Chapter 2
part39
Washe gari tun karfe
tara saura kwata na
safe Badawiyya ta isa
gidansu Nuraddin.
A daren jiya batayi barci ba, zuciyarta cike da
abinda ya wakana
tsakaninta da Amal 'yar
sarkin aljanu.
Badawiyya ta yarda
cewa abinda Amal ta fada gaskiya ne, tabbas
da ace Nuraddin yaci
gaba da zama a haka
gara Amal ta warkar
dashi ta aure shi. Amma
tambayar da Badawiyya ta kasa kawo amsarta
shine, shin anyan kuwa
zata iya zama a duniya
ba tare da Nuri Darling
dinta ba? Ta kuma riga
ta san tsabar taurin kan Nuri ba dole bane ma
idan Amal din ta warkar
shi ya yarda ya aureta
ba. Wadannan
abubuwan su suka
cunkushe kwakwalwarta. Daga
karshe dai ta yanke a
zuciyarta cewa koma dai
menene gara ta amince
da sharudan Amal in har
zata warkar da Nuri, dadai yayi ta zama a
haka a nannade har iya
rayuwarsa gara ta bari
Amal din ta warkar
dashi ta aura din. Akalla
dai, badawiyya tace cikin zuciyarta, koda
mutuwa nayi, nabar
abin tarihi mutane na
baya masu zuwa idan
sunji labarin zasu san
cewa ban zalunci Nuri ba, kuma na mutu a
kokarin ceto shi daga
mummunan kangin
rayuwa.
Da wannan hukunci a
zuciyarta ta isa gidansu Nuri. Tana zuwa suka
gaisa da mahaifiyarsa
sannan ta wuce kai
tsaye zuwa inda Nuri ke
kwance kamar
kwarangwal, an lullube shi da farin kyalle kamar
gawa babu komai a
jikinsa sai diras.
Badawiyya tasa hannu
ta yaye kyallan zuwa iya
fuskarsa lokaci guda kuma ta ajiye jakar
dake hannunta ta zauna
kusa dashi ta kura masa
idanu.
"sannu Nuri... Allah ya
sauwakema kaji"? Tace dashi. Wani zazzafao
hawayen bakin ciki yayi
sartu akan kuncinta,
Badawiyya tayi saurin
dauke kanta gefe guda
ta goge hawayen saboda tasan duk da
yakedai Nuri baya iya
koda motsi, idan yaga
hawayen sai zuciyarsa
ta soye dan bakin ciki.
Badawiyya ta dubi agogon dake hannunta,
karfe tara daidai, lokaci
baiwa Nuri abinci yayi
tace cikin zuciyarta. Dan
haka ciki gaggawa ta
dauko kwanon farar tasar dake kusa dashi
wanda a cikinsa kulum
take juya madar kafin ta
bashi, domin baya iya
sha kai tsaye daga
kwalbar. Badawiyya ta zaro kwalbar madarar
mai sanyi daga cikin
jakar da tazo da ita, ta
juye madarar cikin
kwanon. Badawiyya na
kokarin bashi madarar kenan sai taga kamar
madarar tayi kauri da
yawa, sai ta dan kara
ruwa ciki, sannan tasa
dan yatsanta guda daya
wanda ke sanye da zobe ta fara gauraya
madarar, bayan ta gama
sai ta tsotse dan yatsan
da tasa cikin madarar a
bakinta, sannan sai ta
lura da cewa duk madarar ta bata zoben
dan haka shima zoben
saita sashi a bakinta ta
tsotse shi cikin jindadi
domin tasan zoben ya
taba zama a hannun Nuri.
Ahankali cikin
tausayawa ta tallafi kan
Nuri ta dora akan
cinyarta, sannan ta
dauko kwanon tasar da madarar ke ciki ta
dungura a bakin Nuri da
niyar ya sha.
"Kada ki bashi! Kada ki
kuskura ki bashi! Idan
kika bashi mutuwa zaiyi". Wata fikakkiyar
murya ce take fadin
maganar cikin karaji,
akwai alamar razana
karara a muryar.
Badawiyya ta juya a tsorace bata ga kowa
ba.
"kada ki bashi! Zai mutu
idan yasha"! Cikin firgici.
Badawiyya ta dubi
idanun Nuri abinda ta gani sun bata al'ajabi,
fuskarsa ta fara motsi
tana kokarin nuna mata
wani abu, tabbas
idanunsa nuni suke da
cewa abashi madarar yasha. Badawiyya bata
bata lokaci ba sai ta
durawa Nuri abaki.
Nuri ya hadiyi madarar
kut!.
"wayyo Allah na shiga uku na lalace wallahi
Badawiyya kin cuceni"
muryar ce ke ihu tana
kuka.
Ga mamakin Badawiyya
sai taji kamar jikin Nuri ya fara nauyi akan
ciyarta, da farko bata
gane abinda ke shirin
faruwaba, saida ta kura
masa idanu sannan taga
jikinsa ya fara rikidewa yana dada kumbura,
kifin kiftawa da
bismillah jikin Nuraddin
ya warware ya koma
kamar yadda yake abin
kamar a mafarki. "Alhamdulillah" nuri yace ya
tashi zaune.
Badawiyya ta mike
tsaye zumbur a kidime,
ta rungume Nuraddin
cikin Kuka.
"NURADDIN... Wayyo Allah Nuraddin ya akayi
ka warke"?
Nuri ya mike tsaye,
Badawiyya ta dubeshi
sai taga ya warke garau
babu sauran wata nakasa a jikinsa kamar
ma wani abu bai taba
samunsa ba.
Nuri ya kama dan
yatsan Badawiyya
sannan ya rike zoben daya bata yace. "Har
kullum kwanan duniya
nakan gwada miki da
idanuna cewa ki jikamin
zoben nan ki bani nasha,
amma kin kasa ganewa sai yau Allah yasa kika
gauraya madarar da
danyatsanki mai zoben".
Yadan yi shiru yana
duban jikinsa kana yaci
gaba. Wallahi daga yau dinnan makircinta ya
kare agaremu har abada
domin duk wanda yasha
wani abu da ya taba
zobennan bazata taba
iya cutar dashi ba, shi ya sa kikaga tunda farko
ta kasa tabaki, duk
karyar banza take fada
miki da ace tanada iko
da tuni ta nannade ki
kamar ni".
ALJANI YA TAKA WUTA KARSHEN LABARI.
"Nuri darlin! Wayyo Allah nurina"! Badawiyya ta
dada rungumeshi. Gaba daya nema take ta zama
mahaukaciya.
Mahaifiyar Nuraddin tana daki sai ta jiyo
hayaniyarsu a waje. Gabanta ya fadi sa'ar da taji
wata murya kamar ta danta Nuraddin. Wannan
shiyasa ta fitowa waje cikin gaggawa sai suka yi
ido biyu da Nuraddin. Atake a gurin ta fadi
summamiya.
"Nuri darling na godewa Alla daya warkar dakai,
don Allah zo mutafi gidanmu yanzun nan mama
ta ganka".
Nuraddin yayi murmushi "Amal ta fadamin labarin
komai, wai da wani mijin za'a aura miki ko"?
Gaban Badawiyya ya fadi ta dubeshi cikin
damuwa tace. "yaushe ta fada ma?
Nuraddin yace. Jiya da tsakar dare, kinsan kullum
saita kawomin labarin da zai konamin zuciya.
Yayi shiru gami da murmushi, sannan sai ya
kama hannun Badawiyya yace.
"zo mu tafi gidan naku mu bata mamaki me
yiyuwa ita ma idan ta ganni sai an zuba mata
ruwa saboda kaduwa".
Cikin farin ciki marar misaltuwa, Badawiyya ta
kama hannunsa suka nufi zaure. Koda suka zo
daf da kofar gidan zasu fita sai Badawiyya ta
rkeshi suka tsaya sannan sai ta dubeshi ta
kyalkyale da dariya tace.
"Nuri darling Duk mun rude dubi fa a yadda
jikinka yake har zamu fita waje. Ka koma gida ka
sako wandonka da riga sannan ka yayyafawa
mamanmu ruwa". Badawiyya ta sake fashewa da
dariya.
Nuraddin ya dubi jikinsa cikin mamaki domin
ganin abinda take yiwa dariya. Sannanne to ya
lura ashe tik yake tsirara daga shi sai DIRAS!.
KARSHEN LABARI.
ALHAMDULILLAH.
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
Table of Contents