*'YAR ZAMAN ƊAKI* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Ban amince a sauya min littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, don haka a kiyaye.⚠️ https://chat.whatsapp.com/HFVRd4aXG6A8v3OngGn29A 1&2 Manyan motoci ne a jere sun yi jerin gwano kala-kala, idan ka ƙare musu kallo kusan kalolin motar launi biyu ne akwai launi farare da baƙaƙe. Abokan ango ne tsaitsaye kusan kowanne yana jiran ƴan matan da ya sauke don mayar da su gida, kallo ɗaya za ka yi musu ka fahimci suna cikin farincikin taya abokinsu murnar aure. Gidan babba ne amma plat ne cike yake da kayan more rayuwa, ya sha ƙyalƙyali da hasken ƙan lantarki. Kana ƙare wa gidan kallo za ka fahimci dukiya ta samu makwanci a wurin, duba da irin ɗimbin dukiyar da aka narka a ciki. "To Zarah kin ga dai kin samu gida irin wanda kowacce ƴa mace take fata, ki yi biyayya ga mijinki ku zauna lafiya, shi zaman aure ɗan haƙuri ne yi na yi bari na bari..." Wata Dattijuwa da take kusa da Amarya Zarah ta riƙa yi mata nasihar zaman aure, ƴan matan da ke tsaitsaye sai kalle-kalle suke yi kowacce tana ayyana ina ma gidanta ne. Matan auren cikin su mafi yawa suna raya Allah ya hore wa mazajensu suma daƙara musu kamarsa, wasu daga cikin iyaye kuma na fatan suma Allah ya bawa nasu ƴaƴa irin wannan gida. Zarah bata furta komai ba kasancewar kanta na cikin mayafi, har mutanen da suke cikin gidan suka watse sakamakon abokan Ango sai zabga horn suke yi. Ɗakin Zarah ya rage daga ita sai ƙawayenta uku, a hankali ta zame mayafinta tana ƙare wa ɗakin kallo. Amma kana ƙare wa fuskarta kallo za ka fahimci akwai ɓacin rai a tattare da ita, Lubna da ke gefe ta ce: "Zarah ya dai na ga har yanzu ba ki da walwala ko dai akan maganar nan ne?" Dogon tsaki Zarah ta yi ta furta, "Lubna an yi min adalci kenan? Ace daren farkona wai za a kawo min wata ƴar zaman ɗaki?" Aisha ta taɓe baki tana faɗin, "Ni fa ban ga abin damuwa ba, kuna ɗakinku tana nata. Kuma mutumin nan yana tsananin ƙaunarki, ki dangwali arziki ki bar arziki a mazauninsa." Sadiya ta yi gajeren tsaki tana cewa, "Wallahi Zarah abin haushi gare ki, bakya cin uwar yarinya idan ta ji wuya da ƙafarta za ta gudu.Ki zauna wata ƙanƙanuwar yarinya ta ɓata miki farincikinki, ki zo ki yi biyu babu." Nan take ƙawayen Zarah suka ci gaba da bata shawarwari na kyau da na banza, lokaci ɗaya ta ware tana farinciki don ta fahimci abin da suke ɗorata a kai. Ba a jima ba Ango ya ƙaraso shi da abokansa, fito wa ya yi daga motar abokinsa Sani. Bayan motar ya buɗe Walida na zaune tana ƴan kalle-kalle, tana ganin ya buɗe mata ta yi masa murmushi. Hannunta ya kama ya ce, "Fito mun zo gida." Wani Abokinsa Yunusa da ke gefe ya ce, "Mutumina ba ka so cin amarci ba, haka kawai ranar aurenka ka ɗauko yarinya yoo ko ƴar cikinka ce ai ka kaita ajiya." Khalid ango ya yi dariya ya ce, "Ku dai kuka sani kanku ake ji." Cikin raha abokansa suka raka shi, aka yi barkwancin da aka saba tsakanin Angwaye da Amare, daga ƙarshe aka yi sayen baki ƙawayen amarya da abokan ango suka watse. Zarah ban da yaƙe babu abin da take yi don kar ta nunawa Khalid bata so zuwan Walida ba, Khalida ya ɗauko manyan ledoji biyu duka cike suke da kaji. Gefe ɗaya katan-katan ɗin lemuka ne sai manyan yegot da kayan ƙwalam da maƙwalashe. Khalid da kansa ya ɗauki Walida ya kaita ɗakinta haɗe da ajiye mata ƙaramar ledarta da ya saya mata kazarta guda ɗaya a ciki, sai lemon jarka da alawoyi. A madadin Khalida ya fita sai ya zauna a gefen gadon, shi kaɗai ya yi jim kamar mai nazari sannan ya furta, "Wannan wacce irin rayuwa ce haka ni ban haifa ba, ba dangin iya ba na baba amma na ƙare da dakon wahala." Walida da ke gefe ta zuba masa ido ta ce, "Uncle magana kake yi?" Khalid ya wayance da dariyar yaƙe ya ce, "A'a Walida. Cewa na yi Walida ƴar Uncle, yanzu dai ga namanki ko sai da safe za ki ci?" Walida ta leƙa ledar tana juyar da kanta gefe tana shinshine-shinshine ta ce, "Amma dai wannan kazar ba gashin inji ba ce?" Khalid ya zuba mata ido wani takaici ya kama shi, a ɗiƙile ya furta, "Idan bakya ci ki bari sai da safe kya ci." Khalid na gama maganar ya nufi bakin ƙofa tun bai ƙarasa ba Walida yanƙare baki ta fashe da kuka. Riƙe ƙugu Khalid ya yi a ƙagauce ya dawo murya a shaƙe ya ce, "Me ye kuma?" Ledar kazarta ta nuna masa tana maƙale hannu ta ce, "Kazar nan ce take cizo na a hannu, kuma ni ka zo ka kwanta a nan." Da mamaki Khalid ya furta, "Kaza kuma? Gasasshiyar kazar ce take cizonki..." Khalid bai rufe baki ba ya ji ledar kazar ta bada ƙaraas alamun taunar ƙashi, da sauri Khalid ya sake buɗe wa sai dai ga mamakinsa yana buɗe ledar ya ga sai taunannun ƙashi, wasu ma an yi dugu-dugu da shi. Cinyoyin kazar ne kawai aka cinye tsokokin ba tare da an tauye ƙashin ba. Yana shirin yin magana ya ji Walida ta saki ƙatuwar gyatsa sannan ta ce, "Uncle zan sha ruwa." Khalid ya ƙwalalo ido waje ya ce, "Ina kazar cikin ledar?" Walida ta ce, "To ai sai na sha ruwa zan ci." Khalid ya sake bankaɗe ledar ya ce, "Ba yanzu na nuna buɗe kazar har kika ce ba gashin inji ba ce?" Walida ta sake sakin gatsa haɗe da ɗaukan tsinken sakace tana kwakwule haƙoranta. MEYE HARSASHENKU AKAN WALIDA? 😂 LITTAFIN KYAUTA NE AMMA BAN YI ALƘAWARIN YIN TYPING MAI TSAYI BA SABODA LITTAFIN KUƊIN DA NAKE YI, ZAN YI ƘOƘARIN YIN POSTING KULLIN INSHA ALLAH.🥰 *'YAR ZAMAN ƊAKI* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Ban amince a sauya min littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, don haka a kiyaye.⚠️ https://chat.whatsapp.com/HFVRd4aXG6A8v3OngGn29A 3&4 Khalid zuru ya yi yana kallon Walida da take sakace tana lumshe ido, sai da ta gama sakace ta ɗago daga kishinɗe ta ce, "Uncle ƙishirwa nake ji." Ba tare da ya kalli wurin da yake tsammanin anan ruwa da yegot ɗin suke ba, ya miƙa hannu har lokacin idonsa na kan Walida, yana taɓa robar yegot ɗaya ya ji ba faɗi garam alamar an shanye abin da yake ciki. Wannan karon sai da cikinsa ya kaɗa amma don kar ya nuna mata ya ɗan tsorata ya hau borin kunya da cewar, "Wai me yake faruwa ne? Kaji tun ba a je ko'ina ba sun ƙare shi ma yegot ɗin an shanye shi duka, wallahi duk uban da yake aikata min haka daidai nake da zamaninsa." Amarya Zarah tana can zaune tana jiran dawowar Khalid ango, ƙamshin kazar ne ya gama cika mata hanci ban da haɗiyar yawu babu abin da take yi. Jin shirun Khalid ya yi yawa ya sa ta fara jin haushi saboda tana tuna Walida wani takaici yake mamaye birnin zuciyarta, a hankali ta miƙe ta isa bakin ledar kazar. Ta faki ido tana kallon hanyar shigo wa amma jin shirun da ta ji ya sa ta kai hannu da niyyar buɗe ledar, lokaci ɗaya ta ji kamar an ce. "Wayyo ni Amarya Kaza." A ɗan zabure Zarah ta ja da baya tana waige-waige don yadda ta ji kazar na magana raɗau a kunnenta, da sauri ta nufi sashen da ta ga Khalid ya bi. Tana zuwa ta samu Khalid tsugunne a gaban Walida yana cewa, "Walida ki yi bacci kin ga Auntynki na can tana jirana." Walida ta kwaɓe baki ta ce, "A'a ni dai ka kwana a nan." Ganin yanda Khalid yake lallaɓa Walida ya tunzura zuciyar Zarah, tun daga bakin ƙofa ta saki uban ashar tana faɗin: "Khalid me kake yi haka? Wai ni ce Amaryar ko yarinyar nan? Tun da ka shigo gidan nan ka taho wurin yarinyar nan ni ina can ina zaman jiranka, wallahi da na san wulaƙancin nan za a min da..." Tun bata ƙarasa ba Walida ta tashi zaune ta ce, "Don Allah ki yi haƙuri Aunty." A zafafe Zarah ta dakatar da ita da cewar, "Rufe min baki munafuka ƙanƙanuwarki da ke sai iyayi." Khalid ya miƙe jiki a sanyaye ya ce, "Don Allah ki yi haƙuri Zarah, ni fa ba wani abu ne ya tsayar da ni ba. Dubi ledar nan." Khalid ya yi maganar yana ɗago wa Zarah ledar kazar. Ganin taunannun ƙashi ya ƙara harzuƙata ta ce, "Eh to tun da kun cinye gani ƴar iska ai dole ka nuna min ƙashi amma gaskiya Khalid ka cuce ni da na san cin kashin da za ka min kenan da..." Khalid ya katse Zarah tare da zayyane mata abin da ya faru. Da farko ta so ƙaryatawa amma da ta tuna abin da ta ji sai tsoro ya sake kamata. Suna nan tsaye Walida ta ɗago ta ce, "Uncle ku je ni fa bacci nake ji." Khalid ba ƙaramin daɗi ya ji ba, cikin shauƙi, so da ƙauna ta riƙo hannun Zarah suka wuce sashensu. Suna zuwa Khalid ya rungumo Zarah yana kashe mata ido ɗaya ya ce, "Habibity kin ga yadda kika yi kyau kuwa?" Kafin Zarah ta yi magana suka ji magana kamar raɗa an ce, "Duk kyawunta ta kai kaza." A firgice duk suka waiga, Khalid ya fara leƙe ta window ya ce, "Zarah amma dai babu wanda aka bari a ƴan kawo amarya ko?" A daƙile Zarah ta ce, "Sai ƴar zaman ɗaki waya sani ko laɓe take mana." Khalid ya wayance da cewar, "Haba dai Walida ba za ta yi haka ba. Yanzu dai miƙo min ledar kazar nan ki ga." Zarah ta yi baya cikin zaro ido tana faɗin, "Wa ni? Ai idan ka ganni a lahira kaini aka yi. Jin kunnena na ji kazar nan ta yi magana, kai anya Khalid gidan nan ka sa an yi masa sauka kuwa?" Khalid ya ƙarasa ya ɗauko ledar kazar yana cewa, "Ban da almara ya za a yi Kaza ta yi magana kina son dai tsorata kanki ne." Yana gama maganar ya baje musu kazar suka zauna sai dai har lokacin Zarah bata gama sakin jikinta ba." Katuwar cinyar kaza Khalid ya ɗauko ya gutsira sannan ya miƙa wa Zarah ya ce, "Buɗe baki My love." Zarah ta buɗe baki yana miƙa mata a baki sai ji ta yi zuwait an zuge tsokar sai ƙashi. Zarah da take baki a buɗe ta kalli Khalid, shi kuma sam bai lura da abin da ya faru ba. Wata tsokar naman ya sake ɗauko mata ya miƙa mata, a wannan karon Zarah ta cinye amma tana yin tauna ɗaya taji an ce. "Wayyooo cinyata ni kaza." Da sauri ta kalli Khalid ta ce, "Hubby ka ji me na ji kuwa." Khalid ya tura tsoka baki yana tauna ya ce, "Zarah don Allah ki kwantar da hankalinki, na fa gidanki ne karki tsorata kanki." Babu yadda ta iya haka ta ja bakinta ta yi shiru don ta ga Khalid bai yarda da abin da ta faɗa ba, yana sake bata kazar ta nuna masa ta ƙoshi. Sai lemo ta sha kaɗan amma har lokacin zuciyarta wasu-wasi take. Bayan sun kammala Khalid ya tuna da wani magani da abokansa suka bashi, da sauri ya tashi cikin dabara ya nufi kitchen acen ya buɗe jarkar ya shanye gabaɗaya. Ita ma Zarah yana fita ta zuge jakarta ta ɗauko wani tsumi da aka bata ta shanye, tana jin motsinsa ta wurga jarkar ƙarƙashin gado. Khalid na zuwa ya cire kaya ya ɗaura towel yana faɗin, "Dear bari na watsa ruwa sai mu ɗaura alwala mu yi sallah." A kunyace Zarah ta amsa tana sunne kai ƙasa ita a dole kunya take ji, tana nan zaune Khalid ya faɗa banɗaki. Shigar Khalid ba wuya ta fara jin kyarkyara a kofar ɗaki kamar kaza za ta saki ƙwai, a hankali ta tashi ta leƙa ta window ga mamakinta sai gani ta yi gasasshiyar kaza na rawa babu kai a jikinta. Ajiyar zuciya ta sauke zuciyarta na lugude ta ji an furta, "Mu kashe mu binne mu sha amarci da angona." Khalid da ke toilet ɗin cikin ɗaki bayan ya sakale towel yana shirin kwara ruwa a jikinsa kamar almara ya ji an ce. "Sannu mijin kaza." Da sauri ya waiga yana dube-dube nan take ya ji ƙamshin gasasshiyar kaza ta game hancinsa, yana shirin janyo towel don ya fita ya ji an shafo bayansa. Da gudu ya fisgi towel ya hau kiciniyar ɗaurawa, hannunsa har rawa yake zai buɗe ƙofa ya ji an sake cewa, "Mijin Kaza yau fa ranar farinciki ce." Wani tunani ne ya faɗo wa Khalid ya ga idan ya yi ƙarfin halin magana koma waye zai tsorata shi za su dawo daidai. Tsayawa ya yi a wurin ya ce, "A gidan uwar wa na zama mijin kaza ga matata can Zarah a ɗaki." Yana rufe baki ya ji an ce, "Gashi har magani ka sha min don mu sha soyayya, ka ga daga yau zuwa ƴan kwanaki zan fara sakar maka ƙwai zo ka ji angona." Kafin ya yi wani yunƙuri ya ji an fusgi towel ɗin ya ji alamar yatsun kaza na tsikarinsa a jiki. NA BARKU HAKA DA MIJIN KAZA😂 SU SHA AMARCI LAFIYA. Ummou Aslam Bint Adam.🌚 Ummou Aslam Bint Adam🌚*'YAR ZAMAN ƊAKI* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Ban amince a sauya min littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, don haka a kiyaye.⚠️ https://chat.whatsapp.com/Bkw4WZsTlH5I8pEbP946SA 5&6 Khalid bai za ci lamarin haka yake ba don haka ya kai duka da gwiwar hannunsa, a daidai wurin da yake jin alamar ana kartarsa da yatsun kaji. Yana kai dukan ya ji siririyar muryar ta sake cewa, "Haba mijin kaza kar ka bari mu yi haka da kai." Hantar cikin Khalid ba ƙaramin kaɗawa ta yi ba, da farko ya ɗauka idan ya kutuntuma wa mai maganar ashar za su dawo daidai. Yana tsaka da tunanin ya ji an dafa kafaɗarsa ana cewa, "Mijina na baya ma gardama ya so ya yi min, kaima karka min haka mijina, don idan ka min gardama gunduleka zan yi." Khalid ko saurara bai gama yi ba ya zuba uwar ƙara yana ƙoƙarin jan ƙofa amma ta ƙi buɗuwa. Ganin ba shi da mafita ya sa ya fara ƙwala wa Zarah kira, don yadda ya ji ana shafar ƙeyarsa abin ba ƙaramin tsorata shi ya yi ba. Zarah ba ƙaramin tsorata ta yi ba don haka ta koma can ƙuryar gado ta duƙunƙune kanta a ciki, tana nan zaune ta ji ƙarar dirar abu a kan gado. A hankali ta zaro kanta don ganin abin da ya faɗo saboda ilahirin jikinta rawa yake yi, ta gama tsorata har ta ayyana gari na wayewa za ta koma gidansu idan ya so sai dai Khalid ya nemar mata wani gidan. Zarah na ɗago kai ta ci karo da ƙatuwar soyayyar cinyar kaza tana murginawa tana faɗin, "Sai ni ƙanin kaza wato zakara, yayata za ta tasha amarci da mijinta Khalid ni ma ga tawa amaryar tana jirana, amma ni dai ki gafarce ni ɗan ƙunan baƙin wake ne amaren mata nake bi ina kaiwa farmaki." Zarah ta waro ido waje don ko a mafarki bata taɓa tozali da abin da ta gani ba, tana nan zaune ta ji Khalid ya ƙwala ihu yana kiran sunanta. Zarah na jin haka ta fasa ihu cikin tashin hankali tana cewa, "Khalid don Allah ka fito ka ga kaza tana magana wallahi gidan nan aljanu sun yi yawa a ciki." Zarah na rufe baki ta ji cinyar kazar gabanta ta buga tsalle ta ce, "Ki daina mayar da mace don ni ba Kaza ba ce, yanzu haka haƙƙina na zo karɓa yau mu ɓarje amarci." Cinyar na gama magana ta fara fisgo zanin Zarah nan take Zarah ta fara jan zaninta suka fara kiciniya da cinyar kaza. Khalid na jin abin da Zarah ta ce ya sake waigawa ya fisgo towel ɗin yana faɗin, "Wallahi ni ma ina cikin wani hali Zarah ki kawo min ɗauki." Daga bayansa ya ga an ɗauke towel ɗin an yi saman toilet ɗin da shi aka ce, "Wallahi ka bani haɗin kai ko na kira ƙannena zakaru su sheme min kai na haike maka yanzu." Khalid na jin haka ya rushe da kuka kamar ƙaramin yaro har da majina ya ce, "Don Allah ku yi haƙuri ku sake ni wallahi ni ba mijin Kaza bane." Shiru ya ji ba a amsa masa ba don haka ya yi tsammanin ko an rabu da shi ne, ƙofar ya ci gaba da fisga yana bugawa da ƙarfi kamar almara sai ji ya yi ƙofa ta buɗe. Da sauri ya fice daga banɗakin a lokacin ya samu cinyar kaza na ta kiciniya shiga zanin Zarah. Daga wurin da yake a tsaye ya yi kukan kura ya faɗa kan gadon da niyyar ya janye matarsa daga kaidin cinyar kazar, sai ji ya yi an ɗauke shi an buga da ƙasa sannan ya ji an ce, "Ka tashi kasa kayanka ka tafi wani ɗakin ba wannan ba, kuma karka sake ka tafi ɗakin da babu ɗan'adam a ciki. Idan so samu ne ka je ɗakin Walida ko ta zo ta same ka." Khalid duk irin buguwar da ya yi bai sa ya karaya ya ce, "Wai uban waye yake son shiga tsakanin ma'aurata a daren amarcinsu? Babu inda za ni kowanne matsoraci ne ya fito mu yi gaba da gaba." Khalid tun bai rufa baki ba sai ji ya yi an yi saman fanka da shi, ƙafafuwansa na jikin fanka kansa yana ƙasa yana reto. Tsoro azaba da wuya ta sa ya sako fitsari daga sama ba tare da ya sani ba, Zarah na ganin an tasamma halaka mijinta ta sa kuka tana faɗin: "Don Allah ku ƙyale shi karku kashe min mijina." Zarah bata rufe baki ba sai ji ta yi an turo ƙofar ɗakinsu an shigo, Khalid yana daga saman fanka idanunsa suka hango masa wata ƙatuwar kaza, tsayi da girman kazar za su iya yin girman yaro mai shekara huɗu. Cikinsa ne ya fara kaɗawa cikin rawar murya ya ce, "Wayyo Zarah Kazaaaaaa." Zarah na shirin yin magana Kazar da take tafe tiƙis tiƙis ta karɓe zancen da cewar, "Haba Mijin kaza zuwa na yi da kaina ba aike ba, na tafi da kai mu ɓarje amarci ko na biyo ka sama Angona." Khalid ya fara saka hannuwa yana kare jikinsa ya ce, "Don Allah ki koma ni wallahi ba mijinki ba ne." Khalid tun bai rufe baki ba Kaza ta hau saman madubin Zarah tana tafe tana wata irin girgiza za ta ɗafe saman fanka, Zarah na daga zaune Cinyar kazar ta ce mata: "Zarah ki bani haɗin kai ko na yi kidinafin ɗinki." Khalid na ganin Kaza ta tunkaro shi gadan-gadan ya sake ƙwallah ƙara yana faɗin, "Zarah kazaaaaaaa, wayyo za ta min fyaɗe." Zarah ita ma ta kanta take yi don haka ta ce, "Khalid Zakara zai yi kidinafin ɗina." Kaza na hawa saman fanka ta yi tsallake ma maƙale hannun Khalid yana cewa, "Angonaaaaaa." NI MA SAI NA CE NA BARKU LAFIYA KU TAFI CETO KAR KAZA TA HAIKE WA ANGO, NA YI NAN BYEEEEEEEEE😂😂😂 Ummou Aslam Bint Adam🌚*'YAR ZAMAN ƊAKI* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Ban amince a sauya min littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, don haka a kiyaye.⚠️ 7&8 Khalid na jin yanda Kaza ta cafki hannunsa ya ware murya cikin tashin hankali ya ce, "Wayyooooo Allah Kaza za ta haike min." Kazar ta ra gwaɗar da kai tana girgiza tozonta ta ce, "Angona yau fa ranar farinciki ne ka taimaki kanka ka ba ni haɗin kai." Tana gama maganar ta miƙa bakinta wurin saitin fuskar Khalid ta ce, "Matso na sumbace ka masoyi." Khalida ta juyar fa kai gefe yana tofar da yawu. Kazar ta tashu sama firrr kamar tsuntsuwa tana kaɗa fukafukanta, bata dira a ko'ina ba sai kan tafin ƙafar Khalid da suke can saman fanka. Khalid na jin Kaza a daidai ƙafarsa ya fashe da wani matsanancin kuka tare da faɗin, "Wayyo za ta mayar da ni Zakara, wayyo Zarah Kaza za ta mayar da ni zakara." Kaza ta sa faratan ƙafarta ta shafo gwiwar Khalid tana faɗin. "Me ya yi saura Angona da kai da Zakara duk ɗaya ne a wurina." Zarah na shirin yin magana ta ji cinyar kaza ta ce, "Amaryata ki ba ni dama kar ba tafi da ke a neme ki a rasa." Zarah na jin haka ita ma ta fashe da kuka don wannan karon ta kai maƙura, ta gama saddaƙarwa rayuwarta. Suna cikin wannan halin wayar Zara fara ringing, ringtone ɗinta karatun alƙur'ani ne, yana fara ƙara duka suka nemi komai suka rasa daga kazar har cinyar kazar da take iƙirarin ita zakara ce. Khalid da yake maƙale a saman fanka sai ji kake faaaaaaaf ya faɗo kan gado, zumu-zumu ya yi saboda yadda ya galabaita. Ya juyar da kansa ya kalli Zarah murya a shaƙe ya ce, "Zarah yai muna ganin rayuwa." Zarah ta goge ƙwallar idonta ta ce, "Khalid wallahi gari na wayewa zan bar maka gidanka, kana gani cinyar kaza wannan ƙaramar hallita tana cewa za ta min fyaɗe." Khalid ya shafa wurin da Kaza ta taɓa ya ce, "Ki gode wa Allah Kaza ba ta haike min ba, kina ji fa wai kaza ce za ta min fyaɗe." Zarah bata kula shi ba ta ɗauki wayarta, za ta bi kiran da aka yi mata daga can ƙofar ɗaki suka ji takun tafiya ƙwas ƙwas ƙwas. Da sauri Khalida ya wawuro zanin gado ya zagaya ta gefen Zarah ya ce, "Zarah ki ɓoye ni wallahi ta dawo, daga ji Kaza je wallahi haike min za ta yi." Kafin Zarah ta yi magana daga bakin ƙofar suka ji an ce, "Kun ci sa'a amma babu komai a juri zuwa rafi." Jikinsu ba ƙaramin sanyi ya sake yi ba, Khalid na son yin waya yana tsoron tashi daga wurin. Dabara ce ta faɗowa Zarah va shiri ta saka wayarta a Airplane mode ta kunna karatun Alƙur'ani, tun suna jin taku a bakin ƙofar har suka daina. A hankali Khalid ya janyo doguwar riga ya saka sannan ya ɗauki wayarsa ya wuce wani ɗakin da aka ware don hutawarsu. Yana shiga ya ciro wayarsa ya nemo wata lamba sai da ya kira sau biyar aka ɗauka, tun ba a fara magana ba Khalid ya fara magana bakinsa har rawa yake. "Mai turakar Aljanu akwai babbar matsala fa. Yau daren amarcina amma Kaza da zakara sun hana ni walawa, yanzu haka da ƙyar na sha wai ni Kaza za ta yi wa fyaɗe..." Khalid bai rufe baki ba kukan Walida a ƙofar ɗakinsu, wani dogon tsaki ya Khalid kamar zai yi kuka ya ce, "Mai turaka don Allah ka yi wani abu wallahi ina cikin damuwa." Daga can ɓangaren aka bashi amsa da cewar, "Khalid ka ji da yarinyar da take yin kuka idan ka daidaita nutsuwarka sai mu yi magana." Khalid ya guɗe baki zai yi magam ƙit ya ji Mai turakar aljanu ya katse. Khalid tsabar takaici bai san lokacin da ya fashe da kuka ba, yana tafe yana hawaye ya isa bakin ƙofar ya buɗe. Walida na ganin Khalid ta goge hawaye ta ce, "Uncle na kasa bacci." Khalid baƙinciki ya sake kama shi a daƙile ya ce, "Mu ma ai ba mu yi ba." Walida ta fara shinshine-shinahine ta ce, "Uncle ƙanshin zakara nake ji." Khalid ya fisgi hannun Walida cikin ɗakin yace, "Sai ki ci idan kin gan shi." Zarah na hango Walida ta kashe karatun ta diro gabanta fuska a haɗe ta ce, "Ke! Me ya hanaki bacci." Ta haye kan gadon Zarah ta kishingiɗa tana lumshe ido ta ce, "Uncle bacci zan yi." Zuciya ta ɗebi Zarah ta kai wa Walida duka ta ce, "Ɗaga min gado ko na ci uwarki wallahi." Khalid ya zaburo a fusace ya ce, "Ke Zarah me ye haka?" Walida ta fice daga ɗakin tana kuka ta nufi sashen da Khalid ya fara kaita, da gudu Khalid ya rufa mata baya sai da ya je tsakiyar gidan ya ji fuurrrr a saman kansa. Yana ɗago kai ya hangi Kaza tana ɗaga fuka-fukai ta ce, "Yau babu mai hana ni abin da na yi niyya, ƴan uwa ku kawo min ɗauki." Tana rufe baki sai ga tawagar kaji sun dira a kan Khalid masu danne hannuwa na yi masu danne ƙafa na yi. Kazar ta fara rangwaɗa ta ce, "Bari fara salon jan hankali don na birge Angona." Rufe bakinta kw da wuya sai ga gashin jikinta na salewa. Khalid bai yi aune ba ya ganta a sulluɓe ba shiri ya ƙwallah ƙara yana faɗin, "Zarah Ki zo wallahi za ta haike min ta mayar da ni Zakara." ANGON KAZA A SHA AMARCI LAFIYA, GOBE MAJE GANIN AMARYA DA ANGO😂 AYI HKR DA ERRORS BAN YI EDITING BA. Ummou Aslam Bint Adam🌚*'YAR ZAMAN ƊAKI* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Ban amince a sauya min littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, don haka a kiyaye.⚠️ 9&10 AMNASH BAKERY PRACTICAL CLASS Mun ɗaura ɗamarar koyar da sana'o'in gashe-gashe da girke-girke kamar: VANILLA CAKE, DOUGHNUT, CHINCHIN, MEATFIE, COOKIES, CHICKEN NUGHET, BIRTHDAY CAKE, CAKE PERFAIT da sauran girke-girken sari a farashi mai rahusa 5K kacal domin masu farawa daga farko. ADDRESS: NO EA70 TITIN ADAMU ƊAN KURA GANDU KAFIN GIDAN BASHIR TOFA OPPOSITE MASALLACIN ƘADIRIYYA. KANO STATE MUNINCIPAL L.G PHONE NUMBER: 07038826617 for watsapp and call. KU GARZAYO KU KARƁI SAMI FORM ƊINKU DON KAR WANNAN DAMAR TA WUCE KU. Zarah na daga wurin da take a zaune kan gado ta ji yo ihun Khalid nan take hantar cikinta ta sake kaɗawa, takurewa ta yi a lungun gado tana karanto duk wata addu'a da tasan ta taɓa biyata a bakinta don lamarin ba ƙaramin kaɗamata ciki ya yi ba. Saboda tsabar tsoro ta karanta addu'a har da ta hawa abin hawa tun bata direta ba sake ɗaukan wata. Kaza na jin abin da Khalid ya faɗa ta waiga tana ɗaɗɗaga ƙafa ɗaya ta ce, "Haba Angona wa za ka kira mana a wannan yanayin da muke ciki." Khalid ya fara ja da baya yana kallon sauran kajin da suka haye kan hannunsa sannan ya ce, "Don Allah ki rabu da ni wallahi ni ko da mace bil'adam ƴar uwata ban taɓa yin zina ba, me ye haɗina da ke kina Kaza ina mutum." Kaza ta turo masa ciki gaba sannan ta ce, "Wannan cikin da ka gani sai da ya ɗauki cikin mazan bil'adam bakwai. Kai ne na takwas kuma duk namijin da na yi mu'amala da shi Zakara yake komawa, kalli can." Kazar ta yi magana tana nuna masa kusurwar bango nan take Khalid ya kai idanunsa, bai yi aune ba sai gani ya yi zakaru na fitowa ɗaya bayan ɗaya daga cikin kusurwar bango. A tsorace ya zaro ido yana shirin yin magana zakaran farkon ya buga tsalle sai da ya yi sama sannan ya fara buɗa fuka-fukai sannan ya miƙa wuya gaba ya ce, "Kukkurukuuuuu." Khalid ya saki baki yana kallon ikon Allah don duka jikin zakarun a saɓule yake babu gashi, zakaran yana gama cara ya kalli Khalid ya ce, "Ɗan uwana ina yi maka murna da shirin fara sabuwar rayuwa, don nan ba da jimawa ba kaima za ka dawo zakara kamar mu. Ni sunana Bala Mai leda yau shekarata huɗu a cikin siffar zakara." Zakaran farko na gama magana sauran suka riƙa gabatar da kansu, na ƙarshen cikinsu ya yi girgiza sannan ya : "Jikinka zai ɗau raɗaɗi fatarka za ta saluɓe kafin ka koma Zakara zan gaya maka gaskiya ka yi ta kanta don fyaɗen wannan kazar ba alheri ba ne. Ni nan da ka ganni Harisu sunana Bakanike ne shekarata ɗaya a haka..." Kazar na daga wurinta ta bugawa Zakaran da ya ke magana tsawa na take ya katse sauran maganar da yake yi. Khalid wani wawan kuka ya saki ba tare da ya shirya ba, ya dubi Kazar da ta yi ƙerere a gabansa, tana banƙaro ƙirji gaba ya ce, "Yanzu waɗannan da gaske mutane ne kamar ni?" Kaza ta kai tsinin bakinta za ta sunbaci bakin Khalid da sauri ya goce. Zakaran da yake gefe ya ce, "Ɗan uwa ka yi duk mai yi wa ka tsira da kanka." Khalid na jin haka ya zabura ya watsar da kajin da suka danne shi, ya riƙa surarsu ɗaya bayan ɗaya yana buga su da ƙasa. Duk wacce ya buga da ƙasa sai dai ka ji ta girgije ta ce, "Ka tsokanowa kanka wallahi nima sai na ɗana bayan uwar gayya ta gama da kai." Kaza na shirin faɗo masa gadan-gadan ya yi sufa da gudu ya faɗa ɗaki haɗe da danno ƙofa ya sakar mata sakata. Da gudu ya faɗa gefen Zarah ya riƙo hanunta sai kawai ya fashe da kuka. Zarah ita ma kukan ta saka masa don rayuwarta gabaɗaya a dagule take, cikin kuka ta dubi Khalid ta ce. "Khalid wannan wacce irin rayuwa muka samu kanmu a ciki?" Khalid ya matse ƙallar idonsa ya ce, "Zarah yau na ga mutanen da suka koma Zakaru da idona, yanzu haka ni kaina kaɗan ya rage Kazar cen ta haike min, da tuni na koma zakara angon kaza." Saboda takaici Zarah shiru ta yi suka ci gana da zurawa sarautar Allah ido, suna nan zaune sautin karatu na ci gaba da tashi daga nan har bacci ya yi gaba da su. PLS SHARE 🌚 Ummou Aslam Bint Adam🌚*'YAR ZAMAN ƊAKI* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Ban amince a sauya min littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, don haka a kiyaye.⚠️ 11&12 AMNASH BAKERY PRACTICAL CLASS Mun ɗaura ɗamarar koyar da sana'o'in gashe-gashe da girke-girke kamar: VANILLA CAKE, DOUGHNUT, CHINCHIN, MEATFIE, COOKIES, CHICKEN NUGHET, BIRTHDAY CAKE, CAKE PERFAIT da sauran girke-girken sari a farashi mai rahusa 5K kacal domin masu farawa daga farko. ADDRESS: NO EA70 TITIN ADAMU ƊAN KURA GANDU KAFIN GIDAN BASHIR TOFA OPPOSITE MASALLACIN ƘADIRIYYA. KANO STATE MUNINCIPAL L.G PHONE NUMBER: 07038826617 for watsapp and call. KU GARZAYO KU KARƁI SAMI FORM ƊINKU DON KAR WANNAN DAMAR TA WUCE KU. Washegari. Asubar fari Zarah ce ta fara farkawa daga bacci, da sauri ta ƙarasa ta fara tashin Khalid da ya saki baki da hanci yana shaƙar bacci. A firgice ya tashi yana faɗin, "Zarah! Zarah ina kazar?" Zarah ta yi ƙasa da murya ta ce, "Khalid gari ya fara wayewa ka tashi mu yi sallah ka buɗe ƙofar mu fita, wallahi ni da ka gani ba zan sake wuni a gidan nan ba." Khalid ya fara muttsuka ido yana dube-dube ya ce, "Zarah ina nan yadda nake ko?" Zarah ta dube shi da mamaki tana faɗin, "Ban gane ba." Hannunta ya janyo shafa mata a jikinsa sannan ya ce, "Don Allah a mutum nake ko na koma Zakara? Kin san zakarun nan fa suma har magana suna yi." Zarah ta yi guntun tsaki ta ce, "Idan so kake ka koma Zakaran sai ka bari idan na tafi gidanmu ba zakara ba ko Toro (Mijin agwagwa.) Sai ka koma." Ta ƙarasa maganar tana janyo jarkar faro ɗaya, ta fisgo bargon da yake kan gadonta, ta shinfiɗa a ƙasa ta fara yin alwala a kai. Khalid ya kalle ta ya ce, "Zarah ga banɗaki me kike yi haka?" Zarah ta yi masa kallon sheƙeƙe ta ce, "Jiya ina jinka da ƙyar ka ƙwaci kanka amma za ka ce min na shiga banɗaki, wallahi ko kashi na ji kafin na tafi gidanmu a nan zan yi." Shiru Khalid ya yi Zarah ta ci gaba da alwala. Tana gamawa shi ma ya suri robar ruwa ɗaya, ya gabatar da alwala suka yi sallah. Bayan sun idar Zarah ta dubi Khalid ta ce, "Khalid ka leƙa idan babu komai a waje ka buɗe mana na tafi gidanmu wallahi ba zan ƙara kwana a nan ba." Khalid ya riƙo hannun Zarah cikin shauƙi ya ce, "Haba my love amma ai ko raya darenmu ba mu yi ba." Zarah ta haɗe fuska ta ce, "Khalid!" Yanda ya ji ta kira sunansa ya sa ya tsaya tsam yana sauraronta. Ta nuna masa ƙofa ta ce, "Wallahi ba dare ba ko safiya ba za mu raya ba, da na samu na kwaci kaina a hannun zakara yana ƙoƙarin haike mun. Ni tun da nake na taɓa ganin masifa irin wannan? A ce kaza da zakara sune za su yi wa mutum fyaɗe wai har da kidinafin." Ta miƙe tsaye ta ɗaura ɗankwalinta ta je wurin ƙofa ta ce, "Don Allah ka zo ka buɗe min na tafi." Khalid ya haɗiyi yawu makwat sannan ya ce, "Haba Zarah ango nake fa ki tausaya min kina ganin baƙar wuyar da na ci hannun kaza kafin na tsero ɗaki." Zarah ta ɗaga kafaɗa ta ce, "Yanzu ma dama na wurinka ka zauna sai ku kashe amarcin kai da amaryarka kaza, amma wallahi wuni ba zan ƙara a gidan nan ba." Zarah da Khalid haka suka yi ta ja'inja har gari ya waye suna ɗaki kowannensu na tsoron buɗe ƙofa. Suna nan cikin ɗaki Walida ta ƙaraso bakin ƙofar ɗakin ta fara bugawa, ta window Khalid ya leƙa ya ce, "Walida kin tashi." Walida ta yi miƙa haɗe da hamma ta ce, "Wallahi Uncle na tashi don ma jiya ban samu bacci da wuri ba." Zaro ido Khalid ya yi suka haɗa ido da Zarah don shi a tunaninsa ko abin da ya faru tsakaninsa da kaza ne ya hanata bacci, ya tattaro murmushin ƙarfin hali ya ce: "Me ya hana ki bacci Walida?" Walida ta sake sakin hamma sannan ta ce, "Ga jikina duk tsami yake na so huce gajiyata amma haka bata samu ba, amma zan sake gwada sa'ata anjima." Khalid na shirin yin magana wayarsa ta fara ƙara. Lambar mahaifinsa ya gani da mamaki ya ɗauka don lokacin ko tara bata yi ba. Cikin girmamawa ya ɗauka da sallama, tun bai rufe baki ba Mahaifinsa ya rufe shi da faɗa. "Kai wanne irin mara hankali ne? Kai ka haifi kanka da ba za a gaya magana kaji ba? Tsabar ka raina mutane ba sai da nace maka yarinyar nan babu inda za ka da ita amma ka mayar da ni ɗan iska ko? Wallahi tun wuri ka haɗa kayanta ka dawo da ita ina dalili ka ɗauki son duniya ka ɗorawa yarinya, a daren aurenka ka ce za ka tare da ita." Khalid ban da gyaɗa kai ba abin da yake yi. Sai da mahaifinsa ya gama magana sannan ya zayyane masa duk abin da yake faruwa. Da farko bai yarda ba sai da ya ce a bawa Zarah tukunna, Zarah na karɓar wayar ta sakawa Mahaifin Khalid kuka ita ma ta ƙara yi masa jawabi. Wayar ta miƙa wa Khalid, murya a sanyaye ya ce: "Baba yanzu haka mun kasa buɗe ƙofar wallahi tsoro muke ji don Allah ku taho daga gida ka taho da su Halifa su haura ta katanga, idan kuka zo sai mu fito amma wallahi tsoro muke ji." Hankalin Mahaifin Khalid ba ƙaramin tashi ya yi ba, a gaggauce ya ce masa: "Ba damuwa gamu nan zuwa." Khalid na gama waya Zarah ta kira mahaifiyarta ita ma ta sanar mata abin da yake faruwa, hankali a tashe Mahaifiyar Zarah ta sanarwa da Mahifin Zarah nan take suma suka ce ga su nan tafe zuwa gidan. Walida na daga bakin ƙofa bayan sun gama wayar ta sake buga ƙofar ta ce, "Uncle buɗe min na shigo man." Takaici ya kama Zarah don yanda take jin haushin Walida ji take kamar ta janyota ta hau dukanta. Sai da Khalid ya sake leƙawa ta window sannan ya buɗe ƙofar da sauri ya fisgo hannun Walida ya datse ƙofar. Walida ta samu wuri a gefen katifa ta zauna tana kallon Zarah da take wurga mata harara ta ce, "Aunty ba dai gida za ki tafi ba." A ƙufule Zarah ta ce, "Idan gidan ubanki ne zai ki hana ni tafiya." Khalid ya ɗan ɓata fuska ya ce, "Haba Dear me ya sa kike haka ne." Zarah ta ɗauke kai gefe ba tare da ta kula shi ba. Bayan wani lokaci. Bugun ƙofa suka fara ji wanda ya nuna musu alamar Mahaifansu Khalid da Zarah sun ƙaraso ƙofar gidan, wayar Zarah ce ta fara ringing da sauri ta ɗauka. Daga can ɓangaren Mama ta fara cewa, "Zarah ga mu da su Haruna sai iyayen mijinki ko haurowa za a yi ne." Tun Mama bata gama magana ba Zarah ta ce, "Mama a hauro don Allah." Mama na jin haka ta katse wayar. Walida ta kishingiɗa kamar wata babba ta miƙa hannu ta dafa kafaɗar Khalid ta ce, "Khalid!" Lokaci ɗaya suka kalli Walida shi da Zarah don yanda ta yi maganar kaɗai sai da ya basu mamaki. Walida bata damu ba ta ci gaba da cewa, "Allah ya sani ka lasa min zuma a baka, ina ji ina gani za ka tsere min ne? Sam ba zai yuwu ba Angona." Khalid da sauri ya matsa jikin Zarah ya maƙaleta. Yana shirin yin magana ya riski muryar Walida na ci gaba da cewa, "Ka ba ni haɗin kai ko yanzu na yi maka fyaɗe don na jima ina jiran wannan lokacin jiya ka kubce min, amma yau ba a yi haka ba." Kuna son more barkwanci ko kina cikin damuwa zuciyarki ta yi wasai💃🏼 ki nemi littafin *DUBU JIKAR MAI CARBI* Cmplt ɗinsa 300 kacal🥱 Ki ji yadda ake tafka kishi tsakanin matar aljani da bil'adam, zallar soyayyar Aljani da ɗaukan darrusa nemi littafin *ZAUJATU JINNUL-ASHIQ*🤒 300 ne rak karki bari a yi babu ke. Sarƙaƙiya, makirci da rikicin masarauta. Ki ji yadda ake rayuwa da ruhin mutum uku, sannan kuma a ɗauki fansa da kowanne ruhi. Izzar mulki da rayuwar masarauta ki nemi *AN YA BAIWA CE* Cmplt 300 ne 🥱 Ki siya ki huta nema a groups💃🏼 Aisha Adam 3090957579 Firstbank 0706 206 2624 turo da evidence🥱 Ummou Aslam Bint Adam🌚*'YAR ZAMAN ƊAKI* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Ban amince a sauya min littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, don haka a kiyaye.⚠️ 13&14 AMNASH BAKERY PRACTICAL CLASS Mun ɗaura ɗamarar koyar da sana'o'in gashe-gashe da girke-girke kamar: VANILLA CAKE, DOUGHNUT, CHINCHIN, MEATFIE, COOKIES, CHICKEN NUGHET, BIRTHDAY CAKE, CAKE PERFAIT da sauran girke-girken sari a farashi mai rahusa 5K kacal domin masu farawa daga farko. ADDRESS: NO EA70 TITIN ADAMU ƊAN KURA GANDU KAFIN GIDAN BASHIR TOFA OPPOSITE MASALLACIN ƘADIRIYYA. KANO STATE MUNINCIPAL L.G PHONE NUMBER: 07038826617 for watsapp and call. KU GARZAYO KU KARƁI SAMI FORM ƊINKU DON KAR WANNAN DAMAR TA WUCE KU. Zarah ba ƙaramin mamaki ta yi da jin maganar da Walida ta yi ba, haɗe fuska ta sake yi ta dubi Khalid ta ce, "Dama shi ya sa ka nace sai ka ɗauko yarinyar nan? Dubi yarinya ƙarama yadda take faɗar maganganu marasa ɗa'a, an ya Khalid baka lalubar yarinyar nan a bayan fage? Idan ba haka ba ya za a yi ta faɗi haka?" Khalid ya yi fiƙi-fiƙi da ido don abin ba ƙaramin ɗaure masa kai ya yi ba. Khalid ya kalli Walida fuska a haɗe ya ce, "Ke Walida yaushe muka yi haka da ke? Baki da kunya ne an gaya miki ana gayawa babba haka?" Walida ta yi wani faarrr da ido ta sake kashe murya ta ce, "Kabar kewaye-kewaye ka matso ka bani haɗin kai saboda tun jiya na yi niyyar mayar da kai Zakara Allah bai nufa ba. Ni fa a duk cikin zakarun da na aura kai ka bani wahala." Cikin Khalid ne ya bada sautin ƙuuuuu! Har sai da suka haɗa ido da Zarah. Tsoro ya fara kama shi don maganganun Walida kama suke yi masa da na Kazar daren jiya. Ita kanta Zarah ayar tambaya ta fara ɗora wa Walida don haka ta ja bakinta ta tsuke, babban burinta mutanen gidansu su shigo ta buɗe ƙofa ta fita don ta ci alwashin ko auren ne tana iya haƙura da Khalid. Khalid haɗe fuska ya yi shi a dole yana son nuna dakiya don kar ta fahimci ya tsorata, yana shirin yin magana ya ga Walida ta tsugunna a wurin ta fara kyarkyara. Hannu ta zura ta ɗebo kwayaye kaji manya guda huɗu ta ce, "Ungo Zarah je ki soya min su." Daga Khalid Har Zarah baya suka yi jikinsu na karkarwa, Zarah ta nuna Walida baki na rawa ta ce, "Ko kece kazar ne?" Walida sake sako ƙwai uku sannan ta ce, "Ni ce kaza shi kuma a yanzu ba sai anjima ba zai koma Zakara." Khalid na jin haka ya maƙale Zarah hawaye na bin fuskarsa ya ce, "Zarah ki taimaka min don Allah za ta mayar da ni zakara, wallahi jiya ganin idona na ga Zakaru suna magana." Walida ta karɓe zancensa da cewar, "Ita ma ba sha za ta yi ba, don jiya dama Ƙanina Ɗanliti ya so yin gaba da ita dukkanku babu mai fita daga gidan nan. Suma waɗanda kuka kira ɗin su ƙaraso ina nan jiransu." Walida na gama magana suka ji muryar su Mama a cikin gidan da alama har sun saka an hauro gidan. Wata gauruwar ajiyar zuciya suka sauke a tare don gani suke mafita ta zo musu, Walida na ganin haka ta yi tsalle sai ga ta fuurrrrr ta koma ƙatuwar kazar daren jiya tana buɗa fuka-fiki. Zarah da Khalid a tare suka yi baya cike da tsoro, kazar ta fara takawa gabansu gashin jikinta na saɓulewa sannan ta ce, "Ku dube ni da kyau, wallahi duk wanda ya tona asirina a gaban mutanen nan ba gida ba ko ina kuka koma sai na biku na hallaka ku." Khalid sai gyaɗa kai yake kamar kaɗangare. Zarah ba bakin magana sai ruwan hawaye, Kaza ta yi girgiza sai gashi ta dawo siffarta ta Walida. A daidai lokacin Mama ta ƙaraso wurin ƙofar, Walida da kanta ta buɗe ƙofar ɗakin Mahaifiyar Khalid na ganinta ta ce, "Walin Walin 'Yan zaman ɗaki antashi ƙalau?" Walida ta yi murmushi ta ce, "Mama ya ce muje falo." Mama ta waiga ta ce, "Halifa ka ce da su Babanku da Hajiya Amina su shigo." Tana gama magana suka wuce Falon, shigar su babu wuya sai ga Zarah da Khalid sun shiga, lokaci ɗaya falon ya cika maƙil sukan su goma a ɗakin, iyayen Zarah da Khalid sai ƙannensu. Mahaifin Khalid ya dubi Mahaifin Zarah ya ce, "Alhaji ya muka ji da abin da yaran nan suka gaya mana?" Mahaifin Zarah ya ce, "Wannan aikin shaiɗu ne kawai, ta yuwu ba a yi wa gidan sauka ba shi ya sa suke son hana zama a ciki." Mahaifin Khalid yana shirin yin magana ya hango giftawar saluɓaɓɓan zakara ya wuce ko gashi ɗaya babu a jikinsa yana tafe yana jan buhun shinkafa, da sauri ya kauda idonsa don ya san shi ma buɗe masa ido suka yi. Halifa na daga gefe ya yi dariya ya ce, "Ni fa wallahi Abba duk jin su nake, ya za a yi a ce wai kaza har ta yi magana kawai dai sun ruɗa kansu ne." Khalid da Zarah suka kalli juna suka sunkuyar da kai ƙasa, Mahaifiyar Khalid ta ce, "Amma dai Allah sakawa yaran nan wannan wacce irin la'ananniyar kaza ce za ta hana yara sukuni." Khalid ya ɗago ya kalli Walida sannan ya kalli Mahaifiyarsa ya ce, "A yi dai abin da za a yi amma don Allah a daina zagin kazar nan tana jin ku." Gabaɗaya suka saki baki suna kallon Khalid da duk ya yi zuru-zuru, Mahaifiyarsa dama irin mutanan nan ne masu faɗa ta sake cewa, "Zagin kazar wani zunubi ne ban da la'ananniya ka ƙere gida kamar wannan amma ta riƙa tsorata ku wai har da wani tsinannan zakara. Wallahi ka ji jiki Khalid da baka bige shegiya ka karya ƙafafuwanta ba." Mama na yin shiru Mahaifin Khalid ya sake hango wani saluɓaɓɓan zakaran ya zo wucewa kansa ɗauke da tukunya yana tafiya. Cikin Abba ne ya fara kaɗawa, Khalid zai yi magana Baba ya ce, "Yanzu dai ku zo mu wuce gida su Kaji daraja gare su, ƙimarsu har ta fi ta mutum shi ya sa ko namansu ya fi na komai daɗi. Allah dai ya yi musu albarka." Walida na daga wurin da take ta ce, "Baba ai kun zo kenan, kai kanka yawuna ya tsinke da kai kaima ina jin zakaran za ka koma. Na ji daɗin kalamanka kaine mijin da zan aura na tara." Halifa na kusa da ita ya zabga mata mari dama ya jima yana jin haushinta tun lokacin da Khalid ya kawota. Cikin faɗa ya ce, "Wai ke baki da mutumci waye sa'anki? Yaya Khalid shi ya ɗaure miki kike iskanci dama." Khalid ya girgizawa Halifa kai ya ce, "Ummm-Ummm Halifa wallahi yanzu za ka iya komawa zakara ka yi ta kanka." Walida ta kalli kusuwar bangon ɗakin ta ce, "Ɗanladi" Tana rufe baki sai ga wani dogon zakara ya fito yana miƙa wuya gaba jikinsa babu gashi ko ɗaya." Mama na ganin haka ta maƙale Mahaifin Zarah duk a tunaninta Mijinta ne ta ce, "La'ilaha'illallahu. Kai Khalid baka ce min haka sheɗanun gidan suke." Walida ta dubi Zakaran ta ce, "Ɗanladi je ka tsattsage wa Halifa gemu sai ka cire shi tass idan ka gama da gemun ka koma kansa." Tana rufe baki zakaran ya ce, "Dama yunwa nake ji babbar yaya." Halifa na jin haka ya sa hannu ya dafe gemu ya ce, "Ku taimaka min Ɗanladi zai tsattsage ni." 😂 Ku yo ɗauki kun san a cikin Kaji har da wanzamai😂😂 Kuna son more barkwanci ko kina cikin damuwa zuciyarki ta yi wasai💃🏼 ki nemi littafin *DUBU JIKAR MAI CARBI* Cmplt ɗinsa 300 kacal🥱 Ki ji yadda ake tafka kishi tsakanin matar aljani da bil'adam, zallar soyayyar Aljani da ɗaukan darrusa nemi littafin *ZAUJATU JINNUL-ASHIQ*🤒 300 ne rak karki bari a yi babu ke. Sarƙaƙiya, makirci da rikicin masarauta. Ki ji yadda ake rayuwa da ruhin mutum uku, sannan kuma a ɗauki fansa da kowanne ruhi. Izzar mulki da rayuwar masarauta ki nemi *AN YA BAIWA CE* Cmplt 300 ne 🥱 Ki siya ki huta nema a groups💃🏼 Aisha Adam 3090957579 Firstbank 0706 206 2624 turo da evidence🥱 Ummou Aslam Bint Adam🌚*'YAR ZAMAN ƊAKI* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Ban amince a sauya min littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, don haka a kiyaye.⚠️ 13&14 AMNASH BAKERY PRACTICAL CLASS Mun ɗaura ɗamarar koyar da sana'o'in gashe-gashe da girke-girke kamar: VANILLA CAKE, DOUGHNUT, CHINCHIN, MEATFIE, COOKIES, CHICKEN NUGHET, BIRTHDAY CAKE, CAKE PERFAIT da sauran girke-girken sari a farashi mai rahusa 5K kacal domin masu farawa daga farko. ADDRESS: NO EA70 TITIN ADAMU ƊAN KURA GANDU KAFIN GIDAN BASHIR TOFA OPPOSITE MASALLACIN ƘADIRIYYA. KANO STATE MUNINCIPAL L.G PHONE NUMBER: 07038826617 for watsapp and call. KU GARZAYO KU KARƁI SAMI FORM ƊINKU DON KAR WANNAN DAMAR TA WUCE KU. Zarah ba ƙaramin mamaki ta yi da jin maganar da Walida ta yi ba, haɗe fuska ta sake yi ta dubi Khalid ta ce, "Dama shi ya sa ka nace sai ka ɗauko yarinyar nan? Dubi yarinya ƙarama yadda take faɗar maganganu marasa ɗa'a, an ya Khalid baka lalubar yarinyar nan a bayan fage? Idan ba haka ba ya za a yi ta faɗi haka?" Khalid ya yi fiƙi-fiƙi da ido don abin ba ƙaramin ɗaure masa kai ya yi ba. Khalid ya kalli Walida fuska a haɗe ya ce, "Ke Walida yaushe muka yi haka da ke? Baki da kunya ne an gaya miki ana gayawa babba haka?" Walida ta yi wani faarrr da ido ta sake kashe murya ta ce, "Kabar kewaye-kewaye ka matso ka bani haɗin kai saboda tun jiya na yi niyyar mayar da kai Zakara Allah bai nufa ba. Ni fa a duk cikin zakarun da na aura kai ka bani wahala." Cikin Khalid ne ya bada sautin ƙuuuuu! Har sai da suka haɗa ido da Zarah. Tsoro ya fara kama shi don maganganun Walida kama suke yi masa da na Kazar daren jiya. Ita kanta Zarah ayar tambaya ta fara ɗora wa Walida don haka ta ja bakinta ta tsuke, babban burinta mutanen gidansu su shigo ta buɗe ƙofa ta fita don ta ci alwashin ko auren ne tana iya haƙura da Khalid. Khalid haɗe fuska ya yi shi a dole yana son nuna dakiya don kar ta fahimci ya tsorata, yana shirin yin magana ya ga Walida ta tsugunna a wurin ta fara kyarkyara. Hannu ta zura ta ɗebo kwayaye kaji manya guda huɗu ta ce, "Ungo Zarah je ki soya min su." Daga Khalid Har Zarah baya suka yi jikinsu na karkarwa, Zarah ta nuna Walida baki na rawa ta ce, "Ko kece kazar ne?" Walida sake sako ƙwai uku sannan ta ce, "Ni ce kaza shi kuma a yanzu ba sai anjima ba zai koma Zakara." Khalid na jin haka ya maƙale Zarah hawaye na bin fuskarsa ya ce, "Zarah ki taimaka min don Allah za ta mayar da ni zakara, wallahi jiya ganin idona na ga Zakaru suna magana." Walida ta karɓe zancensa da cewar, "Ita ma ba sha za ta yi ba, don jiya dama Ƙanina Ɗanliti ya so yin gaba da ita dukkanku babu mai fita daga gidan nan. Suma waɗanda kuka kira ɗin su ƙaraso ina nan jiransu." Walida na gama magana suka ji muryar su Mama a cikin gidan da alama har sun saka an hauro gidan. Wata gauruwar ajiyar zuciya suka sauke a tare don gani suke mafita ta zo musu, Walida na ganin haka ta yi tsalle sai ga ta fuurrrrr ta koma ƙatuwar kazar daren jiya tana buɗa fuka-fiki. Zarah da Khalid a tare suka yi baya cike da tsoro, kazar ta fara takawa gabansu gashin jikinta na saɓulewa sannan ta ce, "Ku dube ni da kyau, wallahi duk wanda ya tona asirina a gaban mutanen nan ba gida ba ko ina kuka koma sai na biku na hallaka ku." Khalid sai gyaɗa kai yake kamar kaɗangare. Zarah ba bakin magana sai ruwan hawaye, Kaza ta yi girgiza sai gashi ta dawo siffarta ta Walida. A daidai lokacin Mama ta ƙaraso wurin ƙofar, Walida da kanta ta buɗe ƙofar ɗakin Mahaifiyar Khalid na ganinta ta ce, "Walin Walin 'Yan zaman ɗaki antashi ƙalau?" Walida ta yi murmushi ta ce, "Mama ya ce muje falo." Mama ta waiga ta ce, "Halifa ka ce da su Babanku da Hajiya Amina su shigo." Tana gama magana suka wuce Falon, shigar su babu wuya sai ga Zarah da Khalid sun shiga, lokaci ɗaya falon ya cika maƙil sukan su goma a ɗakin, iyayen Zarah da Khalid sai ƙannensu. Mahaifin Khalid ya dubi Mahaifin Zarah ya ce, "Alhaji ya muka ji da abin da yaran nan suka gaya mana?" Mahaifin Zarah ya ce, "Wannan aikin shaiɗu ne kawai, ta yuwu ba a yi wa gidan sauka ba shi ya sa suke son hana zama a ciki." Mahaifin Khalid yana shirin yin magana ya hango giftawar saluɓaɓɓan zakara ya wuce ko gashi ɗaya babu a jikinsa yana tafe yana jan buhun shinkafa, da sauri ya kauda idonsa don ya san shi ma buɗe masa ido suka yi. Halifa na daga gefe ya yi dariya ya ce, "Ni fa wallahi Abba duk jin su nake, ya za a yi a ce wai kaza har ta yi magana kawai dai sun ruɗa kansu ne." Khalid da Zarah suka kalli juna suka sunkuyar da kai ƙasa, Mahaifiyar Khalid ta ce, "Amma dai Allah sakawa yaran nan wannan wacce irin la'ananniyar kaza ce za ta hana yara sukuni." Khalid ya ɗago ya kalli Walida sannan ya kalli Mahaifiyarsa ya ce, "A yi dai abin da za a yi amma don Allah a daina zagin kazar nan tana jin ku." Gabaɗaya suka saki baki suna kallon Khalid da duk ya yi zuru-zuru, Mahaifiyarsa dama irin mutanan nan ne masu faɗa ta sake cewa, "Zagin kazar wani zunubi ne ban da la'ananniya ka ƙere gida kamar wannan amma ta riƙa tsorata ku wai har da wani tsinannan zakara. Wallahi ka ji jiki Khalid da baka bige shegiya ka karya ƙafafuwanta ba." Mama na yin shiru Mahaifin Khalid ya sake hango wani saluɓaɓɓan zakaran ya zo wucewa kansa ɗauke da tukunya yana tafiya. Cikin Abba ne ya fara kaɗawa, Khalid zai yi magana Baba ya ce, "Yanzu dai ku zo mu wuce gida su Kaji daraja gare su, ƙimarsu har ta fi ta mutum shi ya sa ko namansu ya fi na komai daɗi. Allah dai ya yi musu albarka." Walida na daga wurin da take ta ce, "Baba ai kun zo kenan, kai kanka yawuna ya tsinke da kai kaima ina jin zakaran za ka koma. Na ji daɗin kalamanka kaine mijin da zan aura na tara." Halifa na kusa da ita ya zabga mata mari dama ya jima yana jin haushinta tun lokacin da Khalid ya kawota. Cikin faɗa ya ce, "Wai ke baki da mutumci waye sa'anki? Yaya Khalid shi ya ɗaure miki kike iskanci dama." Khalid ya girgizawa Halifa kai ya ce, "Ummm-Ummm Halifa wallahi yanzu za ka iya komawa zakara ka yi ta kanka." Walida ta kalli kusuwar bangon ɗakin ta ce, "Ɗanladi" Tana rufe baki sai ga wani dogon zakara ya fito yana miƙa wuya gaba jikinsa babu gashi ko ɗaya." Mama na ganin haka ta maƙale Mahaifin Zarah duk a tunaninta Mijinta ne ta ce, "La'ilaha'illallahu. Kai Khalid baka ce min haka sheɗanun gidan suke." Walida ta dubi Zakaran ta ce, "Ɗanladi je ka tsattsage wa Halifa gemu sai ka cire shi tass idan ka gama da gemun ka koma kansa." Tana rufe baki zakaran ya ce, "Dama yunwa nake ji babbar yaya." Halifa na jin haka ya sa hannu ya dafe gemu ya ce, "Ku taimaka min Ɗanladi zai tsattsage ni." 😂 Ku yo ɗauki kun san a cikin Kaji har da wanzamai😂😂 Kuna son more barkwanci ko kina cikin damuwa zuciyarki ta yi wasai💃🏼 ki nemi littafin *DUBU JIKAR MAI CARBI* Cmplt ɗinsa 300 kacal🥱 Ki ji yadda ake tafka kishi tsakanin matar aljani da bil'adam, zallar soyayyar Aljani da ɗaukan darrusa nemi littafin *ZAUJATU JINNUL-ASHIQ*🤒 300 ne rak karki bari a yi babu ke. Sarƙaƙiya, makirci da rikicin masarauta. Ki ji yadda ake rayuwa da ruhin mutum uku, sannan kuma a ɗauki fansa da kowanne ruhi. Izzar mulki da rayuwar masarauta ki nemi *AN YA BAIWA CE* Cmplt 300 ne 🥱 Ki siya ki huta nema a groups💃🏼 Aisha Adam 3090957579 Firstbank 0706 206 2624 turo da evidence🥱 Ummou Aslam Bint Adam🌚http://www.amiraadam.com.ng/2022/08/yar-zaman-aki_26.html *'YAR ZAMAN ƊAKI* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Ban amince a sauya min littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, don haka a kiyaye.⚠️ 15&16 AMNASH BAKERY PRACTICAL CLASS Mun ɗaura ɗamarar koyar da sana'o'in gashe-gashe da girke-girke kamar: VANILLA CAKE, DOUGHNUT, CHINCHIN, MEATFIE, COOKIES, CHICKEN NUGHET, BIRTHDAY CAKE, CAKE PERFAIT da sauran girke-girken sari a farashi mai rahusa 5K kacal domin masu farawa daga farko. ADDRESS: NO EA70 TITIN ADAMU ƊAN KURA GANDU KAFIN GIDAN BASHIR TOFA OPPOSITE MASALLACIN ƘADIRIYYA. KANO STATE MUNINCIPAL L.G PHONE NUMBER: 07038826617 for watsapp and call. KU GARZAYO KU KARƁI SAMI FORM ƊINKU DON KAR WANNAN DAMAR TA WUCE KU. Ɗanladi ya fara tafiya yana miƙa wuya gaba ya buga tsalle ya haye kafaɗar Halifa ya fara kai caki gemunsa, Halifa na jin haka ya ƙwallah ƙara ya fara kiciniyar kare gemunsa. Walida ta sake kallon kusurwar bango ta ce, "Ɗan lasan!" Tun bata rufe baki ba Sai ga wani dogon zakara tsayinsa zai yi tsayin yaro ɗan shekara goma sha biyu. Shi kuma yana fitowa tun Walida bata bashi umarni ba ya fara baza hanci yana shinshine-shinshine, da sauri ya buga tsalle yana shirin kai wa Mahaifiyar Khalid cafka, Walida ta buga masa tsawa da cewar, "Kai Ɗan lasan ka kama kanka bana buƙatar rawar kai, ka san aikinka yanzu?" Ɗan lasan ya ware idanu akan Mahaifiyar Khalid ya ce, "Idan kika bar min wannan ma kaɗai ta isa, don da ganinta babban kai ce." Ga link nan ku bi don ci gaban labarin💃🏼 Masu tambayata ko littafin kuɗi ne, na faɗa tun shafin farko littafin nan freebook ne🤒http://www.amiraadam.com.ng/2022/08/yar-zaman-aki-page-17.html *'YAR ZAMAN ƊAKI* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Ban amince a sauya min littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, don haka a kiyaye.⚠️ 17&18 AMNASH BAKERY PRACTICAL CLASS Mun ɗaura ɗamarar koyar da sana'o'in gashe-gashe da girke-girke kamar: VANILLA CAKE, DOUGHNUT, CHINCHIN, MEATFIE, COOKIES, CHICKEN NUGHET, BIRTHDAY CAKE, CAKE PERFAIT da sauran girke-girken sari a farashi mai rahusa 5K kacal domin masu farawa daga farko. ADDRESS: NO EA70 TITIN ADAMU ƊAN KURA GANDU KAFIN GIDAN BASHIR TOFA OPPOSITE MASALLACIN ƘADIRIYYA. KANO STATE MUNINCIPAL L.G PHONE NUMBER: 07038826617 for watsapp and call. KU GARZAYO KU KARƁI SAMI FORM ƊINKU DON KAR WANNAN DAMAR TA WUCE KU. Jin carar da Khalid ya yi ya sa Balele tuntsirewa da dariya har da riƙe ciki, wata gajeriya kaza ce ta ɓullo ta ƙarƙashin ƙasa tafe tana ɗingisawa. Ɗan lasan na ganinta ya ce, "Ke ƴar chogal me ya kawo ki keda ba a gayyace ki ba?" Kazar ta sake chogala ƙafa ɗaya ta ce, "Kale na zo don kasan ba za a yi babu ni ba." Ƴar chogal na gama magana ta nufin ƙofar da Walida ta shige da Khalid, sai da ta kara kunnenta a wurin ta ce, "Babbar yaya don Allah idan kin gama da Angon naki ki bani ɗani ko siɗin kwano na samu." Walida na daga cikin ɗaki ta ce, "Duk cikin Angwayen da nake samu babu fitacce zazzafa kamar wannan, idan baki ba ni wuri ba ranki zai yi mummunan ɓaci." Ƴar chogal na jin haka ta matsa da baya har ta yi niyyar tafiya sai ta hango Mahaifin Zarah a zaune suna ta kiciniya da Ɗanlasan. Mahaifiyar Khalid duk ta yi zuru-zuru don Ɗanlasan kai caki yake yi mata ta ko'ina, shi kuwa mahaifin Zarah na zaune ya miƙa wa Allah lamuransa sai kabarbari yake. Cikinsa gabaɗaya Ɗanlasan ya caccake shi, ban da raɗaɗi da zugi babu abin da yake yi masa. Halifa na maƙale a hannun Ɗanladi ya taƙarƙare ya kaiwa Ɗanladi duka a kansa. Lokaci ɗaya ya ga Ɗanladi ya faɗi gefe, kamar yadda tangaran yake fashewa haka ya ga Ɗanladi ya wargaje ya yi ɗaiɗai. Farinciki ne ya kama Halifa yana miƙe wa tsaye ya fara shafo geminsa sai ji ya yi fayau babu gashi a jiki, abin da ya ɗaga masa hankali ganin jini na bin hannunsa. Motsi ya fara ji kamar na ƙarar ƙarafuna yana kallon wurin da Ɗan ladii yake ya ga ya fara haɗe gaɓoɓin jikinsa, tsoro na ya sake kama Halifa yana shirin guduwa Ƴar chogal ta yi tsalle ta cafo Halifa tana cewa: "Ɗanlami ka gama da wannan kayan na yi gaba da shi?" Halifa na jin an ce za a yi gaba da shi ba shiri ya fara sakin fitsari a wando, hawaye na zuba ya ce:" Aunty 'yar chogal don Allah ki yi min rai." Ƴar chogal daɗi ya kama ta don ta san ko ba koma za ta yi kalace da Halifa. Ɗan Lasan sai da ya ƙare wa Mama kallo ya ce, "Ki ba ni Mama na sha idan ba haka ba zan sauke su ƙasa." Mahaifiyar Khalid na jin haka ta sake fashe wa da kuka ta ce, "Yaro ka dubi girman Allah kar ka yi mini haka." Ƙarar bugun gate ne ya karaɗe ɗakin don da alama su su Zarah sun kasa buɗe ƙofa ta ƙi buɗuwa, Ɗan lasan ya buga tsalle ya faɗa kitchen ɗin Zarah, Mama na shirin arcewa sai ga shi ya dawo hannunsa ɗauke da sharɓeɓiyar wuƙa. A gaban Mama ya tsaya ya ce, "Ki ban na zuƙe ko kawai na farke ki da wannan." Kafin Mama ta yi wani yunƙuri suka riski Ƴar chogal na cewa Halifa. "Haba matashin saurayi ka ba ni haɗin kai mana, ni ban damu da sai na mayar da kai zakara ba amma idan ka ba ni haɗin kai daga yau muzuru za ka koma, sai mu ci karenmu babu babbaka." Halifa yana shirin ja da baya sai ji suka yi Baaaam an banko ƙofar da ƙarfi. Halifa na kai idonsa wurin ya ci karo da wani tsololon zakara, tsayinsa zai kai yaro ɗan shekara goma. Jikinsa a saluɓe yake babu gashi sai tozon kansa da aka liƙawa wata tuta, kallon mutanen wurin ya fara yi ɗaiɗai. A tsorace Halifa ya ja baya don ya yi tsammanin kansa zai sake yowa, Mama da Mahaifin Zarah suka yi saranda suna jiran ko ta kwana. Zakaran yana nan tsaye suka ga ya fara tsalle yana ɗaga saluɓaɓɓun fukafukansa. Kaza ce ta turo ƙofa tana tafe tana kwarkwasa, ganin haka ya sa Zakaran ya ce, "Kai Halifa ku zo mu gudu kafin su halaka mu." Da mamaki Halifa ya dubi Khalid ya ce, "Khalid kaima ka koma Zakaran ne?" Khalid ya yo kan Halifa ya ce, "Don ubanka na ce ka zo mu gudu kana min zancen zakara." Ganin zakaran mai ban tsoro ya yo kan Halifa ya sa gabaɗaya suka ɗiba a guje suka nufi hanyar gate. Khalid ya ke cikin siffar Zakara ya rufa musu baya, Kaza ta bi bayansa tana faɗin, "Angona ina za ka tafi ka bar ni, ai ni da kai mutu ka raba." Na Samu ƙorafi akan link ɗin rannan da na saka, zan ci gaba da typing amma ba kullin zan ke saka wa ta whatsapp ba. Idan wannan page ɗin an karanta da whatsapp next page sai a tafi duniyar Chrome wato a bi link🤒 Kuna son more barkwanci ko kina cikin damuwa zuciyarki ta yi wasai💃🏼 ki nemi littafin *DUBU JIKAR MAI CARBI* Cmplt ɗinsa 300 kacal🥱 Ki ji yadda ake tafka kishi tsakanin matar aljani da bil'adam, zallar soyayyar Aljani da ɗaukan darrusa nemi littafin *ZAUJATU JINNUL-ASHIQ*🤒 300 ne rak karki bari a yi babu ke. Sarƙaƙiya, makirci da rikicin masarauta. Ki ji yadda ake rayuwa da ruhin mutum uku, sannan kuma a ɗauki fansa da kowanne ruhi. Izzar mulki da rayuwar masarauta ki nemi *AN YA BAIWA CE* Cmplt 300 ne 🥱 Ki siya ki huta nema a groups💃🏼 Aisha Adam 3090957579 Firstbank 0706 206 2624 turo da evidence🥱http://www.amiraadam.com.ng/2022/08/yar-zaman-aki-end.html *'YAR ZAMAN ƊAKI* ©AMEERA ADAM *FIRST CLASS WRITER'S ASSO...* Ban amince a sauya min littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, don haka a kiyaye.⚠️ 🔚🔚🔚🔚🔚 AMNASH BAKERY PRACTICAL CLASS Mun ɗaura ɗamarar koyar da sana'o'in gashe-gashe da girke-girke kamar: VANILLA CAKE, DOUGHNUT, CHINCHIN, MEATFIE, COOKIES, CHICKEN NUGHET, BIRTHDAY CAKE, CAKE PERFAIT da sauran girke-girken sari a farashi mai rahusa 5K kacal domin masu farawa daga farko. ADDRESS: NO EA70 TITIN ADAMU ƊAN KURA GANDU KAFIN GIDAN BASHIR TOFA OPPOSITE MASALLACIN ƘADIRIYYA. KANO STATE MUNINCIPAL L.G PHONE NUMBER: 07038826617 for watsapp and call. KU GARZAYO KU KARƁI SAMI FORM ƊINKU DON KAR WANNAN DAMAR TA WUCE KU. Lokacin da su Halifa suka je bakin gate a daidai lokacin Allah ya bawa su Zarah nasarar ficewa daga gidan. Su Halifa suma suna zuwa sula rufa musi baya, Khalid na zuwa bai yi wata-wata ba ya fice yana ƙwala musu kira amma ko waige babu wanda ya yi balle ya saka ran za su kula shi. Kaza da sauri ta buɗe ƙofar ta rufa wa Khalid baya tana tafe tana faɗin, "Angona ka zo mu sasanta don Allah." Khalid bai bi ta kanta ba suka ci gaba da zabga gudu. Da yake unguwar ta su babu nisa da gidan Khalid nan take suka ƙarasa gida, sai dai wannan karon hatta iyayen Zarah da ita gidan su Khalid suka faɗa, Malam Liman yana ƙofar gida ya riƙa kallon su da mamaki, bai tsinke da lamarin ba sai da ya hango Mahaifin Khalid da Halifa suna tafe zakara da kaza na biye da su. A madadin Mahaifin Khalid ya faɗa gidan sai ya maƙale Malam Liman ya ce, "Don Allah Malam ka taimaka mana yaron nan Khalid ya janyo nana masifa." Malam Liman zai yi magana karaf suka ji kazaran ya ce, "Abba wallahi sharrin shaiɗan da na Mai turakar aljanu." Malam Liman ya zaro ido waje ya ce, "Me nake gani haka kamar zakara yana magana?" Abba ya ce, "Malam mu je ciki wallahi akwai magana, wai Khalid ne fa ya koma zakara." Ku bi link don jin yadda turka-turkar ta ƙare💃🏼 Wai ma Wacece Walida? Ya ka yi Khalid ya samo ta? Wannan ne shafin ƙarshe shi zai warware muku komai💃🏼 Son so nake muku fisabilillah🥰🌚