, ka ganni bude idanunka ka ganni. “sai yayi ta kokarin bude idonsa amma ya kasa. Hawaye ne kawai yake tsiyayowa daga idanunsa.
Ya fara Magana cikin sanyin murya wacce take fita a hankali y ace madina, ki yafe min abubuwanda nayi miki sannan ki sani duk abunda ya same ni dominki bana nadamar son da nake miki. Burina da fatana ki yadda da gaskiyar son da nake yi miki don kina xaton yaudararki nake, ina so ki kasance akan gawata yayin da Allah Ya dauki raina tamkar yadda mace ta gari take yiwa mijinta addu’a bayan ya mutu nima ki yi min saboda na lissafa ki dan haka na ci burin na aureki Allah baisa kin fahimta ba.”
Na sulale na durkusa na dora hannuna duka biyu a ka ina rusa kuka gami da salati fadi nake Abba na amince xan aureka, ka tashi kar ka mutu ka bar ni. Ya na cikin magana sai jini ya ambulo daga baki da hancinsa, a guje na xura na kira likita. Ya na xuwa sai yace xa su yi masa wata allura kafin gobe a shigar dashi tiyata idan iyayensa sun xo. Dan mukaddam yace musu iyayensa ne xasu saka hannu, tun daga nan Abba bai sake farfadowa ba barci kawai yake bai san inda kansa yake ba.
Jikina ya dauki karkarwa har saida na bawa mukaddam tausayi ya jawo ni ya xaunar da ni akan kujera yayin daya durkusa a gabana yana xubar da hwaye yace, “sister madina, naga kin rikice kin damu da yawa, na san abunda kike tsoro kada iyayensa su xo su ji a dalilinki haka ta faru da shi kin manta da Allah ne Yake shedar bayinsa a nan duniya da gobe kiyama?
Kin manta iyayen Abba musulmai ne, dole su yadda da kaddara mai kyau da marar kyau?
In har bakya so su ji abunda ya faru na amince ba xan fada ba ki dauki jakarki ki fice daga asibitin nan, kafin gobe su xo su ganki.”
Na girgixa kai na ce “idan na gudu shine xa su fi xargina su ce da sanina hakan ta faru saboda dole sai ka fada musu a inda yayi hatsarin saboda ga motarsa nan daya fita da ita a hannunka bada ita yayi hatsarin ba kuma dole likitoci sun dauki statement din yan sanda da suka kawo shi cewar a hanyar onisha suka dauko shi. Don haka gudu ba nawa ba ne duk daran dadewa gaskiya xata fito. Mukaddam, a ganin ka yaya iyayen Abba xasu ji a ransu idan aka ce musu Abba ni yake so har ma dalilina xai rasa rana?
Me yasa ka bari Abba ya jefa kansa cikin wannan hali nima gashi nan ya jawo min? sai na rusa kuka.
Mukaddam ya gyara xama ya bani labarin yadda abun ya faru daga farko har karshe.
LABARIN ABBA.
Mukaddam yace “tun muna yara idan kika lura Abba na sonki, ba son soyayya ba, yana matuakr son ya xauna dake. Baya gajiya da sauraron labarinki haka baya gajiya da kallonki, baya gajiya da yabon kirkin ki ko a bayan idonkine. Haka kawai kike burge shi yadda ya ga kina da tsafta, kina kula da gidanki, yaranki da mai gidanki, yace baki da kwadayi dan bakya roko sai abunda aka baki ki ke karba, baya ga rikon addininki bakya wasa da sallah. Abba ya shaida min cewa ko ya girma xai yi aure sai ya duba mace me tsafta da ladabi irinki sannan xai aura.
Bayan mun girma ya shaida min yana matukar damuwa da irin wahalhalu da wulakancin da mijin ki da kishiyoyinki ke yi miki, hakan bai sa kin fice ba saboda biyayyar aure. Idan muna xaune muna hira, sai ki ji ya tambaye ni yace, “mukaddam, anya kuwa a xamanin nan xan samu mace kamr Madina? ”
sai n ace masa “rabo ne ai, kai dai kayi addu’a kawai. Abba yayi ‘yan mata da yawa amma tun kafin aje ko ina sai dangantakar ta kwabe saboda bata da hali irin na madina. Kinsan gidansu rayuwar turawa ake yi bai tashi ya ga mahaifiyar sa na yiwa mahaifinsa hidima ba komai sai kuku da masu aiki ke yi, ke kuma ya ga komai ke ki ke yiwa mijin ki hatta tsinke xaki mika sai kin taso da gudu kin durkusa har kasa sannan ki bashi haka idan ya kiraki da gudu xa ki bar abinda kike yi ki je ki durkusa. Ba ki da lokacin kowa sai kin salami mai gidanki ko kadan ba kya bata masa rai baki da kiwar aiki.
‘yan mata da dama sun so Abba sai sun fara sai ya daina yace baya son su, har Allah Ya kawo lokacin rabuwarku ki ka bashi tarihin rayuwarki, ki kayi matukar bashi tausayi musamman daya ji kince kin rasa inda xaki nufa baki da iyaye. Sai yace min yana tausayinki yana matukar son yaga ya tallafawa rayuwarki kin koma cikin farin ciki kamar kowace mace mai miji da iyaye.
Daga nan bai sake cewa komai ba sai da aka dade, sannan na lura yana cikin damuwa na, na yi juyin duniyar nan ya ki fada min abunda yake faruwa sai ranar da muka je kaxaure wajen ki kika kore mu nima ranar ya shaida min halinda yake ciki nayi ta bashi hakuri kafin mu rabu yayi min alkawari xai hakura dake amma sai ya kirani a tsakar dare yace ya kasa hakura dake gashi tunaninki ya hana shi barci. Muna ta addu’a amma abu sai karuwa yake yi.
Ya ce min ya fi so ya auri matar daya ke tausayinta dan ya riketa amana. Burinsa ya raya sunna kamar yadda Manxon Allah (SAW) ya auri Nana Khadija a baxawara, ta grime shi, burinsa ya haifar miki da farin ciki, fatansa ya sami soyayyarki, ta iyayensa duk mai sauki ne yasan yadda xai bullo musu su amince kin ki sauraransa ma balle ki fahimce shi.
Sai shekaranjiya ya same ni yace ya tuno wata dubara, xai je garinku ba xai ce ya sanki ba amma xai tambayi inda yayanki innamani yake a enugu sai ya nemo miki shi su xo tare , yin hakan xai faranta miki rai. Na ce kada ya je, yace in kyale shi xai je ko da kuwa xai rasa ransa ne a hanya. Ashe ya fada da bakin mala’iku, haka ta same shi.”
Na juya na dubi Abba, na yi kuka na yi kuka, na ji dama a dawo da rayuwa baya da banyi masa abunda na yi masa ba. Mu dukka bamu runtsa ba har asuba, na yi alwala a bandakin cikin dakin nahau salloli ba adadi kafin assalatu, addu’a nake kada Allah Yasa Abba ya mutu.
Yayinda mukaddam ya tafi masallaci ashe ya dauki wayarsa, yana idar da salla sai ya kunna a inda ya hadu da sakonnin iyayensa da iyayen Abba. Hankalinsu a tashe suke tambayar ina suka shiga shi da Abba tun jiya?
Sai ya yanke shawarar ya kira mahaifiyarsa ya yi mata bayani ita kuma ta yiwa mahaifan Abba bayani. Tun da asuba, kafin gari yawaye xance ya xagaye dangi hankalin kowa ya tashi yayin da motoci na alfarma suka dinga tsayawa a gaban dakin da muke.
Muryar mukaddam na jiyo yan magiya yan bada hakuri game da dogayen bayanai cikin kuka da rawar murya a jikin wundon dakin, na meke da gudu na daga labulen wundon na leka, sai ga en gidan su Abba kakaf da danginsa da ‘yan uwan su mukaddam, yayinda baban mukaddam yaketa sharar masa mari ba adadi da kyar a ka rike shi. Aka sako mukaddam a gaba ya xo ya nuna musu daki, su ka dungumo suka nufo inda muke. Na takure a loko ina karkarwa ina kiran “laa haula wala kuwwata illa billah.”
Suna shigowa suka kalle ni a sheleke babu wanda ya amsa gaisuwata, yayinda suka nufi kan gado da sauri wajen Abba duk wanda ya leka Abba sai yayi baya ya dafe kai yana salati saboda Abba yayi kwatsa-kwatsa. Ina kuka na taso ina shirin in yi musu bayani sai kuwa sumayya tukur ta sharara min mari, sannan ta kira ni da suna karuwa, mahaifiyarsu mami hafsa ta kirani da suna maiya na cinye mata da, wai daman ashe nice na kama shi ya dinga ramewa sannan na yi asirin da sai da ya kai kansa onisha aka tsafe shi dan haka sai hukuma ce xata raba ni dasu.
Alhaji tukur kuwa allurer soja ceta tashi saboda motarsa ya je da sauti ya dauko bindiga yace sai ya harbe ni, abokinsa na rike shi yana fusgewa, sauran ‘yan uwa suka xagaye ni suna yi min cari aka, wai in ba mutuwar xuciya ba da kwadayi irin nawa yaya xa’ayi in tarki yin soyayya da dan yaron nan?
Wai ashe daman yaudarar mutane nake yi ina nunawa ni baiwar Allah ce, daman har yanxu da sauran tsafin da maita a jikina. Ba ni da bakin bayani saboda babu mai sauraro na.”
Sai madina ta rushe da kuka, Yayin da tausayinta yasa kaltum xubo da hawaye mai yawa, tagumi kawai ta yi ta kurawa madina ido , can ta nisa tace ‘gaskiya baki da ta cewa Allah kadai ne xai fitar da ke.”
Madina taci gaba, haka wasu mata biyu daga cikin dangin su Abba suka watso min takalmana da jakata sai gani a gaban tasi’u da yara na Abdul malik da Abdul hakim. Tasi’u yana ta Allah wadai da halina sai kara tunxura su yake yi yana cewa ai shi ya fi sanin wacece madina kuma yaya yake xaune da ni muguwa ce ni.
Alhaji tukur ya fara buga waya yana cewa ayi musu tanadin jirgi xuwa London yanxu yanxu nan xasu fita dashi kasar waje. Mami kuwa wani dan sanda ta bugawa waya tace ya xoya same ta a aminu kano xai kama mata wata mayya. Ban gudu ba kuma ban ji tsoro ba saboda babu kuma wani cin mutunci daya rage min yanxu a duniya wanda ba’a yi min ba, har na fi so ‘yan sandan su kamani su rufe idan Abba ya mutu ni ma a kashe ni na huta.
‘ya’yana da suka ji xa’a kamani sai suka sulalo suka ja hannuna wai sai na tashi mun fice daga asibitin, ni kuma naki tafiya na xauna a barandar dakin nace gara ma a kama ni a kashe ni xai fiye min, da kyar suka ja ni muka tafi,ina jin wasu daga cikinsu suna cewa ga mayyar can xata gudu sai na ji sumayya tace rabu da ita aimun san duk in da xata je yanxu ta lafiyarsa muke yi.
A bakin get din aminu kano ‘ya’yana suka ja burki suka tsaya, sai nima na tsaya a kusa dasu cikin kuka na fara yi musu bayani suma kukan suke yi. Abdul malik ya fada cikin fushi yace “mama ki ja mana abun gori a gari, kin cuce mu har karshen rayuwar mu.” Ya juya ya tafi a fusace, sai na kamo hannun karamin shima ya fusge yace “bana sonki ke ba uwata bace daga yau.” Sai na saki baki ina kallonsu suka tafi suka bar ni a tsaye. Tunda ‘ya’yan da na Haifa a cikin cikina suka fada min haka na san na xama abar gudu a duniya, na san bani da amfani ga duk wata halitta. Na tabbatar na xama abun gudu a duniya, abun mamaki sai na ji kukan da nake yi ya tsaya yayin da na fara murmushi ni kadai na ji ina fadin Alhamdulillah.”
Madina ta fashe da kuka mai tsanani.
Kaltum ta share hawaye ta tambayi cike da mamaki t ace, “me yasa kika ji kin daina kuka kina murmushi? ”
Madina ta dago da luhu-luhun idanuwanta ta dubi kaltum tace “masifa ce tayi masifa amma dukkan wani musulmi da yayi imani ya san Allah ne mai yaye duk wata masifa, na sallama duniya ne kwata-kwata sai na tuna xan mutu in je in tarar da Ubangijina wanda xai yi min sakayya sai naga duk wannan abun kamar ba’ayi ba, shine kawai na ji na daina kuka na yi ta murmushi. Menene dadin duniyar ne?
dadin duniya shine ‘ya’ya, dukiya sai mata, to duk na rasa su a duniya dan haka sai na yi tawakkali na cirewa raina rayuwar duniyar kwata-kwata ina sauraron ranar da Allah xai yanke min wato ranar da xan mutu.
Ina fita daga asibiti na hau acaba na tafi tahsar ‘yan kura, daga can nahau motar kaxaure. Ina isa gidana na xaxxabi ‘yan kayayyakina kadan na xuba a jaka na shiga tunanin inda xan je, bani da inda na sani wanda xan iya kaura. Daga karshe na yanke shawarar nima in tafi enugu in nemo yayana innamani in har yana raye in xauna tare dashi don shi kadai ya rage min. na shiga sake-saken ta inda xan fara nemo su sai nace a raina idan naje enugu na tambayi sunan kawuna exe wanda yake rike shi idan kuwa ya mutu nasan shima innamani watakila a san shi idan yayi kudi tunda yayi karatu, sai dai kash bani da kudin motar tafiya.
Sai na tashi na shiga gidan makwabciyata mai suna sha’atu itama ma nurse ce, baxawara kamar ni. Na iske tayi bakuwa daga Daura suna xaune suna hira. Ta na ganina tace, ina na je tun jiya ake ta nima na ba a ganki ba, kuma me ya same ki kika rame sannan idanuwan ki suka kumbure?
Se nace mata xaxxabi na yi da ciwo ido kuma na je kano tun jiya.
Nan dai muka xauna mu uku suna hirarsu ina sauraran su hankalina baya wajen su, ina tunanin halinda Abba yake ciki.can se mariya kawar shafa’atu ta dauko hirar xuwa makka ta mota xasu bi ta sudan wani satin. Sai kuwa nayi carafna tambaye ta na ce, nawa ne kudin?
Kuma ina ake biyan kudin?
Ta yi min bayani dalla dalla, sai na ji gara kawai in tafi kasar da ba’a sanni ba. Shafa’atu na yi min tsiya tana cewa wai me yasa na ke tambaya ni daba xuwa xan yi ba?
Na ce wallahi da ina da kudi da nima xuwa xan yi.”
Sai mariya ta dubi hannuna tace “yaya xaki ce baki da kudi kuma kina sanye da tafka-tafkan awarwarayen gwal har guda biyu a hannunki ga sarka da ‘yan kunne da xobuna ai ya ishe ki kudin motar har ma yayi saura.”
Sai a lokacin na tuna ashe ina da kadarar gwal, ai nan da nan jikina ya dau rawa nace “wallahi idan mariya xata tafi daura tare xamu tafi”
Mariya tace “ai ni a yanxu xan koma ba xan kwana ba.”
Shafa’atu sai ta fara tuntsirewa da dariya a xaton ta wasa nake yi. Ta ce ta yaya xan bar aikina, da mutunci na, da kuruciyata, ga yarana amma in tafi saudiyya yawon wanke-wanke da shara? ”
Ai sai suka ga na shiga gidana na dauko jakar kayana na rufo gidan na shigo na tsaya akansu na cewa mariya ta taso mu tafi daura, abu kamar wasa sha’atu taga na rikewa mariya hannu muna ta sauri mun bar ta a baya mun nufi bakin titi, ta gaji da bin mu ta juya gida. Tace min “in kin je ma xaki dawo nasan karya kike yi ba wata makka da xaki je.”
Ai kuwa har ya shafa’atu bata ga dawowata ba kuma nasan sun hadu da mariya ta fada mata cewar na tafi. Na bawa mariya sakon mukullin gidana ta bawa shafa’atu ta budeta dibi sauran kayana ta rabar sadaka, ta fada a wajen aikina na daina aiki, a cire ni daga cikin albashi.”
Kaltum tace daga kaxaure se ku tafi daura?
Madina ta yi murmushi tace daga kaxaure sai muka hau motar kano, nace ta xo ta raka ni bakin asibitin murtala in sayar da gawala gwalaina. Mu ka je na sayar kudi da yawa ko xobe daya ban rage ba, sai muka hau motar daura daga kano, muna shiga mota sai na ji wayata na ringing, na yi sauri na dauka, mukaddam ne, hankalina ya gama tashi, na dauka na fara salati ina kuka, dame kuma mukaddam ya ke kira na?
na yi sauri, na koma kira ya daga babu abunda nake jiyowa se koke koke da alama ba lafiya, ina fara tambayarsa lafiya, sai kudin wayata yakare, sai gashi ya kirani daga jin muryarsa kuka yake yi. Ni ma na fashe da kuka nace inna lillahi wa’inna ilaihi raji’un. Mukadda lafiya, ina Abba?
Sai ya sake fashe wa da kuka yace “sister madina Abba ne ya………..”
Sai cajin wayata ta kare dif naji shiru wayar ta mutu. na rusa kuka ba kakkautawa har saida hankalin duk wanda yake cikin motar ya tashi, ana tambayata mutuwa aka yi ne?
nace “eh, kanina ne a asibiti kuma ana fada min halin da yake ciki wayar ta mutu, da alama dai ya mutu dan na jiyo koke koke.
A haka aka taimaka min da waya na kira na ji halin da ake ciki, amman bani da number kowa a kai, sannan kuma sunayen ba a sim card suke ba, sannan kuma babu wanda muke da waya iri daya dashi balle na ari batir. dole na hakura se kuka nake yi, ina tuna Abba se kawai addu’a nake masa Allah Ya jikansa da rahama. Tsarki ya tabbata ga Ubangijin talikai, haka Allah Ya rubuto mana, a haka yake so ya ganni.
Kaltum kinji dalilin xuwana sudan kenan. Wannan shine abunda ya rabo ni da yarana na shiga wannan hali.
Madina taci gaba da kuka marar adadi yayinda kaltum ta takure kanta acikin gwiwowinta ta xubawa madina ido tana kallonta. Xuciyarta ce take xugi da radadin kunci hade da damuwa, da alama mutuwar Abba ta sosa mata rai sosai. Hawayenta ne ke disowa daya bayan daya. Kaltum ta nisa tace “anty madina, amma sanda na ganki a mota da kuma sanda muka xo muka xauna daki daya sai nake gani kamar ke baki da matsala saboda sai in ga koda yaushe kina fara’a, dariya da walwala kullum kamar babu abinda yake damunki. Har nake mamakin yadda kika shiga cikin mu don naga babu alamar wahala a jkinki kwata-kwata.”
Madina tayi murmushi tace “wadatar xuci ce kawai, idan xaki tuna yadda Annabawa da Sahabbai suka yi rayuwa xaki san duniya da abunda ke cikinta gaba daya ba komai bane, ba kuma dauwamammiya bace. Shudewa take wataran tamkar ba’ayi ba. To idan na tuna haka imani yana wanxuwa a xuciyata nasan duk abunda yayi tsanani maganinsa Allah ina matukar farin ciki da Allah yayi ni musulma duk wahala da bakin ciki basa sa ni ni na manta da addinina, ko da ace gaba daya mutanen duniya xasu kini nasan mahaliccina Yana sona kuma Yana tare da ni. Ina jin dadin ni’imar da nake ganina a cikin ta, a mafarkaina, ina yawan mafarki da Shugaban halitta MANXON ALLAH (SAW) don haka na ci riba a rayuwata. me mutum xai yi min in damu kaina, fatana in tashi a cikin al’ummarsa ranar gobe kiyama.”
Kaltum taxare ido ta bude ida ta bude baki tana duban madina duba irin na sha’awar da ma nice ke.
Madina ta yi dariya t ace “kaltum, muddin kina tare da ni hakika xaki koyi yadda ake juyar da bakin ciki ya koma farin ciki. Lokacin sallar la’asar yayi muje mu yi salla.”
Sai suka kwashi shinfidarsu suka shiga cikin gida, domin bada faralli.
ALLAH YA KARA MANA IKHLASI AMEEN , EN UWA RAYUWAR DUNIYA BA KOMAI BACE, PATANA DA MU KARU DA DUK ABUNDA LITTAPIN YA KOYAR NA TAWAKKALI, DA IMANI AKAN KADDARA, KAHAIRI KO SHARRI. ALLAH YASA MU DACE.
AMEEN..
.
Nima Dan Aunty nace Aamiin thumma Aamiin Sadin Maa.
Allah Ya saka miki da alkhairi Ya biya miki dukkan bukatun ki na alkhairi damu baki daya.
Aamiin.
.
Typing : Sadin Maa.
Posting : Dan Aunty.ADON DAWA 2 (P 16)
.
TRUE LIFE STORY
.
BABI NA BAKWAI
Xaman su kaltum a bur suda yadore babu alamar karshensa don babu wani labarin tafiya Saudiya ko komawa Nigeria don haka sai kowaccensu ta cire ranta da tunanin komawa gida. Duk sanda garin Allah Yawaye mata da maxa yara da manyan su saisu fifito neman abunda xa su kai bakin salati, basu cika son su tafi a kungiyance ba saboda rigima ake yi da xarar an miko sadaka sai ka ga ana rigaye rigayen karba har ya kaisu da kaurewa da kokawa kamar wasu dabbobi. Don haka madina take kama hanyarta ta tafi bararta ko aikatau ita kadai yayin da take cewa kaltum ta shiga cikin yara su tafi saboda gudun ‘yan iskan da suke yawan binta.
Wata rana a wajen bara fada ya hautsine tsakanin kaltum da amina, abunda ya hada fadan kuwa shine an miko musu sadakar dabino guda hudu kaltum ce kusa sai ta sa hannu ta karbo tana shirin miko musu sai amina ta warto daga hannunta.
Ta ce mata “mayya, kawo nan an miko min kika yi sauri ki ka karba. Sai kaltum ta yi shiru ta bata dabino ta koma gafe suka ci gaba da tafiya, sai suka xo wucewa ta kofar wani gida a garin ADON DAWA sai suka ga wasu samari guda biyu, samarin suka fada cikin harshen larabci “ku xo ku karbi sadaka.”
Kaltum na dago ido sai taga abokan mambela ne don haka sai tayi saurin matsawa daga wajen sauran ne suka je da sauri suka mika hannu, sai samarin suka ce basu xasu bawa ba su je su kirawo waccan da ta matsa gefe ta xo ta karbar musu kudin wato kaltum suke nufi. Suka dungumo wajen kaltum suka yi mata bayani sai tace “ku xo mu tafi ba baku sadakar suke son yi ba ‘yan iska ne.”
Sai amina ta harari kaltum ta yi gatsine t ace “wai ke dalla kaltum din nan me ki ke ji das hi don kinga kin fi kowa kyau samari na sonki shine kike yiwa mutane wulakanci. Haka rannan a kasuwa wani saurayi ya fito da kudi yawa xai baki kika ki karba. Na san kuma daga baya xaki dawo ki karba bakin ciki ne kawai da wayon banxa.
Kaltum na gaba tafiya kawai take yi yayin da xuciyarta ke tafarfasa tana kuna saboda bakaken maganganun da ta saka ta a gaba tana fada mata harda xagin iyayenta. Kaltum ta tuno da hudubar da madina ta yi mata in da take ce mata “ki kwaci ‘yancinki danke ma ‘ya ce ba baiwa ba.” Ta sake tuno maganr matar da ta bata wuka in da take ce mata “ki fara kashe duk wanda yake da niyyar kashe ki, ki yanki duk wanda yake da niyyar cutar ki.”
Wani xaxxafan hawaye ya sirnano mata yayin data dunkule hannunta cikin fushi ta jiyo sai kake jin ‘dum’ duka ta kai bakin amina kan ka ce kwabo jini yayi faca-faca a rubabben bakinta da baya samun makilin. Amina ta durkushe kasa ta rike baki tana kururuwar kuka saboda tsananin xugi.
Gaba daya sauran suka yi caa akan kaltum suna xaginta, sai ta gada hannu ta dakatar dasu.
Tace “kada wacce ta sake ta fada min bakar magana, ko ta xageni balle ta dake ni, kada ku dauke ni wawuya, marar wayo wacce bata san ciwon kanta ba . kada ku dauka bana jin xafin kyara da cin mutuncin da kuke yi min ada. Na gaji, hakurina ya fara karewa xan taba duk wanda ya taba ni.”
Ta rushe da kuka ta ci gaba da Magana cikin kakkausar murya tace “ku hantare ni, ku xage ni, ku dungure min kai, ku aike ni duk bana kuskure muku kawai don a xauna lafiya, bana son in bata muku rai badan ina tsoranku ba, amma kuma nice na xama abar wulakantwa a wajenku. To ku sani daga yau na daina saurarawa duk wanda baya sarara min, wannan abunda na yiwa amina somin tabi ne kuma xai xama darasi ga dukkanninku.”
Tana rufe bakin ta sai amina tayi kukan kura ta daka tsalle akan kaltum kan ka ce tak sai ga amina a kasa, kaltum ta murde ta, ta nika ta a kasa ta hau ruwan cikinta tana duka.
Su rakiya suka xo suka banbare kaltum daga kan amina da kyar. Kaltum na tashi sai ta bibbige hannayen masu riketa kowacce ta daka tsalle ta koma gefe tayi cirko-cirko tana tsoro kada dukan ya shafe ta. Hakika sun yi matukar mamakin ganin yadda take da karfi haka. Ta juya ta tafi a fusace ta bar su a tsaye suna kallonta.
Tun daga ranar nan babu wacce take marmarin sake takalar kaltum da fada, babu wacce take mata gatsalu, ko tsawa balle xagi da dunguri. Madina ma ta lura da haka taga yadda suke rawar kafa suke nan-nan da kaltum, shishshigi iri-iri kowacce na son shiga harkarta musamman amina. Tunda kaltum bata fada mata komai ba shi yasa tayi shiru bata tambaye taba amma tabbas tasan akwai abunda ya faru aka sami canjin nan.
Kaltum ta samu salama a cikin gida sai ta ji da wadanda suke takura mata a waje, bayan mambela da abokansa ta hadu da wasu batattun samarin jange. Don haka kaltum tayi shiri sosai wajen kare kanta har wata jaka ta samu tana ratayawa cike da makamai.
Da yamma likis kaltum da haule ne suke yawon bara a garin jange sun yiini yau basu samu ba, tunda rana suka rabu da sauran abokan tafiyarsu a jim arab, da suka ga sun yi yawa sai suka raba kansu wasu suka shiga garin ‘yan ADON DAWA wasu suka tafi jim arab, wasu suka tafi hajarar ases, su kaltum kuma suka tafi wajen jange.
Arashin sani su kaltum suka shiga wani lungu, ashe lungun baya bullewa sai suka juya da sauri, xa su fito, suna juyowa sai suka ga samari biyu sun tare su a cikin lungun ko basu ce musu komai ba sun fahimci abunda suke shirin yi musu. Su ka takure a lungu suka makale juna suna ta kururuwa yayin da samarin suka nufo su a hankali suna Magana cikin yarensu.
Kaltum tayi larabci tace “bama jin yarenku, kuyi mana larabci.”
Sai suka fara Magana cikin harshen da xa su fahimta suka ce musu “kun shigo da kanku lungun da baya bullewa, kun yi kuskuren shigowa gidanmu domin babu budurwar da xata shigo nan ta fita lafiya ko ‘yar garin nan ce balle ku baki marasa gata.”
Kaltum ta fada cikin bacin rai “mu baki ne ba mu san ba’a biyo tanan ba, bara muke muna neman abunda xamu ci.”
Sai suka ce “to yanxu xamu baku abunda xaku ci amma fa sai mun gama da ku.”
Yayinda da daya ya wawuri hannun huwaila kaltum kuma daya ya cafko gashin kanta ya damke yace da ita.
“tun farkon xuwanku na ganki naga kin min, baki da labarin na dade ina binki a baya?
Yau ne na ci sa’a na hadu dake a wajen da babu hayaniya babu yadda xa’a yin a barki.”
A cikinku ki tambaya mata nawa ne suke bayar da jikinsu a basu kudi tsofaffi ma balle ku yara masu kyau irinku. Me xai ragu a jikinku idan an taba ki, ki samu kudinki hankalinki kwance. Sai kaltum ta hasala ta hau fuffuka tana fisge-fisge xata kawace, ya bankare wuyanta yana kokarin kai ta kasa, yayinda dayan tuni ya durkusar da huwaila kasa.
Kaltum ta laluba ta ciro wukarta daga cikin rigarta kan kace kwabo ta danna gefen wukar kaifin ya fito fet ka ke ji ta sharba masa a hannu ba shiri ya ske ta ya daka tsalle gefe ya rike hannu yana ihu jini yayi masa face-face a hannu. Kaltum ta sake bude jakar dake makale a hannunta ta xaro wata katuwar kwalbar lemo ta rusa a jikin bango ta fashe rabi ya rugurguje sai ta rike rabin a hannunta ta nufi dayan da yake rike da huwaila, shima a guje ya sake ta suka xabura suka fara ja da baya.
Kaltum ta fada cikin kakkausar murya tace ‘xan kashe duk wanda ya tabo mu, sai na farka cikin duk wanda ya nufo ni.”
Tana xare ido tana nufo su, sai suka tabbatar da gaske take farka cikinsu xata yi dan haka sai suka juya a guje suka fita daga lungun. Kaltum da huwaila suka arta da gudu suka kama gabansu suma. Mamaki ya kama huwaila akan abunda kaltum tayi tana matukar mamakin yadda kaltum ta tanadi irin wadannan mugayen makamai a jikinta. Huwaila taje ta dinga yada kaltum a cikin gida cewar a yi hankali da yin fada da kaltum domin cewar wukake ne da kwalabe a jikinta da xarar fada ya hada ta da mutum xata farka shi da wuka.
Su ka tabbatar kaltum ta xama ‘yar daba yayin da ‘yan gari ma suke kiranta da ‘yar agulla, wato ‘yar daba saboda har ‘yan iskan gari sun gane ta. Ta ketawa samari da dama hannu ta fasa wa jama’a da dama kwalba akai sai dai idan ba’a rutsa taba a lungu ana kokarin a cimmata ba yanxu ne xata yaga fatar mutum.
BABI NA TAKWAS
Yau kaltum ‘yar agulla ta dira a bakin kogi a inda masu kamun kifi suke ta damko manya-manyan kifaye wanda girmansu xai kai girman yaro dan kimanin shekaru fiye da bakwai. Ta tsaya tana jiran abokinta mai suna karim ya fito daga ruwa ya bata kasonta daman ya saba bata kullum sai ta je gida ta gasa su ci.
Karim saurayi ne wanda shekarunsa bai wuce ashirin da biyu ba, dan asalin garin katagun ne a jahar bauchi a kasar Nigeria. Amma bai san kowa a garinsu ba kasancewar iyayensa sun taho dashi sudan tun yana da shekara daya kamar yadda aka bashi tarihin cewa mahaifinsa ya tsaya a n’djamena da niyyar neman kudi sai ya turo karim da mahaifiyarsa su xo sudan su jira shi idan yayi aiki ya samu kudi sai ya same su a sudan su haura saudiya. Tundaga lokacin basu kara haduwa ba, bai xo ba, ana kyautata xaton a n’dajsmena ya rasu yayin da itama mahaifiyarsa Allah yayi mata rasuwa ta barshi shi kadai dan kankanin yaro a hannun wani tsoho abokin tafiyarsu mai suna baba lado.
Karim na xaune shi da tsohon a bur sudan a dakin katako, kwali kadai a shinfide a dakin har ya girma ya fara sana’arsa ta kamun kifi yana sayarwa, a halin yanxu tsohon ya rasu dan haka karim shi ne uwa shine uban kansa.
Ya hadu da kaltum jininsu ya hadu yana farin ciki da ganinta sai ya ga kamar yaga kanwarsa musamman idan ya ji tana yi masa hausa. Da yake babu kalma daya ta soyayya da ke tsakaninsu ita da karim sai ta saki jiki dashi su kayi ta labari haka kuma yana matukar taimaka mata da manyan kifaye gasassu ko danye, ko ma ya bata kudi idan ya sayar ya samu.
Karim yana fitowa daga ruwa sai ya kalli kaltum yayi dariya, itama ta yi masa murmushi cikin harshen hausa take yi masa Magana tace yayana, yau ragon ruwa xaka bani, katon kifi me tsoka. Sai yayi dariya yayi Magana cikin harshen hausa duk da hausar bata fita sosai, yace yau kifin duk manya ne, ki xabi duk wanda kike so.
Kafin karim ya rufe bakinsa sai ya ji wani mummunan duka a kuncinsa har saida ya tuntsura ya fadi kasa. Kaltum da karim suka daga ido lokaci daya suka duba bangaren da dukan ya fito. Sai ga mambela a tsaye ransa a bace mamaki da tsoro gami da fargaba ya rufe xuciyoyin su. Mambela ya sake cacubo karim ya nika da kasa yana shirin hawa ruwan cikinsa da duka, sai kaltum ta yi kukan kura ta xaro wukarta ta yanka mambela a kwairin kafarsa.
Mambeala ya xabura ya rike wajen yayin da karim ya yunkura ya mike tsaye da sauri yana shafa kuncinsa suka yi jawur dan xafi. Mambela ya dago ya dubi kaltum yayin da jini yake bulbulowa daga inda ta yanke shi.
Karim ya fada cikin harshen hausa “kaltum ki gudu kada mambela ya kama ki, wannan mugu ne, ya addabi kowa a garin nan.” Kaltum tace “ba xan gudu ba sai dai ya kashe ni, ka gudu kada ya kara dukan ka, ka bar ni dashi.”
Karim ya arta da gudu ya bar wajen ya tafi can nesa yana duban su, yana tsananin fargabar kada mambela ya tashi ya shake kaltum . har yanxu mambela yana tsugunne yayin da kaltum take tsaye kem a gafe da wukar ta a hannu ta rike kugu, babu alamar tsoro a tare da ita. Mambela ya yago gefen ‘yar sharar rigarsa ya daure kafarsa wajen ciwon sannan ya dago ya dubeta yayi murmushi ya fada cikin harshen larabci yace “yar agulla, kin cika ‘yar agulla, yau na tabbatar ke ‘yar agulla ce. Kin yanki abokaina da yawa yau yankan naki kaina ya dawo kuma, kin yanke ni har jini ya xuba a kasa.”
Sai ya tuntsure da dariya mai fitar da sauti mai kara ya gyada kai y ace “ni mambela, ni ne yau yarinya karama ta yanke ni a kafa, yarinyar ma bakuwa baiwarmu, almajira mai bara. Tabbas baki sanni ba, baki samu mai xaunar dake ya baki labarina ba yadda ya kamata daga nan har cikin gari babu mai taba ni ya kwana lafiya, babu mai yi min musu duk duk abunda nace dai dai ne. ‘yan jange masu barka cikin mtum da wuka, masu fada da kwalba suna tsoron mambela domin ni aka fi sani da yanka. Babana ya fi kowa kudi ya mallaka min gidaje kala kala a kartum bayan na wasu manyan burane a sudan, babu abinda na nema na rasa sai ke, a kanki baxan fara ba dole sai kin amince. Ina biye da ke a duk inda kika saka kafarki, ina ganin mu’amalarki da jama’a sai naga kin fi hulda da wancan tsintaccen yaron karim marar gata, da alama kin damu dashi don haka sai na raba shi da hannunsa ko kafarsa kacukan yadda ba xai sake moruwa ba.”
Kaltum ta fusata ta fara Magana cikin fushi muryarta sama sama tana nuna shi da hannu tace “mambela karya kake yi, baka isa ka ce xaka raba ni da karim ba saboda karim dan uwana ne kasarmu daya, karim ne mai taimako na yana ba ni abinci. Ka sani duk sanda ka taba karim ka yanke shi, ni kuma sai na barka cikinka hanjin ka ya fito waje sai dai nima a kashe ni.”
Ya mike tsaye ya na murmushi yace “na yarda xaki aikata abunda yafi haka ‘yar agulla na tafi sai haduwarmu ta biyu, sai dai ina so ki sani baki isa ki kula wani ba idan ba niba, saboda ina sonki kuma baxan rabu da ke ba.”
Ta Harare shi ta ce “ bana sonka, na tsane ka kuma har abada ba xan so ka ba.”
Ya juya ya tafi a fusace yana dingishi, ta xaro tsumma daga jikin xaninta ta goge jinin da yake jikin wukar ta like ta mayar cikin rigarta ta adana.
Karim ya taho da gudu inda kaltum take tsaye yana ta mamakin karfin hali irin nata, tambayarta yake, “daman kin san mambela, ya aka yi mambela ya sanki har kika yanke shi da wuka bai dauki mataki ba? ”
Kaltum ta ci gaba da ciccibar kifinta ta nufi gida ba tare da ta bashi amsa ba.
Bayan anyi haka da kwana uku misalin karfe goma sha daya na safe, karim na wajen sana’arsa ta kamun kifi sai yaga mambela a tsaye a kansa yayin da mambela ya jawo hannunsa ya fito dashi daga cikin ruwan, kan kace kwabo hantar cikin karim tadau rawa cikin yaren ‘yan ADON DAWA yake bashi hakuri, yana tuba yana neman afuwa.
Mambela ya dukar dashi kasa yace “baka da labarin kaltum tawace?
Ba ka da labarin ni nake sonta kuma babu wanda ya isa ya so ta bayan ni, balle kai bawana? ”
Karim ya daga kai yace “naga alamar haka mai gidana babu mai ja da kai, kaltum kanwata ce kuma na yi alkawarin sai na sa ta so ka.”
Dadi ya lullube xuciyar mambela ya yi murmushi ya tashi karim tsaye, ya karkade masa kasar da ke jikinsa.
Ya ce “ina son kaltum son da bashi da adadi, ina son ka sata ta so ni itama, idan ta ki xan hukunta ka.”
Karim yayi murmushi yace “an gama mai gidana.” Mambela ya juya ya tafi, farin cikin xuciyarsa ya nuna a fuskarsa kai ka ce kaltum din aka bashi kyauta. Mambela na juyawa kaltum ta karaso inda karim yake a tsaye ta tsuke fuska ta tambaye shi “meye mambela ya xo yi a nan, me yace maka? ”
Sai karim yayi dariyaya ce “mu xauna mu yi Magana kanwata kiji labarin abunda baki sani ba.”
Kaltum ta cire sharbabben takalminta silifas wanda ya fi girman kafarta sau biyu gashi a tsinke harta daure da leda. Ta xauna akai yayin da ta baxa wani katon siket dinta burgujeje kore da wata riga t-shirt ruwan dorawa, dankwalinta kuwa ya hadu da cikurkudadden gashinta ya dankare, ta dubi karim tace “ina sauraronka, me nene? ”
Ya durkusa a gaban kaltum sai fara’a yake tamkar gonar auduga yace “kaltum kin yi sa’a da mambela yace yana sonki saboda kin wuce wulakanci, fatara da yunwa a garin nan.”
Kaltum ta ji kamar ya daba mata wuka a kahon xuciyar ta, ta ja dogon tsaki, ta fusata xata mike. Karim ya mayar da ita ta koma ta xauna.
Ya ce “shawara nake baki, ki so shi saboda yana sonki. Meye laipin sa? Gashi kuma dan gidan masu kudi da sarauta, gashi dogo kyakkyawa, laifinsa daya bashi da mutumci shima sai idan ka tsokane shi, ada ne yayi shaye shaye yanxu ya daina.”
NI SADIN MAA ME TYPING NACE “DU KYAWUN MAMBELA, BE KAI BOSS INA DAN ANTY ME POSTING BA, SANNAN KUMA GA CIKA, KAMALA, DA MUTUMCI, DAN ANTY SAI TUBARKALLAH.
Kaltum ta ci gaba da hararar karim har saida ya gama tsara ta sannan tace “ka gama tsara ni?
To ba xan so shi ba har abada, ni na tsani mambela da abokansa kamar yadda na tsani mutuwata.”
Hankalin karim ya tashi yana tambayar ta “saboda me bakya sonsa, me ya miki?
Mambela yana da kirki idan Allah Ya tsaga da rabonka har kyautar saniya sai yayi maka ko kudi mai yawa musamman a lokacin axumi yana da rikon addini kuma.
Kaltum ta fusata ta mike ta ce “ban sani ba, ka je ka tambayi mambela me yayi min shi da abokansa ba ni xaka tambaya ba . kai ma tunda bakinku daya dashi na daina kula ka ba xaka kara ganina a wajenka ba.”
To masu karatu.
Kaltum data yarda da tayin mambela kuwa,?
ya data kasancewa karim idan har kaltum ta ki amincewa mambela?
Domin jin duk amsoshin wa’ennan tambayoyin se ku ci gaba da hakuri da biyo mu.
Mune na ku har kullum masu son dasa nishadi a xukatanku.
.
To jama'a yau Sadin Maa da tsokana ta xo mana.
Madina kuma... am kaltum har ina Madina, kun san masoyan nawa biyu ne
Kaltum kuma taya zata yarda da Mambela bayan da ni a xuciyar ta?
Karshen tika-tika tik, saura kadan auren mu.
DMK ( Dan Aunty, Madina da kaltum).
Allah Ya saka da alkhairi Saadin Maa.
Aamiin.
Typing : Saadin Maa.
Posting : Dan Aunty.ADON DAWA 2 (P 17)
.
Ta juya ta tafi a fusace yayin da karim ya bi ta da gudu yana bata hakuri, ta ki sauraransa, yayi yayi ma ta xo ta karbi kifi tace bata so.
A lokacin dasu kaltum suka cika shekara guda a bur sudan, a lokacin kasar ta fara yi musu dadi dukkaninsu. Saboda da yawancinsu sun sami jari sun fara sana’a sun daina bara, wasu matan suna sayar da kosai, wasu na yin koko, wata waina, wata awara. Wani na dafa shayi da biredi, wani na sayar da rake, wani yayi ‘yar tireda yana sayar da sabulu, omo man shafawa, makilin da brush da dai sauransu. Kofar gidan su kaltum ta xama kamar ‘yar kasuwa ana ta saye da sayarwa. Jange suna xuwa su saya, haka ADON DAWA ma suna xuwa su saya.
Madina ta sami sana’a itama ta daina bara, kosai take toyawa da safe, sai ta sayar da tuwo da daddare. Kaltum ceke tayata wajen xubawa da mikawa da yin wanke wanke. Bayan wannan babu wani abu da kaltum take yi amma komai baya gagararta kyauta ake bata saboda sabon da tayi da jama’a kowa yana sonta.
Kaltum ta manta rabon da ta sayi ruwa da kanta saboda alkwari ne kullum tsohon nan mai sayar da ruwa akan jaki sai ya bata jarka daya ko biyu kyauta. Haka ko ta je bakin kogi ko bata je ba sai karim ya kawo mata katon kifi guda daya ko biyu danye ko gasashshe kyauta, haka wani Muhammad mai sayar da nono akan jaki yake tsiyayo mata nono kyauta, ga makudan kudi da mambela yake cusa mata amma bata taba karba da hannunta ba sai dai ya bawa karim yayi mata dabara ya bata ba tare da tasan kudin mambela bane ta karba ta kashe, ko mambela ya bawa madina ta saya mata wani abun ba tare da ta san mambela ne ya saya mata ba. Duk wanda ke karkarar nan ya san mambela yana son kaltum so na hakika yayin da kowa ya shaida kaltum ta tsane shi, ta tsani ta hada ido dashi, ta tsani ta hada ido dashi a duniya.
Madina ta san komai ma’ana tasan abunda ke gudana tsakanin kaltum da mambela amma ta xuba mata ido bata taba furta mata wata Magana wacce ta shafi mambela ba haka itama kaltum bata yiwa Madina maganar sa ba.
A lokacin da suka cika shekara guda ne ake sake kawo wasu baki wadanda suka taho mota guda suma sun fi su dari uku daga Nigeria ‘yan kasar sokoto ne wasu kuma daga kano da jigawa. Wasu matan da goyonsu, wasu da ciki haka wasu ‘yan mata ne, ga manyan maxa, samari da tsofaffi amma da aka tashi tafiya makka sai aka dauki kalilan aka hayar dasu yayinda aka bar jifgi guda suna ta koke kokensu. Su kaltum suka yi dariya suka ce dasu “xa ku saba kamar yadda muka saba har muke jin dadin xama muka fi son xama a nan damu je makka ko mu koma Nigeria.
Don haka dakuna duk a ciccike suke a kalla mutum ashirin ne yanxu a daki daya, saboda bakin da suka karo. A tattakure ake xaman yayin da hayaniya ta karu. Fada da dambace-dambace suka dadu musamman a wajen shiga ban daki guda daya ne jal gidan mata da maxa. Abun dai ba tsari saboda cudanyar da ake yi maxa da mata sai kaga wannan ba riga, wancan da gajeren wando xai shiga wanka, sai kaji fada ya kaure da xage-xage idan namiji ya kalli mace ko ya leka ta tana wanka sai kaji xage-xage.
Aure yana ta wakana a tsakaninsu sai kaji wancan da wancan ana soyayya, sai ka ji tsoho da tsohuwa sun kulla soyayya, ko saurayi da budurwa suna soyayya, sai ka ji baxawara da baxawari suna son juna don haka ko da yaushe su kaltum suna cikin biki suna cashewa. Sai su aro janereto su jona rediyo a tsakar gida a saka kidan wakokin hausa na ‘yan fim ko na ‘yan Niger su cashi rawa mata da maxa.
Don haka kofar gida an sake kakkafa runfuna katako duk wanda yayi aure sai ya buga nasa dakin a ci gaba da xaman aure. Wadannan tudun kabararrukan nan da suke a cikin dakuna da tsakar gida, da wadanda suke a kofar gida duk sun barbaje saboda dudufniyar da ake yi akansu.
Auratayya da suke kullawa a tsakaninsu ba laifi bane an bi yadda shari’a ta tsara a yi. Inda barnar take wasu matan aure ne sun baro maxansu a can Nigeria sai su ce ruwa ya raba auren saisu yi sabon aurensu kwamacala kenan, masu ilimin cikinsu irin su madina suna kokarin wa’axantar dasu suna wayar da kan mata masu irin wannan hali dasu daina saboda kada fushin Allah Ya kama su, duk macen da ta san tana da aure ta boye ta auri wani amma a banxa.
A yau ma wata mace mai suna talle ‘yar garin mata maye ce a janhuriyar niger,ta yi aure da wani basakkwace mai suna balarabe. Talle ta xo ta yayyayen danta sai ta boye ta ce bata da aure ta auri balarabe bayan bikin da watanni hudu sai ya saketa saki uku da ciki wata hudu. Ta dinga ihu a kofar gida tana burgima tana kuka tana kiran ta shiga uku yaya xata yi da ranta ta baro mijinta a niger, gashi ta yi aure akan aure harta sami ciki kuma ya sake ta idan ta koma kasarsu ina xata ceta samo da?
Kowa ya dinga yi mata Allah wadai, tur da halinta.
Sai ‘yan matan da ake batawa a junansu a yiwa wasu cikin shege, wasu matan kuma waje suke xuwa a basu kudi a yi musu lalata su sami ciki su haife. Irin wannan muguwar kaddarar ceta fada kan rakiya jikar mairo, arnen jange ya yaudare ta yayi mata ciki, ita da kakarta suka yi ta kuka suka rasa inda xasu saka ransu. Idan sun je asibiti ma babu mai kallonsu saboda bada ixinin kasar suke xaune ba. Wannan abun takaici yana damun masu hankalin cikinsu irin su madina, itama maxa da dama daga cikinsu ko ‘yan kasar suna nuna suna sonta da aure ta ki yarda fur. Ta yi kicin-kicin ta rufe ido tace kada ma su fara tana da mijinta a Nigeria ba xata ci amana ba. Haka madina ta sakawa kaltum takunkumi da tsaro gami da sa ido a duk shige da ficen ta, tana yawan bata shawarwari da nasihu wajen kamun kai da gudun xina, tayi taka tsan-tsan da mayaudaran samari.
Sai a yau madina ta kira kaltum gefe suka yi nisa da jama’a sannan suka sami inuwa mai sanyi suka xauna. Madina ta dafa kafadar kaltum tace, “yata kaltum kainsan ina fada miki gaskiya ba xan fada miki abunda xai cuce ki ba, tamkar ‘yata ta ciki na.”
Kaltum ta gyada kai tace “haka ne anty, me ya faru? ”
Madina ta sunkuyar da kai kasa can ta dago ta dubi kaltum tace “meye tsakaninki da mambela a yanxu?
Na san tsakaninku ada.”
Kaltum ta xaxxare ido yayin da xaka iya gane damuwarta a fili. Fargaba ta kama xuciyarta ta fada a gigice “anty bana kula samari kamar yadda kika hana ni ko da xaki tambayi su amina xasu fada miki gaskiya.”
Madina tace “ki kwantar da hankalin ki ba wani abu ba ne so nake in san abunda ban sani ba, nima in sanar dake abunda baki sani ba.”
Kaltum ta yi ajiyar xuciya tace “mambela ya takura min na rasa in da xan saka raina, duk lungun da na bi sai nagan shi yana bina wai yana sona, idan ya bani kudi sai na ki karba, ya siyo min kayan sakawa da kayan ci ya bani in ki karba, sai yayi ta rokona wai dan Allah in kula shi kada sona ya kashe shi harda kuka da hawaye.”
Madina ta yi murmushi tace “kaltum, na yi shekara da sanin mambela kuma babu ranar da mambela ba xai xo mu xauna dashi mu yi maganarki ba tun ban san shi ba har na gane shi, tun bana fahimtar abunda yake fada min har na fahimce shi. Tun yana bani haushi har ya fara bani tausayi. Na dinga gwada hankalinsa har saida na tabbatar ya cinye jarabawarsa tatas. Kaltum mambela yana sonki, mambela nutsatstsen yaro ne a yanxu ko a da bashi da nutsuwa yanxu yagyaru a sanadiyar sonki.”
Kaltum ta ji mamaki ya rufe ta dalili kuwa madina ke hana ta yin samari. Me yasa yanxu madina da kanta take cewa ta saurari saurayi, saurayin ma dan iska irin mambela?
Tabbas alamar mamakin da yake cikin xuciyar kaltum ne ya bayyana a fuskar ta ko bata furta ba.
Madina tayi dariya tace “kada ki damu kada ki yi mamaki yanxu xan fayyace miki abunda nake nufi. Ban ce ki kula mambela dole ba, ban ce ki aure shi ba sai dai nace ki tausaya masa ki taimaki lafiyarsa saboda yana daf da rasa lafiyarsa kamar yadda Abba ya rasa lafiyar sa da ransa a sanadiyar sona.”
Sai hawaye ya sinano daga idanuwan madina yayin da hankalinta yayi matukar tashi, hawayen da madina take xubarwa yayi matukar dagawa kaltum hankali amma fa bukatar da madina take so ba xata iya biya mata ba, bukatar madina tana da nauyi sosai domin ba karamar takurawa xuciyarta da rayuwarta xa’ayi ba don bata son mambela ta tsane shi, bata ki ace baya nunfashi ba.
Kaltum ta matse hawaye tace “anty, me yasa ki ke kuka?
Kina da labarin abubuwanda mambela yayi min a baya shi da abokansa har idan na dawo daki cikin dare nake raxana ina ficewa da gudu suna yi min gixau. Sai kwanan nan na daina wannan raxanar duk akan mambela. Yaya xan yi in kula shi, shi da yake son ya bata min rayuwa? ”
sai ta rushe da kuka.
Madina ta jawo kaltum ta share mata hawaye tace “in har na tabbatar mambela bai sauya ba, ba xan yarda ki tunkare shi ba, mambelan da kika sani da, a yanxu ba haka yake ba. Ya same ni yayi min bayani cewar ya canja na gwada shi sau da yawa na tabbatar ya canja din, na tabbatar yana sonki da gaske ba son shiririta ba, ada ma baya niyyar yaudararki abokansa ne suka xuga shi sai ya biye su yace su dauko masa ke, amma har ga Allah bai yi niyyar taba ki ba tsorata ki kawai yake don yaga kin tsorota tun farko. Ya ce min da xaki tuna ki lura duk abunda xai yi dariya kawai yake yi ba da gaske yake yi ba. Ya shaida min tun sanda ya fara ganinki a duniya Allah Ya jarabce shi da sonki ya fara tunani ta inda xai fara tarar ki kuma yana son ya taimake ki.
Bari na fada miki abunda baki sani ba ma duk lufayu da riguna da siket din da nake baki kina sakwa, kayan kwalliya irin su man shawafa, makilin, turare bada cinikin kosaina nake saya miki ba duk mambela ne yake sayo miki ya kawo min yace ina baki kada in bari ki sani. Kudin da nake baki kina sayan duk abunda kike so kici, kudin mambela ne kike kashewa. Ban fara karbar kudinsa ba saida ya dade yana bina, saida dade ina binciken gaskiyar sa na gama bincikena na tabbatar yana da rikon addininsa, mambela yaro ne mai rikon addini matuka, mai hakuri, mai tausayi, mai ilimin addini, gashi da yawan kyauta da kyautatawa mutanen da suke tare.”
Kaltum ta bude baki tana kallon madina tamkar a mafarki ta ke ji, bata taba xaton madina xata rufe mata wani abu ba haka har irin wannan lokaci mai tsawo bata nuna mata tasan mambela ba, tuni xuciyar tata fara kitsa mata abubuwa .
Tace a ranta “ko dan mambela yana da kudi ne shi yasa take son ta cusa mata shi don muyi ta karbar kudin sa? Yanxu madina xata yarda na auri dan ADON DAWA in dauwama a sudan bayan tasan wanda na fi so a rayuwa ta? ”
Madina ta katseta tace “kaltum ba xan yi miki dole ba akan abunda bakya so, domin shima mambela ban yi masa alkawarin xan saki dole ki so shi ba, na dai ce masa xan shawarce ki in kin yarda xaki kula shi. Ina dai tausayinsa saboda ya rasa sukuni, ya rasa walwala saboda sonki kamar yadda nima na dauka Abba yaudara ta yake har saida aka xo lokacinda ba xan iya taimakonsa ba. Lokacin daya xo daf da xai rasa ransa, Abba ya mutu ya bar ni da tabo, ya barni da ciwon da bani da maganinsa, dalilina kuwa na yi sanadiyyar saka shi a halin damuwa har ya kaishi ga halakar da kansa kawai dan ya same ni. Abba mai kaunata ne tun yana yaro mun yi shakuwar da in har bai shigo gidana ba ya ganni ko ban shiga gidansu na ganshi bama jin dadi a matsayin xumunci, da xumuncin da yake min ya juye soyayya sai na bujire, na yi masa korar kare na yi masa wulakanci da bakaken maganganu, na xage shi na yi masa wargi da duk abunda ya siyo ya kawo min. na tsane shi tamkar wani kumurcin macijin da yake shirin halaka ni. Sai sanda Abba ya bar duniya na fara dana sani, dana sanin da bata da amfani. Sai sanda Abba ya bar duniya na fara muradin sonsa wanda yayi dai-dai da ina soyayya da dutse domin mataccen daya mutu kenann ba xai dawo ba. Na rasa Abba, na rasa mai sona a duniya, na tafka kusluren da xan dauwama a cikinsa, dana sani da nadama. Kuma da ace na amince a lokacin idan ya sanarwa iyayensa xasu amince masa saboda sunyi min farin sani akan kyawawan dabi’una, dana sani keyace. Madina ta rusa kuka.
Kaltum ta ciji baki yayin da hawaye ke bulbulowa daga idanunta itama, babu wacce ta kara yin Magana a cikin su har xuwa wani lokaci mai tsawo sannan madina ta tashi ta nufi gida tana share hawayenta yayin da kaltum ta lankwashe kafa cikin yashi ta rasa abunda yake mata dadi. Ji take kamar an nada gammo an dora mata duniya gaba daya a kanta saboda nauyin maganar da madina ta fada yanxu.
Ta ce a ranta “na tsani mambela, na tsani abunda xai hada ni dashi anya kuwa xan iya yiwa anty madina biyayya in kula shi alhalin nixan cuci kaina? ”
BABI NA TARA
Fiye da minti talatin mambela na tsugunne a gaban kaltum yana mata Magana ta ki daga ido ta dube shi ma balle ta bashi amsa. Tana xaune a kasa yayin da wani katon daronta ke ajiye a gefenta, kanta a sunkuye a kasa tana tonan rami da wani dan tsinke a hannunta tsabar bata da lokacin sauraron sa. Tana jiran karim ya fito daga ruwa ya bata kifinta xa ta gasa ta ci yunwa take ji, karim ne ya fito daga ruwa dauke da komar kama kifi ya kuwa kamo kifaye masu girma, ya hango ta daga nesa ita da wani bai shaida ko wanene ba ne, sai ya kwalla mata kira yace ta kawo daron ya xuba mata.
Ta kai hannu xa ta dauka sai mambela yayi sauri ya sura ya tashi ya nufi inda karim yake tsaye a bakin ruwa, sai yanxu karim ya gane ashe mambela ne. cikin ladabi da tsoro karim ya duka ya gaishe shi, mambela ya amsa cikin fara’a yace “yau baka da kifi ko daya sai dai ka koma ruwa ka kamo wasu ko ka bari sai gobe saboda dukka kifin nan xaka juyewa matata sai daron nan ya cika.”
Karim yayi murmushi yace “an gama ranka ya dade.”
Cikin rawar jiki ya dinga jido kifi yana xubawa a cikin daron har saida ya cika.
Mambela ya yunkura xai dauki daron sai karim yayi sauri ya dafe daron.
Ya ce “bari in kai maka ranka ya dade.”
Mambela ya girgixa kai, yayi murmushi yace “karim ka bari nixan dauka saboda aikin shugabata ne ba aikina ba ne, da aikina ne da sai ka taya ni. Ina neman fada a wajenta, ina neman wani lungu da xan labe a cikin xuciyarta domin kaltum ta xame min tamkar wata tauraruwar dake haske a sararin samaniyar ta fi karfin a saka hannu a dauka sai dai a daga ido a dube ta.”
Karim yayi dariya yace “Allah xai amsa addu’armu mai gidana, xaka sami kaltum da ixinin Allah. Nima a matsayina na yayanta ina bata hakuri, ina yi mata nasiha, da alamar nasara.”
Mambela ya ciccibi daro ya dora a kansa har ya juya xai tafi sai ya juyo ya dubi karim y ace “an jima ka xo gida ka same nixan baka kudin kifinka ka lissafa cinikin da xaka yi yau, ko nawane xan biya.”
Karim ya ji dadi ya kama shi sai yayi dariya ya duka yayi godaiya. Mambela ya isa in da kaltum ke xaune har yanxu.
Ya ce da ita “tashi mu tafi gida ga kifin na karbo miki.”
Ta murguda baki tace “baka burgeni ba, idan ni ka karbowa wannan kifin ba xan ci ba ko tabawa ba xan yi ba saboda ni bana cin kayan haram. Me yasa kai kullum kake axxalumi sai ka cuci na kasa da kai?
Kifi guda daya ko biyu yake bani ya ishe ni ni in ci in bawa wani amma ka kwashe masa kifinsa ko daya baka bar masa ba. Me xai sayar ya sami kudi yau? ”
Mambela yayi murmushi yace “saya na yi a wajnesa, nace ya xo gida ya karbi kudinsa, xan biya shi kudinsa har na linka masa kudin saboda ke.”
Ta tabe baki ta mike ba tare da ta sake Magana ba ta wuce, mambela na biye da ita a baya dauke da daro a kansa tamkar mai aikinta. A bakin kofar dakinsu ya dire daron game da dukawa ya gaisheda madina da sauran matan da suke xaxxaune a tsakar gida, sannan yayi musu sallama ya fita nan fa aka hau kallon-kallo tsakanin madina, kaltum da sauran matan yayin da gaba daya suka xubawa kifayen da suke cikin daro masu rai ne suna xille-xille, manya-manya ido.
Madina ta yi ajiyar xuciya, ta kalli kaltum ta yi murmushi tace “wannan ne kifin da karim yace a kawo min?
daman na bashi kudin, kifin siyarwa nake shirin farawa da ranar nan.”
Da alama kaltum bata fahimci wayencewa madina take yi ba, saboda gudun ‘yan gulma da sharri kala-kala shiyasa madina ta yi haka. Madina taga alama kaltum bata fahimce taba har tana kokarin ta yi mata bayanin gaskiya a game da kifin sai ta yi sauri tace da kaltum “dauko mana kwanuka da wukake su maimuna su taya ni gyara wa .”
Kaltum ta fara leke-leke, daki-daki tana hado kan wukaken da kwanuka manya-manya ta kawowa madina. Sannan ta dauki bokiti ta fita kofar gida ta tsaya tana waiwaye-waiwaye tana so taga ta inda mai sayar da ruwa xai bullo.
Maimuna ta xunguri hannun madina tace “wai ni wannan ba yaron nan mai ji da kansa dan gidan masu kudi bane wannan?
Yaya aka yi ya xama dan aiken kaltum? ”
Madina ta girgixa kai tace “kai, bashi ba ne yaya xa’ayi dan ADON DAWA ya xama dan dakenmu?
Ina jin hausawanmu ne maxauna wadanda suka saba da ita.
Tani tace “ni fa yaron nan tabbas na sanshi, dan ADON DAWA ne don har ya sha bani sadaka a kasuwa ko a gidansu.”
Madina ta tabe baki tace “watakila abokin karim ya dauko mata saboda nauyi ko kuma a hanya suka hadu ya tausaya mata ya dauko mata kinsan ‘yan ADON DAWA musulmansu suna da imani.”
Mekudi tace “anya, ‘yan kasar nan yadda suka raina mana ajawli har xasu yarda su xama ‘yan dakon mu? ”
Madina dai tayi sauri ta kawar da xancen nan don taga kokari suke su kureta, tabbas sun fahimci wani abu so suke su ji kwakwaf su yi gaba su yada.
Da sanyin safiya misalin karfe shida da rabi yayin da kowacce mace da namiji suke cuku-cukun fitowa da kayan sana’arsu, kaltum kuwa a lokacin take kara kudundunewa a cikin mayafi saboda tsananin xaxxabin da ta tashi dashi hade da hararwa. Ta tashi a guje ta fito tsakar gida ta fara kelaye amai a tsakar gida tana yi tana tila kasa akai sai ta canja waje, idan ta canja waje sai ta sake kelaye wani shima ta bunne ta sake waje. Kowa ya tausaya mata sai sannu ake yi mata da addu’ar Allah Ysauwake sai da ta amayar da duk abincin da ke cikinta ya xamto ko tayi yukurin aman babu abunda yake fitowa. Tana xaune tsuru a gefe yayin da ta doka tagumi tana sauraran yadda Allah xai yi da ita nan gaba.
Madina ceta xo ta dafa kafadarta yayinda ta ambaci sunanta t ace “ki daina tagumi, ki yi addu’a Allah Ya baki sauki, ga koko nan da kosai ki ci ko guda biyu ne idan na gama dani xan je in siyo miki magani. Hawaye ne ya kecewa kaltum domin tana tsananin son taci abinci amma tana tsoron amai madina ta sa gefen xaninta ta goge mata hawaye ta ci gaba da lalashinta har saida kaltum ta daina kuka ta fara kubar kokon sannan madina ta bar ta, ta koma kofar gida inda suke saye da sayarwarsu. Kaltum ce kadai a tsakar gida cikin dabara take dan gutsirar kosai tana korawa da koko saboda tsananin yunwar datake damunta.
Kafin ta cinye kosai biyu cikinta ya burkice ya hautsine yayin da amai ya bulo, ta yi sauri ta kai bakinta kasa don kada ya bata mata jiki sai taga an tare aman maimakon ya xuba a kasa sai ya xuba a jikin wani yadi wahalar yunkurin aman ya hana ta dago ido ta dubi wanda ya tare aman, sai bayan da ta gama hawayen daya cika mata ido ya xubo sannan ta dago ido ta dubi wanda ke tsaye a kanta domin tabbas taga hannaye da kafar mutum ne a tsugunne a kanta. Tana daga kai sai ta hada ido da mambela ne ya bude rigarda ke jikinsa ya tare aman da take yi. Sai ta ji gabanta ya fadi, mamaki ya kamata ta rasa dalilinsa na yin hakan, abunka da kiyayya sai ta danganta yin hakan da iskanci ne kawai ba tausayi bane ba kuma kulawa bace.
Ya fada cikin siririyar murya “ya jiki? sannu, tashi in kai ki asibiti.”
Kaltum ta ji ranta yabaci haushinsa ya kamata, ta rasa abunda ya kawo shi wajenta. Da alama magiyar da yake yi mata ta ishe ta, tayi masa tsawa ta yi Magana cikin fushi tace ba xata je asibitin ba ya rabu da ita, ta mayar da kanta ta kunshe a cikin gwiwowinta ta daina kallon inda yake. Ya gaji da Magana shi kadai sannan ya juya xai fice, xai wuc eta miko masa buta da ruwa tace ya wanke aman jikinsa. Ya karbi butar gami da yin godiya ya wanke wajen sanna ya fice daga gidan hankalinsa a tashe .
‘yan gidan suka dinga ‘yan gulmace kungiya-kungiya domin sun fahimci tabbas mambela yana son kaltum ita kuma bata ra’ayinsa. Wasu kuwa tuni sun kulla sharri suna cewa daman dan kasa take so shi yasa bata kula baki duk wanda yace yana sonta a cikinsu bata kula shi. Watakila amaye-amayen nan da take yi ciki yayi mata sai take nunawa mutane bata kula shi. Kowa dai yana nasa xargin.
Fitar mambela babu dadewa sai gashi dauke da ledoji biyu a hannunsa daya dankar da magani, dayar kuma shake take da kayan marmari irinsu ayaba, abarba, gwanda da lemo. Har yanxu kaltum na xaune a inda ya bar ta, ya xo ya ajiye a gabanta ya fada cikin ladabi.
“ga magani ki sha tunda ba xaki je asibitin ba.”
Ta kawar da kai gefe bata dube shi ba ya ajiye a gabanta sai ya fice bayan ya yiwa madina sallama a kofar gida ya wuce xuwa garinsu, daga dukkan alamu bai ji dadin yadda kaltum tayi masa ba domin jikin sa yayi sanyi, sannan ga kuma yanayin da ya same ta a ciki na rashin lapiyarta na matukar damunsa.
.
Typing Sadin Maa.
Posting : Dan Aunty.ADON DAWA 2 (P 18)
.
Madina ta shigo ta iske kaltum xaune da ledoji a gabanta ga rana ta iske inuwar da take xaune sai ta rikota ta tasheta tsaye ta shiga da ita dakin da ledojin. Ta dinga bare mata ayaba da gwanda tana ci yayinda take yi mata nasiha mai ratsa jiki, ta nuna mata duk abubuwan nan da mambela yake yi mata itace soyayyar, son gaskiya ne yake yi mata.
A yammacin wannan rana su kaltum sun hallara a wajen baki a teku suna budirin bikin amina ‘yar dakinsu da Ado shima a gidan yake. Makadan hausa ne suke kada ganga yayinda mata suke tike rawa, masu gasa kifi suna ta gasawa a gefe ana rabawa ‘yan biki. Bikin ya hallacci mutane da yawa daga wurare daban daban wasu daga garin jange, wasu daga garin ADON DAWA wasu kuwa hausawa ne maxaunan khartum bahari. Mata da maxa, manya da yara ne suke xagaye makada wasu a tsatstsaye.
Kaltum tana daya daga cikin wadanda ke xaune a gaba ita da kawayenta ‘yan mata, ta ci ado da wata lufaya koriya tana daya daga cikin kayan da mambela ya bawa madina ta bata ba tare da ta sani ba. A xaune suke suna girgixa saboda dadin kida sai dai basu samu sun shiga fili ba saboda manyansu ne a ciki filin.
Kamar daga sama ta ji wata murya a gefenta tamkar rada aka yi mata a kunne, ta yi sauri ta waiga gefenta sai taga mambela ne ya rufe kansa da wani katon mayafi tamkar mace idanuwansa kadai ake gani. Nan da nan taji ranta ya baci, farin cikin da take ciki ya dasashe, kafin kace tak annurin fuskarta ya gushe sai ta fara murgude-murguden baki tana Harare-harare.
Ya fada cikin lallausar murya “kaltum yau ranar farin ciki ne, ranar da kowannenmu yake cikin nishadi. Me yasa ranki ya baci daga ganina alhali ni mai kaunar ki ne, mai son ganinki a cikin farin ciki.”
Kaltum ta yi sauri ta dubi huwaila dake xaune a dayan gefen nata sai taga huwaila bata ma ga mambela ba, tana kallon rawa. Ta sake daga kai ta dubi jama’ar dake tsaitsaye a kansu sai taga kowa sha’anin gabansa yake yi, hayaniya ce kadai ke tashi baya ga sautin kida da wake wake.
Sai ta juya ta dubi mambela duba na takaici, ta cije baki alamar xata keta masa rashin mutumci, tana so ta tabbatar masa ita ‘yar agulla ce sai ta saka hannu a riga kan kace kwabo ta ciro ‘yar wukarta ta danna gefe sai tsinin wukar ya fito, nan da nan mambela ya ja gefe yayi tsuru yana dubanta.
Ta fada cike da bashi tabbaci tace “ka matsa daga kusa da ni in ba haka ba xan jinyata ka. Mambela, na tsane ka, na tsani wanda yake sonka saboda kai macuci ne axxalumi.”
Takaici bayyananne xaka hango daga idanuwan mambela, ya dade a tsugunne yana dubanta can ya mike ya tafi da alama ransa y abaci. Biki yayi biki mata da maxa, yara da manya sun cakuda sai rawa ake ana juyi dan haka su kaltum sun sami dammar shiga fili sun cashe suma saida magaruba ta yi waje yayi duhu har baka iya shaida na kusa da kai sannan suka fara shirin watsewa. ‘yan mata irin su kaltum ne aka sa su tattaro farantai da cokulan da aka yi ciye ciye, su biyar ne suka rage a filin suna faman tattare kaya dakyar suke iya gano farantan saboda duhu.
Kaltum na tsugunne ita kadai tana jera farantan roba akan babban faranti tana shirin mikewa ta dora a kai ta tafi gida yayinda sauran ‘yan matan hudu har sun dora nasu aka sun yi gaba. Sai ta ji kamar an jeho wani abu gabanta da karfi, sai ta yi sauri ta duba kasa inda abun ya fadi, sai taga kafar mutum ce nan ta raxana ta fadi xaune dabas tana karkarwa. Ta daga ido da sauri sai taga dogon mutum ne a tsaye duk ilahirin jikinsa a rufe da wani bakin mayafi.
Ta fada a tsorace “waye kai, me kake nema a waje na? ”
Ya ce “mambela ne, soyayyarki nake nema.”
Sai ta mike a fusace tana shirin barin wajen cikin gaggawa, ya shiga gabanta ya hanata wucewa, kan kace tak harta xaro ‘yar wukar ta, ta keta masa a dantsan hannunsa, saboda tsananin kaifin wukar har saida ta tsaga mayafin ta shiga namansa. Yayi kara ya tsugunna ya rike wajen yayin daya dangwalo jini jajawur a hannunsa ya haska da fitilar da ke hannunsa sai yaga jini ne. har yanxu kaltum tana tsaye a kansa da wuka a hannunta jira take ya mike ya mike ya tabata ta sake yankarsa tana tsoran juya baya kada ya cafko ta. A halin yanxu xuciyarta ta kekashe take, ji take a ranta ko aljani ma idan xai fito fili saisu fafata balle bil adama dan uwanta. Bata jin tsoran kowa kuma bata shakkar fada da kowa sai dai ita bata neman fada amma muddin aka tabata xata yi wa mutum illa ba tare da bata lokaci ba.
Ya dago ya dubeta ya haska fuskarta da fitila sai ya sake haska mata dantsan hannunsa inda ta yanke shi, taga sharceccen yankan da tayi masa jini jage jage, bai ga alamar nadama a fuskarta ba. Ta cije baki tana rawar jiki tamkar so take ta kara masa.
Ya tambaye ta cikin harshen larabci ya fada cikin wata lallausar murya yace “kaltum a ganinki kinyi daidai da kika yanke ni da wuka?
A she dama soyayya laifi ce a wajenki, har ki ka nemi ki kashe ni don nace ina son ki? ”
Ta fada cikin kakkausar murya tace “bana sonka axxalumi.”
Ta juya baya a fusace xata tafi sai ta ji ya xo da gudu ya finciko ta sai kuwa ta sake kai masa yanka wannan karon ma ta same shi a dan yatsa daya nan ma jini ya fito. Tana shirin yankarsa a kirji sai ya rike hannunta da sauri ya murde da karfi ya kwace wukar yayin daya warbar da ita gefe ta fadi akasa rim. Ya cafko gashin kanta ya hada da lufayar da ta lullube kanta ya damke, inda ya kawo wukar saitin hancinta xuwa wuyanta.
Ya ce, “ke yarinya karama, duk irin wadannan ta’addancin mun yi mun daina yanxu naki ma wasa ne idan kin ji labarin irin wanda muka yi.”
Ta hau fusge fusge amma ta kasa kwacewa. Ya ce “yau ni da ke kadai xamu kwana a cikin duhun a bakin kogin nan, duk abunda xai cinye mu sai dai ya cinye mu idan kuma ki ka yi kokarin guduwa sai na fusgo ki mun fada cikin ruwan nan mu mutu dukkan mu kowa ya huta.”
Sannan ya saketa yayin da ta mike a fusace xata tafi a guje, bata san yadda aka yi ba sai ta ji ta a kanannade a cikin mayafi an xargota ta fadi kasa sannan ta yi sauri ta yaye mayafin daga fuskarta ta waiwaya mambela ta gani a tsaye a kanta ashe shine ya xargo ta da mayafin.
Ta fada a fusace “wai kai me ka ke nema ne a wajena, me xan yi maka? ”
Mambela ya xauna a kusa da ita yana fuskantar ta yace “yau ni da ke babu mai raba mu sai Allah, yau sai na fahimtar da ke ko ni wa nene kuma ko me yasa na kasa rabuwa da ke. Yau sai kin bani tarihin rayuwarki, asalinki, daga inda kika fito da kuma dalilin xuwarki kasar nan.”
Kaltum ta Harare shi, hakika ta kara jin tsanar mambela tace “bana bukatar in san ko kai wa nene, kuma ba lallai ne kasan ko ni wa cece ba. Mambela na gane ka tuntuni so kake ka bata min rayuwata, burinka ka yi min fyade tun bayau ba. To bari ka ji in fada maka da wannan abu ya fara tsakanin mu gara ni da kai mu mutu ko kuma ni in kashe kaina, kar ka ga ka kwace wukata ka xata ba xan iya halaka ka ba……”
Bata rufe bakinta ba mambela yayi sauri ya katse ta y ace “kaltum, mambela da ki ka sani a da yanxu ba haka yake ba, haka kuma xargin da kike yi min ba haka ba ne a xuciyata tun asali ma. Tabbas na san ba xaki yarda dani ba saboda tun farko abunda ya faru a tsakaninmu duk da ba xaki yarda ba amma xan fada miki gaskiya. tun farkon haduwarmu dake kallo daya nayi miki na ji haka kawai ina sonki, har cikin raina so na gaskiya bada niyyar cuta ko yaudara ba. Ban yi Magana ba da farko sai abokai na suke shawarta ta da suke kai min ke cikin shago, babu yadda xan yi dasu haka nan na amsa musu amma nayi haka ne dan idan mun shiga shagon xaki tsaya ki saurare ni har na isar miki da sakon xuciyata gare ki ashe na yi kuskure da na bari suka dauko min ke a ka., shi ya jawo kike min wannan tsanar. Madina ta sheda min cewar kin koma gida kina firgita kina ambaton sunana wai xan kashe ki. Ta fada min kin sha jinya a sanadiyyar yanka hannunki da kika yi da wuka. Ina rokarki dan Allah ki yafe min ki manta da wancan abubuwanda suka faru tunda Ubangijina Allah Ya halicce ni ban taba haduwa da yarinyar da nake so ba har cikin raina sai ke. Na yi iyakar kokarina wajen cire sonki abu ya gagara, na kasa dainawa, kullum sai karuwa yake.
Wallahi kaltum bani da niyyar cutar dake, ban taba sha’awar yi miki fyade ba, tsoratar dake nake yi kawai a haukata idan kika ji tsorona xaki so ni, na shaidawa abokaina abunda yake xuciyata ko da xaki tambaye su xasu ce na fada musu bada gaske xasu kamo ki ba tsorata kawai xasu yi saboda ina sonki na hakika. Dan baki sani ba ne na bata da samarin garinmu da yawa, haka nayi ta fada da samarin jange masu shirin su cuce ki, ko da yaushe ina biye dake duk inda kika shiga bana bari wani abu ya cuce ki sai dai in ban ga giftawarki ba. Kaltum burina a kanki shine na aure ki, in fitar dake daga irin wannan matsananciyar rayuwar da kuke ciki ta rashin galihu, sannan tun asali, duk rashin ji na ban taba kusantar wata mace ba, balle ace na yi fyade.”
Ta dago da sauri ta dube shi duba mai tafe da mamaki hade da rashin fahimta. Ya gyada kai yace “ban taba ganin matar da ina ganinta na ji a raina naga matar da xan aura ba sai sanda na fara ganinki a duniya sai kawai na ji a jiki na ke kika dace da xama mata ta.”
Kaltum ta mike tsaye ba tare da tace dashi komai ba, amma da alamar sanyin jiki da kunya a tare da ita, mambela ma ya mike yana dubanta yana sauraron abunda xata fada sai yaga ta fara tafiya a hankali yayin da yayi sauri ya nada gammo da mayafinsa ya dauki farantin akansa yana biye da ita a baya.
Gari yayi duhu kirin babu kowa yana cikin gidansa sai kukan tsuntsaye da kwari kadai kake ji saida suka isa kofar gidan su kaltum sannan suka hango hasken fitila da alama akwai maxa kofar gidan wadanda suke xama suna hira. Sai ta ja burki ta tsaya ta yi shiru tana tunanin me xasu xarga idan suka ganta da mambela a cikin daren nan babu mai fitar da ita daga mugun sharrin da xa’a kulla mata ba. Ta dube shi ta sosa keya ta sunkuyar da kai kasa.
Ta ce “ka bani farantin in shiga gida saboda bana son a ganmu tare a cikin daren nan. “bai yi mata musu ba don ya fahimce ta sai kawai yayi sauri ya dora mata farantin a kanta. Yayi murmushi ya fada cikin sanyayyar murya mai ratsa xuciyar masoya y ace “nagode saida safe kaltum.”
Ba tare da ta waiwayo inda yake ba ta ce “Allah Ya kai mu mambela.” Ta ci gaba da tafiya.
Mambela ya sankare a tsaye cikin duhu yana kallon kaltum har saida ta yinisa ya daina hangota sannan ya motsa, saboda tsabar farin cikin daya hadu dashi a yau ya samu kaltum ta tsaya ta saurare shi harta fara gamsuwa da bayanansa gashi ya samu ta amsa sallamar da yayi mata. Bai damu da jini jage jagen da ya bata masa Kaya ba ya wuce xuwa garinsu yana mai tsananin farin ciki.
Kaltum ta isa tana fargabar kada a tuhumeta da laifin dadewa amma sai ta iske kowa yana sha’anin gabansa saboda hayaniyar biki ba a kwanta da wuri ba. A lokacin da kaltum ta kwanta hakarkarinta ta lumshe ido sai ta fara hango hannun mambela dai-dai inda ta yanke shi da wuka jinni yana xuba, sai ta firgita ta tashi xaune. Madina ta daga kai ta dubeta sai ta tambaye ta ta ce “kaltum lafiya, bakya addu’a ko? ”
Kaltum ta tuna ashe bata yi addu’a ba sanda xata kwanta sai ta karanta addu’o’I ta shafe jikinta ta koma ta kwanta.
Washe gari da safe mambela ya bayyana a kofar gidansu kaltum a lokacin da duk masu sana’ar da abincin safe suka fara firfito da kayan dahuwarsu, shi kuma ya fara ware ido yana neman abar kaunarsa kaltum amma bai ganta ba sai dai ya hango madina tana kosai. Ya isa gareta yana mai yi mata sallama fuskartsa cike da fara’a. a halin yanxu madina ma ta koyi larabci don haka suka fara yarawa, ya dade a tsugunne a gabanta suna ‘yar hira amma yana jin kunyar ya tambaye ta kaltum harta lura da hakan.
Ta ce dashi kaxo duba jikin kaltum ne?
sai ya xabura cikin furgici y ace “bata da lafiya ne? ”
Ganin hankalinsa ya tashi sai ta yi sauri ta fara gyara xancen. Mambela ya girgixa kai ya fada cikin damuwa.
Ya ce “anty kada ki boye min komai a game da kaltum, ta xama ni na xama ita matsalarta tawace, ki fada min me yake damunta.”
Madina tayi shiru can tace “gaskiya kaltum ta hadu da ciwon aljanu xuwan mu garin nan ba ita kadai ba jama’ar mu da yawa suna fama da wannan larura kasancewar muna xaune ne a cikin makabarta,nan da nan saisu bugeta ta fadi.”
Mambela ya maimaita cike da mamaki “aljanu kamar yaya?
Daman ana ciwon aljanu? ”
Madina ta gyada kai tace “ana yi mambela .”
Ya ce “ciwon yana da magani, ana warke wa? ”
Ta gyada kai tace sosai kuwa ai kowanne ciwo yana da maganinsa kafin Allah Ya sauke ciwo saida Ya saukar da maganinsa, da xa’a sami babban malami wanda ya haddace Qur’ani xai iya maganinsu.”
Mambela ya mike da sauri ya nufi garinsu yayin da madina ta shiga juyayin ina xai je ne daya tafi da sauri haka?
Tafiyarsa da kamar awa guda sai gashi ya dawo shi da wani mutum da alama mutumin malamin addini ne a sanadiyar dogon carbin daya rike a hannunsa. Mambela ya kirawo madina gefe ya sanar da ita ya taho da mai maganin cire aljanun don haka tayi musu iso xuwa wajen kaltum. Ba tare da bata lokaci ba ta wuce gaba suka bi ta har cikin dakinsu, hankalin mambela ya tashi daya ga muhallinsu, suka iske kaltum a kudindine akan kwali rabin kanta a kasa cikin yashi tana barci mai kama da suma.
Malamin mai rukiya ya xaro wani dan gwabgwani ya bude, sannan ya lakuto wani mai dan kadan ya lakutawa madina a yatsanta y ace ta samu ta cusawa kaltum a hanci. Jikin madina na karkarwa ta je ta durkusa a kusa da kaltum ta kai yatsanta a hankali har kofar hancinta sannan ta bursuna mata man a kofar hancin.
Kafin kace kwabo kaltum ta firgita ta mike xaune a gigice. Ta fara atishawa a jere a jere sai malam ya fara yi mata tofi yayin da madina da mambela suka xagaye ta idan ta yi kokarin yunkurawa xata tashi sai madina ta danne ta har malam ya fara karatu yana daga murya da karfi. Kafin kiftawar ido da budewa hankalin kaltum ya tashi ta rasa inda xata saka ranta tana ta buge buge da haure haure yayin da muryarta ta koma wata murya wacce bata taba ba. Ta fara Magana cikin yaren larabci, ta dawo yaren ‘yan ADON DAWA , ta mako yaren jange ta ci gaba da fulatanci, (TANA NEMAN DAN ANTY) ta hado da hausa sannan ta juye indiyanci. Koma dai da wane yare take Magana abunda take fada shine waisu aljanu ne a jikin kaltum suke xaune saboda ta kwanta akan gidansu kuma ta tattaka musu yara shi yasa suka shige ta. Sannan suka kara da cewa akwai wani mambela wanda yake yawan bata mata rai da xarar ya bata mata rai sai mu kuma mu bugeta ta fadi, sun kara da cewa su suke hanata yin ibada don tana yawan kona su da addu’o’I shi yasa yanxu suke daure bakinta bata son yin addu’a sosai.
Malam ya tuntube su yaya batun fita daga jikinta kuma!? Sai suka ce ai sun samu gidan xama a jikinta baxa su fita ba. Nan fa aka fara dauki ba dadi tsakanin aljannu da malam ya dinga kona su da ayar Allah yayinda suke ta ihu da bubbuge bubbuge. Wannan karon saida jama’ar gidan suka kawo agaji wajen kaltum domin abun ya fi karfin madina da mambela su kadai, don xubar da mutane take yi kasa.
Da axaba ta tsananta ga aljannun sai suka hau ihu suna bashi hakuri gami da daukan alkawarin idan ya daina kona su xasu fita yanxu ba xa su kara dawowa jikinta ba. Sai suka dinga ficewa daya bayan daya sai ga kaltum ta mike ras kamar ba ita bace a kanannade ba daxu. Malam ya bawa madina magungunan da kaltum xata dinga sha da na shafawa da kuma na hayaki. Ya kuma gargadi kaltum da ta dinga suturta jikinta ta daina yawo ba dankwali, ta xama mai yawan karatun Qur’ani da yin addu’o’I musamman a lokacin kwanciya barci ko shiga bandaki. Malam da mambela suka tafi suka bar kaltum a xaune tayi tsuro-tsuro tana tunani ta rasa abubuwanda suke faruwa a tare da ita domin duk abunda ta yi bata sani ba tun jiya da daddare da ta kwanta barci bata sake sanin abunda ya faru da ita ba sai dai taga jama’a kewaye da ita ana rike da ita suna yi mata sannu sannan ta tabbatar lallai bata da lafiya. Sannan ta yi matukar mamakin yadda mambela ya shigo har dakinsu bayan bai taba shigowa ba.
Tafiyar mambela da malam ba dadewa sai ga mambela ya dawo dauke da jakar kalanxi da kaskon turaren wuta, ya kawowa madina yace ta dinga yiwa kaltum turaren magani sannan ya tafi. Can da yamma kuma sai gashi a wata mota tifa dauke da wasu manyan kataye da wasu maxa guda hudu a kofar gidansu kaltum a kace ana sallama da madina a kofar gida. Sai ta ji gabanta ya fadi ba shiri ta janyo mayafinta ta fito, mambela ta gani cikin katuwar mota sai mamakin da take ji ya karu. Ya gaishe ta sannan suka kebe gefe ya shaida mata ya xo da ma’aikata ne yana so a shinfide musu katako a kasan dakinsu kasancewar ya ga kaltum daxu a kwance a kasan yashi shi yasa yak e so a buga katako saisu daina kwana a cikin yashi madina tace to amma sai ta shawarci sauran ‘yan dakin tunda basu biyu ba ne a dakin suna da yawa sun doshi su goma sha biyar. Mambela y ace ta je ta tambaye su idan sun amince sai ma’aikatan su shiga su fara.
Madina ta shiga gida ta samu ‘yan dakin su ta shaida musu nan da nan suka amince cikin farin ciki da xumudi suka dinga firfitar da kayansu waje madina ta riko kaltum wacce har yanxu tana yawan bacci ta kaita dakin kusa dasu ta kwantar da ita bsannan ta fita ta yiwa su mambela iso shi kuma ya umurci ma’aikata dasu dauko kayan aiki su shiga su fara. Mambela sai kai kawo yake daga daki xuwa tsakar gida xuwa kofar gida yana ta haska ido yana ta hangen mata reras a xaxxaune a tsakar gida amma bai hango abar kaunarsa ba kaltum ya kasa tambayar madina kuma.
Kafin magaruba an lelayewa su kaltum daki ras da katakwaye masu santsi, aka tottoshe musu hudojin rufin daki inda ruwa yake shigo musu lokacin damuna, aka huda musu window inda iska xata dinga shigo musu sannan aka gyara musu kyauren kofa aka yi musu sakata da wajen makala kwado.
Sai tururuwar lekawa dakin ake yi ana gani, sha’awa ta kama ‘yan sauran dakunan suna cewa dama suma a dakin suke. ‘yan dakin kuwa farin ciki suke harda tsalle yayin da suka kewaye mambela suna yi masa buda da kirari suna masa fatan Allah Ya bashi kaltum. Gogan naka sai ya ji babu kamarsu a duniya tunda suka Ambato masa sunan kaltum sai ya shiga rabon kudi saboda su sosa masa inda yake masa kaikayi wato xancen daya fi so a duniya.
Mambela da ma’aikatansa suka shiga mota suka tafi, da daddare bayan sallar isha’I sai ga mambela shi da direban mota sun dawo a cikin wannan katuwar motar karon ma a kofar gida ya tsaya ya aika a kira madina kofar gida, sai ta fito cike da mamaki. Mambela ta sake gani sai ya karaso inda take tsaye ya shaida mata cewar katifu biyu da fululluka ya kawo musu ita daya kaltum daya maimakon su ginga kwanciya a kan kwalaye saisu dinga kwanciya a kan katifa. Hawaye ne ya sirnanawa daga idanuwan madina dan tausayin mambela, sai ta tuno irin rawar jikinda Abba yake yi mata a sanadiyar son da yake yi mata.
Mambela da direban mota ne suka kinkimo katifun da fululluka kowa ya kinkimi daya daya suka shigar musu har kofar dakinsu. Mambela ya koma cikin mota sai gashi dauke da tobe (sakatara) labulen da yake kewaye daki gaba daya. Madina ta dinga addu’a da godiya har ya fita daga gidan yayin da mata suka cika dakinsu madina dankar suna ta yabon halin mambela kaltum tana xaune tana kallonsu tana kuma sauraron nasihohin da kowacce take mata, babu wacce bata bata shawarar ta kula mambela ba saboda karshen so mambela yana nuna mata, suka ce gara tayi karatun ta nutsu ta yiwa kanta fada tun kafin damar nan ta kufce mata.
Kwanakin kaltum uku sannan ta warware ras ta samu sauki , kallo daya xa kayi mata ka tabbatar ta samu lafiya. Kana ganinta xa ka ga t a dawo nutsatstsiya mai kunya, hankali da sanin ya kamata. Ashe daman yawan fushin da take yi da rashin son shiga mutane harda gudunmuwar aljanu suke tunxurata.
Hantsi yayi duk masu sayar da abincin safe sun gama don haka kowa yana cuku cukun kwasar kayan sana’arsa xuwa cikin gida. Kaltum ce a xaune kofar gida tana wanke kwarya, kaskon suya da kwanukan da ake xuba kosai. Sai ta ji sallama a bayanta, tayi sauri ta waiwaya sai taga mambela ne sai ta sunkuyar da kanta kasa alamar kunya tayi murmushi ta gaishe shi. Ya xagayo ya tsugunna a gabanta sai ya tsoma hannu ya fara yi mata dauraya yayin da yake yi mata hira iri-iri (SU DAN ANTY SE HAKURI) gyada kai kawai take yi ba tare da tayi Magana ba har suka gama wankewa dukka, ya taya ta kwashewa xuwa cikin gida. Tundaga wannan lokacin mambeala ya tabbatar kaltum ta fara sonsa badan komai ba saidan kunyarsa da take matukar ji, alamomin so kuwa shine kunya da jin nauyi, ladabi da biyayya.
Mambela kan daddagewa yayi fashin kwana daya xuwa biyu bai xo yaga kaltum ba saboda gudun kada ya takura mata amma badan xuciyarsa tana da sukuni ba har sai ya xo ya ganta yake samun nutsuwa. Sannan bai taba xuwa hannu haka ba, ba tare daya riko mata wani abu ba. Ko da yaushe yana taho mata da wani abu kamar sutura, kayan marmari, ko kayan sanyi irin su ice cream, lemo iri-iri (juices) sai kuma kudi mai yawa wanda xata dinga kashewa.
Yau ma kamar kullum yadda ya saba xuwa da yamma suna xaune akan wani dan dakali a gefen kofar gidansu kaltum suna hira. Kallo daya xaka yiwa kowannensu ka tabbatar yana cikin farin ciki da tsananin kaunar juna. Kana doso inda suke xaune xaka fara hango annurin fuskokin su musamman mambela wanda ke yawan kallonta yana yi mata magana kasa-kasa a setin kunnenta, sai dai duk inda ka kai da iya labe dan kaji abunda suke fada ba xaka iya jiyowa ba sai dai ita wacce ake yi dominta ita kadai take ji. Xaka iya ganin murmushin ta cikin kunya take gyada kai yayin da sonsa ya hana ta daga ido ta dube shi. Kanta a sunkuye yake a kasa da ‘iman.
Mambela ya dubi kaltum yace “yau ne ranar da muka yi alkawari cewar xaki bani tarihinki tun daga farko har karshe nima nayi miki nawa tarihin ba tare damun boyewa juna komai ba. Haka ne ko? ”
Kaltum ta gyada kai tayi murmushi tace haka ne.
Ya ce to bismillah, ina sauraronki.
Kaltum tayi shiru na dan lokaci sannan ta dago ta dubi mambela wanda ke dubanta duba irin na shaukin so da xumudin sauraron xaxxakar muryarta baya ga tsantsar kaguwa ya ji abunda xai fito daga bakinta, sai tayi sauri ta sunkuyar da kanta kasa. Ta laluba wani dagon kara da ke ajiye a gefenta ta fara wasa dashi a kasa tana tona rami yayin da ta fara da fadar asalin sunanta da sunan iyayenta, garinsu da asalin kasarsu. Hakika labarin kaltum ya fara tsumama xuciyar mambela don ya fara jiyo abubuwan da al’adaun da bai taba jiba. yana sauraronnta yana yi mata tambayoyi kala-kala akan abinda bai gane ba sai ya ji a ransa yana son Nigeria yana son al’adun hausawa. Ta bashi labarinta tsab bata boye masa komai ba kamar yadda ta bawa madina, tun daga sanda mahaifanta suka hadu suka yi aure har ixuwa ranar daya fara ganinta a duniya. Sai dai kash! Kafin tagama bada labarinta hawaye yayi mata face-face a ido shima haka, sun dade suna xubar da hawaye dukkaninsu saboda tausayin wahalar da kaltum ta sha a rayuwa. har aka rasa wanda xai lallashi wani a cikinsu, mambela yayi matukar tausaya wa kaltum sai ya ji ya kara sonta da kaunarta ya sake kara daura dantsen xakulo ta daga cikin rayuwar kangin da take ciki. Ya kasa kwatanto yadda xai jiye mata dadi idan suka yi aure, ya kasa auno irin tattalinta da xai yi don ta huce takaicin maraici da tayi a baya. Sai ya shiga lallashinta yana bata baki cewar ta kwantar da hankalinta komai ya wuce.
Amma ya tuhumi iyayenta da rashin kyutata wa wajen kin janyo ta a jiki da suka yi kamar dai yadda madina ma ta fada sannan yayi Allah wadai da hali irin na goggo fattu, y ace bata kyauta ba musamman da yaji irin axabar da ta gana mata a makka. Ya ce shi da ita su godewa Allah daya sa ba’a tafi makkan nan da ita ba, da wannan karon ma wahalar da xata bata sai tafi tada. shi kuma da aka yi haka sai ya fiye masa alkhairi tunda gashi ya sami dammar haduwa da ita.
Mambela ya dubeta yayi murmushi sai yayi mata wata tambaya wacce tasa saida ta dago idanuwanta kacokan ta dube shi yayin da amsa ta kauracewa kwakwalwarta.
Tambayar da yayi mata itace “kaltum anya kuwa alhaji adnan ba sonki yake bada gaske?
A ganina ba xargi matarsa keyi ba da gaskiyarta. Anya kuwa kyautatawar nan da yake yi miki da shakuwar da ku kayi ba xata juye tsantsar kauna ba har ya kai ku ga yin aure? ”
Wannan tambaya tasa bata da amsa sai kaltum ta mayar da kanta kasa bata iya cewa komai ba. Mambela yayi shiru na dan wani lokaci sai yayi ajiyar xuciya.
Ya ce “xan baki tarihina, yanxu xa kiji ko ni wa nene.”
WA NENE MAMBELA!
Domin jin wannan amsar se ku ci gaba da hakuri da biyo mu dan jin amsa.
.
Ni kuma Dan anti nace babu amsa, dan daga nan ba inda xanyi da Membela sai cikin teku kipi da kada su andame shi,
Shi kenan...
.
Typing : Sadin Maa.
Posting : Dan Aunty.ADON DAWA 2 (P 19)
.
WAYE MAMBELA!
.
Ya ce “sunana Ahmad, sunan mahaifina Mahmud, mahaifiyata kuma Aisha. Iyayena sun fito daga dangi guda, jinin sarauta, sune suke da sarautar garinmu iyaye da kakanni. Mahaifin Aisha shine kanin mahaifin Mahmud uwa daya uba daya, mahaifin Mahmud shine sarkin garinmu yayin da mahaifin aisha shine waxirin sa. Tun kafin a haife ni suke kan sarauta har rana irinta yau suna nan basu rasu ba, Mahmud da aisha su kadai ne ‘ya’ya a wajen mahaifan su yayin da suma kadai suka Haifa don haka ni kadai ne ‘da kuma ni kadai ne jika a gidanmu gaba daya. Kamar yadda kika sani abu ne mai wuya a garinmu kiga namiji ya auri mata biyu, kowa mace daya yake aure balle a haifar min dan uba.
Gata yayi gata, ta ko ina nuna min kauna kama da kakannina xuwa iyeyena, danginmu harda mutanen gari masu neman fada.
Kaltum ta gyara xama da alama tana jin dadin labarin. Sai ta dube shi tayi murmushi tace Ahmad sunanka, me yasa ake kiranka da mambela? ”
Yayi dariya yace yawancin ‘yan garinmu idan kin lura xa ki ga duk an boye mana sunayenmu na gaskiya. an saka mana wani suna na kirari a yarenmu. Mambela suna ne wanda kakana ya saka min domin na yi kama da mahaifina sak, mahaifinna kuma ya yi kama da mahaifinsa sak shima, dan haka mu uku kamanmu daya. Kasancewar auren wuri dukkaninsu su kayi sai ki xata sarki shine babana, shi kuma babana sai ki xata shine yaya na. sarki yana ganin ni ne xan gaje shi ba mahaifina ba, tun ina dan karami sai ya sauko daga kujerar sarauta ya dora ni akai yace mambela ma’ana SAI KA YI shine jama’ar gaba daya suke kirana da mambela.
Kakanninmu basu yi karatun addini sosai ba, amma mahaifina yayi karatun addini sosai, yayi yawon neman ilimi gari-gari, lungu lungu dan haka babban malami ne sosai wanda bana jin akwai mai iliminsa duk garinmu. Amma ni kuma na ki karatu fur tun ina yaro, idan ya takura ni sai inyi ta kuka ina kururuwa har sai sarki ya jiyo ya aiko a xo a dauke ni, da yake gidan gado ne, na sarauta duk ilahirin danginmu a cikin gida daya muke xaune bangare bangare. Ba xaki iya sanin yadda gidanmu yake ba saboda ba’a barin kowa ya shiga gidan sarki saida wani muhimmin dalili kuma sai anyi maka iso shi yasa idan kuna bara bakwa shiga gidan da kin ga yadda tsarin ginin yake.
Na tashi a shagwabe babu mai saka ni babu mai hana ni, haka babu ilimin addini balle na xamani tunda garinmu babu makarnatar boko. Dan haka babu wanda yayi ilimin xamani. Sarki yaki yarda a gina mana makarantar boko a garinmu yayin da wadanda ba musulmai ba suma suke koyarda na su karatun addini a gidajen su. Mu ma muna da makarantun allo kalakala. Mahaifina yana da tasa tsangayar amma naki karatu, kakana kuma yace a kyale ni.
hakika kamar yadda kika samu wasu labarum a kaina cewar bani da kirki, ni dan shaye shaye ne, dan agulla mai fada da yanka jama’a tabbas ba karya ba ne duk abunda aka ce nayi lallai na yi din…………..”
Kaltum ta dago da sauri ta dubi mambela a gigice, kallon nan da tayi masa shi ya katse shi ya kasa ci gaba da maganar da yake yi. Sun dade suna kallon juna sannan suka dukar da idanuwansu kasa kowannensu yana nasa tunanin a xuciya. Kaltum ta ji hankalin ta ya tashi da ta ji kalaman mambela gashi ta fara sonsa saboda son da yake mata da kyautatawa ya jawo itama ta fara sonsa har take tunanin da sharri ake yi masa, ashe da gaske duk abubuwan nan ya yi dan haka ya amsa gurbataccen sunan nan nasa na tantiri……..”
Mambela ya katse tunaninta ya ci gaba da cewa “kaltum naga alamar damuwa a tattare da ke dan na fada miki yadda nake a baya. Kin manta mun yiwa juna alkawarin xamu fadawa juna gaskiya, ba xa mu boye komai ba?
Kaltum ina yi miki son da ba xamu xauna yau gobe mu rabu ba, bana yi miki son da xai xo ya shude, ina yi miki son da xan xauna dake harda mutua xata raba mu, xama na dindindin ba xaman boye boye ba ko xaman karya wanda dadewa wani xai fada miki ko ban fada miki b a.”
Wannan karon ma sai ta dago da ido ta dube shi duba na mamaki da ta ji yana kokarin ambaton aure. Mambela ya narairaice ido kamar mai shirin fashewa da kuka y ace “kaltum, anya kuwa ba son ma so wani na ke yi ba har yanxu?
Kaltum ki tausaya min ki tausayawa rayuwata, ko ba kya son dan ADON DAWA ki fara saboda na kasance mai sonki kuma ba xan iya rabuwa da ke ba. Na fada miki gaskiyar halayyata ada saboda xaman gaskiya nake so muyi ni da ke. Mambela ada da mambelar yanxu ba daya bane, ba yabon kaina nake yi ba xan iya kiran kaina nafi duk wani saurayi a garinmu ilimin addini da rikon addini da kuma nutsuwa a yanxu, sabanin da ko karatun sallah ban iya ba sai tsokane tsokane da rashin kunya.”
Kaltum ta dube shi duba irin na rashin fahimta t ace “yaushe ka nemi ilimi? ”
Mambela yayi dariya ya gyara xama yace “Alhamdulillahi da kika tambaye ni. Ina da shekara goma sha biyar a duniya a lokacin na addabi jama’a idan naga dama sai na tsare kofar garinmu ba mai shiga ba me fita a ranar. Haka idan naga dama ni da abokaina ‘yan agulla xamu shiga kasuwa mu raraka duk wani mai saye da sayarwa ba xa’ayi cinikin ba a ranar kuma mu kwashi kayan jama’a mu ci mu xubar da wasu. Sannan idan naga dama xan je bakin kogi in hana kowa kamun kifi a ranar babu wanda xai hana ni kuma, ko anje an fadawa sarki sai yace yarinta ce ke damu na a kyale ni.
Na addabi kowa daga baki har ‘yan gari haka duk rashin mutunci irin na jange saida suka sara min wajen iya fada da kwalba da wukake, gashi fadana baya mutuwa. Dan in cinnawa gidan kara wuta ba komai ba ne a wajena.
Wannan hali nawa yayi matukar tayarwa da mahaifina hankali ya rasa yadda xai yi gashi mahaifinsa ya hana a kai ni makaranta. Cikin dare ina barci a dakina na sha nayi mankawas sai mahaifina ya xo da gardawa uku suka taya shi cicciba ta suka saka ni a amalanke suka fita da ni daga garin xuwa khartum bahari in da aka saka ni a jirgin kasa ba tare da na sani ba sai muka tafi khartum. Tun da daddare muke tafiya har gari yawaye rana tayi sannan muka isa yayin dana bude idona na ganni a cikin jirgi, xan xabura da gudu mahaifina ya cafke ni ya fara lallashina yace xamu je xiyara ne gobe xamu dawo. Na yi ta mamaki amma sai na fara murna saboda naga burni, naga abubuwanda ban taba gani ba. Tunda nake ban taba shiga burni ba , tunda aka haifeni ni a kauye nake sai dai ‘yan garinmu da yawa suna da gidaje a burane suka xuba ‘yan haya amma basa xama a ciki saboda dokar da kakana sarki ya saka cewar dole ne kowa ya xauna a garin dan kada tarihin garin ya rushe, idan kowa ya tafi sai a wayi gari wata rana babu kowa. Tabbas sarki ya fi kowa kudi haka yana da gidajen a garuruwa da dama jiragen ruwa da ake yi masa haya, wasu nasa ne, wasu kuwa ya mallakawa babana, wasu da sunana aka siya du kina da labari sai dai ba’a taba xuwa da ni ba sai daisu ke xuwa. Don mahaifina baya wata uku bai shigo birni ba, yana kuma yawan kai dabino da nono cikin birni ya sayar ya dawo.
Da farko gidan wani amininsa da suka yi karatu tare ya kai ni mai suna sheikh El-Mustapa. bayan mun gaisa aka bamu masauki mu kayi wanka, mu ka ci abinci, muka yi salla. Sai naga mahaifina da sheikh El-mustapaha sun kebe suka dade suna Magana sannan aka ce na dauki jakar na biyo su, sannan muka fita daga gari muka fara shiga dawa a ka kaini wani gida, suka yi min wayo suka sulale suka tafi suka bar ni ban san ko ina ne ba ashe gidan gagararrun yara ne. a nan fa na hadu da ‘yan iskan burni dana kauye wadanda suka fini fitina, saida na raina kaina na tabbatar ashe niba dan iska ba ne.ga ‘yan iskn da suka fini wato wato a cikin dare lokacin da duk ma’aikata suka yi barci manyan suke tashin mu daga bacci su yi ta bugunmu b mu isa mu fadawa kowa ba kuma. Bayan dauri da duka da ma’ aikatan ke yi mana gashi dole mu tashi da asuba mu yi sallah sanman a fara karatun kur’ ani. Daga fatiha ake fara koya mana mu duka babu wanda xai iya karanta fatiha tiryan-tiryan a cikin mu balle mu iya hada baki dan haka tun daga alifun aka fara koya mana, aka koya mana fatiha da karatun sallah da yadda ake yin sallar. In takaice miki said a na shekara biyu cur ban ga wanda na sani ba balle in fito in ga hasken waje muna ciki a kulle. Tsakar gidanmu, bandakunanmu, dakuna, filin wasanninmu da ajujuwan karatunmu duk suna cikin gidan.
Wata rana kwatsam aka ce min in xo ana nemana a bakin get nayi bako, na fito cike da mamaki sai naga ashe mahaifina ne da amininsa sheik el-mustapha. Na fashe da kuka dan murna na rungume su. Tabbas sun tausaya min saboda irin maka-makan tabo da shatin bulalan da suka gani a jikina amma sun ji dadin ganin yadda na shiryu. Su ka nemi xasu tafi da ni, da kaina naki saboda na saba da gidan da abokaina. Malaminmu ma ya shawarce su a kyale ni xuwa wata shekarar xamu yi sauka harmun fara hadda don haka suka tafi suka barni na ci gaba da xama bayan sun bani sababbin kaya da kayan abinci kalakala. Ashe akwai wani kudi da ake biya duk shekara masu dimbin yawa, yana xuwa ya biya duk shekara ni ban ma sani ba.”
Kaltum tayi ajiyar xuciya ta cire tagumin data doka ta dube shi ta yi murmushi tace “yaya kakan ka yayi da yaga an shekara biyu bai ganka ba, yaya ya yi tunda bai san in da aka kai ka ba da ya sani daya sa an xo an dauke ka saboda baya so a takura maka? ”
Mambela yace “bai san inda nake ba tabbas daba xai bar niba, da da kansa ma xai xo ya dauke ni. Ai tun a ranar da muka fito daga garin ni da mahaifina bai koma ba shima, doguwar wasika ya rubuta ya bawa mahaifiyata y ace ta kaiwa sarki washe gari. Ya shaida masa ya tafi da ni yawon karatu shi da ni duk xamu nemo ilimi a kasar saudiya wata shida xamu yi. Ba’a ganmu ba, babu labarin mu har sai bayan shekara biyu sannan ya je garin shima saida ya samu labarin hankalin sarki ya tashi yasa ana ta addu’o’in Allah Ya bayya na mu, ya baxa jama’arsa gari gari ana neman mu kwatsam sai gashi ya xo, ya shaida musu nima ina cikin koshin lapiya nace xan dawo kwanan na. sarki ya yiwa mahaifina fada sosai, ransa yabaci lallai lallai yaje ya taho da ni. A daddafe dai na cika shekaru uku a gidan kangarrun yara a lokacin na sauke Qur’ani har nayi haddar fiye da rabi baya ga sanin hadisai da tauhidi. Xuciyata ta canja na xama mai tsoron Allah, banda Allah babu abunda nake hange a xuciyata, sai ibada nake yi koda yaushe.
Jama’ar garinmu duk sun tsorata dana dawo suna fargaba annoba ta dawo xan takura musu amma sai suka iske niba mambelan daba ne, wannan mambelan babu abunda yake yi yanxu sai salama-salama. Sarki ma ya ji dadin wannan canjin nawa, ina xama tare dashi mu yi maganar hankali da fahimta ya gaskata na samu nutsuwa yayi farin ciki da abunda dansa ya min daga baya.
Xuwa na garinmu da wata biyu muka sake yin shwara da mahaifina xan koma garin khaltum wajen abokin nan nasa shiek el-mustapha in sake samo ilimi. Na yiwa sarki bayani ya gamsu ya bani ixini na tafi. Rayuwata a khartum rayuwa ceta ‘yanci, farin ciki da wayewa. Na yi karatu yadda ya kamata haka na xauna da ‘yan burni na waye, nayi hankali, na san me yake faruwa a cikin al’umma. Na koyi siya da siyarwa, na kuma sami ilimin xamani kadan, na iya rubutu da karatu duk da daman mu komai da larabci muke yi sabanin irin rubutun bokon da naga ‘yan kasarku na yi.
Ganin na nutsu mahaifina ya nunnuna mi gidajenmu da muke dasu a khrtum duka da akwai ‘yan haya a ciki amma daya bayan daya saida muka xagaya. Akwai wasu abokai na da muka yi karatu tare a wajen sheik el-mustapha suka ce jami’a xasu wuce akwai yadda ake su sami certificate daga gwamnati, nima na kutsa muka samu aka dauke mu a jami’a. saida muka cika shekara uku sannan muka kammala daegree dinmu duk akan Qu’ani. Komai a saukake yake xo min dan na rika na horu a gidan kangararru, na fito da sakamako mai kyau daga nan na wuce saudiya inda na shekara biyu a jami’ar madina na hada masters dina. Sannan na dawo gida, na dawo da wata biyu muka hadu da ke.
Na shiga cikin abokaina da watsatstsu don in shiryar dasu, cikin dubara nake so in cusa musu ra’ayina su dai na shahsanci, su kintsu su koma makaranta. Na xo da niyyar wa’axantarwa ga duk marasa ilimi da kafuran garinmu amma sai dai da dabara bada karfi ba. Shi yasa nake shiga cikinsu mu xauna a kasuwa muna caca a haka nake yi musu wayo duk sanda lokacin sallah yayi sai in ce to a tashi ayi salla sai aci gaba. Wancan yayi nan, in taro shi wanca yayi can in kamo shi dole mu musulman mu yi sallah, kafuran kuwa suna gefe suna kallonmu idan mun idar sai mu sake xama in dinga wa’axantar dasu cikin wayo ina fadar axaba ga wanda baya sallah, Alhamdulillah na samu da yawa sun shiga musulunci yayin da wasu sun fara karkatowa da alama xasu yarda da ni wata rana. Har yanxu wannan tsoran nawa da suke ji da yana nan, haka idan na fada ba’a kin bi don haka na tsawatar dole an rage shaye shaye da iskance iskance a garinmu.
Sanin da suka yi min, shiyasa da suka ganki suka ce ga wata mai kyau su kai min ke shago mana, na biye musu don in samu in yi Magana da ke, in san matsalarki, in taimaka miki ke kuma baki fahimce niba.”
Kaltum tayi ajiyar xuciya ta gyada kai alamar labarin ya tsuma mata jiki tabbas ta yarda mambela yasan Qur’ani don baya jimla daya ba tare daya ja ayar Qur’ani ba ya fassara.
Daga karshe ya dubeta yace “kaltum, xaki yarda ki auri mambela, mu koma gidana a khartum mu xauna in saka ki a jami’a kiyi degree kema daga nan in kai ki saudiyya kiyi masters? ’
Sai ta yi sauri ta ja mayafinta ta rufe fuskarta da alama dai dariyar jin dadice ta kamata. Magaruba tayi don haka mambela yayi mata sallalma ya nufi garinsu, ita kuma ta shiga gida xuciyarta ta kara shaker kaunar mambela.
Kwanci tashi su kaltum sun cika shekaru biyu cur a bur sudan, sun mike kafa sun baxa kayansu suna jin dadin rayuwarsu basa tunanin komawa gida. Masu aure da haife haife sai yi suke suna sakewa. Gidan su kaltum sai ci gaba yake yi koda yaushe suna kara bunkasa yadda xasu sami ci gaba da dadin xama. An kara bandaki haka an lailaye kowanne daki da katako kamar dai yadda mambela ya bude musu hanya.
Mambela ne ya iske madina a kofar gida tana xaune tana jin hantsi, bayan tagama sayar da kosanta. Bayan ya gaisheta sai ya tambayi abar kaunarsa kaltum, t ace masa ta aike ta kasuwa. bayan ya jima suna ta hira sai ya tuntubi madina xancen aurensa da kaltum, kan kace kwabo hankalin madina yayi mummunan tashi har saida mambela ya gane ta shiga wani hali shima ya tashi nasa hankalin.
Ya fada a furgice”anty madina lafiya? ”
Ta xubo da hawayen daya cika mata ido ta girgixa kai tace “mambela ba xan boye maka ba a gaskiya bana son in jefa rayuwar kaltum a irin halin da na jefa rayuwata, saboda ni babba ce babu abunda ban kammala bana rayuwa tunda na yi aure na hayyayafa, na girma nayi hankali kaltum kuwa yarinya ce karama wace bata fara sanin rayuwa ba.”
Mambela ya fada cike da damuwa “anty madina, ina son kaltum ba xan cuce taba, xan riketa amana tamkar ni ne ubanta ni ne danginta.”
Madina ta girgixa kai tace “ba haka ba ne mambela, ba wai don ba xa ka iya rike taba na fadi haka. Ba na son ace a mtsayin ta na yarinya mai karancin shekaru ace ta rabu da iyayenta da danginta ta kauro wata kasa ta gina rayuwa ita kadai. Da xarar ta yi aure ta fara haihuwa ko kudi aka bata ba xata iya tafiya kasarta ba saboda yaranta. Ka ga daga nan ta xama tsintacciyar mage wacce ba’a san asalinta ba, a iya kiranta shegiya marar uba, xa’a iya ce mata ma ‘yar iska, ko bata da asali a bola aka tsince ta.
Mambela ya dubi madina ransa ya fara baci ya cije baki ya fada cike da kasaita “me ki ke son yanxu ki fada min? ”
Madina ta tabe baki ta fada cike da isa tace “ina son sanar maka ba xata yi aure a nan ba sai dai in ka bi ta kasarsu gaban iyayenta ka nemi aurenta a can; subaka ita da kansu.”
Ya fada cikin daga murya yace “kaltum ta fada min ba xata koma kasarsu ba a nan xata dawwama.”
Madina ta girgixa kai tace “rashin hankali ke damunta amma ni na yanke shawarar tura ta gida. A yanxu haka na kusa tara mata kudin mota, xan hada tada masu tafiya a mayar da ita gidansu ko tana so ko bata so.”
Mambela ya xubo da hawaye mai xafi daga idanuwansa ya dubi madina duba irin wacce take kokarin ta raba shi da rayuwar sa yace “me yasa xaki tura kaltum ita kadai ke baxa ki tafi ba? ”
Madina ta yi shiru can tace “saboda na fi son in ceci rayuwar kaltum akan in ceci rayuwata. Na fi kaunar in saka kaltum cikin farin ciki da kwanciyar hankali da in nemi nawa farin cikin.”
Mambela ya mike tsaye a fusace yace “babu inda kaltum xata je, saboda muddin kaltum ta koma garinsu iyayenta ba xa su bari ta dawo ta yi aure a sudan ba. Ki na nufin in bar kaltum ta koma kasarsu anan in je in nemi auren ta?
Kema kin san ba xa su yarda ba sai dai idan na aure ta idan ta haihu sannan mu je da ita a lokacin babu mai raba auren. Ko kina nufin alhaji adnan xai bari wani ya aureta in bashi ba yadda yake nuna tsananin sonta………..
Kafin yarufe baki sai ga kaltum a tsaye a tsakaninsu yayin da aka hau kallon kallo tsakanin kaltum da mambela, kaltum da madina. Kaltum ta rushe da kuka, ta dora hannu aka tana rurawa.
Ta ce “mambela ya isa haka, bana son irin wannan, anty madina ce uwata, ubana a kasar nan ba dan ita ba da ban kawo yanxu ba, babu wahala da wulakancin da ban gani ba a baya ita ta kwace ni da tuni an kashe ni. Me yasa xaka dinga yi mata tsawa da ihu akan tana fadan ra’ayinta tasan abunda take hangowa wanda mu da dukka ni da kai ba xa mu hango ba. Mambela ba xan iya auren ka ba tunda ka fara yiwa mahaifiyata haka.”
Sai mambela ya sulale kasa ya durkusa yana rokar madina da kaltum afuwa.
Madina ta rushe da kuka ta jawo kaltum jikinta ta rungume ta, su dukka ukun kukan suke yi, har yin hakan ya jawo hankalin jama’a suka taho suna tambayarsu lafiya. Nan da nan kowannensu ya share hawaye, ya nuna babu komai.
Sai madina ta mike tace dasu, su biyo ta suka yi tafiya mai nisa xuwa bakin ruwa can gefen da babu kowa sai yashi turmus da iska mai tafe da feshin ruwa mai sanyi yake firfita su. Suka samu inuwa suka xauna a kasa yayin da madina ta saka su a tsakiya. Ta dubi mambela ta juya ta dubi kaltum sai hawaye ya sirnano mata daga idanunta, ta sa gefen mayafinta ta goge sai ta yi murmushi.
Ta ce “mambela xan baka labarina wanda nake ganin ban ji dadin abunda ya faru da niba shi yasa bana son irinsa ya faru da rayuwar kaltum.”
Sai ta gyara xama ta bawa mambela tarihin rayuwarta kacokan kamar yadda ta bawa kaltum a baya, ta bashi labarin haduwarta da tasi’u, xamansu, har xuwa rabuwarsu. Sannan ta bashi labarin Abba da yadda ajalinsa ya xo.
Ta nuna masa irin halin da ta shiga da irin wulakance wulakancen da ta fuskanta a garin da ba’a san asalinta ba, ta nuna masa irin gorin da korar Karen da ake yi mata don an san bata san kowa ba kuma bata da kowa. Ta nuna masa irin tsananin son da tasi’u ya ya nuna mata amma da xama ya yi xama ya sake ta, ya kore ta alhalin ya fi kowa sanin bata da kowa a garin shi yasa bata son kaltum ta xama haka itama. Ta kuma nuna masa cewar ba xa ta so ya fadi halin da Abba ya shiga ba sanadiyar son kaltum, ba xata so ta dauke masa kaltum ba, ya rasa taba, amma ta amince ya bi kaltum kasarsu wajen iyayenta ya nemi aurenta idan sun amince su aura masa ita, su biyo su xo aga muhallinta; yin haka ba wahala ba ne a wajen Ubangiji.
Mambela ya sirnano da hawaye ya girgixa kai yace “abu ne mai wuya iyayen kaltum su yarda su su bani ita, ko sun amince alhaji adnan ba xai bari ba. Don in bi kaltum Nigeria nida iyayena ba wahala ba ne amma xai yi wahala su yarda in auri ‘yarsu in taho da ita alhali suna can suna neman ta ido a rufe hankalinsu xai tashi idan suka ji labarin cewar tana sudan ba’a saudiyya ba.”
Kaltum tayi shiru tana kallon mambela hawaye kadai yake kwarara tana sake gaskata abunda mambela yake fadi gaskiya ne cewar tabbas ko iyayenta sun amince ta auri mambela to alhaji adnan ba xai amince ba ko ba xai aure taba.
Madina taci gaba da lallashin , mambela amma fa tana nan akan bakanta na dole sai dai yabi kaltum Nigeria ba xai aureta anan ba. Yayin da kaltum a xuciyarta take sake tabbatarwa cewar ita kuwa sai dai a kai gawarta Nigeria amma ba xata koma ba don tafi jin dadin xamanta a nan akan a gaban iyayenta. Rugumutsi kenan yaya xa’ayi ken an , tunda kowa da nasa ra’asyin a cikin su ukun ?
A hka aka rabu ba tare da kowa ya san a wacce shawara aka tsaya ba.
Tun daga lokacin mambela ya shiga damuwa, walwalarsa ta ragu, fara’arsa ta disashe ya xama tamkar mutum mutmi gashi dai a xaune amma xuciyarsa tana tunanin yadda xa’a ayi ya auri kaltum.
Haka ko ya xo hira wajenta hirar bata wuce kaltum karki tafi kasarku ki bar niba, idan kika tafi ban san yadda xanyi in yi rayuwa ni kadai ba, ba ke. Bata bashi amsa ba, amm sai dai ta lankwabe kai tayi kamar xata yi kuka saboda itam bata san mafita ba. Kwanaki uku bata ga mambela ba sai taji labarin ashe bashi da lafiya sosai, ko kofar gida baya iya fitowa. Hankalinta yayi matukar tashi kana kallonta xaka tabbatar da a cikin damuwa take. Da yamma kaltum tayi jugum akan katifarta yayin da abincinta na rana na gefe bata iya ci da yawa ba, sai madina ta xo ta tsaya a kanta ta dubeta tayi dan murmushi yayin da itama kaltum tayi mata murmushin karfin hali.
Madina t ace “tashi ki shirya, kiyi kwalliya ki sami kawayenki biyu su raka ki garin ‘yan ADON DAWA gidan sarkinsu ki gaishe da marar lafiya yarima mambela sai hankalinki da nasa ya kwanta.”
Kaltum ta kwashe da dariya ta kifa kai akan filo, ta rufe fuska alamar kunya. Madina ta janyo hannuta.
Ta ce “wallahi sai kin je kunyar karya ce kike yi, gashi nan kin kasa cin abinci tun jiya da aka fada miki bashi da lafiya kika shiga damuwa. So kike ayi majinyata biyu keda shi? ”
Kaltum ta tashi tana farin ciki amma fa tana wayencen har cewa har cewa take yi “ni na mantama an ce mambela bashi da lafiya.”
Kaltum da kawayenta biyu amina da hansai ne suka ci ado suka nufi garin ADON DAWA . Tabbas kana hango ‘yan matan nan uku xaka san wacce tayi kama da amrayar yarima mambela. Amina ta saka riga fara (t-shirt) da siket baki, da shudin gyale. Yayin da hansai ta saka farar riga (t-shirt) da xanin atamfa, ta ci dammara da gyale kore. Kana ganinsu kasan wadannan basu taba shiga aji ba, a kasarsu ma ‘yan talla ne. kaltum kuwa baya ga kyakkyawar halittar da Allah Yayi mata ta iya tsara ado, saboda daman can tana da wayewa da ajinta ta xo.
Kaltum ta ci kawalliya da wasu riga da siket matsatsu farare, sai ta nada lufaya fara wacce akayi mata xanen fulawa baki, ta saka wani takalmi mai tsini baki duk mambela ne yakesaya mata. Kananan kitso ne a kanta yirin yirin wanda ya xubo goshinta yayinda fuskarta ta dauki hoda, jan baki, da kwalli rangadadai.
Kaltum ce a tsakiyar kawayenta suna tafe suna hira har suka isa garin ‘yan ADON DAWA fadar sarki suka nufa. Sai suka fara takawa a hankali sakamakon dandaxon samarin da suka hasko a kofar gidan suna xaxxaune akan wata katuwar tabarma.
Kaltum t ace da kawayenta su juya su koma gida ita ta fasa xuwa dubiyar, yayin dasu amina suka ce su je kawai dn suna so su shiga gidan sarki daman basu taba shiga ba. Ko ba’a fada musu ba daya daga cikin samarin ne ya hango su ya wafto sauran ya nuna musu su saisu kaga gaba daya sun waigo suna kallon su. Harda wasu da suke kwankwance sai suka mike xaune suna duban su. Suka daure suka ci gaba da tahowa amma fa suna nonnokewa.
Sai daya daga cikin samarin ya fada cikin yarensu y ace kalli ta tsakiyar ku gani yadda take da kyau . dama a kauyukan nan akwai hadaddiya haka?
Wannan ai itace ADON DAWA sai suka kwashe da dariya su duka.
Amma dasu kaltum suka kusn isowa karkashin bishuyar sai suka gane su waye yayin da suma samarin suka gane ashe kaltum ce.
Mambela na daya daga cikin samarin shine wanda yake kwance sai ya tashi ya xauna nan da nan farin ciki ya kama shi ya hango abar kaunarsa kaltum, yayin da ita ma ta ji sanyi a ranta da ta ganshi. Suna hada ido sai suka yiwa juna murmushi, mambelan da ake rikewa idan xai tashi, shine yayi xumbur ya tashi da kansa ya taho da sauri ya tare su tun kafin su karaso.
Ya fada cikin murna ‘yau sai kun shiga kun gaisa da sarki daman ina bashi labarin ki yana so ya ganki.”
Kamar kaltum ta nutse a cikin kasa haka taji nauyi da munyar dandaxon matan da suka dinga diddigowa daga dakunan su suna fitowa kallon amaryar mambela, sai buda ake ana yabon kyawunta da hankalinta. Don daukaka sai ga kaltum a gaban sarki tana kwasar gaisuwa. Sarki yasa hannu ya dafa kanta, ya dafa kan mambela yayi musu addu’ar fatan alkhairi sannan suka tashi suka fito yayin da aka saka bayin gidan suka rako su da kwaryar dabino daya da kwaryar nono biyu har kofar gidansu.
Mata su ka taru a tsakar gida suka kewaye su kaltum suka dinga bayar da labarin yadda suka isa gaban sarki. Yayin da sha’awa ta kama ta kama sauran mata kowacce tana cewa dama itace ta sami dan sarki mambela.
Sallamar wata bakuwa ceta katse hayaniyar da ake yi, suka waiwayo gaba daya suna duban ta.
Jama’a wace ce wannan matar? ,
daga ina ta xo? ,
wa take nema?
Domin jin amsoshin, se ku dada hakuri da biyo mu.
Naku masu son ku har kullum.
Typing:Sadin Maa
Posting:Dan Anty.ADON DAWA
LITTAFI NA 2 (PART 20)
.
Matar dai bakuwar fuska ce amma kuma bahaushiya ce, hausar katsina take yi. Bayan ta karaso tsakar gidan ne aka mika mata karamar kujera ta xauna yayin da ta yi jam’I ta gaishe da kowa. Sai ta fara gabatar da sunanta da kuma garinsu. Ta ce sunanta Hauwa’u ‘yar asalin garin ‘yan tumaki ne a jahar katsina, sanna ta ambaci sunan wata mata wai shatutuwa ta xo nema. Sunan matar da ta ambata babu ita a cikin gidan nan don haka suka tabbatar mata basu san taba. Sannan ta fara dogon kwatance sai can suka gae shatutuwar da take nufi it ace matar da ta mutu a hanya a wajen haihuwa, sauran ‘yan uwanta kuwa sun haye makka. Sai suka shaida mata shatutuwa ta mutu tun a hanya a garin haihuwa.
Sai ta fashe da kuka tana cewa “kanwata ce uwa daya uba daya. Ni ce na aika mata da kudi nace ta xo mu hadu a khartum mu tara kudi sai mu wuce makka, na ji shiru shiru bata karaso ba har yanxu kuma bama waya dasu tunda kauyen namu babu waya sai na xata so take ta haihu sannan xa ta xo. Shekaranjiya na hadu da ‘yar garin mu itama ta xo kwanan nan shine nake tambayarta shatutuwa sai tace ta dade da tahowa tuntuni. Aka ce in xo nan bur sudan akwai mutanenmu wadanda basu sami tafiya ba in duba ta tabbas tana cikin sudan bata da kudin da xata haura makka.”
Ta sake rushewa da kuka mai tsanani, su kuma suna ta lallashin ta.
Can ta tsagaita da kuka sai tasa hannunta a jaka ta xaro wani hoto a ambulan. Ta ce “ga hoton wata yarinya, ‘yan uwanta sun ce inyi musu cigiyarta a nan.”
Xaibu tasa hannu ta karba ta bude ta xaro hoton, yayin da kowaccensu ta xuro kai suna kallon hoton, saisu dukka suka bude baki suna mamaki yayin da kallo ya dawo kan kaltum. Gabanta ya fara kwaranya daga idanuwanta ta fara kiran “inna lillahi wa’inna ilaihi ra ji’un.”
Hauwa’u tace lafiya, me ya faru da yarinyar, kar dai itama ta mutu?
don an bani tabbacin batahaye ba tana bur sudan shine aka ce lallai lallai a kaita khartum wajen wata mata mai suna kalah itama ‘yar xangon daura ce, kalah ta dade a khartum. Kudin jirgin yarinyar da komai yana wajen ta., iyayenta sun turo da isasshen kudi suka ce lallai a kai musu ita. Shine kalah ta ji ina cewa xan taho tanan sai ta bani hoton nan in taho dashi in cigiyarta, ga sunan yarinyar nan a bayan hoton.” Madina ta karbi ta juya bayan ta karanta sai ga kaltum saleh baro baro a rubuce. Madina tace “Alhamdulillah, Allah Ya yankewa kaltum wahala don haka kaltum shiga daki kiyi marmaxa ki hado kayanki ku tafi.”
Yayin da kowa ya fara taya kaltum murna wasu kuwa suka fara koke koke dama ace suma nasu ‘yan uwan su kawo musu irin wannan agaji wajen aiko musu da kudin tafiya. Wasu kuma suka fara kukan rabuwa da kaltum saboda yarinya ce mai dadin xama.
Kaltum ta ja gefe ta cije takiyin gaba ta ki yin baya ta tsaya kawai tana karkarwar jiki yayin da ta rushe da kuka wanda saida hankalin kowa ya tashi.
Madina ma kukan take yi, ta mike da sauri ta shiga hadawa kaltum kayanta a buhunta kama daga kayanta na sakawa xuwa takalma, soson wanka, sabulu da sauransu. Ta xo ta ja hannun kaltum, sai kaltum ta makale hannu alamar ba xata tafi ba. Cikin fushi da kuka mai tsanani madina tadaka mata tsawa ta ce “ki xo ki wuce ku tafi kafin raina yabaci. Wa kika ajiye, ko wa kike dashi anan da xa kice baxa ki tafi ba?
Ban da larura ma me xai kawo ki cikin wannan rayuwar ta kangi da wulakanci a matsayinki na ‘yar boko?
Da tuni yanxu kina jami’a don haka dole ki tafi, fatana ki koma gaban iyayenki ni kuma in ji da kaina.”
Kaltum ta mika hannu ta karbi Jakarta ta wuce gaba yayin da sauran suka biyo bayanta, tafiya suke jiki sanyi kalau ana tayi mata fatan Allah kiye hanya. Mata da maxa a kofar gida suka fito suka tsaya crko carko ana kallon kaltum sai hawayen da yaketa firfitowa daga idanuwa da yawa daga cikinsu. Iya mairo da jikarta rakiya suka bata sako ta shaidawa ‘yan uwansu na xangon daura cewar suma su hado kudi su aiko musu su koma gida.
Hauwa’u ta dubi kaltum ta yi murmushi tace “banda yarinta keda xa’a kai ki gida cikin gata ina ke ina koke koke kuma?
Mu yi sauri mu tafi kada mu rasa jirgi, da magaruba yake tashi.
Kaltum ta kasa waiwayowa ta dubi jerin mutanen da suke daga mata hannu sai dai ta dora buhun kayanta aka tayi gaba. Madina da hauwa’u ne suke biye da ita a baya suka nufi khartum bahari anan ne xasu hau jirgin kasa.
Suna isa suka iske layin yakar tikiti saura mutane kadan saboda jirgin ya kusa cika. Nan da nan hauwa’u ta shiga layi ta yanko tikiti biyu ita daya, kaltum daya.
Madina ta rushe da kuka yayin da kuka ya ci karfin kaltum itama sai ta ajiye jakar kayanta a kasa ta rungume madina tana kuka. Ta ce anty, bana so in tafi ni kadai in barki a nan. Ki xo mu tafi tare xan fadawa iyayena su aiko da kudin jirginki ko mu shiga mota mu tafi kudin xai ishe mu.”
Madina ta girgixa kai ta sharce hawaye cikin kuka mai tsanani ta ke Magana t ace “ba xan je Nigeria ba kaltum, ba ni da kowa a Nigeria saboda kowa ya guje ni in yi rayuwata anan har lokacin da mutuwata xata xo ta dauke ni ki yi min fatan alkahiri kamar yadda nake yi miki ko bakya tare da ni, ki yafe min duk abunda nayi miki a rayuwa kamar yadda na yafe miki. Ina addu’a Allah Ya hadamu a gidan aljanna bayan mutuwarmu domin xai yi wuya mu sake haduwa har karshen rayuwarmu. Daga karshe ina yi miki nasiha da ki rike addininki, ki tsare kanki daga aikata xina har Allah Ya kawo miki mijin da xa ki aura na gari, kada ki manta da labarina da na baki ki koyi hakurin xaman aure da tattalin miji baya da ladabi da biyayya.
Ki yi min alkawari xa ki sakawa ‘yar ki sunana madina don karki manta da ni a rayuwa.”
Kuka mai tsanani ya ruftowa kaltum sai ta yi sauri ta duka ta dauki jakar kayanta suka nufi kofar shiga jirji saboda axalxalar da hauwa’u take yi mata wai suyi sauri su shiga jirgi su tafi kada a tafi a bar su.
Madina na tsaye tana kallon su yayin da kuka ya ci karfinta sai ta kwalla kiran sunan kaltum. Kaltum ta waiwayo da sauri sai ta tsaya cak su duka kuka suke yi. Madina tayi dan murmushi karfin hali.
Ta ce “kaltum, me xan cewa mambela? ”
Kaltum tayi shiru ta tsaya tana kallon madina kawai!”
Kaltum tayi shiru ta tsaya tana kallon madina kawai can tayi ajiyar xuciya yayin da hawaye xaxxafan hawaye ya xubo sharrrr daga idanuwanta, ta girgixa kai t ace “k ice masa na tafi gida.”
Sannan ta juya ta juya ta shiga jirgi, suka sami waje suka xauna, sun xauna ba dadewa sai aka rufe kofar jirgin aka kunna aka fara tafiya yayin da kuka marar kakkautawa ya ruftowa kaltum da madina. Sai da madina ta tabbatar jirgi ya tafi gida lokacin dare yayi. ‘yan gidan sun dade basu kwanta barci ba suna ta jajen rashin kaltum yayin da madina ta bude shafin kuka kai kace mutuwa kaltum din tayi. Taji hankalinta ya tashi ko sanda ta rabu da ‘ya’yanta bata ji irin wannan ciwon rabuwar ba kamar yadda take jin radadin xafin rabuwa da kaltum a yau. Tunda ta koma gida kalma daya ta kasa furtawa dan takaici sai aka kewaye ta ana bata baki da nasiha kala kala.
Sai washe gari su kaltum suka isa khartum da sassafe amma kaltum bata daina kuka ba. Kaltum taga kayatattun birane masu titi da gine ginen dogayen benaye. Ta shiga mamakin kyawun sudan ashesu a kauye suke ba a sudan ba, don inda suke babu ruwa, babu wuta, birni kuwa ga lantarki nan tarr, ga ruwa afanfuna bayan motoci tsala tsala da mata masu kyau a tituna suna wurwucew kamar su suka yi kansu. Duk da irin wannan kyakkawan gari da kaltum ta gani bai sata daina jin dankararriyar kunar da take ji a ranta ba. Tana tunanin madina da mambela, sai taji tafi son ta xauna dasu da ta koma gidansu. Ko sanda ta baro gida bata ji irin wannan kunar ran ba kamr yadda take ji a halin yanxu.
Sun isa wani gida kato a wata unguwa mai kyau, babban gida ne a lailaye da sumunti mai dauke da dakuna bijik da katon tsakar gida . hausa ne xalla a gidan kuma mata xalla, suna xaune a dakuna kasha kasha kowace da sana’arta wacce xata kula da kanta. A kalla a daki daya akwai mutane takwas xuwa goma da tabarmi a shinshinfide a kowace daki. Gida ne mai kyau na sumunti xalla sabanin irin nasu na bur sudan.
Tabbas kaltum taga fuskoki da yawa da ta sani sai dai ta manta a inda ta san su, suna shiga cikin gidan kafin su isa cikin dakin sai ta tambayi hauwa’u.
Ta ce “nan gidan haya ne? ”
Hauwa’u t ace “gidan Abdul kadir, dan asalin xangon daura ne ya kauro sudan da xama fiye da shekara talatin anan yake, ya xama dan kasa. Shine yayi arxiki yamaka gidan nan ya barwa baki nan bangarensa dana iyalinsa kuma suna can baya. Kyauta kowa yake xama musamman ‘yan xangon daura sun fi xama a nan kowacce ta xo nan garin sai ta nemi nan gidan ta xauna, har ana kiran gidan da suna gidan xango.”
Sai da suka dade suna jira sannan kalah ta dawo gida, ta tare su da murna gami da yiwa hauwa’u godiya marar adadi data nemo mata kaltum. Babu tantama duk wanda ya dubi hoton kaltum yaga fusakarta kuma axahiri ya san itace, ga kamanninta nan rangadadai. Hauwa’u ta danka kaltum a hannun kalah su kayi sallama ta koma garin da take don ita ba a khartum take xaune ba.
Kaltum ta sake dukawa ta gaisheda da kalah sannan ta gaisheda ‘yarta budurwa sa’ar kaltum din ce mai suna lami. Suka amsa mata cikin sakin fuska sannan kalah ta fara yi mata bayani cewar itama ‘yar xangon daura ce babarta kawar goggo fattu ce.
Kalah ta ci gaba da shaidawa kaltum t ace “an kamo goggo fattu daga makka yanxu haka tana xaune a xangon daura saida aka kamo ta ne kwanan nan sannan iyayenki suka san bkya tare da ita a makka, dan haka hankalinsu yayi tsananin tashi suka dinga tunanin yadda xa’ayi a samo ki. Sai Allah Ya sa musa agent din da yayi muku aikin bisa yana da lambata shi suka nemo suka tambayi yadda xa’ayi a same ki. Sai yace bashi da yadda xai yi ya samu wani a bur sudan saboda babu waya kwata kwata a kauyen amma yana da lambata sai dai ni a khartum nake, don haka suka kira ni a waya. Na ce musu gaskiya bana xuwa bur sudan amma idan sun tabbata kina bur sudan to su aiko min da kudin motarki da nawa na xuwa can sannan su aiko da kudin motarki sai in saka ki a mota har kano.
Akwai wani Alh Adnan dashi muke waya shine yace gara a sako ki a jirgi, to dai yanxu sun aiko da hotonki da kudin jirgin kasa na xuwa bur sudan, da ban sami lokaci ba, shine kawata hauwa’u t ace daman tana so ta je ta je ta nemo ‘yar uwarta shine na bata kudin ta je ta taho dake don haka sai ki xauna ki saurari sanda xasu turo da kudin mota ko jirgin xuwa kano sai in je har tasha in turaki.”
Kaltum tayi shiru a lungu tana sauraron abinda kalah take fadi mata, jikinta yayi sanyi kalau ta saddakar ta fawwalawa Allah komai tana fatan Allah Ya xaba mata abinda yafi alkhairi ba abunda ranta ya fi so ba.
Al’amarin mambela kuwa sai washe gari ya samilabarin an tafi da kaltum Nigeria, har cikin dakinsa wani abokinsa ya je ya kwatsa masa wannan mummunanlabarin. Duk da tsananin xaxxabin da ciwon kan da yake yi saida ya taso da kyar ya taho gidansu kaltum, kai tsaye ya fada tsakar cikin gidan ya kuwa ci sa’a ya iske madina a xaune tayi gum tayi tagumi itama da alama takaicin rashin kaltum ya dame ta. Yana ganinta sai ya fara hawaye itama ta fara xubar da wani xaxxafan hawaye mai radadi.
Ya fada cike da fargaba yace “da gaske an tafi da kaltum Nigeria? ”
Madina ta gyada kai tace “haka ne, kaltum ta tafi Nigeria, iyayenta ne suka aiko a tafi da ita…”
Bata rufe bakinta ba sai suka gay a yi juyi ya daki katakon dakin har saida dakunan su kayi girgixa.
Ya fada cikin fushi yace “tunda kaltum ta tafi daga garin nan, ko wacce sai ta tafi babu wacce xata sake xama a kasarmu.
Nan da nan kowa yayi carko carko suna duban mambela a tsorace, hankalinsu duk ya tashi kan ka ce kobo sai jikinsu ya dau makerketa. Ya dakwa duk wanda yayi kokari matso kusa dashi xasu bashi hakuri.
BABI NA GOMA
RAYUWAR KALTUM A KHARTUM
Kwanakin kaltum uku a khartum a lokacin ta ji rayuwa ta fara tsananta a gareta saboda tsananin wulakanci, dabakin halin da kalah da ‘yarta lami suke nuna mata . kalah ma sana’ar sayar da kosai take yi irin na madina. Kaltum taxage tana taya su aiki, itace mai wankin wake, itace ixa wuta da wanke wanke ashe ba’a son ransu take yi musu wannan hidimar ba, suna ciyar da ita ne kawai amma ba’a son ransu ba.
Suna wajen sayar da kosai da safe sai kalah ta dubi kaltum ta tsuke fuska t ace “kaltum ina fatan dai kin san yadda rayuwar sudan take, kowa ta kansa yake kin ma fi kowa sani tunda an ce bara ku ke yi a bur sudan. Dan haka ka’idar ciyar da bako kwanaki uku ne kin cika kwanaki uku yau, don haka ki fita ki nemi naki tunda har yanxu iyayenki basu bugo waya ba balle su turo da kudin jirgi.”
Hankalin kaltum ya tashi ta rasa abinda yake damunta, ta dubi gabas da yamma, kudu da arewa babu inda ta sani , bata san inda xata fara neman kudi ba don haka sai ta fara kuka ta fada cikin tashin hankali.
Ta ce “kalah, ina xan je in nemo abinci bayan ni bakuwa ce?
Ki taimaka min ki kira iyaye na a waya su turo da kudin jirgi ko mota sai in tafi………”
Kalah ta katse ta tun kafin ta rufe baki. Kin bani kudi ne da xaki ce in kira su a wayata, su baxa su kira niba sai ni, ashe ni na damu suga ‘yar su. Baxan kira ba in daisu ba xasu kira niba.
Lami ta jakunnen kaltum da karfi tace “ki bude kunnuwanki ki ji, ki sani anan khartum ba’a bara ba kamar a bur sudan ba, idan ki ka yi bara a nan kama ki xa’ayi a kai ki dajin mujawara a yarda ke, ke ba a nigeri ba ke ba a sudan ba har sai wahala ta kashe ki.”
Kaltum ta fashe da kuka ta juya ta koma gida ta shiga daki ta xauna akan buhun kayanta, tayi tagumi tayi kuka har kamar idanuwanta xasu fice. Ta yi takaici akan rabo tada aka yi da bur sudan aka kawo ta nan inda bata san kowa ba, babu mai taimakonta. Haka ta yini da yunwa ba abincin safe babu na rana saida daddare tana kallon kalah da ‘yarta suka dafa abincinsu suka juya mata baya suka ci saida suka rage saura suka bata ta ci ta sude kwano sannan ta iya samun dan barci.
Gari na wayewa bayan kaltum ta yi sallah sai ta shiga wankewa kalah wake, a fusace lami ta xo ta fuxge kwaryar da waken yake ciki ta sake maimaita mata cewar ba xasu iya ci gaba da ciyar da ita ba ta je ta nemi sana’arta. Kaltum ta koma gefe ta tsuguna tana kuka tana ganinsu suka dauki kayan suyar kosansu suka tafi wajen sayarwa.
Hantsi yayi cikinta kuwa ya dau rurin yunwa tana tunanin in da xata nufa gashi bata san kowa ba a garin sai taji an dafa kafadarta ta baya tana dagowa sai taga wata matashiyar budurwa ‘yar kusa da dakinsu ce mai suna fatsima.
Ta ce da kaltum”lafiya kike xaune kina kuka ke kadai? ”
Sai kaltum ta fara share hawaye tana murmushin karfin hali tayi sauri ta gyara xancen ta ce wai ciwon kai ne yake damun ta. Fatsima ta girgixa kai tace “babu wani ciwon kai da yake damunki mun san komai tun sanda kika xo muke tausaya miki saboda mun san xaki hadu da wulakanci a wajen kala da ‘yar ta saboda basu da kirki kowa ya san bakin halinsu ko kadan basu da mutunci gasu da rowa. Ki tashi muje kiyi irin sana’ar da muke yi.”
Kaltum ta mike jikinta a sanyaye xuciyarta cike da fargaba saboda bata san sana’ar da suke yi ba, haramtacciya ce ko halattaciya. Tafiya suke yi xugwi xugwi babu wanda yake Magana a cikinsu har suka isa bakin wata katuwar kasuwa wacce ake kira da suna makadi. Kasuwar markadi itace kasuwar da ake sauke danyan kaya mota mota irin su tattasai, tumatur, atarugu, dankali, salad, kabeji da dai sauransu. Sai suka tafi wajen wata katuwar bola in da ake jibge lalatattun kwanduna da gwalagwajin kayan miya ma’ana rubabbun kayan miyar da aka tsince aka xubar.
Sai taga fatsima ta samo Kwando ta tsugunna ta fara tsintar masu dan kyau tana Tarawa a cikin kwandon.
Kaltum ta tambaya cike da mamaki “me xa muyi dashi? ”
Fatsima tace “ke dai kawai ki samo Kwando ki xo ki fara tsintar masu kyau kina Tarawa.”
Kaltum ta aiwatar da abunda fatsima ta umurce ta su yi, suka tottona sosai da hannunsu ga wari bolar tana yi harda suka tabbatar sun tara da yawa sannan fatsima ta nuna mata fanfo suka je suka wanke tsaf, suka wanke kwandunan ma sannan tace su dauka aka su tafi kasuwar adare karamar kasuwa ce. Suna isa adare kuwa Allah Ya kawo wasu mata suka saya na kowannensu hamsin jine, ya isa su ci abincin yau ko babu nama. Farin ciki ya kama kaltum ta dinga yiwa fatsima godiya da ta nuna mata hanyar cin abinci badan ita ba, da batan san yadda xa ta yi ba.
Haka fatsima da kaltum suke yi kullum gari na wayewa saisu nufi markadi a gabansu ake sauke kwandunan danyan kaya daga mota. Suna tsaye ake ware rubabbun yayin da suma suke ware masu saukin rubar suna tarawa har sai sun tsince masu dan kyaun wani lokaci har su sami masu kyau sosai saisu wanke tas su je su sayar a adare.
Xuwan kaltum sai ya xamowa fatsima alkhairi domin a yanxu tafi da samun kudi, mai makon su siyar hamsin jine har metan jine suke yi saisu hada kudin su je su sayo danyen kaya su xo su dafa abinci lafiyayya harda kifi ko nama su ci su koshi idan da canji su kora da lemun kwalba.
Kawance ya kullu tsakanin kaltum da fatsima yayin da haushi da hassada ta kama kalah da ‘yar ta har suka daina yi mata Magana don bahaka suka soba, sun so kaltum ta rasa yadda xata yi tayi ta bin su, suna yi mata wulakanci. Ta kai ta kawo ko gaishe su kaltum tayi basa amsawa idan a taba kayansu ko buta ce sai su kwace su kyareta.
Xuwan kaltum khartum da sati uku da magaruba bayan ta idar da salla a daki sai taji muryar kalah da lami suna yiwa mutanen gidan sallama a daki daki da alama bulaguro xasu yi, nan da nan kaltum ta fito daga daki sai ta gansu niki niki da kayansu aka da alama dai kaura xasu yi. Hankalinta ya tashi ta fito a gigice ta tsaya tana kallonsu tana sauraron abinda xasu ce mata. Amma sai taga ko kallonta basu yi ba sun kada kai xasu fice, sai ta fashe da kuka ta bi su har kofar gida.
Ta ce kalah ina xaku je ku bar ni, ni kadai ban san kowa ba a nan sai ku?
Kala ta tabe baki sannan ta kai mata duka kaltum tayi sauri ta kauce.
Ta ce “ina ruwana ki mutu mana iyayenki ne suka ce a kawo ki khartu, ga khartum nan kiyi xama. Goyonki xanyi ko kuwa nono xan baki? ”
Kaltum ta fada cikin kuka “dan Allah ki kira su awaya, kice gani na xo su aiko da kudin mota in tafi, ko ki bani number su. Idan kika tafi basu san numer kowa ba sai taki ita kadai ce suke tunani xasu same ni.”
Kalah tace “ba xan bayar da lambar ba, idan kina da karfi ki xo ki kwata.”
Ta ja hannun ‘yarta lami suka yi tafiyar su, lami tana ta xagin kaltum.
Kaltum ta rushe da kuka ta shiga tsakar gida tana rusawa, kukan kaltum ya sa kowacce ta fito a gigice suka hau tambayarta me yake faruwa?
Tana kuka tana Magana t ace “kalah ceta tafi ta bar ni alhali ban san kowa ba a nan sai a bur sudan ni kuma bani da kudin da xan koma bur sudan wajen wadanda na saba.”
Gaje ta yi salati ta salance t ace “af ke ce kaltum wacce iyayenki suka aiko da kudin jirgin ki suka ce a saka ki a jirgi ki tafi Nigeria? ”
Kaltum tace “kaltum t ace “kala tace basu turo kudin jirgin ba ammam dai sun ce mata xasu turo.”
Gaje tace a’a sun turo mata kudin jirgin kasa na xuwanta da dawowarku daga bur sudan sannan suka turo mata kudin jirginki har xuwa kano. Sannan itama kalah suka bata kudi mai yawa ladan dauko ki. A gabana dan aiken ya bata kudin da hotanki, sai dai in duka kudaden ta hada xata haye don yanxu haka makka xasu tafi fitar nan da suka yi ta barauniyar hanya ake shiga kwale kwale cikin dare sai a tsallaka ruwa a shiga jidda.”
Sai jama’ar wajen suka fara Allah wadai da cin amanar da kalah tayi, suna tausayawa kaltum
Kaltum ta rushe da kuka yayin da ta tsugunna tana ihu ta rasa yadda xa tayi da ranta gashi bata da lambar wayar iyayenta balle su san kudin da suka turo bai isa gareta ba balle su turo mata wani. Ita ba a bur sudan ba, ita ba a Nigeria ba, gata a khartum bata san kowa ba kuma bata da komai……..
Nan xa mu tsaya, se mun sake haduwa a ADON DAWA NA 3
Shin yaya rayuwar kaltum xata kasance a Khartoum?
Shin wane hali iyayen kaltum xasu shiga idan suka rasa kalah a waya kuma basu ga kaltum ba, alhalin sun turo mata da isasshen kudin jirgi?
Shin wane hali mambela xai kasance daya sami labarin tafiyar kaltum alahli yana tsananin sonta, xai kori bakin gidan su madina ko xai hakura ya kyale su?
Shin yaya rayuwar madina xata kasance, a bur sudan xata dauwama ne har karshen rayuwarta, ko kuwa xata samu ta haura makka, ko dai xata canja shawara ta dawo Nigeria wajen yaranta kamar yadda ta ji bata jin dadin xuciyarta saboda tafiyar kaltum?
Shin yaya rayuwar kalah da ‘yar ta xasu kasance a makka, xasu samu su haura ko a'a?
Duk amsoshin tambayar nan suna nan tafe a ADON DAWA 3.
.
Sadin Maa.ADON DAWA 21
.
LITTAFI NA UKU
.
Jama ar gida suka tashi kaltum tsaye da kyar daga durkuson datayi tana kuka takaraji bata kaunar taci gaba da rayuwa gara ace bata raye zaifiye mata alkhairi .tafi kaunar takoma bur sudan wejan madina da mambela akan takoma nigeriya wajen iyayenta taje ta kwanta akan figeggiyar tabarmarta kukan ma yadaina fita sai ajiyar zuciya takeyi saboda tsananin tafarfasar da zuciyanta takeyi, tsanani yayi tsanani yayinda damuwa tarufi tsananin yunwa da takeji idan kanta yajuya saitaji hankalinta yagushe tamkar ba a duniya takeba
fiye da awowi uku tana kwance cikin halin tunani me kunshe da bakin ciki Saiji tayi ana zuba mata ruwa tafarka firgigit saita ga dandazon mata a tsaye akanta wasu nazuba mata ruwa yayinda wasu na yimata fifita dukda fankar da yake kadawa a saman silin,
mamaki yarufe kaltum ta dinga bin daya bayan daya tana fadi aranta lafiya kuwa meyake faruwa?
Sannu kaltum yaya jiki?
Allah ya sauwake kalamanda suke fitowa daga bakin ko waccensu .magajiya matarda tabarmar kaltum ke kusa da tata itace tadaga kaltum tsaye ta dowo da ita tabarmarta saboda na kaltum ya jike da ruwanda aka yayayyafa
ta kwantar da ita ta lullubeta da zani ita dai kaltum mamaki ne ya ke addabarta yayin da kwakwalwanta ta dinga kokarin tunano mata abunda yafaru takasa tunawa abinda zata iya tunawa shine lokacin da kala da lami suka tafi akace makkah zasu tafi sun kunshe kudin da iyayenta suka turo mata sun tafiya dasu .
sai hawaye yaci gaba da surnano mata daga idanuwanta aka fita da tabarma kultum aka tsane ruwan a waje,sannan kowaccensu ta juya ta nufi dakinta ,suna masu yiwa kaltum patan samun sauki .
Magajiya ta tura kofarsu tarufe,ta kashe fitila ta kuntsa ta tsakiyarsu hajiya zaliha ta kwanta duk en dakinne ,tabar wa kaltum tabarmanta .kafin kiftawar ido da BismiLlah gurnanin munshari yafara tashi a dakin nawanan nadukan na wancen ,hade da kyawawan mafarkai,
domin burin ko waccensu ta ganta haye makkah ta hada daurin gumama akanta tana talla tana kuma aikawa nageria ana
rabawa danginta suna tsalle suna murna ,suna cewa hajia wance tayi kudi a makkah.
yawanci da abunda ka kwanta a ranka shi kake mafarki ,don haka yawancinsu mafarkinda suka sunduma kenan .
ita kuwa kaltum a bangarenta bahaka bane da zarar ta ritse ido saitaga madina a idonta ,da ta bude saitaga kamar mambelane agabanta ,sai hawaye metarin yawa ya surnano daga idanuwanta,tayi doguwar ajiyan zuciya tana shesshekar kuka .
kaltum mehaka ?
Wata murya taji daga gefinta ,saita zabura ta waiga a tsorace .magajiya tagani a zaune duk da duhunda yake dakin
wannan amsa tagagari bakin kaltum.
magaji ta sake tambaya. "me yake damunki kike qoqarin kashe kanki?
Ke ba musulma ba ce?
Ba ki san kaddara ba, baki yarda da kaddara mai dadi da mara dadi ba daga ubangiji?
Idan an rabo ki da bur sudan ba a kai ki nigeria ba aka kawo ki khartum, ba sai ki hakura ki zauna ba har kiga yarda Allah zai yi dake ba. tunda Shi ya tsara miki haka, ya fi ki sanin dalilin yin hakan. mu
dakike zaune da mu ba mutane bane, kuraye ne,cinye ki zamu yi?
ki yi hakuri, ki fauwalawa Allah lamuranki, ki kai karan duk wanda ya zalunce ki gurinSa, shi zai yi miki sakayya. Allah ba ya zalunci, ba ya tare da mai zalunci, kuma yana bayan duk wanda aka zalunta. ki tashi kiyi alwala,kiyi sallar isha'i don bakiyi sallah ba ,kiyi nafilfili ki fadawa Allah halinda kike ciki ,don Yafiki sani.kikai karar kalah da yar ta wajen Sa,Yagaugauta yimiki sakayyar cutarki da sukayi ,domin addu'ar wanda aka zalunta karbabbabiyace.
Allah na gaugauta karbar addu'ar wanda aka zalunta,sannan ki koma gefe ki zubawa sarautar Allah ido ,kiga yadda zaiyi dasu nan gaba,
kaltum tayi shiru tana sauraron magajiya tana gaskata abunda take fadi saidai kash kaltum batada kwarin da zata iya tashi tayi sallar farillah ma,balle nafila,saboda tsananin yunwa datake addabarta .
magajiya ce ta sake magana tana umurtar kaltum data tashi tayi sallah .dole ce tasa kaltum yunkura ta tashi zaune ,saidataji dif.bata gani jiri .ta dade a zaune sannan ta dafa kasa ,game da cije baki tayunkura zata mike tsaye sai tayi taga taga zata fadi,saita koma jabar ta zauna .
magajiya tambayeta cike da kulawa kaltum,anya kuwa ba yunwa bace take damunki ?
Kaltum ta kada kai cikin jin nauyi tace yunwa nakeji aunty
Magajiya tace , Allah tsarki ,yarinya me kawaici badan jiri ya daukeki bazaki fada min ba kenan?
To tashi a hankali ki rarrafa ga tukunyanta can a bakin kofa bude da sauran shinkafa kici
farin ciki ya lullubeta zuciyar kaltum ta mike a hankali ta karasa bakin kofa ta laluba ta bude tunkunya ba ta yi wata wata bata tsundum hannu a cikin tukunyar,kasancewar shinkafar ba ta da yawa, ta fara kaiwa cikinta hakkinsa yayin da 'yayan hanjinta suka dauki ruri da kokawa,ni ban samu ba ni ban samu ba.
kowacce cuta da maganinta, cikin yan mintina ciwon jirin da ya ke damun kaltum ya ware,ta sami karfi mikewa tsaye ta bude kofa tafita bandaki .ruwa ya wadata a bandaki don haka ta bude famfo ta sharuwa ta koshi,ta dauro alwala tafito.atsaye ta kwana harsaida aka kira assalatu tana nafilfili tana mika kukanta zuwa ga mahaliccinta,tana me neman agaji da neman mafita akan mawuyacin halinda take ciki .tana mai neman Allah ya saka mata bisa cutarda kalah tayi mata ita abumda yafi damunta da aka rabota da wajen su Madina .
misalin karfe bakwai na safe fatsuma ce tashigo dakin su kaltum ta isketa ta a kudun dune akan tabarma ,bacci mai dadi ya kamata hade da maparkin abun kaunarta mambela, kasancewar kwanan da ta yi a tsaye tana sallah.
kaltum kaltum tashi mutafi " fatsuma take fada yayinda take girgiza kaltum ,ta firgigit ta tashi zaune ta murtsike ido.
fatsuma ta dube ta cike da mamaki ,sannan ta tambaya.haryanzu barci ki keyi , ko jikinne?
Kaltum ta girgiza kai,lafiyata kalau ai "ta mike game da tawo wata cukurkudaddiyar lafayarta ta lauye jikinta suka dunguma suka fita ,yayinda yan gida kakaf sun dunguma wajen neman abinci.tafiya suke zugui zugui fatsuma ce mai dan tabo hira,amma ta lura hankalin kaltum ba a wajenta yakeba .ta dubi kaltum tace ,kaltum wacece madina ?
Wanene mambela?
Nanda nan taji gabanta ya fadi ,yayinda ta waiwayo da sauri ta tsura wa fatsuma ido tana mamakin yadda fatsuma tayi mata wannan tambaya.
A ina tasan madina?
A ina taji sunan mambela?
fatsuma ta sake maimaitawa, tace, 'kin yi shiru baki bani amsaba'
kaltum ta tambaya, 'a ina ki kasan madina mambela?'
fatima tace, 'mimmikewa ki kayi kika kakkafe kina ta kiran sunan mambela da madina' sai kaltum ta fashe da kuka, ba tare da tasan amsar da zata bawa fatima ta tabbatar larurar aljanun nan ce ba su bar ta ba. Ta tuna irin hidima da kokarin da mambela yayi mata wajen nemo mata maganin aljanu, gashi yanzu bacin rai ya dawo da aljanun, ga mambela ba ya kusa kuma.
Ta rushe da kuka, ta yi ta rusawa suna tafe a hanya ana kallonsu.
Fatima ce ta dafa ta tana lallashinta tana ba ta hakuri, har suka karasa bakin bolar da suke tsintar kayan miya suka samo kwando suka tsugunna suna ta tsintar kayan miya masu rangwamen ruba, amma hawaye ne ya ke kwaranya shaf-shaf daga idanuwan kaltum.
Fatima ta dube ta, sai ta girgiza kai, saboda tausayin kaltum da ta ke ji, don a halin yanzu tafi tausayin kaltum fiye da karin kanta. Tabbas fatima abar tausayi ce,
saboda itama da kanwar mahaifiyarta sukazo da zummar zasu sallake makkah akazubesu anan.kanwar mahaifiyarta tace kowa yayi ta kansa ko lomar tuwo bata hadasu,kowa nasa yake nema.to amma ita fatsuma ta saba da khartum tana jin dadin rayuwarta tamkar a presidential bila take ,musamman ranarda taci sa'ar bolannan ta cika da rubabbun kayan miya tasamu ta cika kwandonta da kayan miya taje ta sayar ta sayo shinkafa ko taliya da kifi ,ko nama taje ta gida ta dafa tahado da lemon kwalba mai sanyi ,tabbas wannan ranar ta fiye mata ranar sallah.sabanin kaltum wacce ta tsinti kanta a Khartoum tamkar wacce akayi mata dabaibayi cikin rami ,
batajin dadin rayuwanta tarasa me yake yi mata dadi musamman daga jiya abinda kalah tamata .
idan kaltum ta tona bola ta tsinci kayan miya ,saita kifa kai a gwiwarta tayi kuka harta gaji,sannan ta cigaba da tsinta ta tuno cewar inbata tsinta ba babu ita babu cin abincin yau.
duk da haka bata tsinci abun kirki ba ko rabin kwando baiyi ba sabanin na fatsima wanda har yafi rabin kwando a haka suka tashi suka tafi famfo suka wanke suka nufi kasuwar adare.
sun dade suna zagaya kasuwar da kwado akan su suna tallata hajar su, da kyar suka samu aka saye bada wani kudin kirki ba ma,
Na fatsima da ya fi yawa yafi yawan kudi.
a hanya fatsima take tsuye kaltum akan abun da taja musu yau sun makara basu kai kayan miya da wuri ba har kowa ya gama siya asanadiyyar koke-koken data zauna tanayi tun dazu
kaltum batayi magana ba tafiya take zokai-zokai abun duniya ya ishe ta babu abunda tafi bege tafi bukata a zuciyarta irin ta rufe ido ta ganta a bur sudan ba haka bata kula irin gidan kusa da membela .
kwalla ta cika mata ido da ta tuno rayuwarta da yan gidansu na bur sudan ga kawayenta yadda suke wata yawarsu .bata damu rashin wuta da ruwa irin na bur sudan ba,haka bata kula da irin gidan katakon dasuke rayuwa ba ,bata duba yanzu a babban birni da take ba,ga wutar lantarki koda yaushe ba a daukewa ,fanka fil fil fil najuwa ,ga ruwa a famfuna yana kwaranya koda yaushe .
kaltum bata damu data koma nigeria ba don taga iyayenta da kannen ta ba,balle kuma alhaji adnan duk ta shafesu a cikin ranta basa lissafinta ta cire ran sake ganinsu a rayuwarta har abadh .
fatsuma ce da katse tunaninta da take yi tace zo muje musayo danwake muci tunda kudi bazai isa mu je mu auni shinkafa ba mu dafa
kaltum nabiye da ita har gaban me murhun me danwake.
baiwar Allah fatsuma ta karbi dan kudin dake hannun kaltum ta hada danata me yawan suka sayi danwaken chanjin suka sayi ruwan sanyi ,saboda yunwa a wajen suka tsugunna suke ci basu damu da mazanda ke zazzaune a wajenba haka basu damu da motocinda ke wurwucewa ba ana lekensu ana nuna su ,basu lura da kasar musulunci da shari'a sukeba
burinsu su warware hanjin cikinsu daya kanannade ya cure a gefe daya saboda yunwa.har wasu samari biyu da suka zo wucewa suka yada musu da magana cikin harshen Larabci.
kaltum data fi su jin larabci ta fi fahimtar abun da suka fada musu, don haka nan da nan yanayin fuskarta ya sauya, sanyin jiki ya far mata. ta bi su da kallo har suka kure.
samari biyu kyawawan fararen larabawa dayan ya dubi dayan,
sannan ya juya ya nuna masu su kaltum ya yamutse fuska ya ce, 'dubi wadannan 'yammatan a tsugunne a gefen titi, suna ciye-ciye saboda tsabar ba su san darajar da Allah ya yi musu ba ta 'ya'ya mata. rayuwa suke yi kamar dabbobi babu kamun kai'
dayan ya ce 'yan nigeria ne, ai zasu yi abun da ya fi haka ma. kai daga gani ba sai ka tambaya ba, duk haka suke rayuwa suna bata mana tarbiyyar kasa. ga su da nacin jaraba ko an kwashe su sai sun dawo ba za su zauna a kasar su ba.
ko ina dimbin arzikin kasarsu yake sukazo suka kunace mu suna cutarmu don duk yadda ka hada huldarka dasu sai sun zalunceka .
dayan yabashi ansa da cewa ,ehto baduka yan nigerian bane macuta sunada masu kirki ,kamun kai ,rikon addini da kyawawan halayya.
kaltum tayi ajiyar zuciya yayin da ta tsame hannunta tsam daga kwanon dan wake ta mike tsaye gami dacewa ,nakoshi ,ki cinye duka .
fatsuma cike da mamaki da tambayan ranta meyasa kaltum ta barma ta danwake har goma?
nan da nan ta halakasu ta tsuda kwanon ta kora ruwan sanyi suka kara gaba.
suna shiga sakar gida suka iske damdazon matan gidan kwansu da korkotansu a tsaye suna ta ce ce kuce .
hayaniya tayi yawa har ba zaka iya tsintar kalma daya ba kamar fada akeyi ko mayarda zance ,labari ne suke yi ko kuwa jajanta wani abu sukeyi wajunansu?
Allah shi Ya barwa kanSa sani.
fargaba gami da mummunar bugawar zuciyace ta fado wa kaltum asanda taga gaba daya matan sun yiwo kanta suna fadin ,yauwa ga kaltum din nan yar....
.
Sadin Maa.ADON DAWA 22
.
,yauwa ga kaltum din nan yar halak .
ta dafe kirji ta fada cikin,fargaba InnaLillahi wa'inna ilaihi Raji'un .me nayi ,lafiya?
Magajiya tafada cike tausayawa ,tace,sai kikaji abun da ya sami kalah da yar lami?
Kaltum tasake jin mummunar damuwa.tace meyasami kalah da lami?
Sai taga hawaye yana kwaranya daga idanuwan wasu daga cikin su ,saboda
tausayawa .kankace kwabo kaltum tafashe da kuka,yayinda jikinta ya dau karkarwa tana tambayarsu cikin matsananciyar damuwa mai hade da fargaba amsar da zasu bata .wai me yake faruwa ne ?
Ku fada mini.
magajiya ta sharce hawaye tace ,kalah da yarta lami ne suka yi hatsari a kwale kwale a
hanyarsu ta hayewa makkah ta barauniyar hanya jiya da tsakar dare,
kalah na asibiti rai ahannun Allah ,yayinda lami da sauran mata uku Allah Ya a
musu rasuwa kalmar innalillahi wa inna ilaihi
raji un ce ke fitowa daga harshen kaltum ,ta tsulale ta tsugunna yayinda ta hada kai da gwiwa tana rusa kuka .
magajiya tace kowa anan yasan hakkinkine yakama kalah da yarta kowa yasansu kalah suncuceki ,Allah baya Ya fe wa wani laifin
wani,sai kin yafe musu susami rahama kaltum kiyafewa lami wacce ta rigamu gidan gaskiya,kalah kuwa da bakinta take cewa anemo mata ke tanemi gafararki yanzuma daga asibiti muke bata anbaton kowa sai akiraki tanemi gafararki tasan ta cuceki mun duba duk inda zamu samoki tunda safe bamu gankiba
kaltum tafada nan da nan nayafe musu asabebe tace tashi muje asibitin taji da kunnenta ko hankalinta zai kwanta kaltum ta mike da sauri yayinda kowaccensu ta zaro gyalenta tafiya sukeyi fakam-fakam cikin sauri suna tayar da kura kai kace garken shanu aka bude aka korosu kiwo .
kowaccensu ka duba sai ka rantse daga kabari ta fito butu-butu wasu da goyo wasu da yayayyun 'yaya sunrike hannunsu mata fiye da ashirin ne suka taho duba kalah.
nan da nan ma aikatan suka taho da sauri suka tare bakin kofarda kalah ke kwance .
tambayarsu suke lafiya?
Asabe ce ta koro musu bayani ,wannan itace kaltum da kalah kecewa anemo tunda tsafe suka bar asabebe da kaltum suka shiga ragowawar aka tura keyarsu baya .akarkashin wata itaciya suka tarufi, takaici ya ishesu baza arasa tsaki da harare harareba harda yan tsirarun ashariya duk sun kutuntumawa ma'aikatan cikin harshen hausa tunda basaji ,
fargaba da kidimewane suka hadu a zuciyar kaltum dai dai lokacinda tayi ido hudu da kalah yanayin jikin kalah zai tayarwa da duk bil adama hankali musulmi harda wanda ba musulmiba saboda mugayen raunukan da ke jikinta kama daga kanta zuwa kafarta duk bandejine,
karkarwa kawai kaltum keyi yayinda taja burki tayi turus tana duban kalah.itama tana dubanta hawaye masu zafine ke kwaranya daga idanuwansu,
yayin da bakin kowaccensu ke karkarwa. kalah na kwance reran an nadeta da farin bandeji, wanda ya yi nashe-nashe da jini. kafafuwanta dukka biyun, da hannunta data dorin karaya ne. fuskarta luhu-luhu a kumbure idan ba an fada maka ita ba ce babu yadda zaka kalleta sau daya ka gane ta. da kyar kalah ta daga hannun ta fada cikin wata shamulalliyar murya marar kuzari, 'zo nan kaltum, zo wajena, kun ga yadda Allah ya yi da ni. na cuce ki, amma kaina na cuta' kaltum ta matso a hankali ta raba ta zauna a gefen gadon kalah tana mata duban tausayawa,hawayen dai bai tsagaita ba daga idanuwan kowaccensu, su ukun har da asabebe.
kalah ta kara da cewa,
'me za'a yi da halina, me za'a yi da zalunci, cin amana da damfara?
kaltum, na damfari iyayenki ,nacuce ki ,najawo kaina.shin me kudin nan dana cuce ku ya karamin yanzu?
mezamu fada wa Ubangijinmu nida lami ?
kuka me yawa ya ruftowa kalah takasa
cigaba da bayani asabebe nashafa hannunta tana bata hakuri tana cewa daina kuka kalah fuskarki duk dinkine kada ya sake kuburi yihakuri kaltum tariga tayafemuku,
kalah ta fara magana cikin nadama Allah ya yafemin ,kaltuma kiyafe min inkinje gida
kicewa alhaji adnan yayafemini domin naci amanarsa akwai wani Inuwa agent dan Daura ne wanda duk shiyakawomu nan shi alhaji adnan yaje yasamo har Daura ya tambayi inda kike inuwa agent yace ya dade baiyi wannan harkarba ta kawo mutane sudan saidai zaisa a binciko inda kike bansan inda
inuwa yasamo labarin bur sudan ba andai tabbatar masa kina cen saisuka shiga tunani yanda za ayi adaukoki da farko shida alhajinne suka shirya tahowa bur sudan dinsu taho dake sai gani kwasam nabugowa inuwa agent waya inaso yakaiwa 'yaya na wayarsa muyi magana dasu don basuda waya sai kuwa yaji dadi daganin numbata
daganan sai labari ya canja cewar intaikesu in dauko musu ke daga bur sudan in dauraki ajirgi kitafi kano nan da nan na kalallamesu da dadin baki danaji maganan kudin jirgi na
nunamusu ciwon 'ya mace na ' ya mace ne, d'a ai na kowa ne, na daukan musu alkawari zan kawo musu kaltum har gida kada ma su bata lokaci da kudin jirgi har na mutane biyu zuwa da dawowa ga wahalar zuwa bur sudan godiya iri iri da shi albarka suka dinga mini basusan abunda na kudurta azuciyata ba
mukayi lissafin kudin jirgin kasanda zai kaini bur sudan da wanda zamu dawo Khartoum ni dake da kudin abincinda za muci a hanya sannan da kudin jirgin sama nawa da naki daga Khartoum zuwa kano hatta da kudin taxi da zamu hau daga filin jirgi zuwa unguwarku saida ya lissafo ya aiko min .
Inuwa agent yasan inda suke tura kudi daga wapa zuwa nan khartum har gida suka bawa mai canjin adireshina da lambar waya ta saigashi yakawo min makuden kudi nan shaidan ya zugani naji bazan iya kashesu ta hanyarda aka umurceni ba abunda nake
nemane ido rufe shekara da shekaru muna fafutuka a sudan mun kasa hade kudi mu karasa saudiyyah .
da gudumawar shawarar 'yata lami na nade kudi na boye nayi zamana na manta da alkawarinda na dauka .yawan damuna da wayar da alhaji.adnan da inuwa agent ke yi ga wa' azi da gargadin da kawayena wadanda agabansu na karbi kudin ke yi shi yasa na canja shawara inje bur sudan in dauko kaltum insakata amota ta tafi kano ita kadai sauran kudin in rike, inasaka ranar tafiya bur sudan natsami mai tafiya Hauwa saina bata sako ta taho min dake zuwan ki khairtum naji
bazan iya cire zunzurutun wannan kudi ba in biya miki kudin motar zuwa nigeria ba don haka nacire numban wayata na yar yadda su inuwa agent ba za su sake samuna a waya ba balle su dame ni da tambaya, domin duk karairayin da nake shirga musu sun kare, ban san kuma abun da zan dinga fada musu ba.''
kalah ta fashe da kuka mai tsanani, yayin da kaltum ta ji kukan da ta ke yi ya kafe, takaici ya ishe ta, ta tsurawa kalah ido tana dubanta tana tuna irin wannan cin amana da son zuciya irin ta mutanenmu.
asabebe kuwa fadi ta ke,
''cafdijam! duniya ina zaki damu?
kalah, kin yi kuskure a rayuwarki. me kudin nan zai yi miki a rayuwa, ki ka sani idan da
kin kai musu 'yarsu su baki fiye da abun da suka turo miki tun da masu hali ne?''
kalah ta jima tana kuka kafin ta ci gaba da
magana. ta ce 'na yi niyyar yin biza ta kirki mu yanki tikiti mu hau jirgi mu shiga makkah yadda doka ta tsara sai kawayena suka bani shawarar kada in kashe kudina. ni da kawayena guda biyu da tshohuwa daya muka shirya tafiya makkah ta barauniyar hanya''
kaltum ta tambaya cike da neman karin
bayani, 'ta barauniyar hanya kamar ya ya?
kalah ta matse hawaye tace
eh ta barauniyar hanyace domin da tsakar dare ake fara tafiya alokacinda jami' an tsaro ke barci ko ince babu kowa a kogin sai ahaye saboda hatsarinda ke tattare da tafiyan da
rashin tabbas ba ama biyan me kwale kwalen harsai yasallakar da ku saboda adayan biyu kuke ko kuhaye ko akamaku, ba makkah zai tsallakar da ku bafa wasu kauyukane agefen ruwan suma en kauyen sana'ar da suleyi kenan kuna isowa cikin dare sai ku biya me kwale kwale kudinsa yacika aikinsa sukuma en kauyen sai su kwasheku cikin sanda da leke-leke sai su shigar daku cikin gidajensu cikin gidanma a cen kuryar daki karkashin gado zasu boyeku saboda jami'an tsaro na iya zuwa bincika ko akwai irinmu idan bakuyi sa a ba aka kamaku to tabbas daku da matafiya da masu gidan zaku fuskanci fushin hukuma ,
kasancewar akwai wasu daga cikin yan kauyen da suke kaiwa jami'an saro gulma idan ansami labari irin wannan sai suzo
sufara bincike gidajen daya bayan daya dan haka ake tsoron boyemu saidai wadanda suka tari aradu da ka ne basu daina ba
kaltum ta gyara zama taci gaba da kurawa kalah ido tanasonjin karshen labari .meya hada duk wannan labari da mummunan
hatsarinda suka samu harda rasa rayuka ?
takaici ya isheta da takejin hanyoyin karya doka da mutanen mu yan nigeria keyi adole sai sun shiga makkah alhali a makkah dimma a wulakance suke koda yaushe askarawa nabin su da gudu suna kamawa suna dawo dasu kasarsu suba ibadar suke samu suyi
ba sai neman kudi yaki halak yaki haram ana kyararsu ana korarsu, kaltum tafi bukatan ta dauwama a sudan da tashiga makkah saboda tasan azabarda tasha awancan karon
kalah ta katse mata tunani taci gaba da cewa kamar yadda aka mana bayanin yadda akeyi idan kukayi kwanaki kamar biyu a boye agidan kauyawan nan idan suka tabbatar yan saka ido sun daina zargin an boye mutane hankalin kowa baya kansu da tsakar dare sai su fito daku ta bayar gari sununa muku hanya ta inda zakubi ku bulla jidda sannan kubiyasu kudin aikinsu to da dabara da boye boye ga yar karan tafiya mai yawa har ku samu kushiga jidda shikenan hukuma batasan kun shigo ba daganan sai kowacce tayi ta kanta idan ajidda zaku zauna to idan mota zaku hau ku tafi makkah ko Madina to yarage naku,
asabebe tace ni abunda banganeba ku a ina
kakayi hatsari har kuka sami raunuka haka ne asudan ko a saudiyyah ?
Kalah ta girgiza kai yayinda ta zubo da hawaye daya cika mata ido tace a sudan abun ya samemu bamu kaiga hayewa ba bamu dade da fara tafiya ba a cikin kwale-kwalen mu biyar ne dukka matane sai matukin ne kadai na miji kamar yadda na fada muku da tsakar dare ake fara tafiya a lokacin da duk wata halitta ke barci a hankali yake tuka jirgin ko tari bai umurcemu muyi ba balle magana muna cikin tafiya kwasam
saiya hango haske daga nesa an haskemu da alamar babbar jirgine na ma'aikata sai mu kaji magana da lasifika ana umurtanmu
da mu tsaya a inda muke kasancewar yanada labarin irin mummunan hukunci da za ayi masa idan aka kamashi sai ya gigice ya fara azazzalarmu yana daka mana tsawa waimu fice masa daga jirgi ganin ya gigice sai muma muka fishi rudewa don haka mun manta a tsakiyar ruwa muke saisu dukansu harda lami suka daka salle cikin ruwa ba a kara ganinta ba saidai mutsu-mutsunsu tunda basu iya ruwaba suduka suka mutu nice naki fita ina ta ihu na dora hannu a kai kiran yata lami nake shiru lami bata amsa ba ta lume cikin ruwa bankara ganinta ba ashe bazan sake ganin ta ba har abada?
Su dukka ukun suka fashe da kuka a lokaci guda cikin kuka kalah taci gaba da cewa baidaina yimini tsawa infice masa daga jirgin kwale kwalensaba amma naki fita gudu yakeyi yana wuce kima musamman dayaga hasken fitilar nan ya nufo mu aguje arashin sani baisan ta inda ya nufo ba ashe wani gungumemen dutse yanufo a gaban ruwa jirginmu ya daki dutsen mu mu duka muka tarwatse mukayi sama muka fada cikin ruwa damu da jirgin namu ni kadai nayi rai gawarwaki biyar aka fitar daga cikin ruwa har da direban mu nice asume da wadannan raunukan
ina fatan nima zan mutu inje inhadu dasu lami don bani da anfanin zama aduniyannan sai kalah tarushe da kuka yayinda kaltum ta sunkuyar da idanuwanta da sauri kasa hawaye yana kwaranya saboda tausayinsu lokaci me tsawo babu wanda ya iya magana a cikinsu can kaltum ta dago da luhu-luhun
idanunta tadubi kalah tana magana cikin marainiyar murya tace kalah na yafe miki nayafewa lami Allah Ya yafe mana
gabaki dayan mu,
sai kalah ta rushe da kuka me karfi har saida
majinyatanda ke kwance asauran gadajen suka firgita yayinda ma'aikatan jinya suka yi tsawa suna cewa kalah ta rufe musu baki tana damun marasa lafiya tamkar xugata suke ai sai ta bude baki gaba daya tana rusa ihu magana take cikin harshen larabci yadda kowa zaiji tace na zalunci kaltum na zalunci
kaina akan abun duniya idan na mutu mezance wa Allah ?
ban mori kudin ba ko sisi ya watse aruwa na rasa yata lami na rasa lafiyata nibanje makka ba kuma sunana yabace a garin mu saboda inuwa agent zai fada wa dangina abun kunyarda nayi
hankalin kaltum da asabebe a tashe suka dinga rufe mata baki suna danneta don kada taci gaba da tonawa kanta asiri saboda abun ya zame mata tamkar tabin hankali daga karshe su ma su kaltum aka koresu waje yayinda aka dannawa kalah allurar barci a cikin karin ruwan da ake yimata tun tana magana har ta fara lunshe ido,
kaltum da asabebe suka fito wajen yan uwansu kallo daya suka taro su suna jero musu tambayoyi, kaltum ba ta iya magana ba
gefe dasu ta tsugunna ya yinda asabebe take kora musu bayanin abubuwan da basu sani ba muryar daya daga cikin ma'aikan jinya ce tace dasu kuje ku suyowa kalah abinci mai ruwa kamar lemo da shayi tunda aka kawo ta bataci komai ba nanfa aka hau kallo kallon aka rasa wacce zata ce wani abu
sai kowannensu tafara cewa ban fito da jaka ba a'a bubu canji da na bayar,
cikin marainiyar murya kaltum ke rokarsu tace dan Allah ku taimaka mata a suyo mata shayi tasha bakin ta ya bushe babu abinci banida kudi ni kuma,
da kyar uku daga cikin suka fitar da wahid jine dai dai salas jine kenan suka ba wa kaltum ta falfala bakin get ta siyo shayi kofi daya da gutsiren biredi ta shiga ta kai wa kalah. Ta iske ta a kwance barci na fisgarta sama-sama amma tana kokarin bude ido
kadan-kadan magana ta ke yi,amma ba a ji,tabbas ruwa ta ke cewa a bata.
kaltum ta daddage ta dago ta zauna zauna gami dayimata weji da filo a bayanta ta dan kishingide duk da karin ruwa da yake hannun ta ga karaya a daya hannun kaltum ta dinga tarfa mata ruwan shayi da cokali a bakinta duk da ta kasa tauna biredi amma ta shanye ruwan shayin tas,
a bandakin dake ciki kaltum tashiga taryo ruwan fomfo a kofi ta kawo ta dinga tarfa mata abaki sannan kalah taji dama-dama kaltum tana gyara mata kwanciyarta saikuwa
tarufe ido ta fara barci mai, nauyi kaltum ta lullube mata jiki da mayafinda ke gefemta sannan tajuya zata fita yayinda tayi arangama da ma'aikaciyar lafiya mai kula da kalah sai ta miko wa kaltum wata zungureriyan takarda ta magungunanda ake
bukatar da ruwanda za a dinga kara mata tana bukatar karin jini kije kukawo,
hankalin kaltum yatashi dataji batun kudi ko
sekon daya bata karaba tace wa matar wallahi banida kudi matar ta harareta tace daman ina kikaga kudi ?
Ki kaiwa iyayenki manya suje su sayo su kawo yanzu,
kaltum tajima a tsaye tana juya takardannan
sannan ta fara tafiya asanyaye ta isa inda har yanzu yan gidansu suke saye ta dubesu daya bayan daya ta fada cike da fargaba saboda shayin jine uku da kyar suka biya balle a ce an ambato irin wadannan makudan kudi tana ambaton musu jerin magungunan suka tabbatar kudin ne mai yawa sai ko waccensu ta fara hada yanata-yanata ma'ana kowaccensu ta zazzage zaninta ta juya ta kalli get din fita kaltum tayi narai-narai da ido kamar mai shirin yin kuka ta fada cikin damuwa ku taimakawa kalah ance bata da jini a jikinta kar ta mutu,
waye mai jini ajiki ?
ai dukkanmu nan idan aka tsaga mu baza a sami jinin kirki ba, shafa'u tafada dai-dai sanda ta fisgi hannun yayayyiyar yarta ta kara gaba ai sai duk sauran suka bi bayan shafau
magajiya ce ma dai ta dan tsaya tabawa kaltum shawara cewa ta taho suyi tafiyarsu kawai tama daina damun kanta kada ma
ta sake zuwa asibitin balle su ganta su tambayeta kudin magani idan sukaga shiru ba yan uwanta gwamnati ce zata dauki nauyinta koda kuwa anzo gida neman yan uwanta kada ta sake tace ta santa ma ko mutuwa tayi sun san yadda zasuyi su bunne ta,
kaltum ta kame a tsaye tana duban ganin
ikon Allah tana tambayar zuciyarta wai ina soyayyanda sukeyiwa kalah a da?
me dalilin rusa kukanda da su asabebe
keyi na tausayin kalah daman bana gaskiya bane ?
idan tausayin ta sukeji da gaske ai zasu siya mata magani donta warke inhar suna son ta rayu,
magajiya ta juya ta tafi da taga alamar kaltum bata da niyar binta sutafi kaltum tayi zaman ta akasa tana rike da doguwar takarda a hannu sai yanzu ta sake tuna madina wacce ta tsaya tsayindaka wajen kula da ita, da haka za a barta a yashe har sai ta zama mushe babu wacce zata taimaki wata da karfinta ba ma da kudinba?
hawaye ya kwaranyo daga idanuwan kaltum tahada kai da gwiwa tana kuka a bayyene take kiran sunan madina da mambela fadi take meyasa aka kawoni garin da wani baya
taimakon wani?
kaltum kaltum ?
muryar wata mace taji daga
wundon gadon da kalah ke kwance tayi farat ta hango ma'aikaciyar jinya a tsaye nanda nan ta mike aguje yayinda zuciyarta ta hau bugawa tana fargaban abunda zata shiga
ta iske tana karasawa kalah ta duba saitaga tana numfashi duk da idanuwanta arufe suke tayi ajiyar zuciya jin dadi tunda ba mutuwa tayiba AlhamduLillah, ma'aikaciyar jinya tadubi kaltum ta yatsune fuska tace kidubi jikin mahaifiyarki ki gyarata,
kaltum ta tambaya cike da rashin fahimta in gyarata kamar yaya?
tayi mata tsawa dakika shigo bakiji wariba?
to kashi tayi gaba daya dakin yakidime da wari kalah fa tana damun marasa lafiyanmu
mun fara gajiya wata ma'aikaciya dake bakin kofa ta toshe hancinta tace wai a tarkatasu mana sukoma kasarsu Nigeria suje cen su karanta, dayan nurse din ta bata amsa, da inafa ?
ai bazasu tafiba ko tsaga jikinsu akeyi da reza kamar baki san su wajen naciba ?
ai ita wannan ko en uwanta sunzo daukarta
baza a bari ta tafi ba saboda yansanda ne suka kawota takardan sammacinta daga kotu tana cikin file dinta da zarar ta warke
kotu zasu shiga ayi shari'a da ita saboda karya dokar da tayi wajen haurawa makkah ta barauniyar hanya,
nandai ma'aikata da leburori harda masu zaman jinya da majinyata suma suka tsoma bakinsu suna Allah wadai da irin rayuwanda yan Nigeria keyi musu akasa jikin kaltum yayi sanyi ta koma jikin gadon kalah ta tsaya tadade a tsaye tana kallonta batare da tasan yanda zatayiba har yanzu ma'aikatan tsawa suke mata wai tsayuwar me takeyi bazata fitar musu da warin nan dake damun su ba ?
kaltum taje gadonda ke kusa da kalah tace don Allah ku bani aron bokitinku idan nacire zani sai in wanke,
nan da nan suka zaburo sukace badai da
bokitinmu za'ayi wankin kashi ba, bazamu bayar ba.
ta sake matsawa gadon kusa dashi tace subata aron bokiti amsar da suka bata tafi ta wadancen muni cemata sukayi ta matsa tabasu waje ko su mareta tasake matsawa dayan gadon tace su taimaka mata da sadakar omo ko sabulu sai taje bakin
fomfo ta wanke shima sukace ta tafi tabasu waje baza subayarba
ranta yabaci yayinda ta fara jin wannan yanayin na ko a ayi rai tabbas da alama kaltum sai ta dawo da halin nan nata na baya na yar agulla sannan zata kwatowa kanta yanci da yancin kasarta ta cije baki ta gyada kai tajuya a fusace ta isa gadon da kalah ke kwance bata damu da ciwuka dake jikin kalah ba sai ta dagata ta fara goge mata jikinta gaba daya zanin jikin ta da mayafinda akafuta ya baci don haka ta warware lufayarta ta raba gida biyu ta tsaga ta daura rabin a jikinta yayinda ta lullubawa kalah rabinta ta cukuikuye kayan kashin a hannunta
ta fice a fusace wari ya turnuke dakin musamman idan ta zo giftawa sai kowa ya toshe hanci tafice daga dakin harta kai baranda waje sai taji an kwalla kiran sunan ta tajuya da sauri sai taga ma'aikaciyar daya ce tabiyota dauke da wani gumtun
sabulu ta wurga mata a wulakance game da cewa ga sabulu nan sai ki dauka kije ki wanke mana zanin gadonmu wani kallon
sama da kasa kaltum tayi mata ta kada kai tayi gaba ko kallon sabulun batayiba mamaki yakama ma'aikaciyar ta rike baki tana mamaki kaltum ta wuce zuwa wani bandaki dake tsakiyar asibiti zata shiga kenan saitaji an dafa bayanta ta juyo da sauri sai taga wata matace wacce gadonta ke kallon gadon
kalah me suna Aishah bata cikin wadanda suka hanata aron bokiti da sabulu amma tana zaune a dakin sanda ake maganar daga dukkan alamu kaltum ta bata tausayi shine ta biyota da bokiti da kullin omo tamikawa kaltum kaltum ta girgiza kai tace banaso kibar shi kawai Aishah tayi kasake da alama bata ji dadi ba dan kaltum bata karba ba tasake bin kaltum cikin bandaki tace ai fushi ma bai kamakiba tunda baki dashi,
kaltum ta juyo afusace tafada cike da takaici tace idan saida sabulunku da bokitinku yan dakinnan zanwanke zannuwan nan to gara asani gaba ace insude da harshena har sai sun fita,
mezanyi da sabulunku ko bokitinku ?
zanfita inyi bara in samo omo tunda daman munsaba sudan bakasarmu bane kunyi
gaskiya nacinda kuke ambato gaskiyane munzo mun nace muku a kasarku bamuda zuciya duk abunda ake yimana mun ki tafiya ku yi hakuri ba dukanmu bane ma....
.
Typing : Sadin Maa.
Posting : Dan Aunty.ADON DAWA 23
.
TRUE LIFE STORY
.
masu son zaman kasarkuba dayawanmu
kaddarace muma badason ran mu ba dolece,
a bakin bandaki aka tsatstsaya ana kallon su kaltum yayinda mamaki ya rufe yan kallo suna tambayar meyake faruwa ne meyakawo zancen zama akasar sudan?
kaltum ta wuce wajen fomfo batare da ta iya tsayawaba tabasu ansa ba Aisha ce ta tsaya tana bayanin abunda yafaru, gaba daya suka bawa kaltum gaskiya suka bawa ma'aikatan da yan dakin rashin gaskiya koba yan kasa bane ba ai musulmai ne, wulakanci bashi da dadi kuma yan sudan nawa ne a nigeria sunacin arziki abun duniya suke tarawa a Nigeria su dawo sudan suna zagawa,
akwai auratayyah asakaninsu dan haka
anzama daya,
aka cika bandaki ana bawa kaltum hakuri akanta karbi bokiti da omo tayi wanki taki karba tace ai ta rantse indai bokitin yan dakinne bazatayi anfani dashiba
saida wata tabata sabulu sannan ta karba na
aishane bazata karba ba tunda tana dakin tana ganin wulakancin da akeyi mata bata fitar da ita kunya ba sai daga baya zata biyota saboda kar yan dakin su tsaneta kome?
kaltum rigima da kyar ta karba sabulun ta wanke taje ta shanya igiyanda dake gaban dakinsu tashigo dakin tana kallon kowa daya bayan daya jira takeyi ayi magana tayi tsiwa babu mai iya hada ido da ita domin Aisha
takawo musu labarin abunda kaltum tafada abandaki
ta isa gadon kalah har yanxu shirkif take cikin barci, ta fada abayyane cikin harshen larabci kalah zantafi cikin gari insamo miki abunda zakici nabar amana agurin ALLAH domin Shi Ya halacci talaka Ya halacci me kudi ya halacci dan sudan ya halacci dan Nigeria
sai kowacce tayi kiri-kiri tana duban kaltum sunsan magana ta yasar musu ta wuce kere-kere ba mayafi kasancewar taraba mayafinta gida biyu ta rufa kalah
ma'aikatar daya ta dubi kaltum ta gyada kai
tace lalle yarinyarnan batada mutunci ashe.
kaltumta murguda baki ta fice yayinda suduka suka bita da kallo kaltum nashiga gidansu matan gidan sukayo kanta suna tambayan yaya jikin kalah an sayi magungunan kuwa?
Wannan tambayan nasu ta bata mata rai don haka bata basu amsar tambayarsu ba ta kada kai tayi daki,
buhun kayanta ta jawo ta bude ta daura wata lafayan tacire ta jikinta, yau zancen wanka babushi tafice ko wacce taja bakinta tayi shiru babu wacce ta sake tambayarta komai sunga ranta yabace kuma sunsan basu kyauta ba kallonta sukeyi harda lekenta akofar gida su ga inda zata nufa asibiti ko
kasuwa,
hanyar kasuwa ta nufa don haka suka gaskata neman kudi zataje
nan suka dasa kujerar gulma cewa banda
yarinta ma meyasa kaltum zata damu kanta akan kalah, matarda ta cuceta takawota Khartoum ta wulakantata ita da yarta , kaltum babu abunda basuyi mataba na wukanci
fatsumace ta hango kaltum ahanya yayinda tafito daga wani gida ta bullo da gudu ta iso inda kaltum ke tafiya ta dafa bayanta firgigit ta tsorata ta waigo da sauri sai taga fatsumace sukayi murmushi alokaci guda fatsuma tace yaya jikin kalah, kin san fa tsoron asibiti gareni shi yasa banbiku asibiti ba,
kaltum ta tabe baki tace bai kamaki bane dole dakinje,
fatsuma tace banda abunkima inake ina zuwa duba kalah duk irin muguntan da tayi miki mezakije kiyi mata koda mutuwa tayi ma ina ruwanki?
kaltum tayi murmushin karfin hali tace muna yiwa Allah laipi muroke Shi Ya yafemana meyasa bazan yafewa kalah ba?
yarta lami ta mutu meyasa bazan taimaketa ba tunda bata da kowa?
fatsuma ta tabe baki tace lallai kaltum dama haka kike da tausayi kamar lokacin Sahabbai?
kaltum tayi daria, saboda na hadu da lalurar rashin lafiya nima Madina ta taimakeni yayinda sauran suka gujeni shiyasa na kudiri niyyar taimakon duk wani mara lafiya acikinmu tunda muna kasar da ba namu ba, babu iyaye babu dangi,
fatsuma tayi ajiyar zuciya tace gaskiyane yanzu ina zakije ?
Kaltum tace kasuwa zanje na nemo wa kalah abinci kafin magariba fatsuma ta yamutse fuska tace mezaki sayar kisami kudi?
kaltum tace bara zanyi .
fatsuma ta dafe kirji tafada a bayyane cike da fargaba bara?
Bara fa kikace kaltum to Wallahi ba'a bara anan sai akamaki akaiki Chad ko maiduguri ayar, nan ba bur sudan bace babban birninsu ne ba a wannan rashin hankali kame akeyi.
kaltum tayi kasake tana tunani to in banyi bara to mezanyi na sami kudi tunda sana'ar tamu ta sassafene kawai muma sau daya samu muci abinci ko sau biyu saikuma wata goben....
fatsuma ta katse tunaninta tace yanzu nan da ganni daga cen gidan nafito nasami sabon aiki da yamma zandinga zuwa kuma kudi da abinci matar tace zata dinga bani kullum.
kaltum ta tambayeta cike da fara'a wanne
irin aikine ?
*fatsuma tayi murmushi tace gidan kunshi ne
da gyaran jiki (alewa da dilke )matane dankar suke taruwa ana bin layi ita kadaice don haka aiki yayi mata yawa take neman masu tayata kamar masu yi mata aikin gida da masu wanke wa mutane lalle da shafa mahallabiya nidai renon jaririyarta neke yi mata yanzu ma aikena tayi insayo mata mahallabiya akasuwa zo muje ki rakani saimuje gidan tare ki dinga tayani aiki idan kikaci sa'a kema saita daukeki aiki,
tafiya sukeyi fatsuma hira takeyiwa kaltum yayinda ita kuma addu'a kawai takeyi azuciyarta tana fatan Allah Ya taimaketa matarnan tadauketa aiki asirinta yarufu ,
akusa da mai sayar da mahallabiya akwai masu sayarda madarar turare anan ne kaltum tahadu da wani farin saurayi mesuna Abbas,
kallo daya ya wa kaltum yaji zuciyarsa taharba ta tsansar kaunanta ya dinga shisshige mata yana tsoma baki acinkin cinkinsu ko kallo bai isheta ba domin ita duk abunnan da akeyi hankalinta na gun aiki da tunanin halinda kalah ke ciki, saida Abbas
yamiko mata kwalbar turare sannan ma ta daga ido ta dubeshi ta sa hannu takarba batare datasan manufarsaba ta manta ana godiya idan anwa mutum kyauta ta kada kai tayi gaba fatsuma tace ta tsaya tana surutu dasu sannan can ta taho suka tafi a hanya take shaidawa kaltum cewa Abbas ne ya tsaryar da ita yana tambayarta gidansu wai kaltum yakeso,
kaltum ta tabe baki ta fada a yatsune au shine yabani turare ai danasan manufarsa da
bazan karba ba,
fatsuma ta zungureta tace ke wawuya ce ki so shi kawai yadinga zuwa zance yana kawo mana kudi, abinci,sutura da kayan dadi,
kaltum tace Allah Ya sawake na so wannan.
fatsuma ta harareta tace yafiki kyau fa, balarabene fa kobaki kare masa kallo bane?
kaltum tace bai dameni bafa ya kyaleni,
haka dai suke tautauna harsuka isa gidan me kunshi katafaren tsakar gidane aka malale da kafet hade da manyan fululluka mata birjik kowacce a kishingide an yarda mata kunshi a laulausan fatarta da alama mai kunshin ta bunkasa domin matan manyane duk a wajen daga dukkan alama motocinsu da direbobinsu a waje kofar gida suna jiran su,
kallonsu kawai kaltum keyi tana sha'awar baiwarda Allah Ya yi musu dama nice nasami
kwanciyan hankali da daula irin wannan, kaltum tafada azuciyarta dai-dai lokacinda ta durgushe gabansu tana kwasar gaisuwa.
fatima wannan fa?
ina kika samo yar kyakyawan kawa itama yar
nigeria ne ko yar mali?
Inji Jawahir me kunshi.
fasuma tayi dariya tace kawatace kasarmu daya gidanmu daya kaltum sunan ta,
gaba daya suka zubawa kaltum ido sai ta sunkuyar da kanta kasa ta fada cikin marainiyar murya hajiya kitaimake ni ki bani aiki mahaifiyata na asibiti akwance abinci na
fito nemar mata,
sai hawaye ya kewa kaltum gaba daya suka tausaya mata harda masu tayata kuka,
kankace kwabo sunfara bude jaka ana zaro
sabbabin kudi ana mika mata sadaka tamike tana bi tana karba tana tarawa ta durkushe a gabansu tayi godiya gami da kwawawan addu o I,
Jawahir takara mata da albishir da daga gobe tafara zuwa aiki ta dauketa aiki zata dinga biyan ta,
kaltum tayi sauri ta dubi fatsuma farin ciki ya lullubeta su kayi dariya lokaci daya sannan sukayi godiya tare,
kaltum tamike tsaye ta kara godiya tace zan koma asibiti wajenta gobe zan fara zuwa. Jawahir tayi murmushi,
Ta ce Allah Ya kaimu kiyi mata sannu Allah ya sauka ke.
kaltum ta amsa da amin ta fice tana murna yayinda tafara kidaya kudinta metan wa tamanin jine ma'ana dari biyu da tamanin saita kyalkwale da daria saboda farin ciki tashiga tunanin abunda zata sayawa kalah wanda zataci tana tafe tana tunani saita yanke shawara taje restourant ta sayo mata gasheshshiyar kazar da ake gasawa a inji mai laushi da tiriri, marar lafiya zaiji dadin taunawa don haka kai tsaye ta wuce al-amana resturant ta sayo wata dankwaleliyar kaza gashesshiya mai zafin gaske har tiriri takeyi ta ashara jine tashiga super market ta cefano kayan shayi na hamsin wa ashirin jine fal leda ta nupi asibiti ta ayyanawa a ranta cewar yan dakinsu na asibiti zasu sha mamaki idan sukaga ta tilowa kalah wadannan kayan dadi a gaban ta kamar ba yanzu suka gama mata wulakanci ba akan guntun sabulu saita yi murmushi ta gode wa Allah daya dubeta Ya turo mata kudi nan mai dimbin yawa cikin dan kankani lokaci tsaka nin la'asar da magrib, Allah Shine abun godiya kaltum ta fada abayyane tana shiga cikin get din asibiti saita nufi dakin da kalah ke kwance ta duba igiyar data yi shanya saitaga an kwashe zannuwan data shanya saita yi mamakin wayezai kwashe zannuwan nan bata tunani sace wa aka yi tafi zaton
bushewa suka yi aka kaimusu kan gadon kalah,
tashiga dakin teburin ma'aikata ta duba da ke daf da kofar shiga har yanzu masifaffun matan nan ne akan aiki ta dube su ta fada cikin gadara ina takardar maganin nan?
Kubani insayo sai taga sun turus da alama suna mamakin kalam kaltum,
can daya daga cikinsu tace kibarshi an bar matashi kyauta, kaltum ta wuce tana gyara jibgegiyar ledar da ta shako da kayan dadi yayinda duk gadon da tazo giftawa marasa lafiya da masu zaman jinyar su suka bita da kallo,
dadi yakama kaltum ta huce takaicin bakin cikin talaucin da ya addabesu , ita ma
yanzu zata jera kayan shayi akan lokarsu kamar yadda kowanne gado ake jerawa,
kallon ta suke ita ma tana baza ido tana dubansu duba irina ku kallah da kyau nice dai ta dazu wacce ba ta da guntun sabulun wanki,
yanzu Allah Ya hore mata abunda yafi sabulunku,
dadi ne yayiwa kaltum yawa hartayi batan kai
tarasa gadonda kalah ke kwance kokuwa idone yayi mata yawa tafiya take hartakai karshen dakin bataga gadon kalah ba saita juya ta kara tahowa tana baza ido dukka bangarori hagu da dama saigata abakin kofar fita mamaki marar misaltuwa zaka iya gani afuskarta ta fada abayyane ko ba dakin bane?
yayinda ta kara duban fuskokin yan dakin da ma'aikatan, hakika yan dakinne dan haka
daki ma shine babban abun tambaya ina gadon kalah?
Ina kalah ?
Shine kokarinda kaltum takeyi gashi babu wanda yace mata uffan.
.
Kai... 😊
Wannan part din ya min dadi sosai, irin yadda kaltum ta nuna GIRMAMAWA tare da jan AJIN ta a paskar en dakin su,
Girmama kai ba girman kai bane, ta burge ni sosai da ta kasance mai xucia kamar JAN NA MIJI, sai ta kara mugun shiga raina 😍....
Saura kadan kuga katin gayyatar auren mu 👫 ❤️
.
Sadiya Sadiq.
Abbas Abdulkadir Hada Hada.ADON DAWA 24
.
Babban abin tambaya shi ne, ina gadon kallah? Ina kallah ta ke? Shi ne kokarin da kaltum take yi, ga shi babu wacce tace mata uffan, Kallonta suke tamkar a talabijin take ba a zahiri ba. Ta koma ta dawo, se ta je kansu ta tsaya, tana musu duba irin na mamaki da Al'ajabi. Can taetambaya, "don Allah ina mai gadon nan, kallah? "
Caraf ta ji an dafa bayanta, sai ta yi farat ta juya a tunanin ta kallah xata gani da kafarta tana tafiya ko bsndaki ta shiga da kanta, juyawar ta, se ta ga masipappiyar ma'aikaciyar jinyar nan ce, mamaki ya kama kaltum matuka ta bude baki tana dubanta.
Matar ta fada cikin marainiyar murya, "kaltum ki yi hakuri Allah Ya yiwa kalah rasuwa dazu dagafitar ki,ko get baki kai ba. An leka da gudu ba a ganki ba.... "
Duk wannan dogon bayanin da matar ke yi bai shiga kunnen kaltum ba, kalmar da ta rike ita ce, Allah Ya yi wa kalah rasuwa.
Rim! Ka ke ji ledar hannunta a cike da gwangwani ta bare, yayin da lakar hannunta ta saki sai ga himilin kudin da takunso damke a hannunta sun watse a kasa. Ita kuwa sharaf tafado akan ma'aikaciyar sai suka tare ta. A kasa ta mike zunbut kamar mai suma, amma ba suma ba ce, tsabar tashin hankali ne ya tayar mata da mutanen boye jikinta masu naci, ashe ba su bar ta ba.
Kan ka ce kwabo an kinkime ta an dora ta akan wani gado an kira likita ya hau aikin ceto rayuwarta. Idanuwanta a kafe amma duk abun da ya soka mata sai ta fusge, kuma magana take barkatai ga tsananin karfi, sai ta yi tazubar damasu danne ta. Masana suka shaidawa likita ya daina wahalar da kansa, wannan ciwon ba layinsa ba ne, aljannu ne don haka aka gewaye ta ana tofa mata addu'a.
Sai bayan sallar isha'i ta farfado, ta tashi zaune daram zuciyarta cike da mamakin ganin yadda jama'a suka zagayeta, mata da maza, ta lura da an burbursina mata wasu abubuwa a kofar hancinta, sai ta tuno matsalar bugun aljannun da take da su a baya. Sannan ta gaskata su ne suka tashi, sai dai tambayar da take yiwa kanta, me ya tayar da aljannun? Tana tunaADON DAWA 25
.
TRUE LIFE STORY.
.
Tunanin matsananciyar rayuwar da ta tsinci kanta a ciki. Ba ta son khartum haka ba dadin xaman garin take jib a, dama-damarta dan ta hadu ds fatsima kawa mai kaunarta, mai karfafa mata gwiwa. Ba don fatsima bad a rayuwa ta kara yi wa kaltum xafi a khartum kasancewar BABU RUWAN WANI da rayuwar wani , babu taimako ko kadan a xaman gidan nan.
“ya na yi miki Magana”. Fatsima ta xunguri kaltum a lokacin da suke tsugunne a bakin katuwar bola suna tsintar kayan miya.
Kaltum ta daga idanuwanta da sauri ta dubi mutumin da ke tsaye a kanta, Abbas ta gani tsaye a kanta yana murmushi sanye da jallabiyarsa fara tas! Da rwaninsa fari kal irin na larabawan sudan. Murmushi ya sakar mata gami da cewa, “marhaba kaltum.”
Sai ta ji ranta ya dungunxuma y abaci, bakin cikin day a dankare xuciyarta ya sake karuwa. Kallon fuskarta kawai xaka yi ka tabbatar da labarin xuciyarta. Ya yi ta Magana ko daga idonta b ata yi ba balle tab a shi amsa. Da ya dame ta, sai ta yanke shawarar hakura da tsintar kayan miyar, gara kawai ta bar masa wajen. Ta kinkimi kwandonta aka, ta yi tafiyarta ko fatsima bat a yiwa sallama ba saboda ta fuskanci ita ke goyon bayansa. Sai da ta yi nisa sannan ta ji fatsima ta kwalla mata kira. Kaltum ta juyo sai tag a fatsima a guje tana murna.
Ta iso inda kaltum ke tsaye ta mika mata kudi, kaltum ta mika hannu ta karba a sanyaye, sannan ta tambaya cike da mamaki, “waye ya bani”!
Fatsima ta yi dariya ta xaro nata kudin t ace, “ashara jine ya bani, ke kuma ashirin jine y ace in kawo miki.”
Kaltum ta tabe baki sannan ta yi mata tambaya, bad an bata ta sani ba sai don ta ja mata kunne.
“waye ya ba mu kudin!”
Fatima tace, “Abbas mana”.
Kaltum ta ci gaba da Magana cikin fushi da cewar, Abbas ya fita harkarta, ba ita bas hi, ya sami dama ne daga wajen fatsima dab a xai ci gaba da nace mata ba.
Fatsima t ace, ita kuwa ko yanxu idan ya bas u kudi sai ta karbo musu sai dai idan ta bata ta xubar.
Fatsima ta ci gaba da yiwa kaltumtsiya tana cewa, “duk wnnan fadan da kike yi, ban ga kinyi wurgi da kudin ba a damke a hannun ki yake.”
Sai kaltum ta sake damke kudinta b a tare da ta kara cewa uffan ba. Ba ta son Abbas, amma tana da bukatar taimakonsa.
Fatsima ta dinga yi wa kaltum tsiya don t ace bat a son kudin, amma shiru kake ji bat ace komai ba. Suka isa famfo suka wanke kayan miya, sannan suka nufi kasuwar adare don su sayar. Yau bas u dmu da sai sun siyar da tsda ba, saboda aljihunsu da nauyi, kudin da Abbas ya bas u ya ishe su cin abincin yau hard a nama da lemo.
Da rana suka tafi gidan jawahir mai kunshi kamar yadda ta umurce su bayan sallar axahar xa su dinga xuwa saboda mai gidanta bai yarda ta fara xaman kunshi ba sai t agama aikin gida kakaf.
Jawahir tana murna da xuwan kaltum matuka, saboda kaltum ta iya kitso ashe, tabbas xata kwashi kudin kitso. Kaltum da fatsima suna taya ta aikin gida, ko rainon yaranta, suna tayata da wanke lalle idan ya yi da shafa mahallabiya, ko su hura mata garwashi idan xata yi wa mata dukkan.
Ba sa barin gidan jawahir sai bayan sallar isha’I, bayan tab a su abincin dare sun cika cikinsu, sun share mata gidanta tas! Sannan su nufi gida.
A halin yanxu sun rage tafiya markadi tsintar rubabbun kayan miya, saboda dan kudin da suke samu daga wajen jawahir. Babu laifi tana biyansu duk da dai aikin da suke shirga ya fi kudin aikin yawa, tana bas u abinci anda shi ne babbar matsalarsu. Kaltum mai farin jinni, ladabinta da kwaxon aikinta gami da fara’arta sun sa wadanda ta ke yi wa kitso da wankin lalle suna kaunarta, har suna yi mata kyauta akai-akai.
Allahu Akbar! Allah ma ji rokon bayinSa, Allah Yana taimakon duk wanda ya tashi ya neama, haka Yan a bawa duk wanda ya roke Shi. Babu talaka sai mai matacciyar xuciya. Allah ba Ya hana bawanSa lomar da xai kai bakinsa.
BABI NA GOMA SHA DAYA.
BUR SUDAN.
Rayuwar mambela da madina a bur sudan ta xama tamkar gayan tuwo ne marar miya cinsa haka babu dadi. Haka suke rayuwa amma xukatanu babu dadi saboda rashin kaltum din su.
Mambela ya fada ya sake maimaitawa, yyin day a lailayo rantsuwa yam aka a cikin bayanansa a dai dai lokacin day a tara ‘yan gidan su madina kakaf kofar gidan su da sanyin safiyar wannan rana. Yana Magana hawaye na yi masa tsartuwa, hakika daga jin kalamansa xaka tabbatar a cikin matsanancin fushi yake Magana da matukar damuwa. Tabbas babu maganar wasu a cikin lafaxansa, Magana yake cikin gadar da basu tabbacin xartar da hukunci mai tsanani akan duk wanda ya karya masa doka. Ba wai rokarsu yake das u bi abunda yake umartar suba, har ya fi son kada su bi don ya yi was an kura das u.
Ya dube su daya bayan daya ya kawar da ido gefe, yayin day a runtse ido ya xubar da hawayen day a cika masa ido, ya fada cikin harshen larabciwanda yake tunanin kowannen su xai gane, wanda bai gane sosai bad an uwansa xai fassara masa.
Ya ce, “yan Nigeria da niger a da ina sonku fiye da yadda nake son yan kasata sudan. Amma a ynxu bna son ganinku, ban ki in bude idona in ga an kwashe ku ba kada a bar mutum daya saboda xamanku a kusa da ni babban fami ne a cikin xuciyata.
A duk lokacin da nag a irin ku, ko na ji yarenku na hausa sai gabana ya yanke ya fadi, in ji xuciyata ta buga saboda kuna tuno min da KALTUM. Da xarar na fito da safe na hango ku kun fito da kayan sana’arkukamar haka, sai in ga kamar xan hango kaltum a tsugune a can tana wanke-wanke.”
Se ya nuna gefen da madina ke xaune, yayin da kuka ya kece masa, kuma ya kecewa madina.
(NIMA SE DA MAJINA YA KECE MIN)
Mambela ya cije leben ya ci gaba da cewa, “kun ci manata da ku ka bar kaltum ta tafi Nigeria, aka rasa mutum daya da ai tashi ya ruga ya xo ya sanar da ni halin da ake ciki, haka kuka kori yarinyar nan, ku kuma kuka mike kafa a kasarmu. To ba ku isa ba, yadda kaltum ta bar sudan sai kun bar sudan, yada na rasa farin cikin rayuwata, sai kun rasa farin ciki kuma.”
Hankalin kowannensu ya tashi, kana dudan idanuwansu xaka ga sun firfito waje don fargaba.
Kalmar “ma’alesh, ma’alesh ya mambela”. Suke Ambato.
Ma’ana kayi hakuri kai mambela. Sai Kalmar ta xame masa tamkar ashar suke danna masa saboda masu iya magan na cewa, da xarar an fara ba ka hakuri to tabbas an cuce ka.
Ya daka musu tsawa cikin fushi, y ace, su rufe masa bakin su, bay a bukatar bada hakurin su. Tsit kake ji ko tari babu wanda ya sake yi.
Ya share hawaye y ace, “ba ku da imani, ba ku da tausayi, ko wannenku yasan tsakanina da kaltum kun san babu abun da na fi so a duniya irin kaltum ba ni da Magana sai ta kaltum, haka ba ni da wurin xuwa sai ajen kaltum. Ina kwance ba ni da lafiya kaltum ta o ta duba ni, a ranar na kai ta wajen mai martaba ya yaba da hankalinta, tya amince min in aure ta. Mun fara shawarar yaya xamu je kasarsu saboda madina t ace, sai na je gaban iyayenta xan aure ta, tana barin gidan mu kuka tura keyrta ku ka kore ta.
An fada min tana kuka bata so ta tafi, madina kika hada mata kyat a tafi, to ku sani babu ku babu xaman lafiya a garin nan. Kaltum ta tafi ta bar ni, ban san ta inda xan fara nemo Nigeria ba, da garin da kaltum ta ke a Nigeria.
Ni mambela na yi alkawarin takura muku, kun daina walwala kamar yadda na daina, ciwo nake yi a kwance a ranar da kaltum ta xo duba ni, na warke da nag anta, daga lokacin da na ji an dauke ta a lokacin ciwona ya dawo har yau na kasa samun lafiya. To daga yau kun daina xaman lafiya don duk sai na kakkarya kafafuwanku daya bayan daya.”
Kiri-kiri suke yi da ido, yyayin da kowannensu yah au kammala sangalalinsa kada a fara ta kansa. Madina kuwa ta yi tsuru a gefe kanta a sunkuye a kasa, tasan kowanne hukunci xai xartar daga kanta xai fra, don haka ta fara tunanin inda ake siyar da sandar guragu, gara tun da wuri ta tanada.
Mambela ya ci gaba da Magana cikin kakkausar murya, y ace, “babu sana’ar sayar da komai a kofar gidan nan, haka kada inga kafarku a bakin kogi, wajen kamun kifi. Haka kada inga kafarku a kasuwarmu jim arab, kad a wata ta xo garinmu bara, sai na karya duk wanda ya saba wannan doka. Sannu a hankali idan yunwa tai she ku xaku tarkata ku tafi inda kuka fito, yadda kaltum ta tafi ta bar ni.”
Malam nura wani tsoho daga cikin su madina xai yi Magana, mambela ya dunkule hannu xai kai masa bugu, abokansa da ke tsaye a gefensa suka rike shi. Suka ja shi suka tafi, da kyar mambela yake daga kafarsa don tananin tashin hankali. Ya rasa akan wanda xai huce, takaicin rashin kaltum amma ya fi jin haushin madina wacce ta hana su su yi aure tuntuni. Sannan da yaradarta aka dauke masa kaltum dinsa.
Suka rushed a kuka suna kiran, sun shiga uku sun lalace, ya ya xa su yi su rayu idan ba sana’a, ba bara! Madina ta mike a fusace ta fara Magana cikin fushi.
Ta ce, ‘haba jama’a kamar ba musulmai ba, kun manta Allah ne mai rayawa, Shi ne mai kashewa!kun manta Shi Ya ke tsare mutum, Ya yi masa Katanga da duk wani mugu! Ko gexau ban yi bad a mambela ya hana mu sana’ar da xamu ci abinci, Allah da Ya haliccemu Shi xe fito mana da wata hanyr da xa mu ci abinci mu rayu. Jahilci ne ku dinga kiran shiga uku, ku kira Kalmar “inna lillahi wa’inna ilaihi raji’un Allah Xai yi mana jagora.
Ko me ya samu bawa mukaddari ne, shan ruwan kaltum ne yak are a bur sudan dole ta tafi, da shan ruwanta yak are a duniya da wayar gari xa a yi a tarar ta mutu ma karewar tafiya Nigeria.’
Sai suka ji xuciyar su ta yi dan sanyi, sannan kowannensu ya dinga kinkimar kayan siyarwarsa yana shiga gida don kada mambela ya xagayo ya iske su a kofar gida sana’ar yau dai ba a yi ba. Sai asarar da suka yi, saboda mai kosai ta yi markade, mai koko ta dama, haka mai danwake ta kwaba, har gara ma masu shayi da biredi ruwan xafi ne kadai da lipton suka dafa.
Kwanaki biyu haka su madina suke xaune babu mai sayar da komai, babu bara, babu xuwa kogi kamun kifi har sun fara jin jiki.
“mambela ya cuce mu, mugu marar imani”. Kalmomin da suke ta nanataw ken an, duk dakin da ka xo giftawa xaka dinga jiyowa. Suka ga Magana, xage xage a bayan fage ba xai yi musu magani ba sai suka shiga tunanin hanyar neman sulhu, domin komai da sulhu ya fi sauki.
Shawara day ace suka tsayar, maxa su hadu su yi kungiya su je su sami mai martaba sarkin ADON DAWA su kai kukan su, ba kuma karar mambela xa su ce sun kawo ba, a’a neman a rokar musu mambela ya taimaka ya janye takunkumin day a yi musu, ba laifin sub a ne da kaltum ta tafi suma bah aka suka so ba.
Haka aka yi said a suka tabbatar mambela ya fice, an tabbatar yana jim arab shi da abokansa suna shan jabna sannan suka dunguma suka tafi fada, da kyar dai aka yi musu iso, suka fadi gaban sarki suka yi gaisuwa cikin yaren ADON DAWA, sannan suka koro masa bayani cikin harshen larabci don shi suka fi iyawa. Suna gama bawa sarki labara sai ya bushed a dariya ya fada a bayyane har sau uku, “mambela! Mambela!! Mambela!!!”
Ya ce su tashi su tafi duk su fito da kayan sana’ar su, xa su iya xuwa bakin kogi, haka xa su iya xuwa jim arab ba damuwa. Babu abunda mambela xai yi musu, su kwantar da hankalinsu xai yi masa Magana har sai ya huce, daman kuma xafin rabuwa ne.
Godiya suke, addu’ar fatan alkhairi iri-iri suke jerowa sarki. Suka shiga gida suka fesawa mata bayani, yayin da buda da kidan kwarya ya gauraye gidan nan da nan aka sami masu taka rawa mata da maxa.
“ga mambela nan da tawagar san an xuwa”. Inji walidi ya rugo da gudu daga kofar gida.
Gudu da buga kafa a jikin katako kararaf ka ke ji ana karo, yayin da aka yi cilli da kwaryar kida. Wasu suka shige dakuna yayin da wasu bandaki suka cunkusa suka rufe kofa, wasu kuwa da suka gudu suka buya, ashe karya yake yi, xolayarsu yake. Dariya hard a faduwa yake yana fadi, “wasa ne ba mambela ba ne”.
Ran kowa y abaci suka firfito daga maboya suna masu jan Allah Ya isa, saboda tsorata su da yayi, har wasu da yawa sun karkace kafa da jinni.
Washe gari da safe aka rasa wanda xai fara fitar da kayan sana’arsa, kowa ya fito da kaya tsakar gida amma sun kasa karaswa kofar gida. Wannan ya leka ya dawo, wancan ma ta leka kofar gida ta dawo daga karshe aka sami xakakura daya ta fara firfita da kayanta, it ace madina, sannan sauran suka fara firfitar da kayansu su ma. Suna yi suna waige-waige da suka ji shiru sai suka saki jikinsu suka kwantar da hankalinsu, mambela ya hakura.
Kan ka ce kwabo jama’ar jange da ADON DAWA dauke da kwanukansu suka taho siyan abinci domin su ma kwana biyu rashin siyar da abincin ya shafe su.
“ga mambela nan!”. Sama’ila ya fada da karfi, yayin da yake rugawa cikin gida. Dogon tsaki suka yi yayin da ko waigawa bas u yi ba saboda sun san karya ne, tsorata su yake so yayi irin yadda walidi yayi musu jiya.
Dif! Kamar an jeho shi gaban su haka suka ga mambela da tawagarsa a tsaye a kansu. Xancen sama’ila gaskiya ne ashe ba wasa yake yi ba.
Madina bata yi karya ba, Kalmar innalillahi wa’inna ilaihi raji’una tana sanyaya xuciyar mugu ya xamanto mai tausayawa.
Yawancinsu Kalmar da ta xo bakinsu ken an a tare suka fada, kuma a bayyane. Wasu kuwa cewa suka yi, “ihu mun shiga uku, mun gat a kanmu”.
Suka yi wuki-wuki haka kake ganin idanuwansu a waje saboda tsorata.
Ya tsaya cak! Ya na duban rawar jikin da suke yi ba tare day a ce uffan ba.
Malam gali tsohon da yake sayar da goro ya kasa goronsa a fai-fai. Ya ce, “yaro ka yi hakuri, na samo maka labarin kaltum. Kaltum na sudan xata dawo kwanan nan”.
Mambela ya tuntsire da dariyar da bai shirya ba, ya sake kyakyacewa da dariya.
Ya ce, “baba, ka sayar da goronka ba xan hana ku sana’a ba, amma kaltum bat a sudan tana Nigeria. Ko xaka fada min a inda take idan tana sudan!”
Baba ya marairaice y ace, “fada na yi dan ka ji sanyi a ranka don mu ma mu sami sauki”.
Sai gaba daya suka rude da addu’a suna fadin “in Allah Ya yarda kaltum sai ta dawo. Kuma da yaradar Allah kaltum matarsa ce, duk inda take sai ta dawo.”
Mambela ya ji dadin addu’arsu, sai jikinsa ya yi sanyi, ya sunkuyar da kansa kasa yayin da kwalla ta cika masa ido. Ya dade a tsaye yana sauraron dadin bakinsu sai ya yi murmushi ya juya ya dubi madina wacce ke xaune ta sa kaskon kosanta a gaba ta kasa Magana ta kasa sakin kosan sai hawaye take xubarwa kawai. Ya juya ya dubi gefenta sai ya ga kamar xai ga kaltum a tsugunne a kusa da ita tana yi masa murmushin nan nata. Sai ya girgixa kai ya juya ya tafi, yayin da abokansa suka bi bayansa.
Doguwar ajiyar xuciya kake ji a jere a jere. Su madina na yi saboda farin ciki day a same su, sai kiran hamdala suke da godewa mambela.
A yammacin wannan ranar madina ta sami sammacin kira daga mambela cewar, ta same shi a bakin teku. Xuciyarta ta harba, amma sai ta yi addu’a ta xari gyalenta ta tafi ta yrada da cewa Allah xai kare ta, kuma mutum ba xai iya yi wa mutum abunda Allah bai kaddara xai same shiba.
Rayuwarta da mutuwarta duk suna hannun mahaliccinta. Labarin gixo dai bay a wuce na koki, ta san xancen bai wuce na kaltum ba. Ita kuwa duk inda gaskiya ta ke ita xata fada komai dacinta, ba xata fada masa karya ba don yaji dadi. Iyakar abunda ta sani shi xata fada, abun da xai yiwu shi xata fada masa. Haka idan kaltum matarsa ce xai aureta, idan ba matarsa ba ce duk inda ya kai ga mayatar sonta sai dai ya mutu ba xai aure tab a, kamar yadda Abba ya kasance. Har ya rasa rayuwar sa a dalilin damuwar so.
Tana tafe tana matse hawaye yayin da irin wannan kidimewar da mambeala yake yi suke tuno mata da yanayin da Abbanta ya shiga a lokacin da yake raye a sanadiyar so.
Madina ta isa bakin teku ta karasa inda mambela ke xaune turmus cikin yashi yana rike da wani dan karamin kara a hannunsa yana wasa das hi a cikin tashi tamkar yaro.
Ya dago ido ya dubi madina, sai tag a ya yi firgita domin hankalinta a tashe tamkar ta fi shi shiga tashin hanakali. Sai ya yi xumbur ya mike tsaye ya dub eta cike da damuwa ya tambaye ta cike da damuwa da kuma fargabar amsar da xata bas hi.
“madina lafiya!”
Sai ta rushed a kukan dab a ta shirya ba, jikin mambela ya dau rawa, yayi sauri ya warware rawaninsa ya shimfida mata. Ta xauna yayin da shima ya xauna a hankali yana fusakantarta. Ya dafe haba da hannayensa biyu yana dubanta xuciyarsa cike da mamaki da kma faragabar jin abun day a saka ta kuka daga kiranta.
“madina, me yasa kike kuka! Ki kwantar da hankalinki ba cutar da ke xan yi ba, tambayar ki kawai xan yi, kuma in nemi shawarar ki game da yadda xan yi in sami kaltum’. Mambela ya fada cikin sanyin murya.
Madina tad ago da jajayen idanuwanta ta dube shi xuciyarta cike da tausayi. Cikin kuka mai yawa ta fara Magana.
Ta ce, “mambela, ba kukan tsoron ko xaka cutar da ni nake yi ba, nasan ba xaka iya cutar da nib a saboda xuciyoyinmu suna son abu daya, ba wani abu ba ne illa kaltum.
Ina son kaltum, ina mata kaunar da nake jinta raina tamkar ‘yata shahida. Ina tausayin kaltum fiye da yadda nake tausayin kaina. Kana son kaltum na shaida son da kake so ta xama uwar ‘ya’yanka kana so ku kasance tare har sai mutuwa ta raba ku, ita ma na lura tana sonka haka.
Mambela ba xan so in xama sanadin raba wannan kyakkyawar soyayyar taku ba, haka ba xan yi wa xuciyata manakisa ba in raba tad a yarinyar da take kauna tamkar ‘yar da na Haifa ba saboda ba ni da kowa a nan, ita kadai nake gani inji dadi. A duk lokacin da nag a kana tayar da hankalin ka akan kaltum sai hankalina ya fin aka tashi, saboda kana tuno min da Abba wanda ya rasa rayuwarsa a sanadiyar soyayyar soyayya. Mambela na fi son ka bi abun a hankali kada ka halaka kanka akan rashin kaltum”.
Hawaye ya fara kwaranyowa daga idanuwansa, sai ya tambaye ta cikin sanyayyar murya, “madina waye Abba!”
Ta dade tana kuka kafin taiya fara ba shi labarinta. Ta bas hi labarin rayuwata tun daga farko har karshe kamar dai yadda tab a wa kaltum a baya.
Mambela ya dade yana duban madina ya kasa Magana saboda tsananin tausayinta, yayi nadamar takura musu da yayi, yayi nadamar laifinda ya dora mata a game da tafiyar kaltum. Ya tsunduma tsundum! Wajen tunanin yadda rayuwar Abba ta kare, ya kuma sake firgita akan yadda rayuwarsa xata kasance a nan gaba dan ya lura cewar soyayya ba abu b ace da xa’a ce maka ka rage ko ka kara, ko kuma ka daina.
Yana matukar iya kokarinsa wajen cire son kaltum da dannewa amma abu ya ci tura, kullum sonta karuwa yake a xuciyarsa. Ba ya addu’ar haka ta faru, amma daga dukkan alamu haka ne xai faru, yana ganin xai rasa ransa a hanyarsa ta xuwa nemo kaltum kamar yadda Abba ya rasa ransa a hanyar sat a xuwa garin su madina.
Madina c eta katse tunanin da yake yi t ace “abun da nake so da kai , ka yi hakuri, ka yi ta addu’a ka xubawa sarautar Allah ido, Ya yi muku hukunci akan abunda Yak e so.”
Mambela ya dub eta y ace, “ina so ki taimake ni kiyi min alfarma daya bad an kina so ba, sai don ki ceto rayuwata don gudun kada in rasa raina kamar Abba. Ki janye ra’ayin nan naki nab a xa ki kara komawa Nigeria ba har abada, saboda ni da kaltum xa ki janye, mu shirya ki rakani kano in nemo kaltum a jirgi ko a mita, duk wanka kike so.”
Tashin hankali marar musaltuwa xaka iya ganewa daga duban idanuwan madina. Ta ji kirjinta ya harba “bum!” saboda bata kaunar ta koma kano, bat a fatan ta sake yin ido hudu da duk wanda ya santa da.
Mambela ya sake nanatawa, ‘ki taimake ni madina mu tafi a satin nan. Don yau wata hudu da kwana hudu kenan da tafiyar kaltum kada mu dade aje ayi mata miji ko wannan Alh. Adnan din ya aure ta don daga labarinda ta bani na lura yana sonta, damuwar da yayi a kawota na san auren ta yake so ya yi.”
Madina ta ci gaba da kallon mambela tana mamakin yadda ya san labarin Alh. Adnan , tabbas kaltum na son shi da yawa tun da hart a saki jiki take yi masa hira duk wannan xurfin cikin nata.
Can ta nisa ta sunkuyar da kai kasa, don tambayar da xata yi masa ba xai yiwu ta iya hada ido das hi ba, saboda nauyinta, ta tabbatar ba xata yi masa dadi ba.
Ta ce, “misali idan ka je Nigeria aka nemo gidan su kaltum ka ci sa’a ka iske kaltum ka tambayi aurenta, iyayenta suka ki amincewa ko kuma ka je ka tarar har an ba wa Alh. Adnan ya riga ya aure ta. Yaya xaka yi, kuma me ne amfanin xuwanka!”
Kallo daya xaka yiwa mambela ka tabbatar xuciyarsa c eke tafasa saboda xaxxafan kalamanta. Ya kasa ba ta amsar tambayarta .
“mambela ina mai baka shawara ka yi hakuri ka kara hakuri, ka yi addu’a Allah Ya xaba muku abun day a fi alkhairi”. In ji madina.
Ya sunkuyar da kansa kasa saboda takaicin furucinta, don idan ya ci gaba da kallonta xuciya xata iya daukar say a yi mata diban karan mahaukaciya.
Madina ta yi ajiyar xuciya t ace, “a rayuwa babu wanda ya fi mahakurci cin riba, babu wanda ya fi mai tawakkali nasara, haka babu wanda ya fi mai yarda da kaddara morewa a nan gaba. Ka sake hakuri kuma ka tsananta addu’a…..”
Mambela ya katse tad a cewa, “shin xan mike kafa in dinga kallon gajimare ina jiran kaltum ta fado gabana! Ba sai na je nemanta ba Allah Xai dubi xuciya ta sannan Ya amsa addu’ata in nemota ba! Xaki raka ni kasar ku ko ba xaki raka nib a!”
(DARIYA, SU ‘DAN ANTY HO!)
Madina ta yi murmushin karfin hali, t ace, “mambela, ban san kaltum ba sai a mota, haka ban san daga inda ta bullo ba.”
Ya fada a fusace, “amma dai kasarku daya, kuma garin daya, kano ko! Idan muka je kano mun yi mai wuyar. Ni kadai xan iya xuwa kano, amman ban san kowa ba, ban san ko’ina ba, idan babu ke ina nasan hanyar da xan fito daga airport ko tasha! Gara da ke a kalla kin san garin kano, kin san sunan unguwar su kaltum. Kin iya yaren ‘yan garin yadda idan kika tambaya xa a nuna miki. Ban day arena sai larabci nake ji, wanda kun ce ba a larabci a kano sai hausa sai turanci, ni kuma ban iya ba. Shine taimakon da xa ki iya yi min a rayuwata madina.”
Ta girgixa kai ta sharce hawaye t ace, “mambela, ba xan yaudare ka ba, baxan boye maka ba, ko gawata ban a so a kai ta kano saboda abun kunyar da jama’a suka lika min. ka yi hakuri ba xan iya xuwa Nigeria ba, har abada.”
Mambeala ya ji tamkar ta dauko wuka ta kirba a kirjinsa. Ya dub eta, duba na takaici ya cije lebe hawaye yana xuba.
Ya ce, “babu wani taimako ko amfani da xa ki yi min a rayuwata wanda ya wuce wannan, kum kin ce ba xaki yi ba, alhali kina da halin yi min. madina ba kid a sauran amfani a wajena, ba kya kaunar kaltum, ba kya kaunata ki sani duk halin da na shiga ke ce sila. Bana so in sake ganinki a gabana, bana fatan mu sake xama ni da ke irin wanan tun dab a kid a niyyar ceto rayuwata.”
Madina ta fashe da kuka cikin mummunan tashin hankali, don jin kalaman mambela.”
Ya daga hannu ya dakatar da uta, yayin day a nuna mata hanyar gidansu, ma’ana, ta tashi ta tafi. Xata yi Magana ya daka mata tsawa y ace, ta yi shiru bay a bukatar bayananta ta tshi ta tafi kawai.
Madina ta mike cimak ta saka takalminta, t ace, ‘ka yafe min, ka yi min afuwa.”
Ya dago da jajayen idanuwansa ya dubeta y ace, “madina, ba xan yafe miki bat un da kika raba soyayyata da kaltum. Ba na kaunar duk wanda bay a so na tare da kaltum. Ba xan ragawa duk wanda ya raba ni da abar kaunata kaltum ba.”
Madina ta girgixa kai t ace, “Allah Yan a tare da mai gaskiya, Shi xai fitar da ni daga cikin wannan dabaibayi.”
Ta sharce hawaye ta wuce, kamar daga sama ta ji mambela ya kira sunanta. Ta waiwayo a hankali ta ganshi har yanxu a xaune a inda ta bar shi, ya jya mata baya kansa a sunkuye a kasa.
Ya ce, “da aka dauki kaltum daga nan ina aka ce xa a kaita!”
Madina t ace, “jirgin kasa suka hau suka tafi khartum babban birni.”
Ya ce, “khartum a ina, wacce unguwa!”
Madina t ace, ban taba xuwa khartum ba, ban san ko’ina ba, dan haka ban tambaya ba. Saboda bas hi da amfani in sani don an tabbatar min da xarar sun isa khartum ba xai wuce kwana biyu xasu yi ba xa su tafi Nigeria, don kudin jirginta da na ‘yan rakiyarta na hannu an turo musu daga nigeria.”
Mambela ya fada cikin fushi, “bana son bayanan ki, ya ishe ni haka, tafi kawai.”
Xungwi-xungwi ta kama hanyar gida ba tare da sake waiwayowa ba. Mambela yaji takaici a ransa har ya fin a kullum. Ya ji wani tsananin son kaltum ya kara mamaye xuciyarsa. Ya ji ya tsani madina, ya ji daman ace xa a wayi gari a ga gawar sa shi ya fi masa sauki. Ya yi kuka, ya dinga kwalla sunan kaltum shi kadai a bakin teku tamkar tababbe ga magaruba ta yi, duhu ya bayyana. Ya tuna ranar day a tare kaltum a dai-dai inda yake xaune, ranar da ta dinga ynakasa da wuka, kuma a ranar ta fara sonsa.
Bai bar wajen ba said a gari yayi duhu sosai. Ya isa gida ransa a bace. Sallah kadai yayi, ya rufe kansa a daki ya kwanta ba don yana jin barci ba, sai don kawai xuciyarsa ba xata iya jure surutun mutane. Xuciyarsa ta raunana, ji yake tamkar ta hadu da lahani tamkar xata buga.
Sarki ya dinga aike a tambayar masa, anya mambela lafiya ya kwanta da wuri! Ta wundo yake bas u amsa lafiyarsa kalau, barci yake ji.
Talatainin dare daf da asuba sannan barci ya dauke shi, sai ya gan shi tare da kaltum a mafarki suna hirar so da kauna. Farin cikin sa a mafarki bay a musaltuwa, amma day a farka ya ganshi shi kadai ba kaltum a xahiri, sai ya ji tamkar ya kurma ihu don takaici.
“me yasa kika tafi kika bar ni kaltum! Me yasa da aka xo daukarki ba ki rugo kin xo kin fada min mun tafi tare ba!”
Haka mambela yake fada a bayyane a cikin yarensa na adon dawa.
(DAN ANTY, SE YAYA KE NAN! KA HAKURA KAWAI A KAN KALTUM SE NA NEMAR MA WATA KAWAI, KAR A WAYI GARI MAMBELA KO ALH. ADNAN DAYAN SU YA YI NASARA AKAN AUREN TA HAWAN RUWA YA KAMA KA lol)
Typing: Sadin Maa.
Posting: Oga ‘Dan Anty.ninADON DAWA 26
.
TRUE LIFE STORY
.
haka mambela yake ta fada abayyane a cikin yarensa na ADON DAWA.
KHARTOUM
lokacinda mambela yake neman dan rakiya zuwa Nigeria wajen kaltum dinsa ya nema ya rasa badon babu kudin jirgiba ko guzirinda zai rike ba,
ita kuwa kaltum bata bukatar dan rakiyar da zai rakata bur sudan wajen mambela matsalarta shine kudin jirgin kasa take fafutukar tarawa abu yaci tura, duk abunda take samu baiwuci ta ci abinci dashiba sauran tasayi omon wanki da sabulun wanka da sauran su,
idan taci sa a ta tara kudi mai dan yawa tafara tarawa sai wani abu ya bullo mata wanda dole sai takashe kamar sayan magani idan batada lafiya ko idan takalminta silifas ya tsinsinke dole ta sayi wani ko idan rigunanta ko lufayanta sun yayyage dole takai dinki.
yau idan akace maka babu mai taimakonka
kodada loman tuwone komai kaiza nema da kanka to babu sauki, kaltum na aiki tukuru don neman abunda zatasa a yan hanjinta kokuma wanda zata iya shiga jama'a ba a toshe hanciba saboda wari ko datti bata hutawa saboda haka tarame tayi kurket tayi duhu rabonta da kitso tun na bur sudan saboda batada lokaci dakuma wanda zaiyi mata amma ita ta iya kitson har gida gida ake kiranta tanayi ana biyanta.
watan azumi ya kama kaltum bata hutawa yini takeyi tana neman abumda zasuyi buda baki saboda azumi.
yau babu masu zuwa gyaran jiki don haka jawahir ta sallamesu tace su daina zuwa sai a satin sallah sannan zasu dawo saboda haka sukafi mayar da hankalinsu wajen tsinta lemo da abarba sufere wajen rubar sukasa a faranti suje su sayar, kasancewar azumine ba acika sayan kayan miya ba akan da, anfi sayan kayan marnari .
sak almajirai ga yunwa ga kishiruwar azumi gasu sun yini a Kasuwa.
wataran suyi sa'a su sayar wataran su yini suna yawo ba a saya ba, dagaa lasa an ya ruba sai afasa saya daman dai masu rangwamen men kudi ne suke sayen irin wannan masu kudi basa dosar nakan farantin yan talla sai wankanku ajere akan tebur ko acikin firij.
ranarda rana takwabe musu kuwa babu mai saya idan akasha ruwa sai su zauna su shanye abunsu babu kudin cefane bare su dafa abincin buda baki da sahur don haka saisu zarzaya gidanda ake raba sadakar abinci da kwanukansu tun kafin dare yayi abincin sadakan yakare,
kunu dagurasa ko sinasirne sukebin dogon layi ana raba musu shizasuci kobasu koshiba su rage na sahur.
kaltum takanyi kuka cikin dare saboda masananciyar rayuwa da take ciki dumin
a bur sudan tawuce irin wannan rayuwarda ta
fatarar abinci. mambela yakara musu jari ita da madina suna sana'arsu kowannensu abinci ya wadaceshi
sun daina bara asatin da azumi zai kare satin
sallah kenan alokacin watan cinikin jawahir ta
bude ake tururuwan zuwa gyaran jiki da gyaran kai saboda kwalliyar sallah a wannan satin kaltum suka kaura gidan jawahir har kwana suke yi suna aiki saboda jama'a,
dogon layin babu masaka tsinke sakar gidan saboda mata a lokacin kudi yayi ta shigo musu baja-baja duk da jawahir ce mai amshewa,
kalilan da ciki take guntsira musu su ta murna.
wasa wasa kuwa suka tara kudi da yawa ana jibi sallah fatsuma ta shawarci kaltum suje
kasuwa su sayi lafaya da takalmi mai kyau suyi kwalliyar sallah kaltum tace ita tara kudi takeyi akwai abunda zatayi dashi bazatayi kwalliyar sallah ba.
fatsuma tayi tambayarta mezatayi da kudi da har bazata ki sayan sutura da sallah ba wacce ko almajirai suna wanka su canza kaya ballesuda suke kudi mai dama.
kaltum taki fada kuma taki saya fatsuma ce tashiga kasuwa tayi sayayyarta tsaf harda sarka da yan kunne
baya ga lafaya da takalmi coge chanjin kuma
taje kasuwa da ake sayar da wayan tafi da gidan ka (g.s.m)tsohowar waya gwabjejiya wacce aka daina yayinta ta saya aka makala mata sim card yadda zataji dadin waya da musa saurayinda take matukar kauna shima a kasuwar markadi yake dako su suke sauke kwandunan kayan miya daga mota zuwa cikin kasuwa.
ranar sallah kowa ya caba ado cas gwanin sha'awa duk wanda yaga fatsuma sai yayi mamakinta kamar ba fatsumar jiya bace mai
barkakkiyar riga da kanannandaddiyar lafaya
saboda rashin guga kanta duk gunji yau kuwa tayi tsaf bakinta har shekin dangwalin yaba yake.
zanen fuskarta wato bille da uku ukun bakinta sunyi radau saboda jar hoda da ta rarrangada ta dambara baki a bakinta da girarta kaikace tabarya ce masayin kwallin,
ta fito kwas kwas kwas daga dakinsu ta leko dakin su kaltum jama'ar gidansu suka ta mamaki kyawun datayi a yau suna tunanin inda ta sami kudi haka,
fatsuma ta dubi kaltum ta girgiza kai don takaicin kin daukar shawararta datayi datakiyi da tuni sunyi anko yayinda kaltum ta fito daga wanka tana shiryawa a tsaye akan buhun kayanta tsofofin riga da siket ta saka burguza burguza sai ta dauko lafayarta koriya itace mai rangwamen tsufa duk da tawanke tas tayi musu karin guga tana kwana akansu kallo daya zaka yi musu ka tabbatar sofaffi
ne don haka batayi kyauba surutu da gori babu wanda fatsuma bata yiwa kaltum ba akan taurin kan da tayi nakin yarda da shawararta.
kaltum bata damu ba shirinta take yi kawai ta linke dukkanin kayanta ta cusa abuhun ta hada bakin buhun ta daure tace da fatsuma zo muje waje na fada miki wata magana suka fito kofar gida suka tsaya kaltum ta dubi fuskar fatsuma taga yadda tayi wuri wuri tanaso taji labari saita tuntsire da dariya tace fatsuma yau zantashi daga garin nan zan kaura garinmu bur sudan
kaltum ta dafa kafadarta tace ki kwantar da
hankalinki zan dinga kawo miki ziyira akai akai ko kinaso kibini idan naje indawo in daukeki muje can mu zauna?
fatsuma ta girgiza kai tace bazan iya zama
da wadannan mutanen naku na ADON DAWA ba,
kaltum ta harareta tace ADON DAWA ba mutane bane ko ba musulmai bane?
fatsuma tace ADON DAWA saike nikuwa sai ADON BIRNI sukayi daria dukansu.
kaltum tace don bakisan suwaye ADON DAWA bane kike fadar haka musulman cikin su sunada kirki, kyauta, sadaka, zakka, sallah, azumi, tausayi, sunada ilimin addini,
masu kudi kuma kyawawa hanci zuwit..
fatsuma tace tunda kina son mambela fa ai dole kifadi haka nikuma bana son ADON DAWA,
kaltum tace ashe bakya sona tunda ni inason ADON DAWA, a kabila daga hausa sai ADON DAWA nafi so,
fatsuma tace inasonki tunda ke bahaushiyace amma fa banason ADON DAWA gashi kuwa sun janyeki zaki koma wajensu duk abunda nafada miki kinki ji sai kintafi din,
suka isa tashar da kafarsu duk da nisa basu damuba sun saba da tafiyar kafa basajin wahalarta.
suka jira har bayan la'asar jirgi kuwa sai bayan magarib zai tashi kaltum ta umurci
fatsuma tazauna acikin wata rumfa wacce aka tanadar don zaman matafiya gasu nan reras a zauzaune suna jiran jirgi,
zataje tayi fitsari idan ta gama zataje wajen ma'aikatan jirgi ta tambayesu adadin kudin tikiti da yadda ake sayansa,
fatsuma ta zauna da buhun kaya a gabanta tana duban kaltum hartayi nisa ta daina hangota tadade bata dawo ba sannan ta dawo tana zuwa fatsuma ta mike tsaye tace gida zata tafi saboda tafiyar mai nisa ne, ita kadai kada dare ya mata,
kaltum tayi tayi su sake zama suyi yar hira fatsuma taki tace gara ta tafi tayiwa kaltum fatan alkhairi da Allah kiyaye hanya tajuya ta tafi.
kaltum tayi kuri ita kadai taci gaba da kallon
masu wucewa kowa da dan uwansa yana hira amma bata damuba, zama kadanne ya rage mata a shiga jirgi tunda magrib ta kusa farin ciki mara misaltuwane ya bayyana azuciyarta ya huda ya fito ta fuskarta musamman da jirgi ya iso anfara bin layi don yankar tikiti kaltum cike da fara'a tabude bakin buhunta don dauko kullin ledar da ta daure kudinta zataje itama tabi layi ta yanki nata tikitin idan ta tuna jirgi zata shiga yanzu bur sudan tana wayar gari zata ganta kusa da mambela da Madina sai taji farin ciki ya lullubeta jitake kamar rufe ido ta bude idanuwanta ta ganta a bur sudan,
ta kasa kwatanto irin farin cikinda su mambela zasu shiga idan sun ganta ta luma hannu acikin kowane sako lungu da kusurwar buhun kayanta taji har yanzu bata jiyo kullen ledar kudinta ba nan da nan ta fara zazzakulo tsummokaran ciki da sauri tana zazzagawa tana ajewa akasa har buhunya zama wayam ba komai amma babu ledar kudin
don haka hankalinta yatashi matuka ta sake bin kowani zani daya bayan daya ko kudin yamakale ajiki amma shiru kakeji bai fadoba, ta tsake wargaza kayanta akasa kowanne siket riga zani ko lafaya saida ta shimfideshi akasa sanka-sanka babu ledar kudin ta,
saita rushe da kuka na takaici yayinda jama'a suka tabbatar ba lafiya ba tabbas akwai
matsala aka taru ana tambayarta bayani take cikin gigita da dinbun damuwa wasu sun yarda ta ita sun kuma tausaya mata wasu kuma bayanenta yamusu kama da tatsuniya gizo da koki ta mallece kawai domin sun saba ganin irin wadannan mutane wadanda dazarar talauci ya ishesu sai suzo tashar suna ihu suna neman taimako kudin mota suce nasu ya fadi idan aka hadamusu taimakon sai su zame su gudu daman ba motar zasu hauba damfarane kawai,
wake daya yake bata gari inji masu iya magana sun shafawa masu gaskiya kamar yanda suka shafawa kaltum kowa ya kalleta
saiya watsar yawuce abunsa ma'ana sunsaba ganin irinsu tuntuni,
kuka take haikam bayani take bilhakki rokon taimako take yi da duk karfin ta amma dakyar ta samu jine goma sha daya ta garzaya bakin wundon mai sayar da tikiti cikin kuka tayi masa bayani game da fayyace masa abunda take nema agareshi tace tana son ya
taimaketa yabata tikiti tatafi bursudan wajen yan uwanta batada kowa a Khartoum, ansace mata kudinta kakaf sai yanzune ma jama'a suka taimakamata da jine goma shadaya ya
taimaka ya karbi abunda take dashi idan jirgin nan yatafi ya barta batasan yanda zatayiba...
wani takaici yarufeshi tikitin jine dari biyu dahamsin ne zai bata a jine goma shadaya?
kallon tara saura kwata ya mata don haka basai yamata magana ba tasan abunda
ke ransa cikin fargaba ta sharce hawayenta ta sake neman wata alfarma cewar to ya bata rancen tikiti suna isa bur sudan yasawani ya bita gidansu ya karbi kudinsa..
cikin wata dankararriyar murya ya fada cike da takaici ke matsami daga jikin wundo kada ki sake dawowa, kika sake lekowa kika min zancen banza sai nasa yan sandan can sun kamaki, kaji mahaukaciya tikitin gwamnatin ne zan baki bashi ?
Sum sum sum kaltum tayi tabar jikin wundonsa batare da ta sake cewa komaiba daman itama tsausayine yasa ta tambayeshi don daga ganin bakar fuskar nan tasa baki kirin da jajayen idanuwansa tasan bazaiyi mutumci ba ga wani tulelen ciki da kiba da kyar yake juyi kuma tun nan kasa tsinke ka huda yace tush haka yake kamar katuwar balobolonda aka cika da iska saita daina
kuka ta sharce hawayenta da yayi mata face face a fuska batada sauran dabaru ko tunani bata da sauran wani tunani kuma ta cire burinta data kudira saitaje kayanta da ta watsar akasa tana kadewa tana linkewa tana zurawa a buhu jikin ta kalau data gama lenkewa saita koma gefe jikin wani dakali ta jingina da buhunta a gefe tana duban jama ar da Allah ya musu rahma wadanda ya yalwatasu da kudin sayan tikiti sai yanka suke suna shiga jirgi,
dukan uku uku kirjinta takeyi tamkar zata fashe...
.
Saady and Dan Aunty.ADON DAWA 27
.
TRUE LIFE STORY
.
ta fito waje yayinda takejin wani jiri na takaici na neman yakayarda ita kasa,
kuka yaki zuwa saboda abun yafi karfin kuka, don idan tashin hankali ya afku akayi kuka to akwai sauran rangwamen masipa, amma idan masifa yayi masifa to kukama takansa yake abun yafi karfinsa,
nasihar Madina ta tuna wacce a koda yaushe take shawarta ta yawaita addu'a tana neman tsari daga masifun rayuwa, wanda ko Allah Ya aiko da masifa zata zo da sauki kuma da maganinta ta shawarceta data yawaita karanta InnaLillahi wa ina ilaihi raju un
ako yaushe musamman sanda wani abu naki yafaru,
nan da nan kaltum ta cafko kalma InnaLillahi
wa inna ilaiyi raju un a harshenta tana fada
tanasake maimaitawa saita farajin wanan kululun nan daya shaketa awuya yafara lafawa, bugun da zuciyarta ke famanyi ta sausauta tanaji tana gani jirgi ya cika ya tashi yatafi ya barta, yayinda kuka ya kwace mata tana yi ta nanata kalmar InnaLillahi wa inna ilaihi raju'un ta dade a zaune anan har karfe
sha daya na dare.
saida wani dan sanda ya zagayo ya sake zagayowa ya tabbatar ba tada niyyar tashi daga wajen nan sannan ya tsaya ya tambayeta lafiya take zaune haryanzu cikin kuka?
tamasa bayani yace to ai gara ta tashi ta koma inda tafito saboda zamanta anan bai dace ba, ga dare ya fara nausawa gara takoma ta tara wani kudin zaifi mata sauki saita dawo ta yanka tikitin ta tafi baki alaikum don ba wanda zai dunkule wannan makudai kudin ya bata, don kowa takansa yake yi,
kaltum ta mike ta daura buhunta aka tana zubar da hawaye tafiya take amma dakyar take jefa kafarta ta isa gida zuciyarta tamkar tafashe taci sa'a duk yawancin ankwanta
saboda gajiyar sallah , ta sadada tashiga dakinsu ta ajiye kayanta a lungu tayi sallah ta kudundune alungu yayinda duk sanda ta rintse ido saita tayhango Madina da mambela sai ta fashe da kuka.
washegari da safe kaltum taci karo da yan gidan a lokacin da ta fito daga bandaki zatayi alwalar sallar asuba, mamaki mara misaltuwa zaka gani a fuskokinsu
musamman ma kawarta fatsuma,
lah kaltum baki tafi ba?
Meyasa baki tafiba ?
Amsa ya gagari bakin kaltum saitayi shiru tana tunanin abunda zata fada sai can tayi dan murmushi karfin hali tace fasawa nayi ai tun jiya da daddare na dawo,
kika fasa meyasa ?
Suka sake tambayarta ko amsa bata basuba taci gaba da alwalarta kawai,
fatsuma tayi dariya tace gaskiya naji dadi dakika fasa don har ina tunanin yanda zandinga yawo nikadai a garin nan gara muyi zamanmu anan, kaltum ga wuta ga ruwa ga titina ga wayar sadarwa ga samarin birni mezakiyi a bur sudan?
kince babu wuta baruwa babu network na waya gaku a zaune a makabarta duk kabarurruka a dakunanku na katako kamar yadda kika fada min...
sai ko wacce ta tsoma bakinta tanayiwa kaltum nasihar tayy zamanta anan kada ta koma kauye suma yan kauyen addu'a sukeyi sudawo birni.
ta mike sam ta shiga daki batare da tare da tayi musu magana ba, takaicinda ya isheta ya isheta kauyen nan da suke kushewa ita yafi mata birninnan dasuke muradi
kamar yadda suka saba kaltum da fatsuma suka bazama neman na abinci duk da sallah ce amma sunyi sammako suntafi kasuwar markadi , ahanya suna tafiya kaltum ta dubi fatsuma ta langwabar da kai gefe tace bakisan abunda ya sameni bako?
Fatsuma ta dubeta cike da mamaki tace bansaniba me yafaru?
Kaltum tayi ajiyar zuciya tace sace min wannan kudin nawa duka akayi ban gan su ba shiyasa bantafi ba .
fatsuma ta zabura ta dauki dogon salati game da dafe kirji ta tambaya cikin gigicewa yanzu wannan kudin an sace su dukka?
Fiye da jine dari bakwai nefa yanzu wa kike zargin ya dauke miki a dakinku ko atasha aka
dauke ?
Hawaye ya sirnano daga idanuwan kaltum
ta girgiza kai tace bansan inda aka daukeba ni dai nasan ko a daren shekaranjiya ana gobe zantafi kenan saida naga kudin harna sake kirgawa na daure na mayar asanda zamu tafi tasha dai ban duba ba wata kilan sanda nashiga wanka aka dauke,
fatsuma tace watakilan sanda kike kirgawa wata ta ganki kina tashi ta dauke,
nidai kina ganin sanda na dauki buhunki bansaka hannu acikiba agabanki na ajiye miki a tasha natafi, kuma niban hudaba nazakulo da Kinga buhunki huje....
kaltumta zabura tace nifa bance kekika daukanmin kudina bafa ko a mafarki nasan
baza ki min sataba,
suka cigaba dajajatawa har suka isa masana'antarsu wato babbar bolan da suke
sintar kayan miya suka fara gudanan da ayyukansu kamar kullun,
Abbas dai yanakan bakansa na naci dabin kaltum aduk inda take, a yau ma ya riskesu a inda yake tunanin zai samesu adaidai lokacin daya san zai riskosu , yakwada sallama cikin wata kamilalliyar murya mai sanyaya zuciya
lokaci guda suka daga kai don gani mai wannan sanyayyiyar murya sai sukaga fuskar Abbas cike da murmushi irin wannan murmushi fatsuma ta mayar masa gami da amsa sallamar itama a yayinda abangaren kaltum akasamu akasin haka, domin jitayi ranta ya baci nan da nan ta tsuke fuska takawar dakai gefe yasake tsungunawa kanta ya rafka sallama don dama ita yakewa sallama, kuma ita yakeso ta ansa ba fatsuma ba,
kaltum ta fusata ta mike afusace tafada cikin fushi Abbas karabu dani kakyaleni in sake saboda ni ina da mijina a bur sudan don haka kaje kanemi wata,
fatsuma tarike baki don mamaki game da
fargaban kada kaltum tajawo musu dan kudin da dan turaren da yake basu ya pasa,
fadi take ke kaltum me haka karya takeyi batada miji a bur sudan,kaltum taji tamkar ta zageshi,
kishi da tsantsar fusata suka damki zuciyarshi yacije lebe yace nikike fadawa wannan magana kizo kasarmu kinacin arzikinmu dan kin samu anasonki shine zaki zageni?
To zan nuna miki ko ni wanene, ya juya yatafi afusace.
fatsuma na kwala kiran sunan shi tana bashi hakuri yayinda kaltum ke tunzurashi tana cewa ya tafi din wazai tsoratar babu abunda
zai sameta sai alkhairi,
fatsuma ta fara yiwa kaltum fada itama dayake zuciyar akusane saita hargitsa suka hau hayaniya kamar zasu cinye kansu,
ranar dai kowa gabanta takama ba a tafi tallar tareba haka basu daura tukunya dayaba sai washegare fatsuma tabiyo wa kaltum suka hadu suka tafi tare kowaccensu ta huce sai hira suke suna wasa suna daria,
gidan jawahir mai kunshi suka fara zuwa don suji sanda zasu fara zuwa aiki tunda tace musu sai bayan sallah zasu dawo sai suka tarar ana zaman makokinta, Allah Ya mata rasuwa ranar biyu da sallah sukata kuka da ihu ana basu hakuri sannan suka yi shiru a gidan, suka nufi kasuwa jikinsu a sanyi kalau suna isa wajen sana'ar su sai suka iske labari yasha bamban don yau ana kwashe bolan da suke tsintar kayan miya yau a manya-manyan abun kwashe shara ana tarawa sai aje ajuye a motar kwashe shara,
suna isowa wasu ma'aikata masu uniform suka taso sukace oh kune daman masu tsintar rubabbun kayan miya ku wanke ku sayarwa mutane suci ko?
Don haka yanzu zamu wuce daku wajen hukuma a hukunta ku,
hankalinsu yatashi sai suka hau rokonsu afuwa da alkawarin sun daina daga yau, da kyar suna koke-koke aka kyalesu suka tafi akace kada su sake dawowa, daga wanna ranar su kaltum basu sake zuwa bola ba sai suka shiga tunanin sabuwar sana'ar da zasuyi su dinga samun abinci,
aranar kaltum da fatsuma suka jeru ajikin bangon kofar gidan su yunwa ya addabi hanjinsu fatsuma ta daga kai da kyar ta dubi kaltum tace meza mu dingayi muna samun abinci ?
Kaltum tace ni bakuwa ina na sani, kece yar gari kikasan kowa suma suka sanki,
fatsuma ta zabura ta mike tacewa kaltum taso muje wani waje kaltum na biye da ita abaya har suka isa wani gida alungu gidan wata hajiya Maryam mai saro kaya daga makkah sababbi da gumama, ,
fatsuma ta lankwashe kafa ta langwabe kai ta koro mata bayani cewar suna neman sana'a suna so tabasu tallah ta dinga biyansu
dayake tasan kanwar babarta asabebe tasan
gidansu saboda haka tasan ko sun cuceta ta san inda zata zakulosu, ta amince ta daura musu tallah, idan sunyi ciniki dayawa ta biyasu dayawa idan ciniki kadane ta biya su kadan,
bayan sati guda ne sukaje daukar tallah sai hanasu dauka tayi, tayi musu korar kare batare da sunsan abunda yake faruwaba, kuma bata fada musu daliliba suka koma wajen mai sayar da gurasa suna yimata tallah, bayan kwana biyu ta koresu,
duk Abbas ne yake hada musu tuggu ashe,
kwanci tashi watannin kaltum bakwai cur a Khartoum haka shekarunta uku kenan rabonta da Nigeria,
wulakanci da walagiigi sai karuwa sukeyi maimakon suragu al-amura sun cunkushe musu har gara da abincin da zasukai bakinsu yazam wahala kasancewar anhanasu tsintar kayan bola sannan jawahir mai kunshi da gyaran jiki ta rasu har maigidan yasake aure ko gidan ba a shiga balle su sami wadanda
zasuyi wa gyaran jiki,
Abbas sisinshi ya daina basu tunda batasonshi tuggu iri iri yake hada mata duk wata hanya da yasan kaltum zata bi ta sami
taro ko lomar tuwo sai yaje ya toshe ya batata da bakin shi,
gobe idan ta dawo sai kaga anyi mata korar kare ta shafawa fatsuma, '' idan bera da sata daddawama da wari, idan babu rami mai yakawo zancen rami ?
Inji akuyarda kura tace ta tsallako babu rami abun nufi shine duk wata tsanarda sangwama da akeyiwa mutanenmu yan Nigeria su suke jawowa kansu saboda sau tari idan suka gingimo wata badakalar saikaga ko a labari ko a mafarki yan wannan kasar basu tabajinta ba abubuwa rashin gaskiya da rashin da'a akasashen jama'a mutanenmu ke nunawa, wadanda abun kunya ne da bata sunan wadanda babu ruwansu kuma mutanen kirki ne kamar su kaltum sun zaune agidan amma basusan me
yake faruwaba, kashin kaji aka shafa musu aka hadasu akayi musu hukunci iri daya koda yake wasu masu irin mugayen dabi'u ba yan Nigeria bane wasu yan Niger ne,Ghana ,Togo ,Cameroon ,Chad ko Kenya amma sai ahadasu ace yan nigeria ne,
jama'a da gwamnatin Khartoum ta fara gajiya da rashin bin doka da rashin da ar yan gidansu kaltum aka kira malam Abdulkadir mai gidan su kaltum, ance yamusu gargadi bisa munanan halayen da akace suna kamar zubarda shara a ko ina, kafa teburin sana'o'i ko ina, sayarda rubabbun kayan dasuke tsinta abola kamar irin sana'arsu kaltum,
maza suna haura gidaje suyi sata haka ana ganin mata suna fita karuwanci yan kasa suna daukar su amotoci atafi dasu.
malam yatarasu mazansu da matansu ya shaida musu abunda aka umurceshi daya gargadesu dashi duk da wasu ya sani wasu kuma bai saniba wasu gaskiyane wasuma
karyane koma ma menene aka kara acikin maganar gaskiyar tafi yawa haka ba bukatar
bincikensu waye suke aikata wannan badakalar kosu waye babu ruwansa burinsa kawai su daina idan bahaka shizai kori kowa agidanshi,
sai su kayi kamar sun gamsu suka yi ta bashi hakuri,
gobe wani sabon rashin mutuncin zasu suka,
yasake kiransu yayi wa'azi yayi lallashi ya jawo ayoyi daga AL QUR'ANI MAGIRMA yayi fadan da kumfar baki,
in shaa Allahu jibi ta'andanci saiya karu
saboda sabbabbin mutane suke zuwa su yada zango agidan ba yan zangon daura kadaiba ko yan daura harda kanawa,zazzagawa,zamfarawa,sakkwatawa.gida yazama gidan baitil mali bangaren maza daban saboda malam yace kowa azauna
sadaka ga wuta ga ruwa ga dakuna lailaye da
siminti ba biyan ko sisi abinci ne kawai zaku nema shine suke bin gurbatacciyan hanyarda suke zubarda mutuncin su data kasarsu abunda yake tambaya anan shine wai mutane idan suka bar kasarsu cikin en uwansu inda akasansu sai suyi tayin abunda suka ga dama don ba asansu ba balle ayi musu gori ko ayiwa yayansu gori?.
me yasa mutanane basa kare mutuncin kasarsu aduk inda suka tsinci kansu ?
dadine ace yan kasa kaza basu da gaskiya ko karuwai ne marasa tarbiya ne.
masu iya magana sukace shadda bata wari banza dole muma da halinmu shiyasa ake tsanarmu, babban tabon ma shine ha'inci da rashin gaskiya
Duk yanda kahada hulda da mutanen mu sai
ancuceka wannan itace illarmu babba a kasashen waje da cikin gida,
wani sabon salo kuma wanda su kaltum basu san shiba shine gudun gardi irin nawasu makarantun kwana da akeyi a wasu makarantun kwana na yan mata da akeyi garada ne suke tubewa tsirara su hauro dakunan mata da talatainin dare suyi ihu gardi.
asabebe alokacinda taji motsi a bayanta tana juyowa taga sarkacecen mutum akan akwatinta bayan ya tsinke musu wayoyinsu da suka jona a chaji a bakin kofar dakin yafice da gudu yahaura katanga yayinda gida ya rude da kururuwa matan kowanne daki sun firfito tsakar gida a firgice, dole malam Abdulkadir da sauran mutanen anguwa suka firfito hankali a tashe ana hashaskawa ba a ganshiba,
a safiyan wannan ranar ne kuma fada ya kaure tsakanin wasu mata biyu akan shiga bandaki harda dambe da fashe fashen kai, nan ma dakyar aka kirawo wasu mazan suka rabasu don haka yansanda suka diro
gidan suna kama duk wanda suka samu idan
kukaga irin gudunda kaltum da fatsuma su kayi da tsalleka katanga saikuyi mamaki amma da kyar sukasha bayan gurgurjewa da bubbugewar dasukayi a kafafuwansu, wani sharcecen yankane a gwauri kaltum dajini jage jage amma bata lura ba saida suka isa maboya suka tabbatar sunsha sannan ta duba tagani asanadiyyar radadi mai tsanani da takeji awajen hankalinsu yayi matukar
tashi a sanda suka yi arangama da jinin mai yawa,
fatsuma ta fashe da kuka mun shiga uku kaltum yaya zamuyi da jinin nan kada jinin jikinki fa ya kare ki mutu,?
.
Saady Dan Aunty.ADON DAWA 28
.
TRUE LIFE STORY
.
kaltum ta matse hawayenda ya cika mata
ido tace Allah Ya biye bakinki fatsuma,
dama jinin jikina yakare in mutu in huta, banajin dadin duniyar nan banaso na koma nigeria haka ma yanzu banaso nakoma bur sudan dama in mutu abayan garin nan kada intashi daga inda nake yanzu,
suka rushe da kuka lokaci guda, fatsuma tace gara muyi addu'a mukoma kasarmu ke ai iyayenki sunsan bakya makkah harsun aiko miki da kudin jirgi ki koma, nifa da iyayena suke zaton ina makka inajin dadi kanwar babatace ta dauko ni asabebe muguwace ta gaske.
harkokinta kawai takeyi na iskanci, dama akamata yanzu akaita nigeria idan taje gida zata fada inda nake nima azo a dauke ni, fatsuma ta sake rushewa da kuka tace kaltum kiyafe min don Allah nina jawo miki duk wannan abun da kin tafi dabakyanan akayi wannan rigima, dabaki yage kafa abanza ba,
mamaki mara miraltuwa zaka iya gani a idanuwan kaltum ta dubi fatsuma da sauri tace me kika jawo min ?
ai ni baki jawomin komaiba kalah tajawo min ta tafi tabarni...
fatsuma ta girgiza kai tace bawan nan zuwan naki nake fada ba kaltum da tuni kina bur sudan nice nadauke miki kudinki a jakarki don kada kitafi ki barni.
kaltum taji ta tsani fatsuma harbataso tasake ganinta ta runtse ido don takaici yayinda taji zuciyarta kamar zata fashe da alama fatsuma ta gane haka sai taja da baya ta lankwashe kafa ta zurawa kaltum ido tana jiran hukuncinda zata yanke mata,
kaltum tayi shiru ba tare data furta komai ba sai hawaye dayake fita daga idanunta,
fatsuma tacire dankwalinta ta kama
kafar kaltum ta daure saboda jininda yake zuba haryanzu.
kaltum ta runtse ido yayinda ta jingina kanta
ajikin bishiyar da suke rabe tayi shiru kamar mai gyangyadi nan kuwa rayuwa ce ta tsananta a gareta,
fatsuma ta nisa tace da na dauke kudin ba
wani abun nayi dashiba ajiya nakai da niyar in an kwana biyu inbaki wacce nabawa ajiyar daga baya tace min wai an sace nikuwa nasan karya take cinyewa tayi don haka nayi shiru banfada miki ba don babu kudin..
kaltum dai har yanzu bata bude idanun ta ba bare tabata amsa,
fatsuma ta mike tsaye tace zomuje mu leka kofar gidan mu ga ko an gama kame,
kaltum bata ansa ba sai ta sake cewa kokuma kizauna tunda kafarki nada ciwo inje
indawo shiru ta mata fatsuma ta tafi sannan kaltum ta bude ido tabita da kallo yayinda kuka mai yawa ya kece mata marar kakkautawa tayi ta kuka tana tuje kososon gashin nan nata dake dandankare asanadiyyar rashin kitso har tsawon watanni bakwai daman kanta bata ba dankwali dayar
ahanya wajen haura katanga burgujejen skirt ne da bakar t shirt duk a huhuje itama sadaka aka bata kafafunta babu takalmi kallo daya zakamata ka tabbatar almajirace ko kuma tababbiya sabon kamu, fatar jikinta kososowa yake ana ta abinci waketa man shafawa abincin ma dazasuci shima badon dadi ba sai donsu rayu,
data tsagaita dakukanta saita bingire ta kwanta tana barci bata damu da kashin tsunsaye da suke tsarto mataba haka bata damu da tika tikan jangwale gwadar katangaru da suke dauki ba dadi da matansuba sunata zagayeta barci take kuma kamar bugun aljanu datasaba ta dai fita daga haiyacinta koma dai menene batacikin haiyacinta,
cikin barci kamar ido biyu taji muryan fatsuma tana fadin ga kaltum din ta bude ido da kyar ta dubi mutanen da ke tsaye akanta dusu dusu take ganinsu don haka bata gane ko suwayeba ta komawa jabar tayi ta kwanta
saitaji an girgizata antasheta zaune kaltum kaltum bude idonki ki gani taga fatsumace rumgume da ita cikin larabci, murya tayi magana wacce nan da nan taji ta wartsake gaba daya daga barcin kai wannan ba kaltum dinda nake nema bane daya daga cikin mazajen biyu da suke tsaye akansu ne ya fada, ta dubeshi ya dubeta duba na ido cikin ido yayinda gaba dayan su suka rude mamaki ya bayyana fuskokinsu mai tafe da tsananin farin ciki ya fada cikin wata murya mai sauti abayyane yace kaltum kece kuwa?
AlhamduLillah
yayinda ya durgusa gwiwoyinsa biyu akasa ya daga hannu da idanunsa sama yana gode wa Allah, itama ta zabura ta mike tsaye ta dafe kirji ta fada cike da mamaki lah mambela ya akayi kasan ina nan ?
Fatsuma tafada cike da murna au kaine mambela daga bur sudan ?
Yaji dadi ya dubi fatsuma cikin murya mai sanyi yace nine mambela ashe kinada labarina ?
ya juya ya dubi mutumin da ya rakoshi yace malam itace yarinyanda nake nema, yau sati biyu kenan muna yawo a Khartoum tare dakai saiyau Allah Ya yanke min nagode malam
Allah Ya biyaka sannan mambela yasa hannu a aljihu ya debo kudi mai yawa ya bashi saida
mutumin ya bude baki don mamakin wannan kyauta mai tsoka mambela yakara dacewa kaje masaukina ka dau jakan kayana karike na baka kyauta don bazan koma cikin gariba daganan sai tashar jirgi zamu tafi daman ita nazo nema Allah Ya taimaka na same ta.
farin ciki da godeya ba adadi mutumin nan ya
dinga yi yana mai yimusu adduar Allah Ya basu tare yana tafiya yana nanatawa kamar karatu,
mambela ya tsunguna agaban kaltum yayi tagumi yazura mata ido yana dubanta sama da kasa yayinda itakuma kunya ta rufeta tana rurrufe jiki,
hawaye yacika masa ido ya fada cike da tausayawa yace kaltum yanzu kece kika zama haka kin rame kinyi daka-daka kamar bakece mai tsaftar nan ba?
dubi kanki yanda ya zama duk kura babu kitso har kawarki tafiki kyawun gani,
yasake dubanta sama da kasa yayinda yayi arangama da dankwali jage-jage da jini a daure akafarta yasa hannu ya kwance sai ga yankan namar kafanta awaje, ya firgita ya
tambaya cikin gigita meyasameki akafa haka?
kaltum ta sunkuyar da kanta kasa yayinda hawaye ke zuba a idanuwanta, mambela yazubo da hawayen daya ciko masa ido magana yake har cikin zuciyarsa yace yanzu kaltum daman irin matsananciyar rayuwarda kike ciki a Khartoum?
amma kikaki ki hado kayanki kidawo bur sudan?
yanzu kaltum ina raye a sudan amma kika zauna kika zama almajira?
.
Littapin kamar ya daina dadi, dan an rage comments.
Y?
.
Saady Dan Aunty.ADON DAWA 29
.
NA JAMILA UMAR TANKO (JUT)
TRUE LIFE STORY.
.
Table of Contents