Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 1

DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN K’AI.

So Da Buri Book 1 Complete Hausa Novel – Huda’s Painful Childhood 58,290 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

So da Buri
Free Book
01.

3 years ago.....
A cikin garin kano,a unguwar gandun albasa,cikin wani d’an matsakaicin gida…
kana ganin gidan kai tsaye za ka kirashi da na mai k’aramin k’arfi…daga waje k’ofa ce idan ka shigeta zaka biyo ta wani k’aramin soro,a soron akwai k’ofar d’aki mai band’aki a cikinsa kafin ka karaso cikin tsakar gidan wanda babu ko siminti rairayi ne a malale
wanda ya ke nan a share dukda yanada d’an girma amman hakan bai hana an share shi tsaf ba! Daga gefe guda akwai d’akuna guda hud’u a jere,daga chan ta wajen k’arshen tsakar gidan kuma akwai bayi wanda aka sakaye shi da k’ofar langa langa duk tayi tsatsa,sai kuma opposite d’inshi kitchen ne da ko k’ofar langa langar ma shi babu amman baka iya hango cikin kitchen d’in saboda duhunsa sakamokon bangon da duk yayi bak’i wuluk ta dalilin girki da itace.
Wata y’ar matashiyar budurwa da ba zata gaza shekaru 14 ba ce a tsakar gidan sai uban zufa takeyi,ta yi kneel down ta d’aga hannayenta sama,a kan tafukan hannayen nata kuwa wasu maka makan takalman ball ne d’aya a kowanne hannu…
D’an motsi ta yi wanda hakan ya sanya takalmin dake kan hannun hagun ta ya kusan fad’uwa,tsabar yadda duk ta rikice ta fita a hayyacin ta ga rana ga tsoron bulala ne ya sanya ba ta san lokacin da ta yar da na hannun daman nata tai saurin rik’e na hannun hagun nata ba…
ai kuwa bata k’arasa rik’ewa ba ya d’aga zabgegiyar bulalar dake rik’e a hannunsa ya zabga mata a kan hannayen nata,hakan yasanya ta k’arasa zubar da takalmin itama ta zub’e a nan k’asan saboda ba kad’an ba dukan ya shigeta.
Kamar jira yake yi kuwa ya rufeta ta duka! Babu ji babu gani…
ihu takeyi sosai tana kwala kiran
“Mama!, mama!!,mama!!!”
Mama da ke a d’aki,wadda tun farawar abun take jin su, ta runtse idanunta hawaye na gangaro mata tana adduan Allah ya kawo wanda zai ceci y’ar tata.
Kamar daga sama ya ji an fizge bulalar,juyowa yayi a fusace zai yi masifa suka had’a ido da wani kyakkyawan saurayi!mai manyan idanuwa..yanada cikar gashin kai da na gira da dogon hanci sannan bakinsa bai cika girma ba…skin colour d’insa chocolate ne me d’an haske da shek’i,dan ko kad’an ba za ka kira sa da Bak’i ba.....

cikin b’acin rai Junaidu yake kallon yayan nasa wanda suke mugun kama da juna bambancin kawai Junaidun ya fi yayan nasa kyau da manyan idanuwa da haske,sannan lips d’insa bai yi duhu ba kamar na yayan nasa da suka yi bak’ik’irin instead nasa shi light pink ne…..
tun cikin bacci yake jin hayaniyarsa a tsakar gida sama sama har ya kaiga farkawa ya watstsake yafara jiyosu sosai.
Kallon kwayar idanunsa Junaidun yayi…a zuciye ya yar da bulalar a k’asa kafin ya doka wani uban tsaki sannan yace”yanzu fisabillillahi ya Ja’afar abinda kake yi ya dace kenan??idan za ka hukunta Yarinyar nan ka dinga hukunta ta a lokutan da kake cikin haiyyacinka mana!!!
kalla fa idanunka!
ka je ka yi high!!kawai ka zo sai jubgar y’ar mutane ka ke yi so kake ka illatata??
kuma zan iya dafa Qur’ani akan cewa ba wani laifin kirki ta yi maka ba…a kan laifin da bai taka kara ya karya ba ka zo kanata dukanta haka!
me ta yi maka??”
Ya yi masa tambayar still yana tsare shi da manyan idanuwansa.

Mitsi misi ya Ja’afar d’in yayi da idanuwansa da suka yi jazir sannan ya yi baya kad’an ya d’an yi tangal tangal kamar zai fad’i sai kuma ya dawo daf da Junaidun ya tsaya ya zuba hannayensa cikin aljihun wandonsa sannan ya zuba masa idanuwa kafin yace
“Kai,dan uwarka ni sa’anka ne?”

Shiru Junaidun ya yi yana kallon shi kafin a hankali ya d’an sassauta murya yace
“yi hak’uri,mai tai maka??”

Tsaki ya Ja’afar d’in ya yi sannan yace
“Akan gyaran d’akin da suke yi mini it da Jalila ne,Jalila ta yi mini bayanin ta ta wuce,
Ita wannan makirar sai ta tsaya shara wai Umma ce ta sakata sharar tsakar gida, abun haushin da na shiga d’akin nawa fa ko tsinke ba’a d’aga ba komai yana nan a yadda na barshi…”

shiru Junaidu yayi don in dai zai iya tunawa to jiya da shekaran jiya duk ya ganta tana gyaran d’akin ya Ja’afar,kuma a ka’idarsa shi ya Ja’afar d’in kwana bibbiyu sukeyi itada jalilan…to ya za a yi kuma yau ma yace still itace zatai mishi gyaran d’aki…
Juyawa yai yana kallon hanyar d’akunan gidan kmr yana neman wani abun kafin da k’arfi ya fara kwala kiran
“Jalila!Jalila!!Jalila!!!”
Ya jafar ne ya d’an tab’o hannunsa sannan yace masa
“kai ta tafi jarabawa fa”
juyawa Junaidu ya yi ya kalle sa kafin yace
“ya Ja’afar yau a ka’ida waye zai yi maka gyaran d’aki???”
shiru yayi kafin cikin maganarsa ta y’an shaye shaye yace
“Kagane ko!
a k’a’ida Jalila ce,to ita wannan makirar sharar da ta yi jiya da shekaran jiya duk basu fita ba kai gyaran ma kwata kwata bai yi ba shiyasa yau sai d’akin yayi kmr ba a tab’a gyarawa ba sannan Jalila jarabawa ta tafi,shine na shigo na ganta tana shara kuma Jalila ta sameni a waje ta ce mini ta rok’eta ta gyara d’akin ita ta makara amman ta zazzageta har da marin ta fa tayi!!!
ita dan uwarta a gidan ubanta ba a alfarma ne eh? Shine fa na shigo na sameta tana kwashe shara,ni kuma na d’auki alwashin sassama mata kamanni a yau d’innan tunda ta raina ni,ai ba Jalila ta zaga ba ni ta zaga tunda d’akina ne,kai marin ma ni ta mara tunda ai dai duk akan d’aki na ne”

Junaidu da ya fara fahimta makirci ne kawai Umma da Jalila suka had’a saboda sunga an kwana biyu ba a jibgi baiwar Allah n ba,sannan su Baba ya hana su dukanta shine suka biyo ta hannun ya Ja’afar tunda sunga shi in dai ya bugu to ba iya gane gaskiya da k’arya yake yiba sannan ko baya ga hakama daman chan shi ya tsani Yarinyar….

Sunkuyawar da ya ga ya Ja’afar nayi yana k’ok’arin sake d’auko bulalar ne ya dawo dashi daga nazarin daya tafi,da sauri ya rik’e hannun ya Ja’afar ya shiga lallab’asa akan ya yi hak’uri ya barta za a gyara masa d’akin nasa,amman fur ya k’i hak’ura…
k’arshe dai naira ashirin Junaidu ya d’auko daga aljihu ya basa tukunna ya hak’ura ya karb’a yana murmushi yace ta bar gyaran d’akin ma gobe sai ta yi,idan kuma Jalila bata da jarabawa goben sai ta bari jibi ta karb’i aikinta.
Juyawa ya Ja’afar ya yi yai hanyar fita daga gidan
shikuma Junaidu ya juyo yana kallonta anan a durk’ushe tana kuka tana ajiyar zuciya ta kifa kanta a k’asa….
A hankali ya sunkoyo kanta,kafad’unta ya kama duka biyu ya juyo da ita sannan ya sa hannunsa a hab’arta ya d’ago fuskarta.

Da sauri ta runtse idanuwanta da suka yi luhu luhu fuskarnan tayi jawur tsabar kukan dataci..shiruu ya yi yana kallon ta..tun daga kan lafiyayyan gashin gaban goshinta wanda suka kwanta sukai lub lub akan farar fatar ta,zuwa kan gashin girarta masu kyau da shape kamar ta yi cavn da madaidaitan idanuwanta, zuwa kan dogon hancinta wanda yai kmr M daga k’arshe amman ba sosaiba da dan mitsitsin bakinta….
Cikin seconds d’in da ba su fi uku ba ya yi mata wannan kallon..a hankali ya sauk’e ajiyar zuciya kafin ya kira sunanta“HUDAN”saurin bud’e idanunta tayi ta kallesa!
kamar kuma wadda ta tuna wani abun sai ta yi saurin ture hannunsa daga jikinta ta tashi da gudu tai hanyar d’akin Mama.

Shiru ya d’an yi,chan kuma a hankali ya mik’e tsaye, ya juya da niyyar komawa d’akinsa.

Juyowar da zai yi ya ga Umma a tsaye tana kallonsa sai kuma Anty zainab wadda ke tsaye a chan bakin k’ofar gidan tana d’an lek’a waje da alama bayan Ja’afar wanda ya fita yanzun ta ke bi da kallo.Daga gani ka san basu dad’e da shigowa cikin gidan ba dan ga lullub’i a kanta da kuma jaka a hannunta,itama anty zainab dake bak’in k’ofa haka
amman tabbas ta gansa tare da Huda dan gashi ranta a mugun b’ace yake!
Cikin in inar da bai san yana da ita ba yace
“um um umma dddagaa ina ku ke?”
K’arasowa ta yi gaban sa ta tsaya sannan cikin b’acin rai tace”daga gidan ubanka nake!!….”.
Shiru ya yi ya sunkuyar da kansa yana sauraronta tana fad’a baki da kumfa,Anty Zainab da ta k’arasa shigowa yanzun tana tayata ,
Umma ce tace”wato da ka d’auka ba yanzu zan dawoba ko?shine kaje harda wani d’ago ta kana kallon ta,idan za ta had’iyi zuciya ta mutu Junaidu ina ruwanka da damuwarta?? Ka ga ta inda Ja’afar ya fi ka ko?Yaron nan ko kyalle ne indai nace banaso to kuwa shima ba zai so shiba,anya ni na haifeka kuwa?a ce Yaro kwata kwata baya kishin uwarsa!!anbi an lashe ka an shanye ka to wallahi ba’a isa ba,ni naci uwar boka ma ballantana malami…ka ci gaba da b’ata mini rai har sai ka ja nai maka baki tunda baka jin magana ta dudda dai na san ba yin kanka baneba.”
Anty Zainab itama tace
“ke kuwa Yarinya ta yo gadon munafurci ai ba zai tab’a ganin laifin taba,mu mun buga da wadda ta haifo ta ma ta hak’ura ta barmu,ballantana ita…..”
Ta inda suke shiga ba ta nan suke fita ba hakanan suka yi ta habaici a tsakar gidan babu wanda yace musu ci kanku sukayi suka gama suka shige d’akin Umma suna huci,anan d’in ma maganar sukaitayi,da suka gaji Umma ta bawa anty zainab sak’onta ta mik’e tai mata sallama ta fito ta tafi,har ta fita a gidan mamakin Junaidu takeyi…ba irin yadda ba su yi ba akan ya fita harkar Yarinyar tun bata kai haka ba amman a banza
Ajiyar zuciya ta sauk’e a ranta tana adduar Allah yasa Junaidu dai ba gadon wahala ya yo daga wajen ubansa ba .

Chan d’akin Mama kuwa Hudan ce kwance akan gado ta d’aura kanta a kan cinyar Mama tanata kuka,Mama bata hanata yin kukan taba sai da taji ta d’an sassauta kukan nata tukunna a hankali ta shafa kanta tace”Huda ba na hanaki shiga harkar Junaidu ba?? Dukda a cikin y’an gidan nan shi kad’ai ne baya zaluntarki yake kuma kare ki amman na san kin san cewa banason alak’ar ku ko? Yanzu duba ki ga irin zagin da kika ja mini da ke kanki”.

Shiru Hudan tayi da kukan da takeyi kafin ta dago kanta ta share hawayenta ta kalli mama sannan a hankali cikin sanyi tace”Maamaa ni fa ban kula shi ba Allah,kawai dai ya karb’e bulalar da Ya Ja’afar yake duka nane ya bashi hak’uri amman ni bance masa komaiba.”

Shiru Mama tayi tana kallon y’ar tata kafin tace”to ke Huda mai yasa da Jalila tace ki gyara mishi d’aki kika k’i kika hau shara??”

Raurau Hudan ta yi da idonta kafin tace “Mama jalila k’arya ta yi mini, daman jiya akan ya Junaidu ya hanani wanke mata uniform d’in makarantar ta tace mini wallahi sai ta saka ya Ja’afar ya zaneni, wai tunda na shiga tsakaninta da d’ayan yayan nata bara sai ta sa d’ayan ya zaneni.”

Shiru kawai Mama tayi tana tunani….ko ba a fad’a ba daga yanayin fuskarta ka san ranta a b’ace yake.
Gaskiya ita dai hak’urin ta ya kusan k’arewa,taya still za a mayar mata Yarinya kamar wata jaka,dan ma ta samu sauk’i tun lokacin…
……….
Da ta je wajen Kaka (Baba Bashir) ta kai masa k’orafi akan su Umman da jalilan.
Ran kaka ya yi mugun b’aci a lokacin hakan yasa ya kira Baba ya ja masa kunne akan yayi musu gargad’i mai zafi dan in har ya sake jin ko da marin Hudan ne anyi a tsakanin Umma ko Jalila to bai yafe masa ba.
Baba ya shiga rud’u a wannan lokacin domin kuwa a duniyar nan idan akwai abunda yake jin tsoro to shine b’acin ran Umma amman kuma yanzu ga abunda mahaifin sa ya fad’a wanda ko hauka yakeyi ba zai bari Allah ya isan iyaye ta hau kansa ba,hakan yasa yana dawowa gida ya rufe ido ya tara su a d’akinsa ya cewa Umma da Jalila “kar su k’ara dukan Huda,sannan kar a sake d’aura mata talla,wankinsu su dunga yi da kansu ko sukai gidan wankau,sannan wanke wanke da wankin band’aki tsakanin Huda da Jalila duk ranar da mamanka keda girki kai ne zaka yi,indai har kuwa aka k’etare abunda ya fad’a to a bakin auren Umma
Abunda kawai ya yarda aikin Huda ne parmanent shine sharar tsakar gida domin ita Jalila nazuwa makaranta.”

Umma a wannan lokacin kusan daskarewa ta yi tsabar mamaki..mutumin da ko maida mata magana baya iya yi shine yau harda ik’irarin cewa ‘a bakin aurenta!!’ Tabbas da sake, kasa yin shiru tayi dan haka ta yi gyaran murya sannan tace “Alhaji ka bani mamaki matuk’a amman ba zan yi jainja da kai ba a gaban Yara,abu d’aya wanda na sani shine kana dab da b’ata tarbiyar Yarinyar nan kai da uwarta dan ba zai yiu ace kab gida Yaro babu mai kwab’arsa ba,ga yayunta nan maza amman an nuna mini iyakata,Alhaji ance babu mu ba Huda ko? Saboda ita shafaffiya da mai ce? ni za ka yiwa haka akan wad’annan mutanen???”
Ta yi maganar tana dukan k’irji da kafe Baba da manyan idanunta waenda yake hango tsantsar b’acin rai a cikinsu.

BULAMA ✍️

So da Buri
Free Book
02

Shiru Baba yayi yana tunanin ta hanyar da zai bi ya d’an kwantar ma da Umma hankali…chan ya yunk’ura yai gyaran murya kafin yace
“Sadiya ni bance harda yayunta maza ba,dokar iyaka kanki ne ke da Jalila shima kuma saboda Kaka yayi mini kashedi mai zafi shiyasa, ko kina so Allah ya isan shi ta hau kaina??
yayunta maza sunada ikon hukuntata indai ta yi laifi kuma ai....”

“Aikin banza ma kenan!!!”tsawar Umma ta katse shi
Kafin ta ci gaba da cewa”ai kaga wannan matar”
ta yi maganar tana nuna Mama wadda tunda aka fara maganar bata ce uffan ba. Cikin huci ta d’aura da cewa”tabbas in dai baka taka mata burki ba tunda ta samu Kaka yana goya mata baya zata sake komawa wajen shi ta kai k’arar su Junaidun suma..tunda naga kamar ma tsoronta kafara ji.”
Ta k’arashe maganar tana huci.

Shiru Baba yayi kafin ya d’ago kanshi ya kalli Mama
“MARYAM”
ya kira sunanta cikin kakkausar murya.D’agowa Mama ta yi ta kalleshi kafin a hankali tace “naam”
Nisawa yayi sannan ya ce
“kin kai k’arata wajen mahaifina,an yi miki abunda kike so ko? To nima ga nawa sharad’in,
Indai Huda ta yi laifi kika hana su Ja’afar hukuntata kema a bakin aurenki,don kamar yadda Sadiya ta fad’a ba zai yiu ace Yaro babu mai kwab’arshi a gida ba,
Ita dai da Jalila ga sunan sun bar miki y’ar ki.”
Yana gama fad’in haka ya d’ora da cewa
“Shikenan kowa zai iya tafiya na riga na gama magana.”

Ahaka aka tashi kowa yai d’akinsu .

Umma sam ba haka ta so ba,dan ta san daman auren Baba ba wani d’ad’a Mama yayi da k’asa ba,kawai dai saboda Hudan yasanya take hak’uri take zaman gidan.
Hakanan ranta babu dad’i suka k’arasa d’aki tanata k’ulla ta inda zata b’ullo wa alamarin a ranta.

Mama atunaninta sauk’i zai zowa y’artata sai dai sam abun ba haka yakasance ba domin kusun kullum sai ansan sharrin da aka had’a mata an saka Ja’afar yai mata shegen duka,sannan sharar tsakar gidan da aka ce shine aikinta kullum,tofa a rana sai Umma ta sakata ta yishi sau uku ko fiye da haka duk kuwa da girman shi,da gangan Jalila za ta jefar da abunda bai taka kara ya karya ba ace sai ta share duka ai daman yayi datti. Sauk’i d’aya zuwa biyu ta samu shine na talla da wankin su,amman ko wankin band’aki ranar na Jalila kwara ruwa kawai takeyi kusan ita ce za’ace take wanke band’akin duk ranar yinta.......
……………….
K’arar buga k’auren ne ya dawo da Mama daga duniyar tunanin da ta tafi
K’arar bata gama barin dodon kunnenta ba ta ji an shigo gidan ana wak’a,ko ba a
fad’a mata ba ta san Jalila ce.
Huda Mama ta juya ta kalla tace “kikace bata ce miki ki gyara d’akin yayanku ba ko?”
Kai Hudan ta d’aga mata alamar ‘eh’
Mik’ewa Maman tayi ta juyo ta kalli Hudan tace mata
“zauna kar ki fito” daga haka ta yi waje.

wata budurwa ce take K’arasowa tsakar gidan…ba za’a kirata da bak’a ba sannan kuma ba fara bace fat!!shekarunta ba za su wuce goma sha shidda ba,tanada manyan idanuwa da d’an matsakaicin hanci sannan bakinta ba k’arami bane ba kuma k’atoto bane ba yayi dai dai da yanayin fuskarta
kallo d’aya za ka yi mata ka kirata da kyakkyawa
sannan yanayin shigarta zai tabbatar maka da irin y’an matan nanne marasa kunya…tana tafe tana wak’a had’i da taunar cingum wanda hakan yabawa gefen kumatunta damar lotsawa. Uniform d’in jikinta koren wando ne da farar riga da farin hijabi wanda hakan ke nuni da makarantar da take zuwa ta gwamnati ce…da alama tanada wani muk’amin a makarantar tasu domin d’an kwalin kanta yellow ne ba Fari ba ba kuma kore ba,ta zaro shi daga cikin hijabin nata tayi daurin ture kaga tsiya ta saman hijabin….daga makaranta take amman ta rambada uban jan jambaki,sannan ga idon nan yasha kwalli ya sake fitowa rambad’au!!!! tubarkalla,y’ar
k’aramar jakarta da ba za ta ci littafi biyu ba na sakale a gefen hannun damanta.

Ido suka had’a da Mama wadda ta gama fitowa daga d’akinta yanzun hakan yasa ta jan wani dogon tsaki had’i da tofar da cingum d’in bakinta kafin tace”Ni fa na tsani kallo.”
Sannan ta yi hanyar shiga d’akin Ummansu.

“dakata Jalila, magana za mu yi dake”
Mama ta fad’i hakan tana k’ok’arin K’arasowa inda take.
Juyowa ta yi ta zuba mata ido ta gyara tsayuwarta tare da nad’e hannuwanta akan k’irjinta irin ina jinki d’innan.
Kallon ta Mama ta yi sannan tace”yanzu Jalila saboda Allah dukan da kike sakawa yayanku Ja’afar yana yiwa y’ar uwarki ba tare da hakkinta ba kina ganin ya dace kenan? Ke kenan kullum ba za ki ja k’anwarki a jiki ku zauna lafiya ba?
Ki duba fa
saboda Atule d’in fa da kike sakawa Yara suna yi mata kullum hakan ya sanya dole Babanku ya chanza mata islamiyya aka maida ita ta dare da asabar da lahadi na safe.
Yarinyar da ta taso da k’aunarki acikin ranta kina k’ok’arin maida mata rayuwa kurkuku?Meyasa kike hakane Jalila?mai ya faru kika chanja?”

Umma ce ta hankad’o labule ta fito daga dakinta cikin masifa tace
“Kawai kinga munafuka ki fito fili b’aro b’aro kice tunda na dawo gidan nan na chanjata,akan wanne dalilin za ki tasa mini y’a a gaba kina wani cewa ta chanza hali? To bari kiji in gaya miki Allah ne ya tsameta a cikin munafukai ya dawo da ita cikin masu gaskiya,kuna abu simi sumi da ke da y’arki nankuwa kunfi kowa iya munafurci da cin dunduniyar mutum!.”
Juyawa Mama ta yi ta kalli Jalila wadda ta ga ta yi shiru tana kallon gefe kamar bata wajen,a tunanin Mama nutsuwa ce ta zowa Jalilan,
Juyawa tayi ta kalli Umma wadda har yanzu take fad’a baki da kumfa tace mata
“kinga Sadiya ba dake nake ba, ya Ina shirin shirya tsakanin Yara ke kuma kina k’ok’arin kiga kin b’ata?ki daina shiga fad’an y’an uwa fa dan wataran za ki ji kuny.....”

“In sha Allah ke ce za ki ji kunya ba dai Ummana ba!”

maganar Jalila ta katse ta,

“kuma da kike ta cewa wani wai y’an uwa da ni da Huda shin wai Ubanta ne d’an uwan Baba? ko kuwa ke uwarta ce y’ar uwar Umma???”

Shiru Mama ta yi tana kallon Yarinyar da ta rena ta goya a bayanta ta ci kashinta taci fitsarinta tana rera mata rashin kunya.
Cikin son fahimtar da ita Maman tace
“Jalila ai ko babu y’an uwantaka ke kin san Hudan k’anwarki ce.”

“Chan ki je ki nemo y’an uwanta wallahi ba dai ni ba.”
Jalila ta fad’a cikin d’aga mata Hannu kafin ta d’aura da cewa”kiganni nan kaf y’an uwana na dangin Ummana da Babana suna da nasabarsu kuma suna amsa sunan iyayen su!…da za ki ce wani Ummana za ta ji kunya dan kawai ke kinji kunya shine za ki so kowa ma ya ji?kinje kin Haifo shegiya kin kawo ta cikin gidanmu still za ki yi ta lak’aba mini ita kina wani y’ar uwartace ita?
Idan ba tsoroba ki nuna ubanta mana ki kaita wajenshi Yarinyar da ko sunanta Babanta ba ya so yaj.....”

Jalila bataga k’arasowar Mama daff da ita ba sai kawai wani haske da ta gani sakamokon marin da Mama ta d’auke ta da shi,ai kuwa batai wata wata ba itama ta d’aga hannunta za ta mari Mama.

Ji ta yi an rik’e hannun hakan
ya sanya da sauri ta juyo,nan suka had’a ido da Junaidu ya had’e rai. Matse hannun nata yai da k’arfi sai da tayi k’ara sannan yace mata
“baki da hankali Mama za ki mara?”
Nan Umma daga bakin d’akinta toyo wata super tayi kan Junaidu ta rufe shi da duka tana cewa”saketa ta rama ka saketa nace!!”
duk irin dukan da Umma take yiwa Junaidu hakan bai saka ya saki hannun Jalila da taketa tsalle tana k’ok’arin fizge hannunta ba tana kallon Mama tana”Ya Junaidu ka cika mini hannu in rama Allah yau Mama kin tab’o tsuliyar dodo,idan sama da k’asa za ta had’e sai na rama!!”
duk ta birkice ta tada k’ura tana k’ok’arin fizge hannunta a cikin na Junaidun.
Junaidu da ya ga dambe ma take shirin yi da shi ne yasa ya fizgo ta ya juyo da ita ya d’auke ta da wani irin gigitaccen mari
yace
“ke ki nutsu!”
ya daka mata tsawa,ganin haka yasa Umma tayi kan Mama ta d’aga hannu zata mareta Mama tai saurin rik’e hannun ai kuwa gida ya kacame Umma kawai k’ok’arin ta ta mari Mama ta yi dambe da ita ita kuwa ta k’i bata daman yin hakan ta dai rik’e mata hannu shi kuma Junaidu yana gefe yana fama da Jalila.

“kai!kaii!!kaiii!!!!,lafiyarku kuwa?”
sukaji muryar Baba wanda ya gama parking machine d’in sa a soro yana k’arasowa cikin gidan da d’an sauri ga leda a hannunshi da alama yanzu dawowarsa kenan.
Umma ce ta saki hannun Mama cikin fushi tace”Alhaji gara da Allah ya dawo da kai yanzu,dan yau za ayita ta k’are a cikin gidan nan,matar nan ta kwashi k’afa ta kai k’arar mu gurin kaka,kaka ya goya mata baya an hanamu ni da Jalila ko kallon banza mu yiwa Huda,shine yanzu ni ta d’aga hannu ta zabgawa Jalila mari saboda Allah duba fuskar Yarinyar nan.”
Ta finciko Jalila daga gaban Junaidu da ya sake mata hannu ta hankad’ata wajen da Baba yake tsaye,aikuwa kamar jira take ta fashe mishi da kuka,lallashinta Baba ya shiga yi cikin rawar jiki kafin a fusace ya d’ago ya hau Mama da fad’a,Umma ce ta katseshi ta hanyar cewa
“Ai matar nan ta raina ka,tun ranar da ka hanamu shiga harkar Huda a cikin gidan nan muka daina bi takanta,amman ita da ka ce in an hukunta Hudan kar ta yi magana
shine saboda tsananin raini yau tun safe bata barmu mun sha ruwa ba a cikin gidan nan,saboda an tab’a y’ar gwal kalla yadda ta mari Jalila saboda Allah.”
Junaidu ne ya kalli Baba sannan ya juyo yana kallonta yace “Umma ba fa hakane ya faru ba,yau tun safe Ina cikin gidan nan babu inda naje,a idona aka yi komai, ita Jalila ce bat...”
Tsawar da Umma ta daka masa ne ta sanya shi yin shiru
“Junaidu!! Bar nan”ta nuna mishi hanyar fita da yatsarta manuniya,baki ya bud’e zai yi magana ta sake daka mishi tsawa tace
“bar nan nace!!”
sum sum haka ya juya ya fita ba yadda ya iya.

Juyowa ta yi ta kalli Baba tace “Alhaji a bi mana hakkinmu.”

Shiru ya yi yana kallon Mama wadda ta yi k’asa da kanta,
...Harga Allah yana son Mama, babu abinda ya chanza daga soyayyar da yake yi mata tun suna Yara amman idan ya tuna da yadda ta yi fatali da soyayyarshi saboda waninshi sai yaji wani haushin ta yana shiga masa rai yadunga jin babu abinda yakeda Buri sama da ya cusguna mata itama ta d’and’ana ta ji ya zafin cusgunawan yake...
Umma ce ta katse masa nazari ta hanyar cewa
“Alhaji muna sauraronka.”

Takawa yayi inda Mama take ya tsaya,yai mata nuni da yatsunshi guda biyu sannan ya fara magana
“Maryama a cikin zab’i guda biyu da zan baki yanzu ki d’auki d’aya….
na farko ko ki tsaya Yarinyar nan ta rama marin da ki ka yi mata na biyu ko kuma ki bata hakuri tare da alk’awarin ba za ki k’ara ba, kuma muddin kika k’ara to tabbas a bakin zaman Huda a cikin gidan nan!.”
a razane Mama ta d’ago kai tana kallon shi da idanuwanta da suka kawo kwalla…tausayinta ne ya kama shi tashi d’aya yaji zuciyarsa tana neman yi mishi gardama
dan haka cikin sauri ya juya ya daina kallonta yana me cewa “zab’i ya rage naki.”
Jalila da Umma kuwa zuciyoyinsu sun yi fess sai faman murmushi sukeyi,Jalila har da tattare hijabinta ta yi gaba d’aya ta jefa shi baya ta wajen wuyanta tana hurawa hannun damanta iska ta matso daff da Mama…
ganin da Mama tayi Jalila na neman kifa mata mari, ne ,ya sanya ta yi saurin runtse idanunta tace
“Jalila na mareki tsautsayi ne ki yi hak’uri na yi alk’awarin ba zan sake ba!.”
Da sauri kafin su Jalila su ce wani abun Baba yai saurin cewa “barka to!! kin shafama kanki lafiya,wuce ki tafi d’akinki.”
Jalila kuwa ta b’ata rai za tai magana Umma ta yi saurin rik’o hannunta tai mata alamun ta yi shiru kafin ta juya ta kalli Baba tace
“Alhaji mun gode da adalci”
Daga haka ta ja hannun Jalila suka yi d’aki.
Suna k’arasa shiga d’akin Jalila ta wafce hannunta a cikin na Umma sannan tace
“haba Umma!!mai yasa kika hanani yin magana?”gashi yanzu ban rama marina ba,harfa Ya Junaidu sai da shima ya mareni,kuma abun haushin ni Baba ya hanani dukan Hudan da a kanta zan huce,ni dai gaskiya da kawai kin barni nace ban hak’ura ba na rama marina! yanzu Ina kikeso in kai wannan d’acin da zuciyata take yi mini??”
Ta yi maganar tana mai zama da dukkan k’arfinta a kan y’ar kujerar su two seater da take ita d’aya a d’akin duk ta yayyage.

Murmushi Umma ta yi kafin ta zo ta gabanta a hankali ta d’aura dukka hannayenta akan kafad’arta sannan ta durk’usa a gabanta tare da sauk’e ajiyar zuciya kafin tace
“ta Yaro kyau takeyi bata kwari, ai Jalila ko da ace ta zab’i ki rama marin nan da ta yi miki to fa da ni da kaina ba zan bariba,saboda zab’i na biyun nan da Alhaji ya fad’o shi ji na yi kamar an tsunduma ni a cikin aljanna”
Shiru Jalilan ta yi tana kallon Umma sak’ak’e alamun tana buk’atar k’arin bayani, fahimtar hakan da Umma tayine yasata sauk’e numfashi sannan tace “menene babban burinmu a yanzu??”
Shiru ta yi na y’an sakanni sannan tace
“in auri mai kud’i kuma mu ga bayan Mama da Huda”
Murmushi Umman ta yi kafin tace “yanzu idan Hudan ta bar gidan nan tanada wajen zuwa? Girgizama Umman nata kai tayi kafin Umman ta sake cewa
“wane hali kike tunanin Maryam za ta shiga?”Babu b’ata lokaci Jalila tace”tashin hankali”sannan ta kyalkyale da dariya sai da tayi mai isarta tukunna tace
“Umma idan na fahimceki so kike in sake yi mata abunda zai b’ata mata rai har ta kai ga sake mari ko dukana”
“Abinda nakeso kenan”
Umma ta fad’a tana murmushin jin dad’i mai had’i da dariya kafin ta mike tsaye tana kallon k’ofa kamar mai tunanin wani abun tace
“Jalila ki tuna ata dalilin matarnan na bar gidan nan na rabu dake naje nai rayuwar wahala, itakuma ta dinga gallaza miki azaba
ki tuna da cewa bakiji dad’in tashi a gaban uwa ba kamar ko wacce y’a
ki tuna yadda ta ci amanata ta aure mini miji,
ki tuna! ki tuna!! ki tuna!! dayawan abubuwan da ta yiyyi mana.”

Murmushi Jalila ta yi sannan tace”Ummana kar ki damu, zan tattaro gaba d’ayan abunda na san bataso in yi ta zuba mata har sai ta kai ga tab’a ni,kuma na riga na gano abinda yafi b’ata mata rai
shegiyar y’artan nan ce bataso akira da shegiya ni kuwa yanzu na fara….”
Zuciyar Umma fess ta dawo ta zauna kusa da Jalila sukaci gaba da k’ulla yadda za su k’untatawa Mama…..

A chan d’akin Mama kuwa tana shiga ta saki kukan da take ta k’ok’arin rik’ewa,da sauri Hudan ta taso ta zo ta rungumeta itama kawai sai ta fashe da kuka kowa ya kasa lallashin d’an uwanshi,sai da sukayi mai isarsu tukunna Mama ta d’ago da fuskar Hudan tace mata “mai
ya saki kuka?”
Shiru tayi kafin tace “Mama gani nai kina kuka kuma naji abinda ya faru a tsakar gida”
Sharemata ragowan hawayen nata tayi kafin tace “bakomai ki kwantar da hankalinki”sannan ta mik’e tayi kan gado ta kwanta ta lumshe idanunta….ganin hakan ne yasa itama Hudan ta mik’e taje ta kwanta a kusa da ita tana sauk’e ajiyar zuciya kafin bacci ya yi awon gaba da ita….
SHARE PLS.

BULAMA ✍️

So da Buri
Free Book
03

A hankali Mama ta bud’e idanunta da suka d’an kumbura ta juyo tana kallon fuskar Hudan kafin ta kai hannun a hankali ta shafa kumatunta tausayinta yana sake shigar mata zuciya.

Nasarawa GRA, Kano.

Wani dogon dattijo ne ke tsallako titin da sauri had’e da d’an gudunshi,hannunsa na dama rik’e da agwaluma guda uku a cikin farar leda,na hagun kuma yana amfani da shi wajen mayar da y’an chanjin sa cikin aljihun gabar rigarsa,da alama agwalumar ya tsallaka siyowa.
K’ara saurin gudun nasa yayi sakamokon ganin har motocin da ya hango sun iso bakin mahaukacin gate d’in makeken estate d’in.
Da saurinsa ya zaro wani d’an k’aramin makulli a cikin aljihun gefen wandonsa ya isa gaban wata had’add’iyar k’ofa wadda ke a ta gefen makeken gate d’in wadda colour d’inta da design d’in exactly irin na gate d’in ne, cikin sauri ya zura mukullin a ramin mukulli sannan ya murza k’ofar ta bud’u ya tura da sauri ya shiga har yana tuntub’e, shigarsa ke da wuya waennan motocin da ke jiransa a ta wajen gate d’in suka fara danna masa horn babu k’akk’autawa…tashi d’aya duk ya bi ya rikice hakan yasa ya yi sauri ya fad’a d’akinsa na mai gadi ya d’aga k’asan pillow ya d’auko mukullin babban gate d’in ya fito yanata sauri ya k’araso jikin gate d’in ta baya ya bud’e padlock d’in sannan ya bud’e wani lock kafin ya durk’usa k’asa ya zare wata makekiyar sakata tukunna ya mik’e ya fara k’ok’arin tura gate d’in jikinsa duk yana rawa kana ganinsa ka san a rikice yake gashi an k’ara rikita shi da uban horn d’in da ake ta maka masa babu k’akk’autawa… ,
Bai kai ga k’arasa tura gate d’in ya bud’u duka ba motar farko k’irar benz G wagon Bak’a wuluk! ta danno kai da mugun gudu ta biyun na binta a baya, ba don ya yi hanzarin barin wajen ba da babu abunda zai hana gilashin motar tafiya da y’ar sharar jikinsa.
Ganin motocin sun shige ne yasanya shi K’arasowa bakin gate d’in ya fara turawa domin rufewa, da kyar yake iya turawa saboda tsabar girma da nauyi.

Wani gate d’in motocin suka nufa a cikin jerin gidajen estate d’in da a kalla sun kai 15 kuma gaba d’aya ginin gidajen yanayin tsarin 3D ne masu hawa biyu,tsayuwa fad’an haduwar ginin gidajen b’ata lokaci ne.
Wani kakkauran mutumi ne zaune a bakin gate d’in da suka nufa,sanye cikin uniform d’in sojoji,da alama shi ke gadin wannan particular gate d’in, mik’ewa ya yi sakamokon hango motocin sannan ya shiga ta k’aramar k’ofa ya bud’e musu gate d’in wanda hakan ya bawa farfajiyar gidan damar baiyyana..mahaukacin makeken mansion ne yanayin tsarin ginin 3D shima…
Ma sha Allah aljannar duniya kenan domin kuwa ya had’u har ya gaji da had’uwa da tsaruwa ga kyau ga girma duk ya had’a.
Wajen da aka tanada domin ajijiye motoci suka nufa sannan suka yi parking.

Wani mutum ne ya bud’e motar farko,ta wajen mazaunin driver ya fito ya zagayo ta wajen owners corner da d’an saurin shi ya bud’e murfin motar ya koma gefe ya tsaya .

....K’afarshi ta dama wadda ke sanye cikin had’add’en black d’in covershoe mai tsananin tsada ya fara zurowa waje, kafin ya sauk’o da d’ayar sannan ya mik’o ya fito gaba d’ayansa, ba matashi bane ba ko magidanci ko kuma dattijon Alhaji, tsohon mutum ne ,tukuf da shi!!
Sanye yake cikin wasu zazzafan suit,ash colour, kai kana ganin yanayin kayan ka san ya kai kud’in jarin mai k’aramin k’arfi,idanunsa sanye cikin wani farin glasses wanda kana gani ka san na k’arin k’arfin gani ne,walking stick d’in dake rik’e a hannunsa for sopport ma kanta abar kalloce!! Ka na gani ka san an zuba mak’udan kud’ad’e wajen siyar ta,ga wani had’add’en Rolex watch a hannunsa,
Tsohone amman skin d’insa glowing yake yi wanda kana gani ka san tsabar hutune..to cut it short dai,every part of him is screaming ‘I’M RICH!!’.

Sandar hannunsa ya d’aga domin yin tafiya har ya d’an tura k’afarsa gaba sai kuma ya yi amfani da ita ya juyo ya tsaya yana kallon motar da suka shigo tare.

Wani kyakkyawan saurayi ne ya fito daga mazaunin driver da alama shi ya tuk’o motar da kansa, yana d’an fizgen kama da tsohon sannan kalar fatar su iri d’aya ce.
Ganin da Auwal ya yi kakan nasa ya kafeshi da idanune ya sanya shi K’arasowa wajensa da d’an sauri, tukunna ya d’an rissinar da kansa yana mai kallon k’asa kafin yace”Garanpa,u need something??.”
Ya yi masa tambayar ba tare da ya kallesaba .
Juyawa Grandpa d’in ya yi ba tare da ya sake kallonsa ba,har zuwa lokacin da drivern d’insa ya d’auko suitcase d’inshi ya gama rufe motar yana taka mishi baya….
yana tafiyar ba tare da ya tsayaba cikin muryarsa ta tsofaffi yace”Go and give iliyasu 50k,ask him to leave this house foreva,he is fired!!
Sannan ka cewa Daniel ya nemo sojan da ya san zamu shirya ni da shi,ya fara gadin main gate,within 3 hours.”
Yana magana yana tafiya ko sake waigowa bai yi ba balle ya amsa Auwal wanda yake cewa”Ok Granpa consider it done”.
Ya shige.

Wani shu’umin murmushin jin dad’i Auwal d’in yayi, daman shi ya tsani Malan iliya, domin kuwa kamar gadin sa shi kad’ai yakeyi a gidan,ya saka masa ido dayawa, kullum idan ya dawo dukda kuwa motarshi tinted glass gareta sai Malan iliya ya san yadda yayi ya d’an lek’a ta gaban dukdan ya ga shi kad’ai ya dawo ko kuwa tare da wata yake,sannan bai isa yayi dare ba,yana wuce 12 zai fara ganin kiran Daddyn sa ko da kuwa Daddyn nasa baya gari,ko me yayi in dai malan iliya ya gani to a kunnen Daddynsa, kuma sai an hukuntashi hukunci mai tsanani, ya zame masa kamar wani cctv camera sam ya hanasa sakat duk dan kawai idan ya kai wa Daddyn nasa rahoto yana bashi kud’i da kaya, and the most annoying part of it Daddyn nasa ya hanashi ko da hararar mallan iliya ne,balle wata banzar magana.

Yana wannan nazarin da murmushi akan fuskarsa ya k’arasa bakin gate d’in granpa ya fad’awa Daniel sak’on granpa sannan ya nufi main gate wajen mallan iliya. Daniel kasa b’oye zumud’in sa yayi , a take ya d’au waya ya kira wani abokinsa solomon wanda ya san irin halinsu d’aya, nan da nan kuwa Abokin nasa ya amince bayan Daniel ya fad’a masa nawa ake biyan malan iliya, yace masa ya jira zuwanshi nan da 2 hours yanzunnan zai sallami mamanshi da sistern shi ya taho.

Shikuwa Auwal yana isa maingate ya sanar da malan iliya sak’on granpa,tsabar mugunta dubu hamsin akace ya bashi amman yabashi dubu ashirin,kayansa kuwa kala uku ya bari ya d’iba waenda ya zo gidan da su,ragowar kuwa yace “ba zai d’auka ba ai ta wajen Daddynsa ya samu ta hanyar kai gulmarsa.” Sai da ya tabbatar ya bar gidan tukunna ya k’ulle kayayyakin da ya hanashi tafiya da su ya jefar a babban garbage bin na Estate d’in, ya koma ciki abinsa.

Cike da annashuwa ya nufi wani Triplex a cikin jerin gidajen estate d’in, kamar yadda kowanne yake gate d’inshi daban da compound haka shima wannan, knocking ya yi sannan ya d’an ja ya tsaya, cikin y’an seconds wani tsohon mutumi ya bud’e y’ar k’aramar k’ofar gefen gate d’in gidan ya d’an lek’o, ganin waye a tsaye ya sanya tsohon saurin bud’e k’ofar sannan ya d’an rissina yace
“Barka da yamma.”

“Lafiya”
kawai Auwal d’in yace dashi daga haka ya kutsa kai ya nufi cikin gidan wanda yake zagaye da flowers kala kala,an shafe k’asan compound d’in gidan da interlock, ta tsakiyan compound d’in kuwa wani k’aramin roundabout ne,ta left side na roundabount d’in wani k’awataccen garden ne wanda yake d’auke da su porch swing,hammock chairs da k’ananun kujeru domin hutawa sannan ga shuke shuke kala kala, ta right side kuma parking space ne, sai ta gaba hanyar shigowa,gate kenan,
sannan ta bayan roundabout d’in kuma anan ne k’ofar shiga gidan ta main parlour take.
Kasancewar gidan a zagaye yake..idan ka wuce main door d’in ka yi hanyar baya akwai k’aramar k’ofar kitchen ta shiga kitchen da wajen wanke wanke da d’an k’aramin fili.

Yadda ginin gidan nan yake haka gaba d’ayan gidajen estate d’in suke apart from gidan granpa ,wanda ya fi kowanne girma da tsaruwa.

Karasawa yayi ya shiga y’ar k’aramar varander da aka dan zagayeta da k’arafuna da flowers,sannan ya isa bakin k’ofar parlourn ya danna doorbell.
Wata farar budurwa wadda ba zata wuce shekaru goma sha biyar bace ta bud’e k’ofar,hannunta rik’e da waya kirar iPhone tana daddanawa tana murmushi,da alama chatting d’in da takeyi ya tafi da hankalinta, dan bata ma lura da waye ta bud’ema k’ofar ba,kawai ta juya ta nufi k’aton parlourn nasu mai d’auke da set d’in kujeru uku da katon dining area ,sai staircase biyu.
Juyawa Auwal yayi ya rufe k’ofar sannan da d’an sauri ya biyota ta baya yasaka hannu ya warce wayar,
da sauri ta juyo suna had’a ido da shi ta saki wani sassanyan murmushi.

B’ata rai ya yi sannan yace “da wa kike chattn haka??”
Ya yi mata tambayar yana maida idanunsa kan wayar domin ganin da waye take chattn d’in. Zaro ido ta yi sannan da sauri ta kai hannunta kan wayar da niyyar warcewa amman sai ya yi saurin kama hannun ya rik’e da d’an k’arfi har sai da ta yi k’ara,ganin k’ok’arinsa na ya karanta mata chat ne ya sanya a karo na biyu ta sake yunk’urin karb’ar wayar tata cikin shagwabarta tace
“Ya Auwal dan Allah ka bani waya ta.”

Murmushi ya yi ganin chat d’in nata ita da wata friend d’inta ne, tana bata labarinsa, expressing how much she loves him, har tana ce mata ta fi son smile d’insa saboda hakan yana fitar da dimples dinsa,sake fad’ad’a murmushin nasa yayi sannan yace
“D’ago kanki mana ,ungo wayarki.”
Shiru ta yi,sai hannunta d’ayan da bai rik’e ba da ta d’ago da niyyar karb’ar wayar amma sai ta ji ya had’a da nashi hannun da wayar ya rik’e, da sauri ta d’ago kanta ta yi kalar tausayi tace
“Da zafi fa,ka bani wayata mana.”

Yanayin kallon da yake yi mata babu ko kyaftawa had’e da murmushi ne ,yasanya ta yi saurin mayar da kanta k’asa.

Taku d’aya ya yi ya matso daf da ita,sannan ya yi k’asa da murya a hankali yace
“Da gaske kina son dimples d’ina?”
D’aga masa kai ta yi alamar ‘eh’. Sannan ta d’an yi taku d’aya ta yi baya
Sake takowa ya yi kamar d’azun ya matso da gefen fuskar sa kusa da tata yace “Tou bara in goga miki,kema ki zama mai dimple, kinga sai mu Haifa Yara masu dimples hud’u.”
Yayi maganar yana matso da gefen fuskarshi har yana gogar kumatunta,ba ta san ya akayi ba kawai ta ji ya sakar mata light peck a gefen fuskartata,
tana k’ok’arin matsawa taji ya yi saurin ruk’ota ta hanyar rik’e mata gefen cikinta.

“AAIMA!!!”
Suka ji an fad’a cikin tsawa,
Da sauri ta juyo,a tsorace.

Karkarwa jikinta ya fara yi sakamokon had’a ido da tayi da yayaynta ransa a mugun b’ace.
Sak’k’owa ya fara yi daga benen cikin sauri mai had’e da d’an gudu,yana tafe yana k’ok’arin kwance belt d’in jikin wandonsa, kafin ya k’arasa sak’k’owa kuwa har ya k’arasa zaro belt d’in ya rik’e ta a hannunsa,gadan gadan ya yi kansu.
A take Aiima ta fashe
da kuka tun kan a daketa,ta fara kiran “Mammy!!” da k’arfi.

Mammy da anty Adama da suke kitchen ba su ji shigowar Auwal ba amman tun lokacin da ARSHAAD ya kwala kiran Aiima sukaji suka fito da saurin su.
Ganin Arshaad ya yi kan Aiima da belt ne ya sanya Mammyn k’arasowa da sauri ta shiga gabanta ta tsaya tace”Arshaad meye haka?lafiyarka kuwa?”

Anty Adama kuwa ganin Auwal a tsaye yasa ta kafeshi da idanu kafin ta ce”mai ya faru?”
Sai a lokacin ma shi Arshaad ya lura da Anty Adama a wajen dan gaba d’aya idanunsa sun rufe ransa ya yi mugun b’aci!! Ya so ace yau ya damk’i Yarinyar nan wallahi da sai yayi mata mugun dukan da sai ta yi jinya tunda ya lura kunnen k’ashi gareta kuma ta raina shi, ba sau d’aya ba ya sha ja mata kunne ya hanata shiga harkar Auwal amman ta k’i yarda inda ace Aslam ne ya yi mata magana ya san da tuni ta bari……
Maganar Anty Adama ce ta katse masa tunani,jin ta sake cewa “Wai kai Auwal ba da kai nakeba?mai ya faru wai?me kuka yi mata take kuka??”
Saurin katse ta Auwal yayi yace”Nooo,Mom bani baneba!!”ya yi maganar cikin d’aga tafukan hannayensa biyu kamar za a yi arresting nashi yana tab’e baki,alamun shi fa ba ruwanshi,kafin
ya ci gaba da cewa “ta yaya zan sakata kuka? Zance na zo
fa.
D’azu da muka yi waya da ke kika ce mini kun dawo,shine nace bara inzo in ganta kuma in gaida Mammy,kin ganni daga office wallahi ko wanka banje na yi ba na zo nan mu gaisa,shine fa yana hango mu tare ya zaro belt ya yo kanmu zai dakemu!”

Kallon mamaki Arshaad ya tsaya yana yi mishi ganin yadda ya d’aure sa da jijiyoyin jikinsa,dukda kuwa yadda ya san halin Auwal sarai na iya juya al’amari….haka yake tun suna Yara kamar mace wajen iya makirci,kaf cikin mazan estate d’in sai da ya san yadda yayi kutun kutun ya kawar da kowa ya zama na right hand d’in granpa,yanzu haka shine MD , granpa ya d’aurasa a kan komai saboda shi sai end of the month yake shiga office , ko kuma in akwai Manyan Bak’in da suka zo ya kanje ya gansu, ko kuma wani important meeting,shima still Auwal d’in yana nan manne da shi baya barin kowa ya je jikinshi sosai, idan ma ya ga kuna shiri da granpa d’in to sai ya san yadda yayi ya had’a maka gurmi an maka fata fata.

“Wai Arshaad sai yaushe za ka bar wannan mugun abu daka d’aukarwa kanka ne?”
Ya ji muryan Mammy cikin fad’a, da alamun maganar Auwal ta yi tasiri akanta har ta kai ga b’ata mata rai.
Anty Adama ce ta kalli Arshaad da duk kunyarta ta rufesa,gashi shi mutum ne mai kawaici ba zai iya fad’i a gabanta abinda ya ga Auwal d’in yayi ba .
Takowa ta yi ta zo gaban sa ta tsaya sannan ta sa hannunta ta kamo nashi, cikin yin k’asa da murya tace
“Son, please ku zauna lafiya kai da d’an uwanka mana,kowa yana son had’in nan nasu shi da Aiima ko dan zumunci ya k’ara k’ulluwa, but if there’s anything da kake gani ya sanya baka san Auwal d’in a tare da sistern ka just name it,I promise zanyi putting into consideration and if kanada gaskiya I’ll support u 100%.”

“Bafa shi da wani reason da zai baki,kawai ke kin san halinsa ai tun suna Yara ba shiri sukeyi ba,abu kad’an sai fad’a,shine har yanzun basu san sun girma ba!!!ki barni da shi na san maganin sa”
inji Mammy.

Ganin bashi da niyyar yin magana ne yasanya Anty Adama ta cika hannunsa ta kalli Auwal tace masa “lets go””Mammy za mu k’arasa tattaunawa a waya.”

“Ok” kawai Mammy tace mata…bayan sun fita ne ta maida hankalinta ga Aaima wadda ke durk’ushe a k’asa har yanzun tana gunjin kuka,
Kamo ta tayi ta mik’ar sannan tace mata “goge hawayenki,daina kuka kinji auta wuce ki tafi d’akin ki.”

Da saurinta ta zo ta wuce ta gaban Arshaad dan gani takeyi kamar zai kamota.

Juyowa Mammy tayi ta kallesa sannan tace “Ko ba komai ni na haifeka atleast idan ka so abunda nakeso zan ji dad’i,ko dan Adama da zumuncinmu ya kamata ace ka yi hak’uri ka zauna lafiya da d’anta.
Dukda na san taurin kanka da kuma yadda ka raina ni ba lalle ya bari ka yi abinda nakeso ba
amman ni dai ba zan gaji da fad’a maka gaskiya ba.”

tana gama fad’in haka ta wuceshi…har ta d’an tsaya kamar za ta sake yin magana sai kuma ta juya ta nufi hanyar kitchen,suka barshi a tsaye a wajen.....

Su Auwal suna shiga main parlour ya yi hanyar staircases d’in da yake a hannun dama,da alama ata nan side d’insa yake.
“We’re not finished.”
Ya ji muryan Mom d’insa.

Juyowa ya yi ya kalle ta sannan yace “Let me freshen up first,Ina zuwa .
Ya fara hawa stairs d’in da d’an sauri.

“What did u do??”
Ya ji ta sake tambayar shi.

“A peck.”
kawai yace mata, da ga haka ya ci gaba ta tafiyar sa ba tare da ya juyo ba.

BULAMA✍️

So da Buri
Free Book
04

A nan ya tafi ya barta a tsaye kamar wata statue, kana ganin fuskarta ka san ranta a b’ace yake, ita sam! ta kasa gane kan Auwal kwata kwata,bata son halayyar nan tashi, kalli yanzu k’iri k’iri ya had’a uwa da d’anta fad’a, shikuma Arshaad ta tabbata kunyar ta ce ta sanya ya k’i cewa komai,gashi
Daddy ya rok’eta akan dan Allah su taru ita da shi su dinga rufama d’ansu asiri…shi kad’ai Allah ya basu su daina yayata wasu halayyarshi da kansu a cikin family, domin kuwa duk ranar da aka yi rashin sa’a granpa ya ji to tabbas kashin Auwal ya bushe….
Tana cikin wannan tunanin ta ji an dafa ta…tana juyowa suka had’a ido da Mijinta Alhaji Yusuf MT
murmushi ta yi kafin tace
“Daddy yaushe ka dawo?”

Sai da ya d’an k’ura mata ido kafin yace “Auwal ne ko?”

Murmushin ta sake yi sannan tace”amsa tambaya da tambaya, are we??”

Sauk’e wata nannauyar ajiyar zuciya ya yi kafin ya fara magana”Ta windown kitchen na hangoku Ina waya da doctorn ABBA, shine na fita ta k’aramar k’ofa na rufe na tsaya a k’aramin compound saboda bana son Auwal ya ji ni.
Kin san yadda suke shi da granpa,ba k’aramin aikin sa bane ya kwashe komai ya fad’a mishi
Tunda ya san in dai da granpa a case babu abinda zan iya yi masa.”
Shiru yayi da alamun damuwa a kan fuskarsa kafin ya sauk’e ajiyar zuciya yace
“Adama akwai matsala fa, don sun sake yin wani fad’an da granpa har ya ma fi na last time, sannan shi kuma ya sakawa kanshi damuwa over gashi yanzu har ya kusan shiga next stage.”

“Innalillahi wa inna ilaihirrajiun”shine abinda Mom tace idanunta suna kawo kwallah kafin ta kalle sa sosai tace
“To ai ni da ka bari Auwal d’in ya ji ya fad’a ma granpa d’in watak’ila hakan ya sanya shi ya d’an sauk’o daga fushin.
Na ga kwana biyun nan ma ai kamar yad’an yi sanyi ai ba kamar da ba,ko?”

D’an murmushi Daddy ya yi tukunna yace”babu fa abinda ya chanja daga halin granpa,kawai dai kwana biyun ba a samu wanda ya tab’o sa bane ba shiyasa kika ji shiru…d’azun fa malan iliya ya kirani ya ke ce mini Auwal ya fatattake sa,da na tambayi drivern granpa d’in yace mini shi granpa d’in ne yace a kori mallan iliyan d’azu daga dawowarsu daga meeting,wai dan ya bar bakin main gate ya tafi siyan agwaluma.”

“Allah ya kyauta”
Shine abinda Mom tace, sannan ahankali tace “wai menene ma to abunda ya taso da fad’an nasu shi da Abban??
daa fa har muna murnar almost 2 years lafiya k’alau tsakaninsu,shima kuma Abban ciwon nasa ko tari babu.”

Sai da Daddy ya d’an furzar da numfashi tukunna yace”Wai mafarkai yakeyi da Maryam! da jariri a hannunta,tana kuka tana cewa ya zo ya taimaketa, abun ya kai 3 months yace kullum in ya kwanta sai yayi shinefa ya d’aga hankalinsa…
Da farko,Dad ya samu ya fad’a mishi. Shikuma Dad yace mishi ya yi ta addua kawai…
shine fa tsabar ganganci kawai ya je ya tunkari granpa da maganar..
akan wai yana so yaje ya ganta,ya tabbatar babu Yaro a tsakaninsu,saboda mafarkan da yake ta yi.”

Ba shiri Mom ta zaro ido waje sosai kafin ta yi k’asa da murya tukunna tace”me granpa d’in ya ce??”

“Cewa za ki yi me ya yi masa,ba me yace ba!
In banda abun Abba kai da ka san mutumin nan yanata fushi da kai for morethan 24 years ko ga miciji ba kwa yi da shi, amma shine zaka kwashi k’afa ka je ka tunkare sa da irin wannan zancen?
Ni wallahi Adama nima na fara tunanin ko dai asiri ne matar nan ta yi masa,saboda ki duba kiga yadda he’s willing to risk everything just to talk to her again. Dukda irin bak’ak’en maganganun da ta dinga rubuto masa har da fa threatening nashi da kotu fa ta yi…
Daga k’arshe fa idan ta aiko da sak’o ba ya nuna mana! daina nuna mana yayi ni da Dad
Allah kad’ai ya san irin maganganun da suke a ciki
Shikuma a wannan lokacin kullum cikin bata hak’uri yakeyi yana aikawa.
Da kyar granpa ya samu ya rabasu, shine yanzu yake son tada zaune tsaye, shi ko ta jikinsa da lafiyarsa ma bayayi, gashi yanzu granpa ya yi masa horo mai tsanani…..
..Kinga da farko ya sallame shi a duk wani company da kika sani namu a yanzu babu Abba a ciki,sannan ya hanashi share d’inshi. Kuma ya bashi notice akan ya bar masa estate d’inshi kar ya k’ara ganin shi ko y’ay’ansa.
Yace kuma duk wanda ya bashi hak’uri sai ya had’u da tsananin b’acin ranshi,hatta gramma.”

“Ya subahanallah”
shine abunda Mom ta fad’a
sannan a hankali tace “bara inje wajen Zainab.”

“To” kawai yace mata ya juya ya nufi dining area ya nemi guri ya zauna ya fara zuba abinci,
kana ganin fuskarsa ka san yana cikin matsananciyar damuwa.

Fitowa ta yi tana zancen zuci ta k’arasa bakin gate sannan ta fita ta k’aramar k’ofa,ta nufi d’aya daga cikin gidajen tana d’an sauri,tana isa tayi knocking,kamar kowanne gida nan ma mai gadi ne ya zo ya bud’e mata,ya gaidata ta amsa sannan ta shiga.
Tana shiga ta hango wata k’atuwar moving van ga jakankuna a ajiye a waje da boxes, sannan ana ci gaba da fitowa da wasu.
K’ara saurin tafiyar tata ta yi ta nufi hanyar k’ofar shiga main parlourn wadda ke nan a wangale anata shige da ficen kwashe kaya.
Da sallama a bakinta ta shiga,
tana shiga ta hango wata farar mata zaune a kan 2sitter na d’aya daga cikin jerin kujerun falon,matar ta zabga uban tagumi,kana ganin ta ka san tana cikin damuwa sannan tayi nisa a tunani.
K’arasawa Mom tayi kusa da ita sannan ta dafa ta,ganin kamar ma ba ta san ta dafa tan bane ya sanya ta kira sunanta”Zainab!“
Firgigit!! Ta yi ta juyo,suna had’a idanu da Mom kuwa kamar jira takeyi ta fashe da kuka,sannan ta kamo hannayenta duka biyun kafin ta fara jujjuya kai ahankali tana kallonta tace “Adama inata kiranku yau kwana biyar wayanki baya tafiya,komai ya zo mini k’arshe
kashina ya bushe!! I never saw this coming!!
Shikenan na san yanzu zai yi finding out kum......”

Mom bata bari ta k’arasa ba ta yi saurin zare hannunta wanda ta rik’e ta yi amfani da shi
wajen toshe mata baki sannan ta juya tana kallon falon tana rarraba ido cikin fargabar kar wani ya jiyoso.
Ganin da ta yi ba kowa a falon masu kwasar kayan ma duk sun gama na k’asa sunyi sama ne ya sanya ta kamo d’ayan hannaunta da har yanzu yake cikin nata ta mik’ar da ita sannan ta jata suka nufi d’aya daga cikin d’akunan parlour.

Sai da Mom ta tabbata ta saka key,tukunna ta juyo tace
“Yanzu menene abun yi?”
Share kwallarta Zainab ta yi sannan tace “Granpa ya koremu shiyasa kikaga anata kwash..”
“Na sani“ Mom ta katse ta
sannan tace “Daddy ya fad’a mini komai.”
Shiru Zainab tayi, sannan ta jingina da bango ta d’aga kanta sama ta rufe idanunta a hankali tace “In dai muka bar gidan nan,kin san cewa babu abunda zai hana Abba bibiyar Maryam ko?
Saboda ya kasa yarda da takarda har yau,kin san
cewa ko a kwanakin baya dama na gaya miki Ina ganin kokwanto a fuskarsa….ita kuma mayyar gashi yanzu har a mafarki zuwar masa takeyi.”

Bud’e idanunta ta yi ta kalli Mom sannan ta ci gaba da cewa “4 days ago fa yana tashi yace shi wajenta zai je, ya gaji da wannan mafarke mafarken,da ya je wajen granpa suka yi fad’an nasu da suka saba,dan bai samu an goya masa baya ba shine tun a chan ya zube,sai kwasar shi aka yi ,akai asibiti da shi.
Kwanan mu d’aya da wuni bai san inda kanshi yake ba ana fama.”
Shiru ta yi kafin ta ci gaba da cewa “Adama granpa shi kad’ai yake iya takawa Abba burki akan Matar nan yanzu ya bashi freedom!!Saboda wannan abun fa da akayi da
granpa da mutane ne suke ganinshi as punishment amman a wajen Abba freedom ne.
Can u imagine in 2 weeks time fa granpa yace “mu bar gidan nan amman Abba a jiya da sassafe ya kira masu penti aka fara pentin gidanshi na kundila yanzu kinga yau da safe yace mufara parking, na tabbatar ko kammala pentin ba a yi ba. Atleast ai ya jira ya dawo daga asibiti ko?
Ya samu ya d’an warware maybe b4 then ma granpa ya saukkk’o.”

Murmushi Mom ta yi kafin tace
“Haba Zainab,ke har yanzu ba ki san waye uncle d’inki ba ne?
If there’s one thing that I’m sure of shine granpa ba zai goge decision d’inshi ba sai dai in ya sassauta,yanzu mafita itace abar nema ba wai wannan dogon labarin ba
Dan ba ke kad’ai ba hatta ni da Mammy sai mun raina kanmu idan zance ya fito….
Na san granpa Hates Maryam with passion
But what we did is something da bai kamata ace mu bari a kamamu da laifinshi ba!.”

Ajiyar zuciya Zainab ta sauk’e kafin ta juyo ta kalli Adama sannan ta kama hannuwanta biyu tace” ki taimakeni…
at any cost kar mu bar gidan nan,you always come out with the perfect solution, do something. Har yau ban samu soyyayyar Abba ba,I’ve been trying my best wajen ganin na yi winning nashi kuma na san I’m almost there but in dai
matarnan ta dawo cikin rayuwarsa komai lalacewa zai yi.”

Shiru Mom ta yi tana d’an tunani ta kusan 5minutes sannan ta yi murmushi tace mata “kawo kunnenki kiji wata magana”
Matsowa ta yi sannan ta fara rad’a mata maganar…..
Da farko juyowa ta yi ta kalleta da alamun mamaki mamaki sai kuma ta juya ta ci gaba da sauraronta ahankali ta fara murmushi....

“Ummi!Ummi!!Ummi!!!”
Suka ji murya ana kwala kira a parlour.
Da sauri Zainab ta juyo tace inaga ga su shuraim sun dawo d’azu suka tafi asibiti.”
Har ta kai bakin k’ofa ta murza key d’in za ta fita sai kuma ta juyo ta kalla Mom tace mata
“Kin tabbata babu matsala?”
Murmushi mom ta yi sannan ta d’aga mata kai,alamar’eh.’
Juyawa tayi ta fita itama ta biyo bayanta suka fice a d’akin.

Wani Yarone yake shigowa cikin parlourn fari tass da shi kyakkyawa,suna had’a ido da Zainab ya kalli sama yana kallon d’ayan Yaron da ba zai wuce 10 years ba yanata hawa Bene yana kwala kiran “Ummi!!” ,
da d’an k’arfi ya ce “Sudais!”
Da sauri wanda aka kira da sudais d’in ya juyo yana kallon d’an uwanasa wanda juyowar da ya yi ne zai sanya ka fahimci ashe twins ne dan komai nasu iri d’aya ne.

Nuna masa Zainab ya yi sannan yace “ga Ummin nan.”
Da saurin sa kuwa ya sauk’o ya zo ya rungumeta kafin ya d’ago kai yacee mata “Ummi Abba ya dawo,Dr yace ya warke!suna waje shi da ya Arshaad yanzu zai shigo da shi.”

bai gama rufe bakinsa ba kuwa Arshaad ya shigo
Shi da wani mutumi kyakkyawan gaske,dogo d’an kakkaura amman bashi da k’iba kwata kwata,fari tas da shi, kyakkyawar fuskarshi cike da tsananin kyau haiba da kwarjini ‘ABBA’ ya rik’e hannun Arshaad d’in na dama shikuma Arshaad d’in ya ruk’o kafad’arshi da dayan hannun for support suna tafiya a hankali,kana ganin mutumin ka san bashi da lafiya.
A hankali suka k’arasa Arshaad ya kaisa har kan d’aya daga cikin kujerun parlourn ya zaunar da shi tukunna ya juyo ya kalli su Ummi ya gaida su.
Sai da suka gama gaisawa sannan Ummi ta k’araso kusa da su tace “Abba ya jiki?
Yaushe aka sallameka?
Mai yasa baka kirani ba?”

D’an gyaran murya Arshaad yayi, saida ta d’ago ta kalle sa sannan a hankali yace
“Ummi Dr yace kar a dameshi fa,and yana buk’atar Hutu,sosai!.”

Juyawa ta yi ta kalla gefe ta d’ayan staircase d’in yadda aketa sak’k’owa da kaya ana shige da fice kafin tayi murmushi tace “To Arshaad yanzu daka kowoshi ka ga alamun rashin hayaniya anan d’in?
Kalla fa parking aka hau yi yau d’innan gadan gadan,nima Ina dawowa daga asibitin na tarar da su suna jirana a gate da na
tambaya sukace wai Abban ne yace su zo su fara kwashe kaya suna kaiwa sabon gida,
yanzu saboda Allah idan bai ji da lafiyarsa dan kanshi ko ni ba,ai ya duba Yaran nan”ta yi maganar tana nuna su Sudais tare da share kwallar da ta zubo mata.

A hankali Abban ya yi d’an tari sannan ya gyara zamanshi tukunna yace
“Arshaad.”

“Na’am Abba.”
Arshaad d’in ya fad’a cikin girmamawa ya d’an rankwafo ta saitin shi.
Sai da ya kuma yin
tari sannan yace “Ka duba moving van d’in dake a waje akwai boxes da Ghana most go a ciki ka d’auko empty ones d’in dayawa,ka shiga parlourna da d’akina duk wani abu ka had’a su ka tattare,sannan ka rubuta sunan items d’in da suke ciki a jikin kowanne box da makar saboda kar ya bada wahalar tantancewa idan anje chan.
Ka yi sauri idan ka gama za su shiga yanzu su kwashe furnitures, naga har sun kusan gama chan side d’in.”
Ya k’arashe maganar yana d’an tari.

“To Abba”
shine abinda Arshaad yace,daga haka ya nufi waje domin d’auko boxes d’in.

Juyawa Abba yayi ya kalla su Sudais sannan yace “kuma ku je ku d’auko ku had’a naku kayan.”

Har ya gyara zaman ya d’an jingina ya lumshe idanunsa, sai kuma ya d’ago ya kalli Ummi sannan a hankali yace mata
“Za ki bimu ko a nan za mu barki!”
Yunk’urawa ta yi za ta yi magana ranta na sake b’aci,
Da sauri Mom wadda ke a bayanta ta rik’o hannunta ta d’an matse alamar ta yi shiru.
Shurun kuwa ta yi sannan Mom ta yi gaba tace
“Abba sannu da jiki, Allah ya sa kaffara ne.
Bara muje saman in taya ta had’a kayanta. Idan kana buk’atar wani abu muna sama sai ka kiramu a waya....”

D’aga kanshi ya yi alamar ‘to’
sannan ya mayar da idanunsa ya lumshe ya koma ya jingina a jikin kujerar.
SHARE PLS.
BULAMA✍️

So da Buri
Free Book
05

Jan hannunta Mom ta yi sannan suka yi sama,suna shiga d’akinta tace
“Adama ba fa inda zanje sannan suma babu inda za su je.”

“Na sani”
Shine abinda Mom tace sannan ta fara dube dube kamar tana neman wani abu.
Drowern gaban mudubi ta kai hannunta ta bud’e,aikuwa ta ci karo da abinda take nema..da sauri ta d’auko littafin da ta gani da biro sannan tace “oya d’auko mini takardar gidanki wanda ya baki in kalla signature da wani note haka da ya tab’a rubutawa.”

D’an tsayawa Ummi ta yi tana kallon ta da alamar tsoro a fuskarta.

Ganin haka ya sa Mom ta kawo gabanta ta tsaya sannan tace
“I’m just trying to help,ba mu da ishesshen lokaci,ki daina
dogon nazari.
Besides har yanzu ukune akan ki so don’t worry about one ballantana ma bashi da masaniya,so babushi a lissafi.
Kowa ya sani a estate d’innan kece weakness d’in granpa,ki
duba ki ga abubuwan da yake yi just to make sure u stay happy..I can assure u ba zai bari Abba ya tafi ko Ina ba idan ya ga wannan.”
tayi maganr tana nuna mata takardar da ta yaga daga jikin book d’in.

Shiru Ummi ta yi kafin tace
“Adama I love my husband, banaso in shiga tsakaninshi da mahaifinsa..”
Wannan karon tsaki Mom ta yi sannan tace”Zainab kin fara bani haushi wallahi zan yi tafiyata, shiga tsakani kuma na nawa??
Waye ummulaba’isin fad’an nasu?sai da abu ya zo gangara za ki fara tunanin tsame hannunki?
To bari kiji! ta inda akabi aka hau ta nan ake sauk’a sannan
na san Dr Abba farin sani If things get out of control zan yi paying nashi ya maka masa case na memory loss, a ce yayi for a day ne,
a time din kuma yayi ta misbehaving,sai mu ce a lokacin ne yayi shi kansha kenan bai san yayi ba. Dan mutumin da ya kwana ya wuni bai san inda kansa yake ba ai zai yi morethan this,kuma babu wanda ya isa ya musa.”

Da sauri Ummi tace”ok ok”sannan ta nufi wardrobe d’inta ta d’auko key a k’asan tulin kayanta sannan ta saka key d’in a jikin wani d’an k’aramin locker wanda yake nan ata k’asan kayannata ta murza mukullin ya bud’u. Wani suitcase ta d’auko ta yo kan gadon da shi,a tare suka hau bincikawa har sai da suka d’auko wani file da wata envelope.
File d’in takardun gida ne, envelope d’in kuwa da suka bud’e ta wani had’add’en rubutu ne ya baiyana a cikin da alama wasik’a ce .
Zama Mom ta yi a kan gadon sannan ta saka wannan wasik’ar a gaba ta yi shiruu…ta kai kusan 2 minutes tana k’are mata kallo kafin ta ajjiye ta a gabanta tukunna ta hau rubutu akan wannan blank papern data yago….exactly handwriting d’in irin na wannan wasik’ar takeyi.
Ta d’auki y’an mintuna tana rubutawa kafin ta d’auki dayan file din ta bud’o dai dai wajen signature ta kalla da kyau sannan ta ajiye ta yi irinta a k’asan takardaar da ta gama rubutu a kai.
Tashi tayi daga kan gadon sannan ta juyo ta kalli Ummi tace mata
“Done!!”

Mik’a hannu Ummin ta yi ta karb’a ta karanta sannan ta sauk’e ajiyar zuciya kafin tace
“Yanzu ta Ina zan wuce??
kin san fa yana falo.”

“D’auko mayafinki”
inji Mom.
Cikin wardrobe d’inta ta bud’e wajen mayafai, sannan ta jawo abinda hannunta ya kai kai .
Warewa ta yi tana shirin saka hijabin Mom tace a’a bani nan zan saka a cikin nawa maya fin in fita in yaso sai ki sak’k’o daga baya ki yi kamar kin shiga kitchen,ni kuma zan jiraki a k’aramin compound ta baya,sai ki fito mu wuce.”
Har ta juya za ta fita,sai kuma ta dawo ta k’ara rad’a mata wata magana sannan ta fice.

Yadda Mom d’in ta tsara hakan kuwa akayi…

Bayan sun fita daga gate d’in gidan suka nufi na granpa.
Suna zuwa daniel ya gaidasu suka shige suka isa k’ofar main parlor.
Suna shiga kamar kullum sukaga ba kowa,shiruu sai k’arar ac
Ganin hakane ya sa suka nufi kitchen a tunanin su ko za su ga granma ta yi musu iso,amman nan d’in ma ba su sameta ba,sai masu aiki.
Ganin suna b’atawa kansu lokacine yasa Mom ta d’auko wayarta, ta kira gramma,bugu biyu ana ukun ta d’auka.
“Assalamu alaiki, Adama.”
Aka fad’a daga d’ayan b’angaren.
Cikin girmamawa mom tace
“Ameen wa alaiki assalam,Ina wuni gramma”

“Alhamdulillah”
Shine abinda gramma tace.

Cikin ladabi Mom tace”daman yanzu Zainab ta zo ta sameni akan wata magana,shine muke son ganin granpa,ban sani ba ko yana nan?.”

“Yana nan.”Ta ce,daga haka
ta katse kiran.

Kusan mintuna talatin suka yi a kitchen d’in, har sun fara gajiya sukaji k’arar bud’e k’ofa.
Da sauri suka fito a kitchen d’in dai dai k’ofar da take kallon kitchen d’in aka bud’e sosai wata farar tsohuwa ta fito,bata da tsayi sosai amman tanada k’iba,idanunta sanye cikin medicated eye glasses, tana sanye cikin wata royal blue d’in atamfar super xclusive
ta yi d’aurinta irin na tsoffi. A hankali take tafiya tana tunkaro k’ofar kitchen d’in tana yin mitsi misti da idanu alamun so take ta fahimci su d’inne a wajen domin kuwa dudda glass d’in ba kasafai take iya hango abu idan yayi nesa sosai ba.
Gane hakan da suka yi ne ya sanya suka yi saurin k’arasawa inda take sannan suka d’an rissina suna sake gaida ita. Cikin kulawa ta amsa sannan tace “ina fata dai abu mai muhimmanci ke tafe da ku ba shirme ba,dan kar ku je ku yi ta shiririta,kun san ba yawan son surutu yake ba,yanzu hakan ma da kyar ya yarda zai ganku..”
Takardar hannunta kawai Ummi ta mik’a mata.
Kallonta gramma ta yi sannan ta sa hannun ta karb’a takardar ta fara dubawa….gyara glases d’in idanunta ta yi da kyau cikin zaro ido kafin ta d’ago ta kallesu sannan tace
“Shi Yakubun ya baki wannan???yaushe!??”

K’asa Ummi ta yi da kanta sannan a hankali tace
“Shekaran jiya”
Cikin fad’a gramma tace”kuma to me kika tsaya yi tun shekaran jiya baki zo nan ba?
Ai cewa yayi ki tafi wajen iyayenki,ko kina da iyayen da suka fi mu ne?”.
Da sauri Ummi ta girgiza kai tana share hawaye.
Cikin tausayawa,gramma ta kamo hannunta ta rungumeta tana bubbuga bayanta,sai da ta yi shiru sannan tace su je wajen granpa d’in.

Ta cikin parlourn da gramma ta fito suka shiga,suka bi ta wani had’add’en staircase suka isa wani tafkeken parlour sannan suka sake bin bene kafin su iso wani had’add’en parlour.

A tsaye suka hangosa gaban wani k’atoton glass wanda gaba d’aya bangon wajen glass d’in ne ya cinye…ya
juya baya yana kallon glass d’in wanda ta cikin k’atoton glass d’in kana iya hango har compound d’in estate d’in.

Waje gramma ta nuna musu sannan ta k’arasa gabansa ta mik’a mishi takardar,kafin ahankali tace”ga abinda yake tafe da su”.
Ya kusan 2 minutes tukunna ya ce “Read it loud”

Cikin nutsuwa grmma ta fara karantowa.
“Ni Yakubu Umar Farouk mai turare, na saki matata Zainab Umar Farouk mai turare,saki d’aya…dalilin kuwa Ina gudun shiga hakkin aure domin na kasa bata kulawar da ta kamata da waje a zuciyata
ta koma gidan iyayenta ta ci gaba da zama,nima zan tafi nawa gidan, idan ta samu miji ta yi aure.”

Shiru kakeji d’ip! Kamar ba halitta a parlourn.
Da farko tari Ummi ta fara a hankali,chan kuma sai ta farayi da k’arfi har da kamar kakarin amai kafin a hankali ta sulale daga zaunen da take akan kafet ta kwanta a wajen.

“Ya subahanallah jini!!!”
shine abinda suka ji Mom ta fad’a….da sauri gramma ta yo kansu,itama tana zxuwa ganin alamun jini jini a cikin bakinta yasa a rud’e ta ce
“Adama mai ya faru?innalillahi wa inna ilaihirrajiun, maza d’auko ruwa ga firij chan ki zo ki yayyafa mata…”

Ruwa aka d’auko aka fara yayyafa mata amman a banza sai ma jinin da yake ta biyo yawu yana dalala a k’asa….da sauri gramma tace maza kira wani a cikin samarin nan ya zo a taimaka a kaita asibiti,da sauri mom ta mik’e sai kuma ta tsaya tace “gramma duk basa nan na manta,amma d’azu naga Dr ya zo duba Abba,in kirashi??”

Da sauri gramma tace
“Eh kirawoshi,Allah ya kawo sauk’i ma ai.”

Nan ta fita gramma kuma ta cigaba da jijjiga Zainab tana tofa mata addu‘o’i.
Cikin mintunan da basu gaza ashirin ba Mom ta dawo Dr na biye da ita,suna zuwa aka gyara wa Ummi kwanciya anan kan kafet din Dr ya shiga duba ta da kayan aikin da ya shigo da su.
D’agowa ya yi ya kalli Mom sannan yace”tun yaushe ta fara?”

“Bata tab’a suma irin wannan ba gaskiya,sai dai tarin jini kuma ba ya zuwa sosai kamar na yau.”

“Tun yaushe ta fara?”
Doctor ya sake jeho mata tambayar ba tare da ya kalleta ba dan ya duk’ufa ya tarkata hankalinshi duk a kan Ummi burinsa kawai ya ga ta farfad’o.

Kwanaki ta yi a gaba na har sau biyu,na yi mata magana tace “wai ta je absibi ance ba komai.Yau kuma sau uku kenan har da wannan,shima da naga ta yi ta sakeyi na tamabayeta tace mini ba komai fa.”

“Unhm“
Shine abunda Dr yace yana zuk’o wani ruwan allura sannan ya saita jijiyan hannun Zainab d’in ya juye mata shi a ciki ya ci gaba da bata taimakon da ya kamata.

Bayan wasu y’an mintuna…
A hankali take bud’e idanuwanta waenda suka yi jazir…da sauri gramma ta k’araso gabanta ta fara k’ok’arin mik’ar da ita tanata faman jera mata sannu,Allah sarki gramma duk ta rud’e.

“Doctor mai ka fahimta yana damunta???”
Granpa ya yi mishi tambayar yana dogara sandarshi yana mai k’arasowa wajen.

Mik’ewa tsaye ya yi sannan ya zare farin glasses d’in idonsa ya d’an mutsitsika idon ya maida glass d’in kafin yace
“Heart d’inta ke da matsala, and da alamar ya yi serious gaskiya tunda har ga jini,ban san dalilin da ya sanya ta b’oye ba ta gayawa kowa ba,but this is very serious,idan ba damuwa yanzu zan tafi da ita mu yi ECO, saboda mu san matakin d’auka,dan ba a d’aukar issue na heart irin wannan likely.”

“A wanne asibiti za a sameka?”
Granpa ya sake mishi tamabayar.

Card d’insa ya mik’awa granpa mai d’auke da suna da address na diagnostic center d’inshi sannan yace “nan waje nane it’s a private place.
I’m a consultant a AkTH,idan hankalinku ya fi kwanciya da chan sai ayi mata a chan d’in, dai nasu zai d’auki time kafin a gama.

“Za a sameka a chan (nakan)nan da 1 hour,get every thing ready”

“Ok sir,”shine abinda Doctor yace sannan ya juya ya fita.

“Let me show him the door” Mom tace sannan ta bi bayanshi.

A hankali ya k’arasa takowa inda suke kafin ya kalli gramma yace mata
“Leave us”
A hankali gramma ta mik’e ta juya ta fita.

K’arasowa yayi ya zauna a kan kujerar da take zaune a gefenta kadan a kan kafet sannan yace
“Since when kika yi realizing baki da lafiya??”

“2 years ago”tace.

“Wa kika fad’awa?”

“Ba kowa.”

“Mai ya yi causing abun?”

Shiruu ta yi wannan karon.

Zan b’ata miki rai Ummi,kin san ba na son kame kame da kyaliya.

Hawaye ta share kafin tace
“Abba ne”cikin sheshshek’ar kuka.
Tari ta fara yi sai da ya d’ab tsagaita sannan ta ci gaba da magana
“Ba ya bani time d’inshi,kullum cikin zancen Maryam yake,i tried very well inga na daidaita relationship d’inmu amman na kasa,yak’i ya bani had’in kai
at the end ma gashi ya zo ya rabu da ni gaba d’aya.
Inaji yana waya da Abokinsa wai ya san idan ya had’amu ni da Maryam ranar lahira da shanyayyen b’arin jiki zai tashi…..tunda yanzu ya samu chance d’in da zai iya maida ita…..kuma wai yana jin tausayina,gara ya sauwak’e mini inyi aure nima In samu wanda zai iya bani kulawa tun kafin lokaci ya k’ure.

Granpa it’s like har yanzu suna tare a yanayin maganarsa.”

Tana kaiwa nan ta fara tari irin na marasa lfy,abun tausayi.

A hankali ta ji granpa ya dafa ta sannan yace “ki huta,ya isa haka.”

Waya ya d’auka ya fara lalube sannan da kyar ya nemo numbershi,yayi mamaki da ya samu number dan ya jima basa waya…ko abu zai fad’a mishi sai dai ya gayawa Dad ya fad’a mishi, ko Abban ya kirashi domin ya gaidashi baya amsawa.
Sometimes kuma yayi rejecting
shiyasa tun yana kira har ya zo ya daina shima.

Abba yana zaune Sudais yanata zuba masa surutu ya ji k’arar wayarshi,zaro ta yayi daga aljihun gaban rigarshi ya kalla screen d’in, k’ara kalla yayi ya d’ab bud’e idonshi…ganin da gaske ne yasa yayi saurin d’auka had’e da toshe wa Sudais baki
“Assa...”
Kafin ya k’arasa sallamar ya ji ance
“Ina falona,ka sameni yanzu”
Kit!! Ya ji an kashe wayar.

Mik’ewa yayi a take sai dai da kyar k’afafuwansa suka iya d’aukar sa saboda sanyi da rawar da suke yi dama kuma ga yanayin rashin lafiyar da yake ciki.
Ajiyar zuciya ya sauk’e,ya tattaro dukkanin kuzarinsa sannan ya fara tafiya a hankali domin amsa kiran mahaifin nashi.

Gaban Ummi ne ya fara dukan uku uku gashi Mom bata kusa…dukda sunada mafitar abinda za su fad’a amman hakan bai hanata jin tsoro ba,da kyar ta samu ta saisaita kanta gudun kar granpa ya fahimci wani abu,dukda ta san shi ba mutum ba ne mai zurfafa bincike iyakar abinda akai akan idanunsa da shi yake aiki sannan bashi da time d’in bibiyar abinda bai shafeshi sosai ba above all ya yarda da Ummi yana ji da ita sosai ba ya son abinda zai b’ata mata rai ita kad’ai ce in abu ya shafeta yake sawa ya sauk’o daga dokin zuciya…….tana cikin wannan tunanin suka ji sallamar Abba.

Granpa ne ya amsa sannan yace”k’araso ciki.”

Shigowa ya yi, sannan ya k’araso inda ya ga Ummi a zaune ya nemi guri ya shima ya zauna a d’an gefenta kad’an. “Barka da yamma”
shine abinda Abba yace da granpa, kanshi na kallon k’asa.

Juyowa granpa ya yi ya kalleshi sannan yace
“Ai ban yi tunanin har yanzu Ina da darajar da zaka gaidani ba.”
Bai jira jin abinda zai ce masa ba ya d’aura
“Bara in baka wani gajeran labari,dukda na san ka sani amman bara in sake maimaita maka.”

Mik’ewa ya yi yana dogara sandarsa ya koma wajen da su Ummin suka shigo suka sameshi d’azu ya tsaya yana kallon waje,a hankali ya fara magana...........
…….
“Asalina d’an k’asar Chad ne, mahaifin mahaifiyarmu ma haka,saidai mahaifiyarta ce ta fito daga yankin Niger,Agadaz.

Mu biyu iyayen mu suka haifa a duniyar nan,da ni da d’an uwana…gudun hijira ya sanya muka baro k’asarmu ta haihuwa,domin a lokacin har kakanninmu sai da aka kashe da kyar muka tsira,kasancewar Fulani bamu da yawa a yankin ya sanya aka yi galaba akanmu.
A lokacin inada shekaru tara a duniya d’an uwana kuma yanada 11,tun a hanya na lura mahaifin mu bashi da lafiya,da na tambaye shi sai yace mini gajiyar tafiya ne..
Yanayin gudun hijira ba abu bane mai sauk’i don ko ruwan da mutum zai sha ma aikine.
Mahaifin mu ya zab’a mu bi ta Agadaz domin mu duba ko zamu had’u da dangin mahaifiyar mamana ko zasu taimaka mana akan mu tafi garin da bamu san kowa ba. Mahaifiyarmu ta so yin tirjiya akan gara mu bi ragowar mutanen rugarmu waenda suka yi saura, saboda ta san a wannan lokacin danginta kowa yayi nashi wurin sannan y’an uwanta idan ma za ta samu yanzu mutun d’aya ce, wadda take aure a chan, don mahaifiyar tata su uku aka haifa a gidansu kuma itace auta,Babbar yayyarsu a ghana take aure.
K’in yarda da zancenta da mahaifinmu ya yi ne ya sanya
muka nufi Agadaz
Amma sai muka yi rashin sa’a muna zuwa aka tabbatar mana ciwon k’afa ya kamata an kaita Yemen neman magani.
Da kyar wani makwafcinsu ya bamu gurin kwana da abinci mukai wanka da safe muka nufi marad’i,don Yemen akwai nisa sannan babu ko sisi a wajenmu, dayake mahaifinmu ya tab’a zuwa daura ya sanya shi cewa mu zo daura ko marad’i inyaso idan ya d’an samu aiki yayi ya tara kud’i daga baya sai mu tafi Yemen d’in mu dubota.
kasancewar hanyar Sahara ce ko ina,yasanya muka wahala babu ruwa babu abinci kowannenmu idan ka kalla
a wahale yake
Shiyasa da zaran mahaifinmu ya nemo d’an abinci ko abun sha sai ya bamu mu ci yace mana shi ya ci a hanya saboda yana gudun kar wani abun ya samemu dan a ganinsa laifinshi ne saboda babu yadda mahaifiyar mu batayi da shi ba akan mu bi tawagar y’an hijira mu gudu tare amman ya k’i.

A lokacin naga amfanin ilimi domin da muka k’arasa marad’i babu wanda yake jin yarenmu, sannan muma bama jin nasu, sannan bama jin turanci ballantana mu yi communicating da su.
Hakanan muka kwana a y’ar kasuwarsu da kyar mai k’osai ta bamu sadaka mukaci,da safe muka samu wanda zaije daura ya tausayamana muka bishi a motar katakon shi (kiya kiya ).
Ga wahala ga yunwa ga kuma yin tafiya mai nisa a kiya kiya a wannan lokacin ba dadi .

Tun kafin mu k’arasa mahaifinmu ya fara jijjiga idanunsa suka k’akk’afe, muna isa garin aka taimaka mana muka yi asibiti da shi, ba a jimaba Allah ya karb’i ransa ta sanadin rashin abinci likitoci suka tabbatar mana da cewa ya shiga hypoglycemia ne, sannan bai samu taimakon gaggawa akan lokaci ba.
A lokacin bamu san kowa ba, ganin haka yasa Likitan ya nemo mutane aka sallaci mahaifin mu aka kaishi gidanshi na gaskiya, bayan ya tabbatar da mu Musulmai ne.

Bayan an dawo daga mak’abarta lokacin tafiyar sa gida yayi still ya ga bamu da niyyar tashi, dan haka ya zo ya sami Mamanmu yace mata idan ba damuwa mu bishi gidanshi, kafin a san ya za a yi.
Muna isa gidan kuwa matar sa tace ba za ta rik’e mutum uku ba sai dai a kaimu gidan marayu da ni da d’an uwana In yaso ita mamanmu ta dinga mata wanke wanke da shara.
A lokacin rigima ce ta b’arke tsakanin Likitan nan da matarshi, domin ita tace ‘ba za ta rik’e tsintacciyar mage ba ai ya ma yi sa’a da ta yarda za ra d’auki Maman namu aiki’
Shi kuma ya dage akan sai mun zauna ai daman ba yau ta saba yi mishi irin haka ba!
Taya yana miji amman ita ace ita za ta dinga zartar da hukunci.
Rigima suka hau yi sosai,har ta kai ya fara ik’irarin rabuwa da ita.

Ganin hakan ya sanya Maman mu tace”Ta yarda a kaimu gidan marayun In yaso idan ta yi aikin ko na wata hud’u ne ta d’an tara kud’i sai ta fara sana ‘a taje ta d’auko mu ta kama haya.’
Hakan kuwa aka yi muna kuka muna komai aka kaimu gidan marayu….
Maman mu mace ce da baka iya gane tak’memen abun da yake cikin zuciyar ta amman zan iya cewa a wannan lokacin na ga tsananin tashin hankali da k’unci a fuskarta domin kuwa itama harda kukanta.

Every weekend take zuwa ta dubo mu
A lokacin ne kuma yayana duk da k’arancin shekarun shi ya dage wajen koyan sana‘a, dan zan iya cewa duk wata sana ar da ake koyarwa a gidan marayun nan babu wadda bai iya ba,ba ya isheshen bacci kullum cikin aiki,idan nace mishi ya huta yakan ce mini ‘ba dan kanshi yakeyi ba,saboda ni da mama yakeso ya yi sana’a ya tara kud’i ni da shi mu koma makaranta sannan ya siya mana gida.’
A kullum maganarshi kenan.

Tun muna Yara mun kasance masu tsananin k’aunar juna,soyayyar da yayana yake yi mini ba kad’an bace ba,ba ya son ya ga rai na a b’ace duk da kuwa ni d’in na kasance Miskili ne amman in dai ina tare da shi sai ya san yadda yasa na ware sosai saboda baya bari na ma har sai ya ga Ina dariya.

Kamar yadda mahaifinmu ya dinga sacrifice yana bamu abincin da ya samu(lokacin gudun hijira)haka shima ya dinga yi mini a gidan marayu,gashi ya hanani aikin komai,shi yake had’awa nawa da nashi ya yi,zan iya cewa ni kam ban san wahalar gidan marayu ba kwata kwata.
Mun shafe wata uku a gidan Marayu muna neman shiga na hud’u.

Ranar wata lahadi muka tashi mukai wanka da sassafe muna jiran mahaifiyarmu,kasancewar ranar zuwanta kenan amman har yamma bata iso ba,sai da daddare wannan Likita ya xo ya tura aka kiramu. Muna fitowa da ya had’a idanu da mu kawai sai naga ya fashe da kuka,da sauri muka k’araso gabanshi muka hau tambayarshi amman sai bai amsa mana ba kawai ya cewa shugaban wajen yayi checking namu out zai tafi da mu.

Sai da muka je gidan nasa muka gane dalilin kukanshi…ciwon zuciya mahaifiyarmu take fama da shi tun watanni uku da suka shud’e tanata nuk’u nuk’u babu wanda ta fad’awa yau kuma da safe ta yanke jiki ta fad’i jininta yai high sosai,babu irin taimakon da basu bata ba amman rai yayi halinshi.

A ranar kam mun sha kuka iya kuka hatta wannan matar Likita sai da ta tausaya mana.
A ranar sadakar uku ne kuma ta tada balli tace ‘sai dai mijin ta ya nemi wani wajen ko ya kama mana haya mu koma
dan ba zai barta da Yara maza a gida ba bayan ita mata ne nata kuma k’anana, ai mu maza ne ko aikin k’arfi ne za mu iya mu samu mu rik’e kanmu.’
Hakan kuwa akayi
Sai dai kud’in da mahaifiyarmu ta tara bai isa kama haya ba balle a had’a da Sana’a. Shawara Likita suka yi da yayana aka kama haya shima sai da ya cika mana.
Gefen gidan wata tsohuwa da y’ar jikarta aka kama mana haya, sannan Likitan ya bata amanar mu.
Kasancewar Yayana ya iya sana a kala kala ya sanya yake fita sana a,Allah kuwa ya sanya mishi albarka domin duk abinda yayi ko ya tab’a sai ka ga bud’u da karb’uwa ta koina dukda kuwa k’arancin shekarunshi..hakan ya sanya masu shago suka rik’esa kowa yanaso ya yi aiki da shi.
Acikin shekaru biyar yaya ya bud’e shagon d’inkin sa,da wajen had’a hula da takalma, da turarurruka,sannan ya koma makaranta nima yasaka ni a makaranta,kuma cikin ikon Allah har gidan wannan y’ar tsohuwa shi yake ciyarwa,domin ta zame mana kamar uwa jikarta kuma y’ar uwa Likita kuma ya kan zo duk wata ya duba mu,haka nan muka zama kamar family.

A lokacin da shekaru na suka ja,naje na samu yayana da batun inaso inyi aure don a lokacin ina matuk’ar k’aunar mahaifiyarku, kuma babanta har ya fara shirin maganar zai bata wani d’an uwanta za ai musu aure, to a wannan lokacin shima d’an uwana Ashe yanada tashi budurwa harya gama hada kudin lefe da na siyan gida da komai amman ganin yadda hankali na ya tashi yasanya ya bani kudin lefen muka je ya siya mini gida da duk wani abun da za a buk’ata, sannan ya bani wajen had’a turarenshi a matsayin kyauta yace in kula da Iyalina da shi.
Both mahaifiyar ku da budurwar da yayana yake nema, y’ay’an masu kud’i ne neman auren su ba abu ne mai sauk’i ba hakan ya sanya da yayana ya nemi da a k’ara mishi lokaci ya sake shiryawa, mahaifin ta ya k’i amincewa barema da ya ji k’aninsa zai
yi aure sai ya yi tunanin raina musu hankali yake son yi…
haka nan yanaji yana gani aka aurar da ita kuma ya b’oye mini don ya san ba zan bari ba shi kuma ya fi son ya fi son farin cikina akan nashi.
Shi ya wuce mini gaba ya tabbatar na auri Maijiddah , Likita ya yi mini wakili.

Bayan nan muka ci gaba da karatu da business gadan gadan,Yaya iyakacinshi masters amman ni har PHD sai da ya tabbatar nayi, ya rik’e gaba d’aya companies d’in harda na turare na daya bani wanda a lokacin ya bunk’asa , yace zai iya inje inyi karatun nawa.
Yaya bai yi aure ba,sai bayan shekaru goma mutane sunata gulmace gulmace amman ya toshe kunnuwanshi,saboda shi tunda aka aurar da wacce yake so aure ya fice mishi akai.
Sai da na saka baki ni da Likita tukun ya yarda ya yi auren
a lokacin har kai an Haifa.
Matar Likita wadda ta dinga m korarmu a gidanta itace ta kawo d’aya a cikin y’ay’anta tace ‘ta bashi ya aura’.
Don a lokacin Yaya yayi kud’i na ban mamaki,sai kuma akayi dace ya yarda don yana ganin ta ta kwanta mishi,sannan
kuma ko da ace bayaso yaci ace ya karb’i y’ar Likita a matsayin mata ko dan halaccin ubanta.

Tunda na yi aure nake burin in haifi y’a mace, sannan ina son in saka mata sunan Mahaifiyarmu, amman Allah bai bani ba, da kai da Yusuf da Yahaya Allah ya bani.
Bayan auren Yaya kuwa da shekara d’aya aka haifi Zainab(Ummi)
Da ni da Yaya ban san wa ya fi wani sonta ba gashi sunan mahaifiyarmu gareta.
A lokacin ne kuma Yaya suka yi wani accident wanda akai mishi aiki aka tabbatar mana magudanar kwayayan haihuwanshi sun sami matsala,ba zai sake haihuwa ba! Mun girgiza sosai amman kasancewar mu masu tawakkali ne sai muka mik’awa Ubangiji lamuranmu muka rungumi k’addara.

Abu d’aya muka sa a gaba shine faranta ran Ummi,Yaya ya tab’a gaya mini yana neman kud’ine saboda faranta raina da na mahaifiyarmu amman hakan bata faruba a b’angaren mahaifiyarmu domin mun rasa ta tun kafin ta ji dad’in da muka so bata,shiyasa yayi alk’awarin d’aura dukkan wani gata na duniyar nan akan tilon y’ar sa tunda takwarar ta ce,ya kance idan ya ga Ummi tana dariya gani yake yi kamar mahaifiyarmu ya sanya farinciki, domin kusan halinsu d’aya dan itama Ummi tun tana da shekaru biyu da y’an watanni muka fahimci tanada nuk’u nuk’u da b’oye abu a rai.

Shiyasa ya zama har y’ar rige rige muke ni da Yaya wajen cika mata burinta,muddin ta furta.

Shekararta biyar a duniya Yaya da Likita suka tafi Abuja,a hanyar su ta dawowa suka yi wani mummunan hatsari!! Likita tun a lokacin ya cika sai da aka kawoshi emergency yanata cewa yana son ganina… a lokacin Ina office aka sanar mini ana san ganina a asibiti tun a lokacin gabana ya fara fad’uwa,Ina zuwa kuwa a reception aka ce
mini ai y’an uwanane suka yi hatsari d’ayan ya rasu d’ayan kuma yana wanchan d’akin aka min nuni da d’akin da Yayana yake ciki…
A gigice na shiga inda yake,ina ganinshi cikin jini nai kanshi da gudu na rik’esa ina kuka.
Dukda halin da yake ciki bai hanashi lallashi ba,sai da ya ga na yi shiru tukunnan ya kamo hannuna duka biyu yana d’an tari da nishi da kyar...
Kalmarshi ta k’arshe itace
Dan Allah dan Annabi ka kula mini da Zainab ka bata duk wani farin cikin da kake da iko ga amanarta nan na bar maka
sannan ya yi kalmar shahada daganan na ji jikinshi ya sake idanunsa suna kallon sama.
A lokacin na yi kuka mai yawa dan na rasa rabin jiki na sannan bani da kowa bani da wani bani da elder mai kula da ni.
Maraicin sai ya dawo mini sabo fil.”
……
Hawaye granpa ya share ya gyara tsayuwar shi yace
“Ko mutuwar iyayena ban ji ta ba kamar yadda na ji ta Yaya..na yi alk’awarin faranta mishi ko bayan ranshi ko da kuwa ace hakan zai sanya in karya tawa k’aidar.
Ga matarka nan,ko ka san tana d’auke da ciwon zuciya???”
Ya yi maganar tare da juyowa yana kallon Abba wanda ya juya a razane yana kallon Ummi da kamar mamaki a fuskar shi.

Juyawa granpa ya yi ya ci gaba da cewa
“U won Yakubu, ka yi amfani da weakness d’ina and ka ci nasara a kaina! This time around,zan iya yafe maka laifin da ka yi mini tunda na ga alamar so kake ka dawo da baya yanzu.
Komai ya wuce!!sannan ka rushe maganar tashinka daga estate d’innan babu ita.
Abu d’aya zuwa biyu zan baka umarni shine
“Ka maida matarka yanzunnan, sannan ka kaita asibiti ga katin nan,Dr yana chan yana jiranku.
And
Kamar yadda na fad’a maka a baya,babu kai ba Maryam,amma in dai har ka shiryawa tsinuwa ta to bismillah
Ka je ka bibiyi rayuwarta....
SHARE PLS.

BULAMA✍️

So da Buri
Free Book
06

Shiru Abba ya yi yana so ya gano inda kalmar ‘ka maida ita!’ Ta nufa,dan bai gane ba.
Fusata granpa ya yi jin yadda yayi masa shiru
Dan haka ya daka mishi tsawa ta hanyar cewa
“Ko baka ji na ne Abba!!!”
Tuni Abba ya hau cewa “to granpa in shaa Allah..yanzu yanzu….”
Duk ya bi ya rikice.
Ganin hakan ya sanya Ummi share fuskarta da ta jik’e da hawaye ta faki idon granpa ganin ba su yake kallo ba ya sanya ta d’an tab’a Abba tace
“Ka taso mu tafi,yake nufi.”

Kallon ta Abba ya yi sannan ya mik’e ya ce “taso mu tafi.”
Dan ba ya so ya fara zazzage mata ta cikinsa a gaban granpa. Har ya juya sai kuma ya dawo ya zo ta gaban granpa ya tsugunna yace
“Dan Allah ka yi hak’uri na san na yi maka laifi, ka yafe mini, in shaa Allah duk abinda kace inyi zan yi daga yau ba zan sake k’etare umarnin ka ba.”

Kusan 1 minute tukunna granpa ya juyo ya kalleshi sannan yace “Yafe maka da na yi ba wai yana nufin na manta da abunda ka yi bane,na yafe maka ne saboda ni kaina in samu peace of mind na zama a same environment da kai tunda ka zame mini dole,
it’s all for Ummi’s sake, so idan kanada hankali do your best to keep her happy hakan ne zai sa ka gujewa b’acin rai na, ka samu mu rabu lfy.

Yana gama fad’in haka ya juya ya fara dogara sandarshi
har ya kai k’ofar d’akin shi ya juyo yace mata idan bai yi abunda nace ba, ko kuma ya yi trying anything stupid ki zo ki sameni.”
Daga nan ya shige ya barsu a palon.

Kallon ta kawai Abba yake yi, ji yake kamar ya shak’e ta ya huta, gashi ya yiwa granpa alk’awari…idan ya fahimci kalmar granpa ta ‘ka maida ita’
Tabbas Yaji Ummi ta yo
Ta karkad’e zani ta kawo k’arar sa kenan. Sannan
for her sake ne ma aka hak’ura zai ci gaba da zama a estate d’in….

Muryarta ce ta katse masa tunani
“Doctor is waiting”
Kawai tace ta kama hanyar fita
tana d’an tafiya da kyar tana tari irin na marasa lafiya.

Ta zo daff da fita kenan ta ji muryar gramma tana kiran Abba.
Da k’arfi Ummi ta runtse idanunta domin ta san yanzu kam k’arya ta ta k’are.

Kamar kuwa yadda ta yi zato gramma tana k’arasowa ta rufe Abba da fad’a akan sakin da ya yi, sannan ta hau bada umarnin ya maida ita nan take kuma karya k’ara.

A rikice yake kallon gramma sannan ya juya a fusace yana kallon Ummi wadda kana ganinta ka ga mara gaskiya…gashi babu Mom a wajen bare ta ceceta, fahimtar rashin gaskiya k’arara a kan fuskarta ne ya sanya kawai ya juya ga gramma ya fara k’ok’arin fahimtar da ita.

Hakan ne ya bata damar zaro wayar ta ta hau kiran Mom a rikice.

Abba kuwa hak’uri ya hau bata yana ta rantsuwa a kan “shi bai san da wata maganar saki ba ma, wato shiyasa granpa ya zuciya sosai!! Haba
no wonder
Ai kuwa yanzu sai an koma wajen granpa an wanke shi wallahi”
Ya k’arashe maganar a fusace yana kallon Ummi.

A fusace itama gramma ta cillo masa takardar hannu nata tana cewa
“Wallahi zan yi matuk’ar b’ata maka,bana son rainin hankali, ko a mafarki In aka tasheni na san rubutunka kai da y’an uwan ka.”

Durk’usawa ya yi ya fara k’ok’arin d’aukar takardar yana kallon gramma a ransa
yana cewa ‘yanzu kam ya samu mafita k’arya Ummi ta k’are!! Dama ace cewa ta yi a baki ya fad’a mata tou da da sauk’i, a rubuce kuwa ai ko hauka ake dole a gano inda rubutu ya bambam ta.’
Hannu ya kai kan takardar ya d’auka,bai kalla ba sai da ya mik’e…

A take gabansa ya yi mugun fad’uwa ya k’urawa takardar idanu yana k’ok’arin tuno yaushe ya rubuta….
Tilastawa kwakwalwarshin da ya yi ne ya haddasa masa jiri ya tafi yuuuu zai fad’i.
Da sauri Likita da suka shigo tare da Mom yanzu ya yi saurin taroshi yana
“Be careful,wat happen again??”
Ya yi maganar yana kallon su gramma.

Mom kuwa rufe Ummi tayi da fad’a sosai tana cewa
“Wai ke Zainab so kike ki k’arasa shi ne?
Baki ji abinda Likita ya fad’a bane?
Ina ce magana ta riga ta wuce? dan na tabbatar granpa ya sanya shi ya mayar da ke! To hayaniyar kuma ta mecece? “.

Kuka Ummi ta saka sannan tace”Adama cewa fa yayi wai bashi baneba.”

Ajiyar zuciya Likita ya sauk’e kafin yace ki kwantar da hankalinki,ba shi d’in bane”
Da mamaki duk suke kallonshi.
Ajiyar zuciya ya sake sauk’ewa sannan ya ci gaba “Yanzu haka takardun nan na dawo zan baku,inata sauri d’azu na hawo ba tare da itaba.
Ban so shi Abban ya sani ba gudun abunda ka iya zuwa ya dawo but now I have no choice..”
Hannu gramma ta mik’a mishi sannan tace “bani nan”
Cikin ladabi ya mik’a mata ta saka hannu ta karb’a, Abba bai yi wata wata ba ya lek’a suka hau karantawa suna dubawa a tare.
Sai da suka gama tukunna gramma d’in ta kalleshi da alamun buk’atar Karin bayani.
Gyaran murya Likitan ya yi yace “Tabbas hakane,results d’in basu gama had’uwa ba
sai d’azu da safe, daman a yadda na gansa yana behaving lokacin a asibiti na yi tunanin hakan shiyasa na yanke shawarar yi masa waennan tests d’in and result d’in gashi yadda nake tunani suka fito.
But wannan duk ba damuwa bane ba, ku kwantar da hankalin ku, in sha Allah babu wata matsala muddin aka kiyaye b’acin ranshi…
Black out ne da d’an loss of time ya samu due to stress d’in da ya saka shi misbehaving wanda hakan ya janyo mishi loss of memory,minor.

Tun a lokacin da ya farfad’o na yi mishi magana sai nake ganin kamar ma bai san me ya faru ba shiyasa na d’ab bincika shi.

A nuna wa granpa shima, d’azu mantawa nayi ban hawo da takardar ba, saboda yadda na ga Adama a rikice.
Dan Allah a kiyaye, tun kafin In ga wannan result d’in ma sai da na ja musu kunne akan yawan b’ata mishi rai, yanzu haka kar yayi komai ya huta sosai for some days saboda kwakwalwarshi kanta ta samu sukuni,
If not zai yi ta dinga loosing time gaskiya, dan abun yakan samu mutum ne mostly a old age sosai but shi gashi har ya fara,idan an yi tackling zai tsaya in ba a yi ba kuma gaskiya ban san ya abun zai kasance ba.
Abba kaima amman sai ka dinga taimakon kanka sosai kana kawar da tunani, Allah ya baka lafiya.”
Ya yi maganar yana dafa kafad’ar Abba wanda ya daskare a wajen.
“Na barku lafiya”
Ya fad’a yana mai juyawa saboda ya bar patients da yawa a clinic suna jiransa.

Ahankali gramma ta ja shi ta kai parlourn sannan ta zaunar da shi ta fara lallashinshi da kalamai masu dad’i,dan ta lura maganar likita ba k’aramin girgiza shi ta yi ba, ita kanta ta girgiza ga kuma tausayin d’an nata da ya yi mata rufdugu lokaci guda.

Haka itama Ummi ta shiga tausar shi da kalamai har da Mom suka taru….
Suna a haka granpa ya fito da alamun masallaci zai je dan an fara kiran sallah.

“Wats going on” Ya tambaya yana mai kafe su da idanuwa.

A hankali gramma ta k’arasa ta je gaban sa ta hau nuna mishi takardar da bayani daga k’arshe ta d’ora da cewa
“Likita yace a guji b’ata mishi rai da abunda zai b’ata mishi ran.”

Granpa bai ce komai ba ya taka gaban Abba ya tsaya sannan ya fara magana
“Allah ya baka lafiya.
But yadda baka da lafiya itama matarka haka, so karka bari inji wani abu ya taso daga gareka dan tabbas za a ji kanmu ba tare da na duba health problem d’in ka ba, tunda kai ne ka d’orama kanka since day 1.
Kana iya nemawa kanka sauk’i ta hanyar yayewa kanka idam kuma taurin kai da tirjiya ka zab’a! Ka dai ji abinda Likita yace.
Second option d’inka kuma
‘chanja uba da y’an uwa’ dan muddin nine ubanka to babu kai ba Maryam.

Lokaci yana wucewa ku tashi ku wuce ka kaita asibiti.”
Yana gama fad’an haka ya yi hanyar fita.

A hankali Abba ya juya ya share hawayen da ya taho ta gefen idonsa ba tare da ya bari wani ya gani ba.
Kamar minti biyu parlourn ya yi shiruuu…
Daga baya gramma tace”su wuce kawai,Allah ya sauwwak’e.”
Hakanan suka tafi ba tare da wani yace da d’an uwanshi k’ala ba.

Ganin da ya yi ba zai iya tuk’i ba ya sanya shi kiran Arshaad…shi ya tuk’a su babu mai magana a motar shiru har suka isa…aka shiga da ita dan yin investigations d’in,shi dai Abba yana zauna yana mamakin ciwon Ummi
Ta ya aka yi Ummi ta samu ciwon zuciya? matar da kullum burinshi ya faranta mata ko dan hakkin aure!! Sam ba ya so tana gani kamar bai damu da ita ba…
Sannan ga sabuwar matsalarshi shima yanzu da akace..Tabbas ya yi mugun tsorata da jin wannan lamari
dan ko lokacin da aka ce yana da ciwon zuciya abun bai tsorata shi kamar wannan ba.
Kiran sallar masallacin arean ne ya sanya suka mik’e jikin su duk babu kwari..
A haka dai suka je shi da Arshaad suka yi sallah suka dawo suka ci gaba da jira yanata tufka da warwara.
Muryar Likitan ce ta katse mishi tunani jin yana cewa
“Ha’a Abba!!”
D’agowa Abban yayi suna had’a ido da sauri ya mik’e yace “Dr ya aka yi haka?
Da gaske heart problem ne da ita?”
Kafad’unsa Likitan ya dafa sannan ya zaunar da shi kafin yace “Haba Abba!!Ba nace ka huta ba? Kai da akace ka zauna ko hayaniya kar ayi a kusa da kai.”
Shiru yayi jin Abba yace
“Granpa ne yace in kawota da kaina,shiyasa ka ganni a nan.”

Mik’a mishi takardun kawai yayi sannan yace na d’aurata akan magunguna ku tsaya ku siya babu a nan,Allah ya k’ara sauki. Dan Allah ku koma gida da wuri, sannan ka huta sosai.”
Yana gama fad’in haka ya yi gaba.

Kallon takardun Abba yake yi yana sake maimaitawa, da gaske Ummi ciwon zuciya ne ke damun ta.
A hankali ta fito daga d’akin investigation d’in, Arshaad ne yayi saurin mik’ewa ya ruk’ota ya na jera mata sannu a haka suka fito suka wuce.

A wani pharmacy suka biya suka sayi drugs d’in masu mugun tsada sannan suka wuce gida,zuciyar Ummi fessss.
Arshaad yana gama parking Ummi ta bud’e k’ofa ta fita ta nufi ciki,kai tsaye d’akinta ta shiga ta rufe kofa sannan ta nemo wayarta ta danna kiran Mom, bugu biyu a na uku ta d’auka.
“Har kun dawo?”
Shine abinda Mom tace.
“Eh!yanzun nan.”
Ummi ta bata amsa.
“To ya jikin?”
Mom ta kuma tambayar ta.
Murmushi Ummi ta yi kafin tace “Ke ni kad’ai ce fa Ina d’aki ma.”
Wata shu’umar dariya Mom ta yi kafin tace “Kinga amfanin beetroot yau ko??”
“Hmm” Ummi tace sannan ta cigaba da cewa
“Nifa na tsani abun nan, Abba ya sha gaya mini in dinga jik’awa ina sha yana k’ara jini amman ko ya saka an siyo sai dai ya bushe ko in bawa Lami idan ta tashi tafiya ta tafi da shi.”
Mom ce ta katse ta ta hanyar cewa “Aikuwa yau inda ace za a gwada jinin ki da kaf estate d’innan sai kin iya yi musu donation.”
Dariya itama Ummin ta yi kafin tace “Aikam!! Ni da akace in dinga jik’awa Ina sha, yau nice na dinga taunashi Ina fitar da ruwan Ina had’iye tik’ar..”
A tare gaba d’ayan su suka kwashe da dariya kafin Ummi tace
“Adama thankyou, komai ya tafi according to plan,zan shigo anjima.
Yanzu bara in je in wanke hannuna, kafin abin nan ya zame mini k’unshi…
Yau ba dan hijabi na saka ba da babu abunda zai hana asirina tonuwa.”
“Ok.”
Kawai Mom tace mata sannan ta kashe wayar tana dariya.

Ummi, tana fitowa daga toilet ta gama wanke hannunta tana tsane wa da towel ta ji bugun k’ofa…
Ko ba a fad’a mata ba ta san Abba ne, dan haka ta d’an tsaya a gaban mudubi ta duba fuskarta kafin a hankali ta je ta bud’e mishi.

A hankali ya shigo ya k’arasa bakin gadon d’akin ya zauna jikinshi duk a sanyaye. Sai da ya d’ago ya kalle ta sannan yace “Zo nan ki zauna, we need to talk.”

Sum sum ta zo ta zauna a daf da shi sannan tasa hannayenta ta kamo nashi tun kafin tace wani abu a hankali
yace “I’m sorry,so sorry!
Ga drugs d’inki nan ki dinga sha akan time dan Allah
And, I think zan tafi Uk.”

Da sauri Ummi ta kallesa.
Bai bata daman yin magana ba ya ci gaba da cewa
“I want to go and check on Aslam dama, dukda yace mini zai d’an lek’o soon amman I just want to go and check on him
Sannan Ina buk’atar serious investigation Ina tunanin za mu biya a yi mini checkup d’in a chan.
Ummi I’m scared, so scared…
kun ce na yi wuni d’aya ina misbehaving
I even slapped you,and...”
Sai kuma yayi shiru,d’an numfashi ya ja sannan ya ci gaba “What if brain d’ina ya fara samun matsala ne?
What if I hurt someone in the process?”

Da sauri Ummi ta d’aura hannunta a kan bakinsa sannan tace “Abba duk fa zafin ciwo ne, ai tun ranar ya yi checking naka sosai, kowa ya tsorata matuk’a da marin da ka yi mini tunda baka tab’a yi ba.
Ko d’azu ya tabbatar da zafin
ciwo ne kawai nothing else, pls ka kwantar da hankalinka
And I’m so happy da ba da gaske kake zaka iya rabuwa dani ba…I was scared hankalina ya tashi sosai shiyasa na tafi wajen granpa, I’m sorry for that,ba zan k’araba Ka yafe mini.”
Tayi maganar tana murmushi tare da sake matse hannunshi dake a cikin nata.

Ganin da ta yi yayi shiru yana sauraronta ne ya sanya ta yi ta lalallashinsa, had’e da tsarashi….
Ba ta barshi ba sai da ta tabbatar ya nutsu kuma ya yarda da maganganunta..............

Gandun Albasa
Yau sunday,Jalila na gida kasancewar babu makaranta.
Tun safe take k’ulle k’ulle akan abunda zata yi domin chusgunawa Mama..
Kamar an tsikare ta kuwa ta mik’e daga kan katifar da take kai ta fito tsakar gida kanta ko d’ankwali babu gashi ba kitso a kan gashin nan ya zubo wani yayi baya wani ya zubo ta gefen kafad’arta har saman k’irjinta..
Tana fitowa Ya Ja’afar ya na shigowa cikin gidan..ya bugu ya yi nak!! yana tafe yana layi.

“Ke!!!”
Ta ji ya ce mata.

Tsaki ta yi kafin ta juyo ta kallesa tace “menene?”
Aikuwa kamar jira yake ya nufota, yana tafe yana magana cikin layi da muryarsa wadda ke fita da kyar yace
“Ni kike yi wa tsaki??
Amman Yarinyar nan baki da kunya! Kalli kanki ko d’ankwali babu, so kike ki shiga wuta?”

Tsaki ta k’ara ja,kafin tace
“Wallahi Ya Jafar kana da damuwa!
Ni yanzu ka wani kama ka shigo za ka b’ata mini plan.”
Tayi maganar tana lek’en hanyar kitchen tana so ta hango ko Hudan na chan ta fara wanke wanken ta kasancewar yau Mama ke da girki…ai kuwa chan ta hange ta a tsugunne bakin rijiya hanyar toilet har ta kusan gamawa.
Ajiyar zuciya ta sauk’e sannan cikin sauri ta juya za ta nufi inda take ta ji Ya Jaafar ya rik’o hannunta yana cewa
“Ke Jalila, ban gama da ke ba.
Dan ke kin samu Ina sarara miki bana laftar ki kamar waccar Hudan? to kema idan ba so kike yau ki ji a jikinki ba ki biya ni kamar yadda kika saba, ko yanzun nan in sauya miki halitta.
Dan ke na lura dake duk wani aikin zunubi kin iya
Kina yawo babu d’ankwali
Sannan Ina a matsayin Yayanki amma kina yi mini tsaki
Gashi yau na ga alamar baki da niyyar sallamata.”

Jalila kam zuwa yanzu ta k’ule sosai tana k’ok’arin kwace hannunta tana juyawa tana kallon Huda wadda ke aikin ta cikin nutsuwarta kamar yadda ta saba, har ta juyo za ta yi mishi masifa sai kuma wata dabara ta fad’o mata.
Murmushi ta yi sannan tace
“To naji,zan baka kuma yau naira d’ari ma zan baka.”
Ai kuwa ba shiri ya hau fara’a yana mai sakar mata hannu yace”To to,kin ceci kanki, maza je ki d’auko.”

Juyawa ta yi cikin gudu ta fad’a d’akin nasu…so take ta samu ya kyaleta kafin Hudan ta k’arasa aikin ta dan wallahi yau sai ta kifar da kayan wanke wanken nan a cikin chab’in bakin rijiya tunda ta yi niyya.
Tana d’aga k’asan pillown ta, ta ci karo da naira Hamsin bayan ta san d’ari ta ajjiye a wajen(Hamsin biyu) Tsaki ta yi tace “Umma!!!
Na san d’azu da za ta tafi gidan Baba Laraba ne ta d’auke mini, aikuwa bara ta dawo sai ta biyani, da ace ta san kalar k’arya yunwar da na yiwa malamin maths shekaran jiya a makaranta ya bani d’ari uku, da ba zata tab’a mini kud’iba.
Cikin mita ta d’auko Jakarta ta makaranta ta zaro littafi ta bud’e tsakiyan,ta ci karo da y’an chanjin hamsin da ashirin.
Tsaki ta ja ta ci gaba da mita
“Gaskiya Umma ta b’ata min budget,yanzu ga wanchan shima yana jirana,dama tunda na dawo taketa faman tambayana ko na yi chanji na san kud’i takeso..in banda abun Umma ko me naira hamsin zata yi mata oho…
yanzu na san Ina tambayar ta cewa za ta yi cikawa tayi suka yi kud’in mota ita da Baba Laraba…..”
Tanata mita haka ta d’auko ta fito.

D’an juyowa tayi jin motsi a bayanta suka hada ido da Mama da take k’ok’arin yafa mayafi ga jaka a hannunta kana gani ka san fita zata yi kuma cikin sauri take.

“Kaii!! Allah yana sona.”
Shine abinda Jalila ta fad’a a ranta,dan har wani plan d’in ya kuma zuwa kanta ganin Mama fita zata yi, “plan har biyu yau akwai show a gidannan” ta fad’a a k’asan zuciyarta

“Huda! Huda!”
Mama ta kwala kiran Huda..
Da saurinta ta iso inda Maman take tana goge hannunta da gefen zanin jikinta.
Mama da ta k’araso tsakar gidan ce tace “Zan fita,yanzunnan Ummu ta kira ni Sumayya ba lafiya ciwon ciki takeyi tun safe har da suma..
Sun je asibiti an mata allura ance ta je gida ta huta, yanzu suna gidan Hajiya Shuwa. Zan je in dubo ta.”

Shiru Huda ta yi, ganin Mama ta kama hanyar fita ya sanya tace “Mama dan Allah zan biki nima in dubo jikin nata.”

D’an tsayawa Mama tayi ba tare da ta juyo ba tace mata
“A’a, ki k’arasa aikinki…yanzun nan zan dawo.”

Takowa Hudan ta yi ta d’an biyota murya kamar zata yi
kuka tace”Mama na gama, share wajen kawai zan yi in d’auko hijabina.”

This time around da fad’a Mama tace
“A’a”
Still bata juyo ba.

Dariyar Jalila ce ta sanya Mama juyowa.

Cikin wata irin dariyar raini Jalilan tace
“Kai, amman Hudan ban tab’a ganin dabba mai kwakwalwar kifi kamar ki ba, shiyasa fa muka bawa Baba shawara ya cire ki a makaranta dan asarar uniform da kud’in break kawai za a dinga yi.
In banda abinki, kwanaki fa har gidan nan ita kanta shuwa ta zo ta samu Baba tace ‘kar ya k’ara barin ki ki taka mata k’ofar gida, tunda shi ya ga zai iya rik’e ki ya je yai ta yi ita bata buk’atar ko ganin ki’.”

Shiru duk suka yi ba wanda ya tanka mata illa Mama da ta juya ta fara k’ok’arin saita kanta ta hanyar danne abunda take ji yana taso mata.
Jalila kuwa, cikin takun ta ta k’arasa gaban Hudan ta tsaya sannan ta ci gaba da cewa
“Ba ta son ganinki a gidanta, ba ta son ki Hudan, duk ba’a son ganinki kowa ba ya sonki.
Yanzu ki bar Mamanki ta je gidan, Allah yasa itanma kar Shuwa ta yi mata korar kare!
Ki je ki ci gaba da wanke wanken ki kinji k’anwata.”
Ta yi magnar tana dafa ta sannan tace “Domin shi aka haifo ki duniya, da shara da ragowar ayyukan gida.”

Sharkaf haka fuskar Huda ta jik’e da hawaye, da sauri
ta juya ta nufi d’aki tana goge fuskarta.
Murmushi Jalila ta yi, sannan da d’an k’arfi yadda ta tabbatar za ta jiyota tace
“Shegiya kawai.”

Sarai kuwa Maman ta ji ta amma ba ta ce komai ba kafin ma Jalilan ta juyo ta yi sauri ta fice daga gidan tana share hawayen fuskarta.

Ganin Mama har ta fice yasa ta ce”In kin gama kukan munafurcin ki yi sauri ki fito ki k’arasa tattare wajen wanke wanken nan, dan har k’udaje sun taru.”
Sannan ta juyo ta mik’awa Ya Ja’afar naira hamsin.
Karb’a ya yi ya jujjuya ta kamar yana neman wani abun a jikin hamsin d’in kafin yace
“Hamsin nake gani!”

“Eh,ai wai da d’ari nace zan baka, yanzu kuma sai na ga sauran ashirin da hamsin biyu shine zan baka naira hamsin sai a siyo mana zob’on saba’in a gidan mai tuwo tuwo..
Kaga kenan Naira d’ari da ashirin ma na baka.”

Shiru ya yi yana son ya had’a lissafin amma sam sai ya gagara…ganin hakan yasa tace
“To bani kud’ina na fasa, kawai yau daki kud’inka.”

Da sauri yace
“A’a, barshi kawo in je In siyo.”

Kallonshi ta yi kafin tace
“Wato har ka manta da bashin da take binka ko?
Ranar nan fa har gidan nan waenan k’artin mazan masu tuk’a mata tuwo suka biyoka za su dakeka, da kyar Baba ya basu hak’uri.”

Shiru yayi kafin yace
“Kuma fa hakane,to yanzu ke zaki je kenan?”

Da ido Jalila ta nuna masa Huda wadda ta fito yanzun nan tace
“Ai ga k’arama chan,sai ni za ka aika? tsoronta kakeji ko?”
Da sauri yace
“Haba deee!! a’a.”

Ganin ta fara cin nasara,ya sanya ta ci gaba da cewa
“To kirata mana ga kud’in ka bata, amman wannan Yarinyar ma na san k’arshenta tace ba za ta je ba saboda d’azun nan na ji Mamanta tana cewa indai ka sake aikenta kar ta je , kuma idan ka daketa ta rama!!”

Ai tun kafin ta k’arasa ya wafce kud’in ya hau kwalawa Huda kira yana hura hanci.

Da saurinta ta k’araso tana “Na’am” tace “gani”

Kud’in ya watsa mata yace ‘maza ta je ta siyo mishi zob’o a gidan mai tuwo tuwo’.

Zaro ido ta yi kafin tace
“Maama ta hanani zuwa gidan saboda akwai y’an shaye shaye da maza da yawa, kuma ni ban ma san hanya ba yanzu.”

Cikin zuga Jalila tace
“Ai dama na san za a yi haka, ka ji ko?”
Sai kuma ta kalle ta tace
“Tukunna ma shaye shaye me kenan??”
Ba ta jira ta bata amsa ba tace”Yaya irinfa d’an maganin ciwon kan nan da kake sha yake d’an saka ka jiri shine take zagi! Tab!! kaga kenan ta had’a har da kai ta zage tasss!!!.”

Ai kuwa Jalila ta yi nasara dan Ya Ja’afar cewa yayi “wallahi yau idan Huda za ta suma sai ta je kuma wallahi ta dawo gidan babu zob’on gidan mai tuwo tuwo sai na lahira ya fita jin dad’i.”

Hakanan tana kuka tana komai ta zo ta wuce, sai da ta kai k’ofa ta juyo tace
“Yaya Jalila dan Allah to ko kwatance ne ki yi min.”

Cike da son sake dilmiyar da ita Jalilan tace
“Idan kika fita ki mik’e, ki yi kwana sau bakwai sai ki yi tambaya.”
Haka kawai Jalilan tace da ita sannan ta juyo tai hanyar d’aki har ta tura k’ofar sai kuma ta juyo
Sanin cewa Huda bata da wayo kwata kwata, tunda ba shiga mutane take yi ba ya sa tace mata
“Kuma saura ki biya gidan shuwa ki kai k’ara, ranar da kunne na na ji tace ‘sai ta yanka ki a duk ranar da kika yi
gangancin zuwa mata gida’.”

Hawayenta ta share cike da fargaba da tsoro ta juya ta fita daga gidan.

Kamar yadda Jalilan ta yi mata kwatance haka ta yi amman sai aka ce mata ‘ai nan arean kwata kwata babu gidan mai tuwo tuwo’.

BULAMA✍️

So da Buri
Free Book
07

Tun 11 na safe take bulayin neman gidan mai tuwo tuwo
har 4 na yamma bata samu ba, kusan kaff Unguwar ta Gandun Albasa har kwargiji da wajejen Gada duk babu inda ba ta duba ba.
Ganin ta kusa shiga g r a d’in Sharad’a ne ya sanya ta koma da baya ta ci gaba ta kutsa kai tana nema.
An nuna mata gidan mai tuwo tuwo har biyu amman ba nan bane ba kuma su ba sa siyar da zob’o.

Idan ka ganta sai ka tausaya mata, duk ta yi wujiga wujiga ga yunwa ga gajiya sannan ga k’ishirwa.
Tana cikin tafiya ta ga ta fara hango kwandila a tsallaken titin side d’in da take, sanin da ta yi cewa gidan mai tuwo tuwo ba a kwandila yake ba ne ya sanya ta yanke shawarar komawa gida kawai! Ko da kuwa Ya Ja’afar zai kashe ta da duka ne.
Har za ta juya sai ta hango tuk’a tuk’a, k’ishin da take ji yasa ta yanke shawarar ta tsallaka ta sha ruwan inya so sai ta tsallako ta koma ta tafi gida.
Da kyar ta samu ta tsallaka, ta rok’i wani almajiri ya buga mata, ta samu ta sha.
Ta gama sha kenan!
D’agowar da zata yi sukayi ido biyu da wani mahaukacin kare, da alama shima k’ishin ruwan yake ji dan ya k’urawa ragowan ruwan da bai gama tsiyaya ta kan famfom tuk’a tuk’an ba ido.

Yunk’urawa ya yi ya tunkarota cikin sauri, ai kuwa babu shiri ta nannad’e zanin jikinta ta kwasa a guje, a tunanin ta ita ya biyo. Shikuwa Karen ganin ta hau gudu kamar jira yake yi kawai sai shima ya bita a guje…..

Tsere suke zubawa ita da Karen nan tana ihu tana neman Agaji, musamman ma da ta tuno da wata magana da Sakina ta tab’a gaya mata
“Indai kare ya kama saman dunduniyar k’afar mutum ta baya to cirewa yakeyi gaba d’aya.
Kai da tafiya har abada.”
Ai kuwa nan ta k’ara k’arfin gudun nata….
Wasu su yi mata dariya wasu su ji tausayinta wasu kuma ta basu mamaki….gatanan dai doguwa kyakyyawa y’ar budurwa da ita amman ta zage tana tik’ar gudun ceton rai a wajen Kare.

Ganin da tayi k’afafuwanta sun fara zafi sosai, gashi ta gaji!! Ya sa kawai ta yi kalmar shahada ta tsaya chak! sannan ta juyo ta durk’usa…dai dai Karen ya iso dab da ita, ta rufe idanunta da mugun gudu da k’arfi ta hau had’ashi da Allah tana cewa “Dan Allah dan Annabi ka yi hak’uri, kar ka cijeni, na gaji ka yi hak’uri…”
Ta kusan mintina 2 a haka..
Jin shiru yasa ta bud’e idanunta a hankali k’irjinta na dukan uku uku.
Cikin ikon Allah kuwa babu Kare babu alamar shi. Hamdala ta yi ta mik’e da niyyar tafiya gida…sai ta ganta a tsakiyar kwandila. Layin shiruu ba kowa sai maka makan Gidaje, mota d’aya ta hango a k’ofar wani had’add’en gida da alamar mamallakin motar yana jira ne mai gadi ya bud’e masa ya shige.
Bayan wannan motar babu komai kuma babu kowa a layin. Dubawa ta yi sosai ta ga ba ma ta san a ina take ba, sai a lokacin ta fashe da wani irin kuka ta zauna dab’ass!! A wajen ta cusa fuskarta cikin cinyoyinta.......

Bai dad’e da shigowa cikin Unguwar ba, akwai wasu takardu da Abba ya sanya shi zuwa ya d’auka dan yana son yin amfani da su kuma har an tarkato an kawo sabon Gida.
Yana shirin danna horn kenan ya ji kamar ihu!! Kasancewar bai rufe gaba d’aya glass d’in motar tasa ba.
Yana kallon direction d’in da ya jiyo ihun nata kuwa ya hango ta ita da Karenta. Da farko
abun dariya ya bashi, sai kuma ta fara bashi tausayi…da
har zai je wajenta sai kuma ya fasa ya dannawa sabon mai gadin da aka saka a Gidan horn ya bud’e masa ya shige.
Bai b’ata lokaci ba ya shiga, inda takardun suke ya je ya d’auko ya fito ya shiga motarsa ya sake yin horn aka bud’e mishi gate d’in ya nufi waje.
Kamar ance ya juya, yana juyawa ya ganta this time around ta cusa fuskarta tsakiyan cinyoyinta kuma babu Karen a wajen.

Kawai tsintar kansa yayi da son zuwa wajen ta, da farko kamar ba zai je ba sai kuma yayi tunanin inda Aaima ce a wajen ai da ba zai so a barta ita kad’ai haka ba.

D’an rivers ya yi sannan ya karkata hancin motar ya nufi inda take.

Yana isowa ya d’an tsaya, ya
kasa fitowa kawai yana kallonta, dan ji yakeyi kamar ya juya.

Ya d’an jima a haka sai kuma yayi tsaki ya bud’e motar ya fito ya zo ta gabanta ya tsaya.

“Hey!!”
Ya ji shiru…sake maimaitawa yayi tukunna a hankali jin kamar mutum a tsaye a kanta yasa ta d’ago fuskarta wadda ta jik’e da hawaye tana kallonsa.

Da k’arfi ya ji zuciyarsa ta wani irin bugawa sakamokon had’a idanun da suka yi, ita kuma ganin sa da tayi ya sanya da saurinta ta mik’e tana karkad’e zaninta d’ayan hannun kuma tana goge hawayen da ya k’i tsayawa da bayan hannun.

Tsayawa yayi yana k’are mata kallo a ransa yace”Who’s she??
How can someone be this beautiful??.....”

“Ina yini”
d’in da tace masa ne ya dawo da shi daga duniyar lissafi da k’are mata kallon da ya tafi.

Da kyar ya iya tattaro kalmar
“Alhamdulillah”
Dan zuciyarsa bugawa take yi ba kad’an ba.

“Dan Allah ka san hanyar gidanmu?”
Ya sake jin muryarta.

This time around sai da ya lumshe idanunsa ya bude tukunna ya iya ce mata
“A’a, why are you crying?”.

Ta fahimci tambayar da yayi mata, dukda cewa a iya primary ta tsaya.
Amman kuma sai ta tsinci kanta da kasa bashi amsa…ta ga yawan maganarsa turanci ne, kar taje ta bashi amsa da Hausa ya kasa ganewa kuma
tana tsoron yin turanci dan ba wani iyawa ta yi ba, kar taje yayi mata dariya kamar yadda su Ya Jalila suke mata a duk lokacin da ta yi turanci.

Ganin ta yi shiru yasa ya fara tunanin ko bata jin turancin ne domin kuwa yanayin duk’unk’unennen hijabinta da kod’add’en zanin jikinta kad’ai sun isa su fad’awa mutum ita d’in ba wata shahararriyar y’ar Boko bace ba. Dan haka ya yanke shawarar maimaita mata tambayar da Hausa.
“Me ya saka ki kuka??”

Da mamaki a fuskarta, ta ke kallon sa jin Hausar tasa tarr!! A ranta tace “To ko dai koya yayi??” Dan tabbas ita dai ta san wannan ba bahaushe bane ba, ko dai balarabe ko kuma d’an India ,
Saboda yanayin cikar gashin kansa, gashi a kwance sai kyalli yakeyi, shigen na larabawa, gashi fari sosai, dukda cewa itama bakinta pink ne amman ta san nashi ya fi nata zama pink sosai, ga hancinshi mai kyau d’an dogo, sannan idanunsa irin manyan nan kuma a kwance dogaye, kuma wani ikon Allah yanayin shape na gashin girarsu iri d’aya..ba irin cika d’innan ne da girarba, amman shape d’inta na medium arch ya fito sosai……

Shi kam Arshaad zuwa yanzu ya fara tunanin ko dai kurma ce Yarinyar nan?! To amman kuma ai d’azu har gaida shi ta yi.
A hankali ya sauk’e ajiyar zuciya ya sake ce mata
“Umm?”
Yana mai tsare ta da idanuwa dan yaga kamar ba ta ji na farkon ba.

K’asa ta yi da kanta ta fara wasa da y’an yatsun hannunta kafin tace
“Ya Ja’afar ne yace in siyo mishi zob’o, na manta gidan, tun Ina Yarinya aka hanani zuwa, kuma yanzu na b’ata.“
Ta yi maganar tana share siririn hawayen da ya zubo mata da bayan hannunta.

Shi kam he don’t know Y amman yanayin maganarta burgesa yake yi, komai nata a nutse take yinsa, ya dad’e bai ga mace mai magana cikin nutsuwa da kamewa ba kamar ita.

A hankali ya sauk’e ajiyar zuciya ganin ta d’ago kai ta kalleshi a karo na biyu bayan gama yi masa maganar, sai kuma ta sake yin k’asa da kanta ta cigaba da goge hawayen.

Wani white handkerchief ya zaro daga cikin aljihunsa ya mik’a mata.
Da farko k’in karb’a ta yi sai da yace “Ungo ki goge fuskar ki,ya b’aci da yawa da hawaye, Yara za su yi miki dariya.”
Tukunna a hankali ta sanya hannu ta karb’a ta fara goge fuskarta tana lumshe idanu saboda wani fitinannan k’amshi da yake shigar mata hanci.

Sai da ta goge hawayen tass sannan yace “Zo,mu je ga mota sai in kaiki Gida.”

A hankali ta girgiza masa kai sannan tace “Ban san ka ba, ba zan shiga motar ka ba.”

Wani d’an cute smile ya yi, kafin yace “To in tarar miki napep za ki shiga??”

Da sauri ta d’aga mishi kai alamar ‘eh’.
Smiling ya yi har sai da hak’oransa suka d’an baiyyana, sannan yace “To shi a ina kika sanshi? me napep d’in!”
Rau rau ta yi da idanunta, har za ta yi magana sai kuma tayi shiru tana wasa da yatsun hannunta, dan bata da amsar da za ta bashi.

Ganin hakan yasa yayi locking motanshi daga inda yake da key d’in, sannan ya fara tafiya yace “mu je In saka ki a napep d’in.”

Da saurinta ta bi bayanshi…a
hanyar yake tambayar ta sunan ta, tace masa “Huda.”

Basu wani dad’e suna tafiyar ba, tun kafin su fita a kwandila suka samu napep, ta fad’a mishi inda zai kaita ta shiga.

D’an sunkuyowa ya yi yana kallonta a cikin napep d’in…ji yake kamar kar su rabu amma
da ya tuna ya ji sunan layin Gidan nasu yanzun har ma da d’an guntun kwatancenta da ta yiwa mai napep d’in duk ya haddace. Sai kawai yace mata “ki gaida gida da su Mama.”
Daga haka ya zaro 1k a aljihunshi ya bawa mai napep d’in, kafin ya yi waving nata yana smiling suka yi gaba suka barshi a wajen.

Har ya isa inda motarshi take ya shiga ya ja yai gaba, yana smiling.
Ita kuwa Huda mamakin kyau da had’uwa da gayunshi take ta yi, dukda ta san su Ya Junaidu ma kyawawa ne sosai amman wannan kam ya fi su, gashi da kirki.

Ahaka suka shigo layin su, ta nuna k’ofar gidansu aka ajjiyeta.
K’irgo y’an chanji mai napep d’in ya yi(950), har ta d’an yi gaba ya kirata ta dawo ya mik’a mata.
Sai a lokacin ta ji gabanta ya fad’i domin kuwa ta san tabbas ba za ta b’oyewa Mama abunda ya faru ba, gashi kuma har da sakota a napep har k’ofar gida, ta ina za ta fara bayani, waye shi?? ya aka yi ma ta sake da shi haka bayan jan kunnen da Mama ta sha yi mata a kan maza!? Mai ya sa duk wannan tunanin ba su zo mata ba d’azu??.

Muryar mai napep d’in ce ta katse mata tunanin da take yi
“Ungo mana, ko bakya so?”
D’aga mishi kai ta yi a hankali tace “Ka rik’e na bar maka.”
Daga haka ta juya ta nufi gida da sauri.

Tana d’ago kanta gabanta ya fad’i da k’arfi sakamokon had’a ido da suka yi da Baba ya hard’e hannayenshi a k’irji ya jingina da jikin bangon gidan da tafin kafarshi kwaya d’aya da bayanshi, yana kallonta yana kallon mai napep d’in.
Da sauri ya d’ago daga jinginar da ya yi ya zira silifas d’insa guda d’ayan wanda ya cire ya jingina da k’afar, ya tunkari mai napep d’in da yake shirin buga mashin d’insa ko gaisuwarta bai amsa mata ba.

A hankali ta tura k’auren ta shiga…tun daga soro ta fara jiyo maganar Jalila da Umma, Umma tanata masifa Jalila na zugata, tana ida shiga tsakar gidan kuwa ta hango Mama a zaune a bakin k’ofar d’akinsu tana kuka, Ya Junaidu ya durk’usa a ta gefenta da alama hak’uri yake bata, Umma sai ce masa take yi “shanyayye!! ya tashi a wajen kafin ranshi ya b’aci!!”
Jalila kuma tana cewa “ai dama ya fi son Mama a kan Umman tasu.

Sallamarta ce ta sanya duk suka juyo suka zuba mata idanu.
Ganin Mamanta na kuka
yasa da sauri ta yi inda take ta durk’usa a gabanta ta saka hannu ta hau share mata hawaye.
D’an kama hannunta Mama ta yi sannan ta goge hawayen da d’ayan hannunta kafin tace
“Daga ina kike? ya aka yi kika dad’e? Jalila tace Ina fita kema kika fita.”
Mama ta jero mata tambayoyin tana kafeta da idanu.

Za a wani tsaya ana yi mana kukan munafurci kamar ba ki san Ina ta tafi ba!! Kawai ke dai kice baki san waye saurayin ba amman sarai kin san me ta je ta yi.”
Cewar Umma sannan ta d’aura da cewa “Yo Allah na tuba daman Yaran yanzu ka haifo su ta hanya mai kyau ma ya aka k’are, ballantana ta hanyar da ba ta dace ba!!”.

Da k’arfi Mama ta runtse idanunta wasu zafafan hawaye suka shiga tsiyayo mata…
Umma bata damu ba ta ci gaba da cewa
“Sannan sai ki dinga goya mata baya tana abubuwan da ta ga dama idan anyi magana ki ce sharri aka yi mata saboda bakin ku d’aya ko??
Kina samu tana kawo miki taro da sisi.”

Hudan ce ta mik’e ta k’arasa kusa da Umma tace “Umma dan Allah ki yi shiru kinga fa maganar ki yadda take saka Mama kuka.”

D’an zaro idanu Umma ta yi kafin tace “Eh lalle Yarinyar nan kin rik’a!!!! Ko da yake ba zan ga laifin ki ba, yanzu ai gani kike yi daidai kike da ni tunda duk abinda na sani kema kin sanshi, zafin ciwon nak’uda kawai ya rage.…..”

Da sauri Mama itama ta mik’e ta k’arasa daff da Umma ta ce “Dan Allah dan annabi Sadiya ya isa haka! Za kisa Yarinya ta san abunda shekarunta ma basu kai ba, tun d’azu kinata aibantata da bakinki kuma yanzu kin zo kina irin wannan maganar a gaban Yara saboda Allah.”

Mamaki ne ya cika Umma saboda ta dad’e ba ta ga b’acin ran Mama kamar haka ba, cikin matsowa kusa da sosai itama tace “Lalle Maryam!! na jinjina miki. Son y’arki ya rufe miki ido har kina gaya mini magana dan na fad’i gaskiya??”.

Mama bata bari ta k’arasa ba tace “Wallahi ba gaskiya kika fad’a ba!”
Sannan ta juya ta kamo hannun Huda wadda take ta kuka ganin ana fad’a a kanta, ta kawo ta gaban Umma tace “Zan iya dafa Al Qur’ani akan sharri kuke yi mata,
Allah ne shaida ta na san kalar tarbiyyar da na yi mata.
Idan kuma kina da shedar da zaki tabbatar da abinda kike cewa gaskiya ne to Bismillah Ina sauraron ki.”

Hudan garin k’ok’arin goge hawaye bata saniba handkarcheif d’in da Arshaad ya bata ya fad’o k’asa!
Karaf! kuwa a kan idon Jalila, da sauri ta k’araso inda ta ga handkarcheif d’in ya fad’i,har tana gurd’ewa.
Duk sai suka zubawa inda ta nufa ido, cikin sauri ta durk’usa ta d’auka,sai a lokacin Hudan ta lura aikuwa ta fara rarraba ido gabanta na mugun fad’uwa kana ganin ta ka ga mara gaskiya.

K’arasowa Jalilan ta yi kusa da Mama, dai dai fuskarta ta d’ago handkerchief d’in ta yi mata fifita da shi a dai dai setin fuskarta kafin tace “kowa dai ya ga lokacinda ya fad’o daga hannun Huda ko?
Tambayata a nan itace ‘shin a ina kamila nitsatstsiya Huda ta samu handkerchief mai kyau haka da k’amshin turare wanda na tabbata na maza ne?’.”

Ya Junaidu wanda kishi ya turnuk’e sa a take ne, yace “Kawo in gani!”

Mik’a masa ta yi ya k’arasa warewa…Farine tas! Hanky d’in, kana gani ka ga had’add’en personalize handkerchief, ta chan k’asa an rubuta ‘AY’ da wani had’add’en glitter gold, ga uban k’amshin da yake ta zubawa na had’add’en designer perfume.

Da kyar ya samu ya d’an yi controlling temper d’inshi tukunna ya kalli Huda yace “na waye???“
Ya yi mata tambayar yana tsareta da manyan idanuwanshi da suka fara chanja kala.

Shiru Huda tayi ta fara goge hawayenta da suke zuba a yanzun babu k’akk’autawa.

Mama ma da gabanta yake ta fad’uwa tana kiran sunan Allah da k’ok’arin kawar da mugun tunani akan y’artata tace
“Huda tambayar ki fa akeyi, kin yi shiru ki bamu amsa!”

Baba wanda ya shigo yanzu ne yace “Ku barta ai ba zata tab’a cewa komai ba! Gani nan, ni ne zan baku amsa!.”

BULAMA ✍️

So da Buri
Free Book
08.

Duk juyowa suka yi suna kallonshi da mamaki a kan fuskokinsu.
K’arasowa yayi ya kalli Mama yace “Nace miki Yarinyar nan yawonta ta tafi irin wanda kika yi amma kin k’aryata ni ko??
To mai adaidaita sahun da ya kawota shi na bi na tsare na tambaya ya kuma tabbatar mini da cewa ‘Ita da wani saurayi dogo fari tass suka tsaida shi a wajen kwandila, bayan ta shiga har yana ce mata ta gaida su Mama har ya bada dubu d’aya a kawota, da mai napep d’in ya bata chanji tace ta bar masa.’ Haka akayi ko ba haka ba?”
Ya k’arashe tambayar yana kallon Huda wadda jikinta a yanzu yake mugun karkarwa ga hawaye sai zuba sukeyi ta gagara controlling d’insu.

Mama ce ta k’arasa ta kamo hannunta ta share mata hawaye sannan a hankali tace
“Huda da gaske ne abinda mai napep ya fad’awa Baban ku? Dan Allah kar kiyi mini k’arya.”
Addua Mama take yi a ranta Hudan tace mata ‘A’a’
amman sai taga tana d’aga mata kai alamar ‘Eh’.

Wata uwar gud’a Umma ta rangad’a sannan tace
“Huda Allah dai ya yi miki albarka, gwara da kika fara fitowa fili kina fad’in gaskiya, yanzu sai a daina janta d’aki a na b’oyewa..
Don kowa yanzu ya san hali!
har shi Junaidu mai goya mata baya yau kam ya ji kuma ya gani. A bi dai a hankali kar a kwaso k’anjamau.”

A fusace Mama tace
“Bana son mugun alkaba’i, dan an ganta da wani sai kuma akace wani abun ke tsakaninsu??
Ki fad’i alkhairi ko ki yi shiru mana! Mai ya kawo maganar k’anjamau a nan?”

Baba ne yace “Wallahi Maryam zan yi mugun sab’a miki!!!
Ya da girman mu kina raina mana hankali? Uban mai ya had’ata da shi to da har ya sako ta a adaidaita sahu?
To bari kiji in gaya miki!!
Malam Iro mai kayan Miya da kika rainawa arzik’i kika hana shi auranta, yanzu zan je ince ya turo!! Dan ba zan zauna Yarinya ta lalata mini gida ba.
Amman kafin nan sai na sauya mata kamanni ta yadda shi kansa d’an iskan saurayin nata ba zai iya ganeta ba, kuma gobe ko ance ta je ba za ta je ba.”

Junaidu ne ya sha gaban sa ganin ya yo kan Hudan, kafin
yace “Baba a yi bincike dan Allah, kar a yi saurin yanke hukunci.”

Cikin fushi Umma tace “tou shanyayye!!
binciken me kuma bayan wanda akayi?”

Da sauri yace
“Umma mu tambaye ta mana mu ji, kina gani fa bata b’oyewa kowa ba ta fad’i gaskiya bata k’aryata mai adaidaita sahun ba, ko?”

Yanzu wannan munafukar Yarinyar za ka tambaya???
Kuma kana zaton za ta fad’i gaskiya? Tou Bismillah bari mu ji.”
Umman tace tana mai gyara tsayuwarta da d’aurin d’ankwalinta.

Ahankali cikin nutsuwa Junaidu ya tambaye ta “hanky d’in na waye? sannan waye wannan mutumin da aka gansu tare,a ina ta sanshi?”

Amsa d’aya ta iya bashi,
“hanky d’in na mutumin ne amman ita wallahi ba ta sanshi ba.”
Ta kuma bashi labarin tun daga yadda kare ya biyo ta har lokacin da ya sakota a adaidaita…..

Dariya Umma da Jalila suka saka kafin Jalila tace
“Lalle Huda kin cika tantiriyar mak’aryaciya!”

Junaidu kuwa ganin raina masa hankali ma zata yi yasa ya jefar da hanky d’in kawai ya juya ya fita ranshi a mugun b’ace…..A hanyar fita suka had’u da Ya Jaafar yana shirin shigowa shi kuma, yana tafe yana tangad’i.

Yana shigowa ya hango Mama a gaban Huda ta na k’ok’arin kare ta daga dukan da Baba yake shirin yi mata tana kuka tana bashi hak’uri..saboda ita har ga Allah ta yarda da labarin da Hudan ta basu.

Da saurinshi ya k’araso yace
“Ke dan ubanki Ina zob’o na???tun jiya na k’i shan ruwa ke nake jira, Jalila tace mini tun jiya da yamma muka aikeki, a gidan ubanwa kika kwana?”

Ita Hudan sai yanzu ma ta tuna da kud’in aiken kuma indai za ta iya tuna a inda ta zubar to a wajen gudun kare ne….
Hak’uri ta shiga bashi tana cewa “Bata ga gidan mai tuwo tuwo ba, ta duba duk wani lungu da sak’o na Gabdun Albasa. Sannan kud’in sun fad’i, ya yi hak’uri dan Allah.”

Zancenta na kud’in sun zube kawai ya iya fahimta, dan haka ya yo kanta zai daketa
nan ma Mama ta kuma karewa, ta hau rok’on Baba tana cewa “Dan Allah ka bawa Jaafar hak’uri, ka ga a yanayin da yake ciki, baya cikin hankalinshi kar ya je ya ji mata ciwo.”

Umma ganin kamar Mama za ta yi nasara a kan Baba ne yasa ta sanya gaba d’ayan k’arfin ta ta ja Mama ta cilla ta gefe har saida ta fad’i k’asa.
Ya Jaafar kamar jira yake yi ya hango wani tsohon katako a gefe kawai ya nufe shi ya d’akko.
Mama na ganin haka ta fara k’ok’arin mik’ewa da sauri ta nufi inda suke amma kafin ta k’araso har ya bugawa Hudan a cikinta da dukkan rogowan k’arfinsa.

Aikuwa dukan ya shige ta ba kad’an ba, k’usoshin da suke jikin katakon suka chaketa wanda hakan ya sanya jini ya fara zuba, a take ta fad’i a wajen ta sume.

Sai da numfashin Mama ya d’auke da jinta da ganinta na y’an sakanni tukunna a hankali ta taka ta k’araso ta durk’usa ta fashe da kuka, tana dudduba ta tana neman pulse…..
Da sauri ta mik’e ta nufi d’aki ta
bud’e jakarta ta zaro waya ta hau kiran Ummu.…
Shi kuwa Ya Ja’afar yana ganin ta sume, shi ya d’aukama ko ta mutu ne, dan haka ya kwasa a guje ya yi waje.
Umma da Jalila kuwa d’akinsu suka nufa, haka shima Baba….babu wanda yace uffan a cikinsu.

Ummu,
an ci sa’a har yanzu suna gidan Hajiya Shuwa, dan ya fi
kusa da asibitin, shiyasa suka zauna a nan gudun kar su koma gida ciwon Sumayyan ya sake tasowa. Suna cikin hira ta ji k’arar wayarta,
ganin sunan Mama wanda tayi saving da sister a kan screen d’in ya sanya ta yin murmushi kafin ta d’auka tana mai cewa “Mama jikin nata fa da sauk’i, ki kwantar da hankalinki bacci ma takeyi yanz....”
Jin sheshshek’ar kuka yasa tace “Me ya faru? Ya naji kamar kina kuka??”.
Salati ta fara lokacin da Mama ta fara gaya mata halin da Hudan take ciki… ba ta tsaya
jin ba’asi ba ta zaro mayafinta ta yi waje, ganin hakan ya sanya Sakina biyo ta.
A bakin gate suka ci karo da Madu, ganin yanayinta ya sanya shi tambayarta “mai ya fati?” shi a tunaninsa ma ko jikin Sumayyan ne…nan ta hau
gaya mishi abunda ya samu Hudan….Shiruuu! yayi ba tare da yace komai ba, chan kuma a hankali ya rab’a ta gefenta ya wuce cikin gida.
Wani siririn kuka Mama ta sake fashewa da shi sarai Ummu ta san ta ji yadda sukayi da Madu yanzu da yadda Madun ya nuna halin ko’in kula da lamarin….
Shiru kawai ta yi ta cigaba da tafiya da sauri domin ta je ta iske su ita da Hudan akan lokaci tunda yanzu shine priority.

Sauri takeyi still da wayar kare a kunnanta dan ta cewa Maman “kar ta kashe har ta k’araso.”
A bakin layin suka ci karo da Junaidu, ganin ta da yayi a hargitse yasa ya shiga tambayar ta “mai ya faru??”
Ce masa kawai ta yi “Ya nemo mai adaidata ya kawo k’ofar gidan Baba yanzun nan.”

Da farko kamar ba zai yi ba, domin kuwa shi Yaji! ma yake shirin yiwa gidan gaba d’aya
saboda kwata kwata baya son ya had’u da Huda don idan yana ganin ta kishi zai iya sakawa ya bubbugeta, shi kuma baya son hakan ta faru.
Dan haka ya yanke shawarar barin gidan for some time.

Ji yayi zuciyar shi tana bashi shawarar ya yi abinda Ummun tace dan haka kawai ya nufi titi....

Ummu
sai da ta zo shiga gidan tukunna ta lura da Sakina, dan haka a tare suka kutsa kai suka shige.
Suna isa tsakar gidan kuwa suka hango Hudan a kwance malale cikin jini, ga wani makeken katako a kwance a kan cikinta ragowanshi kuma yana jan k’asa, kanta a kan cinyar Mama wadda taketa kuka tana rik’e da waya a kunnenta dayan hannun kuma tana ta shafa kan Hudan.
Kukan da Sakina ta fashe da shi ne ya janyo hankalin ta garesu, aikuwa ganin y’ar uwarta yasa ta fashe da wani sabon kuka abun tausayi.

Ummu ma bata san lokacin da ta fara kukan ba, Sakina kam da gudu ta k’arasa inda suke ta hau kiran sunan “Huda!”
Jin kamar k’arar adaidaita sahu ne yasa Ummu juyawa tana addua Allah yasa Junaidu ne, aikuwa a soro suka had’u da shi yace mata “mai napep d’in yana waje” sannan ya juya zai fita, da sauri tace “dan Allah Junaidu zo ka taya mu d’aukar Huda.“

Da mamaki yake kallonta sai kuma kawai ya bita suka shiga ciki…gabanshi ne yayi mugun fad’uwa da ganin halin da Hudan take ciki, da gudu shima ya k’arasa yana kiran sunan ta yana tambayar Mama “mai ya faru?” Duk a lokaci d’aya.

Da kyar Mama ta iya ce mishi “Ja’afar ne.”

A zabure ya mik’e ransa a b’ace zai yi waje Ummu ta taro shi, tace “Yanzu ba lokacin wannan bane ba, mu ji da lafiyarta tukunna.”
“Sakina, d’auko zanin gado ko wani babban hijabi mu samu mu raba ta da wannan mugun katakon, mu danne jinin sai mu kaita asibiti.”

Hakan kuwa aka yi…
Daga nan suka kinkimeta da taimakon Junaidu aka sakata a napep aka nufi asibitin kusa da su dan emergency ne….

Sai da Umma da Jalila suka ji fitarsu tukunna suka sauk’e ajiyar zuciya a tare
Jalila ta saka dariya kafin tace”Ai ko banza ta wahala!. Da farko fa amma tsorata nayi Umma dan wallahi na d’auka ta mutu ne, sai da na ga Mama ta duba hannunta da wuyan ta tace ‘Alhamdulillah’ tukunnan hankalina ya d’an kwanta, amman da har na fara shirin guduwa wallahi.”

Umma ce tace “ke dalla chan rufe min baki!!! Banza kawai!! kina nan zaune gashi ita har ta yo saurayi mai kud’i!, ke kina fama da malamin maths wanda sai dai yayi ta lissafa uban kud’ad’e amma ba zai iya baki ko sisi ba.
Wannan kuwa kina gani kin san mai kudi ne, kalli kyallen da ya bata, k’amshin turaren jiki duk ya cika gidan nan.
Tunda na dawo kike ta ce mini kin had’a bomb in jira yau burinmu zai cika ashe ke shirme kika had’a ban sanib..”

Cikin katseta Jalila tace
“Wallahi Umma da gaske ni plan d’ina shine Ya Ja’afar ya zaneta sannan ta yi dare sosai tunda kinga ai ba lalle ta gane gidan ba tunda ta dad’e bata je ba, sannan ita kuma Mama idan ta ji mun aiketa gidan ai kinga ranta zai b’aci
Daganan ni kuma inyi ta fad’an maganganu a kanta yadda Mama zata ji haushi ta fusata.
Ni sam ban yi tunanin za ta yo saurayi b...”

“Aikuwa gashi ta yo kuma mai kud’i, kina jin kan zanjen nata kin san Yaron sonta yake yi.”
Cewar Umma.

Shiru Jalila ta yi kamar mai tunani chan kuma tace “Umma kema kin yarda da labarin da ta bayar kenan?”

“To ai shine gaskiya.”
Inji Umma, kafin ta d’aura da “idan ba hakan ba ta Ina wachchar gab’uwar Yarinyar ta san wani zuwa wajen saurayi??? Ni yanzu babban tashin hankalina kar ya zo ya zubewa Babanku kud’i kin san halinshi in dai yaga kud’i, mu je ya yarda ya bashi ita!
Gashi ita kuma wawiya ta yi kwatancen gidan nan kuma nasan ya ji, zai zo….”

Shiru duk sukayi Umma in banda huci ba abunda take yi kana ganinta ka san hankalinta a mugun tashe yake
sannan tayi zurfi cikin tunani.
Me ta tuna? Allah kad’ai ya sani, haka nan ta fara murmushi kafin tace “Allah ya kawoshi lafiya.”
Kawai, ta fad’i hakan still da murmushi a fusakarta.

Jalila dai ba fahimtarta ta yi ba, hakan yasa ta hau gado ta kwanta tana sinsinar k’amshin jikin handkerchief d’in a haka bacci ya yi awon gaba da ita, ta bar Umma tanata faman tufka da warwara.

A chan asibiti kuwa, suna zuwa aka yi emergency da Huda. Likitoci suka rufu a kanta, Allah sarki Junaidu har da kukan sa shima Ummu da Sakina suma suna taya Mama..Har sai da
wata nurse ta zo ta fara musu fad’a tana cewa
“Addua za ku yi mata ba kuka ba, sanna kai kana Namiji kana kuka wa zai basu hak’uri??”
Tukunnan a hankali Junaidu ya mik’e ya fice ya nufi masallaci
Su Mama suma suka shiga k’ok’arin tsayar da kukan su, suna masu addu’ar Allah ya bata lfy ya kawo mata sassauci, dukda hawayen ba daina zuba yayi ba.

Sai da aka yi! aka yi!! Tukunna suka tsayar da jinin, da kyar suka fito wajen awan su 4, dan numfashinta k’in daidaituwa ya yi da farko.
Likitan ne yace “su godewa Allah k’usoshin basu tab’a komai ba. An yi mata tetanus da duk wani abunda ya kamata, an kaita d’akin hutawa za su iya zuwa.”
Daga haka ya mik’a musu takardar bill.
Cikin mutuwar jiki Mama ta fara k’ok’arin mik’a hannu za ta karb’a, Ummu ta yi saurin amsa tana dubawa, kafin ta cewa Sakina “ta hau Napep ya kaita gidan Hajiya Shuwa ta fad’a musu halin da ake ciki ita da su Baabaa Talatu sannan ta d’auko mata jakarta da atm d’inta.” A take Sakina ta wuce.

Wasu zafafan hawayene suka zubowa Mama, a hankali tasa hannuta ta goge sannan ta mik’e ta nufi d’akin da aka yi musu kwatance, inda Hudan take.

Ummu kawai binta ta yi a baya dan ta san abinda ya zo mata rai yanzun har yasa ta kasa yi mata magana.

Kusan a tare suka shiga d’akin,
Ummu ta zauna wajen k’afarta ita kuma Mama ta zauna a kan kujerar dake kusa da kanta a gefen gadon.
A hankali ta shiga gayawa Ummu abinda ya faru har Ja’afar yayi mata wannan aika aikar…

Share kwalla Ummu ta yi sannan tace “Gaskiya Mama ni kam zan d’auki Huda mu tafi gidana da ita, koda kuwa Hajiya Shuwa zata yi fushi. Dan naga alamar burinsu Sadiya su kashe ta ne, wannan wanne irin abu ne??
Ana sallamrta za mu tafi tare ba za su sake ganin ta ba.”

Da sauri Mama tace “a’a Bilkisu, kar kiyi haka, dan Allah. Fushin Hajiya Shuwa bashi da dad’i ni zan fad’a miki wannan, ba zan so saboda ni ki samu matsala da ita ba.
Kawai ki barmu a yadda muke, Allah yana sane da mu...

Wani irin tausayin su ne ya rufe Ummu, ganin tana shirin fashewa da kuka yasa ta yi saurin mik’ewa tana cewa
“Bara inje inda Sakina ta barmu in jirata, kar tazo tayi ta nemanmu bata ganmu ba.”
Tana gama fad’in haka da sauri ta fita tana sakar kukan daya taho mata babu shiri.

Murmushi Mama tayi dan sarai ta gano k’anwar tata.

A hankali ta fara shafa kan Huda wasu zafafan hawaye suna tsiyaya daga idanunta sakamokon kwakwalwarta da ta fara tariyo mata wasu shud’ad’d’un al’amura da suka wakana shekaru ashirin da shida baya.........

………………..
Alhaji Muhammad Madu shine asalin sunan Mahaifin Mama, Mahaifin sa Babarbarene gaba da baya, Mahaifiyarsa kuma y’ar jahar Yobe ce, Fune, Jajere .
Ya fi kama da Mahaifiyarsa domin idan ka kalle sa yanayin farar fatar sa da siririn jikinsa komai nasa irin na fulani ne.
Iyayaensa shi kad’ai suka haifa, sannan sun rasu ne tun yana Yaro.
Mahaifin Anum (Hajiya Shuwa ) shine ya d’auke sa ya rik’e shi kamar d’an sa.
Bashi da d’a Namiji, Shuwa da yayunta mata biyu Allah ya bashi, shiyasa ya rik’e Madu a matsayin d’ansa, sannan an yi zaman mutumci a lokacin da iyayenshi kafin su rasu.

Mahaifin Hajiya Shuwa da Mahaifiyarta gaba d’aya dangin su Shuwa Arab ne.

Mahaifin ta ya kasance Malami Babba a Maiduguri, domin babu inda zaka tsaya a lokacin ka ambaci sunanshi ace ba a sanshi ba.

Shekarun Madu suna d’an ja suka fara zazzafar soyayya shi da Anum. Mahaifin ta yana fahimtar hakan kuwa, ya tsaida wata biyu aka d’aura musu aure, dukda Mahaifiyarta ba wani so take yi ba, dan Anum d’in a wannan lokacin shekarunta 13 kuma tafiso y’ay’anta duk su yi aure a k’abilarsu, gashi Anum d’in tana da masoya sosai a cikin y’an uwa, dan duk Yara masu shekarunta a wannan lokacin babu mai kyau da gashinta, shiyasa ma sunanta ya b’uya daga Anum kowa yake kiranta da Shuwa.

Shikuma Mahaifin Anum, hazak’a da k’ok’ari irin na Madu ya gani dan kaff cikin d’alibansa babu wanda ya taka sawunsa kamar Madu.

Daman chan tun kafin Mahaifinshi ya rasu ya d’aura shi a kan ilimin addini, yanzu kam kusan tare suke tafsiri a masallatai, gashi da k’ok’arin neman na kai.

Ana d’aura musu aure ya nemi zai tafi Kano tare da iyalinsa… domin akwai business kala kala da Abokin sa yake kwad’aita masa ya zo su yi.
Tare suke kasuwanci shi yana chan kuma yana ganin idan yana kusa harkar zata fi bud’ewa.
Shuwa sai a lokacin ta yi kukan Aure saboda ita da a tunaninta a gida za su zauna tunda ta auri Yayanta.

Haka suka tarkato suka yo Kano tana kuka da kyar ya lallasheta a hanya.

Suna isowa Gandun Albasa suka nufa, domin
nan ne Unguwar Abokin kasuwancin nasa ‘Bashir’ wanda suka had’u
shekaru biyar baya a wani zuwanshi da ya yi Maiduguri shi da uncle d’inshi saro huluna…a lokacin Madu ne Yaron shagon ya yi musu sauk’i sosai, dan haka da suka ji dad’i, suka rik’esa…. Ya kan yi musu aiken sak’on
ma wani lokacin, daga baya su bada kud’in, ko huluna aka yi sai ya fara zab’ar musu tukunna ake fara saidawa jama’a, wannan karamcin nashi yasa Bashir wanda yake tsarar shi shima duk wata hanyar samu sai ya san yadda yayi ya sako Madu a ciki(dukda kuwa k’aranci na shekarunsu a wannan lokacin).
Daga nan kuma sai Abota mai k’arfi ta shiga tsakani.
Shima Bashir ya kan tura musu kaya daganan Kano idan farashinsu ya fi tsada a chan domin su saida su samu tasu ribar suma su Madun haka.

Tun a lokacin Madu yaso dawowa kano, dan farashin kaya suna d’an fin hawa anan kamar su huluna da shadda zai a na turo musu daga Maiduguri
sannan akwai business kala kala da Bashir d’in ya kwad’aitawa masa a Kanon.
Mahaifin Anum shi ya hanashi a wanchan lokacin saboda k’arancin shekarunsa, sannan bai kammala secondary ba,yafi son at least ya samu certificate d’insa kafin ya fara tafiye tafiye, kar ya ji dad’in business ya k’i karatun boko….

Suna isowa direct gidan Bashir suka nufa, A lokacin shi ya dad’e da yin aure ya na tare da matarshi Aisha wadda ake kira da talatu da Yaransa biyu maza Jamilu da Usman, Jamilu shekarshi uku sai Usman wanda bai gama rufe d’aya ba.

Alllah sarki Bashir a gidan sa ya bawa Madu da Shuwa d’aki suka zauna na y’an wasu lokuta har Madu ya samu ya tara kud’in haya.
A layin ya kama haya tukun suka tashi, sannan ya sayi wani d’an Fili a gefe kad’an duk cikin layin, ya fara gininsa shima.

A wannan lokacin layin nasu dogo ne sasai kuma Babba amman kwata kwata gidaje hud’u ne a layin ragowar kuwa duk filaye ne. Gidan farko a layin shine gidan K’asimu yana da mata d’aya Khadijah ana kiranta da Laraba da Yaranshi uku Salmanu Umaru da Hansa’u.

Sai gidan Audu da ya yi aure watanni uku da suka wuce da amaryarsa,sai Bashir sai Madu.

K’asimu,
tun lokacin da Madu ya zo basu samu good start ba, hakanan Madun bai kwanta mishi ba saboda shi K’asimu irin mutannen nan ne masu kishi hassada da kyashi.
Madu yana zuwa layin akwai wani masallaci a bayan layi aka bashi ladani, daganan kuma ya koma Limami, sannan ga gida ya kama haya ga kuma fili yana gini ga karatun daya ci gaba na boko (daman ya gama secondary school tun a Maiduguri)ga kuma kasuwanci, hanya bud’e mishi take yi ta ko Ina, gashi kaff layin matansu basu kai tashi kyau ba.

Waennan abubuwa su suka taru suka k’ara rura wutar k’iyayyar Madu a zuciyar K’asimu, saboda shi tunda ya yi aure yau Yaran shi uku amman yana fama da gidan haya, sannan ya so a bashi wani matsayi a masallaci amma an k’i, gashi kasuwancin ma har yau Yaron shago ne shi Amman shi Madu daga zuwansa ko shekara biyar bai yi ba kalli yadda ya zama shahararre kusan kowa ya sanshi d’aukaka ta ko Ina ya sameta.
SHARE PLS.

BULAMA ✍️

So da Buri
Free Book
09

Tun K’asimu yana b’oyewa har ya zo ya fara nunawa a fili…daga ya je chan ya tsugunna ya zagi Madu sai ya je chan ya tsugunna ya yi masa sharri. Babu inda zai zauna ya tashi bai zage sa ba, shi kuwa Madu harkar gabansa kawai yake yi sam baya bi ta kan K’asimu dan ya lura ko sallama idan yayi masa ba amsawa yake yi ba.

Tsananin tsanar Madu bata sake tabbata a zuciyar K’asimu ba sai a lokacin da kud’in hayar shi K’asimun na wajen shekaru uku ya taru, anyi anyi ya biya ya k’i biya, gashi gidan na marayu ne suma suna fama da yanayin rayuwa…jin labarin sabon limamin da a ka nad’a ba da jimawa ba mai aiki da addini gashi yayi karatun lauyoyi duk unguwa ana girmamashi ne ya sanya waennan Marayu suka garzayo wajen Madu akan ya taya su fad’in gaskiya a basu hakkinsu, ai kuwa Madu bai yi k’asa guiwa ba sai da ya tabbata ya karb’a musu hakkinsu har saida ta kai ga tirsasa K’asimu siyar da y’an dabbobim shi ya biya su hakkinsu da kud’in….

Jarumta da tarin ilimin Madu ne ya sanya aka nad’asa ‘mai unguwa’ a lokacin shekarar sa goma da zuwa garin Kano.

Sai kuma a lokacin ne Allah ya bawa Shuwa ikon samun ciki.
Kusan a tare suka haihu ita da matar Bashir da matar K’asimu.
Matar kasimu itace ta fara haihuwa,ta haifi y’arta mace aka sakamata Halimatus Sa’adiyyah sai matar Bashir ta haifi y’arta itama mace Zainab
Shuwa itama ta haifi mace, Maryama.
Duk a tsakanin haihuwar watanni bibbiyu ne.
Murna a wajen Madu kuwa ba a magana, saboda daman shi akwaishi da son Yara, shiyasa su Usman da Jamilu sunfi sakewa ma da shi fiye da Mahaifinsu dan idan ba sani ka yi ba ko fad’a maka akayi ba to ba zaka tab’a cewa Madu da
Bashir ba y’an uwa baneba
saboda tsananin shak’uwa da k’aunar junan dake a tsakaninsu, gashi yanayin jikin su iri d’aya….

Maryama ta taso cikin gata saboda tsananin so da k’aunar da Mahaifin ta yake nuna mata, ga kuma yayyunta guda biyu Usman da Jamilu dan wani lokaci har fad’a akeyi wajen d’aukar Maryam tsakanin Jamilu da Usman dukda kuwa ga Zainab k’anwarsu.
Idan Maryam tace tana son abu nan da nan Mahaifinta zai nemo sam baya bari ta sake tambayarshi a karo na biyo dukda kuwa ba wani k’arfi ne da shi ba, Law ya karanta a lokacin albashinsa ba wani yawa ne da shi ba amman idan kaga Maryama ko y’ar gidan wani hamshak’in mai kud’in sai haka, suturar jkinta kad’ai abun kallo ne.

Tana isa shekara hud’u Madu ya had’ata da Zainab ya saka a makaranta, a wannan lokacin har sai da Talatu ta bawa shuwa shawarar a nemawa Maryama maganin baki da mayu saboda babu inda zata je ba a tankataba…Yarinyar chubby da ita gata fara farin ta irin mai yellow d’innan, gashin gira da idonta a ciccike ga gashin kai har gadon baya mai sulbi, idan ka kalle ta dole ka k’ara.

A haka rayuwa ta ci gaba da tafiya har Maryam da Zainab suka kai shekaru goma a duniya, sai a lokacin ne kuma aka saka y’ar gidan K’asimu (Sadiya)a makaranta da kyar!
Don a lokacin duniya ta yi masa zafi, yanayin rayuwa sai a hankali kuma shi ya dage ba zai sakata a makarantar gwamnati ba, a dole ta kud’in da su Maryam da Zainab suke zuwa nan itama zata je, a cewarsa ‘ai tare aka haifesu’
Bayan shi basussukan da suke kanshi kad’ai ma abun mamaki ne,dan idan aka gaya maka zaka rasa Ina yake kai kud’in,
abu guda d’aya dai shine ko takalmi ne idan Madu ya sauya yau to tabbata sai ka ga irinshi sak a k’afar K’asimu washegari, duk wai dan ya nunawa duniya ‘ai Madun bai fi sa kud’i ba’ (a cewarshi), sai dai kuma duk inda aka yi sati 1ko2 nan zaka nemi takalmin ko suturar ka rasa saboda ya siyar ya cinye kud’in a banza. Yaransa duka uku babu mai zuwa makaranta da kyar ya saka Sadiya.

Layin nasu zuwa yanzu ya cika sosai dan a k’alla gidaje sun kai sha biyar, Bashir ya sayi filin jikin gidanshi ya had’e ya kuma yin wani had’add’en gini, Madu shima ginisa a layin gwanin ban sha’awa daman shi filin sa tafkeke ne ya siya, amman shi K’asimu har yanzu yana wannan gidan haya na marayu wanda k’arfi da yaji yake so ya danne ya mayar da gidan nasa.
Matarshi ta so ta had’u da Talatu da Shuwa amman tunda ta so had’a su fad’a Allah ya taimaka sukai saurin ganewa munafuka ce, sai suka yi saurin
ja baya da ita, amma duk da ja bayan da suke yi da ita hakanan sai ta yi ta nanik’e
musu. Inda Allah ya taimake su sai wata dillaliya ta tare, nan ta koma suka jone, aikuwa tun daga wannan lokacin in dai ka ji hayaniya da fad’a a layin to ko daga gidan dillaliya, ko gidan K’asimu dan basa barin takwana, ko kallo ne kayi musu bai musu ba nan za su fara surfa ruwan bala’i, ga rashin sanin ya kamata da munafurci......

Wata rana cikin azumi K’asimu yana zaune a bakin titi…duk magidanta da samarin unguwar suna masallaci ana sauraron tafsirin Modu amman shi ya k’i shiga tsabar bak’in hali, saboda baya shiri da Madu kuma akwai maza guda hud’u a cikin masallacin waenda yake gaba da su, dan haka ya gwammaci ya zauna shi d’aya har lokacin shan ruwa ya yi yaje ya amshi abun sadaka yayi gida domin dashi suke karya azumi….ko kwayar shinkafa babu a gidanshi.
Suna cikin masallaci sukaji kamar k’arar jiniyar y’an sanda, sunan nan zaune suka ji k’arar tana ta matsowa. Kasancewar lokacin addu’a ya yi ya sanya suka rufe sukai addua
masu son yin alwala suka mik’e suka yi waje…suna fita kuwa sukaga Yara sunata gudu sunayin titi,wani a cikin su ne ya tare wani Yaro ya tambayeshi “mai ya faru” shine Yaron yake ce musu ,
“wai motar sojiji ne mota uku, da na y’an sanda suka zo za su tafi da Baba K’asimu.”
Da sauri wasunsu suka yi bakin titin wasu kuma suka koma cikin masallaci domin sanar da ragowan mutanen.
Waenda suka yi bakin titin ne suka hango K’asimu ana ta k’ok’arin dannashi a motar y’an sanda yana tirjewa,yana bada hak’uri amman kafin su k’araso wajen har an tafi da shi.

A bakin Yaran gurin suka ji cewa wai “Kud’in wani kurtun soja ya amsa ya sayi mota tun watanni biyar baya, kuma yace zai biya kud’in amman har yanzu be biyaba.”
Cike da tarin mamaki suka koma masallaci domin lokacin shan ruwa ya yi, suna isa suka bud’a baki da dabino da ruwa akai Sallah kowa yayi gida domin karyawa.

Basu samu lokacin bin bayan K’asimu ba sai da suka idar da asham
Da Madu da Bashir da wasu mak’oftansu guda biyu (Kabiru da Nafi’u)suka tafi a motar Madu.
A cikin motar ne su Kabiru suke hira da Baba Nafi’u wanda yake tambayar “shin wai yaushe K’asimu ya sayi mota ne shifa bai tab’a ganin motar ba.”
Nafi’u ne yace “ai tun watanni shida da suka wuce lokacin da Madu ya sayi mota shima ya tada hankalinshi ya dinga bi yana tambayar bashi kusan kaf layin duk wanda baya gaba da shi saida ya tambaya bashi aka hanashi.”
Nafi’un ya d’aura da cewa “nima sanadiyyar ya tambaye ni aron kud’i nace masa bani da kud’i ya sanya ya fara gaba da ni har da ce mini ‘wai ni ba makwafcin gaskiya bane ba, Ina yi mishi bak’in ciki….’
To dai na ganshi da mota after one month kuma ina kyautata zaton a wajen wannan kurtun ya karb’a Aron kud’i dan bai dad’e da tarewa ba a bayan layi lokacin.”

Kabiru Yace ”Ikon Allah to ai ni ban tab’a ganin motar ba.”

Dariya Nafi’u ya yi yace”Ai motar ba ta kwana ba inaga damfarar sa masu siyarwan suka yi. A ranar da ya siyota ya kawo ya zo yayi parking, haka nan ta dunga hayak’i ta cika unguwa saida athmar d’in Laraba ya tashi…nifa da na fara ganin hayak’i wallahi na d’auka gobarace ta tashi a gidan nasa, lokacin dawowa ta kenan daga kasuwa ko gidana ban shiga ba na ce bara in duba gidan nashi inga, Ina lek’awa kuwa na hango shi da salmanu da Umar sunata bulawa motar k’asa don k’ok’arin kashe hayak’in. Hansai kuma tanata kuka ita da Sadiya suna jijjiga mahaifiyarsu wadda ta sassank’are tana numfashi da kyar. Ban bi ta kansu ba naje da kyar na nemo abun hawa aka kai Laraba asibiti, shikuma ya tafi kai mota gyara…kusan duk d’an abin hannunshi saida ya k’are a wajen gyaran motar nan.
Daga karshe ya maidawa wanda ya saya a wajenshi shi kuma ya ce an kwak’ule motar a wajen gyara bata da wani amfani, inaga a dubu hamsin ya saida motar da kyar,ya amshi kud’in, dan ta tashi a aiki....”

Madu ne ya katse musu hirar su ta hanyar ce musu “Mun iso!!”
Suna shiga kuwa sukaci sa’a inda suka je d’in aka kaishi, bayan sun buk’aci ganinsa ne aka fiddoshi
Har an fara sauya mishi kamanni. Da farko ya so yayi tirjiya da b’oye b’oye,amma da yaga ba sarki sai Allah sai kawai ya hak’ura ya gaya musu gaskiya “kud’in kurtu ya karb’a ya sayi mota kuma shi yanzu bashi da halin biya.”

Madu da Bashir su suka had’a kud’i sukai belling shi, bayan ya dawo gida Modu da Bashir suka bada rabin kud’in mota, shima K’asimun d’an kud’in hannun shi ya tattaro ya had’a da adashin Laraba aka had’a duk amman dukda haka kud’in bai cika ba…Da kyar da taimakon wasu makwaftan aka had’a ma kurtu kudinshi dan cewa ya yi “Wallahi bai san Asara ba!.”

Bayan sun dawo gida ne da washegari, Modu ya samu Baashir yace masa “su taimaka su had’awa K’asimu kud’i su bashi ya ja jari ya daina yawon neman bashi,tare aka taso bai kamata su barshi a haka ba.”
Dama shi Bashir da kyar ya yarda, ai kuwa!!…..a cikin azumi suka bashi kud’in lokacin yanata murna yayi ta godiya har da rungume Madu. Bayan Sallah tana yi K’asimu ya rangad’a sabon Aurensa, ya auro baffulatana Yarinya y’ar k’arama shekara d’aya Jamilu ya bata.
Ai kuwa gidan nan nasa ya sake hargitsewa, gashi shi
ba wata tsayayyiyar sana’a garesa ba dan haka kowa zuciyarsa a kusa! kullum cikin fad’a, daman itama amaryar irin marasa kunyar nan ne, kowa baya ragawa kowa.
Yadda basa ragawa junansu hakanan y’an waje ma ko kallo ka yiwa d’aya daga cikin Yaran In bai musu ba duk girman mutun haka zasu zuba maka tujara, shiyasa ake yiwa gidan Lak’ami da
‘Gidan marasa tarbiyya,’
sun kuwa tsani sunan idan sukaji sunan a bakin wani tofa ranar rigima sai inda k’arfinsa ya k’are.

A wannan lokacin ne kuma Shuwa ta sake d’aukar ciki, Maryam da Zainab da Sadiya sunada shekara goma a duniya.
Murna a wajen Maryam da Zainab ba’a magana dan har sun fara shirya kalar party d’in da za su yi idan Shuwa ta sauk’a lafiya.

Kullum kuma cikin addua suke Allah yasa k’anwa za a haifa musu don su dinga yi mata kitso suna yi mata kwalliya.

Wani abun mamaki, Zainab k’awar Maryam ce sosai a da amma tunda ta fara zuwa makarantar su sai suka had’ewa Maryam kai, ita Zainab ashe dama tuntuni tana d’an jin haushin Maryam saboda su Ya Jamilu sun fi sonta, da taimakon zugar Sadiya kuwa k’iyayyar Maryam ta samu waje a zuciyar Zainab, daman chan ita Sadiya ta tsani Maryam domin kuwa ita ya’yan masu kud’i ta so yin huld’a da su amma sam basa kulata Maryam suke so da k’awance duk da ita kuma Maryam d’in bata kulasu sosai dan bata da hayaniya.

Duniya ta fara yiwa Maryam zafi a lokacin da k’awarta kwalli d’aya ta juya mata baya. A yanzu ko kaisu makaranta Zainab bata yarda a yi tare balle a d’aukosu, ta gwammaci ta biyawa Sadiya su tafi a k’afa su dawo a k’afa! Wanda har su je su dawo kuwa basu da aiki sai na zagin Maryam ita ba amma ta san suna yi ba. Ana cikin haka ne Shuwa ta haihu, ta samu y’arta mace ranar suna taci suna ‘Bilkisu’ , bayan suna Maryam ta had’a party duk wani Yaro saanta ta gayyata ana I washegari amman Sadiya sai ta hana Zainab zuwa sannan ta sakata ta sato kud’in Babanta da ya ajjiye, abinda bata taba yi ba.
Haka nan dinga bin Yara suna raba musu kud’i akan ‘ “kar su je Partyn Maryam’ wai ta saka guba a lemo, su jira su gani babu wanda zai je saboda bak’in jini ne da ita.”
Ai kuwa hakan akayi ko wanne Yaro ya karb’i kud’i yak’i zuwa party kar ya je a bashi guba.

A ranar Maryam kwana tayi tana kuka, tun daga ranar kuwa bata isa fitaba sai Yara su fara mata wak’ar ‘mai bak’in jini’ Sadiya ta kafa ta tsare duk wanda taga yana shirin fara yin k’awance da Maryam nan da nan za ta saka Zainab ta je ta sato kud’in mahaifinta ta bawa Yaran tace su zab’a ko kud’i ko k’awance da Maryam.

Bashir tun baya fahimta har ya fara fahimtar ana d’aukar masa kud’i…
A haka shekaru suka yi ta shurawa abun tun yana damun Maryam harta hak’ura ya daina damunta da taimakon Shuwa.

Ranar wata Juma’ah Baba Bashir ya tafi masallaci aka y rashin sa’a ya manta bai d’auki darduma ba kuma ya makara don Madu yayi tafiya so ba tare za su tafi ba, hakan ya sanya ya dawo…yana shiga
d’akinsa kuwa ya kama Zainab dumu dumu, ai kuwa ta daku a ranar kuma ya titsiye ta sai da ta fad’a mishi komai plan d’insu da Sadiya ba abinda ta b’oye…..

Kunya! kamar k’asa ta tsage Bashir da Talatu su shige haka sukaji…mutumin da yake biya mata kud’in makaranta bai tab’a nuna gajiyawa ba shine take yiwa y’ar sa haka??.
A lokacin suna aji biyu a js amman babu shiri aka siya mata form ta yi junior waec , aka fara shirin tura ta boarding. Madu yana dawowa Bashir ya rok’esa yace “yanaso zai had’a da Maryam ya kaisu makarantar kwana, anfi karatu dan kwata kwata Zainab bata karatu”.
Sam Madu bai so hakaba don baya son yayi nesa da Maryam amman kawai sai yayi kawaici ya amince, Bashir a tunanin sa Zainab da Maryam za su shirya ne idan an kaisu boarding tare tunda daman chan k’awaye ne, kuma yana kyautata zaton Sadiya ce ta had’asu fad’a. Sai dai kuma ko da akaje boarding d’inma, farin jinin da Maryam take da shi a wajen Malamai da d’alibai sai ya sake jawo mata bak’in jini a wajen Zainab, sannan Yayanta Usman sai ya zo makarantar sau da yawa wajen Maryam amman ita sai dai ya bada sak’o yace a bata, kuma sai ya cukowa Maryam leda da kayan kwad’ayi amman ita sai ya bada kad’an yace a bata..
Abunda ba ta sani ba a ko da yaushe sai Maryam d’in ta k’ara mata a kan wanda Ya Usman d’in ya bayar yace bata.

Haka kurum sai ta daina kulata ko ta hau yada magana idan ta ganta, shirin da akeso dai su yi bai yiwu ba domin kuwa alamarin k’ara tab’arb’arewa ma yayi don kwata kwata Zainab da Maryam basa shiri,duk mates d’insu sun sani.
Har sai da Zainab ta kai Maryam bango duk kuwa hak’urinta sai da ta tanka mata sukayi wani damben da suka jiwa kansu ciwuka har aka kai ga kiran iyayen su, sai a nan ne Madu ya ji abinda ya faru har Bashir ya kaisu boarding duk dan ya samu daidaita tsakaninsu.
Ganin k’ok’arin Bashir na ganin zaman lafiya ya wanzu ya kuma tabbata a tsakanin Yaran nasu ne ya sanya kawai shima Madu ya barsu sukaci gaba da boarding d’in.

Wanda bayan sun dawo hutun gama ss1 ne Ya Usman ya zo da zungureriyar wasik’ar shi ya bawa Maryam ta inda ya ke bayyyana mata cewa shi fa sonta yakeyi tun tana y’ar k’aramar ta….
Ita dai Maryam ba zata ce bata son Ya Usman ba saboda Yayanta ne kuma ya kula da ita sosai, amman a gaskiya so na soyayya sam bata yi masa kwata kwata. Ko da ta gayawa Umma Talatu da Hajiya Shuwa..kalar murnar da ta gani a kan fuskokinsu ne ya sanya kawai ta amince suka fara soyayyarsu ita da Usman gwanin ban sha’awa.

Zainab kuwa (duk da kaita boarding school d’in da akayi hakan bai saka sun rabu da Sadiya ba, don indai aka aike Zainab to sai ta biya wajen Sadiya a b’oye).
Ai kuwa tanajin labarin soyayyar Maryam da Usman,
Sadiya ce kawai ta fad’o mata a rai, dan ba zata iya irga adadin wasik’un da Sadiya ta bata ta bawa Ya Usman ba..tun tana y’ar shekara sha d’aya take son Ya Usman,
shi kuma Ya Usman idan akwai wadda ya tsana a duniyar nan to Sadiya ce! Idan ka kalli Sadiya sam ba zaka tab’a ce mata mummuna ba, ba doguwa baceba amman tanada manyan idanuwa da matsakaicin hanci bakinta dai dai misali ga dimples a fuskarta sai dai bak’a ce amman tanada dirin jiki mai kyau sannan tanada gashi wanda ya sauk’o har kan kafad’arta, sai dai sam waennan qualities na Sadiya basu d’ad’a Usman da k’asa ba hasalima shi ya tsane ta kwata kwata bata kwanta mishi ba..
A cewarshi Yarinyar bata da kamun kai, ga munafurci irin na Ubanta dan sarai ya san ita ta shiga tsakanin Maryam da Zainab, shiyasa daya ga nacin nata yana neman yi mishi yawa ya had’asu ita da Zainab d’in ya ci ubansu, tun daga ranar ya samu sa’ida.
Sai dai fa dukda hakan da yayi sam soyyarshi a zuciyar Sadiya ba abinda ya ragu sai ma k’aruwa da tayi….

Da wannan tunanin Zainab wadda ta saci hanya ta isa gidansu sadiya, bayan sun gaisa da Baba Laraba ta tambaye ta Ina Sadiya tace mata “Tana d’aki”.
Tana shiga ta sameta a kwance tana bacci, jijjigata Zainab ta shiga yi har sai da ta farka sannan ta shiga koro mata halinda ake ciki

A ranar Zainab ta sake gasgata soyayyar Usman a zuciyar Sadiya domin kuwa kuka ta dinga yi harda ihu kamar wata y’ar k’aramar Yarinya da kyar suka lallasheta ita da Baba Laraba bayan ta shigo Zainab ta gaya mata halin da ake ciki.

kafin ta bar gidan kuwa zazzab’i ne mai zafi ya rufe Sadiya dan ko idanunta bata iya bud’ewa.

Satin Sadiya uku tana rashin lafiya, idan ka ganta sai ka tausaya mata, duk ta rame ta fita a haiyyacinta, har shagon d’inkin Usman taje tai sallama da shi daya fito tayita masa kuka, ganin da yayi abun nata na gaske ne yasa ya lallasheta ya rakata gida, wannan itace rana 1 daya mata magana mai dad’i shiyasa tana dawowa gida har mamakinta Laraba ta dinga yi saboda yadda ta ware kamar ba ita ba.

Hutun makaranta ya k’are!
su Maryam an fara shirin komawa, wannan karan Baba Bashir ne ya yi musu provision da kyar Madu ya bari kuwa.
Ranar Lahadi Usman da Madu suka maidasu makaranta.

BULAMA ✍️

So da Buri
Free Book
10

Ranar Monday aka yi chanjen aji, sannan da yamma aka nad’a shadow prefects wanda a ciki har da Maryam, Maryam ta so an bawa Zainab itama domin zuwa yanzu Maryam ta lura a duk lokacin da ta samu abu Zainab d’in bata samuba ne suke samun matsala da ita.

Duk da k’ok’arin ganin an zauna lafiya da Maryam d’in take yi hakan bai hana Zainab kyarar ta ba kasancewar hostel d’aya suke room d’aya aji d’aya kuma seat d’aya.

washegari Tuesday, suna zaune suna jiran first period na English, English theacher d’in ya shigo tare da wani kyakkyawan saurayi sanye cikin khakin sa na nysc,
kusan duk matan ajin ido suka zuba mishi….
Har suka k’araso bakin board suka tsaya da shi da English teacher d’in idanunsu na a kanshi, shi kam bai ma san suna yi ba don idanunsa suna a k’asa yana kallon k’asa yayinda su kuma ko fahimtar bayanin English teacher wanda yake cewa “ga sabon copper shi zai dinga yi musu English a yanzu for 10 months, daganan idan ya gama service d’inshi ya tafi aiki zai dawo hannunshi kamar farko” basa yi, har sai da yace “Are u guys with me??”
Da d’an k’arfi, tukunna hankulansu ya dawo jikinsu, suka ce “Yes sir.”
Banda Zainab wadda tayi mutuwar zaune, dan a lokaci d’aya ta ji bawan Allah n ya tafi da imanin ta.
Kasancewar Madu da Bashir sun gayawa Malaman su su dinga zaunar da su sit d’aya ita da Maryam ya sanya akoda yaushe suna tare, hakanan wani lokacin zainab sai ta kawo jaka ta saka a tsakiyar su wai kar jikin Maryam ya goge ta ta kwashi bak’in jini,
Amman yau kam zainab bata san lokacin da ta kamo hannun Maryam da k’arfi ba!
Ita maryam d’inma tsorata ta yi dan kwata kwata hankalinta baya ajin, ya tafi ga takardar da take hannun ta tanata bitar debate d’in da za suyi da safen nan, kawai ta ji an damk’o hannunta kamar za a karya ta.
Kallonta ta yi amman sai ta ga hankalinta gaba d’aya baya tare da ita, wani wajen ma daban take kalla.
Da sauri ta kalli inda zainab take kallo ta ga englishi teacher yana ta zuba bayani a gaban board da wani balarabe a gefen sa da koren kaya a jikin sa….dan haka ta juyo gareta cikin kulawa tace
“Zainab menene?”
Kallon ta zainab d’in ta yi sannan tace
“Maryam kinga wannan kyakkyawa ko?.
Dama haka ake ji a lokacin da ka ga wanda kake so? kinji yadda k’irjina yake bugawa kuwa? haka kike ji idan kika kalli ya Usman?”
Ta yi mata tambayar tana mai sake kallon saitin da copper d’in yake.

Wani farin ciki ne ya lullub’e Maryam dan rabon da zainab ta yi mata magana mai tsaho haka har ta manta…dan haka ta saki wani k’ayataccen murmushin da ya sake fito da ainihin kyawun fuskarta sannan ta d’ago kanta domin ta kalla wanda y’ar uwarta ta haukace a kai haka cikin lokaci k’ank’ani. Tana d’ago kan nata dai dai shikuma English teacher ya mik’a masa chalk yana cewa “introduce yourself to them.”
Karb’a yayi sannan ya d’ago
daidai ita kuma Maryam ta juyo tana murmushi a take idanunsu suka sark’e a cikin na juna! Bai san ya aka yi ba kawai ya ji chalk d’in dake hannunsa ya fad’i k’asa! Lokaci d’aya zuciyarsa ta hau bugawa da sauri da sauri….
Itama Maryam kusan hakan ne a nata b’angaren, jin yadda zuciyarta ke bugawa gashi ya tsareta da manyan idanuwanshi farare k’al masu kama dana mai jin bacci, hakan ya sanya ta saurin sunkuyar da kanta k’asa.
Maganar Mr Solomon ce ta dawo da shi daga duniyar daya tsinci kanshi a ciki dak’ik’un k’alilan da suka wuce.
Chalk d’in da ya yar yaga yana mik’a mishi sannan ya sake cewa “introduce yourself to your students.”

A hankali ya saka hannunshi ya karb’a sannan ya sake juyawa ya kalli inda Maryam take a ranshi yana adduar Allah yasa ta sake d’agowa ya kalli fuskarta, domin kuwa baya jin akwai abinda ba zai tab’a gundurar sa a duniyarnan kamar kallon fuskar wannan extraordinary beautiful young lady d’in ba.

Ganin tak’i d’agowa ne yasa shi juyawa…a hankali ya k’arasa jikin black board d’in ya rubutu sunan shi kamar haka
‘YAKUBU UMAR FAROUK M.T’
Sannan ya juyo ya kalli students d’in yace “that’s my name, but u can all call me ‘ABBA’
I’m your new English Teacher....”
Cikin nutsuwa ya karanto musu tsarinshi kamar ‘baya son surutu a aji sannan yana son in ya bada assighment a dinga maida hankali ana yi......’
Sai da ya gama tukunna Solomon yace “akwai debate d’in da ya basu as an assignment group A B and C”.
sannan ya mik’a mishi textbooks d’in da suke hannunshi ya juya ya fita….

Cikin kwarewa da nutsuwa Abba yake koyar da su, sun nutsu kuwa suna fahimta sosai don duk hankalin su yana a kanshi, sai da ya gama yace “Ina masu debate?”
Maryam ita take representing group A, dan haka ta mik’e tsaye. A hankali cikin sauk’e ajiyar zuciya yake kallon ta, kafin ya janye idanunsa ya mayar kan group leaders d’in B and C da suka mik’e sannan yace “su fito gaban board”.

Topic d’in yana magana ne a kan who is more responsible a karatun Yara
A, parents
B, teachers
C kuma both.
Maryam itace mai parents.
Haka suka dunga mahawarar a tsakanin su har kowa ya kawo gaba d’aya points d’inshi.

Points d’in da Maryam ta kawo ko kai shed’an ne dole ka san itace winner! Danhaka ya bawa group d’inta 10/15
ragowar groups biyun kuma ya basu 6.
Bayan sun koma seats d’insu sun zauna ya tambayesu ko “akwai mai question”,
sukace “a’a”hakan yasa ya tattare books d’inshi, ya duba time table yaga sai Friday shida ya sake shigowa ajin. Daga haka ya yi musu sallama ya fita.

Ai kuwa kamar jira sukeyi yana fita kowacce ta hau tofa albarkacin bakinta, wasu su ce balarabe ne wasu suce d’an India wasu kuma pakistan, gashi daga ganin sa ka san d’an masu kud’i ne! Nan ajin ya haukace da zancen sa har sai da malamar next period ta shigo tukunna aka samu ajin ya nutsu da zancenshi.

Kafin kwana biyu, gaba d’aya makarantar ta d’au zancen copper Abba balarabe (sunan da suka saka mishi kenan)
Hatta junior section ba’a barsu a baya ba, masu love letters suma yi suke yi su je su zira ta saman glass d’in motasa
Inda yake d’an bari kad’an a
zuge saboda iska ya d’an dinga shiga.

Zainab tun ranar da ta fara ganinsa ta haukace bata da labari sai na Abba, hannuta kuwa kullum da kalar design d’in da za ayi da biro a cikin heart d’in a rubuta ‘Abba’
duk inda kuwa akace Fridays Mondays ko Tuesdays ( ranakun da suke da English kenan) hakanan za ta rambad’a kwalliya ta yi skipping assembly kuma, dan kar a goge mata.

Kamar yadda y’an makaranta suka haukace da ganinsa hakanan shima zuciyarsa ta haukace tunda ya ga Maryam.
Yau satin sa biyu da fara koyar da su kuma zuwa wannan lokaci kam ya gama fahimtar son Maryam yake yi domin kuwa tun ranar farko daya ganta ya rasa nutsuwarshi gaba d’aya bashi da burin da ya wuce yayi ta ganinta, har Allah Allah yake ranar da zai shiga ajinsu ta yi ya samu ya sake sakata a idanunsa.

Through out this week ko me yake yi kawai tunanin ta yake yi. Ganin da yayi yana b’atawa kanshi lokaci yasa kawai ya yanke shawarar gaya mata in his next period, dukda kuwa yana fargabar mai amsarta za ta kasance, duba da yanayin k’arancin shekarunta amma kuma ya san ‘a bari ya huce shi ke kawo rabon wani.’

Yau Monday!! kasancewar Abba ba’a staff quarters yake da zama ba..gida ne guda mahaifin shi ya siya mishi saboda service d’in da aka turo shi…ya sanya ya tashi da sassafe dan baya son ya makara, kuma akwai d’an tazara tsakaninsu da makarantar.
Har yayi wanka yayi breakfast yana murmushi jifa jifa shi kad’ai, kawai idan ya tuna zai ganta yau sai yaji wani farin ciki ya lulllub’eshi .

Duk saurin shi kuwa sai da aka gama assembly tukunna ya samu ya zo. Zainab yau sneaking ta yi bataje assembly ba saboda ta shafa jambaki da powder ga kwalli ta saka kuma ta san indai aka ganta to punishment ne bayan an sakata ta goge.

Y’an aji suna fara shigowa suka ganta a zaune, wata classmate d’insu ce tace “wato yau sneaking kika kuma yi ko?Hmm bai ma fa san kina yi ba! Dan ko kallonki baya yi.”
Dariya tayi kafin ta sake cewa “tou shadow sai ki rubuta sunan y’ar uwarki, a cikin masu sneaking in dai ba son kai bane abun”
Ta yi maganar referring to Maryam.

Ko gama zama ba su yi ba Abba ya shigo ajin hakan yasa zainab ta had’iye masifar da ta taso mata take shirin juyewa classmate d’in tasu tahau murmushi tana kallonsa.

Cikin dabara ya kalli wajen zaman Maryam yaga tana goge wajen zaman ta da duster kafin a hankali cikin nutsuwarta ta zauna sannan ta fara yiwa Zainab magana a hankali…
Ajiyar zuciya ya sauk’e a hankali sannan ya amsa gaisuwar da suka shiga yi masa.

Bayan ya kammala duk abunda ya kamata yace dasu “su ciro takarda zai yi test”.

Hakan kuwa aka yi….
Lokaci yana cika ba tare da ya b’atawa kanshi lokaci ba ya kalli Maryam yace “ta tattare gaba d’aya papers d’in ta kai mishi office.”
Sai da ya ga fitarta tukunna ya bi ta a baya.
Jin kamar mutum a bayan ta yasa ta juyo, ganin shine ya sanya ta d’an tsaya sai da yayi gaba tukunna ta bishi a baya saboda daman ko taje Admin d’in sai tayi tambaya tunda ba sanin office d’insa tayi ba.

Office d’inshi kusan shine na k’arshe a jerin k’ananun offices d’in da suke wajen…suna zuwa ya saka hannu cikin aljihun wandonshi ya zaro key ya bud’e ya tura ya shiga sannan a hankali yace mata “Bismillah”.
Sallama tayi ta shiga…office d’in d’an k’arami ne, sai dai ya had’u sosai, sai
k’amshi yake fitarwa, ga wata k’ofa a gefe wanda tanada tabbacin toilet ne….
Maganar sa ce ta dawo da ita daga duniyar k’arewa office d’in nasa kallo data tafi, jin yana cewa
“Zauna mana, ga seat.”
A hankali ta ajjiye takardun a kan tebur sannan ta girgiza kai ta juya za ta fita taji yace
“I order u to sit.”
Sai da tayi kusan 1 minute sannan ta zo ta zauna kan kujerar da take facing tashi benci ne kawai a tsakaninsu.

Sai da ya d’an sauk’e ajiyar zuciya kafin yace “from which state are you ?”

“Kano”
ta bashi amsa.

“Which area??”

“Gandun albasa”
Ta fad’a a tak’aice.

“Are u sure?”
Yai mata tambayar kafin yace
“cos banga alama ba, at all”

Da mamaki ta kalleshi, kafin tace “U too”
Sannan ta mik’e tace
“Please sir zan tafi muna da test.”

Mik’ewa shima yayi yana murmushi kafin yace “sai yaushe? Ba kiyi mini kwatancen gidanku ba balle in kawo miki ziyara idan an yi hutu, ko bakya so in zo???“

Da sauri ta d’aga mishi kai
alamar ‘eh’.

With surprise yace
“Y”

“Nothing”
Kawai ta iya ce mishi sannan ta sunkuyar da kanta k’asa, tana adduar Allah yasa ya bata izinin tafiya, dan bata san daliliba in dai suna waje d’aya ji take tamkar zuciyarta za ta
faso k’irjinta ne ta fito waje, tsabar bugawa.

Abba fahimtar da yayi kamar yana yin komai cikin sauri..kar kuma yaje ta k’i shi idan taga zalamarshi…hakan ya sanya ba dan ya gamsu da shawarar da zuciyarshi ta bashi ba kawai ya bata izinin tafiya.

Ai kuwa da sauri ta juya ta fita a office d’in.

Zama yayi a kan kujerar sa, sannan ya bud’a hannunshi kafin ya kaisu duka biyu bayan k’eyarsa kamar zai yi filo da su…
Lumshe idanuwanshi yayi sannan ya fara tunanin duk wani possible hanya da zai b yayi getting close to her, dan ya lura he needs her attention first.

A bakin Admin block d’in taci karo da Zainab tana ta faman kai kawo, tana hango ta kuwa ta iso tana tambayarta inda office d’in nashi yake..kwatance Maryam d’in tayi mata daga haka tayi gaba, bata san ya sukayi ba....

A b’angaren Abba kuwa, a da
k’arfe 2 yake tashi ya tafi gidanshi, amman yanzu voluntarily yayi exceeding time d’inshi har 10 pm (Time d’in tashi daga night prep) ko tsoron hanya baya yi, hakanan
yacewa mai principal kawai zai dinga supervising evening and night prep, Friday kuma zai samu aji ya dinga k’ari a sms. Da murna kuwa principal d’in ta yarda, dan yace ba sai an bashi ko sisi ba.

Kasancewar Maryam shadow ce ya sanya ba a ajin su take night prep ba, a jss2 take zama tana supervising d’insu.

Tana zaune kawai ta ji kamar an shigo tana kallon k’ofa kuwa suka yi ido biyu….kujerar teacher ya janyo ya kawo dai dai gefen sit d’inta ya ajjiye sannan ya zauna kafin yace mata “Good evening ma.”
Da sauri ta kalleshi sai kuma ta yi k’asa da kanta tace “evening sir.”
Murmushi yayi kafin yace “na takura ki ko?”
Girgiza kanta kawai tayi ta ci gaba da karatunta…

Jifa jifa yake mata hira har aka tashi.
Tun daga ranar kuwa haka kullum zai shigo ajin da sunan supervising zai yi
amman su daya kamata ace sun hana Yara surutu har a tashi bakin Abba baya yin shiru na minti goma.

A haka har aka yi sati…
Yau friday Maryam tanata murna ba zasu had’u ba atleast zuciyarta sa ta huta da bugawa da take yi.
Sai dai kuma tana zuwa sms d’in ta ganshi a bakin gate na main mosque yana tarar y’an makara, ai kuwa ganin tazo a makare ba k’aramin dad’i yayi masa ba, sai da ya bawa kowa punishment sannan ya juyo ya fara tanbayarta “mai yasa ta makara bayan tana matsayin shadow?”
Uzurinta ta fad’a mishi…maimakon ya barta ta tafi ko yayi punishing nata, instead, sai kawai ya hau tambayarta ajin da take. Yaso ace itama d’aliba ce amman sai ya ji tace “ajin y’an Izu 60 take koyarwa, thou he was amazed.”
Ganin zata makara sosai ya sanya ya barta ta shiga taje wajen d’alibanta….
Sai da ya samu ajin da tabarmar su take facing tata tukunna yace su zai koyar......

Idan ana maganar ‘Nacii!!’ tou shi Abba yake yiwa Maryam, tun bata sakewa da shi har ta fara, dan ya iya labarin ban dariya, sannan yana burgeta , thou har yanzu bata gama sanin ma’anar bugawar da zuciyarta keyi idan suna tare ba.
Ahaka aka shafe 3 weeks.

Kamar kullum yau ma suna zaune a night prep yana bata labarin Mahaifin sa….tanata mamaki saboda ita dai ita da Mahaifinta they are like best friends sab’anin shi dan a yadda yake bada labarin Mahaifin nasa kamar wani boss na horror movie, he is not even close to him kwata kwata kuma wai a haka duk cikin y’aya’ansa yafi sonshi, saboda ya ci sunan mahaifinsa ne…
Hayaniyar wasu Yara ne ya juyo da hankalinsu suna waigawa kuwa suka ga ana dambe! Da sauri ta tashi ta isa wajen, shima ganin hakan yasa ya biyota….garin k’ok’arin raba damben d’ayar Yarinyar jin an rik’e hannunta ta d’auka y’an class d’insu ne nan ta buge hannun Maryam d’in da k’arfi!! wanda bai sauk’a a koina ba sai a kan louvers na window kuma daman a fashe yake, nan da nan kuwa ta yanke jini ya fara tsiyaya…
Abba bai san lokacin da ya finciko Yarinyar ya wanka mata marin da har sai da ta fad’i kasa itama gefen bakinta ya fashe, sannan yayi sauri ya kamo hannun Maryam, ganin jini ta koina yana zuba duk ya ma rud’e bai san lokacin daya kama k’asan rigar shaddar jikinsa ba ya yaga ya kamo hannun ya d’aure da kyallen sannan ya fara janta yana cewa “ta zo su tafi clinic, a dubata.” Duk ya rikice, dan har kwalla Maryam ta hango ya taru a idanunsa.
Suna fita suka had’u da prep mistress d’in hakan yasa suka d’unguma har ita aka je akayi mata dressing, a tafin hannuta ta yanke amman Allah ya taimaka ba’ai mata d’inki ba. Har sukaje suka dawo yana jera mata sannu ko motsi tayi sai ya tambayi “mai takeso?” Har bakin unity gate ya rakata tukunna ya juya dan a lokacin an tashi daga prep.

Kusan bai samu yayi ishashhsen bacci ba, juyi kawai ya dinga yi yana Allah Allah gari ya waye.

Allah ya taimaka ma washegari za ta kasance Tuesday ne, so yanada su har double period.

Kamar kullum yau ma Zainab tayi kwalliyarta suna zaune suna jiran shigowarshi, yau kamar da rashin mutunci ta tashi dan sai hararar Maryam take yi, tana fama yada mata magana har da cewa “ idan ma za ta ware gara ta ware tun wuri dan ba abinda za ta tayata da shi.”
Ita dai maryam ta yi shiru tana fama da zugin da hannunta ke yi mata, ga idanunta da suka yi jaa, dan jiya bata samu isheshshen bacci ba.
Shigowarsa ce ta sanya ajin yin shiru kowa ta maida hankalin ta gareshi, shi kam yau k’arara kowa sai da ya lura da kalar kallon da yake yiwa Maryam dan tunda ya shigo daga bak’in k’ofa ya kafeta da idanu har ya isa inda bench d’inshi yake, garin kallon ta ma har da d’an yin tuntub’e.
Ganin tak’i d’agowa ta kalleshi yasa kawai ya amsa gaisuwar y’an aji sannan ya fara lesson..dictation ya fara kamar kullum dan baya musu note a board amma yaga Maryam d’in ta kasa yi, k’ok’ari takeyi ta rubuta da hannun hagu amma ta gagara, ganin tana neman fama ciwonta ga ciwon kan da ya addabeta yasa kawai ta tura littafin gefe ta kifa kanta a benchi.

Abba kam zuwa yanzu ji yake kamar ya kori gaba daya y’an ajin ya lallasheta, ganin gaba d’aya hankalinshi baya ajin kar yaje ya fara musu dictating shirme yasa yayi rounding up, sannan yace “akwai mai question?”
Mutane uku ne suka yi question ciki harda Zainab tanata faman karairaya, shi bai ma san tana yi ba, ya bata amsa daga haka yace “Let’s call it a day”.

Sai a lokacin Maryam ta d’ago ta juya ta tambayi wata classmate d’insu ta ara mata note d’inta, bayan ta mik’o mata ta had’a da nata ta ajjiye a kan bench, duk a kan idonsa.. Har ya yi hanyar fita sai kuma
kawai ya dawo ya d’auki littafin nata da na wadda ta karb’a za ta kwafa d’in, ya juya ya fita da sauri.

BULAMA ✍️

So da Buri
Free Book
11

Yana fita y’an ajin suka fara tofa albarkacin bakin su, har da masu cewa ‘ai tayi sneaking ta shigo da waya dan da gani free call suka kwana suna yi jiya shiyasa daga ita har shi idanuwansu suka nuna alamun rashin barci. Wata Ramlat wadda hostel d’insu d’aya kuma k’awar Zainab ce k’ut da k’ut tace
“Tab! Yanzu girman kai zai k’aru, su o’o ba’a da had’add’en saurayi ma ana kallon mutane a kan hanci, ballantana yanzu anyi..”
D’agowa Zainab tayi ta kalleta a take tayi shiru bata k’ara cewa uffanba. Abinda ya bawa Maryam mamaki shine har suka koma hostel, aka yi lesson na evening, suka sake fitowa night prep kwata kwata Zainab bata ce mata uffan akan maganar ba. Sai dai kawai ta ga tanata yawan kallonta.

Straight jss2 ta nufa tana shiga ta gansa a zaune a gefen sit d’inta kamar ko yaushe.
Yana jin shigowa ya d’ago kai ya kafeta da ido har ta k’araso ta zauna ta gaidashi. A hankali ya amsa sannan yace “Ya hannun??”
Itama a hankali tace “ da sauk’i.” Sannan ta fara k’ok’arin bud’e jakarta domin da d’auko littafi ta samu ta fara karatu.
Littattafan d’azu ya mik’o mata yace “gashi, gobe sai ki bata nata ko?!”
D’agowa ta yi ta kalleshi sannan ta d’auka littafin ta bud’a da niyyar ta d’an k’ok’arta ta kwafa, saboda Yarinyar har ta fara mata maganar littafinta wai ‘tanaso za tai karatu’, amma kawai sai ta ga wani had’add’en rubutu ya baiyyana daga dai dai inda suka tsaya, dubawa tayi tai comparing da na k’awar tata taga Note d’in nata ya zama complete, kallonshi tayi taga shima Itan yake kallo da murmushi a kan fuskarshi kafin yace “Ko ban iya rubutu ba?”.
Bata san lokacin da murmushi ya sub’uce mata ba saboda yadda yayi maganar yana wani langab’ar da kansa, kuma harga Allah tayi mugun jin dad’in taya ta d’in da yayi dan bata san ya za tayi ba, bata da wanda zata rok’a ya tayata dan kusan kaff y’an class da room d’insu daga safe zuwa yanzu kamar haushin ta duk suke ji wanda ita bata san dalilin su na Jin haushin nata ba.

Ganin tana murmushi kawai ya tsaya yana ta kallon ta dan ji yake kamar kar ta daina.

A hankali ganin ya kafe ta da ido tace “Ni ka daina kallo na.”
D’auke idanunsa yayi daga fuskanta yana murmushi….idanunsa suka kai
kan hannun rigarta, dayake da d’an jini jini a jiki tun na jiya, har zai tambayeta dalilin da ya sanya bata wankeba sai ya tuna da hannunta, kuma a yadda take da shiru shiru d’innan ya san ba zata iya saka Junior wanki ba.
Dan haka kawai sai yace mata
“Ki dinga kawo kayan wankin ki zan na kai miki wajen wanki har zuwa lokacin da zaki warke .”
Murmushi kawai tayi tace mishi “to”
Sannna yace duk note d’in da bata yi ba ta kawo, da kyar ta bashi na physics, ragowar kuma tace “za ta k’ok’arta da hannun hagu.”
Har aka tashi suna hira yau kam ta sake dashi, hakan kuwa yayi mishi dad’i sosai.

Washegari kam da bata zo da wankin nata ba taga b’acin ransa matuk’a, dan kicin kicin yayi, kuma ko da aka tashi da kyar ya yarda ta tafi bayan ya sanya ta ta rantse akan washegari za ta kawo.”

Hakan kuwa akayi, washegari ta saka a leda ta sako a skul bag d’inta ta kawo mishi.
Ko da yaje gida akwai washing machine, ga dry cleaning a arean da wajen wanki dai kala kala, amman haka Abba ya zage ya tik’i wankin nan nata da hannunshi, abinda bai tab’a yiba kenan tun tasowarshi, cook d’insa kam da mai yi masa gyaran gida tsayawa suka yi suna kallon ikon Allah, dan babu yadda basu yi da shi ba akan ya kawo su wanke ba amma sam ya k’i.
A wajen ya zauna ya jira ya bushe, ya kwashe ya tafi d’aki ya goge mata, yana yi yana murmushi……

Hakanan ya mayar da abun aikin sa….note da wanki shi zai yi mata ko jinkiri ta d’an yi wajen kawowa ya dinga mita kenan yana fushi, hannun nata ya warke amman kwata kwata ya hanata wanki k’arfi da yaji.

Zuwa yanzu shak’uwa sosai ta shiga tsakaninsu, bak’in jini kuwa a wajen y’an class da hostel d’inta ta kwasheshi ba ‘a magana, dan zuwa yanzu kowa ya sani saboda indai ya shigo aji har ya fita hankalinshi gaba d’aya yana a kanta suna had’a ido kuwa zai sakar mata murmushi ba ruwanshi da inda suke.

Ganin da yayi shak’uwa da sabo ya shiga tsakaninsu ya yanke shawarar fad’a mata shifa sonta yake yi, dukda ya San zuwa yanzu ta fahimci hakan, amman dai gara ya fad’a mata baki da baki.
Dan haka ya yanke shawarar sai ranar da za a tafi hutu tukunnan zai gaya mata daganan ya karb’i land line d’insu (idan suna da shi) ta yadda za su dinga communicating.

Ranar hutun kuwa!
Sunyi ita da shi a kan za su had’u 11, amma sai aka yi rashin sa’a ana bud’e gate motar gidansu ce ta fara shigowa, abunda bai tab’a faruwa ba….suna hostel ma lokacin suna shirya wasu kayyayakin su metron ta zo ta kira su, a gurguje suka k’arasa shiryawa suka yiwa ragowan mates d’insu sallama…

Kamar kullum Madu da ya Usman ne suka zo d’aukar su kasancewar shi Ya Jamilu ba mazauni bane ba, kafin yayi wayo yake nacin zama soja shiyasa tun yana k’arami su Madu suka mik’a sa nda....

Tana isowa bakin Admin ta hango Ya Usman wanda tun fitowarta shi alredy ya riga ya ganta ya kafeta da ido yana tsaye da Madu a gefensa, tana k’arasawa ta fad’a jikin Madu ta rungume sa, sannan ta juyo ta gaida Ya Usman, itama Zainab hugging Madun nasu tayi sannan ta yi huggin Ya Usman shima wanda yake ce
musu “suyi sauri su shiga su kama hanya…..”
Sai da suka shiga motar tukunna suke ji, ashe ‘Madu da Shuwa da Ya Usman ne za su tafi Hajji, jirginsu 7 na dare zai tashi yau shiyasa aka zo d’aukar su da wuri dan a samu a kintsa komai a kan lokaci’…ai kuwa nan suka hau murna.

Usman shi yake driving amman har kusan zubar da su yayi a hanya tsabar yadda gaba d’aya hanakalinsa ya tafi kan Maryam wadda ta fara gajiya da kallo da murmushin da yake da zuba mata ta glass d’in saman motar tun tasowarsu.

A haka suka iso gida, ita Maryam gaba d’aya zuciyarta a cunkushe take saboda rashin yin sallama da Abba, shi kuma Usman mamakin girma da kyan da Maryam d’in ta k’ara yake yi…..dan haka yana shiga gida bayan an d’an yi oyoyo
ya samu Baaba Talatu da maganar
“shifa gaskiya ya kamata a fara maganar auren su shi da Maryam”
Har sai da Baaba Talatu ta fara yi masa tsiya tana cewa “shi, ko irin y’ar kunyar nan baya ji??”, tukunnan ta samu ya kyaleta ya tashi ya fita yana murmushi.

K’arfe 5:30 kuwa, da Baba Bashir da Ya Jamilu da Maryam da Zainab da Bilkisu wadda take kuka sai ta bi Shuwa, suka rankaya suka yi musu ranki ya zuwa Airport. Sai da suka zo rabuwa tukunna itama Maryam taji kwalla na shirin zubo mata, dan haka ta yi saurin barin wajen.

Suna komawa gida, Baaba Talatu ta saka Maryam ta k’arasa had’a kayanta da na Bilkisu, daman Shuwa ta kusa gama had’awa, kafin su tafi.
Suna gamawa kuwa aka rufe gidan suka dawo gidan Baba Bashir.

Sai yanzu Maryam ta gano tabbas son Abba take yi…ta yi mugun dana sanin rashin yi mishi kwatancen gidansu da tayi, babu yadda bai yi da itaba amman ta k’i.
Duk da cewa bai tab’a gaya mata ba ta san shima yana sonta…a haka da kyar a daddafe take gurgura hutun Allah Allah kawai take yi a koma….

A b’angaren Abba kuwa kusan d’an k’aramin hauka ya yi….ya je gandun albasa sau babu adadi, yana tambayar gidansu Maryam Muhammad amman bai samu ba (kasancewar Maryam d’in a file dinta ne kawai take amfani da Madu).

A haka aka kusan gama hutun yanata faman zirga zirga…daga k’arshe kawai rashin lafiya ta rufesa, sai da yayi doguwar jinya tukunna ya samu kanshi, yana ta Allah Allah a koma makaranta, dan duk tsawon rayuwarshi bai tab’a ganin hutun da aka yi yayi masa masifar tsaho kamar wannan ba.

Haka akayi Sallah lafiya, a tsakanin Zainab da Maryam in dai sun yi magana tou a gaban mutane ne, sanin yadda Maryam take son Bilkisu ne ya sanya haka kurum idan Zainab ta lura ba kowa a wajen sai ita da Maryam kawai sai ta hau dukan Bilkisu, haka kurum ba abinda ta yi mata duk dan kawai ta bak’antawa Maryam rai, itakam Maryam sai dai taje ta janye Bilkisu uffan ba zata ce da itaba, domin itakam yanzu sha’anin Zainba ba ya d’ad’ata da k’asa.

Yau tun safe a gidan Baba Bashir aketa shirye shirye, dan sun yi waya da su Shuwa yau za su taso tun asuba amman har wajen d’ayan dare shiru.
Washegari ma shiru, wata washegarin ma haka!
A haka har aka shafe sati d’aya da kwana biyar...
Zuwa wannan lokacin y’an unguwa kowa hankalinshi ya tashi Baba Bashir kam shi da Jamilu shiryawa suka yi suka nufi Abuja.
Baaba Talatu kuwa sau uku ana mata k’arin ruwa, idan ka ga Maryam Zainab da Bilkisu sai baka tausayi, basu da aiki sai kuka, yau kam har da Baaba Talatu aka zauna ana shan kuka…Baaba Laraba wadda ta shigo ita da Sadiya ba da jimawa ba ne suke ta basu baki, duka kuwa itama Sadiyar kukan take yi.

Abun yayi musu yawa gashi Babba Bashir da Ya Jamilu ma da suka je Abuja yau kwanan su hud’u suma basu dawo ba, ko ta landline ba su kira ba.

Suna cikin kuka kawai suka ji ana bud’e gate, da sauri da sauri suka hau rige rigen fitowa tsakar gidan, suna isowa suka ga motar Baba Bashir.
K’arasawa suka yi bakin motar da sauri, ta cikin glass d’in suka hango su Shuwa, ai kuwa da kyar suka iya barin su suka samu suka fito dan duk sun rufe motar anata kukan murna.
Sai da suka nutsu suka huta, sannan Madu ya hau basu labari...
“A cikin room mate d’in Usman na hotel d’in da suka sauka ne aka kama cocaine a jakar wani, shine aka kama Usman dan mai jakar yace shi ba tasa baceba ta Usman d’in ce.
Har an tafi da Usman d’in sai wani bawan Allah d’an Nigeria (ambassador) ya tsaya musu tsayin daka dan yaga alama larabawan suna k’ok’arin yin son kai ne saboda wanda aka kama da jakar balarabe ne shima, amman d’an morocco.
Bawan Allahn nan da ya tsaya musu shine ya bada kud’in beli, mak’udan kud’i ba kad’an ba,
sannan ya d’auko y’an rahoto aka tafi airport aka nemo vid wanda cctv camera ta yi capturing ranar da suka isa k’asar.
Allah ya taimaka ba a ga Usman da jakar ba, iyaka jakankunan su shi yake tare da. Bawan Allah bai bar wajen ba sai da ya tabbata an binciko video na ranar da wannan Yaro d’an Morocco ya zo, ai kuwa sai ga jakar ta fito a hannun wata Yarinya wadda ta zo tararsa, suna gaisawa ya amsa jakar suka ci gaba da tafiya suna hira.”

Baaba Talatu ce cikin tarar numfashin Madu, tace “Shi kuwa wannan bawan Allah wanne irin godiya kuka yi masa? a gaskiya ya kamata mu d’unguma gaba d’ayan mu muje gidansa domin yi mishi godiya”.
Usman ne ya tari numfashinta ta hanyar cewa lWallahi Baaba abinda zai baki takaici, mutumin ya na gama had’a takardun komi da komi ya dank’a a hannun Abba Madu, yace su je su taho da ni. Tun a hanya da ake bani labari nake ta son In zo in ganshi dan banma san wacce kalar godiya zan yi masa ba…amma muna zuwa airport d’in bamu same sa ba sai note kawai ya rubuta yace a bamu wai ‘emergency ya taso mishi, ya tafi, an kwantar da k’aninsa a emergency.’
Su kuma suka k’i su bamu information a kansa ballantana mu ga garin da ya tafi,
saboda kin san babban mutum ne. Amman na san garin a yake ba zai wuce Abuja ba.”

Shuwa ce tace “ai ba lalle Abujan ba, kawai dai yanzu
muyi ta saka shi a addu’o’in mu muna yi mishi fatan alkhairi, inda rabo wata rana za a had’u ai.”

“Haka ne kam!”
Cewar, wadda ta k’i tafiya ita da Sadiya sai da sukaji kwakwaf.

Haka dai kowa yayi ta tofa albarkacin bakinsa…sannan aka ci gaba da murnar dawowar su, daga baya Madu da Shuwa suka tafi gida, aka bar Bilkisu da Maryam a gidan Baaba Bashir saboda gidan yayi k’ura sosai, aka bari akan washegari idan an gyara sa dawo.
A ranar Ya Jamilu ya koma saboda daman saboda case d’in ya dawo kuma akwai abubuwa da dama a kanshi.

Da daddare wajajen 8 Ya Usman ya aiki Bilkisu yace ‘ta kira mishi Maryam’.
Tana zaune tana tunanin Abba Bilkisu ta shigo ta fad’a mata sak’on Yayan nasu ta juya ta fita wajen Baaba Talatu…
Da farko kamar ba zata je ba, sai kuma kawai ta mik’e ta fita.
A can waje babban tsakar gida ta iskeshi zaune a kan tabarma, gefen sa ta nema ta zauna ta gaidashi sama sama
tunda ga nan daga ‘um’ sai ‘um um’.
Ko ba a gayawa Usman ba ya san cewa Maryam ta chanza mishi, dan gaba d’aya hankalinta baya gareshi, shi gani yayi ma kamar haushinsa take ji, dan tunda ta fito bata yi mishi dariya ba.
Da kyar! Ya samu ya kawar da tunanin da zuciyar shi take k’ok’arin dasa wa kwakwalshi, dan shi dai ya san makarantar mata take yi, babu maza ballanta tayi saurayi! Da wannan tunanin ya sallameta ya sanyawa ranshi maybe ko bacci take ji yau d’in.
Amman ga mamakinshi washegari ma haka ta yi mishi
wata washegarin ma haka, sai da aka shafe kwana biyar suna a haka.
Da yaga abun yayi yawa yau sai ya chanja lokaci, around 4 na yamma ya aika aka kirata a zatonsa ko yana hanata bacci ne amman yau sai yaga ma b’acin ran da take ciki ya fi na kullum, dan tun daga nesa ta had’e rai!
Ita kuma Maryam a nata b’angaren takaici ne ya rufeta…shi wannan Ya Usman d’in baya tashi kiranta sai ya daidai ci daidai lokacin da take tsakiyan tunanin Abba..

Kasa jurewa Usman yayi, hakan yasa ya ce mata
“Maryam anya har yanzu kina sona kuwa?”
D’agowa tayi ta kalle shi, kafin ta yi k’asa da kanta ta fara tunanin...
‘Gara fa ta fad’a mishi gaskiya, ita daman chan ba sonshi take yi ba! Kar taje su yi aure tana tunanin wani ta yi ta kwasowa kanta zunubi!’
Wata zuciyar ce tace mata ‘to ke Abban aka ce miki sonki yake yi? ko ya tab’a gaya miki ne?’
Da sauri ta rumtse idanunta dan she can’t begin to think of the fact that wai Abba baya sonta! Sai yanzu ta kuma tabbatar wa kanta ta kamu da sonshi ba kad’an ba, dan da basa had’uwar nan ta yi kewarshi ba k’adan ba!’……

“Maryam kin yi shiru@
Muryar Ya Usman ta katse mata tunani..
Bud’e idanuwanta ta yi waenda har sun chanja kala!
Zuwa yanzu kam tabbas Ya Usman ya fara kaita bango…domin kuwa ita a gaskiya bata son naci babu abunda ta tsana kamar takurawa, bata son yawan magana! kuma ya sani.
Shiyasa a makaranta ake mata kallon mai girman kai..mutane
ma dayawa tsoron mata magana suke yi karta yarfa su,
a cewarsu masu kyau daman ance girman kai ne dasu.
Itakam basu san kawai yawan maganar ce bata so….

“Hmmm, tou inaga dai kin d’auko kuramen aljanu a boarding d’in taku.”
Ya Usman ya sake fad’in haka.

A yanzu kam ta gama yanke shawarar…
‘Ko Abba baya sonta, za ta fad’awa Ya Usman gaskiya dan indai ta aureshi a haka tabbas ba zata iya yi mishi biyayya ba, hakan yasa a hankali ta sago ta kalleshi!
Ya kuwa kafe ta da ido ko kyaftawa bayayi, nauyinshi taji shiyasa ta maida kanta k’asa ta fara magana a hankali….
“Ya Usman ka daina cewa bana sonka, Ina sonka a matsayinka na d’an uwana mana, ai kai Yayana ne.”
Shiruuuu!! Ne ya wanzu a wajen, dan ya kai kusan mintuna biyar bai ce mata uffan ba, ita tama yi tunanin ya bar wajen ne dan haka a hankali ta d’ago tana juyowa kuwa suka had’a ido! gabanta ne yayi mugun fad’uwa sakamokon idanuwansa da taga sun koma tamkar garwashi, bata gama fassara yana yin da fuskarshi take ciki ba taji yace “A matsayin saurayin ki fa? mijin da zaki aura uban Ya’yanki??”
Ya yi mata tambayar yana mai kallon cikin kwayar idanuwanta.
K’arya ba halin Maryam bace ba, zuwa yanzu ta so ta d’an b’oye masa ko dan halin da taga yana shirin shiga a cikin y’an mintunan da basu gaza goma ba, amma sai ta tsinci kanta da girgiza mishi kai.

Wannan karon ta tsorata dan hawaye ta gani ya sauk’o ta idonsa d’aya, bata ankara ba taga d’ayan ma ya sake sauk’owa. Dasauri ya mik’e ya bar wajen yayi cikin gida ba tare da yace mata uffan ba.
A hankali itama ta tashi ta bi bayanshi tana mai jin wani nauyi yana sauk’a daga kan m k’irjinta....

Sai da tayi kwana biyar bata sake saka Ya Usman a idonta ba, a lokacin kuma sauransu kwana d’aya su koma makaranta, mutumin da tun tasowarta
in dai yana gari to sai yazo gidansu sau hud’u a rana.
Tana zaune tana had’a kayanta a jaka Shuwa tace “ta je ta kira mata Zainab, Abba Madu yace a tambayeta idan akwai abinda take buk’ata bayan provision d’insu.”
Tana shiga gate d’in gidan gabanta ya fara fad’uwa, ba kowa sai motar Baba Bashir a parke a chan gefe, a hankali ta k’araso ta tura k’ofar k’aramin tsakar gidan ta shiga, nan d’in ma ba kowa. Har ta wuce zata isa k’ofar d’akin Zainab, ta ganshi yana fitowa daga corridor d’in kitchen da plate a hannunshi, bata san dalili ba kawai taji jikinta ya fara rawa kamar wadda ta yi laifi, sosai take mamakin ramar da yayi…tana tafe tana waigen shi dan a tunanin ta zai yi mata magana, bata yi auni ba kawai taji ta yi tuntub’e ta kusa fad’uwa, da sauri ta saita kanta ta tura k’ofar d’akin Zainab ta shige….
Wani abu da ya bata mamaki shine tabbas ta san Ya Usman ya ganta to amman kuma mai yasa bai ce mata komai ba?! Har fa kusan fad’uwa tayi amman bai kulata ba! Mutumin da ada idan ana hirar tsakar gida ko sauro baya so ya hau jikinta, ya dinga yi mata fifita kenan har a tashi.
Yo ai ko babu soyayya shi Yayanta ne so ya kamata ace ya kulata, lallai indai hakane kuwa to hakan yana nufin Ya Usman yayi zuciya kuma da alama ya hak’ura da ita kenan, a cikin zuciyarta tace “barka na”.

“Malama lafiya? Za ki shigo babu sallama?”
Muryar Zainab ta katse mata tunaninta.
Sak’on Shuwa ta fad’a mata, bata jira amsar da zata bata ba ta juya kawai ta fito gudun rikici dan yanzu kam itama bata ragawa Zainab.

Har ta kai k’ofa, sai kuma ta kalli y’ar barandar da zata kaita d’akin Baaba Talatu, tunani ta yi akan bari ta shiga su d’an gaisa dan haka ta nufi k’ofar d’akin nata! Tana isa bakin k’ofar ta saka hannu kenan zata tura taji muryar Ya Usman yana cewa “Baabaa to ai ni a tunanina sharetan da zan dinga yi kamar zai janyo mini in sake fita a ranta ne, yanzu fa har kusan fad’uwa tayi ban kula ta ba, ku.....”
Cikin fad’a fad’a taji Baabaa Talatu tana cewa “Yanzu Usman Ina uwar ka amman ba zaka bi abinda nake gaya maka ba? Yo ai maganar fita a rai kuma ta faru ta k’are! Sai dai bayan auran ku ka nuna mata so ta yadda zata dawo kamar da, ka ji ai da kunnenka Zainab tace ‘Yaron balarabe ne!’
Shi ne ya rud’eta….kawai abunda nake so da kai shine ka nuna mata kamar ka hak’ura ta yadda za ta sakankance, ni iya in sha Allah da kaina zan je in samu Madu…ba zata k’are makarantar nan ba sai da auranka a kanta bi izinillahi.
Ka kwantar da hankalinka, dan k’ank’aninka da kai ka bi ka d’aga hankalinka! Ai kana ji dai
abinda Likita yace ranar ‘jininka ya yi mugun hawa, Allah kad’ai ya taimaka baka samu stroke ba, lokacin da ka fad’i ka suma wallahi na d’auka mutuwa ka yi, nayi mugun tsorata.

Zancen banza ma kenan!!! Ita daa chan ta san bata sonka amma shine ta bari aka kawo har i yanzu?? Ko da yake na san ba yin kanta bane ba, wannan Yaron ne yake neman juya mata tunani.
Amma ba komai na san abunda zan yi kai dai kawai
ka kwantar da hankalinka kaji ko??”

A hankali yace “tou Baaba.”

Jin kamar zai fito yasa Maryam ta yi saurin barin wajen ta fice tana tafiya tana share hawayenta, da kyar ta kai gida dan har wani duhu duhu take gani ga jirin da yake k’ok’arin zubar da ita, tana shiga ta wuce d’akin su ta kwanta a kan gado ko bi ta kan kayanta da take had’awa bata yi ba.
Banda tashin hankalin da yake a ciki sosai mamakin Baaba Talatu ya turnik’e ta yake juya mata Kai! Tabbas tsakanin ‘da da uwa sai Allah, Baaba Talatu da take nuna mata tsananin so
har fa dukan Zainab take yi saboda ita amma wai yau itace take shirin k’ulla mata auren dole kawai dan taga d’anta ya suma, wata zuciyar ce tace mata ai itama tana da tata uwar, taje ta fad’awa Shuwa tun kan ayi mata auren dole.
Da sauri ta shiga girgiza kai ita kad’ai dan ta san yadda gidansu da nasu Baba Bashir yake,
Irin tsananin shak’uwa da zumuncin da yake tsakani ba na wasa baneba, ita kanta bama ta san ba brothers bane iyayen nasu sai kwanaki da suka je Maiduguri karkarsu take fad’a mata.

Tabbas kuwa ta san Shuwa ba zata d’auki wannan shirmen nata ba.
Sai a lokacin ta fahimci kuskurenta, ta kuma gane ta d’aukowa kanta hanyar da ba zata b’ulle ba dan ta san iyayenta ko giyar wake suka sha ba zasu tab’a hana Usman itaba. Kamar ma Shuwa da Madu sun fi son Usman a kaf cikin y’ay’an Baba Bashir, don gashi Madu ya biya mishi hajji sun tafi tare ko Baba Bashir d’in bai biya ma ba.

A take ta yanke shawarar rabuwa da Abba duk da ta san za ta sha wahala, dan da wuya in wannan ba shine ajalinta ba, amman ya ta iya?
a haka bacci ya kwasheta sai la’asar ta farka.

Toilet ta fad’a ta yi alwala ta fito ta yi sallah, sannan ta mik’e ta yi waje, a hanyar kitchen suka had’u da shuwa tana tsugunne kan kujera a bakin kitchen d’in tana gyaran alaiyyahu.
Gaidata Maryam tayi sannan ta zauna a kan takalmanta tasa hannu ta fara tayata.
Lokaci zuwa lokaci Shuwa tana lura da ita…sai da suka gama har za ta mik’e ta kai kitchen ta ji Shuwa tace
“Zauna Ina so za mu yi magana”

Da sauri ta kalleta sai kuma ta koma ta zauna a kan takalmanta da tayi kujera da su.
Cikin nutsuwa Shuwa tace
“Mai yake damunki?
D’azu naga kin shigo kina kuka!
Ga idon ki duk sun kumbura
Da alamun kukan kika yi ta yi ko?
A zuwa yanzu ba san kin daina yiwa Zainab kuka dan haka ba matsalarta baceba, ko?”

A hankali ta d’aga mata kai
Alamar ‘eh’.

“Fad’a min to? menene?”
Inji Shuwa.

Shirun da Maryam ta yi ne yasa ta sake tambayar ta tare da cewa “Ko kinada wadda ta fini da za ki gayawa?
Kin manta tun lokacin da Zainab ta daina k’awance da ke na yi miki alk’awarin na zama babbar k’awar ki?”

Cikin murmushi Maryam ta share kwallar da ta zubo mata tace “a’a”
A hankali Shuwa ta kamo hannayenta duka biyu sannan tace “fad’a min to, menene?”

Tun daga ranar da ta had’u da Abba ta hau gayawa Shuwa har yau d’innan bata b’oye komai ba…

A hankali Shuwa ta sauk’e ajiyar zuciya, bayan Maryam d’in ta gama, sannan cikin nutsuwa tace “Maryam na san menene so, kuma zan so ki auri wanda kikace kina so a yanzu, amman idan muka da ni dake da babanku za ayi mana kallon butulu.
Abu na biyu kuma ki yarda dani idan nace miki, har yanzu k’iba son Usman, tunda ai da kina son shi, kyale kyale na wanchan Yaron shi ya rufe miki ido har kike nema ki guji Usman wanda na san in sha Allah bayan auranku komai zai daidai ta.
Sannan abu na uku, wanchan
Yaron daga yana yin labarinki na fahimcei d’an masu kud’i ne, na gaske! Maryam ke Yarinya ce har yanzu, Yaran masu kud’in nan b’atawa mutum lokaci kawai suka iya.
Tabbas idan kika bincika already akwai Yarinyar da zasu aura wadda aka riga aka had’a su dan basa tab’a yarda su auri y’ay’an talakawa.
Shawara ta anan shine
ki auri Usman, ki zauna a cikin y’an uwan ki, ki manta da batun Abba kar ki bi zuciya ki zama butulu, daa chan baki ji rashin son auranshi ba sai yanzu? Usman zai kula da ke, tun kina k’ank’anuwar ki yake d’awainiya da ke dan zan iya ce miki laulayi da nak’udarki ne kawai Usman bai yi ba amma har Goya ki yake yi, kashi da fitsari babu kalar wanda baki yi masa ba.
Kiyi ta Addu’a zaki ji zuciyarki tana yin sanyi, kinji ko?
Allah ya yi miki albarka.”

A hankali tace “Ameen.”
Ta yadda kuma ta gamsu dukkanin abunda Shuwa ta fad’a gaskiya ne, sai dai kuma tanata so tace mata itafa tun farko daman murnar da taga sunayi ita da Baabaa Talatu ne ya sanya ta yarda da soyayyar ya Usman, amma sanin ko ta fad’a hakan ba lalle a fahimceta ba tunda da chan bata fadaba sai yanzu da take son rabuwa da shi saboda Abba, hakan ya san kawai ta yi shiru ta mik’e ta koma d’aki.
Tana shiga ta nemi bakin gado ta zauna a hankali ta sauk’e ajiyar zuciya, sannan tace “Abban ma da nake ta abu a kanshi maybe ma shi bai san m inayi ba.”

Ahaka dai sukuku ta k’arashe wannan ranar washegari da sassafe Ya Usman da Ya Jamilu wanda ya dawo jiya da daddare suka maida su makaranta, har suka juyo Kano Usman ko kallon inda take bai yi ba, Ya Jamilu ne dai dukda ya kasance Soja baya yawan dariya amman hakan yayi ta janta da hira ganin kamar tanata tunani.

Ana gama checking d’in kayanta ta fara k’ok’arin kaiwa hostel.
Isowarta bakin Unity gate kenan kamar ance ta d’aga kanta gabanta ya yi mugun fad’uwa sakamokon had’a ido da suka yi da Abba, ya kafeta da ido da alamun ya dad’e da ganin tahowarta, yana zaune gefen house mistress d’insu wadda ta mayar da second checking d’abiarta dan duk dawowa hutu bayan an gama duba maka kaya a main gate to itama sai ta sake nata a bakin Unity gate.
Da alamun checking d’in yake tayata, amman sai magana take yi mishi hankalinshi baya wajenta har sai da ta d’an zungureshi tukunna ya mik’a mata abun hannunshi ya taso ya taho inda Maryam d’in take, tana k’ok’arin k’arasowa wajen tana k’ok’arin kaucewa ya sha gabanta…had’a ido sukayi tana mamakin ramar da taga yayi, taji yace “Maryam I could hug u right now! Kin san yadda na dinga nemanki kuwa? You said za mu had’u 11 tun 10 nake Admin Ina jiran ki har kowa ya tafe, and now kin ganni k’ok’ari ma kike yi ki wuce kawai ki tafi, bakiyi missing d’ina ba??”
Ya yi mata tambayar yana kallon ta da yanayin sa kamar na mai shirin yin kuka.

Ahankali tace “sir, i want to pass, u are blocking my way.”

Shek’ek’e!! haka ya tsaya yana kallonta, anya kuwa Maryam ce? to ko dai wani abun yayi mata ana I gobe hutun, maybe ma shiyasa ta tafi ba ta jirashi ba…
Yana cikin wannan tunanin yaga tana k’ok’arin zagaye shi ta wuce.
Shan gabanta ya kuma yi, sannan yace “Wai me yake damunki ne? Kin san halin da na shiga kuwa? Ina ta Allah Allah a dawo makaranta don in sake ganinki, wallahi kinji na rantse har a asibiti na kwanta, all because of u and yanzu shine za ki zo mini da wannan sabon attitude d’in?
To wallahi baki isa ba! Idan ma wani misunderstanding ne u better talk mu yi clearing d’inshi right away cos u can’t turn your back on me like this, ba zan iya jurewa ba, not now, not ever!!!”
Ya fad’a da d’an k’arfi da alamun ranshi ya soma b’aci.

A hankali Maryam cikin sanyin ta, tace “Y? Meye had’ina da kai?”

Ga mamakinta sai taga ya fara murmushi, kafin yace “do I really have to say it?”
Yayi mata tambayar yana kafeta da idanuwanshi data kasa jurewa kalla ta yi k’asa da kanta.

Y’an tsirarrun students ne a wajen, most of them ma y’an ajin su ne, kasancewar sai yamma sosai ake cikowar dawowa, sai house mistress d’in da take checking…
Tafa hannunwanshi Abba ya fara yi yana cewa “attention everyone.”
Cikin k’ank’anin lokaci ya had’a kan y’an mutanen wajen da basu da wani yawa, sai da ya tabbatar attention ya dawo kansu sannan ya durk’usa a gaban Maryam, ya sago yana kallonta ya fara magana.
“Maryam i Found the reason for my smile, the day i found you! In you, my life becomes whole, with you my days become bright.
In your hands i would love to lay, for the rest of my life, you’ve got everything i’ve been searching for in life, i would love for you to grow old with me! The best is yet to be and it begins from the moment you say yes!
I love you, so much Maryam, will you please be my soulmate?, will u marry me?, will u stay with me till death do us apart??”.

Ai kuwa nan students suka hau tafi, suna “Say yes, Maryam say yes!!”
Ihun su ne yasa house mistress d’in ta k’araso wajen.

“Stand up!”
tace mishi.

A hankali ya mik’e, tukunna tace “you know all this is not allowed right?”

Cikin sanyi jiki yace “yes”

Murmushi yaga tayi sannan tace “but I’m willing to sopport you a hundred percent, because I’ve never seen a perfect match like yours!
But don’t do too much of zance at school because it’s not allowed, don’t cause problems for her, you can visit her as much as u want whenever she gets back to her fathers house.”

“Ok.”
Ya cewa house mistress d’in yana d’an murmushi sannan yace “tnx”.

Kamo hannun Maryam tayi tace “ta wuce hostel tayi freshening up, kafin wannan oyinbo boyfriend d’in nata ya hanata.”
A hankali ta wuce…Abba k’ok’ari yake su had’a ido amman tak’i ta bashi damar hakan.

Sai da suka yi kwana biyu tukunna aka fara night prep, ta so ta yi dodging kawai tayi class d’insu amman sai ta kasa.

A hankali ta k’arasa js2, tun ta window ta hango shi zaune wajen zamanshi, yana hango ta ya kafeta da ido har ta k’araso.

Cikin nutsuwarta ta gaidashi ya amsa mata yana kallonta.
Bayan sun d’an gaggaisa sun d’an yi hira tana ta jin nauyin sa ita dai, yace mata ”ya baki fito da wankin ki ba?”.

Da mamaki ta kalleshi tace “ai yanzu na warke!”
Kicin kicin yayi da kyar da nacin da yayi ta zuba mata washegari ta kawo mishi wanki.
.……..
Duk wani gatan da ya dace Abba yana tabbatarwa ta samu, sai dai kamar yadda house mistresses d’insu ta fad’a mishi, baya takurata sosai gudun kar ya ja mata matsala, kuma itama house mistress d’in ta rufa musu asiri kar ya bata kunya, hatta prep d’inma yanzu sai ranar karb’ar wanki da dawowa da shi ne kawai yake zuwa, yana bada tazarar kwana bibbiyu dukda yana takura da hakan amma ya san hakan shine dai dai.
Soyayyarsu sukeyi gwanin burgewa, Maryam ta ma manta ta wani Ya Usman sannan tunda yanzu Abba yace yana son ta,za ta fad’ama Shuwa itafa daman chan ba son Ya Usman take yi ba, don haka a d’aga mata k’afa. Addu’ar ta d’aya Allah yasa su fahimceta su kuma yadda da Abba.
Kamar kullum yau ma suna zaune a night prep suna y’ar hirar su, yake bata labarin yayanshi da irin son da yake yi masa, har yake ce mata yace masa first born d’inshi in Namiji ne takwara zai yi masa.
Murmushi tayi tace
“D’an gatan Yaya.” Tana dubanshi ta k’asa k’asa, dan a yanzu kam kunyarshi takeji kwana biyun nan, kuma take ji bata bari ta kalleshi dan suna had’a ido zai ce mata I luv u.

Garin kallon ne ta kalli fingers d’inshi, sai taga sun d’an kumbura ba kamar ko yaushe ba, hakan yasa tace masa
“Mai ya samu hannunka?”

One thing about him
bai iya k’arya ba, dan haka
ya hau bata labarin tun ranar da ta fara bashi wanki, yadda yake wankewa da gogewa ya ce “maybe yawan tab’a ruwa ne ya sa hannun nasa ya yi haka” shi kam ya ma manta bai kamata ya gaya mata hakan ba.

Maryam haushin kanta ta fara ji, dan a yanzu kam yadda Abba ya damu da ita itama ta san sarai ta damu da shi.
Dan haka tayi fushi yayi yayi ta k’i kulashi, har aka zo tashi.
Ganin tana shirin mik’ewa yasa shi ya rik’e mata jaka, ya fara bata hak’uri, ganin ya k’i sakin jakar kuma Yara har sun fara kallonsu yasa ta koma ta zauna.

Sai da aka gama fita tace “zan hak’ura amman ba zan k’ara kawo maka wanki ba, ai hannun ya warke.”
Shi kuma yace “ba zai barta ta tafi ba har sai ta rantse zata kawo wankin, dan ba zai barta ta dinga shan wahala ba.”

Wasa wasa basu ankaraba, kawai alarm d’inshi na 11 wanda yasa dan lokacin exercise d’inshi kenan b4 going to bed kawai sukaji yana k’ara.
Maryam da taga time a firgice ta mik’e, ko sauraronsa ma bata yi ba ta suri jakarta tayi hostel tana adduar Allah yasa ba a rufe ba.

Shima Abba ganin yadda duk ta rud’e kuma yaga dare yayi yasa bai tsaida ta ba, ya tattare kayan shi ya tafi.

Adduar ta kuwa ta karb’u, dan ba a rufe unity gate d’inba sannan hostel d’insu ma ba a rufeba. Room d’inta nema aka rufe dan sai da tayi knocking tukunna Zainab ta bud’e mata.

Tana ganinta ta juya taje suka ci gaba da hira da ragowan mates d’insu ba tare da ta kalleta ba.

Fitsarin daya isheta tun a chan ga kuma tsoron daya sake ingizo shi yasa itama bata kalli Zainab d’inba kawai kan gadonta ta nufa ta ajjiye jakarta ta zari torch ta fice ta nufi toilet.

Bayan ta gama fitsarin ne taga ashema period d’inta ya d’auke, daman yau take expecting hakan ko gobe da safe, kasancewar ana tsula sanyi ga duwatsun garin na kusa da makarantar, ta san ba zata iya yin wanka da Asubah ba ga kuma isha hakan yasa kawai ta koma d’akin nasu
taje k’asan gadonta ta jawo bokiti mai ruwa. Towels d’inta guda biyu data sak’ale a jikin bunk ta kai hannu ta zari d’aya, ta wuce toilet ta je ta yi wankaan ta, ta dawo.

Hular kanta da ta yi sharkaf da ruwa ta cire, gashin ya zubo.
Ita dai ta san ta bar towel d’aya a jikin bunk amman da tazo da nufin d’auka domin tsane gashin kanta, sai ta neme shi ta rasa…dube dube ta fara yi har su k’asan gado, tana d’agowa suka kusan yin karo da Zainab tana mik’o mata towel d’in, sannan tace
“Sorry na wanke face d’ina ne kuma duk towels d’ina sun yi datti shine na ara na goge fuskana, ungo.”
Murmushi Maryam d’in tayi tasa hannu ta karb’a. Zainab d’in ce tace mata
“Me za kiyi ba ga wani a jikin ki ba?”

“Gashina zan tsane”
Ta bata amsar tana k’ok’arin fara goge kanta. Bata kawo komai a ranta ba, ta hau goge gashin da towel d’in, har ruwan ya d’an fallatsar wa Zainab.

Juyawa Zainab d’in tayi ta nufi Majalisar su.
Ita kuma Maryam sai da ta gama gogewa ta nad’e shi a kanta ta shiga corner d’inta ta shafa mai ta saka kaya, tayi addua abinta ta kwanta .
Har lokacin tana jin k’us k’us d’in maganar su Zainab dan ba suyi bacciba amman a hankali
suke maganar sunata k’us k’us, daga bayama tashi Zainab d’in tayi ta fita ita da wata k’awarta,ita dai Maryam bata san lokacin da suka dawo ba bacci ya kwasheta.

Kiran sallar farkon da aka maka a mosque d’in dake tsakiyar hostels d’in ne ya farkar da ita daga baccinta mai cike da mafarkin Abba…..
‘yana ta zuba mata murmushi ya rik’e hannunta yana janta ita kuma ta kasa zuwa garesa, kamar akwai wani abu da yake janta baya’,
haka ta ji a mafarkin.

BULAMA ✍️

So da Buri
Free Book
12

Da ‘bell’ ta yi amfani wajen tashi y’an hostel d’in nata tukunna ta wuce ta yi alwala ta fice mosque.

Sai da gari ya d’an yi haske
tukunna y’an mosque d’in suka fara dawowa. A hanya ne wata roommate d’insu da suka fito daga mosque d’in tare take ce mata “gaskiya Maryam kin b’ata wayonki, ban yi expecting haka daga gareki ba, gashi yanzu kin janyowa kanki! Allah kad’ai ya san hukuncin da za’a yanke miki.”
Da mamaki Maryam take kallonta kafin tace “Ban gane ba Hafsa, mai nayi?!”.
Tsaki Hafsat d’in tayi kafin tace “Ai ga irinta nan, daman Zainab ta fad’a.. k’aryata mutane zaki yi!
Ni dai shawara ta idan an je wajen principal ki rungumi laifinki, dan wallahi kin san halin principal idan kika yi mata k’arya laifin ki k’aruwa zai yi.”

Zuwa yanzu kam gaban Maryam ya fara dukan uku uku gashi sun iso bakin gate d’in shiga hostel, hakan yasa tayi saurin rik’o hannun Hafsat tace “Hafsa dan Allah d’an tsaya, kin saka ni a duhu, kiyi mini bayani, sai magana kike ta yi a baibai.”
Har Hafsat ta bud’e bakinta zata yi magana, wasu y’an mata biyu suka fito da bokiti a hannunsu, suma duk y’an d’akinsu ne, kallonsu sukayi kafin d’ayar tace
“Ah lalle Hafsa, me ake koya miki? lalube ko shafa mai??.”
Hararar su Hafsat tayi sannan ta cire hannunta a na Maryam ta yi cikin hostel ba tare data waiwayi kowa ba.

Su kuwa dariya suka saka sannan suka nufi unity tap d’in dake tsakiyar hostels d’in domin d’ibar ruwa.

Ita dai Maryam har ta shirya…taje dining aka nufi assembly ground, duk tayi sukuku, k’ok’ari take yi ta fassara kalmar ‘lalube ko shafa mai’ amman ta kasa, saboda amsar da kalmar take bata ba abune mai ma’ana a tsarin rayuwar da take yi a makarantar ba.

Ana shirin roundin up assembly d’in Principal ta rambad’a kiran sunan ta a mic tace kar taje class ta sameta a office d’inta.

To fah!!
Dan yanzu kam Maryam ta gama rud’ewa.
Da kyar a daddafe ta k’arasa office din principal d’in, gaba d’aya jikinta in banda karkarwa ba abunda yake yi, gashi gabanta sai fad’uwa yake.

Knocking tayi,
ta ciki aka bata izinin shiga.
Tana shiga mamaki ya kamata sakamokon ganin Abba, metron da house mistress d’insu duk a zazzaune a cikin office d’in.
Da kyar ta iya k’arasawa ta zauna ta gaishesu, principal d’in ce kawai ta iya amsa ta Abba kuwa kanshi a k’asa yake tunda ta shigo, bai d’ago ba.

Gyaran murya principal d’in tayi sannan ta mik’o mata wata takarda, tace mata “ta karb’a tayi signing.”
A hankali ta mik’e taje ta amsa, tun kafin ta dawo wajen zaman ta ta fara dubawa….ai kuwa bata iya k’arasawa wajen zaman nata ba sakamokon rikicewar da ta sake yi tashi d’aya ta shiga matsanancin tashin hankali……
Karantawa take yi tana sake duba takardar ‘expell’ d’in da aka bata ga sunanta b’aro b’aro a jiki, hankalinta bai gama tashi ba sai da taga dalilin korar!
“Innalillahi wa inna ilaihirraji’un” shine abinda ta fara maimaitawa idanunta na zubar da kwalla, a hankali ta k’araso ta durk’usa a gaban teburin principal d’in ta fara magana muryar ta na rawa
“Ma, wallahi this is not the truth, pls don’t expel me, i promise I won’t talk to Abba ever again!. I don’t want my parents to find out about this. I have been framed here I swear….”

Cikin rashin walwala principal d’in tace mata
“Don’t worry your parents already know about this since yesterday, they are on their way now as we speak.”

Rushewa Maryam tayi da kuka, ta fara magiya, tana cewa “sharri aka yi musu” …..tana alk’awarin rabuwa da Abba har abada, amman principal d’in bata saurareta ba kawai dai tace mata “Ita fa ta riga ta gama magana, so ta jira zuwan iyayenta kawai.”

Metron kuwa munafuka in banda zuga principal babu abunda take yi, hadda cewa “ai ranar tun a clinic ya fara rungumeta. Waye waye”
Sai faman zuba dai take yi,
ba ita tayi shiru ba sai da principal ta aiketa ta je ta kira Zainab da wasu class mates d’insu.

Su Zainab sun shigo bai fi da minti goma ba Madu da Shuwa da Ya Usman suka shigo.
Da gudu Maryam taje ta fad’a jikin Shuwa tana kuka tana cewa “wallahi k’arya ake mata.” Kama kafad’unta Shuwa tayi sannan ta ajjiyeta a kujerar gefe, ba tare da tace da ita komaiba! Ta k’arasa suka je suka zazzauna a kan kujerun suka gaisa da mutanen wajen.

Bayan an gama gaisawa ne principal d’in tayi gyaran murya ta nuna Zainab tace “
Yarinyar nan ta zo ta sameni last week akan maganar sister d’inta da wannan Yaron” ta yi maganar tana nuna Abba kafin ta d’aura da cewa “I was surprised because irin haka bai tab’a faruwa ba, dan it’s a very strict rule ‘ba a soyayya tsakanin malami da d’alibi’!
I don’t know why they choose to break the rule. I called their house mistress first, Ina so ince mata ta sakama Yarinyar ido but to my surprise sai take ce mini ‘ai ta riga ta sani already, amman kawai dai gaisawa suke yi, kuma basa zance. Dai ya fad’a mata yana sonta ne amma basa soyayya a makaranta because she warn them and sun yi biyayya da abunda ta fad’a’ She gave me good reasons, wanda reasons d’in da ta bani ne ya sa na yi deciding to just let it go,
dukda na san it’s not allowed but kamr yadda tace if basa soyayya a makaranta I see no reason da zanyi interfering.

After two days ina zagaye da daddare, wanda ba kowa ne ma ya san ina yin hakan ba, saboda Ina yi ne to make sure all is fine. A time d’in na bi ta jss2 block and I saw them together, I know Maryam very well tunda shadow prefect d’inmu ce and Abbas shima ba b’oyayye bane shiyasa nayi saurin ganesu….ban ji d’ad’in yadda na gansu ba! He was holding a book tana so ta karb’a ya hanata, and they are sitting too close to each other! Na so inyi musu magana but a yadda raina ya b’aci a time d’in sam bana zan ma iya kallon Yaran.
So na yanke shawarar fara yiwa house mistress d’insu magana first, i was very disappointed a ita da su.

So, na sameta nayi mata magana and ta gaya mini cewa ‘wallahi bata san suna zama guri d’aya ba, that was when I called their metron, and she told me ‘ai tun time d’in da Abba ya fara zama night prep tare suke zama kullum, and sometimes they even hug, kuma basa tafiya sai kowa ya watse, in sun gama abinda zasu yi’.”

Kukan Maryam ne ya k’aru kafin tace “wallahi k’arya ne, Hajiya Shuwa dan Allah ki tsaya kiji nawa kar ki yarda da maganar su…..”

Cikin tsananin b’acin rai Ya Usman yace “Wallahi Maryam idan bakiyi mana shiru ba sai na b’abb’allaki a nan!!”
Ganin yadda ya taso yayo kanta kuma taga alamar ranshi a mugun b’ace yake dan bata tab’a ganinshi a irin wannan yanayi ba, ya sanya ta yi shiru, ta hau k’ok’arin tsaida kwallarta ta…

Numfashi principal d’in taja sannan ta ci gaba “Na kira 2 to 3 children a js2 and sunce gaskiya su basu tab’a ganin komai ba, kawai dai basa tafiya tare da su kamar yadda metron tace.
So hankali na ya d’an kwanta but dukda haka sai na kira Zainab saboda Ina son sake jin bayaninta dan Insan ta Ina zan fara “A nan ne ma take sake tabbatar mini da cewa ‘ai Maryam d’in already tana da mijin da zata aura a gida!.’

Na kira Yayan Abba dan in fad’a mishi halin da ake ciki ince yayi wa Abban magana ko In d’auki mataki, amma wani abun mamaki kamar had’in baki sai shima yake gaya mini cewa ai shima Abba tun bai kai hakaba already Mahaifinsu ya zab’a mishi wadda zai aura cousin sister d’insu, kuma kowa ya san da maganar….
Shi Ya’yan nasa ma he was very surprise da yaji wai Abba yana soyayya da wata…..

So definitely kunga ba soyayyar gaskiya Maryam da Abba suke yiwa juna ba kenan, ko?.

A time d’in bana son yanke hukunci cikin sauri, shiyasa
na saka Zainab da those two” ta yi su maganar tana nuna k’awayen Zainab da suka shigo tare, tukunna tace “nace su saka musu ido sosai.!
Yesterday around 11 metron taje gidana, saboda nace musu ko k’arfe nawa ne idan abu ya faru su sameni a gidana na quaters in dai inanan….
Banji dad’in abinda metron ta gaya mini ba at all, although shine abunda nake suspecting
but Maryam is one of our best students sannan d’a na kowa ne.
Kasa bacci nayi da jin maganan metron that’s why
nima kawai immediately na nemi land line d’inku…..”

Shiruuuu!! kowa yayi kafin principal d’in tace “Zainab, ku maimata musu abinda kuka fad’a mana.”

Zainab ce tafara magana
“Daman kullum idan ya shigo aji sai yayi ta kulata, tun yana b’oyewa har ya daina, tou akwai k’anwar k’awar mu a jss 2 itace ta fad’a mana abunda sukeyi, itace ta zo ta samemu jiyama tun kafin a tashi tace wai gashi chan ya d’auketa sun fita ba a san ina suka je ba!.
Mun yi ta jiranta a hostel bata dawo ba, daga k’arshe dai sai after 11 tukunna suka dawo
kuma data shigo har wanka tayi dan sai da na tab’a gashinta na tabbatar!. Shiyasa naje na samu metron ita kuma tace yanzu zata je wajen ki ba sai gobe b..”

Sai a lokacin Abba ya d’ago kai ya kalli Zainab da idanuwanshi da suka chanja kala..wanda hakan ne ya sa ta kasa k’arasa maganar ta.

House mistress d’insu ce tace “amman ku, kun tabbatar fita sukayi kuwa? Because d’azu da sassafe naje wajen gateman yace min jiya Abba shi kad’ai ya fita kuma sai wajajen 11.”

Da sauri Zainab tace “Ai gidansu na coppers
na staff quaters suka je……”

Ita kam Maryam zuwa yanzu muryarta har ta dishe tsabar kuka!! Madu ne ya kirata yace “ta zo!” Tana zuwa yace “Da gaske ne???”
Da sauri ta fara girgiza kai tana kuka, abin tausayi….
Metron sarkin zuga tace “ki ji tsoron Allah har wanka fa sukace kin yi!”.

Cikin k’ok’arin son fahimtar da su Maryam tace “Eh nayi wankan amman wallahi ba wank.....”

Bataga k’arasowar Ya Usman ba sai sauk’ar marin da taji wanda yasa ta fad’uwa a wajen gefen bakinta ya fara zubda jini, tana k’ok’arin tashi taga ya sake yunk’urawa da nufin rufeta da duka…..
Ta gama sadak’arwa tana jira taji sauk’ar dukan!
Jin shiru yasa ta d’ago, Abba ta gani ya kare mata…a hankali ya sunkuyo kanta ya kamo hannunta ya mik’ar da ita cikin tafin hannun nata ta ji yana cusa mata takarda
karb’a tayi tana kallonshi
shima Itan yake kallo
da idanuwanshi da suka yi jazir!! A hankali yace “I luv u Maryam.”
Bai tsaya jin fad’an da su metron suke mishi ba
na ‘ya kama hannunta a gaban iyayenta!’ Kawai ya juya ya fita.

Madu ne ya cewa Shuwa su tashi su tafi, hakan yasa ta mik’e ta yiwa principal sallama
wadda take ta bawa Shuwa hak’uri tana cewa “She is just looking out for Maryam, ba dan hakanba da ta barta a makarantar, gara ta tafi gidan iyayenta su saka mata ido.”

Jinjina kai Shuwa tayi sannan tace “ba damuwa.” Ta juya ta fice.
Ko kayanta su Shuwa basu bari ta koma hostel ta d’auko ba, cewa suka yi ‘Zainab ta taho mata da shi’. Hakanan tana kuka tana komai suka shiga mota aka ja aka yi gida da ita.

Zainab kuwa yau farin ciki a wajenta ba a cewa komai, murna takeyi ai tunda Maryam ta tafi to fa duk wata hanya da zata bi sai ta bi ta cusa soyayyar ta a zuciyar Abba, kasancewar yau suna da period d’inshi daman yasa tun kafin su k’arasa class ta tsaya ta wanke fuskarta a tap, akayi y’an shafe shafe, k’awayen ta suka duba suka tabbatar mata tayi kyau tukunna aka nufi class ana tunanin hanyoyin da za a bi a karkato da zuciyar Abba gareta!
Sai dai kuma har period d’inshi ya shiga ya fita bai shigo ajin ba, washegari ma haka….ahaka suka shafe kusan sati babu Abba babu alamar shi.
Zainab har office d’inshi taje ta tarar a rufe….haka ta dawo jiki duk ba kwari zuciyarta ta a cunkushe, haka take rayuwa a makarantar gaba d’aya komai baya mata dad’i, sauk’inta d’aya ma ba Maryam.

A b’angaren Maryam kuwa tun da suka shiga mota take kuka har suka isa gida, a tunanin ta za a yi mata fad’a ko duka amman ba wanda yace mata komai, amma fa ko gaisheda Shuwa ko Madu tayi a cikinsu babu mai amsa mata, ko suna zaune idan ta zo ta zauna to zasu tashine su bar mata wajen, hatta Bilkisu da suka shak’u sosai a duk lokacin da Shuwa ta gansu tare sai tazo ta d’auketa ta kuma hau yi mata fad’a, tun Bilkisu tana kulata a b’oye har ta daina saboda a d’aki Shuwa take sakata ta kunna mata kallo, ko girki an daina girkawa da Maryam a gidan! A wajen mutum d’aya kawai take samun sauk’i itace Baabaa Talatu dan a gidan ta ma take cin abinci sai kuma Ya Usman wanda yake wani sabon shige mata kwana biyun nan ta kasa gane mishi kwata kwata, itafa ko ba Abba ba zata auri Ya Usman ba! She is not suppose to be feeling this towards Ya Usman amman she can’t help it, kawai ita all she knows bata sonshi kwata kwata bata sonshi ba zata iya zaman aure da shi ba.

Yau satinta d’aya da kwana d’aya da dawowa daga boarding, gaba d’aya duniyar ta yi mata zafi, zuwa yanzu rashin kulata da iyayenta sukeyi ya fara bata tsoro dan har ta rame ba kad’an ba.
In ba wajen Baaba Talatu taje ba tou kullum tana d’aki ita d’aya.
Yau ma ganin shiru zai haddasa mata wata damuwar bayan wadda take ciki ya sanya ta yanke shawarar fita dan shan iska ko ta samu ta d’an ji sauk’i.

Hijabinta ta d’auka ta nufi wajen Baaba Talatu, tana shiga a babban tsakar gidan ta had’u da Ya Usman tare da wani Abokin sa suna hira yana ta dariya, ta dad’e bata ga dariyar sa irin haka ba, tun kafin ta k’araso taji yana cewa
“To kai ba ka tsaya wasa ba?! Kawai ka jira zan baka y’ata ta farko”
Magana Abokin yake mishi amman bata ji sosai sai dai taji kamar yace “Ranar juma’ar nan ne wai da gaske?”.

Ita dai bata gane me suke nufi ba ta zo ta gaishesu.

Sai a lokacin ma Ya Usman ya lura da ita, Abokin ne ya amsa yana cewa “uwar gida ya gida?” Da kyar tace “Lafiya” Dan in Abokanan Ya Usman suka ce mata uwar gida duk sai taji wani iri, shiyasa bata tsaya biyewa tsokanarta d’in daya shiga yi ba tayi wucewarta cikin gida.

Ta isa k’ofar Baaba Talatu kenan har zata tura taji suna magana, sai da ta kara kunnenta tukunna ta gano ita da Ya Jamilu ne…mamaki da murna takeyi a ranata tace “yaushe ya dawo?”.
Har ta fara k’ok’arin shiga sai kuma taji maganar da yake yi daga ji ran shi a b’ace yake dan yana maganane cikin d’aga murya…
“Habaa Baaba! Yanzu abunda za a yi an kyauta kenan??? Shi fa Usman d’in da kansa yake ce mini tace ‘bata sonshi’!
Garin son sake k’ulla zumunci sai kunje kun yi abinda zai tarwatsa komai!!
Ku kanku fa kun san halin Maryam tun tana Yarinya tanada mugun taurin kai!! Ya kamata ku fahimci tunda har tace muku a yanzu wanchan Yaron take so to shi d’in take so a yanzun!
Amma baku tsaya kun yi nazari ba, tashi d’aya kun rabota da shi sannan kuma kawai rana tsaka kun zo kun ce zaku d’aura mata aure wannan juma’ar ita da Usman?? Idan wanchan Yaron ne bakwa so kwata kwata ai at least dai kwa bari idan ma auren ne ita da Usman d’in ya kamata a bari su sake fahimtar juna, dan wallahi idan aka yi auren nan bata sonshi a haka a wannan yanayin da take ciki to ba zata tab’a son shi ba.”

Baba Talatun ce itama ta rufeshi da fad’a tana cewa
“To ubana!!! wanda ya san salon so! Yaushe aka haife ka ne Jamilu??
Bari kaji….rud’u ne yake damun Maryam amman ba wani Abba da takeso ni na san Usman take so, kuma bari kaji, ko da ace bata auri Usman ranar Juma’ar nan ba to tabbas Abban ta zai aurar da ita a sadaka ranar dan yayi wannan alk’awarin, furucin nasa ne ma ya sa Babanku yace ‘ga Usman’ to kaga ai taimakon tama zai yi! Wai dan ma ban ce d’a na ba zai auri ragowar wani ba!?”

“Haba! haba!! Baaba, bai kamata ku yarda da zancen su Zainab akan Yarinyar nan ba fa, idan y’an layi suna yamid’id’i kema sai ki biye su? Maryam fa kamar y’a take a wajen ki, kuma kin san basa shiri da Zainab dama.”

Da sauri Baaba ta karb’e tana cewa “Ai Maryam bata d’aukeni uwa ba tunda gashi k’iri k’iri tana so ta guji Usman. Kuma kana nufin dan basa shiri da Zainab d’in za ta k’ulla mata sharrine??”

Ji tayi Ya Jamilu yaci gaba da magana “Ni dai in za ‘a j....”

Maryam kasa tsayawa ta cigaba da jin maganar tasu tayi. Zuwa yanzu ta fahimci komai, tuni fuskarta ta jik’e sharkaf da hawaye da uban gumi…nan da nan ta fara ganin dishi dishi! Da gudu ta fita a gidan ko bi ta kan Ya Usman da yake kiran ta bataiba!
Taya mahaifinta wanda yake masifar sonta zai yi sadaka da ita??? lalle kuwa zata kashe kanta, wato sun yarda da maganar mutane akan ta kenan?….
Da wannan tunanin ta isa gida tana shiga falon sukai kicib’us da Madu wanda yake shirin fita ..
Goge hawayenta tayi sannan ta durk’usa a gaban shi ta hau magiya “Abba dan Allah ka yi hak’uri, na rantse da Allah sharri aka yi mini, wallahi Abba bana son Ya Usman, kar ka aura mini shi dan Allah…”

Zagayeta Madu yayi ya wuce ya fita ba tare da yace mata komai ba. Mik’ewa ta yi ta nufi Shuwa wadda ta fito daga kitchen yanzu itama ta fara yi magiya tana “Hajiya dan Allah ki kulani yau, ki yarda dani wallahi sharri aka yi mini, baba son Ya Usman kar ku yi mini auren dole, wallahi k’arya su Zainab aka yi mini! Yanzu kin yarda da abinda suka ce??”

Da sauri Shuwa tace
“Na yarda!!! Duk wani abu da aka fad’a na yarda, ko da ace zuciya ta tana son k’aryatawa, to zan tirsasa mata in tilastawa kaina in gasgata hakan ne.
Tunda har zaki iya k’etare umarnina! Maryam a nan”
Ta yi maganar tana nuna k’ofar kitchen, sannan ta ci gaba “A nan na zaunar dake nace miki ki rabu da wannan Yaron, kika nuna mini kin amince, amman saboda kin raina ni, ban isa in baki shawara ki d’aukaba, kuma ki nuna ban isa dake ba shine kika ci gaba da kulashi!!
Jiya principal d’inku duk sai da ta fad’a mana komai har yadda yace “yana son ki a gaban kowa da yake shi bashi da kunya ke kuma kika biye masa bayan kin san da zancen Usman!!
Daman na riga na gama yanke shawarar ko ba a kore ki ba to baza ki ci gaba da zama a makarantar ba!
Maryam kin bani mamaki matuk’a wallahi, banyi tunanin haka daga gareki ba sam,
kuma nima zan baki mamaki, dan wallahi idan baki tsaya kin auri Usman ba to ki saka a ranki babuni babu ke!
Idan taurin kai kike tak’ama dashi ina so ki san cewa a wajena kika gada!
Da ni dake aga wanda zai janye.”

Kuka Maryam ta sake fashewa dashi, ita kuwa Shuwa ta wuce tayi hanyar d’akinta ta barta a wajen…Bilkisu ce ta zo tayi ta lallashinta har aka samu ta d’an yi shiru ta tashi suka tafi dakinta.

Haka ta wuni har dare sukuku, tana d’akin taji Baaba Talatu ta shigo tana tambayarta, wai “Usman yace mata d’azu taje ta lab’e mata ita da Jamilu”
Shuwa ce tace
“Ai yanzu Maryam komai ma akace tayi ba zan musa ba, kiji fa har da lab’e ta koya, tabbas ta yi kam dan nan ta shigo tana ta faman yi mana haukan k’arya….”
Nan dai Shuwa ta hau labarta mata yadda sukayi d’azu…

“Allah ya kyauta”
Baaba Talatu tace.
Daga nan suka hau shirye shirye.

Bayan sun gama ne taji Baaba
Talatu tana cewa “bari ta lek’ata kafin ta tafi, da mugun sauri ta shige bargo ta hau barcin k’arya, tana jinta ta lek’a har fuskarta tana cewa “Ashe ma tayi barci”
Ita dai bata kula taba har ta juya ta fita, dan ita yanzu Baaba Talatu ta fara bata mamaki, k’iri k’iiri take nuna son y’ay’anta, sab’anin su Shuwa.

Da daddare tana daki ta idar da sallah abun duniya ya mata yawa, ita ta rasa ta gudu ne ko ta tsaya bama ta san ta Ina za ta fara ba amma idan akawai abunda yake da yak’ini akai
shine ‘ko sama da k’asa zasu had’e ba zata tab’a yarda da auren Ya Usman ba!!’ Idan ta yarda kenan tama karb’i laifin sharrin da aka k’ala mata ta yarda ta yi d’in kenan!!!Shigowar Shuwa ne ya katse mata tunani.
Da sauri ta mik’e ta hau gaisheta, bata amsa mata ba kawai ta juya tace “kije parlourn Abban ku yana son ganinki.”
Daganan ta sa kai ta fita.

Ninke sallayar Maryam tayi ta bi bayanta ta nufi parlourn Abban nasu.

Tana shiga ta sameshi yana shan shayi, da Al’Qurani a hannunshi…sai da ta jira ya kai aya ya rufe sannan ta gaida shi…cikin kulawa ya amsa mata kafin ya ce “Maryama.”
A hankali ta amsa kanta a k’asa.
Ajiyar zuciya ya sauk’e kafin ya fara magana cikin nutsuwa…
“Ki sani ko da ace duk duniya zasu yarda da abinda akace a kanki ni ba zan tab’a yarda ba.”

Da sauri ta d’ago kanta ta kalleshi wasu hawayen farinciki suna gangaro mata, bata san lokacin da murmushi ya sub’uce mata ba.
Gyad’a mata kai yayi sannan yaci gaba “na san halinki na san tarbiyyar ki, fiye da kowa.
Amman Maryam ya zama dole a d’aura miki aure ranar juma’ar nan!!”.

“Innalillahi wainna ilaihir rajiun.”
Shine abunda Maryam ta fara maimaitawa, tana hawaye sannan tace
“Abba yanzun fa kace ka yarda da ni.”

Jinjina kai yayi alamar ‘eh’, kafin yace “Tabbas Maryam na yarda dake amman kuma auren shine mafi alkhairi a tattare dake, makarantar nan da kika yi sananniyar makaranta ce, yanzu sun baki expel!! Ko kin san cewa babu makarantar da zata d’auke ki da saninsu? Sannan mahaifiyarki tace ‘ba zaki k’ara komawa makaranta ba!’ Zaman me to za ki zauna yi??
Sannan abu na biyu, ban san ya akayi zancen nan ya zagaye gari ba, amman jiya har meeting aka had’a da dattijawan unguwa, saboda ke!! Abun takaicin anan shine ba zan iya kare ki ba saboda all
evidences are against u, abunda nake tsayawa tsayin daka dan ganin al’umma basu fad’a ciki ba, yau nine ake zargin y’ata da shi...

Maryam da ace kin yi abunda ya kaiki makarantar kawai baki tsaya kula Yaron nan ba da duk haka bata taso ba, yanzu idan shekaru suka yi gaba, ba lalle ki auru ba domin kusan kaf layin nan maganarki akeyi, kuma kin san idan miji ya fitowa mace a wajen y’an unguwar su da makarantar da tayi ake bincika halayenta wanda inada tabbacin ba zasu bada shaida mai kyau a kanki ba!
Maryam hakan zai fi yi mini ciwo fiye da aurar dake da zanyi a yanzu, ko ba komai hankalina a kwance yake da Usman, na san zai kula dake matuk’a.

Ki yi hak’uri, wanda ya riga ka zama dole zai riga ka tashi, ki rungumi k’addararki, baki da wayo shiyasa aka yi saurin k’ulla miki sharrin da ba zaki iya fitar da kanki ba….”

Kukan da Maryam take yi ne ya sanya shi sak’k’owa daga kan kujerar da yake, ya shiga lallashinta da fad’a mata kalamai masu kwantar da hankali har sai da yaga tayi shiru tukunna ya sallameta, jikinta a mace haka ta tashi ta fita.

A hankali ya saka yatsarshi ya d’auke kwallar data taru a idonshi, sannan ya koma ya zauna ya jingina da jikin kujerar had’e da lumshe idanuwanshi…….

BULAMA ✍️

So da Buri
Free Book
13

Maryam tana shiga d’aki ta fad’a kan gado ta fashe da wani mugun kuka…ta kusa awa d’aya tana abu d’aya, idanuwanta duk sun kumbura fuskarta tayi jajawur!!! Sai da tayi mai isarta tukunna ta hak’ura ta shiga sauk’e ajiyar zuciya akai akai….
Kamar wadda ta tuna da wani abun ta mike zumburr!! ta nufi wajen kayanta, k’asan ta d’aga ta zaro wata farar takarda..tun ranar da Abba ya bata takardar bata duba ba, warewa ta shiga yi a hankali,
tana gama bud’ewa idanuwanta suka sauk’a kan wasu y’an nambobi a jere waenda ko ba a fad’a mata ba ta san number landline d’inshi ce.
“Lalle ma Abba!! wato ma nice zan kirashi!! despite the fact that na yi mishi kwatancen gidanmu!! he didn’t even bother to come. Sannan kuma all this time already yanada wadda zai aura ya tsaya b’ata mini lokaci……Allah ya isanaa!!”
Ta fad’i hakan a cikin zuciyarta cikin d’aci da zafin zuciya.
Jin zuciyarta tana shirin fashewa ne yasanya ta duk’unk’une takardar ta jefar da ita ta koma ta zauna a kan gado ranta yana sake b’aci.
Gaskiya Shuwa ta fad’a da tace mata “b’ata mata lokaci kawai zai yi amma yanada wadda zai aura.’ Dan kuwa gashi ashe Abba yaudarar ta yake yi ita bata sani ba, dan inda ace son gaskiya yake mata ai da zai lek’o ta.
Ganin zuciyarta tana shirin fashewa tsabar takaicin abinda take tunanin yayi mata gashi zaai mata auren dole kuma duk shi ya ja amman bai ma damu da ya san halin da take ciki ba, kuma duk yadda ta k’ok’arta ta kasa rabashi da zuciyarta! Hakan ya sanya kawai ta yanke shawarar ta d’auki number ta kirashi, ta fad’a mishi ta fa san yaudararta yayi, at least zata rage wani b’angaren na damuwa takaici da tashin hankalin da take a ciki!! kwana biyun nan.
Sai dai kuma Allah yasa yana gidan, dan ta san maybe a time d’innan yana school yanzu….
Da wannan tunanin ta mik’e ta isa inda ta yar da duk’unk’unanniyar takardar….da kyar ta iya bud’ewa dan har sai da ta d’an yage tsabar yadda ta d’unkuleta ta jefar d’azun…Haddace nambobin tayi a kanta sannan ta nufi falo. Kamar ko da yaushe landline d’insu yana kan tebur kusa da tv, kamar munafuka haka ta lek’a kitchen ta tabbatar Shuwa bata nan maybe ko ta fita ne Itada Bilkisu dan gidan shiruu, a hankali ta isa ta murza nambobin ta d’aga ta kara a kunnen ta…ba‘a wani dad’e ba aka d’aga.

“Hello who is there?”
Taji ance mata
A hankali tace “please i want to speak with Abba.”
“Ok! hold on, let me tell him.”
Mutumin yace sannan taji yana magana “Sir, someone wants to talk to you.”
Daga chan nesa taji muryar Abba yana cewa “Who’s it?”kamar bashi da lafiya
Jin muryar tasa kuwa da tayi , sai taji kamar rabin damuwarta ya kau, dukda haushin sa da take ji.
Mutumin ne ya sake tambayar ta “Ma’am pls what’s your name?”
“Maryam”
Ta bashi amsa.
Tanaji mutumin yace mishi “Maryam.”
Kafin kace kwabo muryar Abba har ta iso cikin dodon kunnen ta, da alamun har ya k’araso ya amshi wayar, muryarshi har wani rawa take yi
taji yana cewa
“Maryam! da gaske kece?
Ya kike? how is everything?
Zan zo soon, in shaa Allah…i missed you a lot!”
Ya fad’a kamar zai yi kuka wanda hakan yasa Maryam ta ji tausayinshi a d’ayan b’angaren zuciyarta kuwa tana ganin rainin hankali irin na Abba wai ‘he missed her!’ amman kuma shine ya kasa zuwa ya ganta?.

Murmushin takaici tayi sannan tace “Ai ba zaka damu ka zo ka ganni ba tunda kana da wadda zaka aura, Abba I just call saboda Ina so in tambayeka dalilin da yasa ka tsaya b’ata mini lokaci, bayan ka san an yi maka mata??”
Tayi mishi tambayar ranta yana sake b’aci.

Murmushi taji yana yi, kafin yace “Even your anger sounds sweet to me Maryam, i‘m just happy Ina jin muryar ki yanzu..”

Maryam zuwa yanzu ranta ya b’aci sosai kamar ta fashe da kuka haka take ji…
Jin tayi shiru yasa yace
“Maryam kema idan kin san kina da wanda zaki aura mai yasa kika tsaya kulani??”
Jin tayi shiru yasa shi sake maimaita mata tambayar.
A hankali tace
“Ni bana sonshi, tun farko”
Da sauri yace “nima haka wallahi
&
Inaso ki san cewa ‘ni Abba na yi miki alk’awarin ke! Zan aura duk runtsi, ko menene zai faru after that I don’t care, i‘ll choose our happiness akan koma.......”
Kukan da ta fara yi ne ya saka shi kasa k’arasawa.. nan ya fara tambayarta “mai ya faru??”
Cikin sheshshek’ar kuka tace “Abba duk wannan ba shi da amfani yanzu, da ace ka zo ka lallab’a Abban mu da duk hakan bata faru ba, amman ya....”
Cikin tare numfashin ta yace
“Maryam Yayana ne yayi grounding d’ina for 2 weeks!! Ya ma k’i ya tsaya ya saurareni kwata kwata, gaba d’aya baya kulani…
Bayan tafiyar ku ya zo nema mini transfer, shinefa wannan matar ta tisa shi a gaba ta dinga yi mana sharri…Amman kar ki damu, duk fushin da Yaya zai yi dani na san 2 weeks d’innan yana cika ya huce, kuma zai saurareni, daga nan zan zo in sha Allah..
Yau sauran 5 days ai kwanankin su k’are.”
Ya fad’a sounding so relieved.

“Kafin nan an d’aura mini aure”
Ya ji Maryam d’in ta fad’a..

Ba abinci ko ruwa yake sha ba amma wata muguwar kwarewar da yayi sai da ta d’auke shi kusan minti uku yana tari tukunna ya dawo dai dai.
Cikin tsananin tashin hankali yace “kiyi mini wasa akan komai Maryam amma banda wannan!! me hakan yake nufi???”
Yayi mata tambayar da kakkausar murya…

Duk abinda ya faru daga dawowarta zuwa yanzu babu abunda Maryam ta b’oye mishi.
Ga mamakinta bai ce mata komai ba, kawai taji ya ajjiye wayar.

Ta kai kusan minti d’aya da kan wayar a hannunta, tukunna ta share hawayenta ta ajjiye ta juyo da nufin komawa d’aki suka yi ido biyu da Shuwa.

Gabanta ne yayi mugun fad’uwa, cikin rawar jiki da na murya mai cike da in ina
ta k’arasa inda Shuwan take ta hau kame kame “Da da ddmn kawai nn ccemishi bai kky…”
Wani wawan marin da Shuwa ta kwasheta da shi ne yasa ta kasa k’arasawa, bata dawo dai dai ba ta k’ara mata wani wanda yasa har sai da ta kai k’asa tana shirin tashi ta rufeta da duka…..
Sai da Shuwa tayi mata lilis!! kamar ba ita ta tsugunna ta haifeta ba, dan har sai da takai bata iya kuka tsabar azaba, tukunnan ta kyaleta tana mai cewa
“Tunda na lura kin daina fahimtar yaren magana
watak’il ki fahimci wannan!.
Gani kike yi yanzu kinfi k’arfin kowa ko? To ni da ke mu zuba mu gani.”

Tana gama fad’in haka ta wuce ta isa wajen landline d’in, ta gwada yafi sau nawa amman dai ko ba’a d’auka bane ko kuma bai tafi ba.

A haka tazo ta wuce ta tsallake ta, ta tafi ta barta a kwance a falon tana kukan wahala..
Ganin ba zata iya taimakawa kanta bane yasa kawai ta hak’ura, a wajen baccin wahala ya kwasheta.

Kamar a mafarki taji ana tab’a fuskarta ana haskawa da tochila, bud’e idanuwanta taci gaba da yi, bata ganin komai sai hasken fitilar…sama sama take jin muryar Ya Usman yana cewa “Abba ba sai ka kira Likitanba, ta farfad’o.
Da sauri Madu ya k’araso yana tamabayarta “mai ya faru? Mai ya sameta?”
Bata ida bashi amsa ba Shuwa wadda ke shigowa yanzu tace
“Ni da itane.”
Da mamaki ya mik’e ya juya yana mata kallon tuhuma kafin yace “ke da ita? ban ganeba.”

“Dukanta nayi”
ta fad’a tana k’ok’arin wucewa.

Da sauri yace “mai yasa??dakata mana!! Ina zakije ana magana! Mai ta yi miki?”
Ya fad’i hakan yana k’ok’arin hanata wucewa.

Da mamaki Shuwa take kallon shi dan bai tab’a yi mata haka ba. Kallon Maryam d’in tayi da take k’ok’arin zama, sannan
tace “Kamata nayi ta kira wanchan Yaron na makarantarsu, tana cewa za a yi mata auren dole…
shiyasa na zane ta! tunda kunnenta ya daina jin magana watak’il idan aka tab’a lafiyarta zata fi fahimta tun……”

Madu bai bari ta k’arasa ba ya rufeta da fad’a, shi kanshi ya manta rabon da yayi mata fad’a hakan suna a su kad’ai ma, ballantana a gaban Yara.

Sai da yayi mata tatas tareda kwakkwaran kashedin kar ta sake dukar masa Y’a, tukunna ya juya ya fita ranshi a mugun b’ace! Shi a ganinshi yanzu Maryam ai ta wuce mari ma ballantana irin wannan dukan, kuma abun haushin ta tsallaketa ta barta ko bi ta kanta ma bata yiba, idan ma mutuwa zatayi bata damuba kenan.!
Sai da yaje masallaci ya zauna shi d’aya, daga baya yayita karatun Qur’ani tukunna ya d’an samu zuciyarshi tayi sanyi.

Shi kanshi ya san idan akwai abu mafi soyuwa a rayuwar sa to Maryam ce, bayajin akwai uban da yake son Y’arshi a duniyar nan kamar yadda yake son Maryam, shi yasa idan ya tuna ranar Jumaar nan zai aura mata wanda bata so sai yaji gabanshi yana ta fad’uwa, amman bashi da yadda zai yi ne shiyasa, hakan it’s the right thing to do.

Ita kuwa Shuwa da kyar ta fita daga shock d’in data shiga na fad’an da Madu ya rufeta da shi, aikuwa akan Maryam itama ta zazzage nata fad’an, kafin ta juya tayi d’akinta.

Maryam mamakin yadda Shuwa ta juya mata baya lokaci d’aya take yi, ita kam zata yi k’ok’arin yin yak’i da zuciyarta ta rabu da Abba dan taga abun nasu yana shirin tab’a har zaman lafiyan iyayenta.

Muryar Ya Usman ce ta katse mata tunani, da sauri ta d’ago ta kalleshi…a hankali yake ce mata “Ya jikin?”
“Da sauk’i” tace dashi, tana k’ok’arin kawar da kanta daga kallonshi, dan bata son ganin fuskarshi! Gani take yi shine ummulabaisin haddasa mata duk wata fitinar da take ciki a yanzu.

Sake fuskantar ta yayi ya d’an tsugunna a gabanta sannan yace “Inane yake yi miki ciwo?”

Chan k’asa a hankali murya ciki ciki tace “Babu ko ina.”
Ta fad’i hakan tana turo baki tana k’ok’arin tattaro ragowar k’arfinta domin ta samu ta mik’e.
“Mai kike buk’ata??”
Ya sake tambayarta.
“Ba komai.”
Tace dashi a d’an hassale sannan ta mik’e da sauri dan so take ta bar wajen.

Mik’ewa shima yayi, sannan yace
“Maryam!”.
Tsayawa kawai tayi ba tare da ta amsa ko ta kalleshi ba, dan zuwa yanzu ta fara tunanin anya su Ya Usman basu had’a jini da mayu ba kuwa?….

Maganarshi ce ta katse mata tunani “Ba kya sona ko?”
Yayi mata tambayar yana isowa dab da ita.
Shiru tayi bata ce komai ba.
A hankali ya fara magana....
“Maryam ko baki fad’a ba na san bakya sona a yanzu!
Amman inaso ki san wani abu guda d’aya! ‘Ko da ace bana sonki, auran had’i za ayi mana, kika yi wannan tawayen, kika nunawa duniya bakya sona kika zab’i wani a kai na to tabbas ko sama da k’asa zata had’e wallahi sai na aureki!!
Ballantana kuma Ina sonki!
A yanzu bani da burin da ya wuce In aureki saboda abu uku:
‘Soyayyata a gareki

‘In nuna miki kuskuren ki

‘sannan inaso ki gano soyayya ta da take a cikin zuciyarki wadda wanchan Yaron yake k’ok’arin binnewa…

Dan haka shawarata a gareki itace ki daina d’aga hankalinki kina k’ok’arin hana abunda ba zai tab’a hanuwa ba’.”
Yana gama fad’in haka ya juya ya fita.

Maryam bata samu daman tafiya d’akin da tayi niyya ba, hakan ta koma ta zauna a wajen taci gaba da kuka, har sai da Bilkisu ta zo tayita lallashinta tukunna ta mik’e ta isa d’aki tayi ta jero nafilfilinta..
Dan sai a lokacin ma ta lura ashe dare yayi.

Washegari da safe taga anata shirye shirye, zuwa k’arfe d’aya motocin y’an Maiduguri suka fara sauk’a, sai a lokacin ta tabbatar tabbas aurenta za ayi, kuma tayi alk’awari idan son Abba zai kasheta ba zata sake kiranshi a waya ba, dukda ta karb’i uzurin shi da ya gaya mata, kuma ta yadda ba son Yarinyar yake yi ba amman mai yasa zai kashe mata waya? kuma bai ma fad’a mata magana mai dad’i ba da zata d’an kwantar mata da hankali…..
Tana wannan tunanin wata cousin d’inta ta shigo ta, suna ganin juna suka hau murna, dan ba laifi suna shiri sosai da Maryam d’in.
Bayan sun d’an gaisa tace “turota aka yi ta kirata”
Tayi sauri ta je kafin fushin Inna ya k’aru….
Tunda Maryam taji an ambaci inna gabanta ya hau fad’uwa!
Haka ta zari gyalenta ta fita jiki ba kwari, cousin d’in tata na biye da ita.
Tun kafin ta k’araso Kakar tasu ta fara surfa mata fad’a, da yaren Shuwa da Hausa duk had’awa take yi, dan kaf Shuwa ta labarta mata halin da ake ciki…….tana yi sister’s d’in Shuwa suna tayata, ahaka dai suka yi mata tattass sai kuma aka koma nasiha ana cewa “ta bi zab’in da iyayenta suka yi mata, ta kyale wanchan Yaron waye waye….”
Ita dai Maryam tayi shiru tanata kad’a kai kamar k’adangaruwa, sai da suka gama tukunna suka hau yi mata gyaran jiki, bayan nan akace taje tayi wanka anjima akwai kaulu. Nan suka shirya kayayyakin Al’ada da su tabarma wai zasu kai gidan ango, Shuwa kam sai ce musu take yi “ai da sun bari, dan babu wani shirin aure da akayi, babu ma fa tambaya ba komai kawai dai Madu yace jumaar nan zai aurar da ita ga koma waye shi kuma Baban Usman yace ga Usman nan, to maybe sai a masallacin gobe za ai komai a lokaci d’aya kuma a d’aura auren”
Amma su dai basu biye taba sai da suka kai kayan tukunna hankalinsu ya kwanta, a cewarsu ai wannan dolene dan ma babu lokaci ne da duk wata al’ada sai sunyi…..

Gyaran jikin da aka yiwa Maryam na iya wuni d’aya yayi masifar karb’arta, tayi kyau sosai!!
Tana zaune gaban mirror tana shafa mai fitowarta kenan daga wanka, cousin d’inta ta d’azu ta sake shigowa tace mata
“Wai Shuwa tace tayi sauri taje parlourn Madu yana nemanta yanzu yanada bak’i.”
A gurguje ta shirya ta saka doguwar riga y’ar kanti ta zumbula uban hijabi kalar blue black, ta fita da niyyar idan ta dawo sai tayi shirin Kaulun.

Kowa ya kalleta sai ya k’ara, ana ta yaba kyawun da tayi haka tazo ta wuce su ita dai bata cewa ‘k’ala’ sai dai murmushi.
Tunda aka ce mata Madu yana kiranta haka nan gabanta yake fad’uwa, tana k’arasowa bakin k’ofar falon taji fad’uwar da gabanta yake yi ya tsananta!! Da kyar ta iya saisaita kanta tayi knocking, ta ciki taji muryar Baba Bashir yana cewa “ta shigo”
Hannu tasa ta murza handle d’in k’ofar sannan ta tura had’e da tura kai ta shiga, kanta a k’asa.
Haka nan ta kasa d’agowa sakamokon yadda zuciyar ta ke bugawa sosai sosai, sai da ta samu waje ta zauna tukunna ta d’ago kanta da niyyar gaishesu......

BULAMA ✍️

So da Buri
Free Book
14

idanunta suka sark’e a cikin na Abba wanda ya kafeta da ido ko alamar kyaftawa bayayi.....

Mutumin dake zauna a gefen sa mai tsananin kama da shi ne taji yana cewa “Ma sha Allah, mun sameki lafiya??”

Cikin d’an jin kunya ta sunkuyar da kanta sannan tace “ina wuni.”

Yana murmushi ya amsa mata,
Ita kuma ta juya ta gaida Madu da Baba Bashir, sannan ta gaida Abba wanda ya kasa daina kallonta, ko kunya ta kasa hanashi kallonta a gaban iyayenta.

Da kyar ya iya cewa “Lafiya”
Wanda ba ma kowa ne ya ji ba sai ita d’in da take kallon fuskarsa.

Madu ne yayi gyaran murya sannan ya fara magana “Maryama wannan shine Yayan Abba”
Yayi maganar yana nuna wannan mutumin da yake zaune a gefen Abba.
Jinjina kai Maryam tayi sannan ta sake gaidashi kanta a k’asa
Murmushi shima yayi ya sake amsawa dan a gaskiya Maryam ta burge shi, yanayin nutsuwa da hankalinta sun burgeshi.

Madu ne ya cigaba da cewa “Lokacin da muka dawo daga hajji mun baku labarin wani bawan Allah da ya taimakemu aka tseratar da Usman ko?”
Jinjina kai ta kuma yi.
Ajiyar zuciya Madu ya sauk’e kafin yace
“To gashi nan a zaune”
yayi maganar yana sake nuna mata Yayan Abba, da sauri ta d’ago ta sake kallonshi wanda shi kuma a yanzu Abba yake kallo har yana d’an tab’ashi da alama nuni yake yi masa da ‘kallon ya isa haka’.

Modu ne ya d’aura da cewa
“Sunanshi, Alhaji Yahaya Umar Farouk mai turare, d’azun nan aka yi sallama ana son ganina, abun mamaki ina fita sai na ganshi, mutumin da muke nema ruwa a jallo sai gashi yau har gida.
Daman ni tun ranar da naga Abba a makarantar ku naso tambayarshi saboda tsananin kama da naga sunayi, amman kasancewar yadda abubuwa suka kasance a ranar ya sanya ban samu dama ba.”

Alhaji Yahaya ne yayi gyaran murya sannan yace
“Ina mai baku hak’uri, da kuma rok’on mu manta da wanchan zancen har Abada!
Saboda hakan ba abune mai maana ba especially idan muka yi duba da yanayin hankali da tarbiyyar Yaran.
Laifin su d’aya da suka yi shine da suka tsaya kula juna a makaranta, kowa yasan hakan sab’a doka ne, wanda hakan ne ya sanya ma maganar ta samu gurbi.

Ban san waye ya had’a kuma ya fad’i wannan labarin ba amman tabbas na san k’arya ne…. Mu uku mahaifin mu ya haifa a duniyar nan, bani da d’an uwa mafi kusanci dani kamar Abba, shiyasa ko a lokacin da nayi aure ma tare muka tare a chan part d’ina dashi kuma har yau a gidana yake…. na san abinda Abba zai yi na san wanda ba zai yi ba, dukda ance ba a shedar mutum amma ni kam zan shedi Abba a duk inda yake.

Na hanashi fita ne tun dawowarshi ba dan komaiba sai dan saboda ita Yarinyar,
saboda na san ko wanne Uba idan aka fad’i irin wannan maganar akan y’arsa dole zai d’au zafi ba kad’an ba, so shiyasa na hanashi zuwa nace masa ya d’an bari abubuwa su lafa tukunna sai mu zo, dan already daman na saka a raina zamu zo neman aurenta, dan a duk fad’in duniyar nan bata da mijin da yafi dacewa ta aura kamar Abba.

Sannan Abba ya tabbatar mini da soyayyar ta a cikin zuciyarshi, nutsuwa da hankalinta duk ya gamsu dasu sai a lokacin ne ma yake fad’a mini ashe lokacin da yayi rashin lafiya har na taho ban samu munyi sallamaba wai duk a ta dalilin ya nemi gidan nan ne bai samu ba.

Kuma ya fahimtar dani Yarinyar da aka zab’a mishi a gida sam baya sonta, ko ya aureta ba zasu zauna lafiya ba, shiyasa naga ya dace muje mu samu Mahaifin mu muyi mishi bayani yadda zai fahimta tukunnan muzo nan
To amman kuma jiya sai ya zo mini a hargitse wai jibi za a d’aurawa Maryam aure!! Da na koreshi nace ‘ya jira har sai lokacin da na d’iba mishi yaga maryam d’in yayi tukunna zamuzo’ dan ni a tunanina kawai fad’a yakeyi ba wani aure, dan naga ya k’agu ya ganta d’in
A take ya sume min, da kyar ya farfad’o yau da safe, bayan Likita ya tabbatar mana jinin shi ne ya hau saboda damuwar da take neman yi mishi illa, shiyasa a take na saka shi yayi wanka ya d’an ci abinci ko mai d’akina ma ban samu damar gayawa ba muka taho..

A labarin Maryam, ta gayawa Abba cewa ka ce ranar Jumaah zaka aurar da ita, so a iya yadda na fahimta watak’il baka riga kun tsaida mijin ba,ko?
Saboda haka
gamu nan mun zo neman aurenta ban sani ba ko za a amince a bamu…
…….Very short ya d’an basu biography d’in familyn ‘Mai turare’.”
Dayake sanannen family ne, nan suka ce “ai suna jin ma sunan familyn..”

Baba Bashir ne yace “Alhaaji munji abinda yake tafe da kai, amman kafin komai da farko muna so mu fara yi maka godiya!! Mun gode sosai da taimakon da kayi kwanakin baya, Allah ya saka da alkhairi.
Sannan magana ta biyu,
ni dai kamar uba nake a wajen Maryam dan haka na bawa Abba ita halak malak!! Idan Allah ya kaimu gobe Jummah indai a shirye kuke za’a d’aura aure, sai dai In wani mugun hali muka ji a kansa (dan za muyi bincike kamar yadda ake yi In sha Allah) amman bayaga haka gobe iwar haka bi’izinillahi ta’ala an d’aura musu aure.”

Da sauri Madu ya kalle shi, kafin yace “Bashir maganar Usman fa, ya zamu yi?”.
Murmushi Baba Bashir yayi sannan yace “kar muso kanmu anan mana, Usman fa shi kad’ai yake son Maryam ita bata sonshi, wannan Yaron kuma”
yayi magana yana nuna Abba
sannan yace “yana sonta itama shi takeso.
Sannan abu na biyu, wannan bawan Allah” ya nuna Yayan Abba sannan yace
“Tun ranar da ya taimaki Usman muke son sake ganinshi dan mu gode mishi, yau gashi Allah ya kawoshi yana neman abu a wajenmu! Mai zamu tsaya jira???? Ka tuna shine fa silar fitar da Usman a wanchan had’arin wanda ba dan an gano gaskiya ba, da watak‘ila babu Usman a doron k’asa yanzu.

Kuma dani da kai duk na san auren nan nasu sai yafi kwantar mana da hankali, saboda abubuwa da dama..”

Shiruuu! Madu yayi…..tabbas duk abinda Baba Bashir ya fad’a babu k’arya a ciki, dan haka shima ya yanke shawarar ya bi bayan Baba Bashir d’in a take!
Juyowa yayi ya fuskanci Maryam sannan yace
“Maryama kina sonshi ko?”
Dariya Baba Bashir da Yayan Abba suka yi sannan Baba Bashir yace
“Kaima dai neman magana kake yi.”

Murmushi yayi kafin yace
“kawai ina son inji ta bakinta ne, ta fad’a a gaban kowa.”
Sannan ya sake maimaita mata tambayar……cikin jin nauyi a hankali ta d’aga kanta alamar ‘eh’.
“Alhamdulillah” shine abinda Madu yace, sannan shima ya tabbatarwa Abba ya bashi Maryam…
Yace “Ba sai ya wani had’a lefe ba sadaki kawai suke buk’ata su zo da shi gobe.”

Yayan Abban ne yace
“Maganar b’oye b’oye babu ita a tsakaninmu kuma ni mutum ne daman straight forward….

A gaskiya! Ba lalle mahaifinmu ya yarda da d’aurin auren a gobe ba, duba da yadda ya riga yayi wa Abban mata kuma a yau zamu gaya mishi d’aurin auren, na san za a d’an kai ruwa rana, watak’ila yace sai nan da sati biyu dan zai d’anyi gayyata…
Amman wannan duk ba matsala baceba, za azo a goben ko iya mu uku ne in sha Allah zamu d’aura auren, dan na lura Madu yana so ayi auren a gobe, inyaso daga baya sai a sake sabon aure mai taro idan mahaifinmu ya tsayar da rana…..”
A hakan kuwa aka bar maganar.
Murna a wajen Abba ba’a magana, dan ko kunya bayaji, haka nan ya zage ya dinga jero godiya ga su Madu, har sai da Baba Bashir ya fara tsokanarshi……:

Sallamar Maryam suka yi ta tafi su kuma suka ci gaba da hirar su cikin mutunta juna kafin daga baya suka yiwa juna sallama suka tafi akan gobe za’a had’u a masallaci in sha Allah…..
Da kyar Alhaji Yahaya ya lallashi Abba ya hak’ura
ya bishi suka tafi saboda da shi ya dage ne akan sai ya ga Maryam tukunna zai tafi…..

Shuwa da ragowar mutane sai bin Maryam suke da kallo, Yarinyar da take ta koke koke akan ita bata son auren, amman dubeta yanzu yadda ta ware dan ko makaho idan yaji muryarta sai ya tabbatar da tana cikin farin ciki, haka nan aka sakata a lalle aka yi kaulu lafiya tanata washe baki kamar ba itaba.

Bayan sallar isha kowa ya watse….Madu da Baba Bashir suka nemi ganin Ya Usman, Baaba Talatau Ya Jamilu, Maman Shuwa, Shuwa da y’an uwanta.....
SHARE PLS.

BULAMA ✍️

So da Buri
Free Book
15

Ba tare da b’ata lokaci ba Baba Bashir ya fad’a musu duk abinda ya faru d’azu…
Tun kafin ya k’arasa Baaba Talatu tace “zancen banza ma kenan!!! Ai indai gaskiya za a bi to haramun ne neman aure a cikin aure”.

Cikin b’acin rai Baba Bashir yace “waye kenan yake yi miki zancen banzan?? Sannan ban gane maganarki ta ‘neman aure cikin aure’ ba! Shin a tsakanin ni ko Madu waye kika tab’a ji ya cewa Usman ya bashi Maryam??
Shiyasa fa d’azu na kyaleku ban kiraku ba, dukda yadda na so ace ke da Shuwa kun zo kun yiwa mutumin nan godiyar abinda ya yiwa Usman kwanakin baya, amman kawai sai na fasa domin na san k’aramar kwakwalwa gareku, indai kuka lura shine yayan Abba sai kunsa munji kunya…”

“Ko kuma dai an so shirya munafurci shiyasa aka k’i kiran nasu ba!”
Maman Shuwa ta fad’i hakan
sannan ta mik’e tace “Madu na lura ba zaka iya tsawatarwa Yarinyar nan ba! Ba zaka iya tirsasa mata tayi abinda ya dace ba, a k’a‘ida fa babu ita a hurumin zab’arwa kanta mijin aure, ku iyayenta ku ya kamata ku zab’ar mata.
Allah na tuba yaushe ma Maryam d’in ta NuNa ne wai? Da har ta san wani soyayya?.
Daman ni tunda naga sauyi a tattare da ita d’azun na san da wata a k’asa!.
Son da kake yi mata ya sanya baka son ganin b’acin ranta kwata kwata, to inaso ka sani wannan Maryam d’in da kake shagwab’awa ko bayan raina zaka ce na fad’a maka ‘Wallahi sai ta kunyataka!!’ Ai shi Yaro ba a yi masa haka kwata kwata.
Taya ma za ayi ka bari ta auri wanda suka gama lalacewa a waje? Allah na tuba Yaro ka auresa da mutuncinka ma ya aka k’are ballantana wanda ya sanka tun a waje??
Ai ni wallahi na ma ga k’ok’arin wannan Yaro Usman da ya amince zai aureta, ga mahaifiyarshi itama y’ar albarka bata k’i jininka ba!!
Ana k’ok’arin a rufa maka asiri, kana son tonawa kanka asiri da hannunka.
Ba Baki zan yiwa Maryam ba amman duk daren dad’ewa indai wanchan Yaron zata aura to kuwa auren ba zai d’aure ba! Sai ta dawo gida kuma sai kun yi dana sani!!!”.

Madu kasa jurewa yayi dan haka yace
“Inna na rok’e ki da girman Allah kiyi shiru!! A matsayinki na Babba ba a so ki dinga mugun alkaba’i haka!! Kawai ki bita da fatan alkhairi…”

A hasale Innar tace
“Ank’i a bita da fatan alkhairin!!! Ai sai mutum yaso alkhairi tukunna za a bishi da alkhairi!
Masifa kuke son janyowa kanku kai da ita k’iri k’iri!!!
Yaron nan ko bincike na tabbata ba kuyi ba….Kai nan kaga mai arzik’i ko? Shine zaka fake da wani wai ‘Yayansa ya taimaki Usman’, ai taimako daban neman aure daban.

Wannan karon Baba Bashir
ne yace “Inna tunda suka zo suka tafi muke bincike akan shi, kuma bamu samu wani mugun abu a kanshi ba kowa alkhairi yake fad’a.”

Cikin fad’a sosai Innar ta katseshi ta hanyar cewa
“Amman tabbas yau na tabbatar Yaran nan baku da hankali wallahi!!! Binciken wuni d’aya shine Bincike????”

Madu ne yace “ai ba a son tsananta bincike ko a addini!”

Ga mamakin su kawai sai sukaga Inna ta fashe da kuka a cewarta wai ‘Madu da Bashir sun rainata! taya za a yi tana fad’a suna mayar mata saikace sun samu sa’ar su!?. Nan ta hargitse musu harda cewa “Sister’s din Shuwa su shirya a daren nan zasu wuce Maiduguri ba zata sake kwana a gidan Madu ba!! Dan yaga ba itace ta haifeshiba shiyasa zai yi mata rashin kunya a gaban Yara, kuma sai ta kira Babansu, zata gaya mishi duk halin da ake ciki, wallahi indai tanada rai ba zata bari Maryam ta auri wanchan Yaron da suka gama lalacewa ba, shagwab’ar ai tayi yawa!! Taya Yarinya tayi laifi kuma still lallab’ata akeyi sai abunda takeso tukunna shi za ayi mata??.
Madu ne yau har da yi mata rashin kunya duk akan y’arsa???”
Da kyar su Shuwa suka d’an lallab’ata ta sassauta kukan, sannan ta hak’ura da tafiya amman tace ‘tabbas maganar auren Maryam da Abba babu ita indai tana raye! Dan sai ta hukunta Maryam akan laifin ta,
da fari taso ta kyaleta amman yanzu ubanta ya janyo mata.”

Hayaniyar su ta sanya har su Maryam d’ib da ke a d’aki suka d’an firfito.

Tarin da Ya Usman ya hau yi ne ya karkato da hankalinsu gareshi, gaba d’aya suka nufe shi….kafin su k’arasa har ya zub’e ya fad’i a wajen sumamme….
Nan kuwa Baaba Talatu ta fashe da kuka, tashi d’aya ta rikice!
Hankalin kowa a tashe aka fara k’ok’arin kinkimarshi..ganin baya motsi ko kad’an kamar gawa, ya sanya Baba Talatu ta juyo a zafafe tayi kan Maryam wadda take k’ok’arin k’arasowa wajen, tana matsowa kawai ta d’auketa da mari!! Ta fara magana cikin kuka
“Maryam mai nayi miki a rayuwar nan in banda alkhairi da kike shirin yi mini gib’i a rayuwa?? Tun tasowarki banda soyayya muraran babu abinda nake nuna miki har iyau, mai Usman yayi miki a rayuwa haka? Muguwa kawai!! Wallahi idan wani abun ya samu d’ana ba zan tab’a yafe miki ba!!.”

Madu ne ya katsesu ta hanyar cewa su d’an matsa su bawa Usman d’in iska sannan ya umarci Ya Jamilu da ’ya d’auko mishi makullin motar shi a d’aki’.
Da Baba Bashir da Madu ne
suka d’auki Ya Usman, suka yi waje dashi, Ya Jamilu kuma ya fito da mukulli ya bi bayan su da gudu, ganin haka yasa suma su Shuwa suka bi bayansu….
Da kyar aka lallab’a Baaba Talatu ta hak’ura bata bisu ba.
Tunda suka koma cikin gidan kuwa Baaba Talatu take kuka, su Innaa da Shuwa kuwa in banda tsigale Maryam ba abinda suke yi…Shuwa ta tabbatar mata ta sake tabbatar mata cewa ‘muddin ta auri Abba to sai dai ta nemi wata uwar amma ba ita ba!!!’
A daren Innaa ta kira Baban su Shuwa a landline d’in gidan ta sanar masa komai!
Yayinda shi kuma ya tabbatar mata da ‘in shaa Allah, gobe da sassafe idan Allah ya kaimu zai taho.’

Sai bayan awa hud’u, tukunna Madu da Baba Bashir suka dawo daga asibiti..
Nan suke gaya musu cewa “an kwantar da Ya Usman, Ya Jamilu yana tare da shi and
the bad news is ‘ya samu stroke!!’ A sakamokon jinin shi da yayi mugun hawa.”
Kukan da Baaba Talatu take yi sai ta baka tausayi, haka itama Shuwa.
Gaba d’aya duk sai Maryam taji ba dad’i..
Gidan ranar babu wanda ya runtsa, da sassafe suka yi shirin zuwa dubo Usman har Maryam amman k’iri k’iri da Shuwa da Baaba Talatu suka hanata bin su…

Bayan sun tafi da awa d’aya tana zaune gidan shiru duk ba dad’i ga damuwa tashin hankali da tunani, daga ita sai y’an tsoffin da su Innaa suka taho dasu.
Sallama aketa kwad’awa a waje, hakan yasa ta sanya hijabi ta fita.
Wani Yaro ta gani a tsaye bayan ta bud’e k’ofar gate d’in,
Yaron ya kalleta sannan yace “Wai Maryam taje inji Abba.”
Sai da gabanta ya yanke ya fad’i…abun ya bata mamaki ‘Abba da sassafen nan?, to Allah dai yasa lafiya.’
Ko cikin gida bata komaba, ta k’arasa gaban motar inda ta hango shi a tsaye cikin shigar shadda tazarce fara k’al tayi masa mugun kyau!!.
Cikin kulawa ya amsa bayan ta gaidashi, sannan a hankali yace “Baki da lafiya ne? Naga idanuwanki duk sun kumbura.”
Kwallar da ta zubo mata ta sa hannu ta share sannan ta shiga koro mishi abubuwan da suka faru tun daga jiya har izuwa yanzu bata b’oye masa komai ba.
Nannauyar ajiyar zuciya ya sauk’e sannan yace
“Maryam kin yarda dani?.”
A hankali ta d’aga mishi kai alamar ‘eh’
Cike da bata umarni yace
“Inaso yanzu! Ki shiga cikin gida, duk wani abunda zaki buk’ata ki d’ebo ki zo dasu, zamu d’anyi tafiya ne, maybe sai nan da shekara d’aya ko d’aya da rabi tukunna zamu dawo.”
Cikin rashin fahimta da d’an tsoron daya bayyana akan fuskarta tace “Tafiya kuma?
Zuwa Ina? Kai da wa?.”
Ba tare da b’ata lokaci ba, yace “Ni da ke! K’asar nan zamu bari
bayan an d’aura mana aure yau! In sha Allah.”
Da sauri ta shiga ja da baya tana girgiza kai kafin tace
“Kana nufin fa mu gudu kenan!! Abba mai yayi zafi har haka??”

Da sauri ranshi a b’ace yace
“Maryam komai ma yayi zafi!! Babu abunda bai yi zafi ba.! Kinga idan na saka k’afa na bar k’ofar gidan nan naku a yau batare da kin bini ba, to ki tabbata ba zaki sake ganina ba har abada!! Ta b’angaren ki ta b’angarena ko ina yayi zafi!! Ya kamata mu tashi mu tsayawa kanmu, saboda iyayenmu basu damu da farin cikinmu ba.”
D’an sassauta murya yayi sannan yace
“Jiya bayan mun bar gidan nan, direct wajen mahaifina mukaje.
Bayan Yaya ya gama yi mishi bayani, Ina tunanin goyon bayanshi amman sai naji yace
‘Shi bai hanani in aureki ba, amman tabbas sai na fara auran cousin sister d’ina wadda ya zab’a mini tukunna bayan shekara biyar sai in aureki!’.
Maryam ko a duniyar matattu muke na tabbatar idan na barki nan da kwana biyar ma to kina gidan Usman.
Mahaifiyata itama ta goyawa Mahaifina baya d’ari bisa d’ari!
Yaya shi kuma wanda nake tunanin zamuzo ni da shi a d’aura mana auren dashi a yau, shima ya juya mini baya. Dan Mahaifinmu d’aki ya kirashi suka shige, bayan ya fito dana yi mishi magana yace mini ‘kawai in hak’ura!!!’.

Maryam, ya kikeso inyi?? still ba zaki yarda ki bini ba?.”

Cikin kuka Maryam tace “Tunda nake a rayuwata ban tab’a ganin Hajiya da Abba suna fad’a ba sai da zancen mu ya fara!
Bana son zama silar lalacewar zaman lafiyar su.
Abba kawai muyi abinda suke so, watarana za muga alkahiri.”

Wannan karon hawayene suka zubo daga idanun Abba
“A hankali yace
“Maryama, ko da ace mun auri waenda iyayen namu suka zab’a mana abun bazai yi kyau ba!! Domin kuwa za muyi ta cusgunawa Abokanan zaman namu ne muna d’ibarwa kawunanmu zunubai a wajen Allah, kuma case an dinga yin shi kenan watak’il ma k’arshe a lalata zumuncin gaba d’aya!
Ga uban zunubin da za muyi ta d’iba a wajen mahaliccinmu, especially ma ke da kike a matsayin mace dan na tabbatar ba zaki iya yiwa Usman cikkkiyar biyayya ba
sannan inaso ki rantse mini yanzu akan ‘shin bayan kin auresa ba zaki dinga tunaninaba?!”.
Da sauri ta runtse idanunta.
Bai jira jin me zata ce ba ya cigaba “to ki sani duk wani tunanin ko wish ko feeling da kika samu a kaina kina da zunubi!.
Ni kuma na tabbatar Idan na auri Zainab (cousin sister d’insa) to tabbas ba za muyi sati ba zan saketa, idan kuma aka tilastamin zama da ita na tabbatar tsakanina da mahaifina sai dai kallo daga nesa, domin kuwa na dinga bak’anta mata kenan shi kuma ba zamu shirya da shi ba muddin zan yi hakan and na tabbatar ba zan tab’a iya zaman aure da ita ba!.
Me kenan aka yi a nan Maryam??
Mun lalata rayuwarmu fa kenan mun lalata ta Abokanan zaman mu.

A yanzu inaso ki rufe idanunki, karki duba kowa a duniyar nan, karma kiyi tunanin akwai wata halitta bayan mu biyu kacal a duniya!
I want you to be selfish Maryam just for today for my sake!
Mu so kanmu fiye da kowa mu sanya kanmu a farin ciki, na tabbatar miki, bayan an d’aura mana aure zamu dawo mu basu hak’uri, komai zai dawo dai dai in sha Allah, koma waye yake fushi damu daga baya za kiga ya daina, an dawo an zauna lafiya da kowa.
Please Maryama, pleaseeee.
SHARE PLS.

BULAMA ✍️

So Da Buri
Free Book
16

Cikin sheshshek’ar kuka Maryam tace “Hajiya fa fushi takeyi dani, yanzu idan na gudu zata kuma jin haushi na.”

Hannu biyu Abba ya d’aura a kansa, kafin yace “O my God!!Maryam da wanne yare kikeso in yi miki bayani ne??
Ko bayan auren ki da Usman zata ci gaba da jin haushin ki ne….in dai kika auri Usman to kun yi ta janyo fad’a kenan a tsakanin iyayenku har azo a lalata zumuncin…”
A hankali ya matso kusa da ita yace “Nace miki kar ki duba kowa yanzu, just ki duba mu biyu kawai, and trust me! Please Maryam, this is the right thing to do….”

Cikin share hawaye tace “Abbana fa?”

“Abban ki ya riga ya zab’a miki ni, so Abbanki ba zai ji haushin komai ba, this is his choice Maryama.
Itama Hajiyan blackmailing d’inta aka yi, sannan kunyan Baaba Talatu take ji shiyasa amman da zarar mun yi aure idan taga kina cikin farin ciki tuni zata manta da komai! Burin ko wacce uwa taga farin cikin Y’arta
Maryam i assure you Usman cannot give you the happiness you deserve!.”
Ya k’arashe maganar kamar zai fashe da kuka..

Shiruu, tayi tana tunani..
Tabbas duk abinda Abba ya fad’a haka ne sannan ta yarda dashi d’ari bisa d’ari!

Cikin katse mata tunani a hankali taji yace “muje..idan komai ya d’an lafa na yi miki alk’awari zamu dawo mu bawa su Hajiya hak’uri, na san zata hak’ura in sha Allah.
Abba kuwa na san shikam farin ciki ma zaiy yi, dan munyi abunda ake k’ok’arin hanasa, wanda hakan shine zab’in shi.
Na tabbatar idan mijin Innarku ya zo ba zai bari a d’aura aurenmu ba, kuma Inna da kanta kinji tace ba zata tab’a bari muyi aureba
wanda na tabbatar Abba ba zai tab’a iya shallake umarnin su ba.”

Cike da gamsuwa da maganganunsa Maryam ta hau d’aga kai alamar amincewa kafin tace
“Amman zamu dawo anjima mu gansu, ko iya Abba ne shi kad’ai, na san ya san yadda zaiyi ya lallab’a Hajiya Shuwa watak’l ta hak’ura, kayi
mini wannan alk’awarin?”.

Ajiyar zuciya ya sauk’e kafin yace “Nayi miki!
Amman nima kiyi mini alk’awari idan mun gama ganinsu, anjiman zamu wuce, saboda ina so in yin nesa da mahaifina ko da na wata d’aya ne. Ba zan iya fuskantarshi a yanzu ba, dan ban san hukuncin da zai yanke
mini ba.”
Ajiyar zuciya ta sauk’e kafin tace “Na yarda!.”
Ahankali yace “Alhamdulillah”sannan ya juya ya bud’e mata gaban mota.

Har ta wuce ta shiga, ta zauna sai kuma ta juyo ta kalleshi
yana shirin rufe mata k’ofar tace “Abba, kana ganin ba matsala?”
Murmushi yayi sannan yace
“Yes Maryam, in shaa Allah, just trust me please..”

“Na yi, amma dan Allah kar ka sa in yi dana sani”
Murmushi yayi yace “i promise, I won’t!”.

Sai da ya juyo ya shiga, ya tada motar tukunna idanunta suka sauk’a akan Sadiya wadda take tsaye a k’ofar gidansu gaba d’aya hankalinta yana a kansu…..

Tafiya mai d’an nisa sukayi dan Maryam kam kanta har ya juye abunka da wadda bata fita sosai, tana cikin y’an kalle kallenta suka iso wani tafkeken masallaci a d’an gaba kad’an akwai hotel…
Wuce masallacin sukayi ya shiga cikin hotel d’in wanda ya gaji da had’uwa ga securities ta koina, ya nemi waje yayi parking.
Babu yadda bai yi da ita akan ta fito ta shiga cikin hotel d’in saboda shi yanaso ya je ya samu limamin yayi mishi bayanin komai, kuma akwai y’an shirye shiryen da yake so ya fara so zai kama mata d’aki ita d’aya shikuma ya fara preparations amman tak’i tace “ita a mota zata jirashi har yaje ya dawo”, hakanan ba yadda ya iya ya kunna mata AC ya bata mukullin ya kwashi abubuwan da zai buk’ata.
Sai da yaje wajen Limamin suka tattauna sannan ya fito ya tari motar haya ya shiga aikin gabanshi.
Sai wajajen 12 tukunna ya dawo Maryam har tayi bacci ta tashi ga tsoro ga yunwa, yana zuwa ya kwankwasa, da kyar ta iya bud’e k’ofar ya shigo mata da abinci sannan yace bara yaje yayi Sallah idan an idar zai zo su wuce.
Haka kuwa akayi sai wajen 2:00pm
Time d’in masallacin kowa an watse tukunna ya dawo.
Yana zuwa ya sa key sannan ya umarce ta da ta koma baya, bayan ta koma ya tada motar yaja suka isa bakin masallaci.
Wani dattijo cikin alkyabba da rawani suka tsaya suka d’auka a bakin masallacin sannan suka hau titi, basu yi wani tafiya mai nisa ba suka gangara kan hanya suka shiga wani layi, a bakin wani gida sukayi horn aka bud’e gate d’in suka shiga.
Bayan sunyi parking sun fito
dattijon ya nuna musu babban parlourn gidan yace wa mai gadi “ya kaisu gurin Hajiya”
Shi kuma ya nufi parlourn bak’i dan yanada bak’i.

Matar mai kirki sosai bayan sun gaisa ta dinga yi musu hira aka kawo musu abinci kala kala, Maryam kam fitsarine yake neman yi mata illa ga Abba a wajen balle tace zata yi fitsari, Allah ya taimaketa matar ta shiga tambayarta “ko tayi sallah?” Da sauri ta mik’e tana cewa “a’a”
Nan ta nuna mata d’aki ta shiga….sai da tayi sallah tukunna ta fito suna cikin cin abinci wannan dattijon ya shigo…..
Sake gaisawa suka yi
kafin ya juya ga matar tashi yace ne
“Yakubu ne k’anin Yahaya, kin ganesa ai ko”
Da mamaki matar take kallonshi, nan ta hau yi mishi tsiya tana cewa “baya ziyara.”
Gyaran muryar da dattijon yayi ne ya katsesu, sannan ya kalli Abba yace “nayi waya da Yahaya yanzu ya tabbatar mini da abunda ka fad’a min d’azu, yace tare kukaje dashi jiya. Amman ni da zaku bi ta shawarata da ko Mahaifinta ko wani d’an uwanta a samu a wajen tukunna, ina ganin hakan zai fi, ko?”.

A hankali cikin girmamawa Abba ya hau yi mishi bayanin komai…sai a yanzu matar take fahimtar ba amarya da ango baneba yet.

Bayan ya kai aya ne dattijon
ya sauk’e ajiyar zuciya
sannan cike da
gamsuwa da zancen nasa yace “ai shikenan!! In dai maza sun riga sun gama magana batun mata ba biyeshi akeyi ba…”
Bai gama rufe baki ba wasu magidanta responsible su uku suka shigo, d’auke da huhunan goro da packs d’in alawowi.

Zama d’ayan yayi sannan yace “Akaramakallahu barka da rana ga sak’on da kace in taho dashi nan.” Amsashi yayi sannan yayi mishi nuni da su ajjiye.
Bayan sun ajjiye an gaggaisa anan yake shaida musu “Aure za a d’aura, za suyi shaida”.
Nan suka amince.
Limaminne ya umarci Yakubu da “ya kawo sadaki.”
kamar jira yake, nan ya zaro dubu talatin a aljihun shi…a take aka gudanar da duk abunda ya kamata, Yakubu ya kanshi wakili, limamin nan kuma ya yiwa Maryama.
A take a falon aka d’aura auren

Yakubu Umar Farouk mai turare
Da
Maryam Muhammad Madu
akan sadaki naira dubu talatin….
Aka raba goro da alaawa a y’an falon sannan aka kwashe ragowar domin rabawa In an fita masallaci dan har an fara kiraye kirayen sallar la’asar.

A gidan suka yi har sallar Magrib…matar mai kirki tanata nan nan da Maryam, ita dai Maryam Allah Allah take su tafi dan ta k’agu su koma gida, dukda yadda gabanta ke ta fad’uwa amman dai tanaso taje ta tunkaresu a tura ta k’are!.
Suna idar da Sallar Magrib d’in wani Yaro ya shigo d’akin da alamun d’an matar ne yace “wai ance Maryam ta fito zasu tafi.”
Ai kuwa zumbur!! Haka ta mik’e har matar har tana tsokanarta….ita dai tayi mata godiya ta kimtsa suka fito tare da matar.
Y’ar guntuwar nasiha mai ratsa jiki Limamin nan yayi musu sannan yai musu fatan alkhairi suka mik’e suka yiwa juna sallama suka nufi k’ofar fita daga parlourn.

Abba ne a gaba sai Maryam wadda ke bi mishi baya bumper to bumper..
…goshi da k’irjinta ne taji sun bugu da gadon bayan shi sakamakon burkin da ya jaa ya tsaya chak!
Lokaci guda, yak’i yayi gaba yak’i yayi baya.
Daga yadda yake tsaye zaka iya ganin yadda jikinsa yake karkarwa sannan duk ya rikice tashi d’aya!.

Magana yake son yi amman sai ya hau in ina sam ya gagara furta koda kalma d’aya mai ma’ana.

Bata dawo daga mamakin abinda ya firgita Abba haka lokaci d’aya ba taji an d’auke shi da wani mahaukaciin marin da saida ya kai ga kaiwa k’asa ya tsugunna a gurin.
Tsugunnawar da yayi ne ya bata damar ganin mutumin da yake gaban su ya tare k’ofar,
kana ganinshi ba sai an fad’a maka ba ka san shine Mahaifin Abba, dogo ne sosai fari k’al kyakkyawa yana mugun kama da Abba da Yayanshi da suka zo tare jiya, sai dai shi
ya d’an manyanta, kana gansinshi kaga tsohon dattijo.
Muryarshi ce ta dawo da ita daga nazarin data tafi jin ya daka wata uwar tsawa yana cewa
“Out of my way! stupid boy!!!”.
Maryam bada ita ake ba amman da sauri ta matsa ta koma bayan matar gidan da itama duk ta rikice ta b’uya.
Shima Abba da sauri ya tashi ya matsa yana shafa marin da aka yi mishi.
Cike da k’asaita mahaifin nasu ya k’araso cikin parlourn
Yayan Abba da wasu maza biyu suna binshi a baya, sai kuma wani Yaro matashi da kayan sojoji a jikinshi.
Kujera inda wannan Limamin yake tsaye ya samu ya zauna ya d’aura k’afa d’aya kan d’aya, ko takalmin shi bai cire ba haka ya shigo mishi tsarkakakken falon da shi.
Ahankali Limamin ya d’an zauna akan tum tum d’in kan kafet sannan yace
“Barka da dare Daddie!”.
Batare da ya amsa shi ba yace
“Did u just got them married??.”
Cike da kwarin guiwa yace mishi “Na’aam.”
Gyara zamanshi yayi ya fuskanceshi da kyau kafin yace
“D’ahiru you know I can sue you right??”.
Wannan karon murmushi Limamin yayi, kafin yace
“A tsarinka zaka iya suing d’ina, amman a musulunce ba zaka iya ba, dan Yahaya ma magabacinshine, dan haka kuwa kaga ba zaka iya suing d’ina ba!.
Bayaga haka, Abba iya shi kad’ai ya isa yiwa kanshi wakili….”

“I’ll get back to you later.”
shine kawai abinda Granpa yace dashi cikin katseshi
sannan ya mik’e ya isa gaban Abba ya tsaya.

Hannunshi ya mik’a baya alamun yana so a mik’o mishi wani abun, da sauri Daniel ya zaro wasu takardu da international passport ya mik’o mishi.

Ajiyar zuciya ya sauk’e, kafin yace “Abba, d’azu da Dahiru ya kira Yayanku muna tare!.
Jiya na bawa Yayan naka sak’o nace ya fad’a maka, ashe bai gaya maka ba, right?”
Bai jira jin amsar shi ba ya cigaba “I’m really disappointed in you, and bana so inyi punishing d’inka harshly which is why I’m doing this…
Take this!”
Yayi maganar yana mai mik’a mishi passport d’in hannun shi.
Jiki a mace Abba yasa hannu ya karb’a, passport d’inshi ne da wasu takardun da bai gama dubawa ya gano na menene ba muryar Mahaifin nashi tasa ya maida hankalinshi gareshi jin yana cewa
“Ga passport d’inka, nayi k’ok’ari wajen ganin na had’a har da na amaryar taka in yi muku tare, amman sai na fahimci ita d’in y’ar gidan talakawa ce bata tab’a fita koina ba, so wannan aikinkane yanzu zaka yishi, tunda kaika kwaso ta.
Na baka 5 hours ka bar k’asar nan! Bana son ganin ka…ba zan iya zama a country d’aya da kai ba.
Abba ko labari idan ka ji zanje k’asar da kake, to ka tabbatar ka bar wajen ko kuma duk yadda zaka yi to ka tabbata bamu had’u ba. I don’t think zan iya yafe maka
laifin da kayi min sannan bana son in yi punishing naka harshly kuma na san indai Ina ganin fuskarka ko kuma kana kusa dani to tabbas zan yi maka abunda ba zaka tab’a mantawa ba.
So, as you can see I’m doing my very best to stay calm!
All I want from u shine ‘wannan ya zama last time da idona zai ga naka!! You want freedom right? Kana so kayi abinda kakeso ka auri wadda kakeso ko?
Well, Abba ga freedom nan! I’m giving it to you….Idan ka kuskura muka had’u, ko kak’i barin k’asar nan, u pretty much know wat I’m capable of! Dan wallahi i promise sai nayi making life d’inka a living hell!!.

Kayi addua In iya yafe abinda kayi mini kafin In mutu, maybe I can forgive and call u back.”

Har ya juya zai fita, sai kuma ya dawo ya zo inda su Maryam suke ya tsaya, cikin kakkausar murya yace “Maryam!”
Maryam jikinta har tsuma yakeyi, cikin sake b’oyewa a bayan matar liman kamar zai daketa ne, tace
“Naa ‘aa mm.”
Cike da tsana yake kallonta kafin yace “D’a na kikeso ko?
A kanshi kika bar iyayenki kika gudo kika aure ko?
Well congratulations to you, da shigowa familyn MT!
But let me assure you! Wallahi karnukan family d’ina sai sun fiki daraja! Sannan ko bayan raina ban amince Y’ay’anki suyi bearing family name d’ina ba.
Kuma inaso ki sani, zan iya yafewa Abba kamar yadda na fad’a amman ke kam nida ke karki kuskura ki bari muga juna suma kuma Y’ay’anki haka, bana so su zo ko kusa da inda nake ma talkless of mu had’u da su.
Idan kika kiyaye wannan watak’ilan ki zauna lafiya, idan kuwa baki kiyaye ba to kinga mahaifinki da mahaifiyarki da wannan k’anwar taki, I’ll make sure na kulle su a prison d’in da ko kusa dashi baki isa zuwa ba ballantana ma kiyi tunanin fito dasu, this is my promise to you!!”
Yana gama fad’in haka ya bawa Daniel umarnin ‘ya kai Maryam da Abba suyi preparations d’in tafiya sannan ya ajjiye su a airport, within 5 hours!’. Yana gama fad’in haka ya juya ya nufi hanyar fita, yana mai yiwa Limamin alk’awarin dawowa idan ya samu lokacinshi, dan ba zai barshi haka ba wallahi!….

Kuka Maryam ta dinga yi kamar ranta zai fita.
Tsoro gaba d’aya duk ya rufeta!! Tayaya za a ce babu ita babu family d’in Mijinta waenda sune garkuwar y’ay’anta?? da wanne dangin y’ay’anta za suyi tutiya idan sun taso? dan ba a ado da dangi d’aya!
Daman Abba ya san haka mahaifinshi yake amman shine bai sanar mata ba?? Tukunnan ma taya za a fara tunanin barin ta k’asar nan har abada??
Dan in har lissafinta ya bata daidai ana nufin ita da Abban zasu tafi…….
Waennan al’amura da tunanin ne suka kuma hargitsa ta, ta dinga rusa kuka ko sauraronsu Abba da suke ta bata hak’uri bata yi…
Daniel ne ya d’an rankwafo kan Abba yayi gyaran murya sannan ya nuna mishi agogon hannunshi, harararshi Abban yayi sannan ya mik’e ya fita Daniel d’in yabi bayan shi suka hau shirye shirye gadan gadan.
Bai sha wahalar yi mata passport ba, daman yanada k’aramin hotonta daya cira a file tun suna makaranta, amman da aka zo kan visa ba k’aramin wahala ya sha ba, duk inda yaje ‘embassy’s d’in Kano’ sai ace visar gari dole sai mutum ya jira.
Dakyar ya samu Yayanshi ya kulashi dan shima duk ya tsorace kar Mahaifin nasu ya juyo kanshi..Nacin da Abban ya dinga yi masa ne yasa ya amsa wayar da cook d’in gidan yaketa rok’on shi ya karb’a, yana karb’a Abba ya kwararo mishi abubuwan da yake da buk’ata…..
Da kyar da taimakon sa da taimakon kuma wani baban Abokinsa Maryam ta samu visiting visar Madina, amman shima sai nan da 7 days jirgin zai tashi kuma a Lagos, gashi sauran 1 hour 5 hours d’in da aka bashi ya cika.
Da sauri ya shiga nema musu wani ticket d’in daga Kano zuwa Lagos. Aka yi sa’a kuwa ya samu da wuri, zai tashi in the next 20 minutes, a lokacin sauran 15 minutes time d’in da Mahaifinsa ya basu ya cika.

A gurguje suka samu suka k’araso gidan Limamin shi da Daniel wanda yake ta binshi a baya yana nuna mishi agogo duk bayan minti talatin, Abba ji yake kamar ya shek’e sa amman kuma sanin da yayi ba laifinshi bane shima saka shi akayi kuma bai isa ya hukuntashiba yasa kawai ya rabu da shi.

Yana shigowa a gurguje suka had’u da Limam suka nufi d’akin da Maryam take.
Ai anan kuwa ta birkice!! Ta dinga kuka tace “wallahi babu inda zata je, idan ma zata tafi tou sai taje taga su Shuwa tayi musu sallama sun saka mata albarka.”
Tabbas sun san ta fisu gaskiya ata koina amman zuwa unguwar su Shuwa ma kad’ai sai ya d’auki minti ashiri bare dawowa, nan kuwa suna kusa sosai da airport…
Daga Liman har Abba hadda ma matar Liman d’in duk sun rikice rok’on Maryam kawai suke suna lallab’ata suna mata nasiha akan tayi hak’uri ta bi mijinta su tafi watarana sa dawo…amman fur tak’i!!.

Daniel ne yayi knocking ya shigo, har Abba zai yi mishi masifa dan ya ishesa! Sai yaga ya mik’o mishi envelope.
Sai da yasa hannu ya karb’a sannan Daniel d’in yace “driver d’in Daddie ne ya kawo yanzun nan yace wai a baka.”
Jikin Abba har rawa yake yi haka yasa hannu ya zaro takardar ya fara karantawa…
“Sauran minti goma jirginku ya tashi, yanzu munzo wucewa na sake ganin motar Daniel a k’ofar gidan Liman, which means baka tafi ba and still kuna ma gidan, jirginku zai tashi in the next 10 minutes, I know maybe nan da 7 minutes zaku iya isa airport, which means zaku k’ara 2 minutes akan time d’ina….
Already daman d’azu mun tafi da motarka, tunda ni na siya maka!
Kayanka da credentials d’inka da Yahaya ya had’a maka suna boot d’in motar Daniel…
Ina umartarka da ka bawa Daniel atms d’inka da komai na kadara ya taho mini da su…
If u like ku ci gaba da wasting time, and I’ll not hasitate to keep punishing u.
Ina sane da duk wani single movement d’inka.”

Kawai gani sukayi Abba ya durk’usa a gaban Maryam ya kama hannayenta duka biyu ya fashe da kuka, cikin kukan yake rok’onta yana “Dan Allah dan Annabi Maryama ki tashi mu tafi yanzu shine abu mafi amfani, duk tirjiyarki a k’arshe tafiya zamu yi…. wannan b’ata lokacin da muke yi baki san abubuwan da kike janyo mini ba, zamu dawo idan nayi settling I promise!!!”
Kuka yake yi kamar k’aramin Yaro, hakan yasa Liman shima ya ci gaba da lallab’ata tareda yi mata zazzafar nasiha mai ratsa jiki….
Jikinta duk yayi sanyi hakan yasa tace “zata tafi amman sai yayi mata alk’awarin zasu dawo very soon, kuma hadda su Liman za aje a bawa su Shuwa hak’uri.”
Duk suka amince hakan yasa suka mik’e da sauri sukayi hanyar fita, su Liman suna ta binsu da fatan alkhairi haka suka shiga mota suka tafi, sai sauri sukeyi, dan tuni lokaci yayi.! Allah ne ma ya taimakemusu aka d’an samu delay da tuni sunyi missing flight d’insu.
A gurguje ya had’a duk wani abun da Granpa yace ya bada.
Ya bawa Daniel d’in yace “ya bashi” sannan suka hau layi.
Sai da Daniel ya tabbatar yaga tashin girjinsu tukunna ya juya ya koma mota ya nufi gida
da tunani barkatai a ransa…..
SHARE PLS.

BULAMA ✍️

So da Buri
Free Book
17

Hakanan yana ji yana gani ya bayar da komai ya d’auki d’an briefcase d’inshi na credentials d’insa suka wuce Lagos.

Yaso su zauna a Lagos d’in har zuwa lokacin da Mahaifin nasa zai d’an sauk’o daga fushin da yayi.
Amman ranar da suka cika kwana biyar a garin! Granpa yayi musu chune! Y’an sanda suka zo suka tafi dasu…aka dinga bincikensu akan laifin da basu san dashi ba.
Kwanan su d’aya a station daga k’arshe wani police ya kawowa Abba takarda, yana dubawa yaga sak’on Granpa d’in ne ‘shine ya saka aka kamasu! As a punishment na 5 days d’in da suka k’ara, sannan he should either choose barin k’asar ko kuma zaman station dan zai saka suyi ta zama a wajen ne har abada ba tare da sun san laifin su ba.’
A take Abba ya zab’i tafiya, yayi signing inda aka nuna mishi dan Maryam har ta fara zazzab’i sakamokon sauro da wahalar wajen, shi kansa da yake Namiji daurewa kawai yake yi.
Suna fitowa ya mayar da ita masauk’in su ya fita y’ar buga buga dan kud’in da Yaya ya saka mishi a gaban suitecase d’in credentials d’insa sun k’are tass.
Bai wani samu kud’i sosai ba har dare haka ya dawo, gashi jirginsu 4:00am zai tashi.
Tunda ya tashi Maryam yace “ta fara shiri” take faman yi mishi kukan data mayar sanaarta tun ranar da aka d’aura musu aure.
A haka suka isa airport har ana d’an kallonsu…

Bayan y’an bincike…jirginsu ya d’aga zuwa k’asa mai tsarki.

Tun kukan Maryam yana iya fita har muryarta tazo ta dishashe, ji take yi kamar ta rufe Abba da duka!!! Duk shine ya ja mata shiyasa duk faman aikin lallashin ta da yake ta yi ta yi banza dashi ta k’i kulashi,
shi kam babu abunda yake yi sai aikin lallashi dukda kuwa
shima kamar ya fashe da kukan haka yake ji, saboda in suka sauk’a bai ma san ta ina zai fara ba, duk wani means na kud’i an kwace a hannunshi!
Gashi bai san tayaya zai samu aiki ba, ga iyali a tare dashi…tabbas ya zame masa dole ya tashi ya nemi abunyi
Suturarsu kanta kwata kwata set bibbiyu ne dasu, daga waenda suka baro Kano dasu a jikinsu sai waenda ya saya musu set d’aya d’aya a Lagos…..
Yana cikin wannan tunanin jirgin su ya sauk’a a garin Madina.

Maryam ya d’an tab’a a hankali wadda bacci ya fara kwasa.
A hankali ta bud’e idanuwanta da suka kumbura suka k’ank’ance suka yi jaaa.
“Mun iso.”
Shine abunda yace mata sannan ya fara k’ok’arin mik’ewa itama ya kama hannunta ya mik’ar da ita suka bi ayarin y’an jirgin da suke ta sauk’a, suma suka sauk’a.
Bayan an gama sauk’a mutane suka nufi wajen d’aukar kayansu..
Su kuwa su Abba suite case d’inshi ce kawai garesu,
tana da d’an girma shiyasa ta cinye har ragowan kayansu set d’aya d’aya.

Waje ya samu ya zauna ya fara duba suitecase d’in, bayan sun fito, kamar yana neman wani abu.
Allah yaso su kuwa akwai y’an chanji a ciki…so da yawa idan Yayanshi zai zo yakan biyoshi su taho tare yayi masa rakiya dan yana son garin, ya tuna lokacin daya dawo da kud’in yana taso ya chanja su bai samu time ba haka ya hak’ura ya d’aga k’asan suitecase d’in credentials d’in nashi ya saka.
Shiyasa yanzu da wannan ranar ta fad’o mishi a rai ya duk’ufa yana dubawa had’e da adduar Allah yasa har yanzu kud’in suna nan, ai kuwa ya tsince su yadda ya barsu.
Abun hawa ya fara nema musu, da kyar kuwa ya samu, daganan yace “a kaisu wani d’an hotel haka mai d’an saffa saffa.”
Suna zuwa ya kama d’aki d’aya. Sai da ya kai Maryam d’akin yace mata “tayi wanka ta huta” tukunna ya fito domin ya siyo abinci, acikin hotel d’in ya siyo abincin, sannan bai yarda ya bar wajen ba sai da ya samu aiki a restaurant d’in cikin hotel d’in, bayan ya nuna musu takardunsa kuma sunji yana jin larabci suka bashi aikin ‘waiter’!! Bai wani damu da k’ask’ancin aikin ba ya amsa yana mai farin ciki.
Yana dawowa da abincin ya tarar da Maryam a yadda ya barta tana kuka, hawaye ne ke fita kawai amman ba sauti tsabar yadda muryarta ta disashe.
Da sauri ya k’araso ya d’agata ya zaunar sannan ya ci gaba da aikin lallashi.
Da kyar ta yadda taci abinci
sannan ta shiga tayi wanka ta fito.
Shima mik’ewa yayi yaje yayo wankan sannan ya fito ya tarar da ita a zaune ta mayar da kayanta.
A hankali ba tareda ta kalle shi ba tace “Inane gabas? Zanyi sallah.”
Shima kayan nashi ya maida sannan yaje ya d’aga window ya hau duba garin
Alk’iblar masallacin da ya hango ya duba kafin ya zo ya nuna mata.

D’ankwalinta ta shimfid’a tayi sallar walha….

Yana zaune ya baza takardu yana dubawa dan neman mafita..ta ida sallarta ta nemi waje ta kwanta yana ta duba tarkadun shi da had’a su waje d’aya a haka barci ya saceta
don tunda suka je station basu samu nutsuwa ba.

Kiran sallar azahar ne ya tayar da ita.
Tana juyawa taga Abba shima yana baccin a inda ta barshi da takardun shi a baje da alamun ma a zaune yayi baccin wahalan…
Zuciya da abunda take so sai taji gaba d’aya ya bata tausayi.
A hankali ta k’arasa taje ta durk’usa a gabanshi tana k’are mishi kallo, kana ganin yanayin fuskarshi ka san ba dad’in baccin yakeji ba kawai dai yana yinsa ne.

Hannu ta saka ta d’an tab’a gefen inda yake jingine.
A hankali ya bud’e idanuwanshi, ganin ya farka yasa da sauri ta mik’e tana cewa “ka tashi kayi sallah”daga haka ta fad’a toilet ta yo alwallah.
Tana fitowa shima ya shiga
bai fito ba saida ya sake yin wanka.
A zaune ya tadda ita tayi shiru da alamun tunani take yi.
A gurguje ya shirya, ya tada sallah.
Bayan ya idar da sallah ne ya zo ya kwashe ragowar chanjin da suka yi sannan ya juya ya fita.
Bai wani dad’e ba ya dawo da abinci da y’ar rigar da suka bashi da hula.
A hankali ya zo ya zauna a kusa da ita.
Da farko kamar ba zata yi mishi magana ba sai kuma tace “Ina wuni.”
Amsawa yayi, sannan yace
“Ga abinci nan, d’azu naso gaya miki zan fara yi musu aiki a restaurant saboda kinga muna buk’atar kud’i a hannunmu, amman sai naga kinata kuka.
Zan d’an fita yanzu In k’aro mana kaya ko set bibbiyu ne kafin muga abinda Allah zai yi.
Zan fara neman wani aikin.
Kiyi hak’uri yanzu muji da yadda zamu yi surviving…
In sha after that immediately zan san yadda zan yi ko ke kad’ai ce kije ki wajen su Abba
kinji ko?”

A hankali ta d’aga mishi kai
sannan ta mik’e. Gani tayi shima ya mik’e sannan ya kamo hannayenta.
D’agowa tayi ta kalleshi taga shima itam yake kallo, a hankali yace “That’s all?
Babu irin adduar ‘Allah ya bada sa’a dinnan? Maryama, kuma
still har yanzu ranki a b’ace yake.”

“Allah ya bada sa’a.”
tace, sannan tayi niyyar matsawa amman furr! Ya k’i ya tare hanya, shifa sai tayi murmushi kuma tayi mishi addua tukunna zai fita.
Hakanan ba yadda ta iya ta k’ak’alo murmushi tayi sannan ta yi mishi addu’ar.
A hankali yasa hannu yayi hugging d’inta yafi 5 minutes
tukunna ya sauk’e ajiyar zuciya yace “Ameen.” Sannan ya juya ya fita.

Sai yamma tukunna ya dawo ya kawo mata abinci, kana ganinshi a gajiye yake dan restaurant d’in ana cika sosai kasancewar a hanyar airport d’in yake kuma shi kad’ai ne sannan daman basuda waiter sai shi kad’ai.
Sallah kawai yayi ya d’an ci abincin kad’an sannan yace “mata zai koma.”
Gaba d’aya se sai tausayinshi ya sake kamata.
Ganin ya tsaya yasa tace “a dawo lafiya.”
“Ameen” yace, kafin yace
“Murmushin fa??.”
Wannan karon ba k’ak’alo shi tayi ba, ji tayi kawai ya sub’uce mata.

Sai k’arfe goma sha d’aya na dare ya dawo. Kamar yadda yayi alk’awari da kaya ya taho musu dashi..
AlQurani mai kyau irin mai pieces d’innan izu sittin amman duk izu biyar a rabe ya siyo, da inner wears d’inta set biyu, sai abaya da hijab.
Shi kuma ya siyawa kanshi gajeran wando da jallabiya
Sai lotion, brush da toothpaste sponge da soap na wanka da na wanki da omo.

Gaisuwarta ta sannu da zuwan da take yi mishi ya amsa,
kasancewar a gajiye yake sai da ya d’an huta tukunnan
yake gaya mata
“Ya tambayi mai restaurant d’in nasu ita ta had’a shi da ogan su kai hotel d’in, so ya tambayeshi ko zasu iya zama a d’akin sai a dinga cira a cikin albashin shi?
Mutumin ya yarda amman kasancewar idan an cira zai yiwa albashin gib’i sosai yasa aka d’auke room service, dai an basu d’akin ne amman su za suyi komai…”

Abinci suka fara ci yana ta bata labari, yau kam ta d’an sake ba laifi, haka nan suka sha hirarsu sosai.
Sai da suka gama tace zata yi wanka daga nan ta wanke toilet, so tana so ya bata omo, amman k’iri k’iri yace “taje tayi wankan ta, idan ya shiga shi zai wanke toilet d’in har kayan data cire ma ta barsu a ciki zai wanke!.”
Babu yadda bata yi dashi ba amma ya k’i, hakanan ta je tayi wankan, kamar ya sani bayan 10 minutes ya mik’e ya shiga aikuwa ya kama ta tana shirin wanke kayan, sai da yayi da gaske tukunna ta barshi ta fito har inner wears d’inta saida ya had’a ya karb’a, ba yadda ta iya.
Tukunna yayi wanka ya wanke toilet ya wanke musu kayansu.
Tana zaune tana karatun Al’Qur’ani, ya fito. Sai da ya shirya sannan yazo kusa da ita ya zauna ya kamo hannunta yasa a cikin nashi. Bata kulashi ba sai da ta kai aya sannnan ta juyo bayan ta ajjiye Quranin da d’ayan hannun damanta a gefe,tace
“Abba amman kana ganin Mahaifin ka zai hak’ura?? sannan maiyasa baka gaya min haka yake ba?
Taya za’ace Yaranka ba zasu shiga familyn Baban su ba? A Ina aka tab’a yin haka?”

Ajiyar zuciya ya sauk’e sannan yace “Maryam, i don’t want to lie to you or give u any false hope! Maganar gaskiya ba lalle ya hak’ura ba!.

Ai wannan abunda yayi fa bai ma yi komai ba. Idan na fara baki labarin halinsa, ba lalle ki yadda da wasu abubuwan da yake yi ba.
Kuma kinga a case d’innan fa laifi nane, nine na tab’o shi
To be sincere I was expecting more than this from him.”

B’ata rai tayi sannan ta fara k’ok’arin zare hannunta a cikin nashi kafin tace “yanzu ka kyauta mini kenan??? Abba ba wai fata nake yi ba amman ba a san gawar fari ba!! Yaran mu nake dubawa anan…”

Rik’e hannunta yayi sannan yace “Maryam idan akwai abinda zan iya rantse miki akai shine ‘ko bayan taina na san sai dai Yaya da mahaifin mu su raba gari, suyi baram baram indai akan Y’ay’a nane, dan Yaya ba zai tab’a k’in kula Y’ay’ana ba, sannan ga d’ayan Yayan nawa shima na san ba zai yi abandoning Y’ay’ana ba ko da ina raye talkless of ba na raye’.
Kawai dai one thing is for sure, na san zan had’a rigima ne, da kuma fad’an da ni kaina ba zan iya kuncewa ba, because..definitely mahaifinmu zai so hana brothers d’ina kulani su kuma ba za suyi mishi biyayya ba when it comes to that!
Bar ganin Yaya ya k’i kulamu yanzu, I assure u ba za ayi 3 months ba zakiga ya zo ya fara bibiyata.”

With surprise Maryam take kallon shi kafin tace
“Amman ka san da duk wannan mai yasa kayi taking risk d’in to? Why do you want to tear apart your own family??.”

Murmushi yayi sannan ya matso kusa da ita sosai yayi cupping face d’inta a cikin tafukan hannayensa sannan yayi mata light peck a forehead d’inta… a hankali da idanunsa a lumshe ya sauk’e ajiyar zuciya kafin yace mata
“This is worth it!”
Tana k’ok’arin janye face d’inta yayi mata wani a kan hanci a hankali ya sake furta
“And this”
Bai jira d’aukar lokaci ba dan ya fahimci so take ta kwace fuskan nata yayi mata a lips d’inta yace
“And this….”

Daga nan kuma Maryam ta ji Abba kamar ba shi ba! Duk wani k’ok’arin ta na ganin ta karb’i kanta kasawa tayi, bata tashi sanin abun nashi na gaske bane ba saida taji azaba na shirin d’auke ranta.
A b’angaren Abba kuwa yaso suyi sallah kafin komai amman duk yadda ya k’ok’arta hana kanshi sai ya gagara, domin kuwa tun a karan farko shikam ya manta hanyar garinsu ma balle azo kan maganar hana kai!
Shiyasa duk kalar kuka da magiyar Maryam d’in tashi ya zamana ba jinta yayi ba......

Ahankali yake shafa kanta yanata murmushi kafin ya janyota jikinshi ya rungume a haka bacci ya kwashesu, ita baccinta na wahala ne shi kuwa na cikar farin ciki da nutsuwa ne.

Kiran sallar farko ya tada shi, jikinta yaji yayi zafi da alamar zazzab’i.
Wanka ya fara yi ya taimaka mata itama tayi, sannan yaje ya siyo musu abinci da maganin zazzab’in ta! Dariya taso ta bashi dan kwata kwata tak’i kallonshi gashi sai kumbura baki take yi ita ala dole fushi take dashi amman kuma komai idan zata yi sai da taimakon shi.

Sai da ya tabbata komai ya kimtsu sannan bata buk’atar komai tukunna ya fita aiki,
sai dare ya dawo….yau ma kamar jiya Abba bai kauda kai ba…
Maryam tun tana k’i harta daina…..

Idan ta ce Abba yana son ta, to tama ragewa soyayyar da yake yi mata a zamansu daraja, dan kalmar so tayi kad’an wajen fasaltawa.
Duk wani abu na kulawa da k’auna shi yake gwada mata,
ko tsinke baya bari ta d’auka saidai In a bayan idonshi ko In baya nan tayi sauri tayi, ta yadda idan ya dawo aikin ba zai zama dayawa ba.

Shi zai yi shara yayi moping ya wanke toilet yayi wanki, sannan duk abinda tace tanaso sai ya nemo mata.
Zaman nasu gwanin ban sha awa, yadda yake kyautata mata itama haka take yi mishi biyayya…..

Idan aga Maryam indai ba bakinta ta bud’e tayi maka Hausa ba to bazaka tab’a cewa ba balarabiya bace ba…tayi k’iba ta k’ara fari tayi freshi da kyau abinta.

A hankali ya siya musu d’an electric gas da d’an kayan abinci suka ajjiye a d’akin, wai ko da wani lokacin tana sha’awar yin girkin gida, amman kuma the
funny thing is ‘ya hanata yin girkin’, kasancewar a restaurant yake yanata koyan girki kala kala,idan tace bana sayarwa take son ci ba to yana dawowa break ko kafin ya fita ko bayan ya dawo a aiki zai zage ya girka mata!.
Zaman lafiya da k’aunar juna kankat, shine zaman da Maryam da Abba suke yi a Madina.

Abu d’aya yake damun Abba rashin tsayayyen aiki, ya kai
takardun shi wajaje mabanbanta amman bar yau shiru, bai san daliliba.

A kwana a tashi har suka yi 4 months.
Yau ma kamar kullum yana wajen aiki, wasu bak’i suka zo Larabawa, da alamun manya ne dan yaga yadda managern nasu yake ta rawar kai, ya jere abinci wajen kala goma yace duk a fitar musu…
Tray d’in farko ya fara d’auka ya nufi table d’in da akace suna nan…
Tun kafin ya k’araso yaga d’ayan ya kafe shi da ido, yana k’arasowa ya d’an gaidasu kafin ya ajjiye ya fara niyyar juyawa dan ya d’auko musu wani yaji ance
“Ya’akub!”
Da sauri ya juya jin wannan balarabe ya kira sunan shi rad’au.
Suna had’a ido dashi ya tuna shi Abokin Yayansa ne sosai dan yana yawan zuwa gidansu na nan idan sunzo.
Sake maimaita sunan balaraben yayi, da d’an murmushi Abba ya amsa sannan ya sake gaishe shi.
Amsawa yayi sannan da mamaki yace mishi “aiki yake yi anan!”
D’aga mishi kai kawai Abba yayi.
D’an jimm!! balaraben yayi kafin ya hau bawa Abokanan tafiyartasa labarin waye Abba.
Da mamakinsu suma suka dinga kallonshi kasancewar duk sun san Yahaya MT.
Wannan balaraben yake gaya musu irin tarin alkhairan da Yahayan yayi mishi
kafin ya juyo kan Ya’akub d’in yace masa “bai yi karatu bane? Maiyasa yake aiki a matsayin waiter?”
Da murmushi yace “yazo k’asar ne yayi sabon aure kuma bai san kowa ba shiyasa.”
Da d’an fad’a mutumin ya fara cewa “ya za a yi suna garin nan amma Yahaya ya bar k’anin shi haka? ai ko shi waya d’aya kawai zai yi a dauki k’anin shi a aiki, bara yana komawa gida zai kirashi…”

Abba bai b’oye musu komai ba yace “Ya d’an samu matsala da Mahaifinsu ne, so idan Yahayan ya taimaka mishi, zai iya involving nashi a case d’in shiyasa.”
Cike da gamsuwa balaraben yace “Ina credentials d’inshi? ya kwaso ya zo su tafi yanzu ba sai anjima ba.”
Cike da farin ciki ya nufi d’aki, yana murna, ya isa d’akinsu.
Yana shiga ya tarar Maryam tana bacci, yaso ya tashe ta ya fad’a mata amman kawai sai ya barta ya kwashi abubuwan da yake buk’ata ya fita a hankali gudun kar ya tada ita.

Yana zuwa ya tarar har sun mik’e abincin kad’an suka d’an cachchalkala shi kawai suke jira, shiyasa yana zuwa suka wuce.

Bai sha wahala ba kasancewar companyn Baban d’aya daga cikin mutanen da Yayan nashi ya tab’a taimakawa ne, da Mutumin da Baban nasa ne suka yi mishi interview, Allah sarki mutumin da alama yaji dad’in abinda Yahaya yayi mishi dan a wajen ma yanata gayawa Mahaifinshi ai k’anin Yahaya ne.
A take ba b’ata lokaci bayan an gama interview aka d’auke shi aiki. Har da ardrobe allowance aka had’a mishi.
Sai wajen 5 tukunna ya dawo, da mamaki Maryam take kallonshi yadda ya shigo cike da fara’a..yana shigowa yayi hugging d’inta ya d’agata sama yana juyawa.
Sai da ya ajjiyeta yana dariya ya shiga bata labari, ba k’aramin godiya ga Allah da farin cikin tayi ba, ahankali ya sake hugging d’inta yace
“Maryam ke good luck ce, kiga fa a yadda muka shigo garin nan amman ko wata biyar bamu yi ba yau nine harda office, sannan ko daidai da rana d’aya bamu tagaiyyaraba.”

Cikin murmushi itama ta sa hannu ta rungume shi, suna a haka sukaji knocking!! Mik’ewa yayi yaje ya bud’e aikuwa
yana bud’ewa suka yi ido biyu da manager, ko gaisuwarshi bai amsaba ya hau sirfa mishi bala’i yana cewa “Ya bar bak’i d’azu bai k’arasa kai abinciba sai cook d’inne ya kai da kanshi, saboda tsabar yana so ya nuna hotel d’in bashida tsari ko?
Sannan tun d’azu aketa neman shi baya nan, ina yaje?”

Bai b’oyewa manager d’in ba nan yake gaya mishi “ai aiki ya samu!”.
A tunanin Abba managern zai taya shi farin ciki amman sai yaga sab’anin haka
dan daga k’arshema cewa yayi ya kwashe kayanshi ya nemi waje tunda ya samu aiki, ai daman ba k’aramin discount suka yi mishi ba, wajen 49%! Dan haka indai yana son yaci gaba da zama to saidai ya ajjiye wanchan aikin yaci gaba da yi musu aiki, yabashi 30 minutes yaje yayi making up mind d’inshi.”
Yana gama fad’an haka ya juya ya fita.

Tuni Abba ya yanke shawarar barin wajen ya kama haya tunda da d’an kud’i a hannunshi, amman dai sai da ya sake neman shawarar Maryam wadda itama tunaninta ya zo daidai da nashin. Dan haka a mintunan da basu gaza 20 ba sukayi parking komai nasu suka fito.
Managern yana ganinsu da kaya ya fahimci decision d’in Abba na barin wajen nasu ne kenan, dan haka ya kuma b’ata rai ko godiyar da Abba yake yi mishi bai amsaba. Shi dai Abba bai damu ba yayi mishi sallama suka nufi cikin kitchen d’in dan ko ba komai ba zai manta da manager ba, kuma idan an d’an kwana biyu in sha Allah zai d’an dinga lek’owa suna gaisawa.
A kitchen d’in daman sun tab’a hirar apartments masu sauk’i da cook d’in da suje shiri dan haka ya tambayeshi “inane yake ganin zai fi dacewa ya zauna?”
Cike da farin ciki cook d’in yace “apartment d’in da yake zaune akwai security a estate d’in!
Ya bashi 3 minutes ya chanja kayanshi ya zo suje sai ya rakashi har gidan mai estate d’in, daman Neighbour d’inshi bai dad’e da tashi ba sai ya karb’i gurin.”
Cook d’in yanata murna da taya Abba murnar samun sabon aiki, a haka suka d’unguma, saida suka biya apartment d’in cook d’in, 2 bedroom da parlour da kitchen, anan suka ajjiye kayansu, sannan shi da Abba suka tafi gidan mutumin, aka bar Maryam da matarshi mai mutunci tanata janta a jiki Yaransu uku.

Kamar yadda cook d’in yaso kuwa, apartment d’in gefen su aka bawa Abba, bayan ya biya kud’i ya cike duk wani abun buk’ata.
Sai wajen 1 suka gama settling…har moping sai da mutumin nan da family d’inshi suka tayasu sannan suka yi musu sallama suka tafi nasu gidan.
Washegari da safe Abba ya nufi wajen aiki.

Da kyar Abba ya yarda Maryam ta fara aikin kitchen, shima sai da ta saka mishi kuka, saboda ba fita take yi ba sannan ba aikin da take yi, shiyasa gaba d’aya kafafunta har wani kumbura suka yi.
Sai da yaga dai rashin exercise d’in ka iya yi mata illa tukunna ya yarda, amman dai shara wannaan aikinsa ne idan ya dawo, wankin toilet kuma kafin ya tafi office da safe tare sukeyi idan sun shiga wanka,
wanki kuwa yanzu sunada washing machine abunsu............

Kano, Nigeria.
5months ago…
Da mugun gudu Sadiya ta shiga cikin gidansu Maryam bayan taga tashin motar Abba, tana shiga takaici ya rufeta ganin babu kowa. Gidansu ta koma ta sanarwa Baaba Laraba halin da ake ciki dan ta d’an jiyo maganar Maryam d’in da Abba sama sama…Baaba Laraba kuwa sarkin y’an tsurku nan ta zari mayafi tayi waje…Gidan aminiyarta dillaliya ta fara lek’awa ta fesa mata.
…Wannan gayawa wannan, kafin awa d’aya labari ya baza unguwa ‘Maryam ta gudu da saurayinta wanda aka kamasu a makaranta suna lalata!’.
Har majalisar maza zancen da akeyi kenan, magana har ta kai kunnen tsofaffin unguwa ana ta cewa “Y’ar gidan mai unguwa kuma Limami ta gudu ta bi saurayinta!’.
Ana cikin haka Madu da su Shuwa suka dawo, har da Ya Usman wanda jikinshi ya d’anyi sauk’i dan a asibitin a gabanshi aka yanke shawarar aura mishi Maryam da zarar an dawo gida!.
Duk da sun san ba a neman aure cikin aure amman zasu je su yiwa Yayan Abba bayani su nemi alfarma a wajensu.
Baaba Talatu ma da farin cikin ta ta dawo.

Tun kafin su shigar da mota gida K’asimu ya tsayar da motar da yaga Madu da Bashir a ciki, parking Madu yayi a gefe dan ya bawa motar da Ya Jamilu yake tuk’awa damar wucewa, bayan sun fito, ko gaisawa K’asimu bai bari sun yi ba ga y’an unguwa da ganinsu yasa suka k’araso suma domin suji k’arin bayani….ba tare da tauna zance ko lafazi mai kwantar da hankali ba K’asimu ya shiga koro musu bayani kamar a gabanshi aka yi, har da cewa “sai da Maryam da Abban suka gama rungume rungume ma tun kafin su shiga motar su gudu.”
Ba tare da Madu ya kula kowa ba ya kamo hannun Baba Bashir suka nufi cikin gidan Baba Bashir d’in, tun kafin su k’arasa shiga ya fara jiyo kukan Shuwa, suna shiga tsakar gidan ciki suka tarar da Baabaa laraba da dillaliya suna ta kora mata
bayani tana kuka!.
Ya Jamilu ne yace “dan Allah ya isa haka!!”
Sannan ya cewa su Sadiya “an gode, ku je, za muji da lamarin!.”

Suna fita kamar jira Shuwa take yi ta mik’e ta fara yiwa Madu bala’i kamar ba Mijinta ba, gaba d’aya laifin ta d’aurashi a kansa, a cewarta “Ai shi ya shagwab’a Maryam d’in ,ba dan shi ba da duk haka bata faru ba!
Sannan saboda rashin lissafi yaje ya bawa Yaron da bai gama sani ba Y’arsu, gashi yanzu ya gudu da ita!! Wannan wanne irin abin kunya ne, da wanne ido zata kalli jama’a??? Mai zata ce wa mutane?.
A yanzu haka Innaa tana kasuwa taje siyowa Maryam kayan d’aki! Shin ta Ina zata fara yi mata bayani idan ta dawo? Mai zata ce mata???”
kuka take kamar ranta zai fita tana cewa “Madu ya cuceta duk shi ya jawo mata.”

Baba Bashir ne yace “suje gida su duba koina, a dudduba sosai.” Dan shi bai gama yarda da maganar su Sadiya ba.........

BULAMA ✍️

So da Buri
Free Book
18

Babu inda ba a duba ba, amman babu Maryam babu alamar ta, gaba d’aya hankalin kowa a tashe yake, tunba ma da Innaa ta dawo daga kasuwa nik’i nik’i da kayan d’aki ba!.
Babu kalar zagin da bata yiwa Madu ba, Mallan shima yana k’arasowa ya iske mummunan labari.
Har dare basu zauna ba domin shi Madu ya dage akan ‘bai yarda Maryam guduwa tayi ba!’. Sune har police station
da daddare bayan sallar Isha……..da kyar suka iya cin abinci tun safe…..

Suna zaune a gidan Madun, Inna tana ta yada magana tana cewa “Madu ya janyo musu abun kunya! Itakam Allah ma yaso ta tunda idan aka bi tsattso ba a jikinta ya fito ba!! Kuma kowa ya san Shuwanta bata da laifi…”waye waye….
Har sai da taga ran mallan ya b’aci ya fara yi mata bala’i shima, tukunna tayi shiru.

Sallamar da aka yi da Madu ce ta katse mata guna gunin da take yi akan ‘itafa shiyasa tun farko bata so auren Shuwa da Madun ba’…..

Cikin mutuwar jiki Madu ya mik’e Baba Bashir yana binshi suka fita tare domin amsa kiran da ake yi mishi a waje!.
Suna fita suka tarar da dattawan unguwar, da sauri Madu ya k’arasa ya shiga basu hannu yana tambayar su “ko lafiya??” Dan shi a tunanin sa anga Maryam ne. Amma sab’anin hakan sai yaji wai ‘su meeting d’in gaggawa suka zo ayi saboda guduwar da y’arsa tayi, domin kuwa y’an unguwa sunce ya kamata a chanza sabon Limami.!’
Da mamaki yake kallon su, shi yana ta neman y’arsa, su kuma suna ta muk’ami! shiyasa ba tare da b’ata lokaci ba ya sanar musu da ‘ya sauk’a!’.

Amman hakan bai sanya sun barshi ba saida suka jashi akaje wajen meeting d’in.
Suna zuwa yaga dubban mutane, su kawai ake jira.!

Sai a wannan lokacin Madu ya san ba K’asimu kad’ai ba ne mak’iyinsa a layin!! Harda waenda yake ganinsu Abokanan sa duk cikinsu babu ya bi bayanshi..
Mutum uku ne kawai suka bi bayan Baba Bashir wanda Allah sarki dudda halin da Usman yake ciki bai sa ya juyawa Madun baya ba.

A lokacin mutanen gurin rabuwa sukayi kashi uku
Kashi na farko ‘sune su Baba Bashir su hud’u!’
Kashi na biyu ‘sun ce, y’ar Madu tayi laifi kuma shi ya janyo tunda shine ya shagwab’ata kuma baya son laifinta, amman bai kamata ace laifinta ya hau kanshiba, har a kai ga sauk’e shi ba’.
Kashi na uku kuwa (su K’asimu) sunce ‘ai laifinshi ne y’arsa ta gudu yawon karuwanci, tun farko shine ya yi mata lagalaga ya shagwab’ata, baya tsawatar mata duk abinda takeso baya hanata! Haka k’iri k’iri aka koreta a makaranta saboda abunda take yi amman ya rufe yak’i gayawa kowa idan an tambayeshi sai dai yace chanza mata makarantar yake son yi! Ai y’an unguwar da aka taso sama da shekaru ashirin da biyar tare ya kamata ace yanzu an zama d’aya dan haka su ba zasu dinga bin mutumin da yake ha’intarsu! Sallah ba. Su idan matsala ta taso a nasu gidajen tuni sunzo sun saki baki dan neman shawara da yarda da juna, amman shi y’arsa daya kamata ace tun kafin abun ya kai haka a taka burki yak’i yarda ya bada k’ofar yin hakan kuma shima ta bangarenshi bai yi ba, gashi yanzu ta tafi tabi saurayi.
Saboda haka..
Su baza su bi uban karuwa ba a masallaci har ma da unguwa.’
Harda cewa ‘ci yake yi da addini.’

Nan suka fara jidar kaya za suyi zanga zanga!
Dattawan unguwa na ganin haka suka hau basu hak’uri, sannan a take aka sake sauk’e Madu daga matsayinshi na mai unguwa ma gaba d’aya!
Dan a samu a zauna lafiya.

Babu kalmar da ta fi b’atawa Madu rai irin na kiran ‘Maryam karuwa da aka yi’
Shiyasa tun baya mayar musu har ya zo yafara mayar musu da martani, da kyar Baba Bashir ya janye sa suka bar wajen sukayi gida.
Dishi dishi kawai Madu yake gani, bai san ta Ina zai fara ba,
Da kyar ya iya kai kanshi gida.
Yana shiga Inna ta tisa shi a gaba da tata mitar, harda d’akko mayafinta tace ‘sai ya kaita gidan Yayan Abba! Ai sunce sun yi bincike dan haka ya kaita ko wajen wani nashi ne…’

Madu kuwa tun rana, suke ziryar zuwa ganin Alhaji Yahaya amman mai gadi yace musu wai yace ‘kar a barsu su shiga!!’. Shiyasa ma abun ya kuma dagule musu, amman dai basu fad’awa kowa ba suna so suyi settling ne a tsakaninsu,
shiyasa yanzu furucin Inna ya sake rikitashi!.

Ba yadda ya iya hakanan kawai ya sanya Jamilu ya jasu a mota suka nufi gidan, dan bashi da wani sauran energy.
Har da Inna da Mallan aka tafi,
suna zuwa, daidai motar Alhaji Yahaya tana k’arasowa.
Da sauri Madu ya fita ya isa gaban motar tashi ya tsaya!.
Alhaji Yahaya ganin an ritsa shi yasa kawai ya fito dan babu yadda zaiyi, a hankali ya k’arasa inda Madun yake wanda isar tashi tayi daidai da k’arasowar su Inna wajen.
Duk da rikicin da Madu yake a ciki hakan bai hanashi tsayawa suka gaisa da Alhaji Yahaya wanda ya kasa had’a ido dashi ba.
Inna ce ta matso sannan tace “Kai Yaro!! Ina kuka saka mjni jikata?? fito min da ita dan tun yanzu anan zan fara cin uwar ta kafin mu k’arasa gida.”
Ajiyar zuciya ya sauk’e sannan ya juyo ya fuskanci Madu ya fara kwararo masa bayanin duk abinda ya faru tun daga safiyar yau har kawo yanzu, hatta furucin da granpa ya yiwa Maryam akanshi da Shuwa da Bilkisu duk bai b’oye ba. Sannan ya k’ara da cewa
“Shima dalilin da yasa, yaketa dudging karsu had’u shine ‘mahaifinsu yace indai ya yarda ya sauraresu to ranshi sai yayi mugun b’aci, kuma sai ya kulle zuri’ar su Madu gaba d’ayansu!’.”
Yace “Mahaifin nasu yace ‘babu su babu duk wani abunda ya shafi Maryam da Abba’.”
Ajiyar zuciya ya sauk’e sannan yace “A tunanina zamu iya shawo kanshi, amman ranar da nazo gidan ka bayan mun koma naje na sameshi, b’acin ran dana gani a fuskar shi tabbas yayi matuk’ar tsoratani, shiyasa na cewa Abba ya hak’ura! Amman Yaran zamani kaga abunda suka je sukayi…
Ni ban san ta Ina zan fara baka hak’uri ba, amman yanzu dai Ina rok’on ka da kuyi saurin barin nan, mahaifin mu yana da c i ds da yawa especially ma yanzu da case d’innan yake going! Idan yaji labarin na ganku akwai babbar matsala.”
Yana gama fad’in haka yayi saurin komawa cikin motarshi ya danna horn mai gadi ya bud’e mishi ya shige ciki da gudu.

Da kyar Baba Bashir da Ya Jamilu suka ja Madu suka saka shi a mota, dan daskare musu yayi a wajen kwata kwata yak’i motsi.
Duk tsauri da k’ok’arin Madu sai da hawaye ya zubo ta idonsa…..
Yanzu wannan itace kalar rayuwar da Maryam d’insa zata yi? Da irin wannan mutumin a matsayin suriki?? Wanda d’an cikinsa ma daya
haifa bai sarara wa ba ballantana ita karan kad’a miya!! Gashi k’iri k’iri ya nuna ya tsane ta!
Tabbas Maryam guduwa tayi amman aure tayi! Abu d’aya daya sani shine idan zai had’iyi AlQurani yana rantsuwa yana fad’awa mutane Maryam aure tayi babu wanda zai yarda.

He is very disappointed in Maryam! Sam bai tab’a tunanin zata iya aikata haka ba!
Bai ankaraba yaji fuskarshi ta jik’e sharkaf da hawaye!!! Baba Bashir ma tausayinshi ne yasa ya share tashi kwallar da yake ta k’ok’arin b’oyewa saboda yanaso nunawa Madun kwarin gwiwa.

Inna ma duk surutunta tayi shiruuuu! Kamar ruwa ya cinyeta, tabbas ta san Maryam bata kyauta ba, amman ko da irin wannan surikin aka barta hukuncinta yama yi yawa.
Haka Mallan shima da Ya Jamilu suma duk sun yi shiru….motar shiru baka jin sautin komai sai na sauk’ar ajiyar zuciyar Madu.
A haka suka k’araso, suna
shiga suka tarar dasu Baaba Talatu sunyi cirko cirko, nan suka hau tambayarsu, Innaa ce ta fara labarta musu……

Salatin da Shuwa tasa tare da kuka a lokaci daya ne ya juyo da hankalinsu kanta, aikuwa da gudu suka k’araso , sakamokon ganin Madu a k’asa wanwar kamar babu rai a tare da shi…
A take su Ya Jamilu suka kinkimeshi aka saka a mota
suka nufi asibiti dukkan su. Sai da Likitoci sukayi da gaske tukunna suka samu numfashin sa ya daidaita…
Bai farka ba sai bayan kwana hud’u amma ya samu stroke mai k’arfi dan hatta bakinshi da hancinshi sun koma b’angare daya a fuskarshi.
Idan ka ganshi abun tausayi dole kayi kuka, Likitocin ne suka yi ta basu kwarin guiwa akan zai dawo daidai da yardar Allah da taimokon therapy da excercise d’in da za’a d’aurashi akai.
A hankali ahankali zai dinga samun sauk’i in sha Allah.

Hakan kuwa akayi dan jikin nashi da kad’an kad’an ya fara gyaruwa…

Ya Usman kuwa shaye shaye ya fara gadan gadan babu kama hannun Yaro, cikin wata uku ya lalace gaba d’aya, tun iyayen basu fahimta ba har suka gane, Ya Usman wanda a daa yake fari tass yanzu kam sai ka k’ura ido tukunna zaka iya tantance hasken fatar tashi, dan sai dai a kirashi da chocolate colour, duk ya yamushe ya fige ya rame over!!! Da aka yi k’ok’arin hanashi sai ya nemi haukacewa, dan basu saniba ashe abun ya shiga jikinshi sosai, idan yazo sha ashe shi over dose ma yake yi!
Shiyasa yanzu abun yake neman tab’a kwakwalwasa, ko zuwa kayi kusa dashi idan bakayi masa ba sai dai kaji duka!! Wannan dalili ya sanya kowa yake tsoron rab’arsa, Sadiya! Kad’ai ce take iya zuwa inda yake, duk da kuwa itama d’in idan taje sai ya mareta ko yayi mata duka amman bata gajiya….ita zata je ta kai mishi abinci ta share mishi d’aki ta wanke mishi band’aki!. Tun Laraba da K’asimu suna hanata suna zaginta har suka daina badan suna so ba sai dan rashin kunyar da take zuba musu a duk lokacin da suka so hanatan kuma ba yadda za suyi da ita.

Watan Madu hud’u yana fama, da ikon Allah a wata na biyar ya warke dama anata samun cigaba a hankali a hankali. Bayan ya dawo gida hankalinshi yayi matuk’ar tashi da halin da yaga Usman shiyasa ya duk’ufa ya dinga yi mishi addu’o’i ta tofi, a hankali a hankali kafin wata d’aya shima Allah ya bashi lafiya amman dai kana ganinshi ka san yana cikin damuwa saboda lokuta da dama ma idan ka shiga sai dai ka tarar dashi yana kuka…
D’agawa K’asimu hankali da Sadiya tayi ne yasa ya taso ya zo wajen su Madu akan maganar ta da Usman d’in.
Da ‘to’ kawai suka bishi amman ko suna hauka baza su
bari su had’a Jini da K’asimu ba….dan a lokacin da Al’Amarin Maryam ya faru shi yafi kowa zak’ewa, kusan shi ya yayata maganar ma har kowa yaji, kuma ya tsaya tsayin daka saida aka hukunta Madu
(Da kyar ma aka barshi ya cigaba da sama a unguwar dan da cewa sukayi Madu sai ya bar unguwar).
Sannan sam K’asimu bashi da hali mai kyau!
Shima Usman duk da alkhairin da Sadiya tayi mishi hakan bai sa ya amince da auren ba, dan shi yanzu sana’a ma zai yi ya tara kud’i ya tafi Madina neman Maryam! Sai ya dawo da ita ko da bala’i ne.
Shiyasa ranar da Sadiya tazo mishi gyara, yaji tausayinta dan sai nan nan take yi dashi, dan haka ya yanke shawarar ‘gara ya fad’a mata gaskiya’ saboda a yanzu yana ganin mutunci ta ko ba komai ita ta kula dashi a lokacin da kowa ya k’i shi.
Zaunar da ita yayi ya fad’a mata cewa “shifa babu maganar aure a tsakaninsu, akwai abinda yasa a gabanshi, in ma saboda haka ne taketa kula dashi gara ma ta daina ta nemi wani suarayin tayi aurenta!. Amman yana mai tabbatar mata da bazai tab’a mantawa da irin alkhairin da tayi mishi ba, har abada!! Ya gode ya gode sosai.”

Kuka kawai yaga ta fashe mishi dashi, da kyar ya samu ya lallasheta, ta tashi ta tafi gida.
Tana zuwa gida ta tarar da Baba Laraba da dillaliya suna hira a tsakar gida da gudu ta fad’a kan Baba Laraba tana rusa kuka, nan ta koro mata abunda Ya Usman d’in yace..
Baba Laraba ce ta hauta da fada tana cewa “idan ita ba mayya baceba to ta hak’ura da Usman.”
Dillaliya ce ta katse su ta cewa Sadiyan “ta tashi ta tafi ta daina kuka” sannan ta matso kusa da Baaba Laraban ta rad’a mata wasu maganganu….

Bayan kwana uku da safe, sai ga Baaba Talatu tazo gidansu Sadiya, da yamma Baba Bashir da Ya Jamilu, duk akan neman auren Sadiya….har wani b’oyewa Modu suke yi. Shi kuwa Madu da yaji labari abun ya bashi mamaki amman daya je ya samu Usman yaga yadda shima ya haukace akan Sadiyar sai kawai ya biyesu aka shiga neman auren….
Wata biyu aka saka dan ana so a had’a dana Ya Jamilu, lokaci yana cika da ikon Allah aka sha biki aka d’aura aure.
Sadiya ta tare a gidanta wanda Baba Bashir da Madu suka bawa Ya Usman d’in anan bayan layi nasu, shi kuma Ya Jamilu dake ya samu sabon posting a Ibadan zai sake komawa yayi shekaru hakan yasanya ya d’auki amaryarsa suka tafi tare amman shima akwai gidanshi anan kusa da na Ya Usman d’in, sanin da yayi ba kwana kusa zai dawo garin ba ya sanyashi zuba haya...........

Bayan shekaru bakwai!.

Madina…
Wani d’an mini duplex ne mai d’auke da d’an k’aramin compound da 3 bedrooms 3 parlours sai kitchen da dining area, Maryam da Abba sukaje gani domin yanaso ya siya, a wannan lokacin apart from work na office yana business kala kala so Allah yayi mishi bud’i.
Bai yi wata k’iba ba saboda ba yanayin k’irarsa kenan ba amman ya murmure yayi haske yayi fresh kana ganinshi kaga hutu, kyawunshi ya sake fitowa .
Tsayawa fad’ad kyauwun da Maryam ta k’ara ma b’ata lokacine.

Suna tsaye a cikin gidan
yana magana da masu gidan da lawyer, ita kuwa in banda cika da batsewa ba abunda take yi, jira kawai take a tab’a ta ta fashe da kuka.
Daman already sun gama magana da ganin gidan a hoto Dan Abban ma ya tab’a zuwa sau d’aya yau ya kawo Maryam d’in ne akan idan gidan yayi mata sai a siya.
Koda ya tambayetan kuwa kawai d’aga kai tayi ba tare da tace k’ala ba.
Murmushi kawai yayi ya juya wajen mutanen…har da lauyanshi suka zo, shiyasa kawai aka fara cike cike bayan an gama suka karb’i keys suka nufi apartment d’insu dan suyi parking.
Kamar jira takeyi suna shiga tun a falo ta fara kuka tace “ita wallahi babu inda zata je kawai ya mayar da ita gida, tunda har yayi kud’in da zai iya siyan gida a nan ai zai iya nema mata jirgi taje Nigeria, kuma kwanaki tayita tambayarshi ‘ko waya yaje’ amma yace mata ‘waya bai je Nigeria ba’, nan kuwa waya yaje, jiya neighbour d’insu take ce mata akwai anty d’inta a Nigeria kullum sai sunyi waya.
Kuma tace landline ma yana iya tafiya sometimes…”

Abba tun yana yiwa rigimar tata dariya har ya daina dan yaga abun nata na yau dagskene, dan tace “wallahi ba inda zata je, ko Yaya ne ya kira.
Tunda yanzu ai duk k’arshen shekara yana zuwa dubasu, kuma k’arshen shekara ya zo dan haka ya taho mata da numbern su Shuwa ita ko waya ne ta samu tayi dasu, kafin taje gaskiya hak’urin ta ya k’are!.”

A b’angaren Abba kuwa, duk zuwan da Yayan nasu zaiyi, sai yayi yunk’urin binsa su koma, amman sai Yayan nashi ya hanashi, saboda ba sau d’aya ba Granpa ya kan gaya mishi ‘in dai yaje Madina suka yi tsautsayin had’uwa da Abba to ya gaya masa yana nan akan bakarshi babu abinda ya chanja’, kasancewar ya san yanayin aikin Yahayan a chan yake kuma yana zuwa akai akai(ambassador) shiyasa ba yadda ya iya ya san dole wani lokacin zasu had’u, kuma ya fad’a ya sake maimaitawa yace ta kan Maryam d’in zai fara.
Duk lokacin da Granpa zai zo Madina kuwa sai ya aikawa Abban da sak’o, hakanan In ba lokacin hajji bane zai d’auki Maryam ya d’au leave a wajen aiki su bar k’asar gaba d’aya..

Table of Contents

Chapters

2 chapters
  1. 1 DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN K’AI.
  2. 2 Volume d’in kukan nata data k’ara ne ya katse mishi tunani.
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});