Chapter 2
part d'in Ganez suka fara shiga suka iske Nisah zaune kusa dashi,
Sanah tace " oh! ashe dai har yanzu ana tsinkar korawayen fure?
Duk sukayi dariya kana Ganez yace " a'a aini idan bada ku zan tsinki korayan fure ba,
ai a banza, Khulud tace " kinji shi zayyi mana wayo kullum yayi ta cewa idan ba mu ba sai rijiya,
Sanah tace " kuma yana tsoran matarsa ba,
Nisah tayi dariya kana tace " oh! kuji man yara,
wato kun saka mana ido, ai irin haka ake so,
Khulud tace " mijin ya rink'a jin tsoran matarsa?
Nisah tace " eh mana,
Sanah tace " ina fa dad'i miji ya zama mijin tace,
an dai mayar mana da kakanmu tace kawai,
Nisah tace " wannan ai kan tace ne ma,
duk sukayi dariya kana suka fita suka nufi part d'in Danish,
ganin Erum tayi kwalliya yasa su yin dariya,
Khulud tace " wato ke har yanzu baki dai na kwalliyya bako?
Erum tace " ina ni ina daina kwalliya,
Sanah tace " kici zamaninki kici na wasu ko?
"Sosai ma kuwa cewar Erum,
" a'a kace yau amare nane a gidan,
cewar Danish dake fitowa daga bedroom d'insa,
Sanah tace " mune, munzo a bamu abinda akaci aka rage,,
Danish yace " ku da kuke amare ina ku ina raguwa,
ai sai dai sabuwar dahuwa,
Khulud tace " ai dama kun saba yi mana wayo,
bayan duk tsoron matan ku kukeji,
Erum tace " ai irin wannan k'arshen ake so ayi yara,
ku ma kuyi addu'ar Allah ya baku ita mu,
Sanah tace " wai ma duk ba wannan ba,
ina zaku na ganku duk kunyi kwalliya?
" Mu da muke da walima yau har a tambaye mu inda zamu dan munyi kwalliya,
Erum tayi maganar tana dariya,
Khulud tace " a she walima ce daku,
a ina kuma?
Erum tace " sosai ma, kuma a nan gidan,
Sanah tace " tab wai wacce walimar kuke nufi?
Badai tamu ba ko?
Tayi maganar a lokaci d'aya,
Erum tace " walimar ku ko tamu?
"Ai muke da walima kuwa,
tunda mune manyan k'awaye,
tayi maganar tana dariya,
Khulud tace " mu dai bamu gayyace ku ba,
kuma bamu san gayyar sod'i ehe,
duk sukayi dariya kana suka fita,
Table of Contents