*Shimfiɗa...* Akwai wasu ƙaddarorin da kan zo da wani irin duhu, wanda zai mamaye rayuwar ɗan adam, ta yanda ko da tafin hannunsa ba zai iya gani a cikin wannan duhun ba. Kuma an ce HASKE ne kaɗai ke maganin duhu. Ɗan adam kan shiga halin neman HASKEn da zai yi amfani da shi wurin gusar da wannan duhun dake bibiyar rayuwarsa. Shin menene duhun? Wasu tarin ƙaddarori ne waɗannan da ke tafe da matsanancin duhu?. Shin a ina wannan HASKEn yake? Sannan kuma menene wannan HASKEn? *💡HASKE...💡* _(Maganin duhu!)_ *©SALMA AHMAD ISAH* TAURARI WRITER'S ASSOCIATION. بسم الله الر حمن الر حيم* *Page 01* __(★★)__ *Shekara ta 2000.* *Makoko, Lagos State, Nigeria.* *01:40 Na dare.* Wata matace ke tafe cikin sassarfa, sanye take da atamafa kalar ruwan goro, wanda akewa laƙabi da me dalma. Hannunta riƙe da wani abu, wanda ke duƙunƙune cikin zani. Kanta ta ɗan ɗaga ta kalli sararin samaniya, ta ga yanda hadari yake gangamuwa, ga kuma iska me ƙarfi da aka fara, sai cida da tsawa da ake har da walƙiya. Ƙafafuwanta ne suka taka birki, a lokacin da ta kawo gaɓar ruwan shiga yankin Makoko. Tarin kwale-kwalen dake bakin ruwan ta kalla, sannan ta kalli abun da ke hannunta. Hawaye na bin fuskarta ta girgiza kai tana faɗin. “Ba zan iya aikata haka ba!” Sai kuma ta shiga juyawa tana kallon kewayen wurin da take, babu kowa sai gilmawar karnuka. haka ta nufi wani kwale-kwale dake cikin tarin kwale-kwalen dake wurin, ta shiga cikin kwale-kwalen ba tare da tsoro ba, ta tsuganna tana aje abinda ke hannunta. Kafin a hankali ta kai hannunta kan zanin, ta buɗe shi, nan take fuskar jaririya sabuwar haihuwa ta bayyana, don da alama yanzu ta zo duniya, saboda ko jinin haihuwarta bai bushe daga jikinta ba. Fuskar yarinyar ta ƙara rufewa da zanin, ta ɗora wata sarƙar ƙafa a kan zanin. Sannan ta miƙe ta fita daga cikin kwale-kwalen. Ta dawo ta bayansa, ta shiga turashi cikin ruwan, har ta samu nasarar turashi gaba ɗaya. A kan idonta kwale-kwalen ya shiga yawo a kan ruwan. Ya na nufar gidajen katakwayen dake saman ruwan. Sai da ta share ƙwallar idonta tukkuna, sannan ta juya da gudu ta bar wurin. Ma somin ƙaddarar kenan, a ganinta ta kawo ƙarshen matsalolin, tun da har bata kashe jaririyar ba kamar yanda aka umarceta. Tun da har yarinyar ta yi nesa da gidan, wata ƙila komai zai ƙare. Tana wannan tunanin ne ba tare da sanin cewa yanzu ne komai zai fara ba, dan kuwa barin yarinyar da ta yi a raye, shi ne musabbabbin buɗewar ƙofofinsu wasu tarin ƙaddararo da ko ita kanta bata san da aukuwarsu ba. Saboda ta kashe maciji ne batare da ta sare kansa ba. A yanzu ne komai zai fara!. *Present day...* *Shekara ta 2024.* *Makoko, Lagos State, Nigeria.* *06:30 na Safe.* “Wai Shola ba za ki fito ki tafi wurin aiki ba?... Kin kusa makara fa!” Cewar wata baƙar mata cikin harshen yarbanci, yayin da take zaune a kan dandaryar katakon da aka kafa ginin gidanta da shi. Daga can cikin ƙaramin ɗakin gidan, muryar wata matashiya ta bata amsa cikin faɗin. “Takalmi nake sakawa Gigi!” Matar ta girgiza kanta tana dawo da dubanta kan mijinta dake kwance a gefenta. Fuskarsa ta ɗan leƙa ganin idonsa a rufe, zatonta bacci yake. Amma a zahirin gaskiya ba baccin yake ba, idonsa biyu, tunanin rayuwa ne yasa shi a gaba. Damuwar halin da gidansa ke ciki ita ce ta sako shi a gaba, ba dan 'yarsa ɗaya Shola ta duƙufa wurin nemo kuɗin da zasu ci abinci ba, da tuni gidan nasu ya jima da durƙushewa. A da shi ne yake kula da gidan, amma tun bayan iftila'in hatsari da ya afka masa riƙon gidan nasa ya koma hannun 'yarsa DIYA, wanda sukewa inkiya da SHOLA. “Ga ni na fito” Cewar Shola, bayan da ta fito daga tilon ɗakin gidan nasu, a tare suka dubeta, daga Gigin har mijinta da ya buɗe idonsa. Sanye take cikin wani baƙin wando me faɗi, sai wata farar oxford shirt. Kanta yafe da baƙin gyale. Ƙafafunta sanye da fararen canvas da suka fara jin jiki. Wannan shi ne kayan da ta saba sakawa idan zata je wurin aiki. Fara ce sosai, tana da matsakaicin jiki, idan za ka mata adalci, a kallon farki idan ja mata za ka kirata da bafulatana. Gigi ta yi murmushi. “Ga guntuwar shinkafar jiya, ki ɗan taɓa kafin ki tafi” Shola ta girgiza kanta tana sauƙowa daga kan mattattakalan katakon gidan nasu. “A'a Gigi, ni idan na ci ku me za ku ci?, kawai ku ci, idan na je wurin aiki zan samu abun da zan ci” Gigi ta miƙe tana fitowa daga gidan katakon nasu, ta tsaya kusa da Sholan dake kiran sunan Ekene, wanda yake zaune a gidan dake gaban nasu, dan ya zo ya fitar da ita bakin gaɓar ruwan unguwar tasu, dan ba'a zirga-zirga a unguwar sai da kwale-kwale. “Ya kamata ki taɓa wani abun Shola” Diya ta juyo ta kalleta. “Karki damu da ni Gigi, ko biredi ne zan siya na ci, ke de ki kula, na bar miki ɗari biyar a ɗaki, wata ƙila za ku buƙace ta” Gigi ta yi murmushi tana shafa kanta, tare da saka mata albarka. “Shola ga ni” Cewar Ekenen da take kira, bayan da ya fito daga ɗakinsu na katako. “Na kusa makara Ekene! Ka zo ka fitar da ni” Ta faɗi tana dubansa. Saida ya ɗaga busassun hannayensa ya yi miƙa, kafin ya sauƙe yana jan wata baƙar tsohuwar singlet da ke rataye a jikin wata gwafa ta gidansu. Sannan ya zagaya ta inda kwale-kwalensa yake, ya cinto shi daga jikin wani ƙarfe da ya ɗaureshi, sannan ya shiga yana ɗaukan marar kwale-kwalen, ya zagayo da shi har zuwa ƙofar gidansu Shola. Shola ta yi wa Gigi sallama, sannan ta hau kwale-kwalen. Ekene ya fara tuƙasu. Diya ta ci gaba da kallon irin wahalar rayuwar da ake a yankin nasu. Kaf gidajen yankin na katako ne, kuma a saman ruwa suke, dan gaba ɗayan unguwar ma kanta malale take da ruwa, shi yasa ko ina zaka sai ka hau kwale-kwale. Sosai ake shan wahalar rayuwa a yankin, yawancin mazaunan yankin masu zuwa cirani ne, sai 'yan gudun hijara, da kuma wanda ƙaddara ta zama silar zuwansu wurin. Yankin nasu ya haɗa tarin ƙabulu, da kuma mutane masu mabanbanta halaye. Kowa ta kansa yake a wurin, babu ruwan wani da rayuwar gidan wani. “Mun iso!” Cewar Ekene, sanda suka iso bakin ruwan. A hankali ta miƙe, hannunta riƙe da jakarta. Godiya ta masa tana fita daga kwale-kwalen. Hanya ta yanka ta so ma tafiya. Kafin ta samu isowa tashar bus ɗin da ta saba hawa. Tafiyar munti 55 ce ta kaita cikin Victoria Island. A wani bus stop suka tsaya, ta fito daga motar bus ɗin, tare da sauran mutanen da suka shiga motar. A ƙafa ta fara takawa, har ta iso Cactus restaurant. Wurin da take aikin raba abinci kenan. Memakon ta shiga ta ƙofar gaba kamar yanda kowa ke shiga, sai ta zagaya zuwa backyard ɗin ginin restaurant ɗin, ta shiga ta ƙofar kitchen ɗin restaurant ɗin dake baya. “Shola sai yanzu kika iso?” Ɗaya daga cikin masu girkin wurin ta tambayeta, yayin da take ƙoƙarin saka apron ɗinta dake rataye a jikin wani hook. Zaren apron ɗin ta gama ɗaurawa tana faɗin. “Eh Wallahi, sai yanzu na samu isowa” “Diya! Diya!” Tun daga nesa suke jiyowa muryar Orisa cikin ƙwalla kiran sunan Diya. Kafin Diyan ta amsa, Orisa ta bayyana a cikin kitchen ɗin. “Wai ya aka yi kika makara?.... MD ya zo yana ta faɗa!” Orisa ta faɗa mata cikin harshen yarbanci, Diyah ta saka jakarta cikin wata loka tana amsa mata da. “Yau ban farka da wuri ba ne!” “Lalle kam, ke har wani lokacin miƙe ƙafa ki yi bacci kika samu?” Orisa ta tambaya. Diya ta miƙe tana kallonta. “Orisa mutum idan be huta ba ai sai ya samu matsala, mu yini muna aiki mu koma gida kuma a ce ba za mu yi bacci ba?” Orisa ta gyaɗa kanta. “To yanzu dai ba zan ce za ku tsaya kuna yi ba. Ga wani plate ɗin brown spaghetti can, ki ɗauka ki kai teburi na sha takwas” Cewar Ifunaya, shugabar sashensu na masu kaiwa abinci. “Ok” Diya ta amsa tana raɓa Orisa, plate ɗin brown spaghettin ta ɗauka ta ɗora a kan wani tray me kyau, ta nufi ƙofar shiga cikin restaurant ɗin. Da misalin ƙarfe tara na dare ta kamo hanyar dawowa gida, bayan da ta tashi daga aiki, hannunta na dama riƙe da wata farar leda. Kafaɗarta kuma saƙale da jakarta. Kasancewar a yankin nasu ba ko ina ne me wutar nepa ba, yasa take amfani da hasken wayarta, wurin haska hanya. Kuma har zuwa lokacin akwai sawun mutane a waje. Ranta ne ya ɓaci asanda ta iso bakin ruwan yankin nasu, ta iske babu masu yin fito, sai de tarin kwale-kwale a bakin wurin. Ga shi Ekene tsabar talauci da ya masa kanta ko waya ba shi da ita, bare ta kirashi dan ya zo ya fitar da ita. Haka ta duba ɗaya daga cikin kwale-kwalen da ta san me shi, ta fara tura shi zuwa cikin ruwan, kafin ta ɗale ciki tana ɗaukan marar fiton sa, ta fara tuƙa kwale-kwalen. Ganin hasken fitila kunne a tsohon gidansu da ya kusa durƙushewa ya sa ta fahimci cewar har yanzu basu kwanta ba. A kan matakalar katakon ƙofar gidan nasu na ƙarshe ta dire,sannan ta ɗaure kwale-kwalen a jikin wani ɗan katako dake jikin gidan nasu. Sannan ta ɗebi kayanta da ta aje su a cikin jirgin, ta fara taku a hankali, saboda yanayin jimawar da katakon ginin gidan ya yi, ya sa ba sa taku da ƙarfi, dan abu kaɗan ne zai iya sawa ya karye, saboda wasu wuraren ma sun karye ɗin. A tilon ɗakin nasu ta tarar da su, Gigi na zaune tana wa Papi firfita, sun kunna mosquito coil, sai wata dundurusun fitilarsu mara haske sosai dake ci. Ɗakin babu komai sai wasu lamitssatssun katifu guda biyu, dake yashe a ƙasan ɗakin, sai 'yan wasu jakkukkunansu na kaya. Dan basu cika tara tarkace a ɗakin ba, gudun kada katakon gidan ya ɓalgace. “Ba ku yi bacci ba?” Ta tambaya tana cire viel ɗin jikinta, Gigi ta kalleta tana faɗin. “Tukunna dai, zafi ne ya hana mu kwanciya” Diya ta dawo bakin ƙofar ɗakin nasu, ta ɗauke labulen ɗakin, saboda iska ta ɗan samu ta shigo ciki. Ta dawo ta ɗauki kwandon soso da sabulunta, ta fita waje. Ɗan siririn banɗakin gidan ta shiga, da wani ruwa rabin bokiti ta samu ta ɗan yi wanka, sannan ta fito, jikinta ɗaure da zani, ta dawo ɗakin ta saka wata doguwar rigarta. Sannan ta zauna kusa da Gigi, tana jan ledar da ta shigo da ita. “Papi na samu kuɗin siyan maganinka, amma ɗaya aka samu, sai a yi maneji” Papi ya kalli tilon 'yar tasa, ƙwalla na shirin taruwa a idonsa, a shekarun da suka wuce ya tsinceta, shi ya kula da ita har girmanta, sai ga shi a yau ita ce take kula da shi, rayuwa kenan. “Allah ya miki albarka Shola” Ta sunkuyar da kanta tana amsa masa da amin. “Yau me kuka ci da rana?” Ta faɗi tana fitar da sauran kayan da ke cikin ledar, Gigi ta aje muficin hannunta tana faɗin. “Taliya muka ci” Robar da ta zubo sauran abincin da ya yi saura a restaurant ɗinsu ta fitar, dan idan abinci ya yi saura su ake rabawa. “Ga abinci na zo da shi, Papi ka tashi sai ka ci” Kansa ya girgiza mata. “A'a Shola, ke da Giginki dai ku ci... Amma ni na ƙoshi” Shola ta ɓata fuska. “Idan baka ci ba ni ma ba zan ci ba” Da sauri ya yunƙura ya zauna. “Yi haƙuri to, zan ci” Ta ɗan yi dariya tana kallon Gigi, Gigi ta yi murmushi tana shafa kanta. Haka suka gama cin abincin tana basu labarin abubuwan da suka faru da ita yau a waje, wani abu da tun tana yarinya take yi, duk inda zata je ta dawo, sai ta basu labarin abun da ya faru da ita a wurin. Ko da suka gama cin abincin sai ta ɗauki katafarta ta fita da ita rumfar ƙofar gidan nasu, ta shimfiɗata, ta kawo wani jemammen bedsheet ta shimfiɗa. Kafin ta kawo wani fatattakkakken net ta ɗaura. Ta shiga cikin shimfiɗar tata ta kwanta. Tana hasashen yanda ranar gobe zata kasance, wannan ita ce rayuwar da take gudanarwa tare da iyayenta, rayuwar tasu me wahala ce, amma kuma suna cikin farinciki. Shekaru uku kenan da fara aikinta, kuma a shekaru ukun da suka wuce ne, Papi ya samu hatsarin mota, sannan tun lokacin ƙafarsa ta samu matsala. Har aka buƙaci wasu maƙudan kuɗe wurin mata aiki, Kasancewar basu da su, ya sa suka dawo gida suka zubawa saratar Allah ido. Ganin zaman ba zai kaisu ba ya sa ita Diyan shiga cikin gari neman aiki, kuma cikin nasara ta samu, da shi ne suke iya rayuwa a yanzu. A. ISAH CE✍️. °°°°°°°°°°°°°°°°°°° *💡HASKE...💡️* *©SALMA AHMAD ISAH* TAURARI WRITER'S ASSOCIATION. °°° Akwai ɗaya daga cikin members ɗin gidan nan, da Allah ya yi wa mijinta rasuwa, ina so ku saka shi a addu'a, Allah ya ji ƙansa ya gafarta masa. °°° *Page 02* ~~~ *Coca-Cola Arena, Abu Dhabi, Dubai...* _🎶When I look at you, I see a star, Shining bright, no matter where you are._ _My heart is full of love, it overflows,With you by my side, my joy it grows._ _Your beauty is like a work of art, My love for you comes straight from the heart._ _You're my one and only, it's plain to see, Forever yours, that's how it will be.🎶_ Maƙaƙaren hall ɗin cike yake da mutane. Babu abinda ke tashi a wurin, sai sautin mutanen wurin, suna rera waƙar dake tashi a hall ɗin. Daga can kan stage kuma wani kyakkyawan matashi ne tsaye, sanye cikin baƙar T-shirt, da baƙin khaki trouser. A saman T-shirt ɗin kuma ya ɗora red bomber jacket. Hannunsa na dama riƙe da microphone, sassanyar muryarsa ce ke rera waƙar dake tashi cikin sifikun wurin. A dai-dai lokacin da kiɗan waƙar ya sauya, a lokacin masoyansa dake wurin suka sa ihu, har da masu tsalle, wasu na ɗaukarsa a hoto, wasu video wasu na ɗaga takardu masu ɗauke da sunansa. Yayin da shi kuma ya dage wajen ganin ya farantawa masoyansa ransu. Su ma kuma suna jin daɗin show ɗin na yau, dan burin ransu ne ya cika, yau gasu ga babban masoyinsu, yana rero musu daɗaɗan waƙoƙinsa, cikin nutsatsiya kuma sassanyar muryarsa. Daga baya kuma sai sautin koran sunansa ya cika wurin. Cike da jin daɗi da kuma farin ciki ya tsaya yana kallon masoyan nasa. “TAUQEER AGHA!” * Tsaye yake a gaban katangar glass ɗin dake a ɗakin hotel ɗin da ya sauƙa, idonsa manne kan kyawawan gine-ginen dake garin na Abu Dabhi, shi kansa garin yana masa kyau, musamman da daddare. Duk da ya je ya yi rawa a kan stage, ya yi waƙa, ya yi ihu, amma baya jin gajiya a jikinsa, dan zuwa gobe zai koma ƙasarsa ta gado, wato Nigeria. Ƙaran wayarsa dake kan gado da ya ji ne ya sa shi waigawa. Sannan a hankali ya soma taku zuwa jikin gadon, ya kai hannunsa ya ɗauki wayar. ‘Umma' shi ne sunan dake yawo a kan screen ɗin. Da wani ɗan guntun murmushi a kan fuskarsa ya ɗaga wayar. Sallama ya fara yi cikin daddaɗar muryarsa. Bayana an amsa masa sallamar ta cikin wayar kuma ya gaida matar cikin girmamawa. “TAUQEER zuwa goben za ka dawo?” Kansa ya gyaɗa a hankali yana juyawa. “Insha-Allah Umma!” “To Allah ya dawo da kai lafiya, Allah ya temaka” “Amin” Ya amsa yana sauƙe wayar daga kunnensa, dan wayar ta yanke, sumar kansa ya shafa daga gaba zuwa baya, yana fitar da wani hucin iska daga bakinsa. A hankali ya zauna a bakin gadon yana jujjiya kansa, kafin a hankali ya kwanta a kan gadon, bacci yake san yi, amma kuma baccin ya ƙauracewa idonsa. *Agha Mansion, No.854, Lekki pahse 1, Lagos State, Nigeria.* Wani katafaren gida ne, wanda za'a iya kiransa da fada me zaman kanta, dan ko ginin gidan ya amsa sunan gida. Daga waje ma kawai gidan abun kallo ne, bare kuma ka saka ƙafarka a gate ɗin farko na gidan. Tun daga kan maƙareren gate ɗin gidan, za ka fara cin karo da wata shimfiɗeɗiyyar kwalta, wadda zata sada ka da cikin gidan. Kyakkyawan garden ɗin gidan, shi ne a farkon gidan, kafin ka iske ainahin ƙofar shiga cikin gidan. Gidan ginin bene ne me hawa ɗaya. Kai da ganin gidan ka san cewa wannan ya fi ƙarfin zaman mutum ɗaya, duk da ginin ba na yau ba ne, amma kayan da aka zube a cikinsa sabbbi ne, 'yan ya yi, hakan ke nuna cewar mammallakan gidan na kula da shi yadda ya kamata. Agha Mansion kenan. Gida ne na iyalin mutum ɗaya. Agha Muhammad shi ne ainahin tushen kafuwar ahalin. Shi da matarsa Fariya. Daga Agha har matarsa Fariya dukansu fulanin Yola ne. Allah ya albarkacesu da yara shida: Faruq Agha, shi ne babba cikin 'ya'yan nasu, shi ne mamallakim A. FOODS NIG LTD. Babban kamfanin da ya shahara a faɗin Nigeria, wurin sarrafawa da kuma shige da ficen kayan abinci. Me bi masa kuma shi ne Mas'ud Agha, soja ne, me riƙe da muƙamin General. Sai Tayyab Agha, shi kuma ya kasance likitan ƙashi, sannan ya mallaki asibiti tasa ta kansa. Me bi masa shi ne Muzamil Agha, shi kuma ya bi sahun yayansa Faruq, dan tare suke kasuwancinsu. Sai autarsu, kuma mace ɗaya tilo a cikinsu Abida, wadda ta yi aure, tun da jimawa. Kuma tana zaune a garin Abuja ita da mijinta da kuma yaranta. Kuma duka waɗanan ahalin na zaune ne a cikin Agha Mansion. Domin kaf cikinsu babu wanda bai tara iyali ba. Matar Faruq ɗaya, sunanta Maryam, yaran gidan kuma na kiranta da Umma, mace me kirki da sanin ya kamata, ga hange nesa, da jin ƙan talaka. Yaransa huɗu da ita, TAUQEER shi ne babba, suna masa inkiya da Junior, kasancewar ya ci sunan mahaifin Maryam ɗin ne. Sai Jamal. Me bi masa kuma ita ce Iqra, sai kuma autansu Aabis. Mas'ud na da mata ɗaya shi ma, Hafiza shi ne sunanta, yaran na kiranta da Amma. 'Yar halin ko in kula kenan, dan ita babu ruwanta da sabgar gidan, ko me za'a yi tana gefe, dan bata damu da kowa ba. Yaranta huɗu cas, haihuwarta ta farko 'yan biyu ta haifa, Tajuddin da Saifuddin, sai kuma Muhammad, wanda sukewa inkiya da Hammad, sai auta Khabir. Sau kuma Tayyab, matarsa ta farko sunanta Zayya, yaran gidan kuma na kiranta da mommy, Babban burin Zayya a duniya shi ne ta ga ta fi kowa, sam bata son a fita, shi ya sa komai nata da ban ne da na gidan, ta tsani ta ji an ce yau ga wani wanda ya ɗarata, kullum so take ta ji an ce ita ce on top. Haihuwarta ɗaya, ita ma bayan shafe shekaru masu yawa, Allah ya basu ita, sai matarsa ta biyu Rahila, wadda rana ɗaya aka wayi gari aka rasata ko sama ko ƙasa, ta yi ɓatan dawo, shi ya sa yanzu 'ya ɗaya gareshi, DEENA. Muzamil ma na da mata ɗaya, Rahama yaran gidan na kiranta da Mama, komai da ruwanka kenan, duk wata kurɗa-kurɗa ta gidan babu wadda Mama bata sani ba, ko labarin abun da ya faru a gidan kake nema idan ka tambayi Mama ka samu. Ko zance ake ba da ita ba za ka ji ta saka baki, duk dan de ta samu labarin bayarwa, babu zancen da ba zaka ji a bakinta ba, ita fa tsabar gulmarta, har dustbin ɗin gidan take zuwa ta duba, ko an ci wani abun a gidan bata sani ba. Tana da yara uku, Nasir shi ne babba, sai Abdullahi da suke wa inkiya da Bobo, autar cikinsu kuma ita ce Nimra. Ba ma a cikin 'ya'yan muzamil ɗin kawai ba, duka gidan ma Nimra ta fi kowa ƙananun shekaru. Kaf cikin yaran gidan su goma sha biyu, huɗu daga cikinsu sojoji ne. Sojojin sun haɗa da; Saifuddin Mas'ud Agha, Tajuddin Mas'ud Agha, Jamal Faruq Agha, da Nasir Muzamil Agha. Tauqeer kuma mawaƙi ne, wanda ya shahara a duniyar waƙa. Cikin gida da waje babu inda baya leƙawa dan harkar waƙarsa. Deena kuma actress ce, tana ɗaya daga cikin jaruman da ake ji da su a Nollywood. Iqra da Hammad kuma suna University ne. Bobo da Khabir na secondary school. Yayin da Nimra da Aabis suke junior secondary school. * “Halima dan Allah ki gaggauta ku gama girkin nan, na san duk inda suke zuwa yanzu sun kusa ƙarasowa!” Cewar Umma, yayin da take tsaye daga bakin ƙofar kitchen, tana duban masu aikin dafa abincin gidan. Halima shugabar madafan abincin ta risinar da kai tana amsa umarnin uwar gijiyar tasu. Daga haka Umma ta baro kitchen ɗin ta nufo cikin falon gidan. Kai tsaye ɗakinta ta wuce. “Wai ni me yake faruwa a gidan nan ne?” Hammad da ya dawo daga makaranta ya tambaya yana zama a kan ɗaya daga cikin kujerun falon. Mama dake zaune tana sakatar haƙori ta gyara zama tana faɗin. “Junior ne zai dawo yau” Sai ya gyaɗa kansa yana buɗe wayarsa. Daga gefen Mama kuwa, Amma ce zaune tana latsa wayarta. Daga can ɗayan ɓangaren na falon kuma Nimra, Aabis da Khabir ne ke home work. Yayin da Bobo ke zaune a kan kujera yana shirgawa cikinsa abinci, dan shi haka rayuwarsa take, shi da abinci five and six ne, rayuwarsa gaba ɗayanta ta tafi a kan cin abinci, shi ya sa ya haɗa wata uwar ƙiba. Tsabar ƙibar da ya yi cikinsa har zama yake a kan cinyarsa, ga luɓu-luɓu kumatu kamar yalo. “Bobo! Kai ba za ka yi home work ɗin ba?” Bobo ya sauƙe meat pie ɗin da yake shirin kaiwa bakinsa ya kalli setin inda Hammad ke tsaye. Kuma kafin ya amsa shi, Nimra ta yi caraf tace. “Cewa ya yi ba zai yi ba, kuma yau ma sai da uncle math ya masa horo!” Bobo ya juyo da kansa ya kalli Nimra cikin harar. Ba tare da ya ankara ba, Hammad ya warce plate ɗin meat pie ɗin dake hannunsa yana faɗin. “Gara uwar ci, ka tashi ka je ka ɗauko jakarka ka yi home work ɗin ko sai na mammake ka?!” Miƙewa ya yi yana cillawa Nimra kallon za mu haɗu ɗin nan. Tiɓi-tiɓi ya nufi tagwayen stairs ɗin dake falon, har wani nishi yake idan yana tafiya, tsabar yawan da ƙibar tasa ta masa. Kakarsu da suke kira da Hajiya ce zaune a kan wata kujera, Iqra kuma na mata tausa. “Kakus ki na da goro ne?” Saif da ya fito daga kitchen, hannunsa riƙe da mug ya tambaya yana kallon kakarsu. Hajiya ta wurga masa harara. “Da za ka zo kana tambayata ka siyo ka kawo min ne?” Ta tambaya tana wurga masa wata harar. “Ka ji ni da tsohuwa, daga tambaya?, sai cibo ya zama ƙari? Ƙari kuma ya zama ƙababa?. Inde maganar goro ce Allah ya baki haƙuri” Ya faɗa yana shirin wucewa, sai kuma ta fito da goron daga cikin aljihun doguwar rigar jikinta tana faɗin. “Zo ka karɓa ba dan halinka ba!” “Bana ci!” Ya faɗa ba tare da ya ko waigo ya kalleta ba. Hajiya ta taɓe bakinta tana maida goronta aljihu. Iqra ta musu dariya. Kusan kullum sun saba irin wannan faɗan, ita Hajiya saurin faɗa, shi kuma Saif zuciya. “Bar ni haka 'yar albarka” Cewar Hajiyan tana janye ƙafarta daga hannun Iqran. “Hajiya ai ni yau gani na yi ma ƙafar taki kamarta ƙara jagulewa” Hajiya ta dudduba ƙafar tata tana faɗin. “Ke de bari, wannan ja'irin yaron ne yake ƙara rikita min ita, sai ya zo ya yi ta jagula min ƙafa, wai a dole shi likitan ƙashi” Iqra ta yi dariya tana miƙa mata kwajirinta, ganin tana shirin miƙewa. “Dan girman Allah Taj ka dena taremana! Haba! Ka barmu mu yi kallon nan a tsinake mana!” Cewar Nasir, ganin Taj ya hanasu su kalli film ɗin da suke kallo a tsinake, sai tare musu yake, wai film ɗin be yi kyau ba. “Da waya zaunar da kai yace dole sai ka kalla? Idan ba ka so za ka iya tashi ka barmu mu kalla a tsinake!” Nasir ya faɗi yana juyo da kan system ɗin gareshi. Mommy da Deena ne suke sauƙowa daga kan stairs. Deena sai fara'a take, saboda dawowar masoyinta, farin cikinta, abun alfaharinta, wato Tauqeer, Mommyn ma sai kallonta take cike da alfahari kasancewarta 'yarta. Saif dake ƙoƙarin hawa stairs ɗin ya tsaya yana kallon irin shigar dake jikin Deena. Wata mini dolman dress ce a jikin nata. Tsala-tsalan singalilanta masu kama da tsinken kwakwa bayyane a waje. Ƙafarta sanye da wedge booties me ɗan karan tudu. Kanta kuwa ya ji kitson attachment ya ƙoshi, baƙar fuskarta ta sha make-up. Ita gata wayyayye. Ya ja tsaki a ƙasan numfashinsa yana kallon gefe, dan tsabar takaici. Haka kowa ya bisu da kallo ita da Uwar tata har suka fita daga falon, dan ita Deena tace zata je ta ɗauko Tauqeer daga airport. Hajiya da ta taso dan shiga ɗakinta ta tsaya a setin Saif tana dafa kafaɗarsa. “Sai haƙuri Saifu” Ta bashi haƙurin dan ta san abun da Deena ke yi na ɓata masa rai. Ba ma shi kaɗai ba, kowa dake gidan ba ya jin daɗin shigar da take. “Hajiya abun nata ya yi hawa Wallahi. Kar ki ga hoton da ta yi posting a shafinta na Instagram last week. Hoton ya jawo cecekuce a social media. Babban abun da yake ɓata min rai shi ne kasancewarta a cikin ahalinmu!” “To yaya za ayi Saifu? Dole a yi haƙuri, tun da ka ga ita ma jinin gidan nan ce, kuma da ma irin haka na faruwa, duk inda aka samu yawan ahali ana samun gurɓattattu kamar haka, ku de kawai ku tayata da addu'a” Kasa cewa komai ya yi saboda takaici, ya wuce sama, sai da ya yi nadamar sauƙowa ƙasan, dan da ace be sauƙo ba, da ba zai zo ya ga wannan abun takaicin ba. *Murtala Mohammed International airport, Lagos.* TAUQEER FARUQ AGHA POV. Cike da mutsuwa ya fito daga terminal. Sanye yake da wata farar long sleeve tees, sai farin wandon rigar, ƙafafunsa sanye da fararen sneakers. Kansa sanye da p-cap. Fuskarsa kuma rufe da mask, ya rufe fuskar tasa ne, saboda ba ya son takurawar jama'a, duk da kasancewarsa me nuna so da ƙauna ga masoyansa, amma yau a gajiye yake, ba ya son kowa ya gane shi. Kansa a ƙasa yake tafe. Yayinda duffle bag ɗinsa ke riƙe a hannunsa na dama. Daga can nesa ya hangi Deena ita da securities ɗinta biyu, sai wani yauƙi take kamar kuɓewa. Ita ga celebrity. Kuma tun daga nesan ya iya gano kalar shigar dake jikinta, hakan ya sa ya ja tsaki yana kawar da kansa. Yau shi banda ƙaddara ma me zai yi da wannan abar, dan ba dan an cusa masa ita ba, babu yanda za ayi mutum kamar shi ya yarda da aurenta. Tsabar rashin kunya irin ta Deena ita da kanta ta kaiwa iyayensu maganar tana sonsa, hakan yasa iyayensu maza suka tambaye shi; shin ya na sonta?, be san ya aka yi ba, amma haka ya ji bakinsa ya masa nauyi a lokacin, ya kasa amsa musu da a'a, dan ko da ace zai amsa to amsarsa za ta kasane a'a ce. A rayuwarsa ya tsani mace mara kamun kai, ita kuma Deena rashin kamun kai shi ne adonta. “Laaa! Momy! Deena Agha!” Cewar wata yarinya cike da ɗaukin ganin jarumar dake burgeta. Mahaifiyar yarinyar da suke tafe tare ta kalli wurin da Deenan ke tsaye, sannan tace. “Mu je ku ɗuki hoto mana” “Ki na ga za ta yarda?” “Me zai hana? Je ki gwada” Cike da ɗoki yarinyar ta isa wurin. Bakinta har bayan kunne. Securities ɗin ne suka fara dakatar da ita. “Ke! Ina za ki?” Ɗaya daga cikinsu ne ya daka mata tsawa cikin garjejeyar muryarsa. Hakan yasa yarinyar tsorata, har wayarta na faɗuwa ƙasa. “Ku... Ku yi haƙuri... Hoto nake so na ɗauka da... Da Deena!” A tare securities ɗin suka juya suka kalli Deena. Wadda ta sauƙe sun glasses ɗin idonta, tana watsawa matashiyar kallon banza. “Na miki kama da wadda za ta yi hoto da ƙazama irin ki? Dallah malama ja ƙazamin jikinki ki bar nan wurin!” Nan take ƙwalla ta sauƙo daga idon matashiyar, dan duk sai ta ji ra muzanta, shin lefi ne dan ta nunawa wanda take so soyyaya?. Deena ta ci gaba da taunar chewing gum, rashin mutunci da kuma muzanta ɗan adam hallayarta ce tun tana yarinya, bata ganin kowa da gashi, in dai kai ba wani ba ne, to baka isheta kallo ba, ta tsani wanda bai isa ba, musamman 'ya'yan talakawa, dan cewa take sun fiya tsiwa da iyawa, su ba 'ya'yan uban kowa ba, sai shegen ji da kai. Matashiyar ta share ƙwalla tana tsugunnawa dan ɗaukan wayarta. Ta kai hannun za ta ɗauki wayar, ta ga wani farin hannu ya rigata ɗaukan wayar. Hakan ya sa ta miƙe tana kallon mamallakim hannun. Ko kafin zuciyarta ta faɗa mata cewar bata san shi ba, mutumin ya kai hannunsa ya cire mask ɗin fuskarsa. Idanuwanta ta zaro waje tana kallonsa, nan take ta nemi ƙwallar tata ta rasa, dan ganin babban masoyinta, wanda ya fi Deena matsayi a zuciyarta. “Password?” Wannan sassanyar muryaryar tasa ta tambaya yana buɗe wayarta. “Ummm?” Ta tambaya idonta a kansa, dan ta kasa gane ma'anar password ɗin. “Ina nufin password ɗin wayarki” Bakinta na rawa ta ƙifta idonta. “4457” Password ɗin ya buɗe, ya lalubo camerar cikin wayar, kafin ya shiga, ya matsa kusa da ita yana ɗaga wayar sama. Tsabar mamaki da farin cikin da take ciki, sai ta kasa kallon cameran, ta ci gaba da kallon fuskarsa, kuma a haka ya ɗauki hoton. Ya sauƙe wayar yana miƙa mata, kamar wata doluwa haka ta ɗago da hannuta ta karɓi wayar. Ido ɗaya ya ƙifta mata yana murmushi, sannan ya barta tsaye da baki a sake. Mask ɗinsa ya mayar yana murtike fuska, bayan da idonsa ya sauƙa a kan Deena, wadda ita kuma take masa nata murmushin, kansa ta iyo zata rungumeshi ya yi saurin dakatar da ita ta hanyar ɗaga mata hannu. Ba ta ji daɗin hakan ba kamar kullum, ita har yanzu gani take wayewar Tauqeer ta banza ce, tun da har ba ya irin halayenta. Duk wanda baya hallaya irin tata ganinsa take wawa. Ya raɓata ya wuce ya nufi motar da ta zo da ita, ɗaya daga cikin securities ɗin ne ya buɗe masa motar, ya shiga ba tare da ya jirata ba. Haka ta zagayo ita ma ta shiga ta ɗayan ɓangaren. Kuma har suka kai gida bai ko ƙara kallonta ba, dan daga zarar ya kalleta sai ya ji kamar zunubi yake aikatawa. A. ISAH CE✍️. °°°°°°°°°°°°°°°°° *💡HASKE...💡* *©SALMA AHMAD ISAH* TAURARI WRITER'S ASSOCIATION. *Page 03* ~~~ *GrowTech. AI centre, No. 10, 23rd street, Astoria, NewYork, USA.* Cikin sassarfa wani farin dattijon bature ke tafe, sanye yake cikin baƙar suit, bayan sa kuma biye da wasu matasa wanda yanayin biyyayar da suke masa ko a tafiyarsu ke nuna cewa shi ne gaba da su. Ganin kamar inda suke san nufa ya yi masa nisa ya sa dattijon fara gudu, hankali a tashe ya kutsa kai cikin babban ɗakin kula da computers na tsaron ma'aikatar. “Sir! Sir!, All of our computers have been hacked by an unknown hacker!” Cewar wata matashiya tana miƙewa tsaye daga kan kujrar da take. Cikin halin ruɗu, baturen ya kalli babban allon glass dake manne a jikin wata katanga dake ɗakin, wanda yake ƙunshe da hoton gaba ɗaya fuskokin computers ɗin ma'aikatar. Kamar wanda be yarda da abun da idonsa ke gane masa ba, ya rarumi keyboard ɗin wata desktop dake wurin, ya shiga dannawa a kiɗime, idonsa manne da babban allon glass ɗin. Sai de kuma duk dannawar da yake a banza, don kuwa dannawar tasa bata hana madatsin na'urar kwasar bayanan da ya fara ba. Ɗagowa ya yi daga kallon desktop ɗin, gumi na tsatssafo masa, hannu ya sa a aljihun suit ɗin jikinsa ya ɗauko hanki, sannan ya shiga goge gumin. “Did ram RAM arrive today?” Ya tambaya, idonsa na hango masa mafita a tare da bayyanar RAM ɗin ɓaro-ɓaro. “No sir, he didn't appear today” wannan macen ta amsa masa. “Get in touch with him, now!” *No.675, 361 Stagg Street, Brooklyn, New York, USA.* Abu na farko da za ka farra kalla a ɗakin shi ne, computers, domin kuwa kusan computers biyar ne ke kunne a cikin ɗakin, haka zalika ɗakin babu haske sosai, sai na wata shuɗiyar fitila dake ci daga can wani ɓangare na ɗakin, idan kuma ka ci gaba da wilƙita idonka a ɗakin za ka iya hangowa ƙarafunan robot da ake haɗawa, wasu an haɗasu, wasu kuma ana kan haɗasu. Daga can jikin wata babbar desktop kuma, wani matashi ne zaune kan kujera, ya jingina bayansa da kujerar, yayin da hannyensa biyu duka ke kan keyboard, kuma cikin sauri-sauri yake daddadanawa, sannan idonsa manne kan screen ɗin desktop ɗin, kai ka ce bai ma san madannan da yake dannawa ba. Hannyensa duka biyu na sanye da agogo. Sanye yake cikin wando jeans, da Oxford casual shirt a sama, kasancewar maɓallayen casual shirt ɗin ba a ɓalle suke ba, ya sa za ka iya ganin ash T-shirt ɗin dake ƙasanta. Sumar kansa na da tsayi sosai, don daga baya ta sauƙo har zuwa wuyansa, yayin da daga gaba kuma ta sauƙo kan goshinsa. Sumar kan nasa na da kyau da kuma santsi, don tsabar santsinta har wani kannaneɗewa take. Dogon gemun da ya tara a fuskarsa ne ya ɓoye fiye da rabin kammaninsa, idonsa sanye da farin glashi, yayin da gefen wuyansa ta ɓangaren dama, ke ɗauke da wani zanen baƙin tatto, wanda aka rubuta ‘RAM’. “Feeq! Feeq!...” Tun daga waje yake jin muryar sanyin idaniyarsa na kiran sunan, amma sai ya ƙi amsawa, dan gani yake kamar idan ya kauda idonsa daga kan screen ɗin na sakan ɗaya duk tarin tilin aikin da ya yi a ranar zai ruguje. “Feeq!” Ta kuma kira tana buɗo ƙofar ɗakin. Matar ta kalleshi tana girgiza kai. “Wai ba ka ji ina ta kiranka?” Ta faɗi tana duban bayansa. Ba tare da ya juyo ya kalleta ba, salihar muryarsa ta furta. “Na ji Maa, wani abu nake son ƙarasawa” “Ka aje abun da kake ka fito ko sai na ɓata maka rai?” Ta tambaya ranta na shirin ɓaci. Kamar wanda aka cewa tana ganinsa, ya shagwaɓe fuska yana faɗin. “Maa tun safe nake tsara sashen magana na AI humanoid robot ɗina, amma ban gama ba, Wallahi daga na gama zan fito” “Kada Allah ya sa ka fito ka ci abincin, ai cikinka ne ba nawa ba!” Ta ƙarashe tana rufowa ƙofar ɗakin. Ba dan ya so ba, haka ya dakatar da komai, sannan ya ɗaga hannyensa sama yana miƙa. A hankali cikin natsuwarsa ya miƙe tsaye, sannan ya nufi ƙofar balcony yana gyara rigarsa da ta tattare daga baya saboda zaman da ya sha. A hankali ya buɗe ƙofar, sannan ya kutsa kai. Tsayawa ya yi a jikin ƙarfen balconyn, ya kafe windown ɗakinta da ido. Don ya san za ta iya fitowa a lokaci irin wannan. Kuma kamar da ya auna. A dai-dai lokacin, aka buɗe tagar gidan dake facing nasu. Sannan fuskar wata matashiya ta bayyana. Kallo ɗaya ya mata,zuciyarsa ta buga, kamar wadda take shirin fitowa daga allon ƙirjinsa. Yawu ya haɗiya yana gyara tsayuwarsa, tare da duba agogon hannunsa na hagu, ganin bugun zuciyarsa ya ƙaru da kashi 5 ne ya sa ya sauƙe hannun ya ƙara maida dubansa kan tagar gidan. Zuwa lokacin ita ma ta fito zuwa nata balconyn. Kallonta ya ci gaba da yi, zuciyarsa na rawa. Wata biyar da suka wuce ya fara ganinta, lokacin da ta kama wannan gidan dake kusa da nasu gidan, kuma tun a ganinsa na farko da ita zuciyarsa ta faɗa cikin wani irin yanayi mara fasaltuwa, shi kansa ba zai iya cewa ga abun da yake ji a kanta ba, amma de ya san a duk sanda zai ganta sai bugun zuciyarsa ya ƙaru... Tunaninsa ya katse a sanda ta ɗago masa hannu tana murmushi, hannayensa ya sauƙe, waɗanda ke harɗe a ƙirjinsa ya ci gaba da kallonta yana murmushi. “How is your day going?” Ta tambaya cikin ɗaga murya, dan akwai 'yar tazara a tsakanin gidajen nasu. “Good, Alhamdulillah” Sai ta gyaɗa kanta tana ƙare masa kallo. Ita dai kam yana burgeta, duk da ba ta taɓa ganin fuskarsa duka ba, saboda gemun da ya rufe masa rabin fuska, amma a haka kawai idan ka kalleshi za ka san cewa yana da kyau. Ita ba ta san ɗan wani ƙabila ba ne, amma yana mata kama da baƙaƙen indians, yanayin fatar jikinsa da take Chocolat color, da kuma sunar kansa da take da laushi ko a ido, shi ne yake sawa a kallon farko da mutum zai masa ya ɗauka cewar ba'indiye ne, duk da shi ba fari ba ne. Jin ƙarar wani abu na tashi a ɗakinsa ya sa shi juyawa ya kalli ƙofar balconyn. Sai kuma ya juyo ya kalleta. “Bye!” Ya faɗi yana ɗaga mata hannu. Ita ma hannun ta ɗaga masa tana murmushi. Ɗakin binciken nasa ya koma ya shiga duba computers ɗin nasa da yake da tabbacin sautin daga su yake fita. Daga cikin system ɗinsa sautin kiran ke tashi, dan haka ya zauna kan kujerar dake gabanta yana duba kiran. Duk da ya san babu me iya masa kutse kamar haka idan ba daga CrowTech ba, wato ma'aikatar da yake aiki, ya san cewa wata ƙila kiran wayarsa suka yi ba su samu ba, shi ya sa suka datsi na'urarsa don su aiko masa da kiran. “Ram, ana buƙatarka a center, yanzu-yanzu!” Abun da wani matashin bature ya faɗi kenan, bayan da Ram ɗin ya ɗaga kiran. Sai da ya ɗan juya kansa, sannan yace. “Ok, on my way” Ya faɗi yana katse kiran. Miƙewa ya yi, ya nufi inda backpack ɗinsa take, ya ɗauka, sannan ya saka laptop ɗinsa a ciki, ya goya a bayansa ya fita daga ɗakin. Ƙasa ya sauƙa, inda yake da tabbacin Maansa na can. Ilai kuwa, Zaune ya sameta a kan kujerar danning tana cin abinci. Harara ta maka masa tana kawar da kai. Shi kuma sai ya mata murmushi yana takawa zuwa gareta. Peck ya mata akai yana zama kusa da ita. “Ga ni na fito fa” “Ina za ka je?” Ta tanbaya ganinsa da jaka, ya ɗan yi shiru yana kallon abar son nasa. A kallo ɗaya idon ka musu za ka shaida wannan kalmar ta 'dangantaka' ita ce ke a tsakaninsu, duk da tarin gemun da ya rufe masa fuska bai hana kammaninsa da nata fitowa ba, banbancinsu ɗaya ne, kalar fatarsu, ita ta kasance fara ce sosai, yayin da shi kuma tasa take brown colour,kamar ta baƙaƙen indiyawa. “Daga wurin aiki ne aka kirani, suna buƙatata” Ya amsa mata yana ci gaba da kallon kyakkyawar fuskarta. “Lami! Lami!” Ta shiga ƙwala kiran Lami tana kallon ƙofar kitchen. Ram ya dafe kansa yana girgiza shi, be san yaushe Maan nasa za ta iya faɗin sunan robot ɗin dake girka musu abinci a gidan ba. “Maa Kiyara,! Kiyara ne sunanta ba Lami ba” Ya faɗa mata abun da ya saba faɗi a duk lokacin da ta yi rafkanuwa wurin kiran sun robot ɗin. Maa ta taɓe baki tana aje cup ɗin hannunta. “Ni fa ba zan iya da wannan kiyare-kiyaren naku ba, na riga da na saba da sunan Lami, don haka Lami zan ce ehe...” Ya yi murmushi yana tuno da Lami ɗin. Lami ta kasance 'yar aikin da take taya Maa aiki a gidansu dake Nigeria, ta jima tana aiki a gidan,kafin suka kamata da lefin sata, shi ne suka sallameta, kuma bayan sun sallametan ne Ram ɗin ya haɗa mata Humanoid android robot, wada ya ƙirƙireta akan girki da gyaran gida kawai, kuma tun daga lokacin ita ce take girki a gidan, har zuwa yau. Ita kuma Maa ta riga da ta saba da kiran sunan Lami a duk sanda take buƙatar a mata wata hidima, shi ya sa ko bayan da ya ƙera Kiyara robot bata dena kiranta da sunan ba. “Maa!” Wata murya sak irin ta Maan ta faɗi daga kitchen, kafin suffar silver humanoid robot ɗin ta bayyana a gabansu, a yanayin jikinta macace, kasancewarta macen, amma kuma jikinta babu kaya, da zallarƙarfen silver kawai aka yita, yanayin ƙirarta irin mutum ce, tafiya ce kawai ba ta yi, sai wasu tayoyi da ya saka a ƙasan ƙafafunta. Kuma cikin tafiyarta ta tayar ta iso gabansu tana kallonsu. “Ki sakawa Feeq abinci a filas, zai tafi wurin aiki” “Ok Maa!” Har ta juya Ram ya kirata, jin muryarta ta fito kamar ganga ta fashe. “Kiyara wait” Kiyara ta tsaya kana ta juyowa. Miƙewa ya yi ya isa gareta. “Me ya samu muryarki?” Kiyara ta ci gaba da kallonsa da idanuwanta da suka kasance haske kamar tocila. “Sashen magana... Na jikina... Ne... Ya lalace!” Ta faɗi muryarta na ƙara hargitsewa. “Bolbo kawo min screwdriver!” Ram ya ƙwalla kiran sunan. Bayan shuɗewar wasu sakkani, sai ga wani abu ya fito daga ɗaya daga cikin ƙofafin dake falon, abun de gajere ne, kuma ba normal tafiya yake ba, gangarawa yake a ƙasa kamar ball, a kallo ɗaya de ba za ka iya fasalta yanayin suffar abun ba. Tsayawa ya yi a kusa da Ram, sannan fitar da wani dogon abu me kama da hannu, ya miƙawa Ram screwdrivern da ya buƙata, Ram ya karɓa. “Thanks Bolbo1” “You got it, Ram!” Muryar abun me kama da ta kiriku ta faɗi yana komawa ɗakin da ya fito daga cikinsa. Ram ya zagaya zuwa bayan Kiyara, sannan ya danna wani switch a bayan nata. Nan take hasken idon Kiyaran ya ɗauke, kanta ya sunkuya ƙasa, saboda switching off ɗinta da ya yi. Wani murfi ya buɗe a bayanta, ya yi amfani da screwdrivern hannunsa ya gyara wurin da ya samu matsala a jikinta, ya mayar da murfin ya rufe, sannan ya danna switch. “Hello Kiyara H178rs9Q12!” Ya faɗi yana kallon fuskarta. “Hey RAFEEQ AHMAD MUHAMMAD!” Muryar Kiyara da ta dawo dai-dai ta faɗi. Ram ya yi murmushi yana aje screwdrivern a kan danning. “Yi sauri ki kawomin abincin” Kiyara ta juya a kan tayoyin ƙafarta, ta shiga kitchen. Jim kaɗan ta dawo ta kawo masa wani flask me ɗauke da abincin da ta girka a ranar, Ram ya karɓa yana mata godiya, sannan ya saka a backpack ɗinsa ya yiwa ma Maa sallama, ya fita. A ƙofar entrance ya tsaya yana kallon kekensa dake ake a gefen ɗan ƙaramin compound ɗin gidan. Kasancewar keke yake hawa idan yana USA, dan motarsa tana Nigeria, jakarsa ya goya a bayansa, sannan ya isa wurin keken, ya ɗauka, ya buɗe ƙofa ya fice, ya hau kan titi ya fara tsuga gudu. Kuma bai dakata ba sai da ya iso GrowTech, haɗɗaɗɗen kamfanin sarrafa na'ura me ƙwaƙwalwa, Kamfanin ƙirƙirar robot, kuma Centre ɗin AI (Artificial Intelligence) da ake ji da shi a kaf faɗin USA. Ginin kamfanin ya kasance na beni me hawa 13, yanayin kyan ginin kaɗai ya isa ya tabbatar maka da muhimmancin ma'aikatar. A parking lot ɗin dake ƙasan kamfanin ya aje kekensa, sannan ya nufi ƙofar entrance. Yana tura ƙofar wani abu ya zo ya wuce ta saman kansa yiffff, hakan ya sa ya kaucewa abun yana binsa da kallo. “My bad Ram!... Sorry!” Muryar Henry dake riƙe da remote control ɗin drone ɗin ta faɗi yana kallonsa. Ram da ya juya yana kallon dron ɗin da ya wuce shi, ya juyo ya kalli Henry ɗin. Kafin ya sakar masa murmushi yana faɗin. “Ba komai” Kafin ya raɓa Henry ɗin ya wuce. Shi kansa reception ɗin ma'aikatar abun kallo ne, robotics da harkar AI ce kawai za ka yi ta gani a wurin iya ka ganin idonka. Ko da Ram ya isa elevator shiga ya yi, sannan ya danna hawa na 10, inda office ɗinsa yake. “Kai tun ɗazu ake ta jiranka amma sai yanzu ka zo?” Abu na farko da Abdulrahman babban abokinsa a ma'aikatar ya fara faɗi kenan lokacin da suka haɗu. Ram ya sosa wuyansa setin inda tattoo ɗin sunansa yake, sannan yace. “Wai me yake faruwa ne?” “Wani tantirin aka samu ya datsi babbar na'ura!” Ram ya kalleshi na wasu 'yan sakkani. To wai duk akan an datsi na'ura shi ne ya ga ma'aikatar ta rikice?, shi ai a nan bai ga abun tada hankali ba. “Ram! Mr. Rafeeq!” Aka ƙwala kiran sunayen biyu daga bayansu, hakan ya sa su duka suka kalli wurin, Isabella ce ta iso wurin tana ta haki saboda gudun da ta yi. “Sir Thomas yana jiranka a control room” Ta faɗi tana juyawa, ba tare da Ram da Abdulrahman sun ƙara cewa komai ba, suka bi bayanta har zuwa control room ɗin. “Na gode Allah da ka zo Ram!” Cewar Mr. Thomas yana kallon Ram ɗin da ya shigo wurin. Ram ya shiga bin ƙaton allon glass ɗin dake sama. “Gaba ɗaya na'urorinmu aka datsa, sannan ana ɗaukar bayanan mu na sirri zuwa wata computerr” Cewar Isabella, Ram ya ja kujera ya zauna yana sauƙe jakar bayansa. “Dan Allah Ram ka san abun yi, sun kusa kwashe duka bayananmu” Cewar Mr. Thomas hankali tashe. A nutse Ram ya fito da laptop ɗinsa dake cikin jaka, sannan ya aje ta akan wani table yana buɗeta. Danne-danne ya shiga yi yana duba allon glass ɗin nan. Kowa ya yi shiru, ana jiran ganin warwarewar matsalar, saboda tun da ha Ram ya zo, komai ya zo ƙarshe. Cikin abun da bai fi muntuna uku ba, ya cire wani flash drive daga jikin laptop ɗinsa ya miƙawa Isabella. “Ki yi sauri ki saka a jikin babbar na'urar” Ta karɓa da sauri tana nufar wurin babban system ɗin, buɗewa ta yi, sannan ta saka flash ɗin. Daga nan kuma sai kallon kowa ya koma kan babban allon glashin nan. Sakan ɗaya... Biyu... Uku... A sakan na uku ne, komai ya tsaya cak, duka naurorin suka ɗauke. Mr. Thomas ya buɗe baki zai yi wa Ram magana, na'urorin suka kawo wuta. Komai ya dawo dai-dai, na'urorin suka dawo under control ɗinsu. Sauran ma'aikatan wurin suka sa ihu, har da masu tafi. Ram ya miƙe yana rufe laptop ɗinsa. Mr. Thomas ya dafa kafaɗarsa cike da alfahari, don zai iya cewa kaf ma'aikatar tasu babu wanda ya kai Ram fasahar sanin kan na'ura me ƙwaƙwalwa, haka robot. “Ina alfahari da kai Mr. Rafeeq” Ram ya yi murmushi yana sosa gemunsa. “Godiya nake” “Kwana biyu na lura da baka zuwa, fatan dai lafiya?” Mr. Thomas ya tambaya, a sanda suka fito daga control room ɗin. Ram ya gyara zaman backpack ɗin bayansa. “Ka san ina tsara ɓangaren karɓar bayanai na AI humanoid robot ɗin nan nawa, shi ya sa ba na fitowa” “Shi ya sa na ga ka tara gemu?” Ram ya yi dariya yana shafa gemun nasa. A lokacin kuma Mr. Thomas ya tsaya, hakan ya sa Ram ɗin ma tsayawa suka fuskanci juna. “Zuwa gobe baƙin da muke jira za su zo, sun ce za su zo su ga device ɗin, kuma suna so su yi testing ɗinsa, idan har ta musu za a iya ƙera musu wasunsu, dan haka ya kamata ka zo” Ram ya gyaɗa kansa, don ya gane wasu mutanene za su zo ɗin, mutanen da saboda su aka ɗauko shi daga branch ɗin GrowTech na Nigeria aka kawoshi na USA, don kawai ya haɗa musu device ɗin ake amfani da shi yasa mota tuƙa kanta da kanta, wato self-driving car. Kuma a zamansa na wata huɗu da ya yi a garin, ya samu nasarar haɗa musu device ɗin da yake saka mota a self-driving mode, duk da ba shi ne karo na farko da ya fara ƙera device ɗin ba, saboda ko motarsa tqna tafiya a kan tsarin self-driving ne. Kuma yanzu shi ne masu kamfanin motar za su zo don su duba device ɗin. “Sai goben” Mr. Thomas ya faɗi yana miƙa masa hannu, alamun su gaisa, shi ma miƙa masa hannun ya yi, suka gaisa sannan ya juya yana kiran Abdulrahman. * RAFEEQ AHMAD MUHAMMAD, wanda aka fi sani da RAM haifaffen ƙasar Nigeria ne. A asalin sunan mahaifiyarsa shi ne Salamatu. Salamatu ta kasance ɗaya daga cikin fulanin tashi na rigar Shariga. A cikin yawon kafa rigarsu ne suka sauƙa a wani daji dake kusa da garin Nguru dake jahar Yobe. Saida nono ya kasance sana'a ga duka matan aure da 'yan matan rigar. Hakan ya sa bayan sun sauƙa a dajin suka fara kaiwa tallar nono cikin garin Nguru. Kuma a nan ne Allah ya haɗa Salamatu da wani buzun Niger me sunan Ahmadu. Tun farkon haɗuwarta da shi ya sanar mata da cewar shi maraya ne, kuma ci rani shi ne abun da ya kawoshi ƙasar Nigeria. Kan ka ce me soyyaya me ƙarfi ta ƙullu tsakanin Salamatu da Ahmadu. Har ta kai ga Ahmadu ya fara mata zancen aure. Hakan ta sa Salamatu turashi zuwa ga mahaifinta. Ahmadu da limamin masallacin unguwar Hausari da Ahmadun ya sauƙa a gidan dake maƙotaka da nasa suka shirya domin zuwa nemawa Ahmadu auren Salamatu ɗiyar fulanin rifar Shariga. Ko da suka je ba su samu tarbar girmamawa dag mahaifin Salamatun ba, don korar kare ya musu, tare da faɗa musu cewar shi ba zai aura wa 'yarsa kaɗo ba ma bare a je ga wata ƙabila da babu irinta a Nigeria wai su buzaye, don haka kada ya ƙara ganin ƙafarsu. Haka Ahmadu da limamin nan me sunan Zakar suka kwaso ƙafafunsa gwiwoyi a sanyaye suka dawo Nguru. Ba don Ahmadu ya so ba, sai dan ya zame masa dole haka ya haƙura da soyyayar Salamatu, ya ci gaba da gudanar da sana'arsa ta kayan miya a kasuwar Nguru. Kwatsam rana ɗaya sai ga Salamu a rumfar saida kayan miyan nasa, ganinta da kaya ba ƙaramin ɗaga masa hankali ya yi ba, ko da ya tambayeta me yake faruwa sai take sanar masa da cewar ita ta gudo daga rigarsu ne don su yi aure, a lokacin sai ya shiga yunƙurin ganar da ita kuskuren aikata hakan amma saboda soyyaya ta rufe mata ido sai ta nuna masa cewar ita fa ta riga da ta yanke hukunci, idan yana sonta su yi aure kawai, idan kuma ba ya sonta zata shiga duniya. Gudun rasata ya sa ya amince da cewar za su yi auren, ya ɗauketa ya kaita gidan Kawu Zakar, sannan ya tsara masa halin da ake ciki, hatta da shi kansa kawu Zakar ɗin sai da ya yi ƙoƙarin ganin ya nunawa Salamatu kuskurenta, amma ta ƙi yarda da abun da yace. Washe garin ranar da Salamatu ta gudo daga rigarsu, aka ɗaura aurenta da na Ahmadu, a ka sakata a gidan da Ahmadun ke haya, wanda yake kusa dana kawu Zakar. Tun kafin aurensu, Ahmadu ya riga da ya sanar mata da matsalar ciwon zuciya da yake fama da shi, wanda ya yi gadonsa daga wurin mahaifinsa. Kuma bayan aurensu da shekara ɗaya ciwon nasa ya fara ƙamari, tun yanayin ciwon a tattafe, har ta kaishi ga kwanciya, a lokacin suna da shekara uku da aure, kuma a lokacin ta samu ciki. Bayan doguwar jinyar da ya yi fama a ita ta tsawon shekaru Allah ya amshi ran Ahmadu. Ba ƙaramar damuwa mutuwarsa ta saka Salamatu ba, don har sai da aka bata gado a asibiti, ga tsohon cikinta haihuwa yau ko gobe, bayan an tasota daga asibitin, kawu Zakar yace ta dawo gidansa da zama. Ta ci gaba da zama da matarsa da kuma yaransa biyu. Bayan wasu wattani Salamatu ta haihu, ta haifo kyakkyawan yaronta na miji, wanda yake tsananin kama da ita, a lokacin sumar kansa ce kawai irin ta Ahmadu. Bayan haihuwarta da wata uku, kawu Zakar ya tisata a gaba suka tafi zuwa rigar Shariga, domin ta je ta nemi yafiyar mahaifinta. Sai de kuma kash, sun makara, don kuwa ba su tarar da kowa a rigar ba sai wani mutu ɗaya, kuma shi ne ya sanar musu da cewar ai mahaifin Salamutu ya rasu shekara ɗaya baya, mahafiyarta kam da ma ta daɗe da rasuwa. Ƙawarta Dija ce kaɗai ta rage. Kuma sauran mutanen rigar sun tashi, ko shi ma ya saida wasu daga cikin shanunsa ne yana jiran a bashi kuɗin, daga an bashi zai bi bayansu. Amma kuma ya sanar musu da cewar mahafin Salamatun bai rasu ba sai da yace ya yafe mata. Haka Salamatu ta sha kukanta ta gode Allah, kafin ta ɗauki ɗanta ta bi kawu Zakar zuwa Nguru. Haka ta ci gaba da zama a gidansa, tana renon ɗanta me suna Rafeeq. A lokacin da Rafeeq ya fara tasawa ta fuskanci cewar nauyi ya yiwa kawu Zakar yawa, hakan ya sa ta shiga yin sana'o'i da ban da ban, duk domin ganin goben ɗanta ta yi kyau. Rafeeq na da shekara biyar a duniya suka fara fanin alamun ciwon mahaifinsa tare da shi, kawu Zakar da kansa ya ɗauke shi ya kaishi asibiti, kuma a asibitin ne suka sanar musu da cewar ciwon zuciya yake ɗauke da shi,wanda suke kyautata zaton gadarsa ya yi. Haka suka jera musu tarin ƙa'idojin da ya kamata ace sun kiyaye ganin ɗan nasu ya samu sauƙi, don babu batun warkewa gaba ɗaya a ciwon nasa. Salamatu da Rafeeq ke kira da Maa tun yana yaro, ta ci gaba da fafutuka wurin ganin ɗanta Rafeeq ya taso cikin gata da kuma turba ta gari. Tun Rafeeq na ƙarami alamun baiwa da hazaƙarsu suka fara bayyana. Domin shi ba kamar sauran yara gama gari yake ba, akwai shi da wata irin ƙwaƙwalwa me kaifi da kuma saurin haddace abu, ga shi da sanin makamar ƙirƙire ƙiren abubuwa. Yana ss2 a makaranta ya ƙera wani jirgin helicopter na kwali, hakan ya sa malaman makarantarsu suka ɗauki jirgin zuwa local government secretaria, daga nan ya tafi zuwa government house, kuma a nan ne aka saka sunansa a jerin ɗaliban da za su tafi ƙasar America domin yin karatun gaba da sakandire. A lokacin ba ƙaramin farin ciki suka shiga ba shi da mahaifiyarsa, don Maa har da hawayenta. Bayan Rafeeq ya kamlla secondary kai tsaye ya wuce ƙasar USA domin ci gaba da karatunsa na matakin jami'a, inda ya fara karantar fannin mechatronics engineering. Kuma ko bayan da ya gama degree be dawo ba sai da ya haɗa da masters. Ko a lokacin da ya na Universityn babu wanda bai san RAFEEQ AHMAD MUHAMMAD ba, kuma tsabar ƙoƙarinsa da sanin kan computer ne ya sa aka laƙabamasa sunan RAM, wato (Random Access Memory), wasu kuma kan kirashi da sunan ne domin su rage yawan sunansa, don idan ka kira sunan nasa a taƙaice RAM ɗin zai baka. Ƙwazonsa da hazaƙarsa ne ya sa bayan ya kammala makarantar manyan kamfanonin ƙere-ƙeren robotics da na software suka riƙa kawo masa dammamaki na yin aiki a ƙarƙashinsu. Amma haka ya toshe kunnensa ya nuna sam shi ba ya buƙatar zama a ƙasarsu, ya fi so ya koma tasa ƙasar,domin su amfana a baiwar da yake da ita. Su kuma sam ba sa so su yi asarar ɗan baiwa kamar sa, hakan ya sa wani kamfani me sunan ‘GrowTech’ da suke da branch a Nigeria suka ba shi aiki. Kuma sai suka yi sa'a ya karɓi aikin. Daga nan ya tattara nasa ya nasa ya antayo Nigeria. Sosai Maa ta yi farin cikin ganin tilon ɗan nata bayan shafewar tsawon shekaru, don tun bayan tafiyarsa ko sau ɗaya bai leƙo gida ba. Satinsa biyu a garin Nguru, ya ɗauki Maa suka shilla garin Abuja, a inda branch ɗin GrowTech ɗin yake, kuma da kuɗaɗen da suka ba shi ya sai musu wani madaidaicin kyakkyawan gida. Sai de kuma a sunane yake ya bar USA, don har wa yau idan wani aiki ya tashi sai ya koma can ya je ya yi, hakan ta sa a can ɗin ma ya siyi gidan da zasu riƙa zama idan sun sauƙa a can US ɗin. ________ _Kun dai ji yanda tafiyar ta soma_ _Kun tuna da RAM ma'aikaci a ƙarƙashin KULIYA da ZAID?_ _To shi ne wagga_ A. ISAH CE✍️. 08131549317 °°°°°°°°°°°°°°°° *💡️HASKE...️💡* *©SALMA AHMAD ISAH* TAURARI WRITER'S ASSOCIATION. *Page 04* ~~~ *Ƙauyen Wagini, Batsari local government, Katsina state, Nigeria.* *07:00 na safe.* A cikin wani madaidaicin gidan ƙasa, wanda ya ƙunshi ɗakuna huɗu, uku daga cikin gidan, ya yin da ɗaya ya kasance a soron gidan, wata farar mata da a ƙiyasin shekaru ba zata wuce shekara 44 ba, ta fito daga wani ɗaki ta na hama tare da miƙa, ɗankwalin kanta da ya since ta kai hannu tanan gyarawa, a lokancin da idonta ya. Kai kan tilon 'yarta dake zaune a rumfar da suka saba girki tana hura wuta. A lokaci guda ta saki murmushi. “SALAME!” Ta kira sunaun tana kallonta. A hankali matashiyar ta juyo tana aje maficin hannunta. “Har kin tashi Inna?... Ina kwana” Matar ta ƙarasa. Kusa da rumfar tana amsa gaisuwarta. “Yayanki ya dawo?” Salame ta ɗauki maficin tana amsawa da. “Eh to, na ji motsinsa sanda na fito, amma ban sani ba ko ya ƙara fita” Inna ta juya ta kalli hanyar soro, kasancewar ɗakin yayan Salamen a soron yake. “Audu! Audu!” Ta ƙwala kiran sunan yayan Salamen. “Na'am Inna, gani nan” Suka ji muryar Audu ta faɗi daga soro, kafin kuma ya shigo cikin gidan, har ƙasa ya tsugunna yana gaida mahaifiyar tasu, sai da ta amsa shi, tukkuna ya miƙe tsaye. “Hamma Audu ina kwana” Salame ta. Faɗi tana duban yayanta, da murmushinsa yace. “Lafiya ƙalau Salma... Fatan kin tashi lafiya?” Ya kirata da sunanta na gaskiya, kamar yadda ya saba kiranta da shi. Amsashi ta yi tana ɗora tukuyar ɗumamen dake aje a gefenta a kan murhu. “Yau Muja lafiya?, Dan ban ga ya je masallci ba” Cewar Audu yana duban mahaifiyarsu. “Ah-ah, bai je masallaci ba kuma?. Sai da na tasheshi fa” Inna ta faɗi tana duban ƙofar ɗakinta, inda ta san autan nata na ciki yana bacci. “Ai kuwa bai je masallaci ba” “Mts! Ba ri na je na taso shi” Ta faɗi tana nufar ɗikinta. Yayin da Audu kuma ya nufi ɗakin babansu dake wani sashi na gidan. Salame kuma ta ci gaba da firfita wutar murhun dake gabanta. “Inna na yi sallah fa” Cewar Mujan da Inna ta samu nasarar koro ƙeyarsa daga ɗakinta. Ya fito sai murza ido yake. Salame ta kalleshi. “Banda ƙarya auta, na san ba ka yi sallahr nan ba fa” Salamen ta faɗi tana ci gaba da dubansa. Kuma a lokacin Inna ta fito daga ɗakin, ta ɗaga carbin da ta saba lazimi da shi ta cauɗawa autan nata a bayansa tana faɗin. “Ai Wallahi Muja sai kowa ya ji kan mu ni da Kai a cikin gidan nan, in dai a kan Sallah ne, sai na yi maganinka, saboda iskanci irin naka, na tasheka dan ka je ka yi sallahr sai ka koma ka kwanta dan ka raina ni?!” Tun bayan da ta samu nasarar cauɗa masa carbin ya finciki buta ya shiga banɗaki da gudu. Salame da Audu me za su yi in ba dariya ba. “Ah-ah, ke Dija! A kan me za ki dakar min jika da safiyar Allah ta'ala!” Cewar kakarsu Iya Abu tana ɗage labulen ɗakinta, tare da leƙowa kanta. “Sallah ce fa be yi ba ” Salame ta bata amsa tana dariya. Iya Abu ta ƙarasa fitowa daga ɗakin tana yatsina fuska. “Kuma dan be yi sallah ba shi ne zata dake shi? Ai har yanzu Mujahid yaro ne, da sauransa, sai ana ɗaga masa ƙafa” “Ban da abunki Iya, Muja fa ya kai shekara goma, idan be fara yin salah tun daga yanzu ba sai yaushe kenan?” Inna Dija ta tambaya. Iya Abu na bata amsa, Baba ya fito daga ɗakinsa yana kallon Audu dake tsaye a bakin ɗakin. Audu na dariya suka ƙara gaisawa da maihaifin nasu, kasancewar tare suka je sallahr asuba. “Iya kuma ma fa na yi sallahr, masanllacin ne kawai ban je ba” Muja ya faɗi yana fitowa daga banɗakin, sai cuno baki gaba yake. “Zo nan ɗan jikkallena, ai na san za ka yi sallahr, su ne ba su sanka ba” Iya Abu ta faɗi tana miƙa masa hannu, a ɗarare ya gifta Inna ya isa zuwa ga Iya Abu, duk kuwa da ya san ba lalle Innan ta sake dukansa ba, tun da ga Iya abu da Baba a wurin. “Ka zo ka siyo mana koko a gidan Marka” Cewar Inna tana miƙa ma ɗari biyu. Iya Abu ta kai hannu ta fisge kuɗi. “Kai Sa'adu! Wai ni kai ne ka ɗaurewa Dija gindi take bautar mi da jika?” Baba dake tsaye a ƙofar ɗakinsa ya girgiza kai. “Ni a wa? Kare da gudun layya, Wallahi Iya ban san zancen ba” Iya Abu ta yi ƙwafa. “Ke Salame sai ki tashi ki je ki siyo kokon, jikana bai ƙoshi da bacci ba, dan haka zai koma” Ta ƙara she tana miƙawa Salame kuɗin. Salame ta miƙe, ta ja hijabinta na yadin tayabo yalo, dake rataye a jikin igiyar shanya. Ta saka hijabin, sannan ta karɓi kuɗin. Ta fita tana dariya. Tana fita daga gidan suka haɗu da ƙawarta Karime. “Salame in zuwa haka?” Salame ta tsaya tana kallonta. “Siyan koko zan je, yanzu Iya Abu ta tada balli da sassafen nan, wai auta ba zai je siyan koko ba” Karime ta yi dariya yayin da suka ci gaba da tafiya, dan ita ma gidan Markan ta nufa. “Iya Abu hoo... Yau za ki je yin ice?” Salame ta gyaɗa mata kai. “Kin san yau ranar kasuwa, baba da hamma za su je kasuwa, shegiyar ƙiwar auta ba za ta barshi ya je daji ba, dan haka babu me zuwan sai ni...” Haka suka ci gaba da hira har suka kai gidan Marka me koko. A tare suka dawo bayan sun sai kokon, Salame ta shiga gidansu, yayin da ita ma Karime ta wuce nasu gidan dake ɗan gaba da na su Salame. ________________ *11:04 na rana.* “Zo ka raka ni auta” Cewar Salame tana zura hijabinta dake riƙe a hannunta. Auta dake zaune yana haɗa dokin kara a tsakar gidan, ya ɗago da kansa ya kalleta. “Ina?” Ya tambaya. “Yin ice” Ta bashi amsa tana dubansa. Inna dake zaune a kan tabarma tana tsintar shinkafa ta dubesu tana faɗin. “Ba tare da Karime kika ce zaku je ba?” Salame ta dubeta. “Eh, ina so na yi itacen da yawa, kin ga ai sai ya tayani da ɗauka ko?” “Kuma haka ne” Inna ta faɗa tana meda hankalinta kan tsintar da take. “Ko ba zaka je ba?” Salame ta tambaya ganin Mujan ba shi da niyyar miƙewa. “Idan ba zai je ba kar ki takurashi mana” Cewar Iya Abu da ta fito daga banɗaki, hannunt riƙe da buta. “A'a, zan je” Cewar Muja da ya miƙe tsaye. Salame ta sashi a gaba suka fita. “Kukula fa Salame!” Cewar Iya Abu. “In Allah ya yarda!” Salame ta amsa suna ficewa daga gidan. Sai da suka biya ta gidan su Karime, kafin suka nufi daji dan yin ice. Ko da suka iyo icen Muja be bar Salame ta ɗauka da kanta ba, duka ya loda a kansa yana faɗin. “Muje Adda” Salame ta yi murmushi, duk ƙiwar Muja a kan Salame ba ta aiki, dan zai iya yi wa kowa ƙiwa, amma ban da ita. *Makoko, Lagos State, Nigeria.* *06:44 na yamma.* DIYA SHOLA POV. Tana dawowa daga wurin aiki ta shiga wanka, bayan ta fito ta sauya kayanta, a 'yar rumfar dake gaban gidansu ta iske Papi zaune a kan tabarma kamar kullum, ya miƙe ƙafarsa me lafiya, yayin da guntilalliyar ƙafar tasa ke nan a yanda take. Ɗaki ta shiga, inda ta iske Gigi tana zuba musu eba da stew ɗin da ta girka. “Yauwwa Diya, zo ki miƙawa Ekene nasa” Cewar Gigin tana miƙa mata kwanon dake ɗauke da anbincin Ekene. Shola ta saka ɗan ƙaramin farin hijanbin data saba sakawa, sannan ta ɗauki kwanon tana faɗin. “O dara (To)” Fita ta yi daga ɗankin, ta wuce Papi dake zaune a kan tabarma. “Ina zaki je?” Ya tambayeta. “Ekene zan miƙawa abinci” Ta amsa masa tana juyowa, kansa ya gyaɗa mata sannan ta juya ta tsaya a jikin rumfar gidan kwanan su Ekene ta shiga ƙwala masa kira. Asalin sunan Ekene shi ne Musa, musulmi ne kuma ɗan ƙabilar igbo, haifaffen wani ƙauye ne dake can Enugu. Tun yana ƙarami iyayensa suka rasu, kuma ya girma ne a hannun wani kawunsa da matarsa da yasha wahala a wurinsu, bayan ya girma ne ya gudo daga ƙauyensu ya iyo garin lagos. Kuma tun bayan zuwansa Makoko Allah ya haɗa jininsu da Gigi da kuma Diya, hakan tasa ya zama kamar ɗan gidan, dan har kwanan gobe ba shi da 'yan uwan da suka wuce su Gigi, sai abokansa da suke kwana tare. “Musa! Musa!...” Shola ta kira sunansa na gaskiya, jin har yanzu bai amsa ba balle ya fito. “Mu kin cika mana kunne da kiran Ekene, ni ba kya nema na?” Diya ta juya ta kalli gidan dake manne da nasu, dan ta san muryar babbar ƙawarta ce, FA'IZA. Kuma kamar yanda ta sani, ita ɗin ce ta leƙo daga tagar ɗakinsu. Sai wani murmushi take mata. “Ni ban sanki ba” Cewar Diya cikin harshen yarbanci. Fa'ee ta wurgo mata harara. “Wata gulma ce kuma ta sauya harshen?. Malama ina za ki min hausa ki min, ni bana san gulma ehe!” Fa'ee ta ƙarashe tana ƙara manna mata harara. Shola ta yi murmushi. “Wasa nake miki fa, ina nemanki Allah, ɗazu kafin na fita ma sai da na tambayi Mama ina kike, tace min wai kin je aiki” Ta faɗi cikin harshen Hausa, kamar ita kaɗai ce yaran da ta iya. Fa'iza ta fito daga ɗakinsu tana taka katakwayen da suka haɗa gidansu da na su Shola tana faɗin. “Wallahi, kin san ogan namu ne ba sauƙi, kana kuskurewa zai seta maka hanya” ta ƙarashe tana tsayawa a setinta. “Wai ina Ekene ne?” Fa'ee ta tambaya tana kallon ɗakinsu Ekene. Nan take fuskar Shola ta rikiɗa zuwa damuwa. “Yau da safe ma fa banganshi ba, sai Oliver ne ya fitar da ni, ban sani ba ma ko ba shi da lafiya...” Ta ɗan dakata da maganar, ganin Lamu abokin Ekene ya fito daga ɗakin kwanansu, fuskarsa ɗauke da damuwa yake dubansu. “Lamu ina Ekene?” Diya ta tambaya, ko kafin ya bata amsa, Gigi dake zaune a rumfa ta fito ta tsaya kusa da su hankali tashe, dan duk abun da suke faɗi tana ji, haka Papi ma kallonsu yake, dan ya ji me ke faruwa da Ekene. Lamu ya sunkuyar da kansa yana sosa hannunsa. Sannan ya furta abun da ya zama sannadiyyar haɗuwarsu da dalilin sauyawar rayuwar ɗaya daga cikinsu. “Jiya da daddare muna zaune a rumfarmu ta 'yan fito, 'yan sanda suka zo suka rufamu da duka, daga bisani kuma suka ɗauki Ekene suka tafida shi!” Nan take kwanon Ebar dake hannun Diya ya suɓuce ya faɗo ƙasa. Bakinta a buɗe hankalinta a tashe take duban Lamu. Ita ta san cewa Ekene bai aikata wani lefin da za'a kamashi ba, dole abun da aka saba yi wa sauran matasan Makoko ne ya faɗa kansa. Wannan abun sababbe ne a yankin Makoko, gurɓatattun 'yan sanda dake kusa da yankin Makoko, kan karɓi cin hanci daga hannun manyan masu lefi idan sun kamasu, daga nan sai su sakesu, su zo yankin makoko su kama matasan yankin, sannan sun jefa musu lefin. To bana kuma kan ƙaninta abun ya faɗo?!. *Agha Mansion, Lekki Phase 1, Lagos State, Nigeria.* TAUQEER POV. “You're like a ray of sunshine, Brightening my every day... You're like a breath of fresh air, Filling my lungs with glee... You're like a warm summer breeze, Making me feel free... You're like a song that never ends, Always making me grin... You're my everything, my dear, The joy that I live in...” Waƙar da yake rerawa kenan. Waƙar me sunan Sunshine, na ɗaya daga cikin waƙoƙinsa da ya fi so. Tsaye yake a jikin dressing mirror yana taje sumar kansa irin ta asalin fulani, wadda ba ta cika tsayi ba, kasancewar tana cikin askin buzz cut. Sanye yake da khaki trouser milk color, da kuma baƙar T-shirt, me ɗauke da makeken hoton fuskarsa a gaba, daga ƙasan hoton fuskar tasa kuma sunansa ne a rubuce 'TAUQEER AGHA' yayin da bayan rigar kuma ke ɗauke da rubutun 'GOAT' (Wato Greatest Of All Time). Rigar na ɗaya daga cikin kayansa da ya fiso a duniya. Ba wai dan rigar na da tsada ba, sai dan matsayinta gareshi. Ɗaya daga cikin masoyansa daga ƙasar south Africa ne ya turo masa ita, ranar da ya ƙara yake wani Birthday partynsa. Hakan ya sa yake matuƙar son rigar. Juyawa ya yi ya ɗauki wayarsa bayan da ya gama taje sumar tasa. Sannan ya fita daga ɗakinsa yana nufar babban falon gidan dake down stairs. Yana karyo kwanar da ɗakunan samarin gidan take ya hangi mahaifiyarsa ta fito daga ɗakinta, hannunta riƙe da kwalbar zuma. Wadda ya san a shayin mahaifinsa za'a saka shi. Dan a lokaci irin wannan, mahaifinsa da ƙannensa sukan zauna su sha shayi. Da sauri ya ƙarasa kusa da ita yana rungumarta ta baya. “Ya kike? Habibty” Ya faɗi yana sumbatar gefen fuskarta. Umma ta yi murmushi tana kallonsa yayin da ya saketa. “Lafiyata ƙalau Junior, ya gajiyar hanya?” “Gajiya ta bi jiki Habibty” Ya amsa mata yana karɓar kwalbar hannunta. Tare da ita suka jero har suka sauƙo ƙasa, inda ya iske mutanen gidan gabaki ɗayansu nan zaune. Daga can wani ɓangare na falon iyanyensu maza ne ke zaune suna shan shanyi kamar yanda ya sani, yanyin da a ɗayan ɓangaren kuma, iyayensu mutane ke zaune, kowa yana sabgarsa, daga wani ɓangaren kuma gabaki ɗaya yaran gidan ne ke tasu sabgar. Ɓangaren da iyayensu maza suke ya nufa, yayin da Umma ta nufi inda matan gidan suke, dan daman a wurin take zaune, Abba ya mata magana kan ta ɗauko masa zuman da ya saba sakawa a tea. “Ya kake Habiby?” Tauqeer ya tambaya yana ma Abba side huge. Murmushi kwance a kan fuskar Abba ya amsa masa da. “Lafiya Junior” Abban ya amsa kamar yadda ya saba, kafin Tauqeer ɗin ya shiga gaisawa da kawunansa dake wurin. “Daddy!” Ya kira sunan Daddy da ɗan ƙarfi, ganin ya kirashi har sau biyu bai amsa ba, kuma dama can shi haka yake, sau tari za ka ganshi ya zauna ya yi shiru yana tunani, kuma hakan ya samo asali ne sakamakon ɓatan matarsa ta biyu. Firgigit Alhaji Tayyab Agha ya dawo duniyar zahiri ya dubi Tauqeer. Da ƙyar ya ƙaƙalo murmushin yaƙe ya yafa a kan fuskarsa, kamar yadda ya saba jifan sauran jama'a da irin murmushin. Saboda murmushin kan tsaya a kan laɓɓansa ne kawai, dan tun bayan ɓatan matarsa Rahila ya shiga yin irin wannan rayuwar. “Tauqeer!” Ya faɗi yana kallonsa. Tauqeer ya girgiza kansa yana murmushi, hakan ba wai sabon abu ba ne game da kawunasa. “Na'am Daddy” “Ashe ka dawo?, ya Abu Dhabi?” “Wallahi Baffa, yau da yamma na Samu isowa” Baffan ya gyaɗa kansa yana ƙara yin nitso a cikin kogin tunanin da ya saba linƙaya. Alhaji Muzammil Agha ya girgiza kansa yana murmushi. “Hamma kenan” Ya faɗi yana aje newspapern dake hannnunsa. Tauqeer na murmushi ya miƙe zai bar ɓangren nasu, maganar Abba ta dakatar da shi. “Junior” “Na'am Habiby” Ya amsa yana juyowa. “Fatan Munira (matemakiyarsa) ta faɗa maka meeting ɗinka da kamfanin GU Industry a gobe?” Tauqeer ya gyaɗa kansa. “Eh, ɗazu take sanar da ni, kuma insha-Allah zan halarta...” “Tauqeer! Ɗazu na duba jadawalin shige da ficen kaya na watanan, amma ban ga na satin nan ba, kuma Yahaya ya ce min an turawa kamfanin Almak kaya a satin nan” Cewar Alhaji Muzamill Agha. Tauqeer ya gyaɗa kansa cikin faɗin. “Eh, an tura musu kaya, kuma jiya aka sake sabon jadawali, ban san yaushe ka duba ba” Muzamill Agha da yaran gidan ke kira da Baffa ya gyaɗa kansa yana so sa girarsa. “Eh to da yake shekaran jiya na duba jadawalin, shi ya sa ban ga na satin nan ɗin ba” Tauqeer ya gyaɗa kansa. “An sake sabon jadawali, zan tura office ɗinka zu wa gobe” “Ok sai na jika” Baffa ya faɗa yana dubansa, Tauqeer ya juya ya barsu suka ci gaba da hirarsu da suka saba. Daga nan inda iyayensu mata suke ya nufa, ya gaida su ɗaya bayan ɗaya, Hajiya Zayya ta amsa tana wani murmushi da ita kaɗai ta san na miye, Mama ta amsa baki washe kamar yanda ta saba, Amma kuwa kadaran kadahan ta amsa. Ya miƙe ya bar sashen da suke yana nufar inda sauran 'yan uwansa suke. Gaba ɗaya yaran gidan suna wurin, idan ka ɗauke Deena da dama can ita bata zama a cikinsu kamar kowa, sai Jamal da baya gidan, kusan sati biyu. Kusa da Saif ya zauna suna gaisawa, saboda kaf gidan babu wanda jininsu ya haɗu sosai da shi kamar Saif ɗin, duk da tsaurin halin Saif ɗin da kowa ke ga a gidan, ba ya nunawa Tauqeer, dan sosai suke shiri da shi. “Hamma Taj ka ga makin da na samu a Homework ɗina da aka yi marking yau!” Cewar Nimra tana nunawa Taj littafinta. Taj ya aje wayar hannunsa yana karɓar littafin nata. “La la la la! Ai kuwa kin yi ƙoƙari mutuniyar” Nimra ta ƙyalƙyale da dariyar jin daɗi. “Nawa ta samu?” Hammad ya tambaya yana matsawa kusa da su. Taj ya karkata masa littafin yana bashi amsa da. “7 a cikin 10” Hammad ya karɓi littafin nata yana ci gaba da dubawa. “Suuuuu! Yarinya ta ciyo ta bayan Ronaldo!” Gaba ɗaya suka kwashe da dariya, dan sak irin abun da Ronaldo ɗin ke yi a duk sanda ya yi nasara a wasansa ya gwada. “Kai fa Aabis?” Tauqeer ya tambaya. Da gudunsa Aabis ɗin ya miƙa masa littafin. Kuma tun kafin ya duba abun da ya samu, Aabis ɗin yace. “9 over 10!” “Give me five my friend” Tauqeer ya faɗi yana miƙa masa hannu, Aabis ya ɗaga nasa hannun suna tafawa. “Miƙomin ni ma na gani” Cewar Nasir yana miƙo masa hannu. Tauqeer ya miƙa masa littafin yana faɗin. “Next time ina so ka cin ye duka. Ni na san me zan baka” Ya ƙarashe yana duban Aabis ɗin. “Omoh! Wannan yarinyar fa tana wuta!” Cewar Iqra, a sanda ta gama duba littafin Nimra dake zaune a gefenta. Saif ne ya lura da Bobo da Khabir dake zaune a gefe suna zazzara ido. Zamansa ya gyara yana aje mug ɗin hannunsa. “Bobo, Khabir! Ina naku homework ɗin?” Khabir ya haɗiye yawu, yayin da Bobo ya ci gaba da cin meat pie ɗin dake hannunsa. “Ba ku ji me nace ba ne?” Ya faɗi yana tsaresu da ido, tuni suka shiga taitayinsu, dan da ma kaf gidan babu me zafin rai irin na Saif, kuma halin nasa shi ne ya banbanta shi da Taj. “Nawa ku ka samu?” Hammad ya tambaya, a sanda hankalin kowa ya dawo kansu. “Ni... Ni... Ni 4 na samu” Khabir ya faɗa. “Kai kuma fa?” Taj ya tambayi Bobo. “2 na samu” “Aikin kenan ai, har gwanda Khabir a kan kai Bobo, ban da ci babu abun da ka iya!” Bobo ya turo baki gaba yana aje meat pie ɗin hannunsa. “To yanzu Hamma Saif idan mutum bai ci abinci ba me zai ci?” “Za ka ci duka!” Haka suka ci gaba da yi wa Khabir da Bobo faɗa a kan rashin meda hankalin da suke a kan karatunsu. A dai-dai lokacin Deena ta fito daga kitchen, hannunta riƙe da wani bowl me ɗauke da vanilla yoghurt, ɗayan hannun nata riƙe da wayarta tana dannawa. Tana sanye da pyjamas. Kwatsam ta ci karo da mutum, hakan ya sa yoghurt ɗin dake hannunta zubewa a jikinta. Nan take jikin 'yar aikin gidan me suna Aliya ya shiga ɓari, dan ta san wata ƙila yau tata ta ƙare, har ƙasa ta tsugunna tana bata haƙuri, tuni ta fara hawaye. “Dan Allah Madam ki yi haƙuri, ki yi haƙuri dan Allah, na yi ta kauce miki, ke ce kika bangaje ni!” Deena ta kalli jikinta, sannan ta kalli Aliyan dake durƙushe a gabanta jikinta na kyarma, hannunta ta ɗaga ta sharara mata marin da ya sa Aliyan ɗaukewa wuta. “Shashasha talakar banza, ke har kin isa ki goga jikinki da nawa? Waye ibanki a Lagos? ” Aliya ta share ƙwalla tana miƙewa tsaye, hannunta dafe da kuncinta. “Ki yi haƙuri Madam, amma Wallahi ke ce baki lura ba!...” Hannunta ta ƙara ɗagawa za ta ƙara mata wani marin, ta ji an riƙe hannun nata, ta juyo a fusace ta fisge hannun nata. Cikin matsanancin ɓacin rai ta ci gaba da kallon Saif da ya riƙe mata hannu, dan a duniyar Allahr nan, babu wanda ta tsana kamar Saif ɗin, dan shi ne wanda yake shige mata hanci da ƙudundune. “Kai waye da za ka riƙemun hannu, SAIFUDEEN MAS'UD AGHA?” Ta kira cikakken sunan nasa kamar yadda ta saba. Saif ya shiga goge hannunsa yana faɗin. “Ni ne ya kamata na tuhumi kaina da na riƙe hannun mace mara sanin darajar kanta irinki!” Deena ta yi murmushi tana ci gaba da dubansa. “Saifudeen Agha kai ba sa'an yin faɗana ba ne, dan haka ba ni da lokacin ɓatawa a kanka, ka bari sai ka kai stage ɗin da nake tukunna” Ta juya tana shirin barin wurin. “A haka za ki ƙare babu mijin aure!” Abba ne ya daka masa tsawa cikin faɗin. “Wata irin magana ce wannan Saif? A matsayinta na 'yar uwarka kuma ƙanwarka ya zaka na faɗa mata haka? Memakon ka yi faɗa da duk wanda zai faɗa mata haka sai kai kana faɗa da kanka? Ku kenan kullum cikin faɗa kamar kaji!...” Deena ko juyowa ba ta yi ba ta haye sama. Shi kuma Saif ya sunkuyar da kansa yana bawa Abba haƙuri. Tauqeer dake zaune saɓanin sauran mutanen falon da suka miƙe tsaye tun bayan fara faɗan Deena da Saif ya dafe kansa, dan ya san da ma dole abun ya gangaro zuwa kansa. Damuwarsa biyu ce a duniya, auren Deena da baya so da kuma halin da ƙaninsa ke ciki!. “Dare ya yi, kowa ya je ya nemi makwanci!” Cewar Mas'ud Agha cike da umarni, ɗaya bayan ɗaya yaran suka shiga watsewa suna nufar ɗakunansu. Sai da kowa ya watse a falon, sannan Hajiya Zayya da aka bari ita kaɗai, ta cije leɓenta na ƙasa tana jijjiga kai, dole ne ta yi wa tufkar hanci. ___________ _Hello!. Salmanians!_ _Shin da wa kuke ganin Fa'ee da Diya za su haɗu?_ _Kuma shin wani hali ƙanin Tauqeer wato Jamal ke ciki?_ _Me nene a ran wannan Hajjiya Zayyan?_ A. ISAH CE✍️. 08131549317 °°°°°°°°°°°°°°°° *💡️HASKE...💡️* *©SALMA AHMAD ISAH* TAURARI WRITER'S ASSOCIATION. *Page 05* ~~~ DIYA POV. Da gudu ta shiga cikin ofishin 'yan sandan dake yankin Makoko. Fa'ee ce biye da ita, gaba ɗaya hankalinsu a tashe yake. “Yallaɓai! Yallaɓai! Ƙanina! Ƙanina Yallaɓai...” Shi ne abun da ta shiga faɗi kenan tana hawaye. “Me ya faru za ku zo kuna neman tada mana hankali?” Cewar wani baƙin ɗan sanda me shirgegen ciki yana susar kunne. Diya ta share ƙwallarta tana faɗin. “Ƙanina Yallaɓai, an kamashi ba tare da ya aikata laifin komai ba!” Sheƙeƙe 'yan sanda dake bakin aiki su biyu suka kallesu. “Me kike nufi da bai aikata laifin komai ba?” Cewar ɗaya ƙyamurmurin ɗan sandan yana ƙarewa hallitar jikin Diyan kallo. A wannan karon sai ta kasa magana, dan haka Fa'ee tace. “Yallaɓai ƙaninta ne aka kama ba tare da ya aikata laifin komai ba...” “Ke! I mana shiru! Kuma da aka kama shi sai aka ce yana nan ko?” Baƙin ɗan sandan ya faɗi cikin daka musu tsawa. Ekene Musa dake zaune a cikin cell ya ji kamar muryar 'yar uwarsa na kuka a waje, hakan ya sa ya miƙe daga inda yake zaune ya leƙo ta tskanin ƙarafunan cell ɗin ya kallesu, a lokacin da take ci gaba da yi wa ɗan sandan bayani. Nan take ƙwalla ta cika idonsa, shi da ma ya san cewa Diya ba zata barshi haka ba, babu abun da ya haɗashi da ita, amma ya san da cewa tana jinsa a ranta kamar ɗan uwanta na jini. A sanyaye ya kira sunanta. “Diya!...” Da ƙyar muryar tasa ta fito cikin kiran sunan, Diya data ke ci gaba da yi wa 'yan sandan bayani, ta kalli ƙofar cell ɗin da ta ji kamar muryar ɗan uwanta. Nan take hankalinta ya yi mugun tashi, ganin fuskar ɗan uwan nata da ta ci duka. “Ekene!” Ta kira sunan a iyaka kan leɓenta. Hawaye wasu na bin wasu, kafin ta buɗe baki da ƙyar ta kira shi. “Musa! Musa! Musa... Yallaɓai wancan shi ne ƙanin nawa, shi ne ƙanina Yallaɓai!” Ta faɗi tana nuna masa ƙofar cell ɗin, a tare 'yan sandan biyu suka kalli inda take nunawa, kafin suka juyo suka kalli juna, yanzu suka fahimci inda zancen ya dosa, a jiya aka kawo musu ƙarar wani ɓarawo da ya shiga gidan wani me kuɗi ya yi sata. Kuma ta hanyar bayanan da masu kayan suka basu ne suka kamo me lefin, ama kuma me lefin sai ya basu kuɗaɗe, ya ce dasu su bar shi ya tafi. Kuma sun sake shi ya tafi ɗin. Sanin cewa su masu kayan ba shiru za su yi ba, ya sa su aikata kalar abun da suka saba, wato kamo waɗan da basu ji ba basu gani ba su jefasu a cin lefin. Kuma ko da suka je Makoko Ekene Musa suka kamo, duk kalar dukan da suka masa a jiya kan ya amsa lefin, ya ƙi, ama kuma duk da haka ba su saduda wurin dukan nasa ba. “Kai ku fice ku bar nan!” Baƙin ya faɗi yana miƙewa. Ran Diya ya soma ɓaci. “A kan me za mu fice? Bayan ga ƙanina na ga kun kama, kuma sai ku ce mu fice?” Haka baƙin ya shiga musu korar kare, yayin da ƙyamurmurin ya bada himma wurin ƙarewa Diya kallo. Ba dan su Diya sun so ba haka Fa'ee ta jata suka fita, sai tafiyar ta gagari Diya, hakan ya sa ta zube gwiwoyinta a ƙasa tana risgar kuka, Fa'ee ta dafata tana faɗin. “Dan Allah Shola ki tashi mu tafi, kin san halin 'yan sandan nan ba mutunci ne da su ba” “Me ya sa zan tafi na bar Ekene a nan? Ki na ganin irin dukan da suka masa fa? Idan na tafi wata ƙila su kasheshi! Wallahi babu inda zan matsa daga nan, sai da ɗan uwana!” Fa'ee ta goge ƙwallar tausayin ƙawarta, ta tsugunna ta ci gaba da bata haƙuri. “Na ce ba?” Suka ji muryar ɗan sandan nan a bayansu, hakan ya sa suka juya a tare, ƙyamurmurin nan ne ya ke tsaye a kusa da su yana musu wani irin murmushi. Da sauri Diya ta miƙe tana kallonsa, dan a ganinta, temakonta zai yi. “Ki dena kuka, zan iya temaka miki” Da sauri ta share ƙwallar idonta tana haɗiye yawu. “Za ka iya fito min da shi ne?” Ta tambaya idonta na hasko mata fuskar Ekene ɗauke da raunika. Ɗan sandan ya gyaɗa mata kai yana mata wani irin kallo, tuni Fa'ee ta ɗago jirginsa, banda Diya da hankalinta ya bar gangar jikinta. “Yanzu ma kuwa, amma da sharaɗi!” Ta kuma share wata ƙwallar tana gyaɗa kai. “Menene sharaɗin? Faɗa mij in ji?” Sai da ya haɗiyi miyau, ya juya ya kalli Fa'ee dake masa wani kallo me kama da harara, amma da yake bashi da kunya sai ya yi kamar bai gane ba. Ya dawo da jajayen idonsa kan Diya. “Akwai ɗakina dake bayan layin can, za ki bini muje... Ai kin dai... gane ko?” Ya ƙarashe yana taɓa botirin gaban rigarsa. Diya ta gyaɗa kanta. “Ni kuwa na gane...” Ba ta ƙarashe ba ta ɗauke shi da mari. Ba ɗan sandan kaɗai ba, har da Fa'ee sai da ta tsorata, kuma marin da ta masa ne ya jawo hankalin mutanen dake harabar wurin. Diya bata saduda ba ta nuna shi da yatsa. “Kai a ganinka ni zan iya yarda da ƙazamar buƙatarka? Kun kama ɗan uwana ba bisa laifin komai ba, kuma yanzu ka zo kana buƙatar mutuncina?, Na gwammaci na je na tsaya a kan titi mota ta take ni, da dai na baka mutuncina!...” Haka ta ci gaba da masa wankin babban bargo, har jama'a suka fara taruwa suna tambayart abun da ya faru, shi kuma ɗan sandan ya kasa furta komai. *** A hankali wata farar mota ƙirar Audi Q6 ta yi parking a harabar ofishin 'yan sanda dake Makoko. Cikin abun da bai fi sakan huɗu ba, ƙofar motar daga ɓangaren direba ta buɗe, wani farin kyakkyawan matashin bafulatani ya fito, sanye cikin kayan 'yan sanda. Hannunsa riƙe da wayarsa da kuma hular kayan nasa na 'yan sanda, idonsa manne da baƙin glashi, wanda ya ƙara fito da farin fatarsa. Tun daga jikin motar tasa ya hangi mutane na taruwa a kusa da ofishin 'yan sandan. Ya ɗan yamutsa fuska cikin mamaki, to me yake faruwa?, me zai haɗa ofishin 'yan sanda da hayaniyar faɗa?, Dan bisa ga dukkan alamu faɗa ake a wurin. Hular kayan nasa ya sanya a kansa, sannan ya saka wayarsa a aljihun wandonsa, cikin takunsa na nutsuwa ya soma tafiya yana nufar inda mutanen ke taruwa, duk kuwa da ba shi da niyyar zuwa wurin, dan shi ba a nan ofishinsa yake ba. Kuma ba wai aiki ya kawoshi ofishin ba, saboda tun ƙarfe biyar na yamma ya tashi daga aiki, mantuwa ya yi, shi ya sa ya dawo domin ya ɗauka. “Constable! Me yake faruwa ne?” Saliha, kuma kamillalliyar muryarsa ta faɗi a sanda ƙafafuwansa suka tsaya daf da inda faɗan ke faruwa. Cikin hanzari Constable ya juyo, jin muryar chief inspector SAM. Shi ɗin ne kuwa tsaye a gabansu, nan take cikinsa ya yamutsa cike da tsoro, gumi ya shiga tsatsaffo masa, cikin daburcewa, ya ɗaga hannunsa na dama ya sara masa yana faɗin. “Sir! Sir... Sir wannan yarinyar ce... Ta zo nan take neman tada mana hankali!” A take ya shararo ƙaryar, idonsa na haskawa da matsanancin tsoron dake tasowa tun daga zuciyarsa, dan idan har Chief inspector SAM ya ji abun da suke aikatawa, tasa ta ƙare, dan SAM ba ya ɗaya daga cikin gurɓattattun 'yan sanda, akwai shi da tsayawa gaskiya duk rintsi. Sai a lokacin idonsa ya sauƙa a kan yarinyar dake faɗa da Constable ɗin, nan take zuciyarsa ta buga da ƙarfi, jin wani abu me kama da tsinin mashi ya cakeshi a tsakiyar zuciyarsa, da za'a ɗora masa wuƙa a wuya a dai-dai wannan lokacin, a tambayeshi ya faɗi abun da yake ji a lokacin ba zai iya ba, dan shi kansa bai san sunan wannan abun ba, wani yanayi ne da tun da yake bai taɓa shiga ba. Kuma daga wannan lokacin ne, wani babi na rayuwarsa ya buɗe, dan wannan yanayin da ya tsinci kansa a ciki shi ne zai yi wani tasiri a cikin rayuwar tasa. Ya iuma zama dalilin haɗuwarsa da HASKEn sa. Diya ta yi murmushin takaici, dan Constable ɗin cikin harshen hausa ya yi maganar, a zatonsa ba sa jin hausa, dan tun da suka zo da yarbanci suke magana. Kuma lokaci guda ta kalli ɗan sandan dake tsaye a gabansu. “Ƙarya yake yallaɓai!" Ta faɗi idonta na cika da ƙwalla, chief inspector Sam ya kalleta da kyau, dan sai a sanda ta yi maganar ta dawo da shi zahiri. “Menene ainahin abun da ya faru?” Ya tambaya. Tun daga A har Z sai da Diya ta feɗe masa biri har wutsiya, kuma ta sanar da shi kalar zaluncin da 'yan sanda irin Constable ɗin ke yi a yankinsu. Cike da mamaki da ruɗani ya kalli Constable ɗin, dan wannan ɗin abu ne da bai taɓa cin karo da makamancinsa ba. “Constable Adebayo! Me nake ji haka?” Ya tambaya idonsa na shirin sauya kala, dan tun bayan fara aikinsa a hukumar 'yan sanda, bai taɓa cin karo da makamancin wannan zaluncin ba. Adebayo ya shiga sosa ƙeyarsa cikin tashin hankali, dan shi kam ta sa ta ƙare. Jin shirun Constable Adebayo ya yi yawa ya sa SAM fahimtar cewa gaskiya matashiyar ta faɗa. Saboda haka ya kalleta, kuma sai a lokacin ya lura da cewar su biyu ne, akwai wata ma tare da ita. “Ku shigo ciki Please” Ya faɗi yana nuna musu hanya. Diya ta share ƙwallar idonta tana haɗe hannyenta alamun roƙo. “Yallaɓai ni bani da abun da zan iya baku dan ku sakar min ɗan uwana, ba ni da komai, kuma bani da kowa, dan haka idan kai ma ba za ka iya temakonmu ba za mu kai ƙaranmu zuwa ga mahallicin samai da ƙasai, dan na san cewar babu wanda ya gagareshi” SAM ya girgiza kansa. “A'a, ni ba komai nake buƙata a wurinki ba, ku shigo ciki, akwai tambayoyin da nake so na muku” Sai da Diya ta kalli Fa'ee, sannan ta dube shi, bayan Fa'een ta mata alama da su amince. Cikin ofishin suka koma, sannan SAM ya bi bayansu, a tsorace Adebayo ma ya shiga ya tsaya daga gefe yana kallon yanda asirinsu ke tonuwa. Sai bayan da SAM ya yi wa su Diya tambayoyi ya fuskanci cewar gaskiya suke faɗa. Cikin wani irin tashin hankali da ɓacin rai, ya bawa su Adebayo umarni da a saki Ekene. Jiki na ɓari suka fito da shi. Diya kuwa kasa daurewa ta yi da ganin ɗan uwanta, sai da ta ruga zuwa wajen ɗan uwan nata, ta rungumeshi tana kuka, ko tsayuwa me kyau ba ya iyawa, duka jikinsa shatin duka ne. Diya ta juya ta kalli SAM. “Mun gode Yallaɓai! Allah ya saka maka da alkairi” Kansa kawai ya jinjina musu, kuma suma daga haka ba su sake cewa komai ba, ita da Fa'ee suka kama Ekene suka fita da shi. Wani irin kallo SAM ya wurgawa Adebayo da Chibunna, sannan yace. “Gobe da misalin ƙarfe takwas na safiya, ina so na ganku a ofishina!” “Sir!” Suka faɗi a tare suna sara masa, kuma har sai da ya fice daga wurin suka sauke hannuwansu. “Tamu ta ƙare Chibunna” Cewar Adebayo yana sharce gumi. “Ai duk kai ne ka ja mana, akan dubu ɗari ga shi za mu rasa aikinmu, dan ina da tabbacin chief SAM ba zai barmu ba!” Adebayo ya cire hular kansa yana firfita da ita. A idonsa yake hango tarin abubuwan da za su rushe a rayuwarsa idan aka sallame shi a aiki, saboda ya sani, babu ta yanda za'a yi su ci gaba da aiki bayan wannan lefin da suka aikata. Kallo ɗaya za ka yiwa SAM ka tabbatar da ransa a ɓace yake, yanayin takunsa ma kaɗai zai tabbatar maka da hakan, duk da shi ba mutum ne me kwarafniya ba, komai nasa a nutse yake yinsa. Gaba ɗaya ji yake kansa na sara masa, duniyar na juye masa, ba ya san jalunci, ba ya so ya ga ana zalunci sam. Cikin wannan ɓacin ran ya nufi ofishinsa, ya ɗauko abun da ya zo dominsa, sannan ya dawo ya shiga motarsa ya bar station ɗin. Su Diya na fita suka kama hanyar komawa Makoko, dan a lokacin magariba ta kawo kai. Ga shi Ekene ba ya iya yafiya da kyau, dan gaba ɗaya jikinsa ya yi tsami, kuma daga ita har Fa'ee babu wanda ya fito da ko asi, bare su hau abun hawa. Kamar daga sama suka ji horn ɗin mota, hakan ya sa su juyawa a tare. Duk da duhun magariba da ya kawo kai sun ganeshi, wannan ɗan sandan da ya temakesu ne a cikin motar, kuma ganin hakan ya sa suka dakata. Shi ne ya fito daga motar yana nufar inda suke. “Idan ba damuwa zan iya sauƙeku a gida?” Diya da Fa'ee suka dubi juna. Wannan wani irin mutum ne me kirki haka?, bayan temakonsu da ya yi so yake ya sake temaka musu. “Dan Allah?” Ya faɗi a sigar magiya, da sauri suka dubeshi a tare, su da za'a temakawa akewa magiya?. Lalle wannan mutum akwai kirki. Ba musu suka amince, shi ne ya riƙe Ekene har suka saka shi a mota. Fa'ee ta shiga gidan baya tare da Ekene, yayin da Diya ta zauna a gidan gaba. Haka ya fara jan motar har zuwa Makoko. Kuma ko da suka isa shi ya fitar musu da Ekene, kafin sauran abokansa dake wurin suka gansu suka taso suka riƙeshi, Fa'ee ta bi bayansu, yayin da Diya ta tsaya dan ta yiwa ɗan sandan godiya. “Mun gode sosai da sosai, babu abun da zamu iya biyanka wannan abun da kamana da shi Yallaɓai!” SAM ya girgiza kansa yana kallon cikin idanuwan Diya. “Ban muku komai ba, kawai na yi abun da yake wajibi a gareni ne, sannan ki dena kirana da Yallaɓai, sunana SURAJ ALI MUKTAR!” Diya ta gyaɗa kanta tana karanta abun da ke rubuce a jikin name tag ɗin rigar jikinsa ‘SURAJ A. MUKTAR’ “To Yallaɓai SURAJ, Sai an jima” Ta faɗi tana juyawa, SAM ya kasa amsawa, sai bin bayanta da ya yi da kallo har ta shiga cikin wani kwale-kwale. *Agha Mansion, Lekki phase 1, Lagos state, Nigeria.* DEENA TAYYAB AGHA POV. Tana fitowa daga bathroom ta ga mahaifiyarta Hajiya Zayya zaune a kan gadonta tana ƙare mata kallo. Kanta ta ɗauke tana nufar dressing mirror. “Wanka kika yi?” Hajiya Zayya ta tambaya ganinta ɗaure da towel, Deena ta ɗan dakata daga zaman da take shirin yi a kan stool, ta juyo ta kalleta. “A tunaninki zan iya zama da wannan kayan da waccan shashashar ta zubamin yoghurt?. Ko kuma zan iya bacci ba tare da na yi wanka ba bayan da Saifuddin Mas'ud Agha ya riƙe min hannu?” Ta ƙarashe tana zama a kan stool ɗin. Hjia Zayya ta girgiza kanta. “Na san ba za ki iya ba...” Deena ta gyaɗa kanta tana jan kwalbar man da ta saba shafawa na gyaran jiki, dan ita duk wannan wayer tata, bata yarda da wani abu ba wai shi bleaching, duk kuwa da yanda Mommy ke ta nuna mata cewar ta yi bleaching ɗin, saboda fatarta ta zama kamar ta sauran 'yan Agha Mansion. Saboda kaf yaran gidan babu baƙi sai Taj, kuma shi ma ɗin ba baƙi ba ne, chocolate color ne. Sannan duka gidan ita ta fi kowa baƙi, amma hakan bai dameta ba, a ganinta zaman fatarta a baƙar shi ne burgewa. Hjia Zayyata miƙe daga kan gadon, ta isa zuwa bayan 'yarta, sannan ta dafa kafaɗarta. “Zuwa yanzu ya kamata ace kun yi aure ke da Tauqeer!” Deena ta kalleta ta cikin mirror. “A gaskiya Mommy bani da shirin yin aure a yanzu, bunƙasa carrer ta shi ne abun da ke gabana, idan baki manta ba na faɗa miki cewar a watan da za mu shiga za mu fara shooting sabon film ɗin nan... So ba na jin zan iya aure a nan kusa!” Hjia Zayya ta ja guntun tsaki. “Wai ke me ya sa a duk sanda zan ce miki yi gabar sai ki bauɗe zuwa yamma?...” “Saboda haka nake son yi Mommy. Ni da kika ganni nan ban damu da ra'ayin wani ba, rayuwata nake a yanda nake so, kuma babu wanda ya isa ya hanani yin abun da nake son yi” Ta faɗi tana kallon Hajia Zayya. Hajia Zayya ta ɗaga kanta sama, magana irin wannan ba baƙuwa ba ce tskaninta da 'yar tata, sun saba irin haka. Ta sauƙe kanta tana faɗin. “Ya yi kyau, za ki gane cewa wannan hanyar da kika ɗauka ba me ɓullewa ba ce, a ranar da Tauqeer ya fara soyayya da wata ba ke ba!” Ta faɗi a ƙokarinta na tunzura Deenan, ba wai dan za ta bar hakan ta faru ba, tun da dai har Deena ta furta cewar tana son Tauqeer to fa sai ta aureshi, dan ba ta ji ko ganin wani abu da zai iya dakatar da faruwar hakan. A tunanita kenan, dan kuwa da ace ta san kalar ƙadarar dake tafe nan gaba, da bata yi Irin wannan tunanin ba. Saboda ƙaddarar da za ta kawo HASKE cikin Agha Mansion na nan tafe, ƙaddarar da za ta tarwatsa wannan alwashin nata har guntunsa. Cak Deena ta dakata da shafa man da take, cikin abun da bai gaza sakan biyu ba, fuskarta ta sauya zuwa fushi. “Tauqeer nawa ne Mommy, ba zan taɓa barin wata ta same shi ba, kin fahimta?” “To tun da haka ne sai ki bi hanyar da zaki mallakeshi, ku yi aure, ta hakan ne kaɗai zai dawamma a matsayin naki ke kaɗai!” “Auran Tauqeer da zan yi shi ne zai sa ya zama nawa na har abada?” Hajia Zayya ta gyaɗa mata kai. “Zan aureshi very soon” Hajiya Zayya ta yi murmushi, kafin ta shafa kan 'yarta. Kuma kafin ta sake cewa wani abu Deena tace. “Ki bani wuri zan kwanta” Hajiya Zayya ta ɗan yi murmushin yaƙe, kafin ta saketa tana faɗin. “Ki yi bacci me daɗi” Daga haka kuma ta juya, ranta na mata ba daɗi, a da bata damu da kalar renin da Deena ta mata ba, hasali ma ganinsa take ba a bakin komai ba, amma zuwa yanzu ta fara shiga damuwa a kan hakan, dan idan Deena za ta mata magana, yi take kamar wadda take yi da sa'arta. Deena ta ci gaba da shafa manta, kafin ta miƙe ta shiga closet, ta fito sanye cikin farar night gown, ta kwanta a kan gadonta ba tare da ta kashe wutar ɗakin ba, tunani Tauqeer shi ne kaɗai abun da zuciyarta ke yi, eh ƙwarai ta san da cewa tana sansa, kuma ba ta jin za ta iya barwa wata ahi, dan Tauqeer nata ne ita kaɗai. Cak Hajiya Zayya ta tsaya a ƙofar ɗakin Iqra dake kusa da na Deena, jin kamar tana dariya. Cikin sanɗa ta matsa zuwa jikin ƙofar ɗakin, ta kara kunnenta tana sauraron abun da Iqra ke faɗi. Daga cikin ɗakin kuma, Iqra ce kwance a kan gadonta tana waya da sabon saurayin da ta sake, wanda take ga kamar shi ba zai gujeta ba irin sauran samarin da ta sha yi a baya. Daga saurayi ya nuna yana santa, ta amince suka fara soyayya za ta nemi shi ta rasa. Tun abun ba ya damunta har ta zo ta fara damuwa, amma cikin ikon Allah sai shi wannan Jawad ɗin ya tsaya, kuma a yanda yake nuna mata soyyayarsa a makaranta tana jin kamar shi ba zai kufce ba kamar sauran. “Dare na yi Babe, zan kwanta” Ta faɗi idonta manne a kan agogon ɗakin, daga cikin wayar, muryar Jawad ta ce. “Ok Queen, ki kwanta sai gobe, ai za ki shigo school ba?” Ta ɗan yi dariya. “Insha-Allah!” “Okay I love you!” “I love you more!” Daga haka wayar ta ƙare. Ta ƙanƙame pillow tana murmushi. Hajiya Zayya ta yi murmushi kamar yadda ta saba. A ranta take faɗin; wato ta yi sabon saurayi kenan?. To ayi mu gani, idan tusa za ta hura wuta. Daga haka ta nufi ɓangaren da ɗakinsu ita da mijinta yake a cikin gidan. * Kamar Kullum, Tayyab Agha na tsaye a balcony ɗin cikin ɗakinsa, wayarsa riƙe a hannunsa yana kallon hotonta. RAHILA matarsa da yake matuƙar so da ƙauna, matarsa da rana tsaka ya nemeta ya rasa. Har zuwa yau ciwon rasata bai bar ransa ba, don ɓata ta yi ba tare da ya san inda take ba, da ace ma mutuwa ta yi, ya ga gawarta to da zai haƙura, amma har zuwa gobe bai cire ran sake ganinta ba. “Har gobe ina sanki matata, kuma ba na jin zan dena sanki har zuwa fitar nunfashina na ƙarshe... Ko a ina kike? Shin kin haifi cikin jikinki ko a'a?...” Kamar wanda ya zautu, haka ya ci gaba da yin sambatunsa da baya ƙarewa. Kafin ya fita daga wurin hotuna, ya shiga wurin kira, ya shiga neman lambar yayar Rahila matarsa, wato Anti Badi'a. Ko da ya samo lambar sai ya shiga aika mata da kira, amma kamar kullum, haka ya yi ta gwadawa amma ta ƙi ta ɗauka. “Tayyab!...” Ya ji muryar Zayya ta kira sunan, nan take gabansa ya faɗi, ya ji kamar ana dauɗe ƙwaƙwalwarsa daga tunanin Rahila. A hankali ya juyo ya kalleta, tana tsaye daga cikin ɗakin tana kallonaa, fur ya ƙi yarda su haɗa ido, dan ba ya so ta gane cewa ya ga hotunan Rahila, balle ta gane cewar ya kira Anti Badi'a. “Me kake a nan?” Ta tambaya kamar uwa da ɗanta. “Na... Na... Zan... Zan..” Ya kama inda-inda. “Lokaci na ƙurewa, ka zo ka kwanta!” Ta faɗi jajayen idanuwanta a kansa. Kamar wanda ake controling da remote haka ya dawo zuwa cikin ɗakin da sauri, ya nemi bakin gado ya kwanta ya lumshe idonsa. Hajiya Zayya ta ɗau muntuna a tsaye a wurin, har sai da ta tabbatar da ya yi bacci, kafin ta juya zuwa ga lokarta, ta buɗe ta ɗauko wata doguwar jar riga. Ta tuɓe kayan jikinta sannan ta saka rigar. Ta dawo ƙarƙashin gadonta, ta sa hannu ta janyo wata ƙwarya dake lulluɓe da baƙin ƙyalle. Miƙewa tsaye ta yi, ta buɗe ƙwaryar, wani baƙin ruwa ya bayyana a cikin ƙwaryar. Idonta ta lumshe tana karanto wasu abubuwa da ba zaka iya tantance da wani yaren take magana ba. Bayan ɗan wani lokaci ta buɗe idonta. A hankali-hankali hayaƙi ya turnuƙe ɗakin. Kuma a cikin hayaƙin Hajia Zayya ta ɓace ɓat. Kamar almara. *** Durƙushe take a gaban wani yamushasshen tsoho dake zaune a kan wata baƙar kujera. Fuskarsa baƙin ƙirin, ga wani farin gashi da ya baibaye jikinsa, sanye yake da wasu tufafi na ganye irin na mutan da. Hannunsa na dama rike da tsabga yana kaɗawa. “Yau da wace buƙata kika zo GAMANDI!” Zayya ta ƙara risinawa kamar me shirin yin sujjada tana faɗin. “Ƙunduns abun dogaro, girma naka Ƙundus, babu me bamu bayan kai, a gurinka kaɗai muke nema mu samu, yau ma na zo da tarin buƙatu, kuma ina fatan za'a biya minsu” Tsohon ya yi wata dariya mara daɗin sauraro. “An baki dama Gamandi, faɗi abun da ke tafe da ke” “Ina so a shiga tsakanin Gudaliya da SAIFUDDIN, idan da hali a kawar da shi Ƙundus. Sannan Iqra ta yi sabon saurayi, ina so a rabata da shi kamar yanda aka rabata da sauran. Sai maganar Tayyab, har yanzu bai mance da Rahila ba. Akwai kuma batun Jamal, ina so a ƙara hargitsa rayuwarsa fiye da da ya me girma Ƙundus!” Ta ƙarashe tana kifa kanta a ƙasa. Tsohon ya ɗan yi shiru, kafin yace. “Gamandi wata ƙila kin mance lokacin da na ce miki 'yayan Hafiza ba za su taɓu ba, dan a tsaye take a kan 'ya'yanta, saboda haka Saifuddin ba zai iya taɓuwa ba. Ita ma Maryam ɗin dan ba ta tsaya a kan yaran nata ba ne shi ya sa ake iya taɓasu. Game da Iqra kuwa wannan me sauƙi ne, ki ɗauka an gama miki da wannan buƙatar kamar sauran, batun Tayyab ma ba me wahala ba ne, zan masa abun da zai sa ya ji kamar zai ruga da gudu ko da sunan Rahila aka kira. Haka Jamal ma baki da damuwa” “Godiya nake Ƙundus” Tsoho Ƙundus ya gyara zamansa yana faɗa mata kalaman da ta jima da haddace su a cikin kanta, saboda a duk sanda za ta zo masa da buƙata sai ya faɗa nata su, kuma har wa yau ita ta rasa takamemen ma'anarau. “Amma fa Gamandi ki sani cewa akwai ranar ƙin dillanci, akwai ranar da duk abun da aka binne a ƙasa zai fito, akwai ranar girbi. Sannan akwai ranar karɓar sakamako!” ______________ _To ka ji, Salmanians, an ya kuwa kuna ganin duhun dake mamaye da Agha Mansion?_ _Waye wannan Suraj a.k.a SAM ɗin, dan da alama akwai wani abu gagarumi dake shirin faruwa tsakaninsa da Diya da kuma Fa'ee._ _ Kuma wani hali Jamal ke ciki?_ _To mu je de zuwa, dan ba ayi komai ba ma_ A. ISAH CE ✍️. °°°°°°°°°°°°°°°° *💡HASKE...💡* *©SALMA AHMAD ISAH* TAURARI WRITER'S ASSOCIATION. *Page 06* ~~~ *No.675, 361 Stagg Street, Brooklyn, New York, USA.* RAFEEQ AHMAD MUHAMMAD POV. A hankali ƙafafuwansa ke takowa zuwa down stairs. Sanye yake cikin baƙar suit, wadda a ƙasanta ya saka farar high neck shirt. Ƙafafunsa sanye cikin fararen sneakers. Bayansa goye da backpack, wadda ke ɗauke da laptop ɗinsa. Da murmushinsa ya ƙarasa zuwa wurin Maa dake tsaye a falon. Ta baya ya rungumo kafaɗunta. “Sakeni mana! Sai ka karya ni?” Maan ta faɗi tana juyowa, ta dubeshi. “Zan tafi wurin aiki Maa, ki sakamin albarka” Ya faɗi yana kama hannayenta, Murmushi ta yi tana ƙara dubansa. Yau ya samu ya ɗan rage tsayin gemun da ya tara, amma bai aske shi duka ba, duk kuwa da ta san cewa shi ba ya tara gemu da yawa, a wasu lokutan ma askeshi yake gaba ɗaya. “Allah ya maka albarka, ya bada sa'a!” “Ameen Maa” Ya amsa yana sumbatar hannyenta. Kafin ya saketa yana ɗaukar doguwar trench coat ɗinsa, kasancewar ana cikin yanayin sanyi ne, dan a wasu wuraren ma snow ce ke sauƙa, ya sakata, sannan ya fita. Kekensa dake jingine a jiki balcony ya ɗauka. Ya juya kansa yana nufar ɗan gajeren gate ɗin gidan. Kuma tun kafin ya fito daga gidansu ya hangeta ta fito daga nata gidan. Saboda katangun dake gaban gidan basu da tsayi. Kamar kullum, sai da zyciyarsa ta doka sau biyu a lokaci guda. Kuma ko da ya ɗago da hannunsa na hagu dan ya tabbatar da ƙaruwar bugun ziciyar tasa sai ya ga ya ƙarun, har da kashi 7. Setin zuciyarsa ya dafe a ransa yana faɗin; Da alama yarinyar nan kasheni take son yi. Ita kuma sai a lokacin ta lura da shi, duk da ya ɗan sauya mata yau, kasancewar ya rage gemun da ya saba tarawa. Baki washe ta ɗaga masa hannu. Hakan ya sa keken dake hannun Rafeeq ƙoƙarin suɓucewa, ya yi sauri ya ruƙoshi yana mata murmushin yaƙe. Kafin ya turo keken zuwa jikin gate, ya buɗe gate ɗin, sannan ya fita, sai da ya kafe keken a gefe, ya dawo ya rufe gate ɗin. Kuma har zuwa lokacin tana tsaye a ƙofar gidanta, da titi ne kaɗai ya rabashi da nasa gidan. Keken nasa ya fara turawa yana tafiya, duk da jikinsa na bashi cewar har yanzu kallonsa take. Kuma sai ya ƙara tabbatar da hakan a sanda ya ji muryarta a kusa da shi. “Hey BLACK INDIAN!” Abun da ta faɗi kenan, wanda ya haddasawa zuciyar Rafeeq tarwatsewa a ƙirjinsa, ya dakata da tura keken da yake ya juyo ya kalleta. Ita wai nan kallon ba'indiye take masa?. “Ni Nigerian ne, ba indian ba” Ya faɗi cikin harshen hausa, ido waje take kallonsa, dan a zatonta shi ɗin ɗan indiya ne, ba wai dan ya na da farin fata ba, sai dan yana yanayinsu, kuma ko da bai kasance ba'indiye ba, zai iya kasancewa ɗan Asia. “Wai kai ɗan ƙasarmu ne?” Ta tambaya idonta na haskawa da zallar mamaki. Kansa ya gyaɗa nata yana ƙarewa kyakkyawar fuskarta kallo, dan shi a kallon farko da ya mata ya gane cewa 'yar nigeria ce. “Amma kai shuwa arab ne ba?” Ya girgiza mata kai yana gyara riƙon keken hannunsa. “Ni bafulatani ne” Mamaki ya ƙara kamata. Ita fa Wallahi ba ta taɓa danganta shi da Nigeria ba ma, balle har a ce mata bafulatani ne. Keken hannunsa ta kalla tana faɗin. “Keken waye wannan?” Rafeeq ya kalli keken, sannan ya kalleta. “Nawa ne” Ya bata amsa, nan take kaso tamanin na burgeta da yake ya ragu, wai da ma duk wannan haɗuwar tasa keke yake hawa?. Tun bayan data hasasowa kanta alaƙa da shi, ta ke ta dudduba cikin gidansa, wai ko za ta ganshi da mota, amma bata taɓa gani ba, ƙarewarta ma wai keke gareshi. Tun da kuwa keke yake hawa hakan na nuna cewa ba shi da ƙumbar susa. A ganinta, duk saurayin da bashi da kuɗi, duk haɗuwarsa sunansa sifili. A duniyarta, kuɗi shi ne komai, in baka da su, baka da ƙima a idonta. Da har ta fara hasasowa irin kuɗin da za ta tatsa a wurin wannan ba'indiyen, ashe duk kanwar ja ce, shi ma dai ɗan Nigeria ne, wata ƙila ma talauci ne ya koroshi daga gida. Kuma de ta na ganin cewar gidan da yake ciki ba nasa ba ne, haya yake kamar dai ita. “Helloo!” Ya faɗi yana ƙyasta yatsunsa, a ƙoƙarinsa na dawo da ita hayyacinta, dan ya lura da ta lula zuwa duniyar tunani. Ta yi firgigit ta kalleshi. “Mu je?” Ya faɗi yana nuna mata hanya, a ƙasan numfashinta ta ja tsaki, dan kuwa dai ɓaro-ɓaro take hango rushewar shirinta a kansa. Ta soma tafiya gefensa. “Sunana Rafeeq! Ke fa?” Ciki-ciki ta amsa masa da. “NADRA!” Kansa ya gyaɗa yana haddar sunan a cikin kansa. “Aiki ne ya kawoki nan?” Ta juya ƙwallon idonta cike da ƙosawa. “Eh” “A ina kike aiki?” Sai da ta ɗan kalleshi, sannan ta furta. “Kamfanin ƙera kayan sawa na OP” Ta shararo ƙaryar ba tare da ta ji komai a ranta ba. Dan a zahiri ne take aiki a can ɗin, amma a baɗini ba a can take aiki ba, hasali ma ba wannan aikin ba ne ya kawota USA. “Ni kuma a GroTech AI center nake aiki!” Ji ƙarya! In ba ƙarya ba yana aiki a GroTech ɗin zai zauna ba shi da mota?. A yanda ta san babbar ma'aikatar, babu ta yadda za ayi ma'aikacinsu ya zauna ba shi da mota, dan ba ƙaramin kuɗaɗe ake samu ba. Wata ƙila ma shara yake musu, maƙaryacin banza!. Ta ƙarashe zancen zucin nata tana hararsa a fakaice. Rafeeq ya tsaya a sanda suka iso kwanar da zai yi wadda za ta sada shi da inda ya nufa. “Ni zan yi nan” Ya faɗi yana duban yanayin fuskarta da ta sauya cikin ɗan ƙanƙanin lokaci, ba ya ce ga dalili ba, amma tun bayan da suka yi zancen keke ta sauya. Kallonsa ta ɗan yi sannan ta kalli hanyar da take da niyyar bi. “Ni kuma zan yi nan!” Naman goshinsa ya tattare alamun kokwanto. “Ai nan ce hanyar da za ta sada ki da kamfanin OP” Ya faɗi yana nuna mata hanyar, kasancewar wurin mararraba ne, hanyace da ta kasu kashi huɗu. “Akwai ƙawata da zan biyawa, shi ya sa zan bi ta nan” Ta faɗi tana mamakin yadda ya san kan garin New York. Kansa ya jinjina. Kafin ya laluba aljihunsa, ya ɗauko wallet ɗinsa, yana duba mata kuɗin da zai bata dan ta yi kuɗin taxi, bus ko jirgin ƙasa idan ta so. Nadra ta shiga leƙa cikin wallet din nasa a fakaice tana mamakin yawan kuɗin dake ciki, ka da fa ta yi sake reshe kama ganye, ko da bashi da mota ai yana samun kuɗaɗe, za ta yi manage a haka, ko ba komai ta samu wani ATM machine ɗin. “Ki yi kuɗin abun hawa” Ya faɗi yana miƙa mata kuɗin, ko kunya babu Nadra ta miƙa hannunta ta karɓa tana ayyana yawan kuɗin. “Na gode” Ta faɗi tana ƙarawa gaba. Tsayawa ya yi a wurin duk da ya san cewa ana jiransa a wurin aiki. Amma ba ya son ya tafi ba tare da ya ga tafiyarta ba. Traffic ne ya dakatar da ita daga tsallaka titin da take san isa. Hakan ya sa ta tsaya a gefen titin ita da waau fararen yara guda biyu, suna jiran A basu hannu kafin su tsallaka. Rafeeq na ganin haka ya samu wata kujera dake gefen hanya ya zauna yana sauƙe jakar bayansa. Duk da yau ana sanyi fiye da kullum, haka ya zauna yana daddana laptop ɗinsa a wurin. Kafin ya rufeta yana mayar da ita cikin jaka. Ba zato ba tsammani Nadra ta ga an basu damar tsallaka titin ba tare da lokacin tslallakawar tasu ya yi ba, ba ita kaɗai abun ya bawa mamaki ba, har da masu abeben hawan dake tafiya a kan titin. Haka Nadra da yaran suka tsallaka titin suna ta mamaki a ransu. Sai da Rafeeq yaga tsallakawarsu, sannan ya yi murmushi yana hayewa kekensa. Ya nufi inda yake son zuwa. “Wai a ina ka tsaya ana ta jiranka?” Abdulrahman ya tambayeshi a sanda ya iso ma'aikatar. “Wani uzuri ne ya ɗan riƙeni a hanya...” Ya amsashi yana shiga kyakkywan office ɗinsa dake hawa na shida. Abdulrahman ya biyo bayansa yana faɗin. “Ina Maa?” Rafeeq na cire trenchcoat ɗin jikinsa ya bashi amsa da. “Lafiyarta ƙalau” Abdulrahman ya gyaɗa kansa yana ci gaba da kallon abokinsa. Rafeeq ya nufi jikin mirror yana gyara sumar kansa. “Kowa ya hallara a meeting room ɗin?” “Eh, kowa ya iso, kai kawai ake jira” Ya kuma gyaɗa kansa yana raɓa Abdulrahman ɗin, hannunsa riƙe da wannan laptop ɗin tasa ta amana, dan duk tarin computers ɗin da yake da su, ba su da anfani kamar wannan me ɗauke da zanen suna nasa a bayan screen ɗin. Meeting room ɗin suka nufa a tare yana faɗawa Abdulrahman. “Ina buƙatar hot chocolate, yanzu!” Abdulrahman ya gyaɗa kansa, dan ga duk wanda ya san Ram, ba shi da abun sha da ya wuce Hot chocolate. Babu ruwansa da coffee ko tea, shi dai a bashi hot chocolate. Kuma a take a wurin Abdulrahman ya kira waya ya ce a haɗawa Ram hot chocolate, sannan kada a sa masa gishiri a ciki kamar yanda aka saba haɗa masa, saboda ciwon zuciyar da yake ɗauke dashi, dai-dai lokacin da suka iso ƙofar meeting room ɗin. Ram ɗin ne a kan gaba, ya shiga yana bada haƙuri game da makarar da ya yi. Sannan ya samu wuri ya tsaya daga jikin farin board ɗin dake cikin meeting room ɗin. Bayan ya danƙawa Abdulrahman laptop ɗinsa. Wani switch Abdulrahman ɗin ya danna a jikin taga, nan take curtains ɗin dake sama suka sauƙo zuwa ƙasa, suka rufe ko wace katangar glass dake ɗakin, ya rage sai hasken projector dake haska farin board ɗin tare da Ram dake tsaye a gefensa. “Good morning everyone! I'd like to introduce you to my self-driving car device. It uses sensors, cameras, and artificial intelligence to navigate roads and avoid obstacles. It's still in development, but it has the potential to make our roads safer and our lives easier...” Haka ya ci gaba da kwararo bayanai a kan device ɗin da ya ƙera da hannunsa, dan hatta da matarsa tana amfani da device ɗin. Yana bayanin yana nuna musu hotunan dake playing a jikin bord. Yayin da masu kamfanin motar da Sir Thomas suka nutsu suna sauraronsa. “How does the car know when to stop at a stop sign?” Ɗaya daga cikin masu kamfanin motar ya wullo masa tambayar. Ram ya sosa tattoo ɗin wuyansa yana murmushi. Wani abu da ya kasance ɗabi'arsa. "The car's sensors detect the stop sign and send that information to the car's computer. The computer then compares that information to a database of road signs and recognizes the stop sign. It then calculates the car's speed and distance from the sign, and it instructs the car to slow down and come to a stop” Ya amsa cikin murmushi. Haka suka ci gaba da wurgo masa tambayoyi yana amsa su ɗaya bayan ɗaya. Ko da aka kai karshen tattaunawar tafi suka shiga masa suna jinjina baiwa irin tasa, ba a banza ya ci sunan nasa na RAM ba. “A gaskiya ka burgeni, kuma mun karɓi wannan device ɗin hannu bibbiyu, sannan muna so mu fara gwadashi da motocin mu daga nan zuwa wata uku...” Cewar shugaban kamfanin motocin, Rafeeq na murmushi irin wanda ya saba ya lumshe idonsa alamun ya amsa. Dan abu ne mawuyaci ka ga Ram na dariya, ba wai dan bai iya ba, sai dan ya fi yin murmushi. Kuma murmushin ya fi dace da kamillalliyar fuskarsa. Kuma wani abun burgewa game da shi shi ne, a duk sanda zai yi magana ba'a iya ganin haƙwaransa sosai, ko zaka gansu sai dai samansu kawai, amma wai ka ga haƙwaran Ram duka sai idan ya yi dariya. Kamar kullum haka Sir Thomas ya shiga faɗa nasa irin alfaharin da suke da shi. Sai da suka fice, kafin Rafeeq da Abdulrahman ma suka fita. “Wai ina hot chocolate ɗin?” Rafeeq ya tambaya yana buɗe ƙofar office dinsa. “Ga shi nan” Muryar ɗaya daga cikin ƙananu ma'aikatansu ta faɗi tana shigowa. A lokacin da yake zama a kan executive chair ɗinsa. “Mrs Matilda kwana biyu?” Ya faɗi yana kallon tsohuwar, Matilda ta ɗan yi dariya. “Na je ƙauye ganin yarana ne, shi ya sa baka ganina” Ya yi murmushi yana sipping hot chocolate ɗinsa. “To ya yaran naki?” Daga haka suka shiga hira da Matildan kamar yanda ya saba da kowa, dan duk ƙaryarka a wurin ba za ka ce ga abokin faɗan Rafeeq ba, kowa nasa ne, shi ma na kowa ne. Sai da Matilda ta fice Abdulrahman yace. “Da alama fa bamu ba komawa Nigeria kwana kusa” “Ni kaina ban so hakan ba, amma babu yanda za mu yi, dole mu tsaya zuwa wata ukun!” “To Allah ya kaimu” “Ameen” *Makoko, Lagos state, Nigeria.* Gigi ce zaune kusa da Papi tana risgar kuka. Shi kuma Papin sai aikin lallashi yake. “Kin ga Khadijatu, da yardar Allah Ekene zai fito lafiya!” Papi ya faɗi a ƙorinsa na kwantar mata da hankali. Gigi ta fyace hanci tana faɗin. “Ya za ayi na kwantar da hankalina? Sanin kanka ne idan 'yan sandanan marasa imani suka kama matasan yankin nan ba'a ƙara jin ɗuriyarsu... Wata ƙila shi ma hakan ce za ta faru da shi, na shiga uku ni Khadijatu! Me ya sa rayuwa ba ta min adalci? Ɗan marayan Allahn ma ba za'a ƙyale ba...” Ganin mutum tsaye a kansu ya sa ta yi shiru, suka dubi wanda ke tsaye a kan nasu a tare, tashin hankali ya sa sam ba su ga shigowarsa cikin gidan ba. Cike da razani Gigi da Papi suka dubi juna. Lazarus me gidan hayar da suke ciki ne, sun san halinsa, ba shi da mutunci. Hakan ya sa Gigi dubansa tana goge ƙwallar idonta. “Sannu da zuwa Lazarus... Ga wuri zauna!” Ta faɗi tana miƙa masa wata kujera a kusa da ita. Gabjejen mutumin me sunan Lazarus ya musu wani banzan kallo yana zuƙar karan sigarin hannunsa, ya furzar musu da hayaƙin yana faɗin. “Ba zama ne ya kawoni ba, ina 'yarku take?” Cikin inda-inda Gigi ta kalli Papi kafin tace. “Yan sanda ne suka kama Ekene, shi ne ta je ta yi belinsa...” Ba ta ko rufe bakinta ba, Lazarus ya bushe da dariya. “'Yar wahala kawai, na faɗa mata cewar wannan abun da take wahalar da kanta take a banza, amma ta ƙi fahimta, ina so ku fahintar da ita, ta aureni, zan hutar da ita” Gigi ta goge ƙwalla. “Dan Allah kayi haƙuri Lazarus, Shola ba ta san aurenka, ka yi haƙuri ka ƙyaleta” Ta faɗi wata ƙwallar na ƙara silalo mata. Lazarus yay musu wani wulaƙanttaccen kallo. “Okay, ba damuwa tun da haka kuka ce, ku shirya barin gidan nan, nan da sati ɗaya, sati ɗaya na baku, ka da ku kuskura ku haura hakan” Yana kaiwa nan, ya juya ya daka uban tsalle ya faɗa cikin kwale-kwalen da ya zo gidan da shi. Gigi ta kuma fashewa da kuka tana ɗora hannunta a ka. “Wayyo Allahna ni Khadijatu na ga ta kaina” Papi ne ya ɗan muskuta kusa da ita yana dafa kafaɗarta. “Ki dena kukan, ga su Ekene nan sun dawo, duba can ki ga!” Da sauri ta ɗago da kanta ta kalli ƙofar gidan, inda ta hango Shola, Ekene, Fa'ee da abokan Ekenen guda biyu. Har ta miƙe Papi ya riƙo hannunta, ta kalleshi. “Ka da ki faɗawa Shola abun da ya faru” Ta san a kan me yake magana, dan haka ta gyaɗa masa kai tana ƙara miƙewa. Zuciyarta cike fal da tashin hankalin da ba ta san ranar ƙarewarsa ba, don da a ce sun bar Shola ta auri mutum kamar Lazaru, gwanda su bar masa gidan nasa. Kuma yin hakan ma ba mafita ba ce, saboda ba su san inda za su je idan sun bar nan ɗin ba. *No. 811, Poka, Epe, Lagos state, Nigeria.* SURAJ ALI MUKTAR (SAM) POV. Zaune yake a ɗakinsa, ya kafe balcony da ido, kamar me ƙirga adadin iskar dake shige da fice ta wurin. Tunani ne fal ransa, tunaninta, ita ɗin da bai ko san sunanta ba. Kyawawan fararen idanuwanta sune suka manne a cikin tunaninsa. “Hamma Sam! Hamma Suraj!” Ya jiyo ƙanwarsa Narjis na ƙwala masa kira tun daga ƙasa. Kuma har ta shigo katafaren ɗakin nasa bai amsa ba. Mamaki ya kama Narjis ganin yayan nata zaune a kan sofa ya kafe balcony da ido. Ƙarasowa cikin ɗakin ta yi, ta zauna kusa da shi tana bangazarsa da kafaɗarta. “Ya dai officer, tunanin me kake?” Ya juyo ya kalleta. Sai ta shiga ɗaga masa gira cikin alamun tambaya. Zamansa ya gyara yana kallonta da kyau. “Narjis!” Ya kira sunanta, ita ma nata zaman ta gyara tana miƙa masa hankalinta kacokam. “Na'am Hammana” Ya lashi lips ɗinsa yana so ya kwatanta mata irin yanayin da yake ciki, dan duk wani sirrinsu tare suke tattaunashi, bata ɓoye masa komai, shi kuma ba ya ɓoye mata komai. “Wani abu nake ji yana yawo a zuciyata. Tun bayan da na ga wata yarinya a station yau. Zuciyata ta buga da ƙarfi, na ji ina son na kalli cikin idanuwanta, kuma na ji ina son na ci gaba da kasancewa da ita, ban... Ban ma san ya zan kwatanta miki abun ba” Narjis ta lumshe idonta ta buɗe. “Bro!” Ta kira. “Na'am Narjis!” Ya amsa. “Ka san menene sunan wannan halin da kake ciki?” Ya girgiza mata kai da sauri, dan bai sani ɗin ba, bai ma san halin da zuciyarsa take ciki ba, bai taɓa tsintar kansa a cikin hali makamancin wannan ɗin ba. “Love at first sight... You're in love Bro!” “Da gaske kike?” Ya tambaya yana kafeta da ido. “Ƙwarai, ka faɗa soyyaya, ina da tabbacin sonta kake” Wata ƙaƙƙarfar ajiyar zuciya ya sauƙe yana ɗauke kai. “Yanzu menene mafita?” Hannunsa ta kama, hakan ya sa ya kalleta. “Ka sameta... Ka faɗa mata...” Sai ya yi shiru yana jujjuya maganar tata. Kamar kada ya yarda, kuma kamar ya amince... “Wato ke da aka aiko ki kirashi, shi ne kema kika samu wuri kika darfe kamar bawan da aka aika garinsu ko?” Cewar wata farar mata tana tsaye daga ƙofar ɗakin, a tare suka kalleta. Kafin Narjis ta dafe kanta. “Wallahi na manta ma. Ka fito mu ci abinci” Ta ƙarashe tana mikewa. Har zuwa lokacin matar nan na tsaye a bakin ƙofar,ta rungume hannyenta tana kallon 'yan'yan nata biyu rak da Allah ya azurtata da su. Shi ma Suraj ɗin miƙewa ya yi suka nufo bakin ƙofar, sai a lokacin matar ta juya ta fita. Narjis da Suraj na take mata baya sun ƙus-ƙus kamar yadda suka saba. Da haka har suka sauƙa ƙasa zuwa katafaren falon gidan dake ƙasa. Daga nan suka zarce zuwa daninng area. Babu kowa a daninng ɗin sai wani farin datijjo dake sanye da farin gilashin da ya ƙara fitar da kammanin fuskarsa. Sai kuma tarin kala-kalar abincin da aka jere a kan daninng table. Datijjon ne ya ɗago daga duban wayarsa ya kallesu, a lokacin da Narjis ke zama a kan kujera. Yayin da Suraj ya kewa zuwa setinsa, ya sunkuya yana masa side hug. “Yaushe ka dawo Daddy?” Suraj ya faɗi a sanda ya saki mahaifin nasa, ya shiga jan kujerar dake kusa da ta Daddyn nasa. Daddy ya aje wayar hannunsa yana faɗin. “Ban jima ba... Mummyn ku ta ce kusan tare muka dawo da kai... Ya aka yi ka makara yau?” Ya ƙarashe yana wurga masa tambayar. Suraj ya buɗe plate ɗin dake setinsa yana murmushi. “Har na dawo gida, sai kuma na tuna da cewar na yi mantuwa a office ɗin... Shi ne fa na koma” A lokacin Mummy ta shiga zuba musu abincin da ta girka. “Aikin naku ba sauƙi Suraj” Ya ɗan yi murmushi. “To ya za ayi Daddy?. Tun da dan al'umma za ayi. So sai an daure” “Ka aje aikin mana!” Mommy ta faɗi a bakin gaskiyarta, dan ita dai kam bata son wannan aikin nasa na 'yan sanda. Shi da ya kasance magaji ɗaya tal na dukiyar Alhaji Ali Muktar, wai shi ne ya ɓuge da aikin ɗan sanda. Allah ya sani har cikin ranta bata san wannan aikin nasa tun sanda zai fara. Kuma sai da ta nuna masa ƙin amincewarta a lokacin, amma mahaifinsa ya yi uwa ya yi makarɓiya ya shige masa gaba har ya samu aikin. “Haba Badi'a!? Wai sau nawa za mu yi wannan maganar ne, yaron nan ya na san aikinsa, baki san abun da Allah ya hukunta faruwar sa a cikin aikin nasa ba!” Bakinta ta taɓe tana jan kujera, sannan ta ɗauke kai. Wayarta ce ta shiga ruri, hakan ya sa ta kalli screen ɗin. ‘TAYYAB AGHA!’ Shi ne sunan da ya fito ɓaro-ɓaro. Tsaki ta ja tana saka wayar a silent. Daddy ya dubeta yana tauna abincin bakinsa ya ce. “Ki ɗaga mana” Kanta ra girgiza ranta na suya na tunowa da 'yar uwarta ƙwallo ɗaya da ta yi. “Me zai cemin? Ai ba na tunanin akwai wani abu da ya rage da zamu tattauna tsakanina da shi, tun da har ba zai iya ganomin inda ƙanwata take ba” Ta ƙarashe muryarta na rawa. Nan take jikin yaranta ya yi sanyi, dan sun saba ganin mahaifiyar tasu a cikin irin wannan halin. Narjis ce ta dafa kafaɗarta. “Dan Allah Mummy” Kanta ta girgiza. “Ba komai fa!” Surja ya ci gaba da kallonta yana lissafa tazarar dake tsakaninsa da samawa mahaifiyarsa farin ciki. Tun tasowarsa ya fahimci cewar rabin farin cikin mahaifiyarsa na tattare da ƙanwarta Rahila. Kuma tun bayan da Rahilan ta ɓata rabin farin cikin mahaifiyarsu ya ragu, hakan tasa ya dage kan shi ɗan sanda yake san zama, ba dan komai ba sai dan ya nemo inda Ƙanwar mahaifyarsa take. Amma har zuwa yau bai samo komai ba. _______________ _To fa, waye ya hango duhun dake tunkarar RAM?_ _Sannan ga Lazarus dake shirin ɓallo ruwa_ _Shin kun gane cewa Anti Badi'an da Tayyab Agha ke kira ita ce mahaifiyar Suraj!._ _Ga kuma Suraj ya kwarewa Diya Shola ɗiyar yarabawa..._ _A juri zuwa rafi dai_ A. ISAH CE ✍️. °°°°°°°°°°°°°°°° *💡HASKE...💡* *©SALMA AHMAD ISAH* TAURARI WRITER'S ASSOCIATION. *Page 07* ~~~ *Ƙauyen Wagini, Batsari Local government, Katsina state, Nigeria.* *08:00 na dare.* SALMA SA'AD (SALAME) POV. Zaune suke a kan tabarma suna cin tuwon dare ita da Muja, yayin da Inna ke zaune a kan dakalin ƙofar ɗakinta tana saƙa hular sanyi ta yara, kasancewar saƙa sana'arta ce tun da can. Iya Abu kuma na zaune a cikin ɗakinta tana lazumi. Sallamar Baba da Audu suka ji daga soro. Salame da Inna suka amsa a tare, yayin da Muja ya fita da gudu ya nufi Baba yana shirin rungumeshi, Baba ya riƙeshi yana faɗin. “Bari bari bari Mujahid! Kar ka ɓatamin kaya” Muja ya shiga yi wa Baba shagwaɓa irin tasu ta autanni. Yayin da Salame, Inna da Ya Audu suke musu dariya. “Wasa nake maka Autana, zo nan” Baba ya faɗi yana janyoshi. Muja na maƙale da ƙafarsa suka shigo cikin gidan. “Sannu da zuwa Malam!” Inna ta faɗa. “Baba sannu da zuwa! Hamma Audu sannu da zuwa!” Cewar Salame, suka amsa su duka. Hamma Audu na zama a kusa da Salame, yayin da Baba ya zarce ɗakinsa Auta maƙale da shi. “Salma ga wannan!” Hamma Audu ya faɗi yana miƙowa Salame wani abu a cikin baƙar leda. Hannu bibbiyu ta sa ta karɓa, haɗi da masa godiya. Kuma tun kafin ta buɗe ta san miye a ciki. Awara ce me ɗumi da fura me sanyi irin wadda ya saba kawo mata kullum ranar kasuwa, kasancewar tana san fura sosai. “A kawo maka abinci?” Inna ta faɗi ganin ya miƙe. Kansa ya girgiza. “A'a tukkuna dai... Zan je wurin su Suma'ila ne” “To sai ka dawo” Ya gyaɗa kansa yana juyawa. “Hamma zan kai maka abincin naka ɗakinka, dan wata ƙila sanda zaka dawo mun kwanta” Cewar Salame tana kallon bayansa, juyowa ya yi ya kalleta yana murmushi, kafin ya gyaɗa mata kai ya fice, ta bishi da adawo lafiya. Tuni ta ture kwanon tuwon dake gabanta, ta buɗe ledojin da Hammanta ya bata. Inna ta fara miƙawa tana faɗin. “Inna awara” Inna ta girgiza kai tana miƙewa don ta kaiwa mijinta abinci. “Na ƙoshi Salame” “Furar fa?” Inna ta yi dariya tana nufar rumfar da suke girki. “Na ƙoshi na ce miki...” “Muja! Muja! Muja!” Salame ta shiga ƙwala masa kira. Da sauri ya fito daga ɗakin Baba, hannunsa riƙe da ledar kilishin da Baba ya siyo masa. “Zo mu ci awara da fura, hamma ne ya kawomin” Muja ya zauna kusa da ita yana nuna mata ledar hannunsa. A lokaci guda kuma yana tauna kilishin bakinsa. “Ni ma Baba ya kawomin kilishi” “To mu je ɗakin iya mu ci a can” A tare suka miƙe suka shiga ɗakin Iya. Fitilar ƙwan dake ɗakin ta haska musu ita. Zaune take a kan darduma tana lazuminta na kullum. Hannunta na dama na jan carbin da ta saba jansa a kullum rana. Zama suka yi kusa da ita suna mata bismillah. Kanta kawai ta girgiza musu alamun ba za ta ci ba. Haka Salame da Muja suka cinye kayansu tas. Kafin Salame ta fita zuwa gidansu Karime, bayan da ta kaiwa Audu abinci ɗakinsa. Yayin da Muja ya nufi wurin abokansa dan su yi wasa. Kasancewar yankin nasu na fama da rashin tsaro. Dan ƙauyukan dake kusa da nasu duk an farmakesu, nasun ne kaɗai ba'a taɓa shiga ba. Hakan ta sa ba sa jimawa a waje idan dare ya yi. Da wuri Salame ta koma gida. Tana taka soron gidan za ta shiga ciki, ta tsinkayo hirar iyayenta dake zaune a tsakar gida. “Ɗazu Malam Halliru ya zo ya sameni da wata magana a kan Salamatu!” Jin hakan ya sa ƙafafunta cin birki a soron, ta tsaya tana kasa kunne dan jin batun da za ayi a kanta, duk kuwa da ta san maganar ba za ta wuce ta aurenta da ɗan gidan Malam Hallirun da ake shirin yi ba. Aure! Ita tun da take ba ta taɓa ganin ko fuskar Haladun da aka ce za'a aura mata ba, dan ita ba yawo take ba. Daga gida sai makarantar boko sanda tana zuwa kenan, kafin ta yi candy, sai kuma ta Allo da suke zuwa ita da Muja da asuba. Sai gidan su Karime, sai kuma aike idan ya taso. Ko irin tallar nan da 'yan matan ƙauye ke yi ita ba ta yi, dan Baba ba zai bari ba, hakan ya sa ta zama kifin rijiya. Kuma auren nata irin auren nan ne na haɗi, dan ko shi angon me suna Haladu ba ta jin ya taɓa ganinta. Iya dake zaune kusa da shi Sa'adu tace. “Me yace?” “Magana ce a kan bikin Salame da Haladu, ya ce ya na so a yanke bikin nan da sati ɗaya, dan su a shirye suke” Inna dake zaune a ɗaya ɓarin nasa ta gyaɗa kai. “To kai me ka ce masa?” Iya ta kuma tambaya. Baba ya sunkuyar da kansa yana faɗin. “To me zan ce da ya wuce to, kawai na amince da abun da ya zo da shi ɗin. Dan ban ga dalilin jiran ba, tun da mu ma a shirye muke...” A lokacin Salame ta yi sallama sannan ta shigo cikin gidan. Ba tare da ta ce musu komai ba ta faɗa ɗakin Inna. Auta ta fara yi wa shimfiɗa, wanda ta iske kwance a kan gadon ƙarfen Inna yana bacci. Kafin ta yi tata shimfiɗar. Ta tashi Mujan ta ce masa ya je ya yi fitsari ya zo ya kwanta. Yana cuna baki cikin magagin barci ya fice daga ɗakin, yayin da ita kuma ta shiga cikin nata gidan sauron ta kwanta. Tunani barkatai a kanta. Ita ba za ta ce bata son wannan auren ba, kuma ba za ta ce tana so ba, kawai dai tana tsaye a tsakiya ne, ba ta san ina ta dosa ba. Tana nan kwance a wurin har Muja ya dawo ɗakin ya shiga tasa shimfiɗar. Har Inna ta shigo ɗakin ba ta samu bacci ba. Kuma ta rasa abun da ya hanata barcin!. *A. Foods NIG LTD, 38 Eric Moore Road, Iganmu, Lagos, Nigeria.* TAUQEER POV. A hankali tayoyin gray color ɗin motarsa ƙirar Lamborghini Veneno suka tsaya a katafaren wurin aje motoci na kamfanin. Tun kafin ya fito daga cikin motar ma'aikatan dake kai kawo a wurin suka taho da sauri har su biyu suka buɗe masa ƙofar motar. Ya fito ya na ɗan jifansu da murmushi kamar kullum. Sanye yake cikin wata blue suit, wadda ta dace a fatar jikinsa, idanuwansa manne da baƙin glashi. Tafiya ya soma yi, yana nufar ginin ma'aikatar, inda ofisoshinsu suke. Yayin da ɗaya daga cikin ma'aikatan da suka buɗe masa mota ke biye da shi yana riƙe da briefcase ɗinsa. Tun da ya shigo wurin kowa ke gaisheshi, shi kuma yana amsawa cikin mutunci, saboda shi ba ya ganin cewa ba ɗaya suke da shi ba, dan suna aiki a ƙarƙashinsu ba ya nufin cewa su sama suke da su ba. Katafaren office ɗinsa ya nufa, yana shiga ya zauna yana aikawa Secretary ɗinsa kira. Cikin abun da bai wuce minti ɗaya ba sai ga ta ta shigo office ɗin bayan ta nemi izinin shigowa, tambayarta ya yi game da ayyukansa na yau, ta zayyano masa kaf ayyukan da zai yi a yau ɗin, duk da wasu ayyukan ba na yau ɗin ba ne, tafiyar da ya yi ce ta sa suka zama na yau ɗin. Sallamarta ya yi bayan ya bata wani File ya ce ta bawa messenger ya kai office ɗin Baffa Muzamill. Yana duba wani file Asad abokinsa ya shigo. Asad abokinsa ne a harkar waƙa kuma tare suke aiki a kamfani ma. Ɗan kauda kai ya yi daga barin kallon file ɗin ya kalli Asad ɗin. A lokacin da yake zama a kujerar dake fuskantarsa. “Ban san ka dawo ba ai” Cewar Asad ɗin yana gyara zaman tie ɗin wuyansa. Tauqeer ya kauda kai yana ɗan guntun murmushi. “Sai de idan mantawa ka yi... Amma sanda in airport na kiraka” Asad ya ɗan yi shiru yana son tunowa. Saboda cutar mantawa dake damunsa a wasu lokutan. Kansa ya gyaɗa yana gyara zama. “Na tuna yanzu... Magana ce a kan wata yarjejeniya da SSGF record leble...” Da sauri Tauqeer ya dakatar da shi da faɗin. “A office muke ba studio ba Asad, so ba maganar waƙa a nan, aiki kwai!” Asad ya jinjina kansa. Kafin shiru ya ɗan ratsa na wasu sakkani, can kuma sai ya tuno da abun da ya shigo da shi office ɗin Tauqeer ɗin. “Dan Allah Tauqeer so nake ka haɗani da RAM! Jiya da daddare aka yi hacking Facebook page ɗina!” Tauqeer ya dubeshi. “Garin yaya?” Ya ɗan ɗaga kafaɗu cikin taɓe baki. “Ban sani ba Wallahi, kawai jiya ina zaune na ga an yi hacking ɗinsa, kuma ko da na duba ta wayar Ummu Kulsum(Ƙanwarsa) sai na ga sunan wani a kai wai shi ‘Henry Samuel’” Tauqeer ya ɗan yi dariya yana janyowa wayarsa. “Sun kara maka kenan?” “Wallahi! To ya zan yi da rayuwa?” Tauqeer ya jinjina kai yana neman lambar babban abokinsa na jami'a, wato RAFEEQ AHMAD MUHAMMAD a.k.a RANDOM ACCESS MEMORY, a.k.a RAM. Da ƙyar ya iya lalubo lambar, ba wai don lambobin dake cikin wayar tasa suna da yawa ba, sai dan sukan jima ba tare da sun yi waya da Rafeeq ɗin ba, kasancewar shi Ram a duniya bai bawa waya muhimmanci ba. Saboda sai ya fi wata ba tare da ya san duniyar da wayar tasa take ba. Sai da ya jera masa kira biyar, amma ba'a ɗaga ko ɗaya ba, kuma hakan ba sabon abu ba ne gareshi, dan wannan sababbe ne, haushin rashin samun Rafeeq ɗin a waya ya sa ya den kiransa, sai idan shi Rafeeq ɗin ya yi jajensa ya neme shi da kansa. “Mtsww! Shi ai ka ji matsalarsa” Ya faɗi yana ƙara trying. Cikin sa'a a wannan karon sai ya amsa. “Kai kam Rafeeq ka ji jiki!” Daga ɗayan ɓangaren Rafeeq ya yi dariya. Dan ya san faɗan abokin nasa na miye. Yanzun ma Allah ne ya temakeshi ya daga kiran nasa, dan yana duba wani abu cikin kayansa ne Allah ya sa ya ci karo da it, ya ga kiran Tauqeer ɗin, shi ne fa ya ɗaga. Tattoo ɗin wuyansa ya sosa yana faɗin. “Da na yi me?” “Ban sani ba, Ina Maa? Fatan tana lafiya?” Ta jero masa tambayoyin. Sai da Rafeeq ya ɗan juya ya kalli ƙofar ɗakinsa sannan yace. “Lafiyarta ƙalau Wallahi, sai godiya, jiya da na dawo daga aiki take tambayata kai” Tauqeer ya ɗan yi murmushi. “Ka ce mata ina lafiya” Daga ɗayan ɓangaren Rafeeq ya gyaɗa kansa. “Za ta ji da yardar Allah. Ya ya naka ahalin?” Ya tambaya cikin sauƙƙaƙƙiyar jimla, dan idan har yace zai zauna yana lissafo tarin mutanen dake Agha Mansion za su cinye lokaci ne ba tare da sun gama ba. “Kowa lafiya ƙalau. Wai kai yaushe za ka dawo?” “Wata ƙila nan da wata uku, ban de tabbatar ba” A lokacin ne kuma Asad ya ɗaga masa hannu alamun yana nan fa, kuma cikin son ya tunasar da shi dalilin kiran Ram ɗin. Dan idan Tauqeer ya haɗu da Rafeeq shi ne ke kamuwa da cutar mantuwar. Kuma ya manta ɗin, dan haka yace. “Asad ne ya sa na kiraka, wai an yi hacking Facebook page ɗinsa... Shi ne yace na kiraka ko akwai yanda za ayi a dawo masa da shi” Rafeeq ya nemi bakin gadonsa ya zauna tare da janyowa laptop ɗinsa ta kullum, wadda ke ɗauke da manyan rubutun sunan ‘RAM’ cikin manyan baƙi, manne a bayan screen ɗinta. “Ba shi wayar” Ya faɗi yana tare wayar da kafaɗarsa. “Hello! Rafeeq” “Na'am Asad... Faɗomin lambar da ka buɗe facebook ɗin da ita” Cikin sauri Asad ya karanto masa lambar, yayin da shi kuma yake rubutawa a laptop ɗinsa. Ya ɗan yi wasu 'yan danne-danne na minti ɗaya, har zuwa lokacin kiran na tafiya. “Akwai wasu lambobi da za su shigo ta layinka, buɗe ka karonto min su” Rafeeq ya faɗa bayan wani lokaci. Daga ɗayan ɓangaren Asad dake kare da wayar Tauqeer ya lalubo wayarsa. Kuma an turo lambobin, saboda haka ya karantawa Ram su. Cikin minti ɗaya yace. “Shiga ka duba” Hannu na rawa Asad ya shiga dubawa. Bakinsa ya buɗe cikin dariya yana kallon Tauqeer da ya ci gaba da duba file ɗin gabansa. “Ya dawo Wallahi...” “Ok saika kula saboda gaba, na saka maka matakan kariyar da babu wanda zai ƙara hacking ɗin page ɗin... And one more thing, ba da niyya Henry ya sace maka account ba, account yake son buɗewa a instagram. Sai ya danna join facebook account, alhalin bashi da account a Facebook, su kuma da suka tashi sai suka bashi account ɗinka ya buɗe... To ka ji” Asad ya jinjina kai yana ƙara girmama basira da hazaƙar Ram. Tauqeer ya miƙawa waya wanda ke tambayarsa shin account ɗin ya dawo? Cike da murna Asad ya amsa shi da Eh yana barin office ɗin. Sai da Tauqeer ya tabbatar da Asad ya yi nisa daga office ɗin nasa sannan damuwa ta maye fuskarsa. “Feeq ina so ka min wani temako” Rafeeq ya gyara zamansa. “Faɗi ko menene Bro, ni me iya maka ne, in har bai fi ƙarfi na ba” Ya faɗi, idonsa na hasko masa tarin alkairan Tauqeer gareshi a sanda suke karatu. Sai da Tauqeer ya haɗiye yawu, sannan ya goge bakinsa da tafin hannunsa. Kamar me shirin furta wata ƙazamar kalma. “Ka dai san halin da Jamal ya shiga a shekarar nan... To yanzu abun ya yi ƙamari, dan yanzu ba ya kwana a gida. Yanzu haka zancen da nake maka kwanansa takwas bai kwana a gida ba, kuma ba mu san inda yake ba. Shi ne nake so ka bi diddigin layinsa, dan mu san inda yake, Habibty na cikin damuwar rashin ganinsa a gida!” Rafeeq ya yi shiru. “Wallahi Agha sai ka sa na ji kunya, yanzu dan kana so na yi tracking numbern Jamal shi ne sai ka marairaice murya kamar me roƙon guntun buredi?” Tauqeer ya shafa sumarsa ya na ɗan murmushi kaɗan. “Ka fara ba?” “Kawai ka turo min lambarJamal ɗin” Tauqeer ya gyaɗa kansa. “Okay!” *Federal Neuro, Psychiatric Hospital, Yaba, Lagos, Nigeria...* A cikin madai-daicin ɗakin kwantar da marasa lafiya na asitin, kwance a kan gadon marasa lafiya na ƙarfe irin na asibitocin masu fama da cutar taɓin hankali. Wata mata ce, sanye cikin shuɗayen kaya. Idonta a rufe. Kanta babu ɗankwali, hakan ya bayyana kyakkyawar sumar kanta da ta fara sirkawa da fari. Ba wai dan shekarunta sun kai na tsufan ba, sai dan azabar rayuwa da take sha. Hannayenta da ƙafafuwanta kuwa ɗaɗɗaure suke a jiikin ko wani saƙo na gadon, ta yanda babu damar guduwa. Kuma bayan wannan gadon da take kwance a kai, babu komai a ɗakin face ƙarfen saƙala drip. Daga waje kuwa ƙofar ɗakin kulle take da wani garƙamemen kwaɗo. A dai-dai lokacin da rana ta hasko cikin ɗakin daga taga, ta hasko fuskar matar, a dai-dai lokacin, yatsan tsakiya na hannunta ya motsa. Kamar almara kuma sai ta motsa ƙafarta. Da aka ƙara jimawa kuma sai ga ƙwalla ta silalo daga gefen idonta na ɓarin dama. Ƙwallar ta ci gaba da gangariwa daga kwarmin idonta har zuwa cikin kunnenta. A hankali bakinta ya buɗe. Ta furta “‘Yata!” kawai a kan laɓɓanta. A dai-dai lokacin, babu abun da take gani a cikin kanta face yadda aka rabata da ‘Yarta sabuwar haihuwa. ___________________ *Shekara ta 2000.* _Tafe suke ita da Hajia Maryam matar Faruq Agha. Yayin da Maryam ɗin ke riƙe da ita, saboda tsohon cikinta da ya girma, haihuwa yau ko gobe._ _“A hankali!”_ _Cewar Maryam ɗin tana buɗe mata ƙofar ɗakinta. Rahila na murmushi ta ci gaba da taka kumburarrun ƙafafuwanta zuwa cikin ɗakin. A bakin gadon ɗakin Maryam ɗin ta zaunar da ita tana faɗin._ _“Babu abun da kike buƙata?... Dan ina so na je na ɗorawa su Tauqeer abincin rana, saboda na ga lokacin tashi daga makaranta ya yi”_ _Ta ƙarashe tana kallon agogon bangon dake ɗakin. Rahila ta girgiza kai._ _“Babu komai Antina, ki je kawai”_ _“Kin tabbatar?”_ _Rahila na murmushi ta gyaɗa kai. Ita ma Maryam ɗin kanta ta gyaɗa tana nufar ƙofar ɗakin tace._ _“Zan bawa Hafiza apple ta kawo miki!”_ _Rahila ta yi murmushi tana shafa tsohon cikinta. Ba jimawa sai ga Hafizan ta shigo, hannunta rike da plate me ɗauke da yankakkiyar apple. Kuma duk halin shariya da nuna halin ko in kula na Hafiza a gidan, suna shiri da Rahila, dan ko yanzun da ta kawo mata apple ɗin, sai da ta tabbatar da ta cinye, sannan ta ɗauke plate ɗin ta fita, bayan ta ce mata ta kwanta ta huta._ _Kwanciyar ta yi, ba jimawa ta ji wayarta ƙirar Motorola irin ta wancan zamanin ta shiga ruri, hakan ya sa ta janyota. Ganin yayarta Anti Badi'a ce me kiran ya sa ta ɗauka da sauri._ _“Ya jikin naki?”_ _Shi ne abu na biyu da Anti Badi'a ta tambaya bayan Rahila ta gaisheta._ _“Jiki Alhamdullilah. Ina Suraj!”_ _“Ya tafi makaranta, amma duk inda suke na san sun kusa dawowa gida”_ _Hira suka ɗan taɓa, kafin suka yi sallama. Wayar tasu na yankewa, kamar me jira sai ga kiran Tayyab ya shigo wayar tata._ _Dariya ta yi, kafin ta ɗaga kiran da sallama a bakinta. Cike da kulawa irin ta mijin dake tsantsar son matarsa ya shiga tambayarta halin da take ciki. Ita kuma tana bashi amsa cike da ladabi. Kuma wannan ladabin nata shi ne yake ƙara sama mata gu a zuciyarsa. Dan a aurensa na farko bai samu hakan ba._ _Har suka yi sallama yana ƙara jaddada mata kada ta yi aikin komai, ta kwanta ta huta kawai. Yankewar wayar tasu ba ɓata lokaci, ta ji ciwon bayan da ta fara yi tun jiya ya tsikareta, da ciccije baki da komai ta samu ta dafa ta zaune._ _Miƙewa ta yi da niyyar shiga banɗaki ta ji mararta ta yi wani irin juyawa. Ta dafe wurin da sauri tana karanto ‘Innalillahi wa inna'ilaihi raji'un’._ _Kamar daga sama ta ji ana kiran sunanta da ƙarfi. Hakan ya sa ta dafe kunnenta, tana ci gaba da faɗin abun da take faɗa. Ji ta yi kamar ana janta zuwa waje, kamar ana cewa ta fita zuwa waje. Ba tare da ta sani ba ƙafafunta suka juya zuwa ƙofar ɗakin. Bayanta da mararta na ci gaba da amsawa._ _Ko da ta fita daga ɗakin nata bata tsaya a ko ina ba sai tsakiyar ɗakin Hajia Zayya. Hajia Zayyan na ganinta ta jefeta da wani mugun murmushi. Kuma daga wannan murmushin, ba ta ƙara sanin inda take ba, sai farkawa ta yi ta ganta a cikin wani ɗaki me matsanancin duhu. Ga mararta dake ƙara ƙullewa, bayanta ya ci gaba da mata ciwo. Haka ta shafe tsawon awwanin da bata sansu ba a ɗakin, ita kaɗai ta yi naƙuda, har Allah ya bata ikon haihuwa._ _A sanda kukan jaririn ya baza dakin wani irin HASKE ya mamaye ko ina. Kuma ta cikin HASKEn ta ga Hajia Zayya da wani yamushasshen tsoho, tsaye a gabanta suna kallonta._ _Da ƙyar ta iya zama a kan dandaryar ƙasar dake wurin da bata san ina ne ba. Jini mamaye a ƙasan inda ta yi naƙuda. Da ƙyar ta iya ɗaukar jaririn da ta haifa ɗin, ta dudduba jikinsa har ta fahimci cewa mace ce._ _Kuma har zuwa lokacin Hajiya Zayya da wannan tsohon na tsaye a gabanta suna kallonta._ _“Zayya me kika yi?”_ _Ta tambaya da ƙyar. Saboda numfashinta dake sama-sama._ _“Abun da na miki alƙawari a kansa shi nake yi”_ _Hajiya Zayyan ta faɗa._ _“Dan Allah Zayya ki ƙyalemu mu tafi. Kada ki cutar da mu dan Allah...”_ _“Ai tun da kika auri mijina na riga da na yanke cewar mutuwarki a hannuna take, waye ya faɗa miki cewar Zayya tana haɗa miji da wata? Ba'a haifi me zama lafiya da mijin Zayya ba!”_ _Cikin raɗaɗin ciwo Rahila ta yi murmushi._ _“An haifeta mana, gani nan zaune a gabanki, kuma ko ba komai na auri mijinki, na yi zaman farin ciki da shi har na tsawon shekaru biyu, ga kuma ribar aurenmu kina gani da idonki!”_ _Ta ƙarashe tana rungume sabuwar jaririyarta dake kuka har zuwa lokacin. Cikin fusata Hajiya Zayya ta rarumi wani katako, ta yi kan Rahila da shi, kuma tana isa gabanta ba ta yi wata-wata ba wurin ɗaga shi sama tare da buga mata shi a tsakiyar ƙwaƙwalwa. Daga nan kuma bata ƙara sanin komai ba, ba ta sake gane komai ba, ba ta sake jin komai ba sai a yau!._ ______________ Idanuwanta ta ci gaba da motsawa, har ta samu damar buɗesu tar. Bin ɗakin da take ciki ta yi sa kallo. Kafin ta yunƙura da nufin tashi, amma sai ta ji hannayenta a ɗaure tamau, ta motsa ƙafafunta, suma ta ji su a ɗaure, hakan ya sa ta kalli jikinta. Ta ga cewa a ɗaɗɗaure take. Da ƙyar ta motsa bakinta cikin faɗin. “Innalillahi wa inna'ilaihi rajiun!” Saboda kanta da ta ji ya sara. Motsi ta ci gaba da yi da ƙafafuwanta da kuma hannayen. A ƙoƙarinta na kunce ɗaurin da aka mata. Wata nurse ce ta zo wucewa ta ƙofar ɗakin, kuma ta cikin ƙarafunan da suka rufe ƙofar, ta hangi matar dake cikin ɗakin na jijjiga gadon. Idanuwanta ta zaro cike da mamaki. Dan abun akwai abun mamaki, idan ta canka dai-dai, yau kusan shekaru 24 tana asibitin, ba ta taɓa ko da motsa hannunta ba, amma yau sai ga ta tana jijjiga. Da gudu ta juya ta nufi office ɗin Dr. Bashir. Tana zuwo ko neman izini ba ta yi ba ta shiga tana haki. Dr. Bashir dake waya ya sauƙe wayar daga kunnesa ya dubi nurse ɗin cikin ɓacin rai ya furta. “Baraka wannan wani irin rashin hankali ne? Za ki shigo min office babu ko knocking” Ƙirjinta ta dafe tana haki. “Dr wannan matar dake cikin room No.36 ce ta farka!” Cikin Dr. Bashir ya bada sautin Ƙuuuuuu!. Ba shiri ya miƙe tsaye waya riƙe a hannunsa, baki sake yake kallon Baraka. Nan take zufa ta fara keto masa dan tsabar tashin hankali. Da gudu ya fita daga office ɗin nasa Barakan na biye da shi har suka kai ƙofar ɗakin. Ji ya yi yana shirin zamewa zuwa ƙasa. Saboda ƙafafuwansa da suka ɗauki rawa. A sanda ya ɗora idonsa a kan matar dake kwance a kan gadon tana ci gaba da jijjiga shi a ƙoƙarinta na ƙwatar kanta. Kai tsaye ƙwaƙwalwarsa ta hasko masa wani hoto da ya wuce shekara 24 baya. Cikin wani dare ne da ba zai iya manta shi ba. Wata mata ta zo asibitin. Ta sameshi har office ɗinsa, ta bashi maƙudan kuɗaɗe, sannan ta ce masa akwai wata mata da ta zo da ita, tana so ya aje mata matar a nan asibitinsu, ita kuma ta masa alƙawarin za ta riƙa bashi kuɗaɗen da suka ninka yawan albashinsa duk wata. A lokacin sai da ya tsorata da tunanin idan matar ta farka ta ganta a gidan mahaukata alhalin ita da hankalinta me zai faru? Amma matar me suna Hajiya Zayya! Ta sanar masa da cewar har duniya ta naɗe matar ba za ta taɓa farkawa daga wannan doguwar suman da ta shiga ba. Buƙatarta kawai ya aje mata ita a nan asibitin nasu. Kuma har a watan da ya wuce sai da Hajia Zayyan ta bashi kuɗaɗen da ta saba bashi duk wata. Yanzu kuma ga wani zance, matar da aka kawo ta farka, ba ma haka ba, tana cikin hayyacinta, dan a sanda ta lura da tsayuwar mutane a bakin ƙofar ɗakin ta kallesu tace su zo su kunce ta. Juyowa ya yi ya kalli Baraka. “Je ko kawo min allurar Midazolam” (Midazolam allura ce da kan gusar da hankalin mutum ta saka shi bacci nan take. An fi yawan amfani da allurar lokacin da za'a yi surgery) Da gudu Baraka ta bar wurin, har ta je ta dawo yana tsaye a ƙofar ɗakin yana kallon matar da bai san ko sunanta ba. Shi ne ya buɗe kwaɗon ƙofar, sannan ya shiga, Barakan na biye da shi, hannunta riƙe da allurar. Ko da suka shigo sai Rahila ta dena ƙoƙarin kunce kanta, ta shiga rarraba idonta a kansu. Kuma sai da ta gansu ta tabbatar da cewar a asibiti take. Tun da kayan likitoci ne a jikinsu. Ganin namijin ya karɓi allurar yana haɗawa ya sa Rahilan faɗin. “Likita! Likita! Ina 'yata?! Ina jaririyata take?! Dan Allah ka kawomin ita, ku bani 'yata na ganta...” Da ido Dr. Bashir ya yiwa Baraka alama da ta kewata ta ɗayan ɓarin ta rike masa ita. Tuni Rahila ta fara hawaye tana kallonsu. “Dan Allah ku bani 'yata! Ku... Ku... Ku bani jaririyata... 'yata ce! 'Yata! 'Yata!.... 'Yata...” Sai kuma ta yi shiru, saboda allurar da ta soma aiki a jikinta. Tun tana gani dishi-dishi, har ganinta ya ɗauke duka, jikinta ya saki, bakinta ya buɗe, kanta ya koma gefe. Ƙaƙƙarfar ajiyar zuciya Dr. Bashir ya sauƙe, sannan ya juya ya fita, Baraka biye da shi. Ko da ya shiga office ɗinsa sai ya kasa sukuni, ya ɗauki robar ruwa ya sha, ya ja kujera ya zauna yana sharce gumi. Sannan ya janyo wayarsa ya lalubo lambar Hajiya Zayya, ya aika mata kira, ringing ɗaya... Biyu... A na ukun ta ɗaga. “Hajiya akwai matsala!” Shi ne abun da ya fara faɗi tana ɗaga kiran. Daga can Agha Mansion Hajiya Zayya ta miƙe tsaye cikin matsanancin tashin hankali. Da ma tun da ta ga kiransa jikinta ya bata akwai matsala. Wata busasshiyar iska ta haɗiye a maƙoshinta, sannan ta ce. “Me yake faruwa?” Gumi Dr. Bashir ya kuma sharcewa. “Mara lafiyar nan ta farka!” A hankali ba tare da ta ce komai ba ta sauƙe wayar daga kunnenta. Ta yi cilli da ita kan gado. Sannan ta shiga safa da marwa a ɗakinta. Me ya sa Rahila za ta farka yanzu? Me ya sa Rahila ba ta farka ba sai da ta ga tana daf da cika burinta?. Duk laifin Ƙundus ne, tun a waccan lokacin ta so a kashe Rahila gaba ɗaya, amma ya hanata, ya ce wai bai kamata ta mutu yanzu ba. 'Yar tata kawai ya amince da a kashe. Kuma a ranar ta dawo gida da jaririyar. Ta samu Kande, ɗaya daga cikin 'yan aikin gidan, wadda ta yarda da ita, ta kuma san dukanin surrukanta, ta bata jaririyar tare da umartarta da ta je ta binne jaririyar da ranta. Kuma Kanden ta karɓi jaririyar, har ma ta je ta aiwatar da abun da ta umarceta. Komai ya tafi dai-dai a lokacin, ta gama da wannan matsalar, to me zai sa wata matsalar ta sake ɓullowa kuma? Dole ne ta yi wa tufkar hanci, ita ce Zayya! Zayyar da babu wanda ya isa ganin bayanta sai idan ita ta so, babu ma ta yanda za ayi ace ta saduda, dole ta nemawa kanta mafita. Wani murmushi ta saki, a lokacin da ƙwaƙwalwarta ta hasko mata mafita ɓaro-ɓaro. Bakin gadonta ta samu ta zauna tana ƙirga biyar zuwa goma. Ba a haifi wanda zai kawo ƙarshenta ba har yanzu, ta sanda yadda za ta yi da Rahila, kamar yadda ta shafeta daga tunanin kowa na gidan, ciki kuwa har da Tayyab, haka za ta shafeta daga doron duniya!. Shi kenan kuma, wannan matslar ma ta zo ƙarshe. Ta kuma yin wani murmushin. Tunaninta kenan, kuma tana wannan tunanin ne ba tare da sani zuwan wata ƙaddara me tafe da HASKEn da zai kawo ƙarshen duhun da ta mamaye makusantanta da shi. Duhun da ta fake a cikinsa tana cutar da makusantanta. ______________ _Ina tunanin daga wannan shafin za mu tsunduma cikin labarin_ _Dan duka wannan sharar fage ce_ _Mun riga da mun kamo bakin zaren labarin_ _To sai ku gyara zama, dan a yanzu ne za mu fara saƙa zaren labarin bi da bi..._ _Da fatan za ku kasance tare da ni_ A. ISAH CE ✍️. °°°°°°°°°°°°°°°° *💡HASKE...💡* *©SALMA AHMAD ISAH* TAURARI WRITER'S ASSOCIATION. *Page 08* ~~~ *Makoko, Lagos state, Nigeria.* DIYA POV. “Dan Allah Fa'ee ki yi sauri!” Diya ta faɗi yayin da take tsaye a ƙarshen rumfar gidansu tana kallon gidansu Fa'een da take ta jira tun ɗazu, dan ta zo su tafi wurin aiki. “Yi haƙuri Diya! Ga ni nan zuwa” Muryar Fa'ee ta bata amsa daga cikin gidan. Cike da ƙosawa Diya ta juyo ta kalli Gigi, Papi da Ekene dake zaune a kan rumfar gidansu. Ekene na kwance a kan katifa, dan har yanzu jikinsa babu ƙwari, saboda ya doku ba ƙarya. Papi kuma na zaune a wurin da ya saba zama kullum, yayin da Gigi ke zaune a kan kujera ta yi tagumi. Tun shekaran jiya da suka dawo daga police station, Diya ta lura da Gigi da kuma Papi suna cikin damuwa, musamman ma Gigi. Amma ko da ta tambaya sai tace mata babu komai. Sunkuyawa ta yi tana ɗaura igiyar canvas ɗinta da suka tsufa sosai tana faɗin. “Gigi wai ba za ki faɗamin abun da yake damunki ba?” Ta tambaya ba tare da ta kalli Gigin ba. Kuma tambayar da ta mata ce tasa Papi da Ekene kalon Gigin a tare. Gigi ta sauke hannyenta daga kan kuncinta tana kallon Diya. Ƙwalla na ciko idonta tace. “Babu komai fa nace miki!” Diya ta ɗago ta dubeta. “Gigi...” Ba ta kai ga faɗin abun da ke bakinta ba Fa'ee ta shigo rumfar a gaggauce tana faɗin. “Muje Diya, na gama shiryawa!” Kallon Fa'een ta yi, kafin ta juyo za ta yi wa Gigi magana, amma sai Gigin ta yi saurin cewa. “Ya kamata ku tafi Shola, kun makara fa” Shiru ta yi tana ci gaba da karantar Gigi ɗin, kafin ta juya tace da Fa'ee. “Muje!” Juyawa suka yi suka hau kwale-kwalen Lamu abokin Ekene dake jiransu tun ɗazu. Kuma shi ne ya fitar da su har bakin gaɓar yankin nasu. Bus ɗaya suka hau, kafin suka rabu a victoria island. Dan ita Fa'ee kamfanin da take aiki a can cikin victoria island ɗin yake. Cikin hanzari Diya ta faɗa kitchen tana ƙoƙarin saka apron ɗinta. Dan ta makara ba kaɗan ba. “Diya Shola!” Cak ta tsaya da ɗaura apron ɗin da take. Zuciyarta ta buga sau biyu a lokaci guda. Sakamakon jin muryar MD ta kira sunanta. Yawu ta haɗiye, sannan ta juya ta kalleshi a tsorace. Wannan mayen kallon da ya saba binta da shi yau ma shi yake jifanta da shi. Kanta ta sunkuyar ƙasa tana ƙara matse jikinta da drawern da suke aje apron ɗinsu ta aiki. MD ya lashi lips ɗinsa yana ci gaba da mata wani irin kallo. Kafin yace. “Ki zo office ɗina, ina son ganinki!” Da ƙyar ta iya gyaɗa kanta. Sai da ya kuma mata kallon sama da ƙasa, sannan ya juya ya bar wurin. Da ƙyar ta sauƙe wata ajiyar zuciya. Ƙara tsorata ta yi jin an kuma shigowa wurin. Amma sai ta ƙara sauke wata ajiyar zuciyar ganin Orisa ce, dan da farko ta yi tunani cewa shi ne ya dawo. “Me yace miki?” Orisa ta tambaya a sigar gulma tana ƙasa da muryarta. Diya ta ɗan kalleta kaɗan. “Wai na je na sameshi a office” Ta faɗi muryarta na karkarwa. Kamar me shirin fashewa da kuka. Orisa ta dafe ƙirji tare da zaro ido. “Sai ki yi a hankali, tun da kin san halin mutumin nan, ba ɗan arziƙi ba ne” Tsoro ya ƙara kama Diya. Kamar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki haka ta shiga tafiya har ta kawo office ɗin nasa dake cikin restaurant ɗin. Sai da ta shaƙi iska ta furzar, sannan ta kai hannunta kan handle ta murɗa, sannan ta shiga da sallama a tsorace. Tsaye ta sameshi jikin fridge yana zuba juice a cikin wasu wine guda biyu. Tana shigowa ya zubo mata ƙwalƙwalan idanuwansa yana mata irin wannan kallon da ba ta so. Kanta ta sunkuyar ƙasa a sanda ta ga yana tunkarota. A gabanta ya tsaya ya mika mata wine guda daya. “Karɓi ki sha Baby!” Wata ƙararrawa Shola ta ji sunan ya doka a cikin kanta. Ba shiri ta zazzaro idanuwanta tana kallonsa. Ido ɗaya ya kashe mata, sannan ya ƙara miƙa mata wine ɗin. Kasa karɓa ta yi, sai ƙwalla da ta fara silalo mata. Ba tare da ta ankara ba ya kamo hannunta ya danƙa mata wine ɗin. Ta ƙara ruɗewa, hannunta ya shiga karkarwa, har wine ɗin ya suɓuce ba tare da ta sani ba. Kuma ƙarar tarwatsewarsa ce ta dawo da ita hayyacinta. Kusan a tare ita da shi suka kalli fasasshen wine ɗin dake ƙasa, wanda juice ɗin ciki ya zube a kan lallausan carpet ɗin dake ƙasan. “Ba komai Baby! Za a zo a tsaftace, amma kafin nan, akwai maganar da nake so mu yi!” Ta ƙara tsorata tana ja da baya. Kallonta ya shiga yi cike da mamaki. Ganin tana niyyar ficewa ya sa shi yin saurin cafko hannunta ya dawo da ita gabansa. Tazarar dake tsakaninsu kaɗan ce, dan hatta da fitar numfashinsa tana ji a kan fuskarta. Idonta ta rintse da sauri tana jan numfashi da ƙyar. “Babu inda za ki iya guduwa Baby, na san da cewa kin san me cece manufata a kanki, zai fi miki kyau ki bani haɗin kai, komai ya tafi cikin ruwan sanyi. Ina me tabbatar miki da idan hakan ta faru sai kin fi kowa jin daɗi, domin zan wadataki da kuɗaɗen da baki taɓa riƙe kalarsu a rayuwarki ba, amma kuma idan kika ƙi, zan koriki daga aiki, sannan zan tabbatar da baki ƙara samun wani aikin a cikin garin Lagos ba!” Ya ƙarashe yana sakinta. Da gudu Diya ta juya ta fice daga office ɗin, kuma ba ta tsaya a ko ina ba sai toilet. Ta shiga ciki ta kulle ƙofarsa tana sakin kuka me sauti. Ina za ta sa rayuwarta? Me ya sa wasu mutanen basu da imani? Yanzu ita menene laifinta dan tana neman abun da zata rufawa ahalinta asiri?. Ba zata iya amincewa da ƙudirinsa ba, kuma ba zata so ya koreta daga aiki ba, dan idan har ya koreta ba ta san inda za ta samo wani aikin ba, wannan ɗin ma sai da aka kai ruwa rana sannan ta sameshi. Kuma ga shi yana faɗa mata cewar zai tabbatar da bata samu wani aikin ba. Ko dan magungunan Papi da suke da tsada da kuma abincin da zasu riƙa kaiwa bakin salati dole ta yi aiki. To yanzu ina za ta sa ranta idan aka koreta?. Silalewa ta yi ta zauna a kan wata kujera dake cikin bayin. Kafin ta kai hannu ƙafarta ta dama, ta ciro ankle bracelet ɗin dake kafar tata, ta riƙeshi a hannunta tana gani. Tun tasowarta abun yake tare da ita, kuma a duk sanda za ta tambayi Gigi na waye?, Sai Gigin tace mata nata ne, kuma abun yana da matuƙar muhimanci a gareta. *Cactus Restaurant, No. 20 Ozumba Mbadiwe Abe, Victoria Island, Lagos, Nigeria.* SURAJ POV. Zaune suke shi da Narjis a kan kyawawan kujerun dake wajen Restaurant ɗin. Yayin da suke zaɓar abincin da za a kawo musu. “Wallahi Hamma abincin nan wurin yana da daɗi, dan baka taɓa ci ba ne!” Cewar Narjis ɗin tana ƙarewa kyakkyawan Restaurant ɗin kallo, bayan da suka gama zaɓar abun da suke buƙata. Suraj ya ɗan taɓe bakinsa yana jingina da jikin kujerar da yake kai. “Haka kika ce dai!” Ya faɗi yana kallon fitilun wurin da suka ƙara ƙawata wurin cikin duhun magaribar da ya fara shiga. Ga kuma daddaɗar iskar kogin dake bugawa zuwa cikin Restaurant ɗin, kasancewar daga gefen Restaurant ɗin akwai wani kogi. “Wallahi da gaske nake maka, bari su kawo mana ka ji” Kansa ya jinjina yana kallon agogon hannunsa. Shi ba dan ma ta takura tace sai ya tsaya sun shigo ba da ba shigowa zai yi ba, suna tafe a mota za su koma gida bayan da suka dawo daga National theatre, ta ce ya tsaya su ci abinci sai su wuce, shi ne fa suka tsaya ɗin. Abincin aka kawo musu, kuma bayan sun ci suka kwashi kayansu dan su koma gida, kasancewar har magariba ta yi. Ko da suka fito motar Suraj ɗin suka nufa, inda Narjis ta shiga wurin me zaman banza, yayin da shi kuma yake ƙoƙarin buɗe driver seat, idonsa ya kai kanta, tana fitowa daga wata ƙofa. Cak ya tsaya daga shirin buɗe ƙofar da yake, ya tsaya a wurin yana ci gaba da kallonta. Sanye take cikin kayan da ya ga waiters ɗin wurin na sakawa. Fitulun dake parking lot ɗin ne suka haske masa fuskarta dau. Zai iya cewa yau ma yanayin fuskar tata irin na ranar da ya fara ganinta ne, dan fuskar tata a kumbere take, kamar wadda ta yi kuka, haka kuma babu walwala ko kaɗan a tare da fuskar tata. “Hamma shigo mu tafi mana, dare na yi fa...” Narjis ta faɗa tana dubansa, ganin kamar ba shi da niyyar shigowa motar. Juyowa ya yi ya kalleta. “Narjis kin ganta can!” Narjis ta kalli inda yake nuna mata tana faɗin. “Wa kenan?” “Yarinyar mana” Ya bata amsa yana rufe ƙofar motar. Kuma kai tsaye Narjis ta fahimci wata yarinya yake magana a kai. “To ka je ka mata magana mana” “Allah ko?” Ya tambaya kamar wani soko, dan shi a irin waɗanan harkokin za a iya kiransa da sokon. “Eh mana, wata ƙila gida za ta je, ka ga sai mu rage mata hanya. Ko ta ce maka no ka tabbatar ka sata tace yes” Kansa ya gyaɗa yana nufar inda take, dan zuwa lokacin har ta kai gate. Da sauri ya bi bayanta ya na faɗin. “Barka dai!” Diya ta tsaya da tafiyar da take, kuma a hankali ta juyo ta dubeshi, nan take ta ɗan yi wani guntun murmushi. “Yallaɓai Suraj” Ta faɗi sunan nasa tana kallonsa, to ya ma za ayi ta manta da sunan wannan bawan Allahn da ya temaketa sosai. “A'a Suraj dai” Kanta ta sunkuyar tana faɗin. “An ya kuwa zan iya faɗa?” Goshinsa ya tattare cikin alamun kokwanto. “Me ya sa?... Ai yanzu ba na sanye da kayan 'yan sanda” Sai ta ɗan yi murmushin da ba ta yi irinsa ba yau, saboda tun zuwanta MD ya ɓata mata ranarta ta yau, sai ta gyaɗa kanta. “Haka ne” “Gida za ki je?” Ta ɗago da kanta tana amsa shi da. “Eh, lokacin tashina ne ya yi” “Idan ba damuwa sai mu je na sauƙeki” Ta yi saurin girgiza kanta. “A'a Wallahi! Da ka barshi ma” Shi ma nasa kan ya girgiza mata. “Ka da ki damu, tare nake da ƙanwata, mu je sai mu sauƙeki Please!” Ta yi shiru tana jinjina kirki irin na Yallaɓai Suraj, kafin ta gyaɗa kanta, hanya ya nuna mata yana faɗin. “Za mu iya tafiya?” Ta dan yi murmushi sannan ta fara tafiya, yayin da shi yake take mata baya. Ko da suka iso wurin da motar take sai ya ga Narjis har ta fito ta koma gidan baya. Ko da ya kalleta sai ta kanne masa ido ɗaya, murmushi ya mata yana buɗewa Diya ƙofar motar ta gidan gaba. Diya na ta mamaki ta shiga motar. “Barka da yamma Anti!” Diya ta juya baya ta kalli wadda ke gaisheta, ya ce tare yake da ƙanwarsa, kenan wannan ita ce ƙanwar tasa, da ɗan guntun murmushi a fuskarta tace. “Sunana Diya Shola” Narjis ta gyaɗa kanta. “Wannan ita ce ƙanwata Narjis” Cewar Suraj yana rufe ƙofar motar bayan da ya shigo, Diya ta gyaɗa kanta. “Na ji daɗin haɗuwa da ke Narjis” “Ni ma haka Diya” Daga haka kuma babu wanda ya sake cewa komai har suka kai Makoko, zuwa lokacin duhun magariba ya gama mamaye ko ina, yayin da cikin garin Lagos ya yi kyau da kyawawan fitilun da aka kunna na manya-manyan ginninnikan da suka ƙara ƙawata birnin. “Na gode sosai Yallaɓai Suraj” Cewar Diya da ta fito daga motar. “Nop I'm Suraj” Ta dan yi murmushi. Kafin ta yi wa Narjis Sallama ta juya ta nufi cikin yankinsu. Narjis ta dawo gidan gaba tana faɗin. “To muje gida, na san yau Mummy sai ta yi bandarmu, mun jima Wallahi!” Suraj ya yi murmushi. “Ya kika ganta?” Ya tambaya yana wa motar key. Narjis ta yi murmushi. “Tana da kyau sosai, ni da farko na ɗauka bafulatana ce, sai da ta faɗa min sunanta na ji cewar bayerabiya ce” “Menene sunan nata?” Ya tambaya, dan shi bai ji sanda ta faɗi suna nata ba. “Diya Shola!” TAUQEER POV. Zaune yake a cikin motarsa, yayin da tayoyin motar ke tafiya a hankali a kan titi. Fuskarsa kawai idan ka kalla za ka san cewa a gajiye yake. Dan yau ya sha aiki sosai. Wayarsa dake aje a gefe ce ta ɗau ruri, ganin lambar RAM ce ya sa shi ɗagawa da sauri, dan tun ɗazu yake jiran kiran Rafeeq ɗin. “Hello Agha!” “Na'am Ram, ka gano inda yake?” Daga ɗayan ɓangare Rafeeq yace. “Eh, yana ɗaki me lamba 34, Maroko Bayshore!” Tauqeer ya rintse idonsa zuciyarsa na masa ɗaci. Sannan ya buɗe idon nasa yana ci gaba da tuƙa motar da hannu ɗaya. “Na gode Rafeeq, ka gaida Maa” Ya faɗi da ƙyar. “Dan Allah ka bi komai a hankali Agha” “I will insha'Allah!” “Ok ka kula da kanka, kuma ka gida su Umma” Ba tare da ya ce komai ba, ya katse kiran, sannan ya lalubo lambar Saif. “Saif kana gida?” Daga ɗayan ɓangaren Saif yace. “Eh ina gida, ban jima da dawowa daga barrack ba” “Ka sameni a Maroko Bayshore yanzu!” *Room No. 34, Maroko Bayshore Hotel, V.I, Lagos, Nigeria.* Wani matashi ne zaune a kan gadon dake ɗakin, jikinsa sanye da 3qrt me ɗauke da kakin sojoji, sai baƙar T-shirt wadda ta kama jikinsa. A hankali yake furzar da hayaƙin sigarin da yake zuƙa. Idanuwansa a lumshe. Ƙofar banɗakin dake cikin ɗakin ce ta buɗe, wata farar budurwa ta fito daga ciki tana tsane gashin kanta. Idonsa ya buɗe a hankali ya kalleta. Sanye take cikin orange skort trouser, da farar tube top. “Babe ya kamata na tafi fa” A hankali ya ciro karan sigarin dake bakinsa, ya gyaɗa kansa, sannan ya miƙa hannunsa setin side drawer, inda wallet ɗinsa ke aje. Buɗeta ya yi ya zaro kuɗaɗen da shi kansa bai san adadinsu ba, ya miƙa mata. Sai da ta masa wani farr da ido, sannan ta tako zuwa gareshi tana murmushinta na yaudara, ta sa hannu ta karɓi kuɗin tana jujjuyasu. Sunkuyawa ta yi setin fuskarsa ta sumbaci kuncinsa na dama sannan tace. “Na gode Babe, sai yaushe kuma?” Hannunsa ya sa ya cire nata dake taɓa wuyan rigarsa. “Zuwa gobe ki dawo” Murmushi ta kuma yi, sannan ta ɗauki jakarta ta masa sallama ta fita. Kwalbar giyar dake gefe ya ɗauka, ya kafa a bakinsa yana sha. Tauqeer da Saif wanda isowarsa kenan suka hawo hawa na ɗaya dake hotel ɗin, dan an sanar musu da cewar ɗaki me lamba 34 yana hawa na ɗaya. Idan ka kalli idon Tauqeer babu abun da za ka gani a ciki sai tashin hankali, Saif kuwa duk alhini ne ya mamaye fuskarsa. Duk da yanda mutane ke ta kallon Tauqeer ɗin bai damu ba, sai da Saif ya tuna masa ne ma ya sa ya fara rufe fuskarsa dan kada a ga halin da yake ciki. A sanda suka shawo kwanar da ɗakunan suke, suka ga wata budurwa ta fito daga ɗaki me lamba 34. Tauqeer ya haɗiye yawu da ƙarfi, dan bisa ga dukanin alamu ita ce budurwar ƙanin nasa, ko ma de ya kirata da karuwar ƙaninsa, ji ya yi zuciyarsa na wani irin tuƙuƙi. Kamar wanda aka zabura ya ƙara saurin tafiyarsa. Haka suka wuce yarinyar tana lissafa kuɗin dake hannunta, ko ta kanta ba su bi ba, dan ba ita ce matsalarsu ba. Tauqeer ne ya buɗe ƙofar ɗakin da ƙarfi, kuma abun da ya yi arba da shi shi ne ya sa ya ji kamar zai zame ya faɗi ƙasa. Ƙaninsa ne zaune a kan gadon ɗakin hotel yana shan giya!. Ganin kamar zai faɗi ƙasa ne ya sa Saif ya yi hanzarin riƙoshi. “Haba Tauqeer ka kula mana!” Maganar Saif ɗin ita ce ta dawo da hankalin Jamal kansu. Da sauri ya mike yana sakin kwalbar giyar dake hannunsa. Kallonsu yake ido waje. Kansa ya soma girgizawa a sanda Tauqeer ya soma takowa cikin ɗakin. Tauqeer da idonsa ya yi jajir ya kamo hannun ƙaninsa. “Zo mu tafi gida Jamal” Ya faɗa kamar wasu ƙananun yaran da suka tsaya wasa a gefen hanya. Jamal ya girgiza masa kai. “No Tauqeer ba zan iya komawa gidan nan ba” Tauqeer ya dubeshi yana jin kamar ya fasa ihu. “Me ya sa?” Ya tambaya. “Saboda bana son rayuwar gidan. A duk sanda zan sa ƙafata a gidan sai naji na tsani kaina, ji nake kamar na kashe kaina na huta Hamma!” Ya ƙarashe ƙwalla na fita daga idonsa. Tauqeer ya lashi lips ɗinsa da suka bushe, hannayensa biyu dafe da ƙugunsa. Wace iriyar jarabawa ce wannan?. “I understand that you have a strong negative reaction to that house. It sounds like being there is causing you a lot of distress. I know it's not easy to deal with those feelings. I'm here to listen and support you however I can. You're not alone” Ya faɗi a ƙoƙarinsa na tausar ƙaninsa, dan yana ganin kamar lamarin na Jamal ba lafiya ba. A da Jamal ba shi da wani wurin zuwa da ya wuce wurin aikinsa wato barrack, daga barrack kuwa sai zaman gida, kullum yana maƙale da Umma, kuma hakan da yake ne ma ya sa suke kiransa da Mama's boy. Jamal ya zauna a bakin gadon yana dafe kansa tare da fashewa da kuka. Saif ne ya ƙaraso kusa da shi ya zauna yana dafa kafaɗarsa. “Ƙwarai kuwa Jamal ni da Tauqeer duka muna tare da kai” “I dislike that house Saif...” “To a ganinka wannan rayuwar da ka ɗaukawa kanka ta yi dai-dai? Saboda kawai baka san gidanku sai ka ɗauki wannan rayuwar?” Saif ya tambaya, ba tare da ya amsa shi ba ya ci gaba da kukansa. Kafin kuma numfashinsa ya fara sama. Ɗif kukan nasa ya ɗauke tare da numfashinsa. Hankali tashe Tauqeer ya shiga kiran sunansa. Saif da ya taɓa jijiyar hannunsa da ta wuyansa yace masa. “Ba mutuwa ya yi ba, damuwa ce ta masa yawa, mu ɗaukeshi muje gida kawai” Kansa ya gyaɗa yana cicciɓar Jamal ɗin da kansa. *Agha Mansion, Lekki phase 1, Lagos, Nigeria.* *Da misalin 09:40 na dare.* “Wai ni ina Saif ne?” Taj ya tambayi sauran 'yan uwansa, yayin da yake jan kujerar daninng. Mama da bakinta ke ƙaiƙayi wurin furta labarin da take ta dakonsa tun bayan fitar Saif ta dubeshi tace. “Junior ne ya kirashi ɗazu yana dawowa, shi ne ya fita” “Junior kuma? Wai shi ma bai dawo ba?” Abba ya tambaya yana duba agogon dake a sashin katafaren danning area ɗin gidan. Umma dake zuba masa abinci tace. “Ɗazu da na kirashi yace min yana hanyar dawowa gida, ban san me ya sa bai dawo ba kuma” Jin ana danna door bell ne ya katse maganar. “Aliya! Aliya!” Umma ta ƙwalawa Aliya kira tana zama a kusa da mijinta. “Gani Madam” Cewar Aliyan tana risina mata. “Ana danna door bell, je ki duba waye” “Ok Madam” Ta faɗi cikin girmamawa tana nufar hanyar da ƙofar gidan take. Deena dake zaune a kan danning ɗin ita ma ta wurga mata harara. Tun kafin ta kai bakin ƙofar aka buɗo ƙofar, Tauqeer ya shigo, kafaɗarsa ta dama ɗauke da Jamal, Saif kuma na biye da shi. * A hankali ya kwantar da ƙanin nasa a kan gadon dake ɗakinsa. Blanket ɗin dake kan gadon ya janyo, sannan ya rufeshi da shi. Kallon fuskarsa ya ci gaba da yi yana nazarinta. Kamar me son gano halin da yake ciki. Jin sauƙar hannun Abba a kafaɗarsa ne yasa shi sauƙe ajiyar zuciya. Miƙewa ya yi a hankali, sannan ya juya suka fuskanci juna shi da Abban. “A ina kuka samoshi?” Abba ya tambaya yana kallon fuskar Jamal. Shi ma Tauqeer ɗin kallonsa ya yi. “A Maroko Bayshore!” Abba ya dubeshi. “Tun satin da ya wuce na yanke shawarar kaishi Rehab... Na yi shiru ne kawai dan Ummanku” Tauqeer ya dube shi. “Rehab kuma Habiby?” Abba ya gyaɗa kansa. “Ka sani kuma ni ma na sani Junior. Duka waɗanan abubuwan da Jamal ke yi ba yin kansa ba ne, dole da akwai wani abu a ƙasa. Sau nawa yake mana alƙawarin ya dena aikata komai. Ya taɓa denawar ne?” Tauqeer ya girgiza kansa. “A'a Habiby ba ya denawa” “To shi ya sa nake son kaishi can ɗin, ko ba komai idan yana can akwai tsaron da ba zai barshi ya aikata waɗanan abubuwan ba, bayan wasu wattani sai ya dawo gida” “Amma Habiby kana ganin cewa Habibty Za ta yarda?” Abba ya sauƙe numfashi yana haɗe hannyensa waje guda. “Wannan shi ne abun da ya dakatar da ni daga zartar da hukuncin da na yanke... Ban san wani irin hali za ta shiga ba” Tauqeer ya ɗaga kansa sama, wuyansa da kafaɗarsabda ya ɗauko Jamal a kai na masa ciwo. “Shi kenan. Yanzu ka je ka huta, ka samu abinci ka ci, na san a gajiye kake” Kansa ya gyaɗa yana sauke shi ƙasa, kafin ya kalli fuskar Jamal. “Ka da ka damu da shi, zan kula da shi har sanda zai farka, ka je kawai!” Abba ya faɗa. Tauqeer ya gyaɗa masa kai. “Sai da safe” “Ka tashi lafiya Habiby” Ya faɗi yana juyawa. A bakin ƙofar ɗakin Jamal ɗin ya haɗu da Hajiya. “Tsohuwa ina zuwa?” Ya tambaya cikin zolaya, duk da ba ya cikin irin yanayin. Hajiya ta ci gaba da leƙa ƙofar ɗakin Jamal ɗin kamar wadda aka cewa Jamal na tsaye a bayan ƙofar. “Tsohuwa magana fa nake!” Ya faɗa a ƙoƙarinsa na dawo da hankalinta kansa. “Na'am tsoho ya jikin Jamalun?” Ta tambaya kamar wadda ta dawo daga duniyar tunani. Kallonta ya ci gaba da yi, kafin yace. “Bacci fa yake tsohowa, kada ki tada hankalinki mana!” Kanta ta girgiza. “Bari tsoho, lamarin na Jamalu sai dai addu'a” “Shi ne abun da ya kamata ki masa, dan Allah kar ki saka kanki a damuwa” Kanta ta gyaɗa. “Bari na shiga na duba shi to” Ya matsa mata ta shiga cikin ɗakin. Kuma bai bar ƙofar ɗakin ba Abby ya zo. Shi ma tambayoyi ya masa kan inda suka samoshi, sannan ya shiga ɗakin Jamal ɗin. Me makon ya nufi ɗakinsa, sai ya nufi ɗakin Umma, dan a yadda ya ga yanayinta sanda ya shigo gidan da Jamal ya san yanzu tana ɗakinta tana kuka. Umma na zaune a bakin gadon ɗakinta tana kuka, wayarta kare a kunnenta tana faɗawa yayarta Halima halin da take ciki. “Ni fa ba na ganin lefin kowa bayan naki Maryam. Tun yaushe nake faɗa miki cewar akwai wani a bayan lalacewar Jamal? Amma kika ƙi yarda, daga ƙarshe ma sai kika ce wai ke baki da maƙiyin da zai iya miki haka... Shi yanzu Jamal an lalata masa rayuwa, shi kuma Tauqeer za'a lalata masa rayuwa ta hanyar aura masa wannan balamar!” Umma ta dafe kanta. “Wallahi Anti Halima ni kaina bana son auren Tauqeer da Deena, amma ya zan yi, iyayensu maza sun nuna suna son haɗin, kuma shi ma Tauqeer ɗin da aka tambayeshi amincewa ya yi, kin ga kuwa babu abun da zan iya a kai” “Ai sai ki yi ta zama a haka, kina ji kina gani a sabauta miki rayuwar yara!” “Zan iya shigowa?” Muryar Tauqeer ta tambaya daga bakin ƙofar ɗakin, Sallama ta yi da yayar tata, ta goge hawayenta, sannan tace. “Shigo!” Shigowar ya yi, memakon ya ƙaraso cikin ɗakin, sai ya tsaya a jikin ƙofar yana kallonta. Yayin da ita kuma ta ƙi yarda su haɗa ido. Cikin ɗakin ya shigo, sannan ya zauna a kusa da ita yana kamo hannyenta. “Habibty!” Da ƙyar ta iya kallon fuskarsa. Ƙwalla na cika idonta. “Jamal fa na cikin ƙoshin lafiya” Ba tare da ta sani ba wani kuka me ƙarfi ya kufce mata, ta kwantar da kanta a kafaɗarsa tana ci gaba da kukan nata. Kanta ya shafa yana faɗin. “Dan Allah ki kwantar min da hankalinki Habibty, ba na son kina kuka irin haka, ni da Iqra da Aabis da kuma Habiby hankalinmu zai iya tashi” Shiru ta yi, amma ba ta dena hawaye ba, ɗagota ya yi daga jikinsa, sannan ya ƙara kama hannunta. “Habibty mun yi magana da Habiby a kan za'a kai Jamal Rehabilitation center!” Ya yi shiru yana kalon reaction ɗinta. Kallosa kawai ta ci gaba da yi, ta kasa furta komai. “Ba na son ki yi wani mummunan tunani Habibty, za'a tabbatar da yana cikin ƙoshin lafiya, sannan na miki alƙawarin babu wani abun cutarwa da zai sameshi a can ɗin. Kuma a yadda Habiby ya faɗamin za'a kaishi ne domin a ya dena wannan halayen da yake yi” Ba ta ce komai ba, saboda zuciyarta dake mata zullo, dan ji take kamar za ta fashe lokaci guda. Hanci ta ja tana goge ƙwallar da ta ƙi tsaya mata. “Na amince Junior. Ku kaishi can ɗin, in dai har kuna da tabbacin zai dena abubuwan da yake!” Rungumeta ya yi, ganin tana shirin sake fashewa da wani kukan. “Insha'Allah Jamal zai dena komai, zai dawo Mama's boy ɗinsa kamar da... Yanzu dai ki dena wannan kukan” Ya faɗi yana ɗagowa da kanta. Tare da share mata ƙwallar. “Habibty an ya Habiby ya taɓa faɗa miki cewar idan kina kuka muni kike...” Ya ƙarashe yana yamutsa fuska, ta yadda dole sai da ya sata dariya cikin kuka, ta ɗan daki damtsen hannunsa. “Ki dena kukan ba ya miki kyau” Ta yi murmushi tana goge ƙwallar, dan kaso sittin na damuwarta ya ɓace. Kuma hakan ya sa a ko da yaushe Tauqeer yake a sahun na biyu a cikin ranta. Saboda Jamal shi ne kan gaba, dan ta fi kowa kusanci da shi. “Kar ka so ka ga yanda Abbanku yake shiga damuwa a duk sanda zan yi kuka, sanda ina budurwa babu kalar wahalar da ban bashi ba. Ko ka san sanda ina da cikinka tsakar dare nake tashinsa na ce ya fita ya nemo min muruci?!” Ya ƙyaƙyale da dariya, ita ma ta shiga tayashi tana tuno zamanta da mijinta a shekarun baya. “Ki ce shi ya sa na zama dogo!?” Suka kuma yin dariya. “Har yanzu ma yana damuwa da kukanki” “Zan iya shigowa” Iqra dake tsaye a bakin ƙofa, hannunta riƙe da tray ta faɗi. A tare suka dubeta. Tauqeer ne ya mata alama da ta shigo. “Wai baki ci abinci ba?” Ya tambaya a sanda Iqran ta dire trayn dake hannunta. Umma ta sunkuyar da kai tana motsa yatsunta. “Ta zauna za ta ci abincin kuka shigo, shi ne ba ta ci ba, ta dawo ɗaki ta zauna tana kuka” Iqra ta bashi amsa tana zuba mata abincin. “Ya kamata ki ci abinci, ni zan je na ɗan watsa ruwa” Ya fadi yana miƙewa. “Kai ma ai baka ci abincin ba. Iqra ki je ki kai masa abinci...” Ta ƙarashe tana duban Iqra. “A'a Umma, ba yanzu ba, sai na fara zuwa na yi wanka tukkuna, idan na yi wanka zan kiraki, sai ki kawo min” “Ok” Iqra ta amsa tana zama kusa da Umma. HAJIYA ZAYYA POV. Cike da farin ciki ta shiga ɗakinta ta zauna a kan sofa. Haƙiƙa yau tana cikin matsanancin farin ciki, dan na ɗaya daga cikin ɗabi'unta, shiga farin ciki yayin da ta saka wani baƙin ciki. Tana samun farin ciki daga ƙuncin wanda ta zama sanadiyyar shigarsa cikin halin damuwa. Babu abun da ya fi faranta mata rai kamar yanda Maryam ta koma ɗakinta tana kuka. Wayarta ta ɗauka, ta aikawa Dr. Bashir kira. “Barka da dare Hajiya!” Abun da ya faɗi kenan bayan ya amsa sallamarta. Cike da jin kai ta gyara zama. “Ina ajiyata?” “Ajiyarki tana nan, yau ma sai da aka mata allurai uku. Sannan muka samu ta suma” “Hmmm! Ya yi kyau, kana ji na ko? Ina so a haɗata da sauran masu taɓin hankali na asibitinku, a kuma ƙara saka mata matakan tsaro!” “Amma kuma ai tana da hankalinta Hajiya, har magana ma fa tana iya yi” Hajiya Zayya ta turɓune mummunar baƙar fuskarta cikin faɗin. “Ai na san cewa tana da hankalin. So nake ka sakata a cikinsu, ta yadda ita ma za ta haukace ɗin, ka yi abun da nace kawai, za ka ga saƙo ya shigo maka” Jiki na rawa ya amsa da. “To Hajiya!” Ta sauƙe wayar, ranta fes. _________________ _Me kuke ganin zai faru da tsakanin Diya da MD?_ _Me zai faru ifan Rahila ta koma cikin masu taɓin hankalin dakw wacxan asibiti?_ _Mu je zuwa!_ A. ISAH CE✍️. °°°°°°°°°°°°°°°° *💡HASKE...💡* *©SALMA AHMAD ISAH* TAURARI WRITER'S ASSOCIATION. *Page 09* ~~~ SALAME POV. Zaune suke a kan tabarma ita da Iya, yayin da takewa Iya Abun kitso. Inna kuma na daga madafa tana girkin dare, kasancewar me girkin tana kitso. Muja kuwa tun ɗazu da rana ya fita wasa wuri abokansa, Baba da Audu kuwa tun safe ba sa gidan, hakan ya sa daga ita sai Iya Abu sai kuma Inna. “Salamatu Candy uwar riga!” Ta kirata da sunan da ta saba mata waƙa da shi tun tana jaririya. “Na'am Iya!” Salame ta amsa tana duban saman goshin Iyan, dan bata iya ganin fuskarta gaba ɗaya. “Wai me kika shirya a auren nan ne?” Gabanta ya buga da ƙarfi ba tare da ta san dalilin bugwar ba. Yawu ta haɗiye, sannan ta sunkuyar da kai. Ganin Inna ma na kallonta, alamun dai ita ma ta ji tambayar, kuma su duka suna jiran amsarta ne. “Me... Me kuma zan shirya Iya, babu abun da zan shirya ai” Ta basu amsa kanta a ƙasa. Iya Abu ta juyo ta kalleta. “Salamatu ko ba kya son auren nan ne?. In de har ba kya so ba za mu taɓa miki auren dole ba!” Da sauri ta girgiza kanta ƙwalla ta rashin dalili ta silalo mata. “Wallahi Iya ba haka ba ne, kawai de... Kawai ina jin ba daɗi ne na rabuwar da zan yi da ku... Shi... Shi ne kawai!” Ta ƙarashe tana goge ƙwallar da ta sauƙo mata. Iya ta yi murmushi tana kamo hannunta. “Ka da ki damu Salamatu Candyna, ai rabuwar aure ba ta mutuwa ba ce, a garin nan fa za ku zauna, idan kin yi kewarmu za ki iya zuwa ki ganmu idan har mijinki ya barki!” Tunowa da ta yi da nan da wasu 'yan kwanakin zata rabu da su ne ya sa ta ƙara fashewa da kuka tana faɗawa jikin Iya. Iya Abu ta riƙeta tana lallshinta. Inna ta fakaici idonsu ta goge ƙwallarta. “Kada ki damu Salamatu, muna nan tare da ke!” Cewar Iya tana ci gaba da lallshinta. *No.675, 361 Stagg Street, Brooklyn, New York, USA.* * Da misalin 06:30 na safiya.* RAFEEQ POV. A hankali ya miƙe tsaye daga zaunen da yake. Hannunsa na dama riƙe da jar me ɗauke da hot chocolate. Idonsa manne da screen ɗin desktop ɗinsa dake kan desk. Jin jikinsa yake duka babu daɗi. Saboda sammakon da ya yi na fara yin aikin nasa. Ga kuma makarar da ya yi a daren jiya, dan bai kwanta da wuri ba. Ga kuma tarin ayyuka dake jiransa. Saboda abu biyu ne ya sako shi gaba, haɗa AI humanoid robot ɗinsa, da kuma haɗawa kamfanin motocin nan device ɗinsu. Sauƙinsa ɗaya, yana da matemaka, da bai san yanda zai yi da ayyukan ba. A jiya ne ma ya yanke shawarar aje haɗa humanoid robot ɗin nasa, idan ya kammalawa kamafanin motoci aikinsu sai ya ɗora daga inda ya tsaya. Bakinsa ya kai kan straw ɗin dake jikin jar ɗin, ya ɗan yi sipping kaɗan, kafin ya sauƙe da sauri yana kallon windown office ɗinsa. Ya kamata ya ɗan yi jogging. Wata ƙila jijiyoyin jikinsa su ɗan miƙe, kuma ko ba komai ya samu sabon tunani. Kuma ya kamata ya kirata su fita tare. Amma kuma ai shi ba shi da lambarta. Murmushi ya yi a sanda ya tuna da: _“Kamfanin ƙera kayan sawa na OP”_ Abu ne me sauƙi gareshi samun lambarta. Dan haka ya kuma yin murmushi, sannan ya nufi desktop ɗinsa, ya datsi na'urar kamfanin OP. Ta hanyar da ko su kamfanin kansu ba za su san an datsi na'urar tasu ba. Bayanan ma'aikatan dake aiki a kanfanin ya shiga dubawa. Kuma a ciki ya samo nata. ‘NADRA’ Shi ne kawai a rubuce, bayan shi kuma babu komai a gaba. Mamaki ya ɗan kamashi, amma kuma sai ya ture ya nemi lambarta. Ya kwafe a wayarsa da baya bawa muhimmanci. Sannan ya aika mata kira. NADRA POV. Kwance take a jikin sabon saurayin da ta yi a daren jiya, sanda ta je nightclub. Sigari suke sha a tare, idan ya zuƙa ya furzar, sai ya miƙa mata ita ma ta zuƙa ta furzar. Ainahin gaskiyarta kenan! Ainahin aikin da ya kawota New York kenan. Karuwanci ita ce sana'arta ta gaskiya, aikin kamfanin OP kuwa tana fakewa da shi ne domin kauda idon mutane a kanta, duk da nan ƙasar waje ne, duk rayuwar da za ta yi babu me saka mata ido. _“Ki iya takunki Nandra!”_ Waɗanan su ne kalaman mahaifiyarta gareta a ko da yaushe, a ko da yaushe LANTANA mahaifiyarta na nusar da ita hanyar samun kuɗi a hannun samari da mutuncinta. Tun da ita kyakyawa ce, kuma ta iya jan hankalin maza, shi ya sa mahaifiyar tata ta turota nan ƙasar waje, don ta samu kuɗaɗe masu yawa. Ainahin LANTANA mahaifiyar Nadra karuwa ce wadda ke zaune a garin Lagos. A sanda ta samu cikin Nadra babu yadda ba ta yi dan ta zubar da shi ba kamar sauran cikin da ta saba zubawa a harkar karuwancin nata. Amma cikin wani ikon Allah sai cikin ya ƙi zubewa. Hakan ya sa ta bar shi har zuwa lokacin da ta haifeshi. Kuma tun a lokacin da ta ɗora idonta a kan jaririyar tata ta yanke hukunci kafa jari da ita a sanda za ta girma. A lokacin da harkar karuwancin Lantana ya shahara sai ta bar garin Lagos ta dawo garin Suleja ta siyi wani gida ta fara kawalci. Ba wa 'yayan mutane ba kaɗai, har da 'yarta ta cikinta. Idan ka ga yanda Lantana da Nadra ke mu'amala sai ka ce ba 'ya da uwa ba ne, dan kamar yanda kowa yake kiranta da Lantana haka ita ma take kiranta da Lantana nan. Wayarta ƙirar iPhone 'yar ya yi ce ta hau ruri, ta miƙa hannunta ta ɗauka, kamar ba za ta ɗaga ba ganin baƙuwar lamba, sai kuma ta ɗaga. “Hello Nadra!” Abun da ya fara faɗi kenan, kuma tana jin muryarsa ta gane cewa shi ne. Da sauri ta miƙe zaune, sannan ta lalubo rigarta dake yashe a ƙasan gadon, ta saka kana ta sauƙa daga kan gadon, ta fita daga ɗakin, kuma har lokacin bata furta komai ba. Ram da ya fara tunanin ba za ta yi magana ba ya ji tace. “Black indian!?” Murmushi ya ɗan yi jin muryarta. Ya sosa wuyansa yana faɗin. “Eh ni ne... Zan je tattaki ne, shi ne na ce bari na faɗa miki idan za ki iya zuwa mu tafi” Sai da ta waiga ta kalli ƙofar ɗakinta, sannan ta gyaɗa kanta cikin faɗin. “Zan iya zuwa, bari na fito” Cike da farin ciki Rafeeq yace. “Ok, sai na ganki” Daga haka ya sauƙe wayar. Ɗakinta ta koma ta yi wanka, aannan ta sauya kaya. A lokacin saurayin nata me suna Liam ya dubeta yace. “Baby ina za ki je ne!” Kallonsa ta yi ta mudubi tana saka canvas a ƙafarta tace. “Zan je na dawo yanzu, ka kwanta ka yi baccinka ka ji?” “Ok sai kin dawo” Abun da ya faɗi kenan yana kara jan bargo. Ko da ta fita daga gidan a bakin ƙofar nasa gidan ta ganshi tsaye. Sanye yake cikin baƙin sweat pants. Da farar shirt wadda ya ɗorawa bakar hoodie a sama, kasancewar a gaba ɗaya rayuwar Rafeeq ba ya saka kaya ba tare da jacket ba, dan shi ba ma'abocin saka manyan kaya ba ne. Murmushi yake jifanta da shi, yayin da ita ma ta mayar nasa da martani tana tsayawa kusa da shi. “Mu je ba?” Ya faɗi yana nuna mata hanya. Kanta ta gyaɗa a sanda suka jera ita da shi suna tafiya. Sun zaga sosai a unguwar, kafin suka tsaya a wani coffee shop, ya siya mata ta sha ita ɗaya. Sun jima a wurin suna hira, kafin suka dawo gida, ita ta shiga gidanta, yayin da shi ma ya shiga nasa gidan, ransa cike fal da farin ciki. DEENA POV. Zaune suke a inda suka yi shooting yau ita da ƙawarta Bilkisu. Coffee suke sha, dan ba su jima da kammalla shooting ɗin sabon film ɗin Deenan na yau ba. “Mommy ta ce min aure tsakanina da Tauqeer shi ne abun da zai sa na mallakeshi a hannuna... Amma ni ban aminta da hakan ba” Deena ta faɗa tana kallon mug ɗin dake hannunta. Bilkisu ta kalleta tana kurɓar coffee ɗinta. “Ai Mommy tana da gaskiya Deena, aure tsakaninki da Tauqeer shi ne zai sa ki mallakeshi na har abada!” Deena ta girgiza kanta. “A'a Bilkees, a halin yanzu ba na jin zan iya auren Tauqeer. Saboda har zuwa yau bana jin Tauqeer yana sona kamar yanda nake sonsa. Ƙwarai na san ina sonsa, kuma na kan nuna masa hakan a aikace, amma to me ya sa shi ba ya ganin wannan son?” “Wannan kuma laifinki ne Deena, ta ya za ayi ace kina da sauri, amma ba kwa yin wata wayar soyyaya, irin ɗan fita yawon nan ma na masoya ba kwa yi, hirar masoya ba ta haɗaku, kin ga kuwa ai dole ba za'a samu shaƙuwa tsakaninku ba” “Bilkees Tauqeer fa ba ya kirana kwata-kwata, rabon da na ga kiran Tauqeer ya shigo wayata har na manta. A ganinki ni ce zan kirashi? Hmmm jin kaina ba zai sa na yi hakan ba. Bilkees ina da matsayi me girma, kuma ina son a riƙa ba ni girmana. Tauqeer ba ya yin hakan, so kike na riƙa binsa ina neman ya soni?” Bilkees ta girgiza kanta tana murmushi. “Deena look. Tun farko ke ce kike son Tauqeer. Kuma sai da kika kawo zancen aurenku tukkuna ya amince. To me zai hana ki sauƙe jin kanki, ki bi shi sau da ƙafa ki gani idan bai soki ba” Murmushi ta yi tana aje mug ɗin hannunta. “Ba ki san Tauqeer ba ne Bilkees, Tauqeer yana da taurin kai fiye da zatonki. A da yace ya dena soyyaya soboda wata budurwa ta taɓa yaudararsa sanda suna University. Ko amincewarsa da auren nawa ya bani mamaki. Ban san ya aka yi ya amince ba. Da farko na ɗauka cewar har zuciyarsa ya amince ɗin, sai daga baya na gane cewar ba haka ba ne. Mts lamarin Tauqeer sai a hankali Bilkees” “Kin ga, ki kirashi ki ce ya zo ya ɗaukeki a nan, motarki ta lalace, idan kuna tafiya a hanya sai ki ce kina jin yunwa, ya tsaya ku ci abinci, a wurin cin abincin za ki faɗa masa cewar zuwa yanzu ya kamata ku yi aure” Deena ta kawar da kanta tana kalon crew ɗin dake aikin tattara kayan aikin da aka yi amfani da su wurin yin aikin shooting ɗin, ta girgiza kanta. “Wai ba ki ji me na ce ba ne? Ba na shirin yin aure yanzu” “To sai ki zuba ido, kina ji kina gani wata ta zo ta ƙwace shi!” Da sauri ta dubeta tana haɗe rai. “Me kike nufi?” “Idan har baki maida hankali kun yi aure da Tauqeer ba, to kina ji kina gani zai fara soyyaya da wata, har su yi aure ba tare da ke kin iya taɓuka komai ba!” Deena ta yi shiru tana hango rashin yiwuwar hakan. Tauqeer ya auri wata ba ita ba?. Ai wannan gaibu ne Wallahi, matsawar tana da rai ba za ta taɓa barin hakan ta faru ba. Tana wannan tunanin ne ba tare da sanin ƙaddarar dake shirin faruwa cikin wasu 'yan kwanaki ƙalilan ba. Wata kalar ƙaddara da za ta zo da HASKE. Wanda zai HASKA ko ina a cikin Agha Mansion, har ya kaisu ga ganin tarin abubuwan da suke ɓoye a cikin duhu. *Agha Studio, No. 86, Orchird road, Lagos, Nigeria.* TAUQEER POV. “Gaskiya Asad ya kamata a ƙara kiɗan piano a kai!” Cewarsa yana daga zaune a kan kujera, yayin da Asad ke zaune a gefensa, hannunsa riƙe da rubutacciyar waƙar da Tauqeer ɗin zai saki. Daga can jikin kayan kiɗan studio ɗin kuma, DJ Odunola ne ke zaune, bayan da ya haɗa kunna musu kiɗan da ya kamata a ɗora da waƙar. “A'a beats ya kamata a ɗora ba piano ba” Asad ya faɗa yana jinjina kai. “Idan ka duba waƙar za ka ga ba ta buƙatar beats a kiɗanta, wurin zai fi kyau idan aka ƙara ko da busar sarewa ne!” Cewar Odunola. “To tun da haka ne, me zai hana mu ƙara sautin guitar a kai?” Faɗin Tauqeer. “Ƙwarai kuwa guitar sait ta fi hawa... A saka kiɗan guiter ɗin kawai” Faɗin Odunola. “Asad bani guitar ɗin nan!” Asad ya miƙe ya nufi inda instrument ɗin studio ɗin suke, memakon ya ɗauko guitar kamar yadda Tauqeer ya buƙata, sai ya ɗauko piano keyboard. “Asad! Guitar! Guitar ba piano keyboard ba” Tauqeer ya faɗi a ƙoƙarinsa na tuna masa. “Oh sorry. Guitar” Ya faɗi yana juyawa, ya aje piano keyboard ɗin, sannan ya ɗauko guitar da ake buƙata. Tauqeer ne ya karɓa ya shiga kaɗawa suna shawarar yanda ya kamata ace kiɗan ya tafi. “The sun may set, the moon may rise,The seasons change, before our eyes. But through it all, our love will stay, A constant truth, from night to day. The years will pass, our love won't fade, A flame that burns, it won't be swayed. Our hearts are one, our souls as one, A love so true, our story's done...” Rera waƙar ta dakata tare da kiɗan guitar da kuma wanda ke tashi ta cikin sifikun studio ɗin. Saboda wayar Tauqeer ɗin da ta shiga ruri. Guitar ɗin ya aje yana kallon screen ɗin wayar. ‘DEENA’ Abun da sunan me kiran ya nuna kenan. Fuska ya yamutsa yana miƙa hannunsa tare da ɗaukar wayar. “Hello!” Ya faɗi yana miƙewa tsaye, tare da fita daga cikin studio ɗin, ya nufi office ɗinsa. “Am hello Junior!” Muryar Deena ta faɗi daga ɗayan ɓangaren. Ƙofar office ɗinsa ya buɗe yana shiga, sannan yace. “Na'am” “Na je shooting ne, sai motata ta lalace, shi ne na ce idan ba damuwa za ka iya zuwa ka ɗaukeni?” Agogon dake ɗaure a tsintsiyar hannunsa ya duba yana faɗin. “A halin yanzu dai akwai abun da nake, bari na turo ko Hammad ne ya zo ya ɗaukeki!” Da sauri ta girgiza kanta tana faɗin. “Da ace za ka zo da kanka da sai na fi jin daɗi, dan Allah ka zo!” Sai ya yi shiru yana sauraronta, kamar me shawarar kada ya je ɗaukan nata. “Dan Allah Tauqeer!” Ta marairaice murya. “Ok gani nan zuwa” *Cactus Restaurant, No. 20 Ozumba Mbadiwe Abe, Victoria Island, Lagos, Nigeria.* A tare suka shigo restaurant ɗin, Deena sai faɗi take ita yunwa take ji. Tun bayan da ya bar studio ɗaukarta ya je. Kuma bayan ya ɗaukota suna tafiya a mota tace tana jin yunwa dan Allah ya tsaya su ci abinci a Cactus Restaurant. Ba haka ya so ba, dan de kawai ta nuna tana so ne. “Na gaji sosai yau!” Ta faɗi tana jan kujer, tare da zama, shi ma zaman ya yi yana kallon yanda hankalin mutane ya dawo kansu, dan ya san cewa ba shi kaɗai ake kallo ba, har da Deena. “Barka Tauqeer Agha!” Muryar wata budurwa ta faɗi a kansu, kallonsu suka yi a tare, su biyu ne tsaye a wurin suna ta jifan Tauqeer da murmushi. Shi ma murmushin ya musu. “Ko za mu iya ɗaukar hoto?” “Why not” Ya faɗi yana miƙewa. Deena da ta cika ta yi fam, ta bisu da kallo tana jin kmar ta shaƙesu ta hut. A tsakiya suka sashi, sannan suka ɗauki hoton selfie. “Mun gode” Suka faɗi a tare suna barin wurin. Kujerarsa ya ja ya zauna yana murmushi. Idonsa ne ya kai kan Deena dake cika tana batsewa. “Menene?” Ya tambaya cikin halin ko in kula, dan shi bai ga aibun hoton da suka yi da 'yan matan ba. Su fans ɗinsa ne, dan sun yi hoto da ahi ba komai ba ne, tun da ba cewa suka yi suna sonsa ba. Kanta ta kawar tana faɗin. “Junior! Ya kamata ka gane wani abu guda ɗaya, ba'a kishin mutum sai ana sonsa, ka san cewa ina sonka, kuma akwai maganar aure tsakanina da kai, to me ya sa kake tunanin ba zan ji ciwo i idan na ganka da wata ba?” Tauqeer ya yi shiru kawai. Dan shi har ga Allah ya kan manta wanan batun auren dake tsakaninsa da Deena, dan abu ne da ba ya cikin lissafinsa. Tun shekarun baya da suka wuce ya jingine babin soyyaya. Ko shi kansa bai san me ya sa ya amince da aurenta ba. A batun gaskiya shi bai taɓa son Deena ko da da minti ɗaya ba ne. Ba wai ya tsaneta ba ne, a'a, shi yana mata kallon 'yar uwarsa ne ba masoyiyarsa ba. Batun tana kishinsa kuma wata magana ce da ban. Tun da take baɗalancinta da sunan Film bai taɓa nuna mata ƙin abun da take ba. Sai shi dan ya yi hoto da 'yan mata za ta ji haushinsa?. DIYA POV. “Ki kai wannan trayn teburi me lamba 16!” Umarnin ya fito daga bakin shugabarsu. Diya da kanta ke sunkuye ta gyaɗa shi. Sannan ta ɗauki trayn. Damuwar da take ciki a ko da yaushe ƙara girmama take. A kullum kwanan duniya mastaloli na ƙara tunkarar rayuwarta. A jiya jikin Papi ya ƙara tsanani, ga kuma Ekene da har zuwa yanzu bai gama warkewa ba, ga kuma Gigi dake ɓoye mata wani abu da ta kasa gano menene shi. Ga kuma MD da ya uzzurawa rayuwarta. A daren jiya har kiranta ya yi a waya. Ya na ƙara nanata mata mummunan ƙudirinsa a kanta... A lokacin ne kuma abun ya faru. Matakin farko na wanzuwar ƙaddarar dake tafe da jirkitattun al'amura. Tunaninta ya maƙale a iska, sakamakon tsohon canvas ɗinta da ya yage, hakan ya haddasa mata gurɗewa, ta yi gefe zata faɗi. Amma cikin ikon Allah sai ta ji an riƙo hannunta, an fisgota da ƙarfi. Kuma ƙarfin da aka saka wurin janyotan ne ya sa trayn dake hannunta suɓucewa ya faɗi. Ita kuma ta faɗa ƙirjin wanda ya janyota. Idanuwanta a rufe gam-gam. Yayin da hannun mutumin da ya temaka mata ke riƙe da kunkuminta, ita kuma nata hannayen na dunƙule a kan ƙirjinsa. Daddaɗan ƙamshin turarensa ne ya fara dawowa da ita hayyacinta. Kafin sassanyar muryarsa ta doki dodon kunnenta. “Kina lafiya?” Sai ta kasa gaskata abun da kunnuwanta ke jiye mata. Ta saba jin muryarsa cikin waƙa, ta saba jin muryarsa idan ana masa interview. Ta saba jin muryarsa a tallace-tallacen da ake bashi na kamfanunuwa. Ko a barci ta farka babu abun da zai hana mata gane muryarsa. Babban mawaƙin da ke burgeta TAUQEER AGHA! “Kan bala'i! Junior miye hakan?... Akan me za ka riƙeta irin haka a cikin jama'a?” Wata murya ta dawo da ita daga duniyar kokwanton da ta lula. Da sauri ta buɗe idonta tana kallon setin inda muryar ta fito. DEENA AGHA ce. Kuma ganin Deenan ne ya tabbatar mata da wanda take cikin jikinsa a yanzu Tauqeer Agha ne. Cikin jikinsa! Kalmar ta nanata kanta a cikin ƙwaƙwalwarta. Da sauri ta matsa daga jikinsa tana kallon fuskarsa. Ji ta yi zuciyarta ta daka tsalle. Abun kamar a mafarki, yau ita ce tsaye a gaban Tauqeer Agha?. Tauqeer kuwa kallonta kawai yake. Suna cikin magana da Deena ta zo za ta gifta su, da yake hankalinsa na a setin inda ta zo wucewa ne ya sa ya ankara da gurɗewar da ta yi. Shi ya sa ya yi hanzarin miƙewa ya ruƙota. Kuma a sanda ya kalli fuskarta ya ji wani abu na bi ta kan zuciyarsa da bai san sunansa ba. Bai taɓa ganinta ba, bai santa ba, ba ya jin ya taɓa ganin ko da me kamar ta ne balle ita ɗin kanta. Amma haka kawai sai ya ji kamar ya santa. Kamar ya taɓa saninta a wani wurin bayan wannan. Sai ya samu kansa da kasa dena kallon fuskarta har yanzu. Har zuwa yanzun da Deen ta ɗauki glass cup me cike da ruwa ta watsa mata a fuska. Hakan ya sa ta yi saurin rintse idonta. Shi kuma Tauqeer ya yi saurin kallon Deena. “Deena mi ye haka?” Ya tambaya ransa na shirin ɓaci. Dan hankulan tsurarun mutanen dake Restaurant ɗin ya dawo kansu. “Au tambayata ma kake? A kan me zaka riƙe wannan ƙazamar yarinyar a gaban mutane? Ko hannuna ba ka son ka riƙe amma a gaban idona ka riƙe wannan ƙazamar oloshi oloddo, opola ɗin?” Tauqeer ya lumshe idonsa yana so ya hana ransa ɓaci. “Deena ki bata haƙuri!” Deena ta yi dariyar renin hankali. “Wow! Ni ce zan bata haƙuri? Har wannan ƙazamar talakan ta kai na bata haƙuri? To bata isa ba, daga kai har ita baku isa ba!” Tana kaiwa nan ta finciki jakarta ta fice tana harar Tauqeer. A hankali Tauqeer ya matsa kusa da Diya da har zuwa lokacin idonta ke a lumshe tana hawaye. Mutane da dama kan ce Deena Agha bata da mutunci, ta iya wulaƙanta mutane, ba ta taɓa gaskatawa ba sai yau. Ba zato ba tsammani ta ji sauƙar wani lallausan hanki a kan fuskarta, sannan muryar Tauqeer ta biyo baya. “Ki yi haƙuri...” Sai kuma ya yi shiru yana karanta sunan dake rubuce a jikin name tage ɗin rigarta. “DIYA SHOLA!” Yanda ya furta harufan sunan nata ɗaya bayan ɗaya cikin daddaɗar muryarsa ya sa ba shiri ta buɗe idonta ta kalleshi. Tsaye yake kusa da ita, hannunsa na dama riƙe da hanki yana goge mata fuskarta da Deena ta watsa mata ruwa. Idanuwanta ya ci gaba da kalla, yana jin kamar su dawwama a haka yana kallonta. “I'm truly sorry!” Ya kuma faɗi idonsa cikin nata. Diya ta zama daskararriya dan mamaki! Ita fa Wallahi ta kasa yarda da cewar wai yau ita ce tsaye a gaban tauraron duniya lamba ɗaya. Ba haka kawai ba, har sunanta ya furta, a lokaci guda kuma yana bata haƙuri. Hannunta na dama ya kamo, sanyin hannyensa sune suka kunna wuta a cikin jijiyoyin jikin Diya. Dan ji ta yi kamar ya kara mata ƙanƙara. Hankin hannuna ya aje mata a hannun nata. Sannan ya ƙara furta. “Ki yi haƙuri” Ta kasa motsi, ta kasa magana, ta kasa dena kallonsa, ta kasa komai, babu ma wani abu dake aiki a jikinta face zuciyarta dakw kaikawo daga maƙogwaranta zuwa ƙirjinta. Sai kuma idanuwanta da ta kafeshi da su ba ta ko ƙiftawa. Har ya fice a kan idanuwanta bata dena kallonsa ba. Ko da Tauqeer ya fita bai iske Deena ba, dan haka ya shiga motarsa ya koma studio. Kuma ya jima a can. Dan har bayan magariba yana can ɗin. ______________ _LANTANA! Ina so ku samu wani ɗan ƙanƙanin space a cikin ƙwaƙwalanku, ku aje min wannan sunan, dan wannan sunan zai taka tasa muhimmiyar rawar a cikin wanga tafiya._ _Lalle Rafeeq yana lalube ne a cikin duhu, dan da alama zuciyarsa na shirin saka shi ɗaukar dala ba gammo._ _Akwai ƙura fa, dan na lura da Salame ba ta son wannan auren, dannewa kawai take._ _Na lura kamar Tauqeer ya fara son Diya._ _Ga kuma matsalolin dake tunkarar Diya Shola._ _Mu de je zuwa, kun san na ce muku ba fa mu yi komai ba har yanzu... Yanzu aka soma._ A. ISAH CE ✍️. °°°°°°°°°°°°°°°° *💡HASKE...💡* *©SALMA AHMAD ISAH* TAURARI WRITER'S ASSOCIATION. *Page 10* ~~~ *Federal Neuro, Psychiatric Hospital, Yaba, Lagos, Nigeria...* Wata nurse ce ke tura wheelchair. Wadda Rahila ke zaune a kai. Idonta kawai idan ka kalla za ka san cewa ba ta cikin hayyacinta. Dan da ƙyar take iya buɗesu. “Ka buɗe ƙofa. Sabuwar majinyaciya ce” Cewar nurse ɗin a sanda ta iso sashen adana maau taɓin hankali na aibitin. Me gadin ƙofar wurin ya buɗe mata yana faɗin. “Okay” Ci gaba ta yi da tura wheelchair ɗin. Har ta iso ƙofar wani ɗaki baƙinƙirin da shi. Da kantata buɗe kwaɗon ɗakin, sannan ta shigar da wheelchair ɗin, ba ta tsaya ɓatawa kanta lokaci wurin sauƙe Rahila ba, ta hankaɗata ta faɗi ƙasa har tana fasa kanta. Tsabar a galaɓaice take ko damar ihun azaba bata samu ba. Babu imani haka nurse ɗin nan ta juya ta fice daga ɗakin, sannan ta kulle. Haka Rahila ta yi ta murƙususu a ƙasan ɗakin da yake baƙinƙirin kamar sauran sassan ɗakin. Ta shafe sama da awa ɗaya cikin wannan hali, kafin hayyacinta ya dawo jikinta. A daddafe ta miƙe zaune. Sannan ta jingina da bango tana ƙarewa ɗakin kallo. Babu komai a cikinsa sai wata latsatssiyar katifa guda ɗaya. Jikinta ta ƙanƙame waje guda, sannan ta saki kuka me ban tausa. “Ya Allah kana gani! Allah ka ga halin da nake ciki! Ka kawo min mafita ya Allah! Ya Allah ka kawo min mafita” Haka ta faɗi ƙasan ɗakin tana kuka me sauti. Kamar daga sama ta ji an daki ƙarafunan ƙofar ɗakin. Ba ta kai ga fahimtar komai ba wata tsawa ta biyo baya. “Ke! Kukan ub*n me kike mana! Ki ja bakinki ki yi shiru, in ba haka ba jikinki ya gaya miki, mahaukaciyar banza... Ɗauki ki ci!” Lutetiyar matar dake ta bala'in daga bakin ƙofar ɗakin ta ƙarashe tana garo mata wani kwanon silver ta ƙasan ƙarafunan ƙofar ɗakin. Har kwanon ya iso gaban Rahila binsa kawai take da kallo. Sai da ta yi da gaske sannan ta iya gane menene a ciki. Wata cakuɓɓaɓiyyar shinkafa ce, wadda ba ta da maraba da tuwo, saboda ruwan da aka tsula wurin dafata, sai wata baƙar miya a kai. Kallon abincin kaɗai ya sa Rahila jin cikinta na yamutsawa, ta ji amai na shirin fito mata. Dan haka ta yi saurin kawar da kanta daga barin kallon abincin. Ko da dare ya yi kasa bacci ta yi, saboda koke-koke, bige-bige da doke-doken da masu taɓin hankalin dake kusa da ɗakinta ke yi. Haka ta yi ta firgita tana kuka. Kuma gashi ta kasa cin abincin wurin. Dan ko da daddaren ma an kawo mata wani baƙin tuwo da ta kasa gane na miye, da wata miyarsa me kama da ruwan wankin kai. SURAJ POV. Kasancewar yau laraba akwai aiki, kuma bayan ya je ya taso ya yanke shawarar kaiwa Diya Shola ziyara. Cikin wani ikon Allah yana zuwa bakin gaɓar yankin nasu ya hangeta ita da wannan ƙawar tata suna shigowa yankin. Da sauri ya faka motarsa ya fita yana nufarsu. “Kalli can ki gani Diya!” Cewar Fa'ee da ta hangi Suraj na tunkarosu. Diya da ta shagala wurin bawa Fa'ee labarin haɗuwarta da Tauqeer Agha a yau ta juyo ta kalli inda take kallo ita ma. “Da alama fa officer yana ciki” Da sauri Diya ta bigi hannunta tana mata alama da ta yi shiru, ganin Suraj ɗin ya ƙaraso inda suke. “Barka da yamma officer!” Cewar Fa'ee tana ƙunshe dariyarta, ganin yanda Diyan ke tsilli-tsilli da idonta, kamar ɓera a buta. “Lafiya ƙalau” Suraj ya amsa a mutunce. “To bari ni na wuce. Diya! Sai kin iso” Ta ƙarashe tana barin wurin. “Ƙawarki ce?” Suraj ya tambaya yana kallonta. Diya ta sunkuyar da kanta tana faɗin. “Eh, sunanta Fa'iza” Suraj ya ci gaba da kallonta. Shi kam yana mamakin ɗabi'unta, ko a hali ko a kammani ba ta da haɗi da yarabawa, tashin farko idan ka kalli kyan fuskarta da kuma yanayin ɗabi'unta da bafulatana za ka kirata. “Kame ka zo yi a yankin namu ne!” Ta tanbaya jin shirun ya yi yawa. Suraj ya ɗan yi murmusa yana cire hular kansa. “Ko kaɗan kawai de na zo wucewa ne, shi ne na ce bari na tsaya mugaisa da ke!” “Ka kyauta kuwa tun da gashi ka sada zuminci” Ya jijina kansa yana ci gaba da kallonta. “Ni zan koma... Sai an jima” Sai a lokacin ta ɗago da kanta ta dubeshi. “Na gode sosai Yallaɓai Sur...” “Suraj kawai” Ya yi saurin katseta, murmushi ta yi tana kawar da kai. Ba za ta yi wa kanta ƙarya ba, ita dai kam ta san yana burgeta, amma ba za ta kira hakan da so ba. Dan so na nufin haɗuwar zuciyoyi biyu wuri guda. Kuma idan ta yi la'akari da matsayinta da na Suraj sam ba ɗaya ba ne. Akwai tazara me tarin yawa a tsakaninsu, duk da ba ta san waye shi ba, amma ta faɗawa kanta cewar ya fi ƙarfinta, dan haka maganin bari kar a fara. “Suraj!” Ta kira sunan kamar yadda ya buƙata. Suraj ya tsaya ya ci gaba da kallonta kamar kar ya tafi. “Ka fasa tafiyar ne?” Ta tambaya. Da sauri ya girgiza kansa yana juyawa. Har ya kai jikin motsar ya dawo. Ya zaro katinsa, ya miƙata yana faɗin. “Wannan lambar wayata ce, ki kirani idan buƙatar hakan ta taso!” Sai da ta kalli katin sannan ta kalli fuskarsa. Hannunta ta kai ta karɓa, sannan ta masa godiya ta juya. Yana tsaye a wurin har ta sha kwana. Murmushi ya yi yana nufar motarsa ya isa gida ransa fes. Wanka kawai ya yi ya fito ya nufi ɗakin Narjis, ya sameta ya zayyana mata kaf abubuwan da suka faru. “Da kyau Hammana na kaina, a hankali a hankali za ka ci gaba da kusantarta, har zuwa lokacin da zaka bayyana mata sirrin zuciyarka” Murmushi ya yi yana gyara zamansa. “Wacece yarinyar?” Suka jiyo muryar Mummy na tambaya daga bakin ƙofar ɗakin. Dan haka suka juya suka kalleta a tare. Ganin ba su da niyyar bata amsa ya sa ta shigo ɗakin, ta zauna a tsakaninsu. Tana binsu da kallon tuhuma. “Ai kana iya zuwa ka faɗawa ƙanwarka damuwarki, ni ce ba za ka faɗawa ba?” Da sauri Suraj ya girgiza kansa. “Ba... Ba haka ba ne Mummy. Har zuwa yanzu ban faɗa mata ba, na fiso na sanar mata da farko, kafin na kawo maganar gareki!” Shiru ta yi tana kallonsa. “Waye mahaifin yarinyar!” Yawu ya haɗiye yana faɗin. “Ban... Ban san ba Mummy, kawai de na san a Makoko take!” “Makoko?” Ta maimata sunan mamaki kwance kan fuskarta. Kansa ya gyaɗa yana taoron jin abu na gaba da zai fito daga bakin nata. Shiruu na tsawon minti ɗaya. Ban da bugu babu abun da zuciyarsa ke yi. Tsoro yake ji, yana jin tsoron kada Mummy ta ce bata amince da yarinyar ba tun kafin ta ganta. Ga shi kuma ta ƙi yin magana, sai kallonsa kawai da take. Har ya riga da ya fidda rai, sai ya ga ta yi murmushi tana ɗora hannunta a kansa. Murmushin nata ne ya sanyaya zuciyarsa har ya sa shi shi ma ya yi murmushin. “Ka yarda da tarbiyyar yarinyar?” Da sauri ya gyaɗa mata kai. “Eh Mummy” “To Allah ya tabbatar mana da alkairi” Kwanciya ya yi a jikinta yana murmushi. “Ameen Mummy!” “Auta fa?” Cewar Narjis a shagwaɓe. Suraj ya saki Mummy yana dungure mata kai. “Lokacin firstborn ne yanzu” Suka yi dariya suna rungume mahaifiyar tasu. DIYA POV. Tana shan kwana ta samu Fa'ee zaune a cikin kwale-kwale tana jiranta. Murmushi ta yi tana nufar kwale-kwalen. “Allah sarki tawan, ashe jirana kike” “Eh mana, jira nake ki gama soyewar sai mu tafi” Diya ta zauna a cikin kwale-kwalen tana hararta. “Bana son shari Fa'ee” “Wani irin shari kuma? Bayan daga nan ma ina jiyo ƙaurin soyewar da kuka” “Sai ki yi kuma ai” Ta faɗi tana ɗauke kanta. Fa'ee ta yi murmushi. “Allah Diya na lura da ɗan sandan nan yana sonki!” Diya ta juyo ta kalleta da sauri. “Dan Allah Fa'ee kada ki fara abun da ba zai ƙarasu ba. Tskanina da Suraj mutunci ne kawai, ba na jin wata alaƙa me kama da ta soyyaya za ta iya shiga tsakani” Fa'ee ta yi shiru ba tare da ta sake cewa komai ba. Don ko me za ta faɗa Diya ba yarda za ta yi ba, amma dai ita ta san cewa ta hango abun da ita Diyan bata hango ba. A ranta ta musu addu'ar Allah tabbatar musu da alkairi. Kuma har suka iso gida babu wanda ya sake cewa komai. Ko da Fa'ee ta sauƙa a rumfar gidansu Diya sai ta tsallaka zuwa tasu rumfar. Kafin kuma ta shiga cikin gidansu. A ƙwallin ɗaki ɗayan dake gidan nasu ta iske mahaifiyarsu na zaune tana dama koko. Ƙaramin ƙaninta kuma na kwance a gefen mahaifiyar tasu. “An dawo?” Mahaifiyar tata ta tambaya tana dubanta. “Eh Mama, na dawo, kuma Wallahi a gajiye nake gaba ɗaya!” Ta faɗa tana zama kusa da mahaifiyar tasu. “Sannu to!” “Yauwa... Ina Aliyu?” Ta tambaya saboda ba ta ganshi a gidan ba. Mama ta miƙa mata koko a kofi tana faɗin. “Sikari na aikeshi ya siyo min” Fa'ee ta gyaɗa kanta tana karɓar kofin. Ai nahinsu mutanen garin Kano ne, ci rani ne ya kawo mahaifinsu Lagos, kuma ko da ya tashi tahowa sai ya taho da su, a lokacin Fa'ee tana ƙarama. Sannan a nan Makoko aka haifi Aliyu ƙaninta na farko, sannan aka haifi Sadiq autansu. Wanda bayan haihuwarsa ne mahaifinsu ya rasu. Shi ya sa kula da nauyin gidan ya rataya a wuyata. *Ƙauyen Wagini, Batsari Local government, Katsina state, Nigeria.* *11:40 na dare.* SALAME POV. Fitsarin da take ji ne ya tasheta a bacci. Da ƙyar ta miƙe zaune tana mitsikka ido. Fitowa ta yi daga gidan sauronta. Sannan ta laluba kan shimfiɗar Inna, ta ɗauko tocilan ɗinta. Ko da ta kunna fitilar sai ta ƙi kawowa. Hakan yasa ta ɗan bigi kan tocilan ɗin. Hakan ya bawa fitilar damar kawowa haske dal. Kasancewar ɗazu Inna ta saka mata sabbin batura. Kuma ta cikin hasken da fitilar ta bayar ta kalli jan lallen da aka mata a hannayenta. Jan lallen aurenta da wanda bata sani ba. Jan lallen da ya zauna a kan farar fatarta ya yi kyau. Ture zancen wannan auren ta yi daga kanta, sannan ta lallaɓa ta fita daga ɗakin ba tare da ta tada kowa a bacci ba. Ko da ta fito sai ta tsaya a tsakar gida. Kunnuwanta ne suka fara jiyo mata ƙaran babura a cikin shirun daren. Bakinta ta taɓe tana nufar randa dan ta je ta rage mararta. Buta ta ɗauka ta cika ta da ruwa, sannan ta nufi banɗaki. Ko da ta yi fitsarin ta gyara jikinta ta miƙe tana shirin fita daga banɗakin. A lokacin abun ya faru, a lokacin mukullin buɗe ƙofafin ƙaddararta ya wanzu a doron duniya. A ranar a kuma lokacin ne ƙaddararta ta farko ta auku. A lokacin ta saka ƙafarta cikin wani irin duhu dake mamaye gaba ɗaya rayuwarta. Ƙaran baburan da take jiyowa a nesa ne ya matso kusa. Bayan ƙaran baburan akwai wani sauti me razanarwa sautin harbin bindiga. Tuni ƙwaƙwalwarta ta hasaso mata irin abubuwan dake faruwa a maƙotan ƙauyukansu. Da alama 'yan bindiga ne suka shigo musu ƙauye. Nan take jikinta ya soma kyarma, har fitilar dake hannunta ta suɓuce ta faɗo ƙasa. Sabbin baturan dake cikin fitilar suka fice da ƙarfi, hakan ya haddasa ɗaukewar hasken fitilar. Duhu ya mamaye ban ɗakin. Wani irin duhu dake kamanceceniya da ƙaddararta. Tsoro ya hanata motsawa. Tuni ta soma hawaye, bakinta banda rawa babu abun da yake. “Inna! Salma! Iya! Baba! Muja!...” Ta jiyo muryar Hammanta na ƙwala musu kira a tsakar gidan. Baba ne ya fito daga ɗakinsa, dan shi ma ya ji ƙaran Iya ma ta fito haka Inna, duka suka tsaya a tsakar gidan suna tambayarsa abun da ya faru. “Baba 'yan bindiga ne suka shigo Wagini!” Zuciyar Salame ta ƙara dokawa da ƙarfi, a sanda ta jiyo ihun matan gidan dake maƙotaka da nasu. Ƙaran bindiga ya cika ko ina. Zabura ta yi za ta fita daga banɗakin ta ji an banko ƙofar gidansu da ƙarfi. Hakan ya sa ta sandarewa a cikin banɗakin. Ta tsaya ƙiƙam tana kallon 'yan uwanta da ke rafka salati. Fitilun da 'yan bindigar suka haskesu da su shi ne ya haska mata kalar tsoron da ko wannensu ke ciki. Kafin ta yi wani tunani na biyu, sun buɗewa kowa wuta a gidan. Tana ji kuma tana gani suka harbe kowa! Kowan ya haɗa da Inna, Baba, Iya Abu da Hamma Audu. Ƙarar harbin ne ya tashi Muja daga barci, ya fito yana murza ido. Ko kafin ya ce komai shi ma suka harbeshi. Tsoro ruɗani tashin hankali da ɗimuwa suka riftowa Salame a lokaci guda. Ƙafafunta suka gaza wurin ɗaukarta. Hakan ya bata damar zama a ƙasa daɓas!. Bakinta a buɗe, ta kasa furta komai sai ‘Innallilahi wa inna'ilaihi rajiun’ A kan idonta 'yan bindigar suka gama zaga gidan, ba tare da sun lura da ita ba suka fice daga gidan. Ta cikin hasken farin watan da ya haska duniya take kallon gawwawwakin ahalinta yashe a ƙasa cikin jini. Daga nan inda take tana iya jiyo sautin harbe-harbe, da iface-ifacen jama'ar ƙauyen. Amma ta kasa motsawa. Ji take kamar zuciyarta za ta fashe lokaci guda. Ta kasa janye idanuwanta daga kan gawarwakin danginta. Farin cikinta. Ababen alfaharinta. Rayuwarta. To yanzu ita me ya kamata ta zauna ta yi a duniya? An kashe mata kowa, kowa ya mutu, babu kowa, sai ita kaɗai. Cikin ƙasa da muntuna goma rayuwarta ta rugurguje tun daga farko har zuwa tsakiya. To yanzu me za ta yi. Kamar wadda aka cillo daga sama ta miƙe da gudu ta iyo cikin gidan. A kan gawar Baba ta fara durƙushewa. _“Ina so ki yi karatu Salamatu. Mace me ilimi ita ce abar alfaharin ko wace al'uma... Allah ya miki albarka”_ Ire-iren kalamansa gareta kenan. Hannunta na dama ta ɗora a kan ƙirjinsa dake zubar da jini. Ta ɗan jijjiga shi idonta na zubar da hawaye kamar an kunna famfo. “Baba... Babana... Baba...” Da ƙyar ma sautin muryar tata ke fita. Hannunta ta ɗauke daga kansa, sannan ta ɗora a kanta tana rushewa da kuka. Idonta ne ya sauƙa a kan Inna. Da rarrafe ta isa gareta. Hannunta ta riƙe bakinta na rawa wurin faɗin. “Inna! Innata!...” Sai kuma ta kwantar da kanta a jikin Innan tana tuna kalaman Innar gareta yau, sanda ana mata lalle. _“Sai haƙuri Salame. Shi zaman aure ɗan haƙuri ne, ki bi mijinki sau da ƙafa, ki masa biyyaya. Idan kika yi hakan, ina me tabbatar miki da za ki ci riba a nan gaba!”_ “Innaaaaaa!” Ta furta da ƙarfi cikin kuka. Sai kuma idonta ya sauƙaba kan Muja. Da sauri ta miƙe ta isa inda yake, kamoshi ta yi tana rungumeshi a ƙirjinta. _“Adda Salame idan na girma zan siya iki ƙatuwar mota irin ta gidan Alhaji Maude!”_ A lokacin da ya faɗa mata hakan dariya ta yi tana cewa santi yake, dan abinci suke ci a lokacin. “Mujahid!” Ta kira sunan da bata saba kiransa da shi ba. Haka ta saki gawarsa ta isa kan ta Iya Abu. _“Salamatu ko ba kya son auren nan ne?. In de har ba kya so ba za mu taɓa miki auren dole ba!”_ Kuka take sosai tana tattaɓa fuskar Iya Abu. Haka ta koma kan Audu tana kuka. Ta jima a zaune a wurin tana kalon gawarwakinsu. Kamar wadda aka tsikara kukan nata ya tsaya cak. Ta miƙe tsaye tana kallon gawarwakin 'yan uwanta. To yanzu tun da kowa nata ya mutu me za ta yi? Ya kamata ace ita ma ta mutu... Ba tare da ta sani ba, ƙafafuwanta suka fara takawa suna nufar ƙofar gida. Har zuwa lokacin babu abun da ke tashi a ko wani sashi na ƙauyen sai koke-koke da harbe-harbe. Tsayawa ta yi tana kallon ko ina na ƙauyen. Ƙafafuwanta ko takalmi babu, haka ta soma tafiya tana nufar hanyar barin gari. Can kuma da ƙwaƙwalwarta ta tariyo mata irin kisan gillar da aka yiwa ahalinta sai ta fashe da kuka ta fara gudu a kan ƙafafunta. Da haka ta fara kutsawa cikin daji. Babu abun da take so face ta bar ƙauyensu. Ta kutsa dajin nan, ko namun daji ne su cinye namanta ɗanye. Ƙafafuwanta na taka ƙayoyi da kuma ciyayi masu kaifi, amma ko a jikinta. Raunikan da ke gangar jiki kan iya warkewa, ban da na zuciya. Ba tare da ta ankara ba, ta taka wani abu me santsi. Kafin ta yi tuntuɓe da wani tubali. Ta faɗi ƙasa, har tana buga kanta a jikin bishiya. Ƙarar azaba ta saki tana dafe kanta. Kafin kum ta ji wani irin sara a ƙafarta. Raɗaɗin saran ya ratsa har ƙwaƙwalwarta. Daga haka kuma sai ji da ganinta suka yi nisan kiwo. *No.675, 361 Stagg Street, Brooklyn, New York, USA.* RAFEEQ POV. Babu abun da za ka iya gani a shimfiɗeɗen filin Allahr face farin HASKE. Babu kowa a wurin sai shi ƙaɗai. Ko ina farin ne, daga sama har ƙasa. Cikin waige-waigen da yake, ya hango wata farar matashiyar budurwa hannunta riƙe da wuƙa. Hawaye take tana kallonsa. Cikin abun da bai fi ƙiftawar ido ba, setin inda take ya koma ja. Jini ya shiga malala a ƙasa. Hannunta na dama ta ɗaga tana faɗin. “AL'AMEEN! Ka kawo min agaji! Ka taimakeni AL'AMEEN!...” Sai kuma ta yi shiru. Saboda duwatsun da suka fara sauƙowa daga sama. Ƙaran harbe-harbe ya karaɗe ko ina, babu abun da ke gudana a ko ina sai jini. Sai kuma ya ga matashiyar ta durƙushe a ƙasa tana dafe kanta. Wasu muryoyi suka shiga kiran. “SALMA!” Wata muryar na faɗin. “SALAME!” Wata tace. “SALAMATU CANDY!” Wata ma tace. “SALAME!” “ADDA SALAME!...” ~~~ Kirrr! Kirrrr! Kirrrr! Ƙaran alarm ɗin da ya seta ya karaɗe ɗakinsa. Amma ko motsi bai yi ba. Har Maa dake ƙasa ƙaran ya soma damunta. Hakan ya sa ta yi tunanin ko ya shiga wanka ne. Da ƙyar da fama ta hawo saman, dan ita bata son wannan benin, shi ya sa ɗakinta yake a ƙasa. Ƙofar ɗakin nasa ta buɗe. Ta sameshi kwance a kan gado. Mamaki ya kamata. Ta san Rafeeq Sam bai da nauyin bacci. To me yake faruwa. Carbin dake hannunta na dama ta mayar da shi zuwa na hagu. Sannan ta nufi alarm ɗin ta kashe. Tsayawar ƙaran ta yi dai-dai da farkawar Rafeeq a razane. Rigar jikinsa ta jiƙe sharkaf da gumi. Idanuwansa sun firfito waje. Gaba ɗayansa a hautsine yake, kamar wanda aka koro. Ko kuma ya yi gudun abun da zai kasheshi. Da ace agogon da ya saba auna adadin bugun zuciyarsa na tare da shi, da babu abun da zai hana ahi zuwa 100%. Da sauri Maa ta zauna kusa da shi tana tofa masa addu'a. Ba sai ya faɗa ba, ta san cewa irin mafarkan da ya saba yi su ne ya yi a yau. Tun yana ƙarami yake a haka. Abu ne mayuwici ya yi mafarki ka ga bai faru a gaske ba. Akasarin abubuwan da zasu tunkareshi a gaba cikin ikon Allah yana ganinsu a bacci. Tun ɗanta na ƙarami ta riga ta san cewa shi ba kamar saura yake ba, yana da banbanci da saura. Hannunta kai ta goge masa gumin da yake. Har zuwa lokacin da ƙyar yake futar da numfashi. “Maa! Wata yarinya ce!...” “Shhhh! Ya isa, ya isa” Ta faɗi tana ƙara goge masa gumi. Shiru ya yi mafarkin na ƙara dawo masa cikin tunani. Bai san wacece yarinyar ba, bai san a ina take ba. Bai san ta wace siga za ta shigo rayuwarsa ba, abu ɗaya ya sani kuma yake da tabbaci a kansa. Ko ba daɗe, ko ba jima sai wannan yarinyar ta wanzu a cikin rayuwarsa. Bai san ta yaya ? Yaushe ? Kuma a ina hakan za ta faru ba, shi de ya sani, kuma ya tabbatar da za su haɗu, za su haɗu ko a ina take!. “Ka je ka yi sallah. Lokaci na wucewa” Kansa ya gayɗa yana laluben agogonsa da glasses a kan side drawer. Ɗauka ya yi, ya fara da saka glasses ɗin, sannan ya ɗaura agogon a hannunsa na hagu kamar yadda ya saba ɗaurashi a wurin. Sai da ya kunna agogon. Ya jira na wasu 'yan sakkani don ganin ma'aunin bugun zuciyarsa. Kafin agogon ya nuna masa 64%. Idonsa ya lumshe yana buɗewa. Kafin a hankali ya miƙe ya nufi banɗakin. Sai da Maa ta tabbatar da ya shiga banɗakin, sannan ita ma ta fita ta shiga kitchen, ta saka Kiyara girka musu abun karin kumallo. DEENA POV. A fusace ta shigo babban falon dake ƙasa. Tsayawa ta yi tana bin falon da kallo, kafin ta ci gaba da takowa zuwa cikin falon. Ba ta tsaya a ko ina ba sai a sashen da su Abba suke. Ganin yanayinta ya sa Abba, Abby da Baffa miƙewa tsaye suna kallonta. Ban da Daddy dake zaune yana ƙara fantsamawa cikin duniyar tunanin da ya saba ziyarta. “A gaskiyar magana Abba na gaji da abubuwan da Tauqeer yake min!” Maganar tata ta fito babu wata girmamawa. Kamar ba wadda ke magana da yayan mahaifinta ba. Kuma maganar tata ce ta janyo hankalin sauran jama'ar falon. Har Saif ya miƙe yana nufo wurin. “Me Junior ɗin ya yi Deena?” Abby ya tambaya yana dubanta. Kanta ta riƙe tana hawaye. “A gabana fa riƙe wata ƙazamar 'yar yarbawa. A gabana yake riƙeta Abby!” “Ke da kike bawa ko wani kare da doki lasisin taɓa jikinki har kina da bakin da za ki kawo ƙarar Tauqeer akan yariƙe wata?” Saif ya faɗi a fusace yana jin kamar ya mangareta. Wannan rashin kunyar tata da rashin sanin girman na gava da ita shi ne a ko da yaushe yake sawa ya ji baya son Deena. “Ya isa Saiffudeen! Ba da kai take ba. Da mu iyayenta take. Ka barta ta faɗi abun da ke ranta!” Abba ya faɗi yana jin ina ma ace yana da damar da zai hana auren ɗansa da wannan 'yar ɗan uwan nasa da bata gado komai na ahalinsu ba. “Ban ƙaraso kan ka ba Saiffudeen Mas'ud Agha. Ba ni da lokacinka a yanzu!” Deena ta faɗi tana kallonsa. Kasancewar Saif mutum ne mai jin maganar iyayensa, ya sa bai sake cewa komai ba, sai cika da batsewar da yake kamar wanda idan aka tsikar zai fashe. “Abba na gaji da wannan jiran, ya kamata ace kun mana aure ni da Tauqeer. Ba zan saka ido wata ta ƙwace min shi ba!” Babu wanda ya ƙara ko da tari, kallonta kawai suke suna jinjina rashin kunya irin ta Deena. Umma kam ji take ina ma ta sa Tauqeer ya fasa auren wannan mara ɗa'ar. “Aure kike so?” Abby ya tambaya. Cike da rashin kunya Deena tace. “Eh Abby ina so a ɗaura mana aure ni da Tauqeer nan ba da jimawa ba, saboda na gaji!” Abby ya gyaɗa kansa. ”Bari Tauqeer ɗin ya dawo to!” TAUQEER POV. A hankali ya faka motarsa a parking lot ɗin dake ciki Agha Mansion. Idan ka kalli tarin jerin motocin dake wurin cewa za ka yi kamfanin saida motoci ne ba gida ba. Fitowa ya yi ya na kallon ginin gidan. A lokacin da ya fara taka ƙafarsa ta faɗo masa a rai. Diya Shola! YAROBA GIRL!. Murmushi ya samu kansa da shi. Dan bisa ga dukkan alamu ɗaurin da ya yi wa zuciyarsa ne ya kunce. Kwaɗon da ya saka ya kulle zuciyarsa ne aka buɗe shi a yau ɗin nan. Wannan feeling ɗin da yake dannewa a zuciyarsa a ko da yaushe shi ne ya ƙara motsawa a yau. Tabbas ya taɓa soyyaya. Ya san yanda ake yinta. Amma kuma sam bai sha da ɗi a hannun soyyayar ba. Soyyaya ta bar masa tabo me girma a zuciya, ta yadda har ya yanke shawarar ba zai sake yinta ba. Amma a yau ya ƙaryata hakan. Shi kansa ya san cewa ya faɗa soyyayar wannan farar bayerabiyar me kama da fulani... Tunaninsa ya katse, a sanda ya buɗe ƙofar babban fallo. Gaba ɗaya mutanen gidan ya gani tsaye a falon suna kallonsa. In ka ɗauke Hajiya da ya san i yanzu har ta kwanta bacci, Sai su Bobo da su ma ya san cewa suna bacci war haka. To kowa na gidan yana falon ciki kuwa har da Jamal dake tsaye a tsakiyar staris ya jingina da jikin stairs case ɗin yana kallon kowa na falon. Yanayin kallon da kowa ke binsa da shi ne ya sa shi fahimtar cewa ba lafiya ba. Falon ya shigo yana gyara zaman jakar guitar ɗin dake goye a bayansa. “Junoir zo nan!” Muryar Abba ta kirashi a kaurare. Kuma yanda sautin muryar Abban ya fito ne ya sa shi sauron kallon inda suke. Abban ya haɗe girar sama da ta ƙasa, hannayensa rungume a ƙirjinsa yana kallonsa. Dan yau ji yake ina ma ace Deena ba jinin ɗan uwansa ba ce, da ya nuna mata iyakarta. Sun yi shiru sun ƙyaleta tana iskancin da take so da sunan film ba wai dan basu isa da ita ba ne. Tauqeer ya haɗiye yawu, sannan ya sauƙe jakar guitar ɗin dake bayansa ya miƙawa Iqra. Da sauri Iqra ta karɓa tana rarraba ido. Dan su ba su saba ganin Abba cikin irin wannan fushin ba. Hajiya Zayya kuwa na tsaye a gefe tana kallonsu ɗai-ɗai. A cikin ranta take faɗin Wallahi ko kuna so ko bakwa so sai Deena ta samu abun da take so, Tauqeer na Deena ne ko sama da ƙasa za ta gaɗe. Tauqeer ya tsaya a gabansu Abba yana sunkuyar da kansa. Sai da Abba ya juya ya kalli Deena dake daf da fashewa sannan ya kalleshi yana goya hannyensa a baya. “Ɗazu Deena ta zo take sanar da mu cewa wai ka riƙe wata yarinya. Mi ye gaskiyar wannan zancen?...” “Wato ni ba ku yarda da ni ba? Shi ya sa kuke tambayarsa. Shin ni zan muku ƙarya ne?...” “Kar ki sake cewa komai. Ki rufa mana bakinki a wurin ko na bugeki. A sanda kika zo kika tsaya a nan kina mana rashin kunya akwai wanda ya dakatar dake a cikin mu? Babu, dan haka dole ki bari shi ma mu ji daga bakinsa!” Cewar Abby a fusace. Daddy kuwa kallon Deena kawai yake. Shi tun da yake bai taɓa jin yarinyar a ransa ba. Bai taɓa jin wani abu irin na soyyayar uba da ɗa na gudana a tsakaninsu ba. Bai taɓa kallonta a matsayin 'yarsa ba, shi ya sa baya shiga duka sabgarta. Ita ma kuma ba ta jinsa a ranta, saboda duk damuwarta ta duniya Mommy take faɗawa. Ko me za ta buƙata sai dai ta sanar da Mommy tun tana ƙarama har yanzu. Zayya ta rintse idonta ranta na mata zafi. Ko da ƙuda bata fatan ya taɓa Deena. Duk wani abu da zai ɓata mata rai bata sonshi. Ta buɗe idonta tana jin wai me ya sa ba ta kawar da Mas'ud ba ne tuntuni?. “Muna jinka Junior!” Baffa ya faɗa. “Ba da niyya na riƙeta ba. Ta zo wucewa ta kusa da mu, shi ne takalminta ya yage ta gurɗe za ta faɗi. Hakan ya sa na yi sauri na riƙo hannunta dan kar ta faɗi... Shi ne kawai!” Abba ya sauƙe wata ajiyar zuciya asirrance. “Deena tace tana buƙatar ku yi aure nan ba da jimawa ba, dan haka sai ka shirya!” Da sauri ya ɗago da kansa ya kalli Abby. Dan ji ya yi kamar ya buga masa guduma a tsakiyar ka. Aure da Deena? Kai ba za iyu ba. Fuskarta ce ta haska a cikin kansa hakan ya sa ya yi ƙarfin halin ture wani ƙaton dutse da ya danne harshensa wurin faɗin. “A gaskiya Abby ba zan iya auren Deena ba!” DIYA POV. Tafe take a gefen titi. Tafiyar kawai take, dan hankalinta baya jikinta. Hankalinta da nutsuwarta sun yi cilli zuwa wata duniya me nisa. Kuma hakan ya samo asali ne sakamakon tashin hankalin da rayuwarta ke ciki. Babu abun da ya fi ɗaga mata hankali sama da maganar da MD ya zo ya mata ɗazu. Cewa ya bata nan da kwana huɗu. Idan har bata amince da ƙudirinsa ba, zai koreta a aiki, sannan ya tabbatar da ya kawo ƙarshen rayuwarta... Tunaninta ya datse, a sanda wani abu ya bangajeta da ƙarfin da har sai da ta yi baya tana shirin faɗuwa. Da sauri ta kalli matar da ta bangajeta. Sanye take da wasu shuɗayen kaya. Yanayin fuskarta ne kaɗai zai nuna maka cewar ba a hayyacinta take ba. Hannayen Diya ta riƙe gam-gam tana faɗin. “Ka da ki bari su kamani. Ki temakeni 'yata. Wallahi da hankalina!” Sunan 'yarta da ta kirata da shi ne ya sa wani yanki na zuciyarta zaftarewa ya faɗo ƙasa. Kamar yadda manyan gidaje ke rugujewa a sanda aka yi girgizar ƙasa. Ba ta san me ya sa ba, amma haka kawai ta ji matar ta daki zuciyarta da ƙarfi. Fuskarta ta tsirawa ido tana kallon idanuwanta dake kama da nata idanuwan. Da sauri Rahila ta koma bayan Diya ta ɓuya tana kuka, jikinta sai rawa yake. Ɗazu da aka buɗeta za'a bata abinci ne ta samu damar guduwa. Kuma masu tsaron asibitin sun lura da ita. Dan yanzu haka ma sun biyota. Diya ta juyo ta kalleta tana kamo hannyenta. Sai a lokacin ita ma Rahilan ta kalli fuskarta. “Su waye za su kamaki?” Cikin zare ido Rahila tace. “Likitoci ne. Kama ni suka yi. Kuma Wallahi da hankali na 'yata. Sun rabani da jajaririyata tun tana ƙarama. Yanzu kuma so suke ni ma su ga bayana. Ki temakeni!” Ko kafin Diya ta fahimci zancen da matar take mata. Wata motar ambulance ta faka a gefen titin. Sannan cikin abun da bai wuce sakan biyu ba, ƙofar baya ta ambulance ɗin ta buɗe. Wasu nurses biyu suka fito suka nufosu. Rahila ta ƙara fashewa da kuka tana komawa bayan Diya. “Wannan matar ta bayanki majinyaciya ce daga asibitin masu fama da cutar taɓin hankali. A yanzu ta tsere ne ba tare da sanin mu ba, dan haka ki yi gaggawar matsawa daga inda take!” Cewar ɗaya daga cikin nurses ɗin. Diya ta haɗiye yawu tana matsawa. Da sauri su kuma suka cafko Rahila sannan suka zirara mata ruwan allurar dake riƙe a hannun ɗayarsu. Tuni Rahila ta fara layi tana kallon Diya. “Yata kada ki bari su tafi da ni! Ban aikata komai ba. Da hankalina. 'Yata! 'yata!...” Haka ta yi ta faɗi har suka sakata a cikin mota. Har motar ta bar wurin Diya na tsaye a wurin kamar wadda aka dasa. Ita kanta da za'a titsiyeta a dai-dai wannan lokaci da ba za ta iya faɗar takakamen abun da take ji ba. Haka kawai ta ji bata kyauta ba da ta bari suka ɗauke wannan matar. Sannan har cikin zuciyarta ta yarda da abun da matar ke faɗi na cewar ita ba mahaukaciya ba ce!. To me ya kamata ta yi dangane da lamarin wannan baiwar Allahn?. ______________ _Dan dan dan dan! Ana dara, sai ga dare ya yi_ _Shin kun lura da tun kafin HASKE ya shigo cikin Agha Mansion ya fara kauda duhu?_ _Saboda Tauqeer fa ya furta cewa ba zai iya auren Deena ba_ _Wani mataki kuke tunanin Hajia Zayya za ta ɗauka a kan hakan?_ _Kuma Tauqeer ya tabbatar da yana son ɗiyar yarabawa!_ _Salame kuma ta bar gida. Ina kuke ganin za ta nufa?_ _Me ya sa Rafeeq ya yi mafarkin Salame?_ _Diya da Rahila ma sun haɗu fa!_ _Me kuke ganin zai faru?_ _Dan idan baku manta ba Na ce muku yanzu aka soma wannan tafiya_ A. ISAH CE✍️. *** *Assalamu alaikum jama'a!* *A zahirin gaskiya bani da wasu kalmomi da zan yi amfani da su wurin nuna muku irin godiyata gareku. Haƙiƙa ku abun alfahari ne a ko ina. Ina me matuƙar godiya zuwa ga duk waɗanda suke bibiyata a duk rubutun da zan yi... Na gode Allah ya saka muku da alkairi. Allah biyaku da gidan Aljannah.* *Ina me farin cikin sanar da ku cewa daga wannan page ɗin, wato feji na goma zan dakata a free pages. Sauran pages ɗin dake gaban wannan kuma dukansu za su kasance paid. A farashin da nake da tabbacin duk wani Salmanian zai iya biya domin nuna min so da kuma ƙauna.* *Salmanian ku yi sani cewa ku ne ƙwarin gwiwata a ko da yaushe. Ku ne ababen alfaharina. Kuma na san ba zaku bani kunya wurin biyan kuɗin paid pages ba.* *Na gode Na gode sosai!...* ~~~ _Sauran fajin littafi HASKE za su zo muku a kan ₦ 300_ _Ga duk wanda zai biya zai tura kuɗinsa ta wannan account ɗin da zan rubuta a ƙasa..._ _Kuma daga zarar kun biya za ku fara samun update a kan kari. Dan ba dakatawa za mu yi ba_ _A har kullum, kun de san cewa SALMA A. ISAH taku ce_ _Na gode da so da ƙauna_ I LOVE YOU WUJIGA-WUJIGA❤️😘. Biya ta wannan account ɗin: 5487270431 Monie point. Salma Ahmad Isah. Shaidar biyata wannan number: 08131549317 Kada ku manta ₦ 300 ne kacal. #SalmaAhmadIsah #Haske #TaurariWriters.