Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 4

Chapter 4

Sirri Ne Book 1 Complete Hausa Novel 1,197 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

gwaunatin ,kullun bashi barin mu muyi karatu wlh na gaji kujifa har nan da wata uku sannan zasu dawo Allah wannan govnar haushin sa nake ji sosai" ajiyar zuciya Abbu yayi sannan yace. "nine na sanya ki makarantar ? ince ke kika zaba kika ce na gaunati daman abinda yayi miki godu Kenna tun farko amma kika nace sai shi" mikewa yayi tare da d'aga kafad'ar sa alamar wannna matsalata ne sannan yace. "sai kicewa Uncle d'inki ya sauya miki shima saiya ta biye miki kuna b'arin kud'i" daga haka ya fita Umma tace. "mamana Allah ya shirya ki yanzun kuma sai kice Faruq ya canza miki shima wlh da yake biye miki ya fiki mtss" taja tsaki sannan ta shige d'akinta abin haushi ya fara bani nima sai na nufi d'akina dake nisa dasu ni d'ayata babu mai takura min inna shiga toilet na nufa nayi wanka tare da na tsarki sannan na fito na shinfid'a pray mate cikin nutsuwa na gabatar da sallar azahar dan karfe biyu tad'an gota shiryawa nayi cikin uniform na islamaiyar sheik Abubakar mahamud Gumi blue uniform riga da wando sai himar wanda nasa aka min d'inkin har kasa jakan litattafai na na d'auka tare da feshe jikina da turare har zan fita sai Kuma na dawo gaban mirro na rangad'a wani uban make-up kasancewar malaman makarntar basu so ko janbaki idan kika saka to wlh da uniform naki zaki gogo mugaye irinsu malam yusufa a bango zai sa mutum sharewa ,nikuwa yau ontop nake jin k'aina kuma babu malamin da zai dake ni ya zauna lafiya domin sai nasa uncle ya rangad'a masa rashin kirki koda nafito sai naci karo da Umma zata shiga kitchen salati tayi sannan tace. "RAUDA lafiyar,ki kuwa ? wannan uwar kwalliyar sai kace zaki gidan gala ko dinner on ni yazanyi da wannan shegiyar taurin kan taki " saida nayi dry mai isata sannan nace ."wlh umma kin bani dariya sai kace wani abu nayi kwaliyace fa kawai kuma wlh dan ra'ayin wasu banzaye bazanyi nawa ra'ayin ba haka kawai su tauye ni lalala bazan yi haka ba ked'ai sai na dawo" da i'do ta rakata sannan tace. "Adawo lafiya" inna tafiya nace. "Allah yasa hkn" inna zuwa makarntar tsaban isk'anci ma yau da kafa na tako naki hawa machin saboda uncle yace baya so nan na tarar da ana Kama letti inna zuwa ban tsaya ba nayi hucewata cikin hargagi d'aya daga cikin su yace. "Ke dan uwarki zonan.. ?" a fusace na juyo dan banyi tammanin haka ba kodan yasan i'dan yayi magana bazan zoba ne yasa ya had'a da uwata to wlh sai naci maicin uwarsa yau zan nuna mishi nice shugaban tantirai wata yarinya na Kira na bata jakata sannan nace ta k'aimun class d'inmu karasowa nayi gurinsu banyi wata wata ba na d'aukeshi da mari kafin ya dawo daga duniyar mamaki na kuma kara mishi wani. sannan nace ma d'aliban dake gurin "kowa ta huce ajinta yau zanga uwaruwarka uwarka tafi tawa uwarne ko ubanka yafi uban nawa da har kake da bak'in zagar min uwa kai duk buran'uban da zamuyi da mutum karda ya kuskura ya sanyo iyaye na kai ko uncle d'ina domin sai inda k'arfi na ya kare dan kutumar buran'uban ka uwata sa'arka ce...? Ko sa'ar ubanka ce ? shege d'an matsiyaci i'dan ba tsiya da talauci ba uwar me zaka tsaya Kama latti naira hamsi to ka sani daga yau na ringa zuwa latti kenan baka isa ka taba lafiyar jikina ba Haka baka i'sa nabaka sisina ba" shake masa wiya nayi sosai inna zazzaga masa rashin mutumci cikin haka muka fara kokuwa naya kok'arin kwace kansa karna kashe shi amma naki sakinsa domin ba rikon wasa na masa ba zuciyata kuma sai tafarfasa take yi malaman makarntar ne duk suka fito nan suka shiga niman ba'asi mai'ya had'a mu kala bance musu ba saima kallon banza dana bisu dashi suna jin abinda ya faru suka ce bai kyauta ba amma na sake shi yin duniyar nan sunyi su kwaceshi a hannuna amma sun kasa sunyi² na sake shi naki cikin fusata malam yusufa ya d'auko bulala haushi biyu ya had'a ya zane ni ga haushin nayi coki gana taurin k'an dana nuna musu kai duk duk'an da yamin har cikin raina nake ji Amma tsaban k'arfinhali naki sakin Fahat d'an isaka daman inna jin haushin sa domi yayi mugum rena ni a makaranta duka na fitan hankali Malam yusufa ya min naki sakin sa zuwa wannan lokacin numfashin sa ya fara sama masa kamar yanda nima nawa numfashi ya soma sama da kasa jikina ya fara rawa ture Fahat nayi ya fad'i kasa sannan nayi kan malam yusufa rigansa na cukwikuye masa a wiya na shiga kai masa naushi ta ko inna i'danuwana sunyi ja kai da ka ganni kasan bana cikin hayyacina malamai ne suka taro a k'aina da kyar suka kwaceshi a hannuna Ni kuwa sai huci nake i'dona ya firfito abinka da mai'manyan i'danuwa. Malam suraj headmaster d'in makarantar Kenna kare min kallo yayi tass sannan yace. "Meya faru nan suka zayyane masa komai fad'a yayi sosai akan me malam yusufa zai dake ni gashi nan ba i'ta bace aljanine akanta ja da baya suka fara yi ganin yadda i'danuwana suke juyi tamk'ar bani ba tsawa malam Suraj ya daka min Sannan yace. "wanene kai shuru naki mgn so uku yana tambaya amma shuru cikin fad'a yace. "zaka fad'a mana kai waye ko sai mun konaka da ayar Allah ? "Hahahahahaha wani mahaukacin dariya na kwashe dashi sannan nayi magana cikin wani i'rin murya wadda su day k'ansu sai da suka tsorata "sanin wanene mu ba abu mai sauki bane Amma ku sani mu an turomu ne ba shigarta mukayi ba turo mu akayi hahaha" cikin amo suka karasa maganar malamai kusan biyar sunyi sunyi na kwanta ko na zauna inna abin ya gagara domin ni k'aina inna da taurin kai ga kuma ture da aka min nasu taurin k'an ma yafi nawa yin duniya anyi su zauna sunce sam ba zama zasuyi ba nasu na tsayuwa na basu zama i'dan aka takurasu ran kowa zai baci d'auko kur'ani Malam yayi nan ya fara karanto suratul-jinnni kafin na kai aya sunyi aya biyu "wayyo Allah gamu gareka cewar malam yusufa abin mamaki ya ringa basu ana d'auko sura kafin akai aya sune zasu fara kaiwa kai har lokacin tashi yayi Amma ana k'aina suna fama da aljanu haka aka watse d'aya daga cikin malaman ne ya kira Uncle yace yazo yanzun nan babu Bata lokaci saiga Faruq ya shigo yana ganin halin da nake ciki na birkice tare da tambayar ba'asi ana sanar dashi ya wanwanke Malam yusufa da Mari sannan yasa aka Kira masa Fahat saida ya masa duka sosai sannan yaja masa good warning ya fita harka ta saida ya musu rashin mutumci zuwa lokacin Abbun mu yazo shine yayi ta bashi hakuri sannan ya dawo de'de tare da nufar inda nake kwance yana karasawa ya kwantar da murya zare da zabbad'a musu kirari abin mamaki sai gashi yana musu magana cikin sanyi suna bashi Am'sa nan yace su fita sukace sunga gurin Zama basu ba fita an kai ruwa rana sannan

Table of Contents

Chapters

6 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});