[8/25, 2:38 PM] Meenatah: *🌩ANYI WALK'IYA.....🌩* *💡 HASKE WRITERS ASSOCIATION💡* *NA SLIMZY* *Sadaukarwa ga k'awata Faty D'an maliki*            01       2pm Cikin tsananin furgici da kidimewa take kallonsa  kwance warwas cikin jini batare da ko yatsansa Yana motsawa ba,maida dubanta tayi ga rigar jikinta data kasance doguwa pink yadda ta jike sharkaf da jini tamkar an yanka saniya...."innalillahi wa Inna ilaihi rajiun "shine abinda bakinta kawai ya iya furtawa a furgice ta yarda wukar dake hannunta tayi kofar fita gabanta na tsananin faduwa ta  Murda handle din kofar dakin, cikin saa taji kofar a bude take, bata tsaya wata wata ba ta runtuma a guje tun daga third floor take gudu Tana tsallakar matakala kasantuwar ko Ina tsittt, duba da yadda dare ya tsala ko Ina shiru Sai wadatar hasken lantarki a ko ina,harta sakko kasa babu Wanda taci Karo dashi ya ganta, Nan da Nan tayi azama ta fice daga main entrance din shiga guesst house din, tayi kofar gate....   Tana fitowa daga gate din guest house din titi ta tadda Nan da Nan ta shiga waige waige  na neman hanyar da zatabi Dan tsira da rayuwarta,hannun dama ta bi Tana gudu sosai ba kakkautawa har tayi tafiya Mai Dan Nisa ba tare da gajiya ba,batare da ta hadu da kowa ba,  hangen  hasken touch light da tayi ne  gabanta ya Yanke ya Fadi,tsayawa ta danyi sanan ta juya da niyyar chanja hanya,kamar daga sama sautin murya ance "ke dakata a inda kike"cikin kakkausar muryar da Saida ko Ina ya amsa kasantuwar darene.   Bugun zuciyarta ne ya karu,firgicinta ya karu akan Wanda take ciki ji tayi tamkar ta saki fitsari a inda take tsaye, har suka karaso inda take ta kasa kwakkwaran motsi saboda tsabar tsoro da firgicin da take ciki, inhar ba mafarki takeyi ba to tabbas masu tahowa gareta jami'an tsaro ne.....sandarewa tayi a tsaye a inda take, har suka karaso wajen, dukkansu Kara haska ta sukeyi daga sama har kasa ,daya daga cikinsu ne cikin kakkausar murya ya jeho Mata tambaya "ke daga Ina kike cikin Daren Nan?"   Kallonsa kawai ta tsaya yi tamkar wata kurma Sai kyarma da jikinta yakeyi kamar mejin sanyi,shiru tayi batare da ta CE komiba har minti biyu suka shude....Ganin Bata da niyyar amsa Masa tambayarsa, ya Kara jeho Mata  wata tambayar a Karo na biyu "wanan menene a jikinki kamar jini?na  menene shi?"   Kallon jikinta tayi sanan ta dago idanuwanta ta sauke a kansa a Karo na biyu batare da tace uffan ba Sai zufa dake karyowa daga jikinta tamkar Ana watsa Mata ruwa. Dan sandan dake tambayarta Shi ya juyo ya kalli daya daga cikin ukun dake tsaye suna kallon ikon Allah yace "Sargent" "Yes sir" "Arrest her,kasata a mota mu wuce da ita office"   "Ok sir"yace sanan ya juya da sauri cikin minti biyu Sai gashi dauke da hand cuff ya nufeta Dan sanya Mata... Dakatar dashi Dan sandan yayi "kada ka sanya Mata don bamuda tabbacin ita Mai laifice kawai dai sata a gaba kasata a mota muje.... ******* Zaune yake a tangamemen parlornsa Wanda ya Sha kayan alatu na more rayuwar duniya,tsayawa fadar irin dukiyar dake cikin parlorn kansa Bata lokacine,tunda aka kawo Masa jarida ya kifa kansa da ita misalin karfe biyu na Rana ya kasa Koda motsi a inda yake kishingide a kujerarsa 3seater ya runtse idanuwansa ya Lula cikin duniyar tunani....   Ya rasa dalilin da yasa yarinyar ta shiga ransa lokaci daya,yarinyar data kasance batada gata ta taso cikin gidan marayu,yarinyar da besan asalinta ba Amma ta shiga zuciyarta tayi Kane Kane,Wanda har ya kasance babu ranan da zatazo ta wuce batare da yaje ya ganta ba dikda ba samu yakeyi tayi Hira dashi ba,Amma  a  iya fahimtarsa  yarinyace marason hayaniya....   Karfe shida na yamma jiya yaje gidan marayu don ya ganta Amma hakan be yuwuba tunda ya shiga akace Masa Bata Nan ya tsaya jiranta har goma na dare,amma Bata dawoba to Ina taje?Ina FATIMA ZAHRA ta shiga?...haka kawai ya tsunci kansa cikin faduwar gaba wanda besan dalilinsa ba,fatansa Allah yasa dai ba guduwa tayi daga gidan marayu ba, don Koda ta gudu babu inda zataje Dan batada kowa batada gata Sai Allah...   Ajiyar zuciya ya sauke tare da busar da iska Mai zafi daga cikin bakinsa,idanuwansa ya bude wadanda suka kada sukayi jajir ya saukesu kan jaridar da aka kawo mishi ita Awa daya data wuce jujjuyata yakeyi a hannunsa sanan ya bude shafin farko na jaridar Yana budewa idanuwansa suka sauka akan rubutun da akayi da manyan bakake kamar haka *AN TSINCI GAWAR YARIMA HABIB A WANI GUST HOUSE  DAKE CIKIN GARI, WANDA AKAYI AMFANI DA WUKA WAJEN CAKA MASA A KAHON ZUCIYA,... Bugun zuciyarsa ne ya tsananta ya cigaba da karantawa hannunsa na rawa kamar ansa Masa shoking,  NA'URAR CCTV DAKE MAKALE A CIKIN DAKIN TA NUNA FUSKAR YARINYAR DAKE DA ALHAKIN KISAN DUMUDUMU  HANNUNTA DAUKE DA WUKAR DA TAYI AMFANI DA ITA WAJEN  CAKA MASA A KAHON ZUCIYA,WADDA BAZATA WUCE KIMANIN SHEKARU GOMA SHA TARA BA*....zumbur ya Mike tsaye kasantuwar hoton yarinyar dayake kallo a gefen rubutun yayi dishi dishi Amma hakan bazai hanashi gane fuskarta ba a ko wani yanayi, " Fatima Zahra" ya ambata q fili,dik AC dake aiki cikin parlorn be hana zufa keto Masa ta ko Ina ba....idan ba gizo idanuwansa keyi ba to tabbas wanan gawar Dan uwansa ne YARIMA HABIB...   Jifa yayi da jaridar ya furta a fili"No Fatima Zahra bazata taba kisa ba",kisar ma Dan uwansa na jini ta kashe..."Anya habib ne kuwa yayansa?idan haka ne meyasa baa nemesa an sanar Masa ba?   Wayarsa ya janyo kirar iphone7+ ya Danna makunin hasken wayar Sai yaga a kashe take Ashe,kunna wayar yayi ko kafin ya Gama lalubo number da yake nema Tex ya shigo kamar haka Assalamualaikum yarima,Mai martaba sarki Yana nemanka a fada da gaggawa idan har sakon Nan ya iso gareka tun cikin dare ake neman wayarka a kashe.   Zuciyarsa CE ta tsananta harbawa Yana gama karantawa ya kwashe komi nasa ya fice daga parlorn yabar gidan.... ******* Fada ta cika tayi dankam bakajin komi Sai sautin koke koke dake tashi daga bangaren da Mata ke tsattsaye  jigum jigum.. sallamarsa a fadar CE tasanya kowa juyawa da kallonsa gareshi babu Wanda ya amsa mishi haka yake takowa a hankali har ya karaso tsakiyar tangamemen falon da suke Kira fada...tsugunnawa yayi gaban gangar jikin da ya gani a lullube da zani ya sanya hannu ya janye mayafin take yayi tozali da fuskar Dan uwansa habib...."innalillahi wa Inna ilaihi rajiun"shine abinda ya furta a fili...take zuciyarsa ta hasko Masa rubutun jaridar daya karanta dazu da fuskar yarinyar da ya gani....lullube gawar yayi ya Mike jiki a sanyaye yayi hanyar inda mahaifiyarsa ke tsaye Tana sanye da lafaya ta yane jikinta idanuwanta sunyi jajir alamar taci kuka harta gaji...kallonta yakeyi Yana neman Karin bayani daga bakinta,itama kallon nasa takeyi sanan ta bude baki a hankali tace"yadda ka ganshi haka muka ganshi,jiya daddare aka kasheshi Sai da asuba muka samu labari sanan aka kawo Mana gawarsa....runtse idanuwansa yayi take yaji wata juwa na dibarsa da kyar ya saisaita natsuwarsa ya kafe mahaifiyarsa da Ido batare da yace komiba. *******   Yana zaune a office dinsa masinjansa ya shigo da takarda hade da jarida ya tsugunna har kasa ya Mika Masa yasanya hannu ya karba sanan masinjan ya CE "ranka ya Dade wanan takkadar statement CE da aka rubuta game da kisan Dan sarkin  masarautar Barayar Zaki da akayi jiya daddare,wanan jaridar Tana dauke da baya Nan komi"    "Ok"kawai yace Masa ya juya ya fice....ya rufo kofar.   Glass dinsa ya gyara bayan ya Gama karanta statement din sanan ya bude jaridar ya karanta bayanin tsintar gawar da akayi a guest house,kasa Kuma wani hoto ya gani Wanda be fito sosaiba itace yarinyar da ake zargi da kisan...eye glass dinsa ya cire tare da Kara kallon hoton da kyau...tabbas wanan hoton yayi Kama da yarinyar da suka dauko a yawon patrol da suka fita jiya daddare....Kara kallon hoton yayi sanan ya Kara tabbatar da hasashensa.   Wayar salula ya dakko ya Danna lambobi bugu daya cikin na biyu aka dauka Saida yayi gyaran murya sanan ya Soma magana "ranka ya Dade inspector barka da Rana"   "Barka dai ASP Aminu me ake cikine?"   "Ranka ya Dade takadda aka kawomin office yanzun wadda ke dauke da statement Akan kisan da akayiwa yarima habib na masarautar Barayar Zaki,hade da takaddar akwai jarida wadda aka buga da hoton gawarsa da Kuma hoton yarinyar da naura Mai kwakwalwa ta nuna Dumu Dumu da alhakin kisan,ranka ya Dade akwai wata yarinya da muka dauko jiya daga patrol din dare da muka fita Ina kyautata zaton itace yarinyar da ake zargi da kisan YARIMA HABIB"   "Ka tabbatar da abinda kake fada kuwa ASP Aminu?"   "Na tabbatar ranka ya Dade"   "To alhamdulillahi tunda hakane yanzun akara tabbatar da tsaro Akan yarinyar,yanzun zankira masarautar in sanar musu da cewar anga yarinya"...    "To shikenan ranka ya Dade" ******* "Na rantse da Allah inhar yarinyar Nan ta shigo hannu wadda ta kashemun gudan jinina Sai na wulakanta rayuwarta itama Sai anyi Mata kisan wulakanci,bazan taba yafewa wannan yarinyar ba"   Wayarta CE ta shiga ringing lokaci daya takai hannunta gefen kilishin da take kishingide akai Tana famar rizgar kuka Tana sambatu kala kala,kallon screen din wayar tayi taga bakuwar number ce,dauka ta Danna sanan ta Kara wayar a kunnenta,daga can bangaren aka Soma magana "ranki ya Dade ASP Aminu ke magana daga headquarter na Yan sanda"   "Ina jinka"tace a dakile cike da Isa da mulki. "Yarinyar da ake zargi da kisan YARIMA habib yanzun haka Tana hannun hukuma"   Mikewa tayi zaune daga kishingidar da tayi,cikin daga murya tace"kana nufin anga yarinyar data kashemun da'na habibu?"    "Ehh ranki ya Dade"bata bashi amsa ba ta kashe wayar ta Mike tsaye gaba daya Ido ya koma kanta da jin kalmarta ta kashe na ganin yarinyar da tayi kisan Kai kowa jiran Karin bayani yakeyi....   Mutuwar zaune yayi a inda yake Jin abinda mama babba tace....zuciyarsa ta shiga yi Masa lugude tamkar zata Huda kirjinsa ta fito"Allah yasa dai ba ke kikayi kisan Kai ba Fatima Zahra!!!     [8/25, 2:38 PM] Meenatah: *🌩ANYI WALK'IYA.....🌩* *💡 HASKE WRITERS ASSOCIATION💡* *NA SLIMZY* *Sadaukarwa ga k'awata Faty D'an maliki* 02 "Waini kam kuluwa tun jiya da muka tura yaran Nan nida shiru bamuga Fatima Zahra ta dawo ba gasu zainab da su hauwau dik sun dawo an caske Mana Yan canjin mu Amma har yanzun yarinyar Nan Bata dawoba Fatima Zahra Allah yasa dai ba taurin Kai tayiwa yarima ba Dan zata aika wanan shegiyar yarinyar Mai Kama da aljanu Mai shegen miskilancin tsiya da taurin Kai da kyar dakyar muka tura yarinyar Nan baason ranta ba Allah yasadai ba guduwa tayi ba Dan tabbas idan Fatima ta gudu daga gidan Nan kashina ya bushe a wajen yareemah kabir don Shi sonta yakeyi dagaske,Ni tsorona ma kada magana ta fito ya gane Dan uwansa aka turawa ita yayi lalata da ita Dan wallahi a tsorace nake" Murmushi wadda aka Kira da kuluwa tayi tace "in Banda abinki hajiya me zai dameki bayan yarinyar Nan ko Bata tayi babu me nemanki tunda babu Wanda yasan kunayin wanna harkar ta tura marayu neman kudi,sanan ko baaga Fatima Zahra ba bawani Abu da zai faru tunda dama ba galihu garetaba marainiya CE fa ba uwa ba uwa babu dangi waya sani ma ko cikin shegece ita?" Shekewa da dariya sukayi dukansu harda tafawa hajiya ta Nisa tace "ita tasani idan ma Bata yardaba yayi ta karfin tsiya ko a jikina nidai na caske yan canjina a aljihuna tunda ya Dade Yana kwadayim shegiya tanayi Mana bakin ciki Sai jiya Allah ya bamu saa akanta" "Hajiya ai yarinyar CE ta wanku don wallahi ko zainab da manyan masu kudi da Yan siyasa keji da ita saboda diri da kyawu suke hutawa da ita batakai Fatima suffa ba,Fatima dabance Allah ya hore Mata kyau da zati da diri na tabbatar yarima Sai yadawo ya Kara Miki tukwici donshi zai baretq a Leda" "Allah kuluwa?Allah yasa ya karamun tukwici kema Zan San Miki wani Abu don kema kina bamu babbar gudun mawa" "Ameeen dai hajiya" Nan suka cigaba da tattaunawa Akan yadda suke gudanar da rayuwar safarar Yan Mata a gidan marayu Wanda hakan ya zame musu babbar Sanaa da suke samun makudan kudi daga Mayan masu kudi da Yan siyasa... ******* Tunda garin Allah ya waye take sintiri daga cikin inda suke zuwa bakin gate din gidan hankalinta a tsananin tashe,ita babban tashin hankalinta be wuce yau me zata cewa yarima khabir idan yazo neman Fatima ba tun jiya dasu hajiya suka fita da ita har yanzun baa dawo da ita ba tsoronta be wuce Allah yasa dai ba kaita sukayi a lalata taba kamar yadda ake daukarsu daidai da dai dai Ana rabasu da budurcinsu saboda Basu da gata a matsayinsu na marayu bayan Suma Yaya ne Amma bazasu gusheba suna addua Akan AYI WALK'IYA..halin kowa ya fito asirin masu wanan al'amari ya tonu dikda batajin akwai wanna ranan da wanan al'amari zai faru tunda Basu da gata Sai na Allah....wasu zafafan hawayene suka shiga gangarowa a kuncinta Wanda batasan Tana yinsuba tunda ta hada Kai da gate ta fada wanna duniyar tunanin Alamar zaa bude gate taji tayi kaza ta boye a jikin bishiyar da tayiwa gate din kawanya,Wanda ta gani ya shigo a furgice ne tabishi da kallon tsana hannunsa dauke da jarida zufa ta jikeshi sharkaf shaddarsa kamar an zuba Masa ruwa....bayansa tabi da sauri Dan shine ya fita dasu Fatima da yamma. Wajen dasu hajiya da kuluwa ke zaune ya nufa da sauri itama Tana biye dashi a baya har suka kusa Isa wajen da suke kusa da kitchen ne ta ruga ta boye a bayan kofar kitchen...hajiya CE ta wurga mishi wani kallo irin na tsofaffim Yan duniya tace "Kai Kuma fa haruna kaketa mazurai kamar Mara gaskiya" "Hajiya Dole inyi mazurai Dan muna cikin babban tashin hankalin da idan maganar Nan ta fito kashinmu ya bushe" Saida hajiya ta girgiza da Jin abinda yace Amma saita dake ta yatsina fuska tace "meye Kuma ya faru?" "Hajiya kenan meye ma be faruba yanzun Ina cikin gari nakejin wani mummunan labari Wanda ban gasgatashi ba Saida naga wanan jaridar" Ya daga jaridar ya nuna Mata cikin sauri ya bude shafin farko ya dago Kai yace "Fatima Zahra ta kashe yarima Habib yanzun haka anbaza matakan tsaro ma Ana nemanta,wata majiyar ma ance anganta yanzun haka Tana hannun Yan sanda" Mikewa hajiya tayi tsaye ta cire dankwalin kanta gashinta da yayi cibiri cibiri ya bayyana ta Dora hannu aka tace "mun shiga uku tamu ta Kare kashinmu ya bushe ya akayi wanan mummunan al'amari ya faru haruna?" "Bari kedai hajiya dik a rude nake babban fatana da burina be wuce Allah yasadai lokacin da muka dau Fatima babu Wanda ya ganta" Cikin tsananin tashin hankali hajiya tace "akwai domin kawarta bilkisu ta ganmu,Kuma Saida sukayi sallama Kuma ina kyautata zaton Maryam ma ta ganmu Dan itama suna shiri" Kuluwa ta dafe kai cikin tsananin gulma tace "tabdijan lallai abun babban bala'i ne" Haruna ya Nisa yace "yanzun dik inda bilkisu take aje a nemota Dan Maryam me saukice, bilkisu itace raayinsu daya da Fatima Zahra Ana zuwa bincike zata tona Mana asiri Dan tafi Fatima tsauri da shegen taurin Kai kamar kwakwa" Bilkisu dake labe a bayan kofar kitchen ta Dade da sulalewa kasa Tana zubar hawaye kuka takeyi sosai Mara sauti Mai matukar cin Rai da ban tausayi...."innalillahi wa Inna ilaihi rajiun"shine kalmar da take maimaitawa kafin ta furta a fili "shikenan hajiya sunyi sanadiyyar marainiyar Allah".....gabanta ne ya Kara faduwa da ta tunada kalmar haruna "Fatima ta kashe yarima habib"idan Bata mantaba yarima kabir ya taba fada musu Susu biyune maza wajen me martaba sarkin masarautar Barayar Zaki shida Dan uwansa habib Wanda kishiyar mahaifiyarsa ta haifesa Sai kannensu Mata bitu afnan da khausar Susu hudu ne yaran Mai martaba sauran dik yaran riko ne.....ji tayi tamkar itace ta aikata kisan jikinta Nan da Nan ta dauki rawa...... Haruna ya kalli hajiya yace "zamu rufe maganar Nan Koda Fatima Zahra ta dawo gidan Nan babu Wanda zaiji meya faru sanan zamu boyeta idan har Allah yasa ta dawo gidan Nan. Nan suka cigaba da tattaunawa Akan matsalar dake Shirin taso musu..... ******** Tunda labarin bayyanar wadda ta kashe yarima habib ya bayyana a masarauta, Nan da Nan labari ya karade ko Ina a cikin gidan sarautar ko Ina ya dauka dik inda akabi tsegumine ke tashi wajen bayi da wadanda ba haifaffun gidan ba abin mamaki shine yadda akayi karamar yarinya ta kasheshi Yar shekara goma Sha Tara,....it's kanta maman yarima khabir tunani takeyi ya akayi yarinyar ta taka cikin guest house na Yan gidan sarauta?har ta taka part dinsa ta kasheshi wanna kisan akwai alamar tambaya cikinsa.....shiru kawai tayi batare da tace komiba Sai istigfari takeyi da carbi a hannu.... ******** Kaiwa da komowa kawai yakeyi a dakinsa tunda akayi jana'izar Dan uwansa ya kasa Zama cikin Yan zaman makoki tunani kawai yakeyi yadda akayi Fatima Zahra taje har guest house na masarauta daga gidan marayu,ya akayi taje?kaita akayi?bashida amsar wanan tambayar Sai ita Fatima Zahra.....babban tashin hankalin da yake ciki be wuce yadda zaayi ya ga Fatima Zahra yayi Mata tambayoyin da suke a bakinsa Wanda beda amsarsu Sai ita.....gumi ne ya Kara karyo Masa yasa hannu ya share....ya runtse idanuwansa soyayyarta na ratsa sassan jikinsa tanayi masa yawo ko Ina....ya zaayi ya kubutar da Fatima Zahra?Anya bazaisa kakinsa na lawyer ya tsaya Mata ba?to ta Yaya?yayansa fa ta kashe ya zaiyi ya tsaya Mata?me zaa kallesa dashi a idon duniya?hannu yakai sumar kansa dake kwance luff kamar ya shafa Mai ya shafo kansa zuwa sajensa tare da runtse Ido...ita kawai yake kallo a idanuwansa baiwar Allah Fatima Zahra..... ******* A can station kuwa an sanya Fatima Zahra a gaba da tambayoyi wanan ya jefo Mata tambaya wanan ya jefo Mata itadai zare Ido Ido kawai takeyi ba tare da tace uffan ba Sai zufa da takeyi idanuwanta sun kada sunyi jajir tamkar jini ya kwanta Mata a Ido.... "Bazakiyi magana ba Sai kinji azaba?meye hadinki da yarima habib da Kika mishi kisan gilla?" "Wanine ya saki?"tayi shiru batare da tace musu kala ba dik tambayoyin da akayi Mata Taki amsawa, Sai rarraba idanuwa kawai takeyi zuciyarta tamkar ta fasa kirjinta ta fito.....inspector ya bada umarnin a mayar da ita a rufe a jail,ingizata Sargent yayi Tana tafiya da kyar hannunta dauke da hand cuff.... ****** Shiryawa tsaf yayi tsaf da nufin zuwa gidan marayu daganan zaije can station din ya gani ko zaisamu ganinta a asirce batare da wani daga cikin masarautarsu ya saniba..... ******** "Nikam mama ba mutuwar Yaya habib kadaice damu Yaya kabir ba Ina ganin akwai matsala fa" Dago Kai mama karama tayi ta kalli afnan dake wannan maganar,sanan tayi murmushi tace"Ni damuwata Bata wuce kada ya sanya kansa a case din mutuwar yayanki har ace shi ya kasheshi don ya hau sarautar masarautar Barayar Zaki" Girgiza Kai kawai afnan tayi cike da damuwa batare da tace komiba ta fada wani tunanin.... ******* A gidan marayu yayi parking motarsa,bugun zuciyarsa ya tsananta Wanda besan dalilim hakan ba[8/25, 2:38 PM] Meenatah: *🌩ANYI WALK'IYA.....🌩* *💡 HASKE WRITERS ASSOCIATION💡* *NA SLIMZY* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata Faty D'an maliki* 03 Tafe yake cikin mota Yana driving Amma Sam hankalinsa baya wajen gangar jikinsa ce kawai take tukin motar tunaninsa ya Gama gushewa da lissafinsa ga wanan babban ala'amari da ya faru....mafita kawai yake nema minti minti Yana tsaki zuciyarsa na tsananin Kuna da zafi a haka har ya Isa tangamemen gate din gidan marayun,horn yayi da karfi Mai gadi ya leko ta Dan kofar gate din sanan ya juya da sauri Dan bude Masa gate,wangale gate din yayi gaba daya ya koma gefe Yana daga Masa hannu tare da Mika gaisuwa,hannu kawai yarima ya daga Masa alamar amsawa inda sabo ya Saba da yadda yarima khabir ke amsa Masa gaisuwa cike da kasaita da izza irin na jinin sarauta..... Can gefen wata bishiya yayi parking motarsa inda ya Saba ajiyewa idan ya shigo Kuma wajen ne ya kasance wajen zamansu idan yazo,ya Dade a cikin motar Yana waige waige wajen shiru Sai kukan tsuntsaye ko alamar giftawar Yan Mata da ya Saba gani be gani ba ya Dade a wajen a cikin motar Yana kalle kalle ko Allah zai hadashi da daya daga cikin aminanta na gidan Amma bega kowa ba ya kwashi kimanin minti arbain shiru babu wani labari haka yayiwa motarsa key ya juya jiki a sanyaye ya nufi hanyar gida.... ****** Hajiya babba CE zaune da hadimanta a babban parlornta inda take ganawa da mutane ake karbar gaisuwa Tana zaune ta Mike kafarta daya daga cikin bayinta Tana Dan matsa Mata kafa idanuwanta a runtse zuciyarta na tsananin tafasa ta jiyo sallamarsa ,a hankali ta bude idanuwanta ta sauke akansa take taji tausayinsa ya kamata, yadda ya rame lokaci daya ya fita hayya cinsa saboda mutuwar Dan uwansa,a hankali ta bude baki ta amsa da "walaikumussalam" Tsugunnawa yayi har kasa ya dukar da kansa cikin sanyin murya yace "barka da war haka mama?" "Barkadai kabir" Kara dukar da kansa yayi cikin girmamawa yace "ya Karin hakurin mu?" "Hakuri alahamdulillahi" "Allah ya jikansa Allah ya gafarta Masa" "Ameen" Jim kadan ya Mike har ya juya ta tsaidashi "khabir"ta Kira sunansa,tsayawa yayi Jim kadan sanan ya juyo a hankali ya tsugunna batare da yace uffan ba,Bata damu da rashin amsawarsa ba ta cigaba da magana cike da kasaita da gadara wanan Karan magana takeyi sama sama "khabir inaso Kai zakaja ragamar shariar Dan uwanka Habib,inaso kasa kakin ka na lawyer ka hau kan aikinka banaso a ragawa dik Wanda yayi wannan aika aikar,ko wacece ta kashe maka Dan uwa ka tabbatar da kabiwa Dan uwanka hakkinsa nasan Kai gwanine wajen shariah Kuma babu Wanda ya Dace da wanan shariar Sai Kai,anjima nakeso kaje can station din ka bincika Mana yadda ake gudanar da bincike Akan yarinyar akara Bata tsaro saboda kada ta tsere,na lashi takobin dik Wanda ya kashemun da' Shima Sai an kasheshi ko Dan gidan uban waye" Wani irin firgici da tsorone ya ziyarci zuciyarsa a Karo na farko a rayuwa tunda yake babu abinda ya taba tada Masa da hankali ya furgita kamar wannan al'amarin daya kunno Kai Nan Nan zufa ta shiga karyo Masa ta ko Ina be Isa ya tsallake umarnin mama babba ba Amma ta Yaya zai tsaya a shariah a kashe Masa Fatima Zahra?kirjinsa ne ya cigaba da bugu da sauri Amma Sai ya dake yace"zaayi bincike sosai zaayi yadda ya kamata insha allahu" "Allah yayi maka albarka tashi kaje dama maganar kenan" Mikewa yayi jikinsa a sanyaye dakyar yake taka kasa ya haka yake tafiya kansa Yana tsananin Sara Masa tamkar zai rabe biyu haka ya lallaba ya shige bangarensa..... ******* Tunda aka rufeta a cikin wanan dakin da kullum Sai anyi Mata tambayoyi Wanda babu Wanda ta taba amsawa ko abinci baa Bata,Yan hajinta babu abinda sukeyi Sai kukan yunwa dikda babu abinda zata iyasawa a bakinta Koda ruwane, makoshinta ya bushe, idanuwanta sun kasa zubda hawaye, kukan zuci kawai takeyi,babu wani Abu da take tsammani Wanda ya wuce kisan Kai kamar yadda tayi Dan batada sauran Amfani a wanan duniyar me cike da tashin hankali kala kala batada wani sauran Amfani a matsayinta na marainiya babu uwa babu uba babu Dan uwa babu gata Sai Allah.....shin menene makomarta Wanda ya wuce a kasheta ta huta?.....ta rigada ta cire Rai da rayuwa tasanyawa zuciyarta dik Wanda yazo ya Kara tambayarta zata sanar dashi Akan itace tayi kisan gara a kasheta kawai.... ****** Zazzabi ne Mai zafi ya lullubeshi a cikin daki tun bayan daya baro wajen mama babba wadda kalamanta bakaramin tada Masa da hankali sukayi ba tabbas shi ya Dace ya tsayawa yayansa ya kwato Masa hakkin ransa Amma ta Yaya ta Ina zaifara shariah da yarinyar da soyayyarta ta Gama zagaye sassan jikinsa da jijiyoyin jikinsa? Hannu yasa ya dafe kansa daga kwancen da yake tare da runtse idanuwansa saboda yadda kansa ke Sara Masa tamkar zai rabe biyu.... Ya Dade a wanan yanayin yakai minti goma Sha biyar sanan ya Mike ya fada bathroom dinsa don ya watsa ruwa a jikinsa ko zai Samu sassaucin damuwar da yake ciki,bayan yayi wanka ne ya bude wardrobe dinsa ya ciro kayansa kanana wando jeans da tea shirt ya sanya sanan yaje gaban madubin dakin ya dauki turarrrika ya feffesa a jikinsa sanan ya fito,Yayi bangaren mahaifiyarsa, A kan daddumar sallah ya same ta ta idar da sallahr laasar da sallamarsa ya shiga dakin ta amsa Masa yanemi gefenta ya zauna yayi shiru batare da yace komiba,kusan minti goma da zamansa ta waigo ta Dan kallesa tace"hakuri ya kamata kayi ansan cewa mutuwa da ciwo musamman Dan uwanka Wanda ka shaku dashi kuka Saba tare kuka taso, Dole ne ka sanyawa zuciyarka hakuri da dangana haka Allah ya nufa" "Hakuri ya Zama Dole mama Amma rasa Yaya habib tamkar na rasa wani bangarene na rayuwata saboda yadda na shaku dashi yadda da'n uwana ke matukar kaunata" "Kaunar da yakeyi maka,itace ya kamata ka saka Masa da yi Masa addua sanan wanan case din da zaa Mika kotu ka tsayawa Dan uwanka ka kwatar Masa hakkinsa,shariar bazata dauki lokaciba insha allahu duba da yadda jarida ta nuna yadda yarinyar tayi kisan kaga kanada babbar hujjar da zaka nuna a kotu ba saikasha wahala ba" Shiru yayi zuciyarsa na Raya Masa abubuwa da dama game da wanan al'amari Amma ta Yaya zai tunkari shariah batare da bincike ba? "Ka kwantar da hankalinka insha allahu zakayi nasara Akan wanan shariar ai ba ita bace ta farko da ka tabayi,Dan Kaine ka Dace da ita dazun Mai martaba ya kiramu nida mama babba yake fada Mana abinda ya Yanke Akan cewa Kaine zaka tsaya" "Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun kawai"kawai yake maimaitawa a zuciyarsa domin be Isa ya tsallake hukuncin Mai martaba ba..... Har mama ta Gama maganganunta Sam hankalinsa baya wajenta shi so yakeyi ma yaje yayi tozali da ita ko zai Samu kwanciyar hankalin daya rasashi na kwana biyu....sallama yayiwa mahaifiyarsa ya Mike Yana tafe Yana hada hanya,kallo ta bishi dashi tausayinsa na ratsa Mata zuciya Dan tasan rashin Dan uwansa ne yake tabasa.... ******* Misalin karfe biyar na yamma ya shirya tsaf ya fito Dan zuwa station din bashi da bukatar Yan rakiya a wanan lokacin Dan Yana bukatar ganawa da Fatima Zahra sosai dikda yaji labarin dik tambayoyin da akeyi Mata a police station babu Wanda ta amsa Amma zaije ya gwada tashi saar ko zata kulashi dikda bashida tabbacin hakan Amma yasan ko ganinta yayi zai Samu kwanciyar hankali..... ******* Zuciyarsa cunkushe da tsananin fargabar yadda zai ganta be tabba tsintar kansa a yanayine tsoro da tashin hankaliba irin na wanan lokacin,Yana zaune inda ake ganawa da masu laifi yajiyo tashin tafiya hade da Karan kacha.....tun daga kafafuwanta ya Soma kallonta wadanda suke sanye da kacha an rufe da makulli,ya daga idanuwansa ya sauke a kan gangar jikinta Tana sanye da Riga wadda tayi kaca kaca da jini da ya bushe ya dago kansa ya sauke Akan kyakkyawar fuskarta Wanda ta dukar a kasa Tana tafiya har ta iso Dan sandan da ya rakotane ya juya abinshi tare da sarawa yarima khabir..... Kamshin turarensa ne ya gauraye wajen Wanda tunda ta iso bugun zuciyarta ya tsananta tabbas tasan Mai irin wanan kamshin turaren,to me ya kawoshi Nan? Tsayawa tayi a wajen kanta a kasa shi kuwa gogan ya kafeta da Ido jijiyoyin kansa gabaki daya sun fito a gaban goshinsa wani irin tashin hankali ya tsunci kansa kallonta kawai yakeyi baya ko kifta idanuwansa besan inda hankalinsa ya tafi ba tsintar kansa yayi da zubar hawaye.....Wanda tunda aka haifesa yaune na farko da damuwa ta sanyashi kwalla besan yanayi ba..... Jin shiru yayi yawa ya sanya Fatima dago idanuwanta ta sauke akansa aikuwa Nan da Nan ta firgita ta Fara ja da baya a hankali a hankali.... "Fatima kada ki gudu ba nazo Nan wajen Dan in tuhumeki bane da kisan Kai nazone Dan in bincikeki Akan abinda duniya ke zarginki dashi na kisan Kai" Girgiza Kai ta shigayi sai yanzun zuciyarta ta karaya hawaye suka Fara sakkowa daga idanuwanta Tana girgiza Kai hade da runtse Ido..... "Fatima kiyi magana Dan Allah ki bude baki kicemun bake kikayi kisan kan Nan ba" Girgiza Kai kawai takeyi hawaye na gudu a idanuwanta kamar an bude famfo batare da tace komiba.... Cikin tsananin damuwa da kyar ya Kara bude baki yace "Fatima na kasa gasgata kece Kika kashemun Dan uwa,Dan Allah ki fadamun gaskiyar lamari Ni Kuma nayi Miki alkawarin kubuta" Bude idanuwanta tayi ta sauke akansa,da sauri ta kauda kanta gefe batare da tace komiba Babu abinda yarima yafi tsana ya gani a rayuwarsa irin kukan Fatima zahra,idan hawayenta na diga ji yakeyi tamkar Ana zuba Masa wuta a zuciyarsa runtse idanuwansa yayi ya budesu sinyi jajir ya saukesu akanta...... Takowa yayi ya matso inda take a tsaye ya tsaya har tanajin hucin sautin numfashinsa ya daga murya cikin kakkausar murya yace "Fatima kifadamun gaskiya waye ya kashemun Dan uwana?kifadamun idan kece Kika kasheshi menene dalilinki na kasheshi?"...... Dago rinannun idanuwanta tayi ta saukesu akansa,Shima kallonta yakeyi tausayinta na ratsa jikinsa tun daga babban Dan yatsansa har zuwa kwakwalwarsa.....girgiza Kai kawai ya shigayi..... *Muje zuwa Dan Jin yadda zata kasance*..... *SLIMZY CE😍* *🌩ANYI WALK'IYA.....🌩* *💡 HASKE WRITERS ASSOCIATION💡* *NA SLIMZY* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata Faty D'an maliki* 04 "Kitaimakeni Fatima ki tausayawa rayuwata ki tausayawa kanki ki dubi maraicinki ki fadamun gaskiyar lamari Fatima kitaimakeni"..... Kallonsa kawai takeyi batare da tace komiba ganin kallon yaki karewa yasa yaja jikinsa ya jingina da jikin bango ya maida kallonsa ga ceiling din wajen batare da yace komiba... Fargabar data tsinci kanta a wanan lokacin tafi wadda ta tsinci kanta ciki a Daren shekaran jiya shin ta Yaya zata kalli tsabar idon yarima ta fada mishi itace ta kashe dan uwansa?....wani sabon kuka ne ya kubuce Mata Wanda rabon da tasamu tayi kuka hankalinta ya kwanta tun Daren da mummunar kaddara ta fada Mata.... Juyo da dubansa gareta yayi fusace yake kallon yadda take kuka a duniya babu abinda ya Tsana a rayuwarsa sama da kukan Fatima bayaso yaga fatimansa Tana zubar da hawaye ji yakeyi tamkar ya tafka babban sabo,bashida burin da ya wuce ya dauketa ya zame Mata gatan duniya Amma wannan babban ala'amari ya faru,zuciyarsa na tafarfasa tamkar zai bugeta ya Fara magana "look Fatima,banazo wajen Nan Dan sauraron sautin kukanki bane,ki kasa bude baki kiyi magana nayi tunanin kaf duniyar Nan bakida kamata komenene Zaki iya fadamunshi Koda kuwa kisan Kai kikayi Wanda ake zarginki dashi yanzu,na shiga matsananciyar damuwa Wanda fada mikishi a yanzun Bata lokacine babban damuwar Dana shiga be wuce cewa ankamaki da laifin kisan Kai ba,Fatima ta Yaya kikayi kisan Kai kifadamun gaskiya Fatima bazan taba gudunki ba duk runtsi dik bala'i nayi Miki alkawarin kasancewa dake a kowani Hali Koda kece Kika kashemun Dan uwa kifadamun Wanda yayi kisan Nan aka kulla Miki sharri nayi alkawarin tsayawa Akan shariarki matukar kinada gaskiya" Kallonsa takeyi cike da tausayawa,wasu zafafan hawaye na kara zubuwa daga idanuwanta ji takeyi inama ba itace tayi kisan kan Nan ba?inama dik wanan abun dake faruwa mafarkine ba gaskeba da idan ta farka bazata taba komawa bacciba harabada matukar zatayi mafarkin kashe Dan uwan yarimanta.... Takowa tayi ta tsaya a gabansa sanan ta durkusa kasa ta sunkuyar da kanta cikin dasasshiyar murya tace "Nina kasheshi da hannuna" Wani irin faduwar gaba yayi Wanda tunda yazo duniya be tabayin irinta ba Nan da Nan ya kidime jikinsa babu inda baya rawa cikin daga murya yace "Nooooo"sautin muryarsa babu inda be amsaba a wajen saboda yadda yayi maganar a razane,jijiyoyin kansa suka fito rad'a rad'a a gaban goshinsa bakinsa har rawa yakeyi wajen magana, "Fatima bake Kika kashemun yaayaah habib ba,fatima inada tabbacin bazaki taba kisan kaiba ,ko kiyashi baki taba kashewa ba balle mutum Dan Adam Mai Rai da Kuma lafiya,Fatima bakiyi kisan Kai ba wallahi bake kikayi kisan Nan ba,idan bakinki ya Kara cewa kinyi kisan Kai zan dauki mummunan mataki akanki"sambatu kawai yakeyi a haukace batare da sanin abinda yake fadaba Dagota yayi daga tsugunnen da take Tana rusa kuka ya shiga girgizata"Fatima ki tausayamun kada in rasaki ki duba halin da muke ciki kada ki furtawa kowa kece kikayi kisan kan Nan kamar yadda kikayi kuskure wajen fadamun Fatima" Kallonsa kawai takeyi tausayinta na Kara narkar Mata da zuciya yau yarimanta jarumi Wanda ko magana zaiyi yanayinta ne cikin kasaita da sarauta namiji Mai tsananin kwarjini da jarimta shine ya haukace akanta yake fadan maganganu wadanda Tana da tabbacin fadansu kawai yakeyi a matsayinta na tsintacciya maabociyar zaman gidan marayu? Cikin tsananin kuka tace "saidai kayi hakuri yarima Amma tabbas ninayi kisan Kai Kuma bazan taba maka karyaba abinda nakeso dakai shine ka gafarceni kashe maka Dan uwa da nayi....banida wasu kalmomi da zanyi Amfani dasu wajen Kare kaina Akan aikata mummunan aiki da nayi ,idan na boyewa duniya bazan boyewa mahaliccina ba daga amsawar Nan da nayi maka bazakaji wani Abu daga bakina ba fatana Allah ubangiji ya gafarta min yasadani da rahamarsa idan an kasheni" Tana Gama fadin haka ta juya da sauri da kyar take taka kasa Koda ta juya Dan sandan da ya kawota har yazo batare da Bata lokaciba yace "ranka ya Dade lokaci yayi har ka wuce time din da ake badawa" Shiru yayi tamkar an dasashi a wajen Yana bin bayanta da kallo,har Dan sandan ya Gama magana ya juya bece komiba harta bace Yana kallon hanyar databi.... Mikewa tsaye yayi juwa na dibarsa muryarta CE take amsawa a kunnuwansa na kalamanta na karshe"fatana Allah ya gafartamun ya sadani da rahmarsa idan an kasheni"hannu yasa ya toshe kunnuwansa Yana girgiza Kai......"innalillahi wa Inna ilaihi rajiun ,shikenan tafaru ta Kare babbar kaddara ta fada musu yasan Fatima batayi Masa karya Bata tabayi masaba Amma yau yanada tabbacin abinda ta fada karya takeyi......hannu yasa ya sharce zufar dake digowa daga sumar kansa,zuciyarsa na ayyana Masa Anya kuwa maganar Fatima babu kamshin gaskiya ciki?.....Fatima bazatayi kisan kaiba haka kawai Saida dalili,menene dalilinta na kashe Masa Dan uwa?waye yasata?Fatima bazatayi kisan Kai haka kawai batare da samun taimako ba.....ya yarda da maganarta itace tayi kisan Kai Amma meye kwakkwaran dalilinta menene silarta na kisan Kai?.....gabansa ne ya tsananta faduwa daya tuna da kalaman mama babba"dik Wanda ya kashemun da' bazan taba Bari a kyalesaba batare da ankasheshi ba yadda ya kashemun wallahi Sai ankasheshi ko Dan gidan uban waye" "Kabir Kaine ya dace ka tsaya ka kwatarwa Dan uwanka hakkin kasheshi da akayi Dole kasa kaki ka koma fanninka na lawyer"...jikinsa ne ya mutu daya tuna da wadanan kalaman.... Haka Nan ya Mike ya fito jiki babu kwaro ko komawa office din DPO besamuyi ba saboda tashin hankalin da yake ciki.... ******* Ana kiraye kirayen sallahr magriba ya Isa gida,masallacin gidansu ya shiga ya bisu sallah saboda ya tarar zaa tada sallah,bayan ya idar da sallah a massalaci ya Dade a zaune Yana addua sanan ya shafa ya fito....ya doshi hanyar shiga gidansu Koda ya shiga bangaren Mai martaba ya nufa Saida yayi kimanin minti goma sanan ya Isa bangaren a gajiye yake ga faduwar gaba da yakeyi minti minti, Iso ya nema akayi mishi sanan ya shiga lokacin Mai martaba Yana zaune akan katuwar daddumar dake parlorn nasa Wanda aka kawatasa da kayan adon daki irin na sarauta, Tsugunnawa yayi a gaban sarki ya kawo gaisuwa cike da ladabi da girmamawa sanan ya koma gefe ya zauna ya tankwashe kafarsa,sarki ya juyo da dubansa ga da'n nasa yace "kabiru meke tafe dakai ne?ya ake ciki game da case din mutuwar Dan uwanka kaje wajen jami'an tsaron ne" "Ehh Allah ya taimakeka naje" "To Masha allahu,me bimcike ya nuna?ansamu cikakken bayani daga yarinyar ne?" Gabansa ya Yanke ya Fadi cikin tsananin fargaba yace"ehh to har yanzun dai batayi wani bayani ba game da kisan Amma dai tace itace tayi kisan kan" Murmushi sarki yayi yace"a binciketa da kyau ta Fadi gaskiya Amma bana tunanin Wanda yayi kisan Kai zai amsa cewa Shi yayi batare da wani tunani ba,a Kara bincikata sosai zuwa ranan Monday kamar yadda sukace ranan zaa mikata kotu" Cikin tsananin damuwa yarima yace "toh zaa bincika ranka ya Dade" "Allah yayi albarka yanzun saika Fara shirye shiryen gudanar da shariar ko?nasan iyayenka sun fada maka hukuncin da masarauta ta zartar na cewa Kaine zaka tsayawa Dan uwanka Akan wanan shariar" "Eh ranka ya Dade" "Tashi gaje dik abinda yake Nan Sai a sanar Dani Allah ya bada nasara" Jiki a sanyaye yarima yace "ameeen ranka ya Dade,a huta lafiya" Mikewa yayi tamkar Wanda babu kashi a jikinsa haka ya juya Yana tafiya Mai martaba kallonsa kawai yakeyi Yana girgiza Kai Dan bakaramin tausaya Masa yayiba na rashin Dan uwansa da suke matukar son juna Wanda suka taso tare komi tare sukeyi saidai banbancin wasu abubuwa na halayya.... ******* Bangarensa ya koma ya xurfafa kansa a cikin tunani lallai Yana cikin tsaka me wuya,menene yake Shirin faruwa dashi?rasa Dan uwansa da rasa masoyiyarsa yarinyar da ya Dade Yana renon soyayyarta tun Tana kankanuwa ?shin idan ya tsayawa Dan uwansa ya karbar Masa hakkinsa ya tsayane Don kashe Fatima?koko zaiyi watsi da maganar iyayensa ne ya tsayawa marainiyr Allah? Wata zuciyar CE tace 'kada ka manta Kaine kayi alkawarin tsaya ma Fatima dik halin da zata tsunci kanta Kuma baka da tabbacin kisan da ake zarginta dashi ita tayishi,kayi watsi da maganar tsayawa matacce ka tsayawa rayayya ka tsiratar da ita da halakata da zaayi don tabbas Fatima bazatayi kisan Kai da gan gan ba" Mikewa tsaye yayi Yana nazarim shawarar da zuciyarsa ke bashi Amma ba Sai yankewa kansa shawara Kai tsayeba batare da ya samu amininsa ya fada Masa ba,tunda wanan abu ya faru Sai yanzun ya tuna da doctor Ahmad amininsa da suka taso tare sukayi makaranta tare.....kallon agogo yayi yaga karfe Tara da rabi na dare,dare be wani yiba ya Mike da sauri ya zuri key din motarsa ya fice... ******** Zaune suke a parlor yarima Yana korowa Ahmed labarin abinda ke faruwa cikin damuwa da tashin hankali,shi kansa Ahmad ya furgita da Jin wannan lamari dikda yasan da mutuwar na habib don har gaisuwa yaje,dukansu shiru sukayi a parlorn na tsawan lokaci sanan Ahmad ya Nisa yace "friend banaso ka saka kanka cikin matsalar da bazaka fitaba zuciyarka ta rigada ta makance da soyayyar wannan yarinyar da ka dauki yarda da'ri bisa da'ri ka Bata,bakada wata masaniya Akan wani Hali nata na boye sanan bakada tabbacin tanada gaskiya a wanan lamarin" Kallonsa kawai yarima yayi sanan ya kauda kansa yace"friend wallahi tallahi ko kaffara bazanyiba nasan Fatima ba dagangan tayi kisan Nan ba,Ni abinda nake gani wanine ya sata tayi kisan Nan ko Kuma ta taka sahun barawo" "Ta Yaya zata taka sahun barawo a guest house na gidan sarauta kabir ka rinkayin abubuwa da tunani fa yadda akayi ta shiga gidan shine babban kalu bale shawarar da Zan baka shine ka fita lamarin yarinyar Nan da ta taso gidan marayu yaran dake tashi su Zama terrorist a kasa Ni Ina guje maka saka kanka a matsala,babbar matsalar da zaka fuskanta da iyayenka na ka guji shariar Dan uwanka ja jini ka marawa bare baya yarinyar da baasan asalinta ba kadau son duniya ka Dora Mata" Girgiza Kai kawai yarima keyi don ya Dade da sanin Ahmad matsoracine dalilin haka yasa yakiyin course din lawyer a cewarsa hatsarine"bazan juyawa Fatima baya ba bayan da can banyi Mata hakanba Ni Zan tsaya Mata Koda duniya zata juya Mana baya nida ita" A furgice Ahmad keyi Masa kallon tuhuma da alamar tambaya,gira daya khabir ya daga Masa yace "yess Zan tsaya Mata Koda zaa kashemu tare zanyi jihadi Zan sadaukar da komi nawa dan farin cikin marainiyar Allah " "Lallai kasamu matsala kabir ,saika tanadi amsoshin da zaka baiwa Mai martaba da mama babba da mama karama,sanan ka tanadi audugar da zaka toshe kunnenka da ita akan zagin da zakasha a idon duniya,sanan katanadi kalaman da zaka fadawa alkali Dan Kare wadda aka Kama da kisan Kai wadda akwai kwararan hujjoji da suka nuna cewa itace tayi kisan kan Nan ciki ko harda na'urar computer " Babu fargaba babu wani tsoro yarima yace"Kaine wadanan abubuwan da ka lissafo zasu dama babu abinda zai dameni matukar Zan Kare hakkin Dan Adam " Murmushi Ahmad yayi yace "kafara bani tausayi Anya baka samu matsala a kwakwalwarka ba kuwa sanadiyyar wanan mutuwar ta Dan uwanka?" Haushine da takaici ya lullube yarima ya Mike a fusace ya kwashi makullansa yayi hanyar fita Ahmad ya bisa da kallo Yana girgiza Kai ya fice.... ******* Mama babba CE zaune tare da mahaifiyar kabir a parlor bayan sun Gama karin kumallo Wanda dabiar gidance da safe tare suke karyawa kowace mace da yatanta waje daya, "Nikam tun jiya tunda Yaya kabir ya fita da yamma bincike be dawoba har yanzun banganshiba gashi ko abimci bana ganin yanasawa a bakinsa tunda Yaya habib ya rasu"cewar afnan karamar kanwarsu gaba daya, Mama babba CE tace"nikaina tausayin kabir nakeyi domin Yana cikin damuwa na rashin Dan uwansa,ko jiya daya shigo naga dik ya rame yadanyi duhu,nadai sanar Masa da abinda muka xartar Kuma ya amsa nasan insha Allah zai tsaya Akan shariar Nan tunda gobe zaa mikata kotu " "Ai Yaya kabir akwai kokari akwai fasaha nasan dik yadda zaibi yayi nasara a shariar Nan zaiyi,insha Allah Sai an kashe Mana yarinyar Nan da tayi kisan Nan" Itadai mama karama batace komiba Sai Binsu takeyi da kallo batare da tace wani Abu ba, Mama babba ta sauke ajiyar zuciya tace"ai dik Wanda ya kashe habib Sai an kasheshi ko Dan gidan uban waye a garinan" Suna cikin wanan hirar yarima Kabir ya shigo,dik abinda suke fada tun daga farkon hirarsu ya Gama sauraronsu yazone da niyyar fada musu ya janye Akan shariar su nemi lawyan gwamnati Amma Sai wata zuciya ta hanesa da hakan nan da Nan ya zartar da wata shawarar a zuciyarsa....... *Muje zuwa* *SLIMZY🥰✍🏻*[ *🌩ANYI WALK'IYA.....🌩* *💡 HASKE WRITERS ASSOCIATION💡* *NA SLIMZY* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata Faty D'an maliki* 05 Nesa kadan dasu kabir ya nema ya zauna sanan duka iyayensa daya bayan daya ya gaggaishesu suka amsa cike da kulawa sanan Shima kannensa dake gefe suka gaidasa ya amsa, Shiru ne ya biyo baya kusan minti goma babu Wanda yace komi al'adarsu CE haka na rashin magana Koda kuwa dukkansu sun hallara a waje guda kowa Yana ji da irin tasa sarautar, Mama babba CE ta kalli gefen wajen da yake zaune ya tankwashe kafa ya Lula cikin duniyar tunani itace ta fargar dashi ta hanyar jeho Masa tambaya "Wai nikam kabir jiya bakazo ka sanar Dani halin da ake ciki ba domin na Matsu da Inga karshen yarinyar Nan" Da'go kansa yayi ya maida dubansa gareta sanan ya dukar da kansa cike da natsuwa yace "mama wallahi jiya bandawo gida da wuri bane shiyasa banzo wajenkiba mun tattauna,ki kwantar da hankalinki komi na tafiya yadda ya kamata insha Allah mune zamuyi nasara a wanan tafiyar domin na tabbatar da wanan yarinyar batada wata hujja da zata nuna cewa ba ita tayi kisan ba,sanan babban hujjarmu shine ta amsa da bakinta tayi kisan" Dagowa mama tayi da sauri tace"Wai nikam wanan yarinyar Yar gidan uban waye?waye babanta a kasar Nan?meta taka da tazo har cikin gidan sarauta tayi kisan Kai?lallai zata da'n da'na kudarta saitayi danasanin zuwanta duniya ko waye ubanta" Shiru yayi yarima batare da yace komi ba Yana Wasa da yatsunsa,hajiya babba ta Nisa ta Kara cewa "ansamu labarin iyayenta?waye ubanta?lawyoyi nawa suka dauka?" "Har yanzun baasamu labarin iyayenta ba don har yanzun babu Wanda yazo police station din da maganar" Girgiza Kai kawai mama tayi tace"waya sani ko karuwa CE"....da sauri yarima ya da'go Kai ya kalleta domin kalmar ta daki zuciyarsa Nan da Nan yaji ransa ya baci,fatimansa ake jifa da kalmar sunan karuwa?....kallon yadda ya da'go Kai mama tayi tace "ehh babu mamaki ko karuwarce don zaa iya hada Baki Ayi komi dasu zasu iya Saida ransu saboda neman suna,babuko tantama kudi aka Shaka Mata aka hada Baki da ita don ta kasheshi!!!!.....to wallahi yadda ta kasheshi Sai an kasheta karuwar banza" Zumbur yarima yayi ya Mike idanuwansa jajir zuciyarsa na tsananin harbawa sauri da sauri bazai iya jure sauraron wadanan mugayen kalmomin da ake jifan Fatima dashiba domin Fatima baiwar Allah CE.... "Mama Bari inje akwai binciken da nakeso in cigaba da gudanarwa domin kinsan gobe zaa Mika takaddar tuhumarta kotu jibi Kuma zamu shiga to banida sauran lokacin da Zan tsaya ya kamata in shirya komi kafin jibin" Jinjina Kai mama babba tayi cike da gamsuwa da kalaman yarima tace"Allah ya bada saa kabiru" "Ameen mama"ya juya da sauri ya fice a parlorn....Yana tafe Yana sakawa da warwarewa yadda zai bullowa wannan matsalar,Anya ba tunanin da ya bullo masa dazun zaiyi Amfani dashi ba?...Ina zai samu barrister Abdul da matarsa barrister hauwa u?tabbas su ya kamata ya nema domin sune zai kaiwa kukansa su share Masa su rufa Masa asiri su tsayawa Fatima batare da kowa yasani ba, Jikinsa har rawa yakeyi ya Ciro wayarsa ya zauna cikin mota ya shiga scrolling contacts dinsa hankali a tashe yake neman number barrister,idanuwansa ya rufe ya duba contact yafi sau ashirin be ga contact dinba Sai da ya fidda ransa da ganin contact din sanan ya gani barrister.A. yayi Masa saving dashi Nan da Nan yayi dialing cikin saa ta shiga.... Daga can bangaren aka dauka "Ranka ya Dade barrister khabir Allah ya ja kwana dama kana duniya?"cike da barkwanci yayi maganar, Dan murmushin gefen kumatu yarima yayi Wanda hakan be hana dipple dinsa shigewa ba yace cike da kasaita "banason shakiyanci" Dariya sosai barrister Abdul yayi yace "badai ka kirani ka fadamin aurenka ba don nasan inba aure zakayiba bazaka nememuba barrister Dan rabona dakai tun shariar da muka gabatar last 2 years da muka nemi a gajin fasihin barrister" Cikin kosawa da magana yarima yace"yanzun dik mu ajiye wanan maganar,nakira ne saboda wata muhimmiyar bukata data tasomin Wanda nasan insha allahu babu Wanda Zan tunkara da maganar Nan ya tsayamun idan ba kaiba" Dan natsuwa barrister Abdul yayi yace "to Allah yasadai lafiya,meyafaru ne ranka ya Dade?" Ajiyar zuciya yarima yayi yace "yaushe zansameka a gida kaida madam?" "Ranka ya Dade bàma gari gaskiya"Saida gaban yarima ya Yankee ya Fadi, "Amma yau insha allahu zamu biyo jirgin karfe hudu nida madam zamu dawo gari,zuwa bayan ishai zaka iya zuwa mu tattauna matsalar" Wata sassanyar ajiyar zuciya yarima ya sauke tare da hurar da iska a bakinsa yace"alhamdulillahi Allah ya kaimu" "Ameeen" Sukayi sallama..... Motarsa ya tada da sauri ya tada kura ya fice daga gidan a guje, ******* Gidan amininsa Ahmad ya nufa,ya tarar dashi Yana Shirin fita aiki ya shirya tsaf cikin shigarsa ta suits hannunsa dauke da rigar doctor's Fara Kal yanata sauri,yarima ya shiga,"ah ah ai Ina Shirin yau inje bikonka ne tunda jiya daga shawara naga kayi fushi saboda soyayya ta rufe maka Ido kana nema kajawa kanka matsala" Kujera ya nema ya zauna ya Dafe kansa batare da yace wa doctor komiba, Doctor ne cikin tsokana yace"kaifa miskili ne ayita magana kanajin mutane ga sarauta da kake fama da ita itama ta taru tayi maka yawa" Dan tsaki yarima yayi yace "nasamo mafita" Shima Ahmad da sauri ya nemi waje ya zauna Yana fuskantar yarima, Da'go rinanun idanuwansa yayi ya sauke akan doctor Ahmad sanan ya Fara magana cike da kasaita fuskarsa daure tamkar be taba murmushi ba "na janye Akan tsayawa Fatima sharia,nakira barrister Abdul dazun Zan dorasu su biyu akan shariar shida matarsa barrister hauwah,nasan insha allahu zasu tsaya Mata Kuma zasuyi nasara!!!" Hmmmmm"ta Yaya zasuyi nasara kana nufin kafisu iya gudanar da shariah ne?sanan ta Yaya zasuyi nasara akan shariar kisan Kai?shariarda duniya ta shaida itace tayi kisan?" "Dik wanan ba damuwa bane inada tabbacin barrister hauwa matar Abdul ta iya shariah tasan kan komi sanan macece dik yadda zaayi ta bincike Fatima zatayi zanbata tips akan komi yadda bazaa samu matsala ba" Girgiza Kai kawai ahmad yayi yace "to shikenan Allah ya bawa Mai rabo saa,sanan ka kiyaye kada asirinka ya tonu Dan idan asirinka ya tonu kasan sauran a masarauta" Murmushi kawai yarima yayi ya kwantar da kansa jikin kujera yace "kaidai jeka aikinka kawai ka barni a Nan inaso inyi nazari" Dage kafadarsa🤷🏻‍♂ doctor yayi ya juya yace "saina dawo" "Ok"kawai yarima yace tare da runtse idanuwansa,ya fada duniyar tunanin Fatima.... ******* "Babban bala'i Yana Shirin tunkaromu hajiya,ko kinsan Fatima Tana hannu?sanan ta tabbatarwa da hukuma cewa itace tayi kisan Kai?" Dafe kirji hajiya tayi hade da kidimewa tace"tabbas Dole inbar garin Nan domin kuwa kasan yadda akayi Fatima tabar gidan Nan,yanzun Ana shiga kotu zaa bukaci Fatima ta Fadi ita wacece cewa zatayi ita Yar gidan marayu CE kaga kuwa Dole a nemomu,Dan Dole a kiramu mune masu kula da gidan marayu" Tagumi haruna yayi ya shiga girgiza Kai "lallai muna cikin bala'i Amma shawarar da zanbaki itace kada mu gudu hajiya" Zumbur hajiya ta Mike Tana kada Kai cike da masifa tace"me kake nufi haruna?kada mu gudu mu tsaya a kashemu?mu tsaya Fatima ta tona Mana asiri ta fadawa duniya abinda ake aikatawa a gidan marayu?hukuncin da zaa Yanke Mata mu a Yanke Mana kenan ,to kaga idan zakaje kabar jirana" Girgiza Kai haruna yayi tare da kasa da murya yace"hajiya kwantar da hankalinki kiji,inaso kiyi tunani kiyi aiki da hankali,idan muka gudu aka tsare Fatima ta Fadi gaskiya to tabbas komi Daren dadewa Sai ankamamu,hotonmu zaayi yawo dashi a fadin jahar Nan domin kamar munyi fada da gwamnati ne sanan kada ki manta yaron da ta kashe jinin sarautane zaa dauki mummunan mataki akanmu,Abu daya ne idan Fatima ta tona asiri muce bamu Santaba bamu Taba ganinta ba dik maaikatam gidan Nan zamubi mu rufe musu Baki sanan kinsan ko sauran yara bakowa yasan Fatima ba saboda Bata shiga harkar jamaa sanan Abu na gaba kawarta zamu boye bilkisu,shikenan mun rufawa kanmu asiri" Tunda haruna ya Fara bayani hankalin hajiya ya Fara kwanciya tabbas ya kawo shawara hakan zaayi,neman waje tayi ta zauna tace "tabbas maganar da kayi Akan hanya take...idan ba haka ba to wallahi zaayi *WALK'IYA* asirinmu zai tonu asirin kowa ma zai fallasa" "Hakan zaayi"...Nan suka cigaba da kulle kullensu a inda suke Zama can baya wajen kitchen.... *****"Bilkisu ya kamata ki daina tada hankalinki Akan batan Fatima domin Fatima ta tafi da wuya muganta,Dan hajiya tace tunda aka fita Dasu xana jarabawar jamb da aka Gama baasan inda tayiba sunyi nema harsun gaji" Fuskarta jike da hawaye tasa tsumman zaninta ta share hawayenta ta maida dubanta gareta tace "Maryam kenan a cewarsu hajiya ba,Amma su sunsan inda take,komenene yasamu Fatima sune sanadi Allah ya saka Mata sanan Allah ya kawo karshen wanna masifar dake faruwa Allah ya kawo sadin da zaayi *WALK'YA* halin kowa ya bayyana asirin kowa ya tonu Allah yayi Mana sakayya ,saboda muma baason ranmu kaddararmu ta Fado a Zama marayuba"kuka sosai bilkisu takeyi Tana Jin radadin rashin aminiyarta Yar uwarta Fatima.... Batare da Maryam ta fahimci komiba a kalaman bilkisu ta cigaba da lallashinta da ban hakuri Akan ta cire Fatima a zuciyarta tayi Mata addua.... ******** Zaune yake bayan sallah ishai a babban parlorn gidan barrister Abdul,bakajin karar komi Sai karar fanka Sai Kuma bayani da yarima yake korowa barrister da matarsa har ya Gama, Tabbas sun jinjinawa al'amarin Kuma jikinsu dik yayi sanyi da Jin labarin da abin ya faru Akan Yar gidan marayu ne,barrister hauwah CE ta Lula duniyar tunani,tabbas wanan al'amari akwai rikitarwa,tanajin karfin gwiwa akan wanan shariar Koda yarinyar ta aikata,sanan wannan shariar tamkar jihadi CE fatanta Allah ya Basu saa.... Barrister Abdul ne yayi ajiyar zuciya yace "ka kwantar da hankalinka barrister Ni da madam insha allahu zamuyi iya bakin kokarinmu wajen shariar Nan zamu tsaya bakin Rai bakin fama wajen yin wanan jihadin,babu wata alfarma da xaka nema a wajenmu wadda bakasameta ba barrister".... Gyara Zama barrister hauwa tayi matar Abdul tace"barrister kayi addua kawai Amma insha allahu Koda Fatima ita tayi kisan Nan zamu samu hanyar da zata kubita da yardar Allah,insha allahu gobe nida oga zamuje kotu mukai takaddunmu mu shigar da sunayenmu a matsayin wadanda zasu tsayawa Fatima a sharia" Jinjina Kai yarima yayi cike da Jin Dadi yace "Allah ya saka muku da alheri Allah ya bamu saa" "Ameen"suka hada Baki dukansu sanan barrister Abdul ya kalli matarsa yace "gobe idan mun bar kotu zamuje station din kece Zaki zanta da Fatima cikin hikima da wayau inaso kiyi amfani da kwakwalwarki da fasahar da Allah ya baki wajen yin tambayoyi da ita" Jinjina Kai hauwah tayi tace"insha allahu bazaa samu matsala ba" "Allah ameen"suka hada Baki ,Nan suka cigaba da tattaunawa..... ****** Washe gari barrister Abdul da madam dinsa sukaje kotunda aka Kai takadda,yarima yayi musu Tex massage ya sanar dasu Shima Yana wajen,aikuwa Basu Bata lokaciba sukaje suka gabatarwa kotu abinda ya kawosu,Nan aka shiga kallon kallo kowa a wajen kallonsu yakeyi a matsayinsu na masu tsayawa wadda ake tuhuma da laifi,Nan aka rattaba sunansu tare da sanar musu da gobe zaa gudanar da shariah karfe goma, Yarima tamkar besansuba haka yayi acting sanan ya mikawa barrister hannu suka gaisa suka wuce suka bar kotun Shima yarima Yana barin wajen gida yayi.... ***** A babban parlorn sarki ya tarar da iyayen nasa duka ya tsugunna har kasa ya kwashi gaisuwa sanan ya gabatarwa da Mai martaba da iyayen nasa yadda akayi, Mama babba Allah Allah takeyi tayi magana jikinta har rawa yake wajen tambaya"kabir Yaya ansamu masu tsayawa almurar yarinyar can kuwa" Batare da want shakka ba yarima yace "ehh ansamu mama,Mata da miji ne ma su biyu xasu tsaya Mata" Jikinta na tsuma tace "what?kana nufin yanzun da lawyoyi biyu zaka fafata a kotu?" Jinjina Kai yarima yayi ,Sai a sanan Mai martaba yace "ai yaron naki gwarzone a wanan fannin ki kwantar da hankalinki,bazaa samu matsala ba" Jinjina Kai yarima yayi yace "insha allahu ranka ya Dade" Itadai mama babba batace komiba Sai rudani data shiga da tsananin tunanin yadda zaayi a tsayawa Mai laifi bayan an tabbatar matada iyayen yarinyar basu bayyana ba.... ***** Koda aka fito da Fatima don ta gana da barrister hauwa ,data fito tayi mamakin ganin kyakkyawar mace Fara tas da bazata wuce Shekaru ashirin da shida ba a duniya ,Fatima Tasha jinin jikinta data fito cike da fargaba take saidai ganin matar nayi Mata Dan murmushi yasa tadan samu relief dikda bawai ta kwantar da hankalinta bane tsayawa tayi kikam a kanta Tana Kare Mata kallo, Murmushi barrister hauwa tayi ta nuna Mata gefenta tace "zauna Mana Fatima"samun kanta tayi da kasa yi Mata musu ta zauna a darare.... Sunana barrister hauwau muazu Amir nice lawyer da Zan tsaya Miki a shariah nida mijina barrister Abdul Amma shi Yana waje shi ya turoni wajenki don in zanta dake Akan abinda akeyi Miki kazafi dashi ake zarginki wato kisan Kai!!!" Shin menene gaskiyar lamarin?already hauwa ta seta recorder dinta Wanda zata gabatarwa da barrister yarima ya saurara, Girgiza Kai Fatima tayi cikin sanyin murya tace"nice na kasheshi ba kazafi bane ba Kuma zargi bane" Gyara Zama barrister tayi tace "haba kanwata Fatima?banaso ki rinka kirkirowa kanki laifi kina dorawa kanki koda kece kikayi kisan Nan be kamata ki rinka amsawa haka ba cike da kwarin gwiwa shin kinaso a kasheki ne?hukuncinki fa kisa ne" Juyar da Kai Fatima tayi Nan da Nan hawaye ya shiga zarya a idanuwanta tace "dama kun fitar da hannunku daga wanan shariar,Kun mikani ga hukuma a kasheni a matsayina na Mai laifi sanan Koda an kasheni banida wani Amfani a wanan duniyar dama ,niba kowa bace face marainiyar da aka tsinceni a bakin kwata wadda batada wani gata a wanan duniyar" Kalamanta sun taba zuciyar barrister Nan da Nan jikinta yayi sanyi tace"Fatima ki daure ki fadamin yadda akayi kikayi kisan Nan da dalilin da yasa kikayi kisan Nan ninayi Miki alkawarin kubuta,sanan nida mijina mu zamu zame Miki gata a wanan duniyar" Girgiza Kai Fatima tayi tace"nagode da karamci da kauna nasan dik kaunar da kukemum Bata Kai ta mutum daya da yakemun ba a wanan duniyar Shima hakuri zaiyi ya Bari a kasheni"ta fashe da kuka Mai ban tausayi, "Kiyi shiru Fatima kidaure ki sanar Dani dalilin dayasa kikayi kisan Kai,idan wanine yasaki kiyi kisan ki sanarmun" "Babu Wanda ya sani nice kawai nayi kisan Dan kaina,banida sauran amsan da zanbaki"... Dik yadda barrister hauwa tayi Akan Fatima ta sanar matada yadda abin yafaru Taki,tayi iya kokarinta Amma abun yaci tura,Sai kuka kawai da Fatima ke rerawa,hakanan lokacin da aka Basu yayi,barrister tanaji Tana gani haka aka tasa keyar Fatima aka wuce da ita.... Jiki a sanyaye ta fito tasamu mijinta a mota yaja motar,a hanya take sanarda shi yadda sukayi da Fatima, Waya yasa yakira yarima ya sanar dashi yadda barrister sukayi da Fatima hankalinsa a tashe yace gashinan zuwa...... *Ku biyoni don Jin yadda zata kasance...ya wanan baudaddiyar shariar zata yuwu?*.... *SLIMZY✍🏻🥰 🌩 *ANYI* *WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS* *ASSOCIATION* 💡 *NA:SLIMZY✍🏻* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga* *k'awata faty D'an* *maliki* 06 Yarima Wanda ke zaune a dakinsa bayan ya dawo kotu Yana tunanin yadda shariah zata kasance,ya Mike a fusace Jin bayanin da barrister Abdul yayi mishi na Fatima Taki Basu wani bayani Yana fitowa gidansu yayi cikin tsananin tashin hankali ya Isa gidan, A parlor ya tarar dasu da alama Basu Dade da shigowa gidan ba,suna zazzaune barrister hauwa Tana Yan rubuce rubuce a takaddarta,bayan sun gaisane barrister ta gabatar mishi da recording din muryar Fatima na tattaunawa da sukayi ,Dafe kansa kawai yayi bayan ya Gama dauraren komi Nan da Nan hankalinsa yayi kololuwar tashi ga wani haushin Fatima da ya ziyarci zuciyarsa a Karo na farko, Da'go rinanun idanuwansa yayi ya saukesu Akan barrister Abdul dakyar yake motsa labbansa yace "barrister me yarinyar Nan take nufi?ta zabi a kasheta Ni in shiga uku Koh?me take nufi?" Dan murmushi barrister Abdul yayi yace "kadaiji abinda take fada sanan barrister ta tabbatar mun da yadda take maganar cike da confidence Akan itace tayi kisan shi zai baka mamaki" A fusace yarima yace "to idan ma itace tayi kisan meyasa bazata fada Mana dalilinta nayin kisanba ko kuwa Ana kisa Babu daliline?idan wani ne yasata tayi kisan ta fada Mana ta tsaya Tana wahalar damu,fatyma na neman in rasa farin cikina a Karo na biyu,Fatima na nema tasa zuciyata ta buga in mutu inbarta cikin kunci da masifar da take ciki,Fatima Taki tausayawa kanta ta tausayamun Nima"zuwa yanzun yarima yakai karshe cikin tsananin damuwa da tashin hankali....hannu yasa ya Dafe kansa zuciyarsa na harbawa tamkar zata faso kirjinsa ta fito,da yanada dama da ya cireta cikin zuciyarsa,Amma ta Yaya hakan zai kasance bayan Fatima itace jinin dake yawo a jikinsa har zuwa cikin zuciyar tasa?runtse idanuwansa yayi Yana tuna abubuwan da dama dayasa bazai iya barintaba... Tunda ya Dafe kansa,barrister Abdul da madam dinsa suke kallonsa cike da tausayawa barrister hauwa CE ta Nisa tace "Ka kwantar da hankalinka yarima insha allahu Fatima zata kubuta da yardar allah" Da'go kansa yayi cikin kosawa yace "ta Yaya" "Addua zamu dukufa yi sanan mu hadu a kotun gobe" "Shikenan baristers nagode allah ya kaimu goben,Ni zanje gida" "Ka tsaya muci abinci Mana,don daga ganinka bakada lokacin abinci ma"cewar barrister Abdul, Girgiza Kai kawai yarima yayi tare da sauke ajiyar zuciya yace "naci dazun a gida Bari inje kawai" "To shikenan Sai Allah ya kaimu goben" Gyada musu Kai kawai yayi ya juya ya fice jiki a sanyaye dukkansu kallo suka bishi dashi Mai cike da tausayawa... ****** Washe gari da sassafe yarima yayi shirinsa tsaf cikin kananan Kaya Riga jeans da polo shirt masu kyau Wanda sukai matukar amsar jikinsa,Amma hakan be hana Rama fitowa a jikinsa ba fuskarsa tayi fayau kamar yayi zawo da amai, A can fadar sarki ya tarar da a halin gidan dukansu,bayan ya gaida iyayen nasane sukayi Masa adduar samun nasara sanan kannensa biyu suka fada Masa bukatarsu nason zuwa kallon shariar,jinjina musu Kai yayi a shirye suke Nan da Nan aka bada Motoci da matakan tsaro wadanda zasuyi musu rakiya zuwa kotun.... ******* *COURT* Mutanene cike da kotun har waje wadanda keso suga yadda wanan shariar zata kasance, Kallo daya zakayima kotun, ka tabbatar ba karamar Sharia za'ayiba ,duba da yadda take cike makil da da'n adam..... *Courtttttttt* Kowa ya mike a lokacin da Alkali abubukar assadiq yashigo kotu .... Bayan ya zauna sannan kowa ya Sami matsugunni ya zauna ... Yamai girma Mai shariah ayaune ranar 28 ga watan June , kotu zata saurari karar da akeyi na Fatima Zahra wadda ake zargi ta kashe Dan sarki yarima habib Kuma babban Dan siyasa, Bayan anmikama alkali takaddun shariah ya Kara gyara gilashin da ke manne a idonshi Wanda ya fiddo da aynihin kamalar sa da dattako na shekarunshi.... "Koh lauyoyin Wanda ke Kara da wadda ake zargi suna kotu?". A hankali Kabir ya Mike cikin kayanshi na lauyoyi wadda suka mutukar amsar fatar jikinshi ,ya gyara rigar lauyoyinshi yace cike da dakiya da jarimta "Yamai girma Mai shariah sunanan Barr Kabir Mahmud nine lauya, Wanda zai tsayama marigayi yarima habib"yadan rankwafa alamar girmamawa Cikin natsuwa Barr hauwa muazu ta Mike cike da kamala sannan tace" my Lord sunana Barr hauwa muazu nice lauyan Mai Kare wadda ake zargi tare Dani akwai Barr abduljabbar "...shima ya rankwafa alamun gaisuwa sannan suka zauna ...... Yan rubuce rubuce alkali yayi sannan yace "Koh lauyan Wanda aka kashe nada bayani" Itadai Fatima tunda aka shigo da ita aka tsaidata a inda ake ajiye masu laifi idanuwanta a kasa suke yayinda zuciyarta keyi Mata lugude,Sai yanzun ne da alkali yayi wanan tambayar ta da'go kanta ta sauke idanuwanta akab yarima take zuciyarta tayi rauni Jin abinda yace "Inadashi Mai Lord" cewar barrister kabir..... " Kotu na sauraranka" . "Inaso kotu ta bani dama domin in yima wadda ake zargi Yan tambayoyi"... "Kotu ta baka dama Barrister" A hankali ya taka cike da natsuwa ya Isa wurin da ake tuhumar masu laifi sannan ya kalli fatyma Zahra ....wani Abu yaji ya sokesa ga katon zuciya tamkar kibiya,da kyar ya tattaro dik wata natsuwa tasa dake neman guduwa daga jikinsa ,ganin yadda fatyma tafita hayyacinta ,cike da jarumta yace "Kotu zataso tasan sunanki????" Kamar bazatayi maganaba , sannu a hankali ta daga siraran lips dinta tace ,"sunana fatyma Zahra"a takaice tayi maganar Sosai ya Kara daurewa tare da Shan kunu tamkar be taba dariya ba a rayuwarsa sannan yace, "Iyeyenkifa?" "Banidasu" ta fada a takaice , "Toh inane gidanku? " Kallonshi tayi sannan tace" bamuda gidan da yawuce gidan marayu" , Gabansa ne ya cigaba da dukan uku uku ya hadiye miyau Mai kauri sanan yace "Toh malama fatyma kina Ina ranar 20 ga watan June Dede karfe 2 na talatainin dare? Gabantane ya yanke ya Fadi sanan ta Runtse idon ta Tana matso wasu zafafan hawaye tace, " Ina guess house na gidan sarki" Nan da Nan kotu hayaniya da maganganu sama sama suka Fara tashi, aka buga table tare da umarta kowa yayi shiru. Khausar dake gefen afnan itace ke jehowa Fatima Zahra kallon tsana tsantsa Wanda takeji da tanada iko ta Mike ta shaketa saita kaita lahira, "Toh me ya kaiki guess house din?" "Bakomi" tafada a takaice "Kenan wannan na nuna kinada sa hannu a kisan da akayi ?" "Objection my Lord, ya kamata Barrister ya gyara salon tambayarshi, yadena cusama wadda ake zargi laifi domin har yanxu baa tabbatar da ita a matsayin Mai laifiba,nagode ya maishariah" "Barrister ka gyara salon tambayarka" "Nagode ya Mai shariah " "Malama fatyma kotu zataso taji adede lokacin da kike guess house din me kikeyi?ko me kikajeyi?" "Kamar yadda nace Nina kasheshi don Allah Nima a kasheni kawai" Hayaniyace ta kwaure a koton kowa na fadar albarkacin bakinshi ... Sai da aka bubbuga gudamar lauyoyi sannan aka umarci kowa yayi shuru..... "Nagode ya Mai shariah anan na kawo karshen tambayata"ya juya zuciyarsa na tsananin bugawa cike da furgici Wanda ya tattaro jarumtarsa a fili kamar baya cikin furgici ya koma wajen zamansa ya zauna. Bayan Yan rubuce rubuce alkali ya tambaya"Koh lauyan Wanda suke Kare wadda ake Kara sunada abin cewa?" "Inadashi ya Mai shariah ". "Kotu na saurarenki" . Cike da nutsuwa da jarumta ta taka har inda fatima take sannan ta gyara zaman rigar lauyanta,cikin natsuwa ta kalli fatyma tace...."malama fatima ki kwantar da hankalinki, Nan kotun adalci ce Kuma kotu bazata yanke Miki hukunciba har sai ta tabbar da ke Mai laifice, Ki nutsu kiyima kotu bayanin abinda kika sani". Shuru tayi na wasu Yan mintuna, sannan ta share hawayenta Wanda suka Zama abokanan idonta ... "Nima bansan komiba, Abinda kawai zance shine Nina kashe yarima" Dafe kai🤦🏻‍♀Barrister hauwa tayi ganin fatima Bata Bada hadin Kai . A hankali ta juya ta kalli alkali sannan tace" ya Mai shariah zanso kotu ta Kara bamu dama, domin nafahinci fatima Bata cikin kwanciyar hankalin. Da zata bada amsoshi,....inaso kotu ta bani dama domin Kara gabatar Mata da wasu hujjoji azama na gaba insha Allah,nagode my Lord" Bayan Yan rubuce rubuce alkali ya gyara glass dinsa sannan yace ,"duba da wasu Yan hujjoji kotu zata da'ge wannan Zama har zuwa ranar 4 ga watan July domin ciga da sauraren wannan shariah, sannan kotu ta bada umarnin a duba kwakwalwar fatima a tabbatar da ingancinta,sannan kotu tabada dokar aci gaba da tsare fatima har zuwa Zama na Gaba" " Courtttttttt....." Kowa ya miki sannan alkali ya fita, Hayaniya ce kawai ke tashi yayinda dik wani mahalukin dake cikin kotun Saida yayi zufa dikda fankokin dake aiki cikin kotun,jamaa ke tururuwar fita daga kotun Saida kowa ya Gama fita lauyoyi suka fito, Barrister Abdul da madam dinsa ne suke tafe hannunsa rike da rigar lauyoyinsa suka nufi motarsu, Yayinda yarima ya fito a hankali yake takunsa tamkar bazai takaba zuciyarsa cunkushe da bakin ciki ya nufi jerin gwanon motocin da suka rakosu Dantafiya gida,ta gabansa mota ta wuce ta prison wadda ke dauke da Fatima a ciki ,idanuwansu suka hadu waje daya yayinda ko wanne cikinsu Saida zuciyarsa ta harba,tausayin Fatima da soyayyarta suka Kara samun gurbi a zuciyarsa,haka aka fice da ita Yana tafe Yana tunaninta, Motar da kannensa biyu ke ciki ya shiga wanan karon,Yana rufe kofa kausar ta kallesa fuskarta cike da bakin ciki da takaici tace"Wai yaayah wacece wanan barrister din dake Kare shegiyar yarinyar Nan ?meye hadinta da ita bayan tafada cewa ita bakowa bace face tsintacciyar mage,wadda ke zaune gidan marayu?" Kallonta kawai yayi yace "bansaniba Nima" Tsaki kausar tayi a Karo na biyu tace"aikuwa Tana tare da kunya in Allah ya yarda Sai anyiwa shegiya kisan gilla" Da sauri yarima ya kalli khausar ,Sai Kuma ya juyar da kansa ya basar batare da yace uffan ba, Ita kuwa afnan dik maganar da suke batace komiba Sai daddana waya takeyi batare da tace uffan ba, har suka iso gida khausar na bambami... ***** "Turkashi ,lallai akwai wata makarkashiya a wanan shariar,domin Babu yadda zaayi ace matsiyaciya wadda batada kowa ace ansamu wadanda suka tsaya Mata a shariah saidai idan tanada manyanta wadanda suka tsaya Mata tayi kisan shine suka samu lauyoyi suka Basu kudi suka tsaya Mata a shariah,to wallahi wallahi asirin kowa saiya tonu Kuma jinin da'n dana haifa bazai tafi a iska ba dolene mine zamuci shariar Nan" Tunda mama ta Soma jaraba Tana maganganunta yarima bece ko kanzil ba shiru yayi Yana saurare, Khausar dake gefe tace a hasale"Wai babu kunya babu tsoron Allah sabida yarinyar Nan shegiya wadda akayi cikin shegehta a waje tasan abinda ta taka saicewa take Wai ita ta kasheshi a kasheta kawai,ita Kuma shegiyar lauyar Sai cewa tayi Wai Bata cikin hankalinta yasa take amsa wanan maganar dayake mahaukaciya CE" Yarima Sai a sanan yayi magana yace "basuda wata kwakkwaran hujja mama,ki kwantar da hankalinki mukeda nasara ai zamu hadu a Zama na Gaba" Jinjina Kai mama tayi takai takawo tace "zansa a hadamun tafiya a shirya Motoci zanje guest house din zansamu securities da kaina sanan zaa kaini wajen yakubu Wanda keda alhakin kula da wajen a kunnamun computer Inga komi sanan zanbada umarni abamu komi q hannunmu don mu gabatarwa da kotu a yankewa tsinanniya hukuncin kisa,sanan kafin a kasheta ta tonawa wadanda sukasa tayi kisan asiri,sanan wadanan lauyoyin Sai sun muzanta a idon duniya" Dammm kirjin yarima ya buga Nan da Nan ya nemi natsuwarsa ya rasa Jin kalaman da mama babba tayi.... "Sanan Suma gidan marayun zasu da'n da'na kudarsu Dan ta jefasu a bala'i Dole bincike yaje garesu Dole su Fadi gaskiya,idanma a gidan marayun take idan ma baa Nan takeba Dole asirin kowa ya tonu" Shidai yarima zaune yake tamkar mutum mutumi,tamkar an dasashi,ya Lula duniyar tunani,meke Shirin faruwa?ya zaayi ya mallaki recording din yadda Fatima tayi kisa kafin mama tagani?Tabbas idan yaje guest house asirinsa zai tonu masarauta zata gane takunsa.... *Gyan gyan* *Muje zuwa* *SLIMZY🥰😍**🌩ANYI WALK'IYA.....🌩* *💡 HASKE WRITERS ASSOCIATION💡* *NA SLIMZY* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata Faty D'an maliki* 07 Mikewa tsaye yayi jiri na Shirin dibarsa da kyar ya tattaro natsuwarsa cikin dasasshiyar murya yace,"ki kwantar da hankalinki mama jinin da'nki Kuma da'n uwana bazai tafi a iska ba matukar inada Rai Sai naga bayan shariar Nan insha allahu kuma mune keda nasara" Jin jina Kai mama tayi tace "Allah yayi maka albarka,kuma wanan sanyin jikin da kakeyi Ina Lura dakai ka kaudashi nasan ba wani abubane face mutuwar Dan uwanka dake tabaka ,hakuri zakayi,sanan abinda zakayi kawai ka nunawa duniya cewa kana kaunar Dan uwanka shine jajircewa a wanan shariar wadda nasara a wanan shariar me saukine duba da sanin yarinyar ko wacece ba kowa bace face matsiyaciya wadda zatayi zuwan zomo duniya tazo a guje ta koma a guje,babban burina be wuce inga an sa Mata igiya a idon duniya an kasheta kamar yadda ta kashemun gudan jinina ba,dik duniya Babu hallitar Dana tsana kamarta wallahi summa tallahi na tsaneta saboda amfani da akayi da ita wajen yiwa Dana kisan gilla to yadda ta kasheshi itama bazata zauna a duniyarba" Kalmomin mama sun zamewa kabir tamkar wuta,dik jikinsa xafi yakeyi Masa Babu abinda ya Tsana sama da Jin wata mummunar kalma Akan fatimansa dikda abinda ta aikata babban laifine Amma yasan Fatima ba zata aikata wanan laifin Babu hujja ba, Maganar mama CE ta dawo dashi daga tunani"Wai Ni kam kabiru ko kasan wadanan lauyoyin da suke tsayawa yarinyar a kotu?" Da sauri ya dawo hayyacinsa ya girgiza kansa"ah ah mama" "Zansa ayimun bincike Akan kosu wayene Dan ba haka banza suka fito Saida ransu ba akwai abinda suka taka Kuma saina tabbatar da Ganin bayansu a wanan tafiyar" Jinjina Kai kawai yarima yayi Dan har ga Allah mama na tsananin bashi mamaki Koda yake Babu abin mamaki Dan yasan kowaye ita wajen son Kai, "Bari inje indan watsa ruwa mama" Ka'da Kai kawai tayi alamar amsawa ya Mike ya fice daga sasan mama babba,kansa tsaye yayi bangarensa kayan jikinsa ya rage sanan ya nemi gefen gadonsa ya zauna ya maida kallonsa ga dakinsa da yayi kura kaca kaca,tunda bala'in Nan ya faru baisa an gyara Masa dakiba ko ta kan dakin ma bayayi saboda halin da yake ciki, Kwanciya yayi rigingine ya zuro kafafuwansa kasa kansa na kallon fankar dakinsa dake kadawa a hankali,zuciyarsa ke ayyana Masa abubuwa da dama game da Fatima kaddara babu yadda Bata zuwama bawansa ga rashin gata ga babbar kaddara ta fada Mata wadda fitar da ita Sai allah.....Amma tabbas inhar Fatima nada sauran numfashi a duniya Sai ya zamar Mata gatan data rasa na rayuwar duniya.... Runtse idanuwansa yayi fuskarta ya hasko wani lokaci baya tanayi Masa murmushin Nan nata Wanda ya zame Mata tamkar dabiarta CE murmushi tace "da na cire Rai da samun gata a duniya Yaya yarima tunda na farka naganni a wanan yanayin Amma zuwanka rayuwata inasa Rai da Kai rahmane daga Allah zuwa gareni nasan inhar inadakai bazan yi maraicin uwa da uba ba ko yaayaah yarima?" Kafeta da Ido yayi Yana kallon yadda take motsa bakinta Tana magana Mai cike da hikima tamkar wadda ake fadawa, Itama kallonsa tayi Ganin yaki cewa komi Sai idanuwanta suka kawo ruwa tamkar zatayi kuka cike da shagwaba tace"Yaya kodai kafasa zamemun gatan da kayimun alkawari ne infara kukan maraici a Karo na biyu" Hannu yasa ya goge hawayen daya sauko a daga idanuwanta Yana girgiza Kai "harbada inhar Ina Raye Fatima bazakiyi kuka ba kada insake Ganin wanan kwallar ta sakko daga wadanan kyawawan idon" Kifta mishi Ido tayi Tana dariya kasa kasa...... Zumubur yarima ya Mike daga kwanciyar da yayi besan lokacin da ya tsinci kansa hawaye na gangaro masaba a fili yake furta "ya zaayi incika alkawarin Dana daukar Miki Fatima na harabada bazan Bari ki zubar da hawaye ba?," Kansa ya kifa a jikin bango Yana kuka tamkar mace Wanda tunda yake Bai taba zubar da hawayensa Akan wani abuba dik runtsi kuwa dik wahala Sai gashi yau Akan Fatima Yana kuka tamkar mace babban tashin hankalinsa hango Fatima da yakeyi Tana zubar hawaye a kotu Tana yiwa kanta ikirari itace tayi kisan Kai......kuka sosai yakeyi Wanda tunda abin ya faru besamu yayi irinsa ba...."inhar inada Rai Fatima bazakiyi kuka ba bazaki zubar da hawaye ba Ni Zan zame Miki garkuwa a rayuwa".....kuka sosai yakeyi jikinsa har rawa yakeyi,da sauri ya waiga kan wayarsa dake kan gado Tana ringing ,kafe wayar yayi da Ido Ganin bakuwar number CE har ta tsunke be ko motsa ba a Karo na biyu wayar ta Kara ringing... Takowa yayi ya dauki wayar ya Danna receive daga can bangaren aka Fara magana "ranka ya Dade daga Nan head quarter of police ake magana" Cikin dasashiyar murya yace "umhmm Ina sauraro meyafaru?" "Dama game da case din yarinyar da ake tsarone oga ya bada damar aje Ayi bincikenta a tabbatar da Yar gidan marayun CE?ko kuwa karya takewa hukuma?shine akace a sanar maka a matsayinka na lauyan wanda suke Kara,dik statement din da aka samu zaa sanar maka ranka ya Dade" "Ok badamuwa "shine abinda yarima yace be jira Mai Dan sandan zai fadaba ya kashe wayarsa domin dik yasan abinda Yan sandan Nan keso be wuce ace suna kokariba a Shaka musu kudi, Gadonsa ya haye yayi rub da ciki ya rufe idanuwansa ya cigaba da lulawa duniyar tunanin Fatima..... ******* Kafin Yan sanda suje gidan marayu labari yakai musu da zaazo bincike, domin haruna da kansa yaje station yaba wani Dan sanda cin hanci Akan dik abinda ke faruwa ya rinka sanar musu,Babu musu kuwa ya amince, Ba karamin tashin hankali daukacin maaikatan gidan marayu suka shigaba domin,manyan maaikata da kanana sunsan abinda ke faruwa Dan ana San musu nasu,Nan da Nan hankalin hajiya yayi kololuwar tashi ta rasa inda zatasa kanta,yayinda Shi kansa harunan baya cikin kwanciyar hankali.... Kaf yaran dake gidan marayu wadanda ke kwana wuri daya da Fatima aka tarasu tamkar masu assembly,hajiya CE ke magana da kakkausar murya "Ku tabbatar kunyi aiki da abinda muka fada muku,wallahi tallahi dik Wanda yayi kokari tona Mana asiri Sai ya fuskanci azaba,sanan bazamu kyaleba zamu bawa hukuma mutum ya tafi dashi a hada dashi da fatimar a kashe gabaki daya" Wuri yayi tsit Sai wurga idanuwa yara sukeyi batare da fahimtar meke faruwa ba,shasshekar kukan da akaji ne akafara waige waige Jin daga Ina kukan ke zuwa, Sakkowa hajiya tayi a hankali Tana taka takalminta Mai tudu Wanda ko da yaushe irinsa take sawa saboda rashin tsawonta har ta iso inda taga anbada fili an Mar matsa tsawaya tayi a gabanta Tana Kare Mata kallo yayinda yarinyar Ganin hajiya a gabanta yasa tayi shiru kamar anyi ruwa an dauke, Cire gyalen kanta hajiya tayi ta ratayeshi a kafadarta tace cikin daga murya"au munafuka kukan muna furci kikeyi mun?kekadaice kikeson kawo Mana matsala?to wallahi tallahi Ni halima sainayi Miki cikin da Kika kasa haifeshi matukar Kika kuskura Kika fallasa asirinmu ya tonu to wallahi kinsa kanki a bala'i bilkisu,ki bude kunnuwanki da kyau ki saurareni wallahi summa tallahi matukar kikayi gigin fallasa asirinmu kin shiga uku Dan saina kulla Miki sharrin da aka hadaku keda fatimar aka kasheku gaba daya matsiyata marasa asali" Ba karamin ciwo wanan zagin yayiwa bilkisu ba take ta da'go kanta Babu alamar tsoro a tattare da ita tace"ai bamu mukayi kanmu ba,Kuma Allah ne ya haliccemu Yana sane damu" Kyakkyawan Mari hajiya ta sauke a fuskar bilkisu Wanda Saida ta gigice kokafin tayi yunkuri hajiya ta rufeta da duka ta ko Ina Tana janta a kasa suka bar wajen.....dukkansu yaran ba karamin tsorata sukayiba da Jin kalaman hajiya na zaa kashe mutum sanan da hukuncin da tayiwa bilkisu a gaban kowa,Nan da Nan kowa ya shiga taitayinsa suka shiga watsewa..... Can wani daki Mai Nisan gaske cikin daji dajin gidan marayu hajiya ta wulla bilkisu ciki ta rufo kofar....tai tahowarta Dan fadan karfin Hali kawai takeyi ta Gama firgita da lamarin yarinyar Dan tsab bilkisu xata tona Mata asiri Dan mugun taurin Kaine gareta da kafiya. ... ******** Koda Yan sanda sukazo gidan marayu bincike tun daga kofar gate din gidan suka nunawa Mai gadi hoton yarinyar,sanin abinda zai biyo baya yace besanta ba, Dik Wanda aka nunawa hotonta Sai yace besanta ba cikin maaikata har akazo kan yara kowa aka nunawa hoton Fatima Sai gabansa ya Fadi Amma daya tuno kalmomin hajiya Sai yace besanta ba.....haka Yan sanda suka Gama zagayensu kaf basusamu wani labari game da Fatima ba suka koma sukayi station.... ******** Yarima ba karamin mamaki bane ya daure Masa Kai gameda labarin da yaji na cewa Wai Fatima ba Yar gidan marayu bace ta Yaya?to akwai wani kulli kenan a kasa sanan dolene ya nemi bilkisu don Jin cikakken bayani Akan abinda ke faruwa a gidan marayu,domin Dole bazata rasa sanin wani abuba idan har ya karyata cewa Fatima Yar gidan marayu CE to tabbas asirinsa zai Tonu zaa fahimci yanada dangantaka da ita,lallai mutane basu da imani wato saboda kaddara ta sameta yasa suka hade Baki sukace basusanta ba?Koko akwai wani Abu ne a kasa?....ajiyar zuciya kawai ya sauke tare da tattaro wayoyinsa ya fice .... ******* Mama babba CE cikin guest house na gidan sarki dik wani maaikaci dake gidan ya hallara a babban parlor dake floor na biyu,kafin kowa ya tsaya Sai sun kawo gaisuwa wajenta ko wanne cikinsa ya duri ruwa kowa da fargabar da yakeyi a zuciyarsa game da zuwanta Dan sun San halinta tsab zatasa a Kori mutum daga kan aikinsa, Shugaban gidan ta nema gabaki daya Shi yayi mata iso zuwa dakin da computocin gidan suke inda dik abinda ke faruwa na cikin gidan ake kallo ko meye mutum keyi na alheri ko sharri suna kallonsa, Rusunawa yayi sanan ya kawo gaisuwa ta amsa cike da Isa da izza irinta masu mulki, Kujeru biyu ya janyo musu ya goggoge sanan suka zauna ita da khausar dake gefe tanata Harare Harare.... "Abinda ya kawoni gidan Nan shine inaso ka tattaro mun dik wani bayani na abinda ya faru ranan da aka kashe habibu ka fitomin dashi in kalla sanan kabani Shi a hannuna Dan ya zame Mana hujja a kotu,abinda yasa nazo da kaina shine saboda sarki na Lura komi a hankali yake binsa sanan be bawa wanan shariar muhimmanci ba Niko tunda nice aka salwantar da da'na Dole in Mike tsaye dik yadda xanyi Inga jinin Dan Dana haifa be tafi a banza ba,shiyssa na bukaci a kawoninan dikda aikin ba nawa bane aikin kabiru ne Amma kabiru rashin Dan uwansa yasa bashida wani kuzari ,to shiyssa nayi tattaki da kaina" Rankwafawa yayi yace "toh ranki ya Dade yanzun zaa aiwatar da umarninki" Ta gyada Masa Kai,.. Mikewa yayi ya shiga jone jone Nan da Nan ya hada komi ya kunna sanan ya shiga tariyo Mata abinda ya faru a wanan ranan tun daga laasar har safiyar washe gari, Kallo takeyi Amma gabaki daya Tana neman fita hayyacinta saboda tsananin furgicin abinda tagani,Babu inda jikinta baya rawa Babu inda zufa Bata karyo Mata.....har suka Gama kallon video din .... Waigawa tayi ta kalli khausar wadda tayi mutuwar zaune ko motsin kirki batayi..... Jiki a sanyaye khausar ta kalli mamanta tace"turkashi mama?Kinga abinda nagani kuwa?" Ajiyar zuciya mama babba tayi tace "nagani khausar yanzun menene shawararki?" Shiru kausar tayi sanan tace"mama Anya ba shiyssa Yaya kabir ya kasa komiba Akan shariar Nan?shiyssa bashida kwarin jiki ba?" Da sauri mama ta girgiza Kai tace"baisan komiba khausar banajin idan kabir yazonan tunda habib ya mutu,Kinga kuwa inhar hakane to akwai mafita" Mama ta kalli gefenta su kadaine cikin dakin zaune Dan bayan ta kunna musu fita yayi,mama tace"dolene kudurina ya cika akan yarinyar Nan yadda ta kashemun da'itama a kasheta" "Ta Yaya mama?bayan idan mukasake videon Nan yaje kotu mune a ciki?asirin Dan uwana zai Tonu sanan mutunci da kimar masarautar Barayar Zaki Dole ya zube a idon mutanen gari da duniya Baki daya" "Haka ne khausar yanzun abinda nake Ganin zai faru shine,fita ki kiramun yakubun mu tattauna dashi a tsakaninmu matukar akwai mafita Kuma zai rufa Mana asiri to ko nawane Zan salwantar Akan wanan shariar Dan Ganin cikar burinmu..... *SLIMZY😍🥰* ✍🏻*🌩ANYI WALK'IYA.....🌩* *💡 HASKE WRITERS ASSOCIATION💡* *NA SLIMZY* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata Faty D'an maliki* 08 "Yakubu banason a samu matsala Akan wanan aikin Dana saka ka tabbatar da kayi yadda nace baasamu matsala ba,banaso video din Nan ya fito complete idan akaje kotu" Dan rankwafawa yakubu yayi yace "insha Allah zaayi yadda kikace ranki Shi dade,ai Dole abi umarninki ranki Shi Dade" Wayarta ta Ciro ta Mika Masa "samun number ka a Nan sauran bayani zanyi maka aike" "Nagode ranki ya Dade Allah ya Kara girma da arziki" Ba tare da ta amsaba ta juya suka fice a office din,securities da dogarawa suka take musu baya har wajen motocinsu.... ****** "Wanan manakisa ce babba ake Shirin shiryawa Dan anga yarinyar batada gata to wallahi karyane,wanan maganar ruwan kwando CE Babu yadda zaayi ace Ana rikon yaro a gidan marayu ace baasan da zamansa ba bayan dik wani yaro da rikonsa zai koma hannun gwamnati Sai an rubuta sunansa da komi da shekarar da aka kawosa da Wanda ya kawoshi wannan maganar banza ce barrister" Girgiza Kai yarima yayi Sai yanzun hankalinsa ya Dan kwanta Jin wanan maganar daga bakin barrister Abdul"Ni kaina abin ya daure mun Kai domin Ni shaidane Akan zaman Fatima a gidan marayu saidai babu yadda zanyi in furta hakan tunda ga yadda shariar tazo bani nake kareta ba" "Ai ka kwantar da hankalinka Dole ne a koma Ayi bincike tsattsaura Akan gidan marayun Nan domin idan haka ne akwai wata makarkashiya ai wanan abin da sukayi tamkar sun nunawa duniya cewa Suma maha'inta ne ,sanan Babu gaskiya a lamarin Babu Amana" Sai yanzun yarima ya samu karfin gwiwa da kalaman Abdul,hankalinsa ya Dan kwanta yace "to yanzun barrister menene abun yi?me kake Ganin zaayi?" "Ni da kaina zanje police station din,inyi magana da babban DPO din Akan Ni ban yarda da wanan binciken da akaje akayi ba a gidan marayu batare da dauko list din sunayen yaran dake gidan ba,ai a master list ne idan har baaga sunan Fatima da hotonta ba to shine zaa tabbatar da baa gidan marayu take ba wanan karon Dani zaaje saboda akwai binciken da nakeson yi a cikin gidan marayun" Jinjina Kai yarima yayi cike da gamsuwa yace"yauwa barrister Abdul Dan Allah kayi kokari Akan wannan lamarin a duba al'amarin marainiyar Allah dik duniya Fatima batada kowa Sai Allah Sai Ni" Kallonsa barrister Abdul yayi "ban gane inda maganarka ta dosa ba me kake nufi?" "Marainiya ce kamar yadda kasani,sanan Kuma nine a matsayin gatanta na uwa da uba,sauran bayani zanyi maka Shi idan komi ya kwaranye,fatana be wuce a shiga wanan kotun da zaayi musamu cin nasara a wanan shariar" Kalaman yarima ya daurewa barrister Kai Amma Sai ya share yace"Allah ya bamu nasara ranka ya Dade insha allahu Fatima zata kubuta" Murmushi yayi yarima Wanda ya tsaya iya fuskarsa yace'abu na gaba shine yadda zaa Kara zantawa da Fatima Akan abinda ya faru Dan idan ban mantaba jibi ne zaa koma shiga kotu" "Wanan ba matsala bace insha allahu,gobe da safe nakeson zuwa station din yin bincike bazan taba nunar musu da nasan cewa sunyi bincike Akan Fatima ba Yar gidan marayu bace zanyi musu tambayoyine inji me zasuce sanan in gabatar musu da bayanin da nayi maka yanzun,sanan madam zansa ta Kara neman izinin Ganin Fatima domin ta zanta da ita a Karo na biyu" Mikawa barrister hannu yarima yayi suka gaisa hade da rike hannun nasa "nagode sosai barrister bansan da kalmar da zanyi amfani da itaba wajen nuna godiyata da jin dadina Akan wanan halarcin da kayimun nagode Allah ya saka da alheri"suka rungume juna.... ******* Ba karamin farin ciki mama babba tayi ba samun labarin da tayi Akan Fatima baasamu wani cikakken bayani ba akanta a gidan marayu,wanan kadai ya Kara kwantar Mata da hankali ta Kara tabbatar wa da kanta hakarta ta kusa cinma ruwa Dan da zarar aka shiga kotu ta tabbatar da lauyoyin da ke Kare Fatima Basu da wata hujjar data Kai tasu,domin dik hujjar da zasu gabatar a kotu alkali zaiyi watsi da ita ne.... Bayan yarima ya baro wajen barrister Abdul direct gida yayo hankalinsa ya Dan kwanta sanan yasamu kwarin gwiwa da maganganun barrister Abdul,babban tashin hankalinsa da damuwarsa be wuce Fatima ba Allah yasa tayi magana,ta Fadi abinda tasani tayi bayani..... A dakin mama babba yayi matsuguni yau fuskarsa Babu yabo Babu fallasa ba kamar kullum ba da ka gansa kasan Yana cikin damuwa ita kanta fuskarta a sake take sanar Masa da bayanin da akayi Mata game da Fatima ba Yar gidan marayu bace"kaga kenan munada hujja kwakkwara da zamu gabatarwa da kotu ita batare da Anja wanan shariar ba zaa gamata,Kuma gaskiya zatayi halinta" Murmushi kawai yarima yayi yace"to alhamdulillahi wanan labarin da nasamu bakaramin dadinsa naji ba yanzun abinda ya rage shine gabatarwa da kotu hoton video din yadda aka kashe Yaya habib" Jinjina Kai tayi a tsayen da take tace"wanan ba matsala bace domin naje guest house din dazun Kuma na roki alfarmar a bamu aron recording din mu Mika kotu Dan tabbatar wa da duniya cewa kasheshi akayi batare da hakkinsa ba" Da sauri ya kalli mama babba ,hmm lallai wanan matar bala'i CE wato har taje guest house ta aiwatar da abinda tayi niyya,kallon tuhuma ya bita dashi sanan ya kawar da kansa gefe daya cikin dabara ya kakalo murmushi saboda kawar da reaction din da yayi lokacin,Yana jinjina Kai Yana faraa yace"alhamdulillahi nasara Tana garemu" Itama murmushin tayi tace "insha allahu" Dan waigawa yayi kadan yace "Ina su khausar ne?" "Sun shiga garden Wai sun gaji da Zama wuri daya shine akayi musu rankiya don su Sha iska" "Ok"shine abinda yace kawai yayi Mata sallama ya bar sasanta, Sasan mahaifiyarsa ya shiga Tana zaune ta da'n ki shingida gefenta bayi ne guda biyu daya Tana matsa Mata kafa,daya Tana bare Mata fruits, Zubewa yayi a kasa ya kawo gaisuwa,murmushi tayi Tana kallon da'n nata cike da so da kauna ta amsa, "Yarima yadai? Yau Naga fuskarka a sake da alamu kana cikin nishadi" Kasa da kansa yayi hade da murmushi yace"ehh mama nafara samun kwanciyar hankali ne,saboda da alamu zamuyi nasara a wanan shariar Allah zai bayyana Mai gaskiya" Jinjina Kai kawai tayi hade da murmushi sanan tace "Allah yasa" "Ameen,Ni Zan shiga bangarena" "Kafin Nan Mai martaba yanason zantawa dakai,dazu ya sanarmun da hakan domin tafiya ta kamashi da gaggawa Amma dai Ina Ganin ba dadewa zaiyi ba bazai wuce sati da'ya ba" "To Zan shiga wajensa insha allahu,ki huta lafiya" "Allah yayi albarka" "Ameen"ya Mike ya fice.... ******* Washe gari kamar yadda barrister yayiwa yarima alkawarin zuwa police station hakan kuwa akayi,shiryawa yayi tsab shida madam dinsa suka nufi police station din, Gabatar da kansu sukayi sanan suka bukaci Ganin DPO din wajen,sanin kosu din su waye yasa akayi musu iso zuwa office din DPO Bayan sun gaisa ne barrister Abdul ya bukaci Jin ko sunje gidan marayu sunyi bincike Akan yarinyar? Cike da gamsuwa DPO ya yiwa barrister bayanin yadda bin ciken ya kasance da ya tura jamian tsaro sanan an tabbatar musu da baa gidan marayu take da zamaba, Murmushi barrister Abdul yayi yace"ranka ya Dade kada kace nayi maka katsalandan akan aikinka,Amma sorry to say gaskiya ba haka ake bincike ba" Kallonsa DPO yayi ta cikin glass Yana mamaki, "Ehh saboda a sharia babu inda akace idan anje bincike gidan marayu,maaikata zaabi a bincika sanan a bincika yara Ana yawo da hoton yarinya,meye amfanin registarer na gidan da ba zaa bincikeshi ba Akan sanin yarinyar?inace ko wani gidan marayu dake cikin jahohin Nan kafin rikon yaro ya koma hannun gwamnati Sai an yi mishi register da gwamnati?da hotonsa da Wanda ya kawosa sanan da shekarar da aka kawosa da sa hannun Wanda ya kawota da sa hannun gwamnati cewa ta amsa,dik bakubi wannan matakan ba kawai akaje akayi bincike a sama akace Wai baasanta ba,to gaskiya bincikenku beyi ba Dole a sakeshi,Dan abinda ya kawoni kenan inji ko kunyi bincike don insamu abinda zan rubuta in mikawa kotu" Shi kansa DPO din ya gamsu da bayanin barrister abdul Dan tabbas wanan shine binciken kwarai,gyara glass din idonsa yayi yace "to yanzun barrister menene bukatarka?" Gyara Zama barrister Abdul yayi yace"yanzun inaso a hadani da Yan sanda kamar mutum hudu Dan komawa gidan marayu mu gudanar da binciken ainihi ba irin Wanda sukayiba Dan ba bin cike bane" Jinjina Kai DPO yayi ya Danna kararrawa saiga wani Dan sanda ya shigo ya Sara masa, DPO yace "a shirya mota yanzun Dan zaa koma gidan marayu tare da barrister Dan gudanar da bincike a Karo na biyu" Sara masa yakarayi yace "yes sir"ya fice , Barrister Abdul ya Mika Masa hannu suka gaisa sanan suka fito shida barrister hauwa, Yan sanda hudu suka shirya kansu a motarsu yayinda barrister Abdul da matarsa suke tasu motar suna biye dasu har gidan marayun..... Koda suka Isa basusha wahala ba wajen isar dasu office din manager n gidan gaba daya Wanda hade suke da registerer na gidan marayun, Barrister ne ya gabatar da kanshi sanan sauran Yan sanda kowa ya gabatar da kanshi da abinda sukazo yi, Nan da Nan sukayi naam da bukatarsu aka shiga bincike file by file na yaran dake gidan,ko wace shekara da files din dinta,a haka har akazo shekarar 1999 aka Fara bude sunaye da hotuna anyi file na hudu a na biyar saiga hoton Fatima Zahra a jiki da sunanta rad'a rad'a FATIMA ZAHRA.... Nan aka bude file dinta aka tabbatar da tabbas a gidan marayu take da Zama sanan ga hotonta Nan kamaninta tun na yarinta Babu abinda ya canja..... Hajiya ce zaune a jikin bishiya a kofar kitchen Tana Shan iska gefenta maaikatan kitchen ne duk suna zagaye da ita,kallon wadda ke gefenta na dama tayi tace"Wai nikam uwaliya tun dazun nake hangen motar Yan sanda da wata karamar mota a office din oga Wai meke faruwa ne" Tabe Baki wadda aka Kira da uwaliya tayi tace"ohoo hajiya nidake fa a zaune muke a nan,Ina zansan meke faruwa?" Tsinke tasa ta cigaba da Sosa kunnenta batare da tace komiba... A office kuwa barrister ne ke tambayar manager kamar haka "shin Dan Allah ranka ya Dade idan bazaka damuba inada wasu Yan tambayoyi da zanyi makasu wadanda bazasu wuce biyu zuwa uku ba" Maganer yace"Bismillah Ina sauraronka" "Inaso insan cewa shin dik wani shige da fice da yaro zaiyi Wanda yake karkashin gidan Nan kusan dashi?maana Kuna sanin yaro zaibar gidan yaje wani waje ko aa" "Ehh munasani Dan Babu yaron da zai fita gidan Nan baasan da fitarsa ba" Jinjina Kai barrister yayi sanan yace"20 ga watan June daya daga cikin yaran gidan Nan ya nuna ta fita daga gidan Nan zuwa wani waje shin kasani ko ince kunsani?" "Ehh bàma yarinya daya bace yara ne wadanda ke karatu a cikin gidan Nan,aka fitar dasu don zuwa yin jarabawar share fagen jamia" Murmushi barrister yayi yace "da aka fitar dasu an hadasu da wasu ne?wadanda zasu Lura fashige da ficensu na kaiwa da komowa?" "Ehh an hadasu da metro dinsu hajiya halima da malam haruna Wanda shine a matsayin guardian dinsu" "Nagode sosai manager"...dik tambayoyin da barrister Abdul keyi barrister hauwa na gefe Tana rubutawa yayinda Suma Yan sandan daya daga cikinsu Yana daukar statement... Sallama sukayi suka fito ko wanne ya shige motarsu suka nufi police station din..... A mota barrister hauwa kecewa "wadanan bayanin da manager yayi Dole a nemosa a kotu yayisu,sanan alhamdulillahi gaskiya zata fito wanan binciken yayi barrister abinda ya rage Mana jin ta bakin Fatima itace ciwon kaina yarinyar Nan wallahi" Murmushi barrister yayi Yana tuki yace "insha allahu munasa ran wanan karon zatayi bayani,inaso ki lallabeta sosai ta baki labarin abinda ya faru,sanan ki sanar Mata da munyi bincike Akan komi a gidan marayu Kinga idan taji haka inada tabbacin zatayi bayani" Ka'da Kai barrister hauwa tayi tace"Allah yasa" Da wanan tattaunawar suka iso police station din,ofishin DPO suka koma barrister Abdul ya gabatar Masa da komi tare da yi Masa godiya,da Kuma gabatar Masa da bukatar zantawa da Fatima da sukeson yi,DPO ya bada umarnin a fito da ita a kaita dakin da ake zantawa da masu laifi, Ofishin DPO Suka fito yayinda barrister hauwa tayi gaba shiko barrister Abdul wayarsa CE tayi ringing Yana dubawa yaga yarima ne, Murmushi yayi ya amsa "ranka ya Dade yanzun haka mungama komi Ina wajen ma,.....Nan ya kwashe komi briefly ya fada Masa yadda abin ya kasance, Yarima cike da farin ciki yace "alhamdulillahi insha allahu zanzo gida insameka nagode barrister"ya kashe wayar, Barrister hauwa Tana zaune already ta seta recorder dinta lokacin da Fatima ta fito, "Fatima zauna Mana"ta nuna Mata wajen zama...Zama tayi Babu musu sanan barrister hauwa tayi gyaran murya tace "gani na Kara dawowa a Karo na biyu gareki fatima,Amma wannan karon kafin na dawo Saida mukaje gidan marayu mukasamo bayanai sosai akanki sanan nazo kema Dan inji ta bakinki" Da sauri Fatima ta da'go Kai Tana kallon barrister hauwa,Nan da Nan idonta ya kawo ruwa, Jinjina Kai barrister hauwa tayi tace "ehh munsamo bayanai mukazo muji naki bayanin da labarin abinda ya faru daga bakinki,saboda haka Fatima nake rokonki ki dubi girman Allah ki dubi maraicinki ki rufawa kanki asiri kifadi gaskiyar abinda ya faru kada ki boyemun komi" Kad'a Kai Fatima tayi hawaye na sauka a idanuwanta tace "zanyi bayani insha allahu" Gyara Zama barrister hauwa tayi cike da farin ciki tace "Ina sauraronki"..... *Muje zuwa*...... *SLIMZY😍🥰* ✍🏻*🌩ANYI WALK'IYA.....🌩* *💡 HASKE WRITERS ASSOCIATION💡* *NA SLIMZY* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata Faty D'an maliki* 09 Ya kasance a gidan marayu..... Tun Ina yarinya na budi idona na ganni a cikin gidan marayu,muna rayuwa a karkashin kulawar gwamnati Wanda itace take ciyar damu take tufatar damu harda karatun da mukeyi dik munayine a karkashin kulawar gwamnati, Tun Ina kankanuwata nake Ganin abubuwan dake faruwa a cikin gidan marayun Wanda a wanan lokacin banasanin menene hakan yake nufi Saida na girma nakai shekara goma Sha shida a duniya sanan na fuskacin mummunan rayuwar da mukeyi" *WATA RANA!* Zaune muke nida kawayena uku kusan saannin juna muke sanan kanmu guda nidasu saidai dukansu sun girmeni nice karamar cikinsu, Zaune muke a karkashin wata bishiyar mangwaro wadda ta kasance dik laasar na duniya Nan ne zamanmu muke Shan iska muyi ta kallon Yan uwanmu Wanda suke kaiwa da komowa ,bilkisu CE daya daga cikinmu tace "Wai nikam Fatima jiya Kinga uban kayan kwadayin da su zainab suka dawo dashi daki?hmm abin baa cewa komi" Kallonta nayi cikin rashin fahimta da son Karin bayani "kaji bilkisun Nan da shegiyar karya,kina nufin basuci tuwo miyar kuka da akayi Mana ba kenan?Ina zasuga wani kayan Dadi muda ke zaune a wajen Nan kamar kabari Babu shiga Babu fita Babu wani mahalukin duniya dake zuwa ganinmu ballantana mu sabanta abin sawa a Baki Sai Wanda aka kawo aka bamu" "Hmm Fatima kenan to aisu Yan gatan hajiya ne Yan gaban goshi,to Bari kiji jiya idona biyu lokacin da suka dawo daga unguwar da hajiya ta fitar dasu Kuma kaji ne da kayan ciye ciye suka dawo dashi har hajiya aka dibarwa" Zaro Ido nayi waje Ina kallonta cike da mamaki da al'ajabi nace "to su waya Basu?" Tabe Baki bilkisu tayi tace"oho,wayasan inda suka samo bayan mu son Kai akeyi Mana Kiri Kiri,wani lokacin kina gani su zainab zasuce bazasuci abincin da mukaci ba Kuma ta zauna saidai kigansu an Basu me Dadi sunci ,ai mudai Sai Allah ya saka Mana" Kallon bilkisu kawai nakeyi yadda take magana cike da masifa da tsiwa don dik cikin mu ukun ta fimu Baki wallahi Dan ko a cikin gidan Babu me daga Mata yatsa ya sauke ba tare da ta rama ba, Maryam dake gefenmu wadda tunda muke maganar batace komiba sai lokacin ta waiga gefen dama da hagunta ta juyo garemu tare da kasa da murya, "Kunsan Allah wallahi su zainab samari garesu" Dafe kirji nayi hade da zaro Ido cikin furgici nace "samari fa kikace?a Ina suka samesu muda Babu inda muke zuwa,Babu Wanda ke zuwa gidan Nan Sai manyan masu kudi da ke kawo Mana ziyara suna kawo mana tallafin abinci da sutiru?" Kasa da murya tayi wanan karon fiye da dazu tace "hajiya take hadasu da samari masu kudi,sanan hajiya ke fitar dasu takaisu wajen samarinsu idan aka siyo musu kayan Dadi su Raba su Bata Bata kason wallahi da idona nagansu" Bilkisu CE ta ce"wallahi hajiya zata aika Naga take takenta domin ranan Fatima idan bazaki mance ba ranan da tawagar Dan sarki sukazo gidan Nan?kin tuna hajiya to azo muna cikin dakinmu ta tattagomu tace dukanmu Sai mun fito mun kawo gaisuwa,bayan mun gaisa dasu mun juya zamu wuce Ina kallon hajiya na nunaki Tana washe Baki" Ba karamin furgita nayi ba da Jin zancen da bilkisu tayi Akaina,tabbas ranan hajiya tace muzo mu gaida tawagar Dan sarki me jiran gado ya kawo ziyara hade da kawo Mana kayan abinci da suturu masu alfarma Amma Ni dik abinda akeyi a wajen ban maida hankalina a Kai ba, Juyowa nayi na kalli bilkisu nace "to Sai akayi Yaya ?" Wata uwar harara bilkisu ta wurgamun sanan tace "Ina zansani" Ajiyar zuciya na sauke sanan nace "su suka sani"muka kauda zancen ta hanyar mikewa gabaki dayan mu kasantuwar magriba tayi zamuyi sallah muje much abinci..... ******** Bayan munci abinci munyi sallahr ishai a wanan ranan dukanmu mun tafi wajen kwanciyarmu,wuri daya muke kwana mu uku saboda hakikanin gaskiya munshaku nida Yan uwana Amma munfi shakuwa da bilkisu, Mun kwanta a shimfidar,idonmu biyu ba bacci mukeyi ba mukaga hajiya ta shigo sadaf Sadaf ta wuce can lungu wajen kwanciyar sauran Yan Matan dakin hannunta rike da Leda baka,da sauri bilkisu ta taboni na da'go Kai cikin kasa da murya tace "da'go Kai Fatima kiga abinda nake fada Miki" Da'go Kai mukayi nida bilkisu muna kallon hajiya halima ta Ciro Kaya ta tashi Yan Mata uku wadanda kusan dik saanin mu ne ko zasu girmemu bazai wuce shekara daya ba can kasa naji Tana magana "Yi sauri firdausi ku shirya ga haruna Nan yazo daukarku a can zaku kwana kada kudamu da asuba zai dawo daku Zan bude muku kofa" Kallon juna mukayi nida bilkisu zanyi magana ta kaimun zunguri alamar inyi shiru Sai naji daya daga cikin Yan Matan dakin namu Mai suna firdausi Tana cewa "nifa hajiya nafara al'ada" Can kasa da murya hajiya halima tace"shine Baki fadamun ba da wuri bayan kinsan da maganar fitar Nan taku tunda Rana nafada muku zaa fita daku gashi alhaji surajo ya kwadaitu da inkawo mishi ke so daya ya Dan Dana zumarki Amma ya kasa sukuni neman ki yakeyi,ga alkawarin makudan kudi da yayimin shegiyar yarinya zakijamun?ai shiryawa zakiyi kije can ku karata" Batare da wani musu ba firdausi ta dauki doguwar rigar da hajiya ta kawo Mata tasa Mai shegen kyau da tsada ta zura ta shirya tsaf ta yi gaba suna biye da ita.... Tana fita nayi zumbur na Mike na yaye tsumman zanin Dana lulluba dashi saboda sauro,hankalina ba karamin tashi yayiba domin ko baa fadamunba a wanan shekarun nawa Dole in fahimci wani Abu, Hankalina a tashe na shiga dukan bilkisu wadda tayi lamo a gefena ba barci take ba ta tashi firgigit Tana murtsika Ido,cikin duhu nake kallonta cike da tashin hankali nace "badai iskanci hajiya ke dibar Yan uwanmu Tana kaiwa ba" "Da me suke zuwayi kinaji ance acan zasu kwana,hmm to Bari kiji kullum da wadanda hajiya ke dauka a tafi dasu a dawo dasu kisani kilama ya kusa kanmu" A firgice na dafe kirji nace"tabdijan Ashe Wanda ya mutu zai dawo wallahi tallahi Babu inda zaa kaini inje ,kada ma mafarkin hajiya ya Bata cewa zata daukeni takaini wajen maza Allah ya kyauta ya tsareni" "Aiko zamu gani don wallahi nasan a juri zuwa Rafi kema zakibi sahu don kina cikin kyawawan gidan Nan sanan Bari kiji ma wani Abu gobe naji kishin kishin Ana tsegumin cewa tawagar Dan sarki zasuzo duba marayu zasusa ayi Mana gyare gyare wanan karon ma naji ance duka yaran masarautar Barayar Zaki zasu kawo ziyara hade da Yan siyasa" "Ke bilki kirufawa kanki asiri da jita jita a Ina kika jiyo?" "A bakin uwaliya da ke kitchen naji dazun lokacin da naje kankaro Mana kanzon Nan?to a Nan naji,...umm Ni barci nakeji "Nan bilkisu ta gyara kwanciya ta kwanta abinta tabarni Nan zaune a cikin duhu Amma hankalina baa kwance yake ba, Koda na kwanta idona biyu juyi kawai nakeyi Ina tunanin Ina hajiya ta dibi su firdausi ta kaisu domin Ni bawani gasgata magabar bilkisu nayiba dik dauka nake shirmenta ne don Babu abinda masu kudi zasuyi da kazaman yara kamarmu marasa galihu, Kwana nayi ina tunanin maganar hajiya halima,wadda kemun yawo a kunne,juyi kawai nakeyi har gabanin asuba naji karar bude kofar shigowa dogon dakin namu,na dauka anzo tashinmu sallahr asuba ne Nan da Nan nayi zumbur na Mike aikuwa karaf hajiya halima ta hangoni sai ji nayi tace "wace munafukar CE ta mike zaune don iskanci a wanan tsakiyar Daren?uban me kikeyi?" A hankali na sulale na kwanta batare da nayi ko kwakkwaran motsi ba nasan ba karamin aikinta bane ta rufeni da duka a wanan Daren, Idona biyu suka wuce Tana biye dasu firdausi har wajen kwanciyarsu, gefe ta zauna ta daga hannunta tace "nasan bazaku rasa samo kyautar kudi ba Banda Wanda aka bani,to inji dumus Dan vazakuje kuci kaji kusha AC a banza ba anbar kwanan sauro ,kuce baa Dan Baku wani abuba" Cikin rawar jiki suka shiga fitowa da abubuwan da suka samu suna dire Mata Saida ta amshe Yan kudaden tsaf Kuma suka Raba abinda sukazo dashi na ciye ciye suka zube Mata nata,sanan ta umarci ko wacce ta Ciro kayan jikinta tabata, Babu musu Suma shiga cire kayansu suna Bata ta tattara tasasu a jakar ledarta ta fice..... Niko dake gefe tausayin kanmu ne ya lullubeni take naji wani hawaye da bansan daga ina yake ba Yana sauka a kuncina,lallai rashin iyaye babban rashin jigone a rayuwa,inda munada iyaye dik lalacewarsu bazasu yi Mana wanan wulakancinba, Hannu nasa na share hawayen daya wankemun fuska lokaci daya, Jin sanyin iskar asuba na kadani yasa nakara kudundunewa cikin tsumman zanina ina shasshekar kuka.... ******* Da safe bayan anbamu kunu da kosai kwaya uku uku kununma tamkar besan da wata suga ba sunan ansa gashi tsululu yayi ruwa haka ake zuba Mana ludayi biyu biyu a Kofi mun kafa layi muna amsa,bayan mun karya ne hajiya tazo tare da mukarrabanta haruna da sauran maaikatan da sukejin tsoronta ta taramu tafara jawabi cikin daga murya"dik wata yarinya dake bangaren Mata a gidan marayun Nan to ta tabbatar ta bada gudun mawa wajen aikin gayya da zamuyi yanzun Nan domin munada manyan Baki daga gwamnati maana,Dan sarkin garin Nan Kuma Mai takarar sanata ya sanar Mana da zai kawowa marayu ziyara hade da mukarrabansa da ahalin gidan sarki Baki daya,to ina Mai sheda muku ku tabbatar da ko Ina yayi fess Babu datti don zaiyi zagaye" Tana Gama fadin haka aka shiga watso Mana tsintsiyoyin kwakwa wasu da manjagara haka muka kwasa muka shiga aikin Nan Sai wajen karfe daya muka Gama don dama munsani idan zaa kawo Mana ziyara mafi yawan lokuta da yamma ake zuwa... ******* Misalin karfe hudu da rabi muna zaune a daki nida bilki a daki nasamu munyi wanka da kyar Shima kitchen mukaje bilkisu ta dibo Mana batare da kowa ya ganiba mukayi wanka,rabonmu da wanka kwana hudu kenan, Wata kodaddiyar atamfata nasaka ringa da zani Wanda matar Mai girma gwamna ta kawo Mana tallafi ,sanan nakawo farin hijabina Wanda dauda da rashin tsafta yasa ta koma Mai ruwan kasa nasa abuna na shirya tsab,na bude Baki zanyi magana kenan,Maryam ta shigo a guje Tana haki Tana fadin "ku fito ga tawagar gidan sarki Nan da mukarrabansu ku firfito" Sauran tsurarun Yan Matan dake dakin suka shiga ficewa a guje wadanda dik wadda zaka kalla a gidan Nan Babu kayan arziki a jikinta saboda karancin kayan sawa da muke dashi, Bilkisu ta kalleni ta gefe taga banida alamar tashi tace"malama mikewa zakiyi mutafi don kada ayi babumu dan inaga kila ayi Mana rabon kayan sawa" Haka kawai gabana ya yanke ya Fadi na Mike jiki a sanyaye Ina tafiya tamkar wadda kwai ya fashewa a ciki,su kuwa bilkisu da Maryam sun kusan kaiwa inda muke hango dandazon jamaa, Dan tsayawa sukayi suna jirana a hasale Maryam tace "Fatima Naga take takenki idan bazakiyi sauriba mu wuce" Sauri na kamayi Ina hardewa da zanina,yayinda suke tsaye suna jirana nadan tsaya in gyara zanina daya nannade ta kasa bilkisu ta Gama kuluwa ta da'go murya tace"Sai kintaho Allah yasa kada kisamu kayan Nan da zaa raba,Sai shegen yangar tsiya bayan kinfi kowa fatarar Kaya " Sukai tafiyarsu,Niko na tako a hankali na kusa isowa wajen jamaar na hangi mutum a jikin wata bakar mota Yana facing Dina da alama waya yakeyi, Kallonsa na tsayayi tamkar wawuya don tunda Allah ya halicceni ban taba Ganin halitta irin wanan ba fari Tass dashi Yana sanye da bakar shadda dakakkiya wadda Tasha aikin hannu ta matukar karbar farar fatar jikinsa,Nan na shagala Ina kallonsa naji an fincikoni "Fatima meye haka?kinsan me kikeyi kuwa?to Dan sarkine Allah yasa ma yasa a zaneki" Murmushi ya sakar Mana daga inda yake hannunsa sakale da wayar da yake amsawa ya nufomu,aikuwa muka runtuma a guje kamar munga aljani mukayi cikin mutane dukanmu muka rarrabu.... *Muje zuwa ku biyoni a shafi na gaba,kuyi hakuri jina shiru da kukayi kwana biyu hkn ya farune sakamakon rashin lafiya da nayi nagode* *SLIMZY✍🏻😍* 🥰*🌩ANYI WALK'IYA.....🌩* *💡 HASKE WRITERS ASSOCIATION💡* *NA SLIMZY* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata Faty D'an maliki* 10 Kallonmu yakeyi Yana murmushi,ganin yadda muka runtuma a guje yasa ya tsaya daga inda yake takowa zuwa garemu, Mukuwa rarrabuwa mukayi duka mu ukun kowa ya nemi wajen buya,Sai haki nakeyi a jikin wani karfe Ina maida numfarfashi Ina Dan leko da kaina ko Zan hangoshi Amma ban ganshiba,ajiyar zuwa na sauke na dafe kirjina da yake bugawa fatt fatt saboda gudun da mukayi..... Taro sosai ake gudanarwa a wanan ranan domin harda kayan sawa aka kawo Mana tallafi gidan marayu da buhun Hunan abinci,yayinda Yan jarida keta daukar hoto.....shiru Banga Yan uwana ba na fito Ina takawa a hankali tamkar mejin tsoron wani Abu inayi Ina waige waige Sai ji nayi ance cikin wata murya Mai dadin sauraro"har yanzun tsoron be sakeki ba kenan?"cakkk na tsaya wani irin tsoro da furgici suka shigeni lokaci daya nakasa ko kwakkwaran motsi, Takowa ya karasayi ya tsaya a gabana shine dai na dazun Wanda muka gani Yana waya yanzun hakan ma wayarce a kunnensa yakeyi, karkarwa kawai jikina yakeyi, domin har ga Allah na firgita sosai da wanan bawan Allah Sai ji nayi yace "yanzun haka Yan uwanku ake rabawa kayan sawa ke kuwa kina Nan kina buya,to boyon me kikeyi?" Bakina na rawa nace "Dan Allah kada ka saceni kaji?kayi hakuri wallahi bazan sake ba" Cikin mamaki yake kallona yace "Babu abinda kikamun Yan mata,sanan Ni Kuma bame satar mutane bane Koda Kika ganni a Nan ba a cikin mutaneba akwai dalili, dalilin kuwa shine bana son hayaniya shiyasa nadawo gefe inata waya abuna" Jin jina Kai kawai nayi na juya nafara tafiya Ina hardewa har na danyi nesa dashi naji yace "Amma ya sunanki?" Sarai nasan Dani yake na cigaba da tafiya,Sai ya Dan daga murya yace "idan har Baki fadamunba to Zan saceki in gudu dake" Ai da sauri na juyo nace cikin daga murya "Fatima"Ina fada Masa na Ruga a guje ko Ganin gabana banayi saboda tsoron kada ya saceni, Daidai tawagar Mai girma sanata sun taho domin zagayen gidan marayu lokacin na rugu a guje Zan gifta ta gabansu aikuwa hajiya ta kwalamun Kira "ke Fatima meye haka saikace wata akuya kin taho a guje kamar ba mace ba" Da sauri na zube a wajen Ina Bata hakuri "hajiya Dan Allah kiyi hakuri wallahi tsoro naji shiyasa"....da'go idanuwana nayi don kallon yanayin hajiya kawai Sai muka hada Ido da wani kyakkyawan mutum fari Tass tamkar na dazun saidai wanan Shi yanada Dan jiki Kuma be Kai na dazun tsawo ba, Da sauri na sunkuyar da kaina na Mike na wuce tamkar wadda kwai ya fashewa a ciki,su kuwa wucewa sukayi domin zagaye..... Cikin Yan uwana yara na shiga dik Wanda na kalli fuskarsa a wanan ranan cike yake da farin ciki saboda murnar an kawo Mana tallafin kayan sawa da kayan abinci, ...neman su bilkisu na shigayi cikin mutane Amma ban gansuba,Nima kawai Sai na juya na nufi dakin kwanciyar mu ko can sukaje, Haka kuwa akayi,Ina shiga suka tuntsiremun da dariya dukansu dariya suke Babu kakkautawa,cikin dariyar bilkisu ke nunani da yatsa "faty Wai me yace Miki Dana hangoku ya kamaki?"ta Kara tuntsirewa da dariya,haushi ne ya kamani batare da nace komiba na karaso na nemi waje na zauna hade da daure fuskata,domin idan akwai abinda na tsana be wuce a kalleni a rinka yimun dariya ba ,su kuwa Yan uwana dabiarsu kenan musamman bilkisu, ********** Bayan kwana biyu, Muna zazzane a ta bayan kitchen nida su Maryam da Kuma tsurarun yara a wajen Sai mukaji hajiya halima ta rangad'a guda a cikin kitchen,dik Sai muka juya da sauri muna kallon windown kitchen din Wanda hayaki ne kawai ke fitowa, Zumbur muka Mike muka Ruga a guje ta bayan kitchen din muka tsaitsaya muna lekenta,a tsaye take Tana kirga kudi masu yawan gaske fuskarta dauke da faraa take kallon haruna Wanda ke gefenta ya rike kugu Sai washe Baki yakeyi tace "tabdijan babban goro Sai magogin karfe malam haruna" Kara washe baki haruna yayi hade da cewa "hajjin bana damu zaayi hajiya,harka da masu dala ai tayi ki dubi wadanan makudan kudin da aka Aiko dasu na shigar ciniki ne kafin mu Saida Kaya" Kyalkyalewa da dariya hajiya tayi tace"ai Kaya sun siyu,idan cewa yayi a bar Masa ita ta zauna dashi har illah mashaa nibabu abinda ya dameni aika shegiya zanyi,wayasani ko ta sanadin hakan akasamu cikinta?" Dariya sosai haruna yayi sanan yace "hajiya Akan kudi Zaki iya kashe mutum,yanzun menene abunyi hajiya?" "Kabar komi a hannuna haruna nasan abunyi" Jinjina Kai haruna yayi yace "to sauran yaran da zaa fita dasu yaufa?kinsan fa nafada Miki shekaran jiyan Nan da Kika nemeni Kika rasa wajen taro Ina can Ina Kai talla" Dariya hajiya tayi tace"haruna nawa,haruna baka da dama Sai hagu,dik abinda ka fada nasan zaka aikata ka kwantar da hankalinka wanan ba matsala bace inada sababbin Yan Mata gal a Leda"suka Kara fashewa da dariya.... Mukuwa tsuru tsuru mukayi muna kallo da sauraron ikon Allah mun fahimci wadansu maganganun wadansu kuwa bamu fahimta ba ,juyawa nayi nace "kuzo mutafi Dan Allah nagaji da tsayuwa a wajen Nan ga hayaki muba fahimtar abinda suke fada mukeyi ba" Tabe Baki Maryam tayi tace"kece dai Baki fahimta Amma mu muna fahimta" Batare da nace komiba nayi gaba abuna suka biyoni a baya....A daki tunani kala kala nakeyi Wanda nakasa gano bakin zaren abinda su hajiya ke nufi..... ****** Muna bin layi Ana zuba abincin Rana,maaikatan kitchen ke zuba abincin yayinda hajiya na gefe ta cokalo dauri yadda ta Saba har akazo kanmu nida Yan uwana, Maryam CE a gaba Sai bilkisu saini,Ina Mika robata hajiya ta kalleni ta washe Baki tace "Fatima anzo karbar abincin ne?" Murmushi nayi nace "ehh hajiya"...aka zubamin har na juya Zan wuce hajiya tace"Fatima"na juyo da sauri ta yafitoni da hannu naje inda ta koma gefe ta tsaya,ledar hannunta ta bude ta dakko soyayyen nama tasamun nan da Nan na zaro Ido,cike da mamaki nake kallonta ta gyada Kai tace"nakine Fatima daga gida aka kawomun nace Bari insa Miki kema" Washe baki nayi cike da farin ciki,don rabona da nama tun sallah Wanda ake kawo Mana tallafi akesa Mana yanka daya da'ya,dan durkusawa nayi nace nagode na juya abina, Kirana tayi a Karo na biyu tace "anjima bayan laasar kizo office din haruna kisameni idan Kun fito islamiyya kinji?" Gabana ne ya Yanke ya Fadi jiki a sanyaye nace "to hajiya"na tafi abuna.... Tasa abincin nayi a gaba Ina tunani kala kala,domin tunda hajiya ta furta Tana nemana na shiga fargabar da damuwar da bansan dalilinta ba..... ******* Tafe muke muna Hira mun fito islamiyya nida sauran Yan uwana,Sai surutu sukeyi Amma Ni shiru nayi ina sauraren surutunsu Dan gabaki daya hankalina na wajen Kiran da hajiya keyimun Dan bansan meke faruwa ba, Waigowa nayi inda Maryam da bilkisu suke hirarsu nace "Dan Allah Maryam kuyimun rakiya Mana wajen hajiya?" Dafe kirji sukayi a tare sanan suka hada Baki sukace "tabdijan idan kin ganmu a lahira kaimu akayi ,kedai da take Kira kije kiji ko menene Amma bandamu,ki rufa Mana asiri" Kallonsu nakeyi dukansu,Suma kallon nawa sukeyi Ganin yadda na canja fuska tamkar zanyi kuka yasa bilkisu cewa "muje mu rakaki Amma a waje zamu tsaya gaskiya" Da sauri nace "eh na yarda" Nan muka rankaya zuwa ofishin malam haruna Wanda yake can gefe Shi kadai akwai Dan tafiya Mai Nisa daga inda muke takowa, Muna Yar hirarmu har muka iso wajen,sukaja suka tsaya nikuma ilahirin jikina Babu inda baya rawa dakyar nake daga kafata na shiga office din da sallamata.... ******* Ina tsaye gefen hajiya Ina sauraron maganganun da takeyimun su kasa kasa tamkar wani na jinmu, "Ki tsaya ki kwantar da hankalinki kici arziki kibarshi a mazauninsa,Sai kiga sanadiyyar wanan mutumin Allah ya kawo waadin zamanki a gidan Nan Fatima,ki kwantar da hankalinki ki saki jikinki kamar sauran Yan uwanki,Kinga su zainab su fauziyya dik suna wanan harkar,Kuma wallahi ba karamin arziki suke samu ba,sanan suci Mai kyau subarku da wanan kamiyamiyar da ake dafa muku" Kallonta nakeyi cikin rashin fahimtar inda maganganunta suka dosa nace "hajiya ban fahimcekiba kiyimun yadda zangane wani irin aikine zaakaini yi?" Murmushi hajiya tayi tace "bawani aiki zaa kaikiba,kwana daya kacal zakiyi a can idan munkaiki sanan kada ki kuskura kiyi mishi gaddama don babban mutum ne,tunda ya ganki ya kasa sukuni ya kwadaitu da ya kebe dake" "Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun,hajiya iskanci fa kenan" Kallon yadda na furgice hajiya keyi sanan ta Mike ta tsaya a tsaye Tana kallona shekeke tace"iskanci ma zakice?to tunda kince haka Shi nake nufi Sai me?ai iskanci Fatima Dole kuyishi tunda Shi iyayenku sukayi suka watsar daku a titi ake tsintarku daya bayan daya,saboda haka Ina Mai shaida Miki ki shirya don Shi zankaiki kiyi kisama Mana kudi da dukiya Mai yawa dominke kinzo da farin jini".... Ja da baya na shigayi ina girgiza kaina,yayinda hawaye suka shiga gudu a idanuwana Wanda bansan Ina yinsu ba bakina na rawa na Soma magana "Koda iyayenmu sukayi iskanci suka haifemu,hakan Bai bamu lasisin aikata abinda su sukayiba,sanan bamuda tabbacin Zina akayi aka haifemu hajiya,Dan Allah Dan annabi kiyiwa Allah ki janye kudurinki Akaina domin Ni banida wanan raayin,Kuma harabada bazan taba aikata iskanci ba" Wasu kyawawan Mari hajiya ta saukemun guda biyu a kumatuna lokaci daya na nemi natsuwata na rasa"ke harkin Isa kicemun bakida raayi Akan abinda zansaki kiyi?wacece ke?ke asuwa to wallahi Fatima?to wallahi Baki Isa ba zamusa kafan wando daya Dani dake a gidan nan,bace mun daga gani" Juyawa yayi Ina kuka na fito a office din,waige waige na shigayi Ina neman Yan uwana, Can jikin bishiya na hangesu xaune nasan sun gaji da jirana ne sukaje wajen suka zauna,wajen na nufa nasamesu ,dukkansu kallon fuskata sukeyi da alamar tambaya yayinda na cigaba da sharar hawayen da ke zubowa a idanuwana ba kakkautawa..... Cikin tsananin damuwa da tausayawa bilkisu tace"Fatima lafiya?meke damunki?meyasameni?" Lokaci daya take jeromim wadanan tambayoyi,hannu nasanya na goge hawayen dake zubowa daga idanuwana,cikin shasshekar kuka na kwashe dik abinda hajiya ta fadamun na fada musu" Girgiza Kai kawai bilkisu keyi tace "wallahi nasan haka zata faru,domin tunda hajiya tace Tana nemanki nasan cewa akwai wani Abu a kasa,shikenan tafaru takare munfada balai,abin da muke Ganin anasanya Yan uwanmu ya dawo kanmu"..... ....Maryam dake gefe tace"Niko a ganina wallahi ba wani Abu bane karuwarmuce Fatima kudi xaki samu sanan itama hajiya tasamu nata,Kinga kema Zaki shiga jerin yaran da hajiya keji dasu a cikin gidan nan,Kinga kin huta muma dake gefenki zamu ci arziki" Wani irin kallo na Kebin Maryam dashi,hartagama magana sanan nace "Amma bakida hankali Maryam,Zina fa?ita malamin islamiyyarmu yanzun ya Gama waazi akanta Amma kike cewa bawani Abu bane?to harabada Ni Fatima bazan taba aikata zinaba don Ina marainiya banida gata in aikata mummunan aikin da Allah zaiyimun azaba dashi ranan gobe kiyama,Wai don Ina ikirari da rashin gata!!" "Idan kikace zakija da umarnin hajiya wallahi Zaki kurbi azaba a cikin gidan Nan kinadai San halin hajiya Sarai,haka kawai ma hajiya ta azabtar da mutum balle ta bashi umarni yakiyi" "Umarnin hajiya ba fadar Allah bane sanan Bata Isa tayimun abinda Allah beyimunba,wallahi ko mutuwa zanyi saboda azaba bazanyi iskanci insaida mutuncina ba don Ina neman abin duniya" Kuka sosai Fatima keyi Tana fadin "nashiga uku,Allah kana gani kasan dalilin da yasa ka kaddaro Mana wannan rayuwar Allah ka dubamu" Ita kanta bilkisu hawaye takeyi a gefe Tana Mai tausayin Zahra domin tasan Babu makawa tunda hajiya halima ta bada umarni to Dole abishi Munkai Rabin awa muna zaune Saida magriba ta kawokai sanan muka Mike dukanmu muka nufi hanyar masallaci,..... Tunda muka doshi masallaci na ke hangesa tsaye yau ma da waya sagale a kunnensa Yana waige wage kamar me neman wani, Dukaninmu mamakine dauke a fuskokinmu muka kalli juna,....bakin Maryam har rawa yakeyi wajen fadin "Fatima Kinga mutumin mu na ranan ko?wallahi shine " Bilkisu tace"shine Mana ,Allah yasadai ba aljani bana mukadai muke ganinsa" Nidai bance komiba Sai kallonsa kawai da nakeyi har muka karasa wajensa zamu wuce...."Fatima"....shine abinda yace cikin sassanyar muryarsa kamar ranan... Tsayawa mukayi dukanmu muka juyo a tare,kallonsa mukeyi shiko murmushi yayi yace "ku nazo nema fa tun dazun,bangankuba ban kuma San inda Zan sameku ba" Karasowa yayi wajen da muke tsaye yace "Ina wuninku" Dukanmu kunya CE takamamu yayinda lokaci daya yayi Mana kwarjini a tare muka hada Baki wajen gaishesa,murmushi yayi ya amsa sanan yace "Hira nazo wajenku bangankuba nakasa Zama a gida,kasantuwar yau lahadi Babu aiki yasa nace Bari inzo indubaku" "Mungode"muka hada Baki mukace sanan muka juya zamu wuce,da sauri ya Sha gabanmu yace "ya zaku tafi ko sallama Babu" Cikin kosawa da zancensa nace "malam sallah zamuje lokacin sallah yayi" "Ba sunana malam ba sunana kabir,..." Juyawa nayi batare da nace komiba nabarsu tsaye a Nan,inda su bilkisu suka tsaya wajensa nayi tafiyata na barsu domin zuciyata Babu Dadi.... ****** Muna kwance a daki gefena bilkisu ke shaidamun wanan mutumin yace zaizo Mana Hira gobe da yamma ya tambayesu inda zai samemu ta nuna mishi wajen zamanmu, Na kalleta a Dan fusace nace "daga Ganin mutum bakusan ko wayeba Kun tsaya zuba zance dashi kune harda cewa yazo to Allah ya Baku saa ya hadaku da hajiya Ni Babu ruwana wallahi"..... ****** Washe gari kabir yazo gidan marayu wajenmu ,su bilkisu ke zuba surutu nidai saidai inyi murmushi ,tundaga wannan lokacin muka Saba da kabir yake fada Mana Shi Dan sarkine,abinda na Lura da kabir shine yanada tausayi sanan bashida yawan surutu Kuma akwai kwarjini..... ******* Na fito Ina sauri zanje bayi ,na gamu da zainab take shaidamun hajiya na nemana,gabana ne ya Yanke ya Fadi Nan da Nan hankalina ya tashi nasan kwanan zancen,fitsarin Dana fito zanyi ne naji ya koma nayi wurgi da gwangwanin dake hannuna natafi Kiran hajiya..... "Fatima" Na da'go Kai na kalli hajiya sanan na sunkuyar da kaina kasa Ina Wasa da yatsun hannuna, "Nakiraki ne Akan maganar da mukayi dake kwanakin baya,Kika cemun bakida raayi ko?" Na daga Mata Kai idanuwana suka kawo ruwa, "Fatima kitaimakeni ki dubi girman Allah ki amsa bukatarmu wallahi nayi Miki alkawari daga wanan bazaa sake fita dake ba Sau daya kacal zaayi abin Nan a Gama,mutumin Nan babban mutum ne bakisan koshi wayeba kidaure ki amince da wanan bukatar tamu Fatima" Kuka na sanya Mata batare da nace komiba Dan bansan mezance mataba, "Kiyi shiru ba kuka nace kizo kiyimunba a Nan ,bazan taba tilastaki Akan aikata hakan ba Amma Ina Mai shaida Miki da kanki Zaki kawo kanki kice kina bukata......" A Raina nake Raya "aikuwa baxan taba kawo kaina domin aikata sabon Allah ba harabada Ina me addua Allah ya kareni daga mummunan aikin" Shiru nayi a tsaye Ina sauraron me hajiya zata Kara cewa,....kaiwa da komowa ta shigayi Rai a bace tacemun "Fatima ta yaro kyau take Bata karko saboda haka kije idan kinsan wata ai Baki San wata ba"...... Da'go kaina nayi da sauri na dubeta ta dakamun tsawa"nace ki fice Koh?" Sumi Sumi kamar wadda kwai ya fashewa a ciki nake tafiya na fice a wajen Ina sharar hawaye..... Ina tafe Ina kuka,babban abinda ya tadamun da hankali shine kalmarta ta karshe "idan kinsan wata ai Baki San wata ba"....sunayen Allah kawai nake Kira Ina kuka har na karasa inda na hango Yaya yarima tare da su bilkisu..... ******* Kwanci tashi babu wuya wajen Allah,tun daga wanna lokacin hajiya Bata Kara tunkarata da maganar fita Dani yawon iskanci ba yayinda likafa kullum Kara gaba takeyi na fita da Yan Mata, Wajen fita da Yan Matan ne firdausi tasamu ciki a wanan lokacin munga tashin hankali Wanda bamu taba ganiba tun hajiya suna boye boye har aka gano firdausi rashin lafiyar da takeyi,Wanda hajiya da kanta ta kawo Mata magunguna Tasha jini ya balle Mata tamkar zata mutu haka Tasha wahala dakyar ta samu lafiya,hakan besa hajiya daina wannan aika aikar ba, Kwatsam muna zaune akazo da takadda Akan muda muka Gama makaranta tun shekarar data wuce cewa gwamnati zata dauki nauyin karatunmu zaa kaimu domin cika form na jarabawar share fagen karatun jamia,bakaramin murna mukayiba cikin wadanda aka kawo subayensu harda sunana saidai Babu na Yan uwana banji dadin hakanba su kuwa suntayani farin ciki sosai.... Saura kwana biyu mutafi hajiya ta shigo har dakin da muke kwana daddare takiramu takawo sababbin Kaya ta Raba Mana inda Ni aka bani wannan rigar dake jikina pink colour tace insa tagani.... Ina saka rigar ta amshi jikina sosai na da'go Kai Ina kallon hajiya Tana murmushi Wanda bansan dalilinta na hakan ba nikuwa kunyace ta lullubeni na sunkuyar da kaina Ina tsaye.... Hajiya tace "to wadda ta kawo kunya duniya,ko itan ma zakice bazaki iya sawa bane?sarkin musulunci?wadda ta yankewa ustazanci cibiya?Ina abun ustazanci anan anyi cikinki a titi an wurgar dake gwamnati ta taimaka Miki har wata kafafa zakiyi?keda Zaki karar da rayuwarki a gidan marayu batare da ko Kare ya shinshine yace zai aurekiba?saboda Babu Wanda zai dauki tsintacciyar mage Dan Bata mage" Hawayene suka wankemun idanuwa Jin irin cin zarafin da hajiya kemun take na tuna da kalmar Yaya yarima da yacemun a lokacin "insha allahu Ni Zan Zama sanadiyyar farin cikinki Fatima bazaki dawwama a gidan marayu ba inhar Ina Raye"....wani sanyin dadine ya ratsani Dana tunada wanna kalmar saita wankemun cin zarafin da hajiya tayimun....na tube rigar na Mika mata tace"ki ajiyeta a wajenki domin ita zakisa Dan akwai inda nakeson biyawa daku idan kuntashi jarabawar,gabana ne ya shiga faduwa zuciyata ta shiga bugawa sauri da sauri,ilahirin jikina Babu inda baya rawa..... Murmushi hajiya tayi tace "yaro yaro ne"....ta juya abinta ta wuce Ni kuwa na bita da kallo jiki a sanyaye.... ******* Yau ta kasance Ana gobe zamuje jarabawar,tunda na tashi nake Dan Jin zazzabi gabaki daya hankalina baa kwance yakeba tunani nakeyi kala kala yayinda nake tsintar kaina cikin faduwar gaba Wanda bansan dalilinsaba, Ina zaune a Kan benci Yan uwana suka zagayeni na rafka uban tagumi, Hannu bilkisu tasa ta ciremun tagumin tace"Fatima banason kinasawa ranki damuwa nafada Miki hajiya tabar wanan maganar tunda dadewa ki kwantar da hankalinki ki cire damuwa a zuciyarta" Wasu zafafan hawayene suka shiga saukadaga idanuwana Babu kakkautawa juyowa nayi da dubana Ina kallon bilkisu da wani irin kallo Wanda bansan irinsaba nikaina ,kallonta nake Babu kakkautawa, Huramun iska tayi a idon tace"Fatima yadai kikemun wannan kallon Kuma kina hawaye ?saikace wadda idan ta tafi bazata dawoba?" Runtse idanuwana nayi nace"haka nakeji a jikina bilkisu,ji nakeyi tamkar kallon karshe nakeyi Miki tamkar bazan sake rayuwa a cikinkuba,inajin wani bakon lamari a jikina tamkar wani Abu na Shirin faruwa Dani" Bude idanuwana nayi na saukesu Akan bilkisu Naga itama hawayen takeyi....rungume juna mukayi muna kukan da bamusan dalilinsaba...... *Muje zuwa shafi na gaba Kuma karshe Akan labarin Fatima....ya abin zai kasance?* *SLIMZY🥰✍🏻**🌩ANYI WALK'IYA.....🌩* *💡 HASKE WRITERS ASSOCIATION💡* *NA SLIMZY* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata Faty D'an maliki* 11 Kuka sosai mukeyi nida Yar uwata bilkisu Babu me lallashin wan hakikanin gaskiya tausayin kanmu nakeji a wanan lokacin saboda rayuwar da mukeyi ta rashin gata,uwa uba rashin gata yasa ake dibarmu Ana lalata Mana rayuwa,inda a gaban iyayenmu muke hakan bazata faru ba.... Kwana nayi Ina zubda hawaye wanda bansan dalilinsaba haka kawai na tsinci kaina a matsananciyar damuwar da bansan dalilinta ba..... ******** Washe gari da sassafe aka kawo mota yayinda dukanmu muka shirya tsaf damu muka karya da kunu da kosai ,misalin karfe bakwai da rabi mukaita shiga mota....sauran yara Yan uwanmu Sai fatan alheri da samun nasara sukeyi Mana, Har na shiga mota na fito na rungume bilkisu Yar uwata hade da bubbuga bayanta nace "ki kula da kanki Sai Allah ya Kara hadamu" Kwallar da nake boyewa CE to sulalo a idanuwana,ban Bari taganiba nasanya hannuna na goge na kauda fuskata na shige motar aka jamu,Sai daga musu hannu mukeyi..... Tsagaitawa Fatima tayi da labarin ta kalli barrister hauwa wadda ke kuka harda majinu Tana kallon Fatima cike da tsantsar tausayawa ,girgiza Kai Fatima tayi itama Tana hawayen ta cigaba da cewa.... Makarantar da zaa kaimu yin jarabawa Nan aka nufa damu,Sai kallonmu sauran yara sukeyi da jamaar wajen mussaman da akace yaran gidan marayu ne wasu na tausaya Mana wasu najin kyamar mu,nidai ko a jikina tunda nasan cewa baninayi kainaba Allah ne yayini,a haka aka shigar damu ajin jarabawa inda mukabar hajiya da haruna zaune jikin mota suna jiranmu. Nice farkon fitowa da aka Gama babu inda na nufa Sai wajen motar mu,a Nan na tararda su hajiya halima,tun daga nesa sukemun faraa itada haruna Sai jikina be bani ba Amma Sai na kauda zargi a zuciyata Dan babu kyau.... Dan durkusawa nayi nace "sannu da hutawa hajiya"na sunkuyar da kaina, Washe Baki hajiya tayi tace "Fatima kune zaayiwa sannu kuda kukasha Zama a ciki,Allah dai ya bada saa Fatima" "Ameeen hajiya" Na koma jikin mota na jingina, Malam haruna ne ya juyo ya miko min lemon gora guda daya da fanke yacemun ga nawa sauran ma zaa Basu nasu, Hannuna na rawa na amsa nayi Masa godiya,na tako na karasa Kan wani benci wajen Mai Saida abinci na zauna Ina ci Ina kurban lemon Nan saboda yunwar da nakeji,minti minti Ina da'go Kai in kalli wajen dasu hajiya ke zaune tare da haruna saboda kada Yan uwana su fito a tafi a barni ,Sai Inga Basu fitoba hajiya CE ke shewarta itada haruna a wajen. Biyu na Raba lemon da fanken na ajiyewa bilkisu Yar uwata Wanda Zan Kai Mata a matsayin tsaraba idan na koma,Ina Nan zaune shiru shiru nafara gyangyadi wani irin bacci Mai nauyin gaske yake dibata Ina wartsake idona,tun Ina controlling kaina har na kasa,na kifa kaina a cinyata na Soma bacci...... Zuwa wannan lokacin kukan Fatima ya tsananta,barrister hauwa ta dafa kafadarta tace"daure ki karasamun labarin Nan Fatima Kinga ankusa zuwa tafiya dake ga yamma tayi" Share hawaye Fatima tayi ta cigaba da magana.... Wanan baccin da nayi shine Wanda ban farkaba Sai cikin dare Wanda Ina bude idanuwana na ganni Akan babban gado Wanda tunda nazo duniya ban taba Hawa irinsa ba, Zumbur na Mike nafara waige waige,Ganin irin dukiyar dake cikin dakin tamkar dakin wani sarki ko shugaban kasa,kici kicin sakkowa nafarayi Sai naji motsin bude kofa da sauri na waiga, Muna hada Ido dashi na zaro idanuwana waje tamkar zasu fito hade da Dafe kirjina,Nan da Nan jikina ya dauki rawa tamkar mazari dik sanyin AC dake dakin da fanka be hanani sharbewa da gumiba cikin seconds da Basu wuce talatin ba, Kafeni yayi da idanuwansa Yana sanye da jallabiya Fara yace "babe har kintashi?yanzun nake cewa wanan baccin idan ba na mutuwa bane ya kamata kitashi,niyyata idan Baki tashiba in daukeki inyi Miki wanka Kila kitashi" Bakina na rawa nace "wanka Kuma bawan Allah ?" Mai makon ya amsamun Sai ya daga mun gira daya kawai ya nemi kujera ya zauna ya janyo karamin table Wanda ke dauke da apple da wuka akai ya Fara yankawa yanaci Yana kallon tangamemen tv dake faman aiki a dakin,.. Munsamu kimanin minti biyu Babu abinda ke Kara Sai tv sainan ya juyo da dubansa gareni yace "kitashi kiyi wanka ki gargasa jikinki Dan bazan hada jiki dake kina danko na dauda ba" Wani irin bugu kirjina keyi tamkar zuciyata zata fito a Raina nace "hada jiki?"....waya kawoni Nan?...take su hajiya suka fadomin ,gabana ya Yanke ya Fadi Dana tuna da kalmarta ta "ta yaro kyau take Bata karko,idan kinsan wata bakisan wataba" Dago kaina nayi da sauri na dubesa beko kalli inda nake zaune ba apple dinsa kawai yake yanka yanaci tamkar Mai yanga haka yake motsa bakinsa,...tsura Masa idanuwa nayi inaso in tuno a inda nasanshi,....take na tuna shine Dan sarki Wanda sukazo kawo Mana tallafi kwanakin baya masu yawa da suka wuce,sanan shine Dan takarar sanata na wanan jaha tamu....."innalillahi wa Inna ilaihi rajiun"....dama abinda sukeyi kenan su fake da guzuma su harbi karsana?....jikina ya jike da zufa tabbas wanan zaluncine,shin kowa ne yake haka ko kuwa wadansu ne ke Bata wasu cikin masu kudin? Ina cikin wanan tunanin maganarsa ta dawo Dani hayyacina "Fatima sunanki ko?" Da sauri na gyada Masa kaina alamar ehh "nace ki tashi kiyi wanka kinki dare nayi gashi inaso in huta dake,saboda hajiyarku ta tabbatar mun dake cikakkiyar budurwa CE" Nan da Nan naji marata ta kulle inajin fitsari,idan nayi kwakkwaran motsi Zan iya sakin fitsari,zuciyata ke harbawa sauri da sauri.... Bakina na rawa nace "Dan Allah kayi hakuri kada ka lalatamun rayuwa" Wani mayaudarin murmushi yayi ta gefe daya ya waigo ya dubeni yace "dama ku yaran talakawa kunada wata ingantacciyar rayuwa ne?ko kuwa ku da iyayenku suka wofintar daku a titi aka tsunceku aka rufa muku asiri aka killa ceku?" Kallonsa nakeyi Ina hawaye,bakaramin ciwo maganarsa tayimunba,dama suna amfani da damar bamuda gata suke Bata Mana rayuwa?" Kuka sosai nakeyi harda shassheka ya juyo da kallonsa gareni a Karo na biyu yace "tunda bazaki wankanba na Baki minti biyar ki cire rigar jikinki domin idan xan kwanta da mace bana kwanciya da ita da Kaya" Kallonsa nakeyi Ina hawaye nace "Dan girman Allah ka rufamun asiri kada ka rabani da budurcina" Kyalkyalewa da dariya yayi a wanan karon yace "Fatima ai budurcin naki nake bukata,kinsan nawa na kashe Akan wanan kyakkyawan jikin naki da budurcin naki?Koda yake kudi ba matsalata bane,matsalata in kashe kishin ruwanki dake damuna,tunda nasaki a Ido dik macen da aka kawomin bana samun gamsuwa da ita Dana runtse idanuwana ke nake gani ke kawai nake bukata nikuwa ban taba neman Abu narasaba ,dik abinda nasa a gaba saina samu,ki yarda Dani in mallaki wanan Surar da Allah yayi Miki daganan Zan yantaki ki Zama baiwata Mai kula Dani a matsayina na Dan sarki Kuma sarki Mai jiran gado" Gabana ne ya Yanke ya Fadi na shiga girgiza kaina Dana tunada Yaya yarima a kullum burinsa Bai wuce Allah ya bashi ikon ingantamun rayuwaba,Sai gashi Dan uwansa keda burin lalatamun rayuwa....runtse idanuwana nayi Ina Mai adduar Allah ya dauki Raina a wanan lokacin in huta.... Idanuwana a rufe,batare da nasani ba ya Mike ya kashe tv sanan yasa key a kofar yabar key din a jiki ,ya kashe fitulun dakin Sai wata Mai haske kadan ya Bari ya hayo saman gadon ,hannunsa naji ya rungumoni Yana fadin "taho inyi Miki masauki a jikina in share wadanan hawayen dake Bata wanan kyakkyawan fuskan da tazo a gidan marayu" Zabura nayi Zan kwace ya rinkeni tsam a jikinsa tamkar zai ballani,dakyar nake numfashi Ina kici kicin kwacewa ya tura hannunsa saman rigata Yana lalubena,mutsu mutsu nakeyi rikon da yayimun bazan iya kwacewa ba kawai nasa hakorina a kunnensa na yanka Masa cizo zafin da yajine ya sakeni na Mike a guje nayi lungun kujerar da ya zauna yaci apple, Biyoni yayi ya damkoni cikin zafin nama ya rungumeni ya haye jikina ,waige waige nakeyi Babu yadda xanyi in Kara cizonsa,hannunsa daya na cikin rigata Yana wasa da kirjina gashi ya sakarmun nauyi,sosai yake mutsukamin jiki inajin zafi Yana kokarin rabani da rigar jikina, Gefe na hangi Wukar da yaci apple da ita na rinka matsawa da hannuna har nakai wajen Wukar na janyota a hankali na rike a hannuna Babu yadda zaayi inyi motsi, Gyarawa yayi da niyyar hayeni,da sauri na da'go Wukar na ca...ka Masa..... Kuka Mai karfi Fatima ta fashe dashi Tana numfarfashi tamkar zata hadiyi zuciya ta mutu..... Dafe Kai barrister hauwa tayi zuciyarta na tsananin bugawa da sauri da sauri..... Ta dago Kai ta kalli Fatima dake kuka tace "tabbas kece Kika kashe yarima habib Amma kisan Kare Kai" Kuka Fatima takeyi Tana fadin "anty kada kibari a sakeni,kicire hannunki daga kareni a matsayina na Mai laifi kibari a yankemun hukuncin da yayi daidai Dani"..... Tana durkushe Tana kuka barrister hauwa na gefe Tana sharar hawayen dake zubowa a idanuwanta,wani Dan sanda ya shigo yace "lokaci yayi madam".... Ka'da Masa Kai barrister hauwa tayi ta Mike dakyar takejan kafarta ta fito....... *SLIMZY🥰✍🏻*🌩 *ANYI WALK'IYA.....* 🌩 *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA:SLIMZY✍🏼* _wattpad@slimzy33_ *sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* 12 Tafe take Tana sharar hawaye har ta karaso wajen mota inda barrister Abdul tun fitowarta ya kafeta da idanuwa,ta wani fannin zuciyarsa keyi Masa lugude cike da fargabar me zai biyo baya, Mota ta bude ta shigo idanuwanta jajur tamkar wadda akayiwa dukan tsiya,kallonta mijin nata keyi cikin kosawa yace "madam badai yarinyar nan tayi taurin Kai ba" Girgiza Masa Kai tayi cikin dasasshiyar murya tace "ko daya,tayi bayani yadda akeso inaso ka Kira yarima kafin muje gida kace mu hadu a gida" Wayarsa ya zaro a aljihunsa nan da nan yayi dialing number yarima,Wanda bugu daya ya dauka kamar me jira, barrister Abdul yace "ranka ya Dade gamunan zamu taso daga police station kazo gida mu hadu" "Ok"kawai yarima yace ya datse wayar.... Driving barrister Abdul keyi Amma minti minti yakan juyo ya kalli barrister wadda har yanzun hawaye be daina gudu a idanuwantaba,hankalinsa ba karamin tashi yayi,ya kosa su Isa gida yaji meke faruwa? Yana kwanar unguwarsu daike GRA yarima Yana karyo kwana da tasa motar Yana biye dasu Mai gadi ya bude musu gate suka shige a tare, Koda barrister ta fito,kallo daya yarima yayi mata yasan akwai matsala,dik inda hankalinsa yake a wanan lokacin a tashe yake, Haka sukaja jiki barrister hauwa ta kwankwasa kofa,wata matashiyar budurwa Mai tsananin Kama da ita ta bude musu kofa wadda ko baa fada ba kawanwarta ce ,Dan tsugunnawa tayi tace "barkanku da zuwa" Babu Wanda ya amsa sai yareema da ya karba a ciki,sanan tace "Ina yini Yaya yarima" "Lafiya lau Aysha,ya makaranta?" "Alhamdulillah"tace ta juya ta shige dakinta,su Kuma sukai maxauni a parlor.... Barrister hauwa ce ta gabatarwa da yarima da barrister Abdul recording din bayanin Fatima..... Saurare sukeyi Amma ko kafin su Gama barrister Abdul jikinsa ya jike da gumi,yayinda yarima fuskarsa ta jike da hauwaye da zufa a lokaci da'ya,dakyar suka iya karasa sauraren audio din.... A haukace yarima ya Mike ya kauwa iska nushi,idanuwansa tamkar garwashin wuta yayinda jijiyoyin kansa suka fito a goshinsa Rada Rada yace cikin kakkausar murya "biri yayi Kama da mutum,tabbas habib zai aikata hakan domin a rayuwarsa ta duniya Babu abinda yake kauna fiye da mace,gashi mace tayi sanaddiyar aikasa lahira,shin wasu kalamai ya tanada domin yiwa Allah bayani akan abinda yaje aikatawa yayi sanadiyyar bakuntarsa lahira?shin da wani baki zaiyiwa Allah bayanin cewa marainiyar Allah yaje lalatawa rayuwa Allah ya karbi rayuwarsa a wanan lokacin?.....nasani ko Fatima Bata kasheshiba,tunda Allah bai kaddaro zai lalata mata rayuwaba Allah bazai bashi damar yin hakan ba,dik dukiyarsa dik takamarsa da mulki Allah zai karbi numfashinsa a lokacin da yaso,ya godewa Allah ma ba aikata zinar yakeyiba Allah ya karbi numfashinsa"kuka sosai yarima yakeyi Yana kaiwa da komowa cikin parlorn ya rasa inda zaisa rayuwarsa... Hawaye barrister hauwa ta share tace" *ANYI WALK'IYA* halin kowa ya fito,shin wanan muguwar dabiar da akesa yara aikatawa masuyi suna tunanin Allah zai kyalesu?ko asirinsu bai toniba a Nan duniya Allah zai tona musu asiri a lahira ballantana dik Wanda ya cutar da maraya daidai da kwayar zarra sai Allah ya fitar Masa da hakkinsa tun a duniya,yanzun gashi tun baaje ko inaba *ANYI WALK'IYA* halin kowa ya fito...asiri na gab da tonuwa"kuka takeyi tamkar wadda akaiwa mutuwa, Cikin alhini barrister Abdul Wanda jikinsa gabaki daya ya mutu dauriyace da jarumta yasa Shima bai zubarbda hawayen ba yace "kuyi shiru ku kwantar da hankalinku yanzun abinyi zamu tattauna,yadda shariar Nan zata gudana" Juyowa yayi yarima daga kallon gefe daya da yakeyi ya sauke rinannun idanuwansa akan barrister Abdul sanan yace "insha Allahu Fatima zata fita ,a wanan shariar domin self defense ta zo yiwa kanta,sanan koba haka ba akwai casset na CCTV da hajiya babba tace ta anso wadda inada tabbacin akwai komi a ciki Kuma Bata kalla ba ballantana tasan wani Abu,shi zan gabatar a kotu Wanda shine a matsayin shaidata na kisan habib kaga Ina gabatarwa wanan casset shi zai wanke Fatima" Murmushi barrister hauwa tayi Tana hawaye a lokaci da'ya tace"to alhamdulillah insha Allahu nasara na garemu" "Allah yasa"cewar yarima dukkansu suka amsa da "ameeen" Juyowa barrister hauwa tayi ta kwalawa sister dinta Kira "Ashmah!!kawo Mana abinci Dan Allah " "Toh"ta amsa daga cikin daki,sanan ta fito ta shiga shigowa da kululin abinci,Nan suka baje sunaci,dikda yarima cin abincin yakeyi tamkar magani...... ******** Da dawowarsa gida bangaren hajiya babba ya nufa direct,da sallamarsa ya shiga sanan ya durkusa a gabanta ya kawo gaisuwa,ta amsa Masa cike da kasaita,ko kafin yayi magana ta juya gefenta ta dakko wani sabin casset sai WALK'IYA yakeyi ta mikawa yarima ,ya amsa yace "Allah ya bamu nasara" "Ameeen "tace hade da lumshe idanuwanta Tana ayyana abubuwa da dama..... ********* Daren ranan yadda yarima yaga Rana haka yaga dare,da ya kwanta ya rufe idanuwansa amsa kuwwar muryar Fatima yakeji na audio Wanda take bayani,bayasanin lokacin da yake tsuntar kansa cikin hawaye masu dumi Wanda shi kansa besan yanayinsu ba,haka har asuba ta gabato.... ******* Washe gari ko kafin ya shirya ya fito daga bangarensa tawagar motoci da securities dik sun shirya domin wanan tafiyar da hajiya babba zaaiyita wargidan sarki,Wanda yarima yasha mamakin Jin hadda hajiya babba zaaje,tare da kannensa,da tawagar bayi masu take mata baya, Haka kawai ya tsunci kansa cikin faduwar gaba,haka ya daure ya gaida iyayen nasa,sanan yayi musu jagora don tafiya..... ******* Tun daga harabar kotu zaka tabbatar da yau shariar Mai zafice jamaa cike makil har waje, securities ne suke gyarawa Ana budawa tawagar gidan sarki hanya ,inda idanuwan mutane sukai caaa akan sarauniya da yaranta Yan mata Wanda suka fito suna taku daidai suna kallon mutane a wulakance har cikin kotu, Babu wajen Zama Amma haka aka tashi jamaa don matar sarki da yaranta su samu wajen Zama,Nan dogarawa da bayi duka zagayesu.... *Courtttttttt* Kowa ya mike lokacin da maigirma alkali ya shigo kotu... Bayan ya zauna ,sannan kowa ya samu wurin Zama a don sauraren wannan shariah Mai sarkakiya da chakwakwiya... "Ya Mai girma Mai shariah, a yaune kotu zataci gaba da sauraren karar da akeyi akan Fatima Zahra wadda ake zargi ta kashe yarima habibu Dan sarki"... " Koh lauyoyi masu karewa da wadda suke Kara suna kotu?".cewar alkali..... "Eh ,yamai shariah" yarima Kabir ya rankwafa alamar girmamawa Itama Barr hauwa da Abdul suka rankwafa cikin girmamawa..... " Kotu na saurarenku"..... A nutse yarima Kabir ya tashi tsaye sannan yace ... "Yamai shariah zanso kotu ta bani dama domin ingabatar da sheduna, Akan kisan da fatyma Zahra tayi" "Kotu ta baka dama Barrister Kabir".. "Ya Mai shariah ranar 20 ga watan june Fatima Zahra ta ziyarci guess house na masarautar barayar Zaki, inda aka Kamata da kisan Dan gidan sarki habib..." "Objection my Lord ,"Barr hauwa tafada cike da kunar Rai kamar batasan yarima Kabir ba, "yakamata Barrister ya gyara salon tambayarshi, domin har yanxu zargi ake ba a tabbatar da Fatima a matsayin a Mai laifiba" "Ka gyara salon tambayarka Barrister" "Nagode ya Mai shariah" "Ya Mai shariah zanso kotu ta bani dama domin a kunna wannan CCTV cassette na yadda kisan ya kasance" Hajiya babba dake gefe Tana kallon komi sai a wanan lokacin tayi murmushi, A hankali komi ke tafiya tundaga lokacin da Fatima ta farka a firgice Tana kallon yarima har zuwa lokacin da ya koma gefe yanacin apple abinshi , daga Nan Kuma kawai sai aka Nuno Fatima Zahra rike da wuka ta dabamai, Hayaniyace sosai ke tashi , hajiya babba Koh sai wani murmushin nasara take yi Shiko Barrister Kabir mamaki ne da fargaba suka rufeshi don beyi tunanin anyi editing wani Abu a cassette din ba, Dakyar ya Tattaro natsuwar shi da jarumta, sannan yace cikin karyewar zuciya "Yamai shariah wannan cassette shike nuna Fatima Zahra itace tayi kisan da ake zarginta dashi na yarima habib,nagode ya Mai shariah" sannan ya koma mazauninshi, Wasu zafafan hawaye ke zubowa a kuncin Fatima,hade da runtse idanuwanta, Rubuce rubuce alkali yayi sannan yace "Koh lauyan wadda ake zargi sunada abin cewa?"... A hankali Barr hauwa ta Mike take tafiya kamar wadda kwai ya fashemawa a ciki ,da alama zuciyarta a karye take game da case din Fatima Zahra.ta matsa inda Fatima Zahra ke tsaye Tana hawaye, "Mal Fatima , zanso ki kwantar da hankalin ki Nan gidan adalci ne , kiyi bayanin abinda kika sani game da mutuwar yarima habib Dan sarki" Sai da ta share kwallah da ke bisa fuskarta ,sannan taja majina tafara bayani a hankali ........ Daya bayan daya take yarfo bayani kamar yadda tafadama barrister hauwa , sannan ta karashe cikin kuka Mai karfi... Hayaniyace ta kaure a kotun kowa da abinda yake fade , A fakaice Barr hauwa tashare hawayenta da ya digo Mata sannan tace "Ya Mai shariah inaso kotu tayi laakari da cewa Fatima Bata kashe yarima habib daganganba inllah domin ta kare kanta *(self defense)*, "Yamai shariah I refer to section 59 of d penal code ,.Wanda yake bayanin mutum yakashe wani a dalilin Kare kanshi Koh dukiyarshi, Yamai shariah, inaso kotu ta duba lamarin Fatima Zahra duba da wannan section na penal code,nagode ya Mai shariah" "Kotu zataje hutun Rabin lokaci intadawo zaa cigaba" *Courtttttttt*....... Bayan kowa yafita ciki kuwa harda tawagar gidan sarki,ya rage sai kawyoyi kadai cikin kotun suna rubuce rubuce, Barristers Abdul ,hauwa da yarima Kabir sukayi mahada domin Kara tattaunawa kan case din, domin dukkansu sun tsorata da cassette din da suka gani,dikda yarima Yana zargin akwai wata manakisa Wanda babu tantama hajiya babba ce ta hadata, Sosai Barrister hauwa ke kuka wiwi , ta kalli yarima tace cikin kuka , " ranka ya Dade Fatima Zahra na cikin wani Hali wallahi, domin inde alkali be duba lamarin Fatima ba under section 59 to wallahii Babu Mai fitar da ita sai Allah don bamuda wata kwakkwarar hujja ta bayanin da Fatima keyi,". Jan majina tayi sannan tacigaba da cewa " kaduba kaga cassette dinnan wallahi da gani ba complete bane, gashi mukuma bamuda wani shedar da zamu gabatar Wanda zai nuna Kare kanta tazoyi"😭😭😭😭 Sosai ta rikice ,a hankali Barrister Abdul ya rungumeta Yana bubbaga bayanta alamar tayi shuru sannan shima yace , "ki kwantar da hankalinki my jidda, Allah na tare damu insha Allah Fatima Zata kubuta" Yarima Kabir wanda tunda hauwa ta Fara bayani yakarajin ya tsani wannan duniyar da bakomi cikinta sai San zuciya,da cuta da rashin gaskiya, dafe da kanshi yake wadda yakeji kamar zai tsage biyu, Sunfi minti 20 batare da sun samo solution ba, kowannan su ranshi a dagule yake,ganin saura 10minutes, Barrister Abdul yayi karfin halin Basu kwarinvgwiwar kan sucigaba da adduah insha Allah Fatima Zahra zata kubuta......, *Bayan Rabin Awa* " Bayan tattaro dukkannin bayanai da shedu da aka gabatar a gaban kotu , kotu zata gabatar da hukunci kamar haka," "Fatima Zahra ba zaa iya guaranting dinta self defense ba, saboda a cassette din da aka gabatar gaban kotu ya nuna kawai anga ta chakamasa wuka batare da sanin meyamata tayimai hakanba" Gaban barrister yarima ya yanke ya fadi,ya dago idanuwansa hade da kafesu akan alkali, "A bisa dalili da Haka kotu ta yankewa fatimazahra hukuncin kisa ta hanyar,..... "A dakata ya Mai shariah ,adakata" wani maaikacin gidan guest house na gidan sarkine ,Wanda ranan da hajiya babba ta je guest house din ya labe ya saurari komi gameda tattaunawarsu da yakubu ne yashigo Yana haki kamar anjehoshi, Kowa kallonshi yakeyi cike da mamaki , hajiya babba dake gefe kallonsa takeyi cike da fargabar abinda yazoyi, ta tashiga firgici,hade da juyawa gefe da gefenta,ganin habu daya daga cikin masu tsaron guess house din,ta juyo da dubanta hade da kafesa da ido, Sai da ya Dede ta natsuwarshi sannan ya Fara bayani dallah dallah "Yamai shariah wannan shine asalin cassette me dauke dakkannin bayanai game da kisan yarima Kabir" Gaban hajiya babba ne ya yanke ya fadi,tayi kurrr da ido Tana kallonsa, "Wanda aka gabatar a kotu bashi bane na gaskiya,domin an goge wurare da dama a cikinsa...Wanda hakan ya farune a sanadiyyar umarni da aka bada ayi hakan,Wanda basaina fadi Wanda ya bada umarnin hakanba" Nan kotu ta har gitse da hayaniya,saida alkali yayi gyaran murya ya bada umarnin ayi shiru ,Shima ya maida dubansa ga wanan bawan Allah Yana Mai sauraronsa, "Mai shariah na gwammaci in Fadi gaskiya ne domin ubangiji bazai barni cikin kwanciyar hankaliba in har nabari aka yankema wannan marainiyar Allah hukunci bisa kuskure,Wanda ni nasan gaskiya na take sanin," Mika cassette din akayi sannan akasa yafito tar a projector kowa na kwalalo idon ganin ya abin yake...... *Muje zuwa😂🏃🏻‍♀....na gudu tunkafin hajiya babba ta kamoni* *SLIMZY🥰✍🏼*🌩 *ANYI WALK'IYA.....* 🌩 *HASKE WRITERS ASSOCIATION💡* *NA:SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* _Allah ubangiji ya jikanki yayi Miki rahma_ *HAFSAT RADDA* 😭😭😭 13 Tiryan tiryen duk abinda ya faru tsakanin yareema habib da Fatima Zahra ke fita tar a projector da aka kunna a court, Mamakine dankare a fuskokin alumma , Nan da Nan kotu ta kaure da hayaniya, Barrister hauwa farincikinta a lokacin be misaltuwa, ita da Barrister Abdul ganin Allah ya bayyana gaskiya,..gogan Koh hamdala kawai yakeyi Yana kara godema Allah abisa wannan gaskiya da ta bayyana ,sosai yakejin farinciki mara misaltuwa a cikin zuciyarshi, Hajiya babba duk ta rikice take sai zare ido take yi,Amma can kasan zuciyarta ita kadai tasan abubuwan da take ayyanawa, Bayan bubbuga tebir, sannan aka bukaci kowa yayi shuru domin alkali ya gabatar da hukunci, Dattijo Mai cike da kamala da natsuwa wato alkali abubukar assadiq ne ya Gyara zaman gilas dinshi sannan ya dago Kai ya kalli alummar cikin kotun cike da natsuwa hade da kwarjininshi,yayinda kowa yayi tsit tamkar babu jamaa a ciki don sauraren mai alkali zai yanke, "Abisa shedu da suka gabata a gaban kotu , bayan dogon nazari kotu ta yanke hukunci kamar haka" " Kotu tayi laakari da cewa Fatima Zahra Bata kashe yarima habib da ganganba inlla domin Kare kanta, Abisa dalili da Haka kotu tayi granting release na Fatima Zahra akarkashin tsari na section 59 of d penal code,don Haka kotu ta sallami fatyma Zahara (discharge and acquitted) "Sanan kotu tabawa jamian tsaro damar kamo maaikatan gidan marayu wato hajiya halima da haruna, Don kotu ta yanke musu hukuncin zaman gidan kaso na shekara biyar, Duk wani Mai complain zai iya daukaka Kara zuwa kotu ta gaba..." *Courtttttttttttttttt* A hankalinki Fatima Zahra ta runtse idanuwanta tanamai hamdala ga ubangijinta a lokacin da Alkali ya wanketa,ta rasa a wani yanayi ta tsinci kanta a wanan lokacin,farin ciki ne koko bakin ciki?....idanuwanta ta bude karaf sukai ido hudu da yarima,murmushi ya sakar mata a fakaice hade da kanne mata ido daya take ya waske tamkar bashiba, Barrister hauwa kasa boye farincikinta tayi saida ta mikama Barrister Abdul hannu sukayi wani musabaha cikin kauna irin ta Mata da miji, A hankali Barrister Abdul ya Rada Mata a kunne , "yade madam kuka ya karekoh" ......murmushi tayi sosai har saida hokoranta suka bayya cikin tsantsan farinciki, Suna a hakane yarima Kabir yayi gyaran murya sannan ya mikama Barrister Abdul hannu sukayi musabaha,sanan ya juya ya shiga ayarin tawagar gidansu don tafiya gida, Takowa Fatima tayi a hankali har ta iso inda su barrister Abdul ke tsaye shida madam dinsa,Tana kokarin tsugunnawa barrister hauwa ta dagota ta Kai mata runguma ,wani kukan Dadi Fatima ta fashe dashi barrister hauwa na bubbuga bayanta alamar lallashi, Dago kan Fatima tayi tasa hannu ta share Mata hawaye tace"kuka ya Kare Fatima,ai kinyi kuka iyayinki yanzun lokacine da Zaki godewa Allah Akan bayyanar da gaskiya da yayi,lokaci da'ya kika tsinci kanki a balai na duhun masifa Wanda muka kasa bayyana Haske,sai Allah da kansa ya bayyana , *ANYI WALK'IYA* halin kowa ya fito saiki godewa Allah da niimar da yayi Miki" Jinjina Kai Fatima tayi hade da yin murmushi Mai kayatarwa sanan barrister hauwa ta sauke ajiyar zuciya tace"ya kamata muje dake gidana yanzun kiyi wanka ki huta zuwa wani lokaci kafin musan abunyi ko" Harga Allah Fatima bataso haka ba saidai a yanzun batada burin da ya wuce yiwa barrister hauwa biyayya domin ta nuna Mata kauna a lokacin da take tunanin babu Wanda zai kaunaceta a duniya.... Babu musu tabi bayansu har wajen motarsu suka shiga barrister Abdul yaja mota...... ********* "Bazan taba samun kwanciyar hankaliba matukar ban karbi hakkin da'na daya tilo ba,Domin wanan shariar akwai manakisa a cikinta akwai wata kulalliya Kuma wallahi dik Wanda yace zaija Dani to zan iya ganin bayansa" Kallonta khausar keyi sanan tace "Niko a ganina mama bamuda wata hujja da zamu Mika wanan Sharia zuwa want kotu Domin ko mun daukaka Kara Dole sai munbada hujja Kuma bamuda ita" A fusace hajiya babba ta fara balbala masifa tamkar ta Ari baki "meye amfanin mulkin da nake dashi?meye amfanin dukiyar da Allah ya bani?da bazanyi amfani da itaba wajen kwatarwa Dana yancinsa bayan anyi sanadiyyar ransa sanan anbishi da sharri to wallahi da sake" Kamshin turaren yarima ne ya karade dakin lokacin da ya shigo Yana sauraron furucin da hajiya babba keyi, Goya hannunta tayi ta baya Tana kaiwa da komowa cikin parlorn fuskarta babu annuri,sallamarsa ta juyo da ita tace"yanzun nake Shirin aikawa a kiraka don kaji hukuncin Dana yanke na daukaka Kara zuwa supreme Court Dan ni ban yarda da wanan hukuncin ba" Wani malalacin kallo yarima keyi Mata har ta Gama bayani sanan ya yadanyi murmushin karfin Hali yace "wallahi babu hannuna a ciki matukar kika daukaka Kara saidai ki nemi Wanda zai tsaya Miki a kotu Dan badai niba wallahi,munje munsha kunya a kotu Bata ishemuba Kuma sai mun daukaka Kara to wallahi wanan karon bazansa hannuna a cikin abinda zaa wulakanta marainiya ba bayan yunkurin Bata Mata rayuwa da akayi sanan gaskiya tayi halinta Kuma a bita da wani sabon bita da kulli Dan batada kowa?" Kallon mamaki hajiya babba takeyiwa yarima yadda yadda balai Yana daga murya ya manta da wadda yake magana ne? "Kabiru kasan me kake fadamun kuwa?kasan da wadda kake magana kuwa?to ka iya harshenka sanan ka sauya kalamanka Dan wallahi kaima zan iya daukar mataki akanka" Murmushi yarima yayi lokacinda ya dago rinannun idanuwansa Wanda suka sauya lokaci daya "mama ya kamata ki hakura da maganar Nan tunda Mai martaba kansa ya bada umarni akan abar maganar Nan ni Kuma wallahi bazan taba tsallake umarnin mahaifina ba" Cikin kakkausar murya hajiya babba tace "karya kakeyi wallahi baka isaba me akai akayika da zakaja da umarnina to wallahi shi kansa mahaifin naka da kake tutuya da sarautarsa sai abinda nace yakeyi,saboda haka ka shiryawa shariar Dole" "Zan shiryawa shariar Dole ammafa marainiyar Allah zan tsayawa wanan Karo" Da sauri khausar ta kalleshi itama hajiya babba kallonsa takeyi Tana jinjina Kai lokaci daya ta shiga tafa hannu Tana fadin "to kace Kaine ma ka turata ta kashe Dan uwan naka kenan don ka gaji mulki shiyasa yanzun kake ikirarin tsaya Mata a shariah" Zuwa wanan lokacin ran yarima yayi kololuwan baci idanuwansa,jikinsa na rawa bakinsa na kwrkarwa kamar maijin sanyi yace"meye ribata idan na aikata hakan?meye ribata da akan mulki zanyi sanadiyyar Dan uwana bayan inda yaje zanje?gaskiya hajiya kinbani kunya sanan kinbani mamaki ban taba tunanin Zaki wannan furucin akainaba,sai gashi lokaci kankani kina neman banbantani da habib" Mama karama ce ta shigo da sauri har Tana hardewa itada afnan kanwar yarima, Karasowa tayi cikin parlorn ta tsaya cikin kidimewa tafara magana"kabiru ya najin muryarka sama sama akan ta maman naka?meyafaru ne" Kallon raini hajiya babba keyiwa mama karama sanan tace"yazo ne ya nunamin cewa yagirma ban Isa nasashiba ko na hanashi,sanan yazo ne ya sanar Dani abinda nake bukatar sani a kwanakin baya,yazone ya fadamun cewa yanada hannu akan kisan Dan uwansa yarima" Dafe kirji mama karama tayi tace"ban fahimci inda maganar Nan ta dosa ba ku warwaremun ita" Murmushin takaici yarima yayi yace"maganace ta daukaka Kara da mama kesonyi nace babu hannuna a cikinta tunda mahaifina da kowa yace ya cire hannunsa,Kinga ko bazan sabawa mahaifina ba abinda nasani guda daya shine nine zan tsayawa Fatima Zahra a wanan shariar ta supreme Court insha Allahu Kuma muke da nasara" Da sauri mama karama ta wanka mishi mari Yana dagowa ta Kara Kai Masa wani Marin"kana hauka ne?kabiru kasan abinda kake fada kuwa?ko kayi shaye shayene?to wallahi bada yawunaba inhar zaka tsayawa Fatima wadda tayi sanaddiyar zuwan Dan uwanka lahira shariah" Dafe gefen kuncinsa yayi zuciyarsa na tsananin tafarfasa yace"owk saboda ita batada gata?saboda ita batada Wanda zai tsaya mata?to kada ku manta Allah ne ya fiddata a wanan shariar Kuma shine zai tsaya Mata a gaba Kuma Nima zan tsaya Mata babu gudu babu ja da baya" "Ina magana kana magana Kabir?idanuwanka sun rufe ko?to wallahi baka isaba" Itadai hajiya babba kasa magana tayi zuciyarta cike take taf da mamakin haukacewar da yarima yayi musu Wanda tunda suke dashi be taba yi musu hakanba, Hawayene yake gangarowa a idanuwansa Yana kallonsu dafe da kuncinsa"wallahi ko kowa zai juyawa Fatima baya a duniya ni bazan juya mataba,saboda marainiya ce ake Shirin cutar da ita,Kuma rikon Fatima zai dawo hannuna a cikin gidan Nan" "Kana haukane kabiru ai babu mahalukin daya Isa yazo da Fatima ko kofar gidan Nan ballantana maganar shigowa da ita,idan kaga Fatima ta shigo gidan Nan ta rayu saidai tazo a matsayin baiwa Mai bauta,Kuma idan ta kuskura kafarta ta shigo gidan Nan a matsayin baiwar ma saita da'n da'na kudart,saitayi data sanin zuwa duniya,Kuma maganar daukaka Kara idan har kaga ban daukaka karaba to mutuwa nayi mu zuba"....... Kuka yakeyi a fusace ya fice a cikin parlorn yayi hanyar waje..... Mamakine da al'ajabin hade da tsoron kalaman yarima,sanan ga babban tashin hankali Yana neman jafa kansa cikin masifa.....rigima da hajiya babba bakaramar masifa bace Dan macece Mara imani da tausayi......."innalillahi wa Inna ilaihi rajiun kawai mama karama ke furtawa a ranta"ga gumi da yake karyo Mata ta ko Ina...... *Dis is d beginning of d battle😂... Ya wasan Nan zai kasance a gaba?muje zuwa.....yanzun labari ya fara* 🏃🏻‍♀ *SLIMZY🥰✍🏼*🌩 *ANYI WALK'IYA.....* 🌩 *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 *NA:SLIMZY✍🏼* _wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* 14 Kan yarima yayi zafi da kyar yakejan mota tunanin inda zai nufa kawai yakeyi ya samu sanyi,haryayi kwanar da zata sadashi da unguwarsu barrister abdul,wani tunani ya fado kasa take yaja burki kuuuuuuu,hade da tada kura ya Sha kwana a guje mutanen dake zagaye a unguwar sukabi motar da kallo bayan motar kadai ya nunawa jamaa cewa Dan sarkine.....tambarin gidan sarkine manne a bayan motar da alamar Doki a jiki..... Wani gida Naga yarima ya Isa Mai zubin ginin gargajiya irin na da shima zubinsa tamkar gidan sarauta ga dogarawa ko Ina a harabar kofar gidan suna Kai komo.... Horn yayi aka bude Masa gate ya shiga a guje tamkar zai tashi sama yaja burki ya fito ko karasa rufe motar beyiba ya nufi hanyar da zata sadashi da ainihin hanyar shiga gidan,dik kofar daya gifta masu tsarone da jajayen Kaya suna zubewa kasa Dan girmamawa,saidai kawai ya daga musu hannu, Wani babban parlor ya shiga a fusace da wata irin murya yayi sallama "Assalamu alaikum"fuskarsa a daure tamkar be taba dariya ba, Da sauri dukkansu suka bishi da kallon yanayin nasa dake Nuna yana Cikin tsantsar tashin hankali, Wata dattijuwar macece gefenta zagaye da kuyangi da Yan Mata wadanda ko baa fada ba yaranta ne,durkusawa kowa yakeyi Yana Mika gaisuwa Amma ko kallo Basu ishesa ba, Dattijuwar dake kwance a kishingide jikin kalisa Tana Kare Masa kallo tsaf ta fahimci Yana yin NASA sanan tace cike da kasaita"Kai Kuma lafiya ka shigo haka kamar korarre" "Inafa lafiya goggo rahi,akwai babbar matsala" Dan yatsuna fuska tayi sanan tace"ban fahimceka ba khabir karamun haske" Cikin wata iriyar murya ya fara yi Mata bayani daga farkon abinda ya faru a masarauta har karshe da abinda ya hadasa da hajiya babba ya baro gida,.... Kallonsa goggo rahi takeyi shekeke har ya Gama bayani sanan ta Mike daga kishingidar da tayi ta zauna"meye matsalarka Kai?ko kanada dangantaka da ita tsintacciyar magen ce?" Da sauri ya juyo ya kalleta da tsananin mamakin kalmar data fada bai taba tunanin zaiji wannan furucin a bakin goggo rahi ba wadda ta kasance kanwar babansa Kuma Mata a wajen galadiman barayar Zaki....Nan da Nan zuciyarsa ta cigaba da tafarfasa,shiru yayi Yana kallonta ta cigaba da magana cike da Isa da kasaita Wanda dabiartace hakan dik abinda zatayi cikin izza da Isa takeyi "kabir yanzun kazone kafadamun cewa saboda an gano gaskiya ka koma bayan tsintacciyar mage ko me kake Shirin yi" Cikin tsananin bacin Rai yace "haba goggo banyi tunanin zanzo wajenki da wanan matsalar ki watsamun kasa a ido ba,kada ki manta cewa fa wanan yarinyar da ake Shirin tozartawa batada hakki akan wanan kisan illa tayisa ne Akan Kare kanta,sanan Kuma bayan gaskiya tayi halinta ace wai an daukaka Kara Kuma zuwa kotun gaba?sanan hajiya na fadamun cewa nine zan Kara tsayawa a wanan shariar?gaskiya bazai yuwuba Dan wallahi bazan tsayaba a wulakanta marainiyar Allah ba,inhar hajiya ta daukaka Kara to tabbas ni zan bugi kirji in karbi shariar in tsayawa yarinyar sanan Kuma in dawo da rikonta masarauta" Cikin kakkausar murya gwaggo rahi tace"wanan ne baka isaba wallahi kayi kadan ka dauko najasa ka dawo da rikonta cikin zuri'ar tsarkakakku Kai harka Isa me akayi akayika ballantana uwarka?ai dik naji abinda ke faruwa a masarautar Kuma Ina Nan tafe Dan dole ma inzo Akan maganar auren Dan uwanka marigayi Wanda da zaayi da deejamah tunda ya rasu zaka maye gurbinsa" Wani irin faduwar gaba ne ya ziyarcesa Wanda be taba Jin irinsa ba ya juyo ya kalleta sanan ya Kara maida dubansa ga deejamah dake gefe Tana ya mutsa fuska tamkar taga kashin....zuciyarsa ce ta Kara bugawa a karo na biyu sanan yayi karfin Hali cikin sassanyar murya yace"ai bani na nemi deejamah ba saboda haka Koda habib ya rasu bani zan maye gurbinsaba akwai sauran yara a masarautar ai ni yanzun ba wanan bane a gabana" Murmushi gwaggo rahi tayi sanan tace"maganar tsintacciyar magece a gabanka koh?to wanan maganar ruwan kwando ce kadauketa a matsayin mafarki,Dan baka Isa ka dauko Yar kwararo ka kawota cikinmu ba wai Nan ita marainiya,ka maidata can cikin kazantarta tajecan ta cigaba wadanda iyayensu sukai cikinsu a hanyar banza Sukai masu mazauni a titi aka tsinta aka rufawa asiri gwamnati ke rikonsu batare da sanin tsatsansuba ita zaka dauko kabiru?to kayi kadan kadaukota watarana a wayi gari ta kashemu" Girgiza Kai yakeyi Yana Jin zafin munanan kalaman da ake jifar marayun Allah dashi bayan Suma ba su sukai kansuba Allah ne ya haliccesu Kuma babu Wanda keda tabbacin cewa a hanyar banza dukansu aka samesu shine zaa dauki tsanar duniya a Dora musu.....runtse idanuwansa yayi sanan ya budesu,takawa yayi a hankali ya nemi kujera ya zauna saboda yadda dakin ke juya Masa jiri na neman kadashi.....wanan wani irin balai ne ke neman fada Masa lokaci daya?bai Gama kashe wata wutar ba wata ta kunno Masa.....tagumi ya rafka idanuwansa jajir ya kurawa side daya na falon ido Yana kallo,ya fada duniyar tunanin yadda zai bullowa wanan lamarin ga sarki zaiyi Yar tafiya zuwa ran gadi....ga balai na Shirin barkewa.... Mikewa deejamah tayi daga zaunen da take Tana daddana waya tun shigowarsa,taku tayi kadan a yangace ta juyo ta jefa Masa wani kallo Wanda ita kadai tasan na menene sanan tace cikin siririyar murya cike da yanga "Bari insa lantana ta kawo maka alkubus your favorite" Ko kallon inda take beyiba yace"bana bukata".....Dan Jim tayi sanan ta juya ta fice a parlorn.....wata matashiyar budurwa dake zaune a gefe itama ta Mike tabi bayanta, Shiru ne ya biyo baya sanan gwaggo rahi tace"ni zan shiga daga ciki tunda bakada wata magana Mai muhimmanci".....itama ta Mike Tana takama tabar parlorn.... Ya Dade zaune sanan ya Mike jiki babu kwari ya fice ya nufi motarsa ya tada a guje ya figi motarsa yabar gidan..... ******** Zagaye dakin kawai gwaggo rahi takeyi Tana huci deejah ma ta kalli mahaifiyar Tata tace"ni wallahi mama dama hankalina yafi daukuwa Akan Yaya Kabir dama na aminta da zancen auren Yaya habib ne saboda kince shine zai hau karagar mulki Kuma bukatarki na auri Wanda shine zai hau gadon mulki Amma zuciyata tafi kaunar Yaya Kabir Domin yafi Yaya habib haduwa" "Ke dalla tafican maganar haduwa ake ko maganar Wanda zai hau gadon mulki?waya fada miki cewa sarautar barayar Zaki karamar sarauta ce?dik fadin kasar Nan babu masarautar da takai masarautar barayar Zaki mulki cikar mulki da sarauta dik wata mace zataso hada zuria da wanan sarautar,shiyasa banaso wani a cikinsu ya fita waje ya samo Mata nafiso ya samu a cikin gida tunda gaku,a cikin gidanma nafison yasamu a cikin yayan cikina kuda kuke jini daya" Jinjina Kai deejamah tayi hade da sauke lallausan murmushi sanan tace"mama ni dama zai aureni ya dauko tsintacciyar magen ya kawota in maidata baiwa kaskantacciya" "Ya aureki?ya kawo tsintacciyar mage?tabiyo dare ta kasheki?aikoda kikaji Ina wanan banm bamin inayi ne donke bawai don wani abuba Dan nasan babu makawa shine zai maye gurbin habibu a wajenki Dan nasan Shirin da nakeyi saboda haka kidaina mafarkin ya dauko wata kazanta ya kawota gidan sarauta" Murmushi deejamah tayi sanan tace"nayi mamaki yadda kika fututtuke da Yaya yazo da bukatarsa saboda nasan dik masarautar Nan kece mutuniyarsa kece dik abinda yakeso kike Mara Masa baya Amma wanan karon Naga Nan da Nan kin rufesa da fada" Murmushi kawai gwaggo rahi tayi batare da tace uffan ba..... ********* Koda yarima yabar gidan gwaggo rahi bai zarce ko inaba sai gidan barrister Abdul inda ya tarada Fatima ta shirya tsaf tayi kyau abinta kamar ba itaba tanata kallon tv kallonta yayi tausayinta na ratsa sassan jikinsa, Dik Wanda ya kallesa yasan Yana cikin damuwa Nan barrister Abdul ke tambayarsa abinda ke faruwa be boye musu komiba ya Basu labarin rikicin da akeyi Akan daukaka Kara..... Kuka sosai Fatima takeyi harda shassheka cikin kukan take fadin "Kai cona ni Fatima,meke Shirin faruwa Dani?inama baayiniba a cikin wanna duniyar Mai cike da darrusa marasa Dadi babbar kaddara ta fadomin wadda a sanadin maraici hakan ya sameni inda inada iyayena bazasu wofintar Dani haka,bazasu barni infada cikin mummunan Hali hakaba har in aikata abinda zaisa farin ciki yayi kaura a zuciyata,na shiga ukuna.....Yaya yarima kabari kawai akaini a kasheni ka huta Nima in huta da wanan masifar" Tunda tafara magana ya kafeta da idanuwa zuciyarsa na harbawa sauri da sauri ji yakeyi tamkar ya rungumeta a jikinsa ko zaiji sanyi..... Saukowa yayi daga saman kujera ya matso inda take a durkushe Tana faman rizgat kuka,Dan towel ya Ciro a aljihunsa fari Kal yasa Yana share Mata hawaye Yana fadin "ki kwantar da hankalinki ko duniya zata juya Miki baya ni kabiru bazan juyawa Fatima bayaba,sanan wanan shariar da zaayi Dani zaayita nine zan tsaya Miki babu gudu babu ja da baya" Zumbur ta Mike Tana girgiza Kai tanaja da baya Tana fadin"banaso ka jefa kanka cikin matsala Yaya yarima ,akaina bazan Zama sanadiyyar wargaza zamantakewar rayuwarka da iyayenka ba ka kyaleni kawai akaini a yankemun hukuncin daya Dace dani a matsayina na wadda tayi kisan Kai"Tana Gama fadin haka ta shige daki da gudu Tana kuka Mai tsuma zuciya...... Shi kansa baisan lokacinda hawaye suka fara zuba a idanuwansa ba yayinda yabi bayanta da kallo harta shige..... Girgiza Kai kawai barrister hauwa keyi cikin al'ajabi da tausayi tace"ranka ya dade ka kwantar da hankalinka,kuka ba naka bane jajircewa zakayi ka kwatarwa marainiya yancinta tunda ka yarda ka amince Kaine gatanta to Allah ya Zama gatanta kaima ka Zama gatan nata Amma ba kuka zakayiba" Dafa kafadarsa barridter Abdul yayi Yana bubbugawa yace"be A man Mana prince wanan ba abin tada hankali bane I am sure zakayi winning saboda haka ka kwantar da hankalinka yaki ne a gabanka ba kuka ba" Hannu yasa ya goge hawayensa sanan yace"nagode sosai da karamcinku a gareni Dan Allah ku cigaba da ajiyemun Fatima a wajenku zuwa mu Gama wannan shariar da zamu fara" Jinjina Kai barrister hauwa tayi tace"kafi karfin komi ranka ya dade" "Nagode".... ******* "Barrister ninasa a kiraka saboda na daukaka Kara inaso abiwa Dana hakkinsa zan biyaka ko nawane ka bajemun basirarka a kotu ka tabbatar da an yankewa wanan shedaniyar yarinyar kisan gilla kamar yadda tayiwa Dana kisan gilla" Jinjina Kai Wanda aka Kira da barrister yayi yace"insha Allahu ranki ya dade zaayi yadda kikeso" "Ko nawane zan biya Domin Inga bayan wanan shariar barrister ,ko dukiyata zata Kare wallahi sainaga bayan shariar Nan" Dan rankwafawa barrister yayi yace"angama ranki ya dade dik wani abinda ya Dace ayi anyi ranki ya dade takaddar sammacin ma yanzun haka an rubutata ranki ya dade jibi zaa fara shiga kotun" Jinjina Kai mama babba tayi cike da gamsuwa tace"nagode barrister " "Nagode Allah ya baki yawan Rai" ******** Afnan ce fuskarta babu walwala tace"mama ya kamata ki Kira yaayah kiji inda yaje" "Nakira wayarsa a kashe Amma dik inda yake dole ya kwana a gida sanan dole in sanar Masa da inhar ya kuskura ya shiga shariar Nan to ban yafe Masa ba....... *Muje zuwa*🏃🏻‍♀ *SLIMZY🥰✍🏼*🌩 *ANYI WALK'IYA.....* 🌩 *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 *NA:SLIMZY✍🏼* _wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* 15 Yana shigowa gidan direct dakin hajiya babba ya shiga da jiki a sanyaye ya yi sallama,ciki ciki ta amsa Masa Tana zaune Tana kada kafafuwa fuskarta babu annuri tamkar Bata taba dariya ba, Gefen makekiyar daddumar dake dakin ya nemi waje ya zauna ya tankwashe kafafuwansa hade da sunkuyar da kansa.... Kallon gefen da yake zaune tayi a fakaice sanan ta tabe baki tace"kazo ne yau ma ka zazzagamun masifar da kayimun saboda marainiyar Allah kamar yadda kake fada?.....Kabir kenan ka bani mamaki ka nunamin iyawata dik tunkaho da nakeyi da Kai ka dibi kasa ka watsamun ka kasa bani goyon baya Akan kudirina" Dago fuskarsa yayi wanan karon idanuwansa sun kada sunyi jajir cikin sassanyar murya yace"ki gafarceni mama wallahi tallahi ba goyon bayan Fatima nakeyiba don Tana marainiyar Allah,ba ita kadai nakewa wanan yakin ba harda Dan uwana,ki duba kiga ta hanyar ya mutu,sanan ki tunada cewa shariar Nan da akayita tunda aka farata babu wata maaikata ta tv kota gidan radio da aka Bari ta dauki wannan shariar tasa a kafafen yada labarai saboda gudun tozarci da bacin suna,na tabbatar da cewa ranan da aka kammala shariar Nan da mun kuskura wata maaikata ta yada labarai ta dauka da mune zamuji kunya,sanan mune sunan mu zai lalace a idon duniya,aga cewa babban Dan siyasa kamar Yaya habib Kuma babban Dan sarki Mai jiran gado shine yake neman aikata mummunan aiki ba karamin surutu zamuji ba a cikin gari.....ko a cikin masarautar Nan ba kowa yasan abinda ya faruba saboda gudun tsegumi da Cece kuce irin na mutane Dan Allah mama na rokeki ki janye Akan daukaka karar Nan".... Shiru tayi Tana sauraronsa har ya Gama magana tamkar wadda ruwa ya cinye,tafi minti goma a haka har ya fidda ran zatace wani Abu sanan tace"dik wadanan maganganun da kakeyi kake rara gefe basu ne zasusa in janye kudirina Akan abinda nayi niyya ba wani surutun mutane da bacin suna baya gabana babban burina shine dik wani Mai ruwa da tsaki da yayi amfani da wanan yarinyar taje har aka kasheshi to idan taji wuya zata fito dashi Dan ni ban yarda da wadanan maganganun ba na yazo lalatatane ta kasheshi kawaidai abinda nasani abiwa Dana hakkin jininsa" Gauron numfashi ya sauke yace"to shikenan ni Kuma insha Allahu zanyi iya bakin kokarina wajen marawa yarinyar baya a shariar zanyi amfani da basirata da kwarewata a wanan shariar wajen kwatarwa Mai gaskiya hakkinsa" Murmushi hajiya babba tayi tace"kamar yadda kake takama da gwamnati tasan da zamanka da kwarewarka da basirarka haka akwai wadanda suna zaunene zaman kansu sunayi don kudi da dukiya,zanyi hayar lawyoyi wadanda zasu fafata dakai,sanan dik wanan takamar da kakeyi zasu baka Kashi a wanan shariar sanan duniya datasan da zamanka tasan da kwarewarka a shariah wanan karon zaaga kasawarka ai Mai laya kiyayi Mai zamani" Dariya maganarta ta bashi don Harga Allah bezo akan suyi sainsa ba yazone ya fada Mata ainihin manufarsa Akan na rashinso a daukaka Kara Amma ta bullo Masa da haka dariya kadan yayi yace "hajiya dik wani lauya da ya kwana ya tashi a fadin Nigeria yasan da zamana,Kuma babu Wanda yake fatan shariah ta hadani dashi Dan babu Wanda baisan kwarewar da Allah ya baniba alhamdulillah Koda wannan nasan nayi zarra Allah ubangiji yaga zuciyata Akan wanan Abu da ke Shirin tunkarowa insha Allahu bazanji kunyaba idan an rubuta takaddar daukaka karar da sammaci akawomin Domin nine gatan Fatima a yanzu"...... Jinjina Kai tayi batare da tace komiba zuciyarta tafarfasa takeyi tamkar zata Huda kirjinta ta fito ji takeyi inama ace Kabir shine zai bugi kirji ya tsaya a supreme Court da tasan tabbas babu makawa sukeda nasara Dan ita kanta tasan yaron mayene be taba tsayawa a shariah an kadashiba har hayarsa akeyi daga wurare da dama tasan da wuya tasamu Wanda yakai Kabir basira da kwarewa wajen shariah Amma zatayi amfani da kudi tasan babu abinda kudi basayi..... Tayi Nisa cikin tunani dik ta dauka ya fuce saida ta bude idanuwanta daga kishigiden da take ta gansa a zaune ta ce cikin sarkakkiyar murya "ka tashi ka ficemun"...... Mikewa yayi ya fice a dakin ya nufi dakin mahaifiyarsa...... ******** Zubewa yayi a gabanta a durkushe Yana fuskantarta,ganin yadda ta daura fuska yasan tabbas akwai matsala fuskarta babu walwala Rabon da ya ga hakan a tattare da ita ya manta,shiru tayi sai Jan carbi takeyi batare da tace Masa komi ba,sanin sarauta da miskilanci irin na mahaifiyarsa yasan inhar bashi ne yayi Mata magana bazatayiba sanan yasan Harga Allah cewa yayi laifi yadda ya tada muryarsa bisa ta iyayen nasa,sassanyar ajiyar zuciya yayi sanan ya Nisa yace"naso ace Kun fahimci abinda nake nufi game da wanan daukaka karar naso ace kunsan cewa yin hakan tamkar tozarcine ga wanan masarautar da bacin suna ga Dan uwana dik wanan abun da nakeyi inayinsane don inkare mutuncin kanmu Dana gawar Dan uwana banaso ace sunan masarautarmu ya baci a idon duniya,dalilin hakan yasa nake boye wanna shariar data gabata na Hana dik wata maaikata da zata yada abinda ya faru a gidan radiyo da talabijin halartar wanan shariah Amma saidai Kash bakuso hakanba sanan ga babban abin dubawa shine yin abinda zaaci mutuncin maraya dik Wanda ya wulakanta maraya yaci zarafinsa Allah baya barinsa mama ki duba wannan lamarin ki sassauta wanan fushin da kika dauka akaina ki fahimceni" Tunda ya fara magana ta kafesa da ido Tana kallonsa cike da gamsuwa da maganarsa Amma tasan nuna Masa goyon baya bazai yuwuba..... "Dik naji maganarka na fahimceka sanan Nima ba goyon baya nakeyi Akan daukaka kararba Domin shi kansa Mai martaba babu hannunsa a ciki abinda nakeso dakai shine ka janye hannunka a cikin shariar Nan banaso kace zaka tsaya akai ma wanan yarinyar Domin zaka daukarmun magana" "Mama naso ace kin bani goyon baya wajen yin aikin lada Domin Allah kadai yasan dumbin ladan da zansamu wajen Kare hakkin marainiya a matsayinta na wadda aka cuta Dan girman Allah ki yi hakuri kiyimun addua kada ki hanani aikin lada" Ajiyar zuciya tayi ta Nisa tace"babu hannuna a ciki dik abinda ya biyo baya ka kuka da kanka sanan kasani harabada bazan kaunaci wanan yarinyar ba kaidai da kaji ka gani kaje gatanan Amma bana kaunarta saboda ta sanadiyyarta na rasa habibu Dan uwanka Wanda Kai kanka yadda na shaku dashi ban shaku dakai haka ba tashi ka fita" Yaji zafin maganar mahaifiyarsa Amma yasani tsakaninta da habib akwai kauna Mai karfi a tsakaninsu Domin Dan dakinta ne,babu yadda ya iya haka ya Mike jiki babu kwari ya fice sanan beji dadin kalaman ummansa ba na rashin kaunar Fatima...... ********* Washe gari da sassafe ya shirya can Court din da aka gabatar da shariah yaje don yayi bincike Akan abubuwan da ke gudana yanaso ya tabbatar da hajiya tasa a daukaka Kara ko Yaya, Wani office ya shiga ya tarar da wani lawyer zaune da takadda a hannunsa,gaisawa sukayi sanan yake tambayarsa Akan maganar, Da sauri ya dauko wata takadda yace"ranka ya dade maganar daukaka Kara tun shekaran jiya akayita Domin hajiya ta dauki lawyoyo guda uku ta biyasu Akan tsaya Mata Akan shariar yanzun haka ma takadda ta Isa supreme Court jibi zaafara sauraron karar" Saida gabansa ya fadi Amma ya dake ya Mika hannunsa ya karbi takaddar ya gyara Zama ya fara dubawa,can kasan takaddar ya duba ya kalli sunayen wadanda zasu tsaya Mata a kotu akwai Barrister Nasir da Barrister Muhammad da barrister Ibrahim dukkansu lauyoyine masu zaman kansu Wanda ake daukarsu a biyasu Akan shariah su tsayawa mutane kwararrune Wanda Suma ansan da zamansu a wanan jihar,ko darrr yarima bejiba hasalima dukkansu yasansu don babu Wanda be taba shariah dashiba Kuma sun buga sunbarshi indai wadanan ne aikin banza ya daukesu dukkansu sunsan wayeshi saboda haka a shirye yake da ya Kara Dasu.... Jinjina Kai kawai yayi ya Ciro wayarsa ya dauki number wayar daya daga cikinsu yasa a wayarsa sanan ya gabatarwa Wanda yazo wajensa a matsayinsa na lawyer da zai tsayawa Fatima a kotu ta gaba......a rikice yake kallonsa cike da mamaki wanan ala'amari Amma sanin halin yarima yasa bece komiba sai takadda da ya bashi ya Sanya hannu ya fita..... ********* Tun kafin ya tada motarsa yayi dialing number barrister nassir bugu daya ya dauka daga can bangaren barrister Nasir yace"ranka ya dade barka da warhaka" Mirmushin kasaita yarima yayi yace"Ashe kanada number ta" "Ehh ranka ya dade" Jinjina Kai yarima yayi sanan yace"nakiraka ne in shaida maka nine barrister Wanda zai Kare wadda ake Kara wato Fatima Zahra inaso ka shirya da kyau" Saida gaban barrisiter Nasir ya yanke ya fadi Dan dik a tunaninsa yarima bashida lokacinda zai tsayawa shariar ne yasa hajiya babba tasa aka nemesu tabdijan shine abinda ya ambata a ransa sanan yace"to ranka ya dade Allah ya kaimu nagode sosai" Murmushi Mai sauti yarima yayi sanan ya kashe wayar Yana murmushi shi kansa yasan yanzun dik inda hankalin barrister Nasir yake ya tashi Domin sun taba gabatarda shariah beji da dadiba yayi hakan ne ya Dana musu tarko......yasan cewa kudin hajiya babba kawai zasuci Domin babu abinda zasu iya a wanan shariah da gaskiya take kuru kuru..... Motarsa yaja yayi gaba abinsa Yana tuki cike da kwanciyar hankali da karfin gwiwa..... ********* Tunda aka kawo takaddar daukaka karawa barrister Abdul hankalinsa ya tashi Dan tausayin yarinyar da yakeji ta wani fannin kuwa yanasamun kwarin gwiwa idan ya tunada cewa shariar a hannun yarima take yasan waye yarima..... Gidansu yazo a parlor dukkansu ya tarar Dasu sunyi jigum jigum Fatima na gefe Tana famar rizgar kuka kamar wadda akayiwa mutuwa yanayinta kadai ka kalla saita baka tausayi yadda ta rame tayi fari fat tamkar wadda batada jini.... Koda yayi sallama dukkansu kallo suka bisa dashi har ya karaso tsakiyar parlorn ya tsaya ya zura hannunsa a aljihunsa ya zurawa Fatima idanuwansa Yana kallon yadda hawaye ke ambaliya a idanuwanta tamkar an bude famfo,kallonta yakeyi cike da kunar Rai a duniya Babu abinda ya Tsana sama da ganin Fatima Tana kuka..... Idanuwanta ta daga a sanyaye ta saukesa akansa taga itace yake kallo ko kiftawa bayayi ta Sanya hannu ya goge hawayenta tana sauke ajiyar zuciya.... Barrister Abdul ne yace"ranka ya dade angama komi ko?" "Ehh angama yanzun abinda ya rage shine ka mikawa hukuma Fatima yau don dole sune zasu gabatar da ita a kotu tunda shariar a hannun gwamnati take Kuma baa gamaba" Nan da Nan taji jiri na dibarta numfashinta na fita sauri da sauri shikenan ta tabbata cewa tafaru takare Mata a rayuwa itadai Tana cikin balai da mummunar kaddara wani irin kuka Mai karfine ya taso Mata ta toshe bakinta tanayinsa,barrister hauwa ce take famar lallashinta itama idanuwanta sunkada sunyi jajir dauriyace tasa Bata iya zubar da nata hawayen....janyota jikinta tayi ta rungumeta Tana shafa bayanta..... Hawaye na gudu a idanuwanta ta dago Kai da sauri tace"Dan Allah kiyimun Abu guda daya kafin a kashe ni" Dukkansu ido suka zuba Mata tace"ku taimakeni ku kaini in ziyarci Yar uwata a gidan marayu inaso inganta inyi Mata ganin karshe Dan Allah" Saida yarima yayi Mata kallon minti biyu zuwa uku sanan yace"tashi muje" Da sauri ta Mike Tana share hawayenta,gaba yayi abinsa ta zari hijabinta dake kan kujera tabisa a baya,kallo barrister Abdul da madam dinsa Suka bisu dashi suna tsananin tausayinsu..... ****** Tunda suka shiga mota yafara driving bece Mata uffan ba har Suka iso kwanar da zata sadasu da gidan marayu Nan Fatima ta rushe da kuka tamkar wadda zaa cirewa Rai da sauri yaja burki ya tsaya ya daure fuskarsa a fusace yacee"meye haka?Zaki fada musu abinda ke faruwa ne?kokuwa satoki nayi kin tasani a gaba kinamun kuka?kissa hannu ki share hawayenki tun ban juya da motata ba" Da sauri ta sa bayan hannunta ta share hawayenta batare da tace Masa komiba sanan ya taka mota suka wuce,horn yayiwa me gadi ya bude Masa gate a guje ya shige da motarsa sai wawware idanuwa takeyi babu abinda ya canja a cikin gidan....sai yara datake gani suna wucewa da alamar islamiyya zasu shiga,wajen da ya Saba parking ya parker motarsa bece komiba itama batace masa ba can ta hango wata na tahowa a hankali tamkar Tana kirga tafiyarta Tana kallon kasa,kafeta tayi da ido hartazo gab da motar zata gifta da sauri Fatima ta bude mota ta fito ta kwala Mata Kira "bilkisu" Ko a mafarki bilkisu taji muryar Fatima bazata mantaba da sauri ta dago kanta zuwa inda tajiyo Amon sautin Kiran,aikuwamotar da bazata mantaba ta hanga da wata a tsaye da dogon hijabi,a guje ta runtumo da gudu ta karaso suka rungume juna hade da fashewa da matsanancin kuka, Saida sukayi Mai isarsu sanan suka saki juna ko wannensu kallon Dan uwansa yakeyi..... Bilkisu ce hawaye na gudu a idanuwanta ta kalli Fatima Tana murmushi tace"Fatima Ashe xan sake ganinki a rayuwata?Allah na gode maka da ka amshi adduata yar uwata ta kubuta" Hawaye na gudu a idanuwan Fatima ta taka kadan zuwa jikin bishiya ta hada kanta da bishiyar hade da fashewa da kuka karasawa bilkisu tayi wajen ta tsaya,dik abinda sukeyi yarima kallonsu yakeyi a cikin mota shima yanaji tamkar yayi musu kuka saboda tausayi..... Cikin kuka Fatima ta kwashe abinda ya faru da Wanda ke faruwa ta bawa bilkisu labari dukkansu kuka sukeyi, Tsagaitawa da kukan bilkisu tayi tace"labari ya iso mana Amma cikin mu bakowa yasa niba Nima a wajen uwaliya a kitchen nakeji, alhamdulillah Allah ya kwatar Miki hakkinki Domin har gidan Nan yan sanda sukazo suka tarka hajiya da haruna gashi lokacin sun tarar Ana rigimar zainab tayi ciki hajiya ta Bata magani jini ya balle tamkar zata mutu muna cikin tashin hankali lokacin kwatsam saiga Yan sanda saida sumayiwa haruna jina jina da duka don yayi yunkurin guduwa suka tunkuda keyarsa a mota itama hajiyar da suka cafketa saida suka bubbuga Mata kan bindiga Nan fa mukai cincirindo muna kallo Ashe abinda ya faru kenan" Girgiza Kai kawai Fatima keyi tanajin tausayin kansu da tausayin rayuwar da suka tsinci kansu labarin xainab da abinda yasameta ya matukar girgiza ta Allah sarki marainiyar Allah anyi Mata sanadiyyar lalacewa anjefa rayuwarta balai wayasan adadin wadanda sukayi ciki Ana zubarwa yanzun ne Allah ya tona asiri..... Hannu tasa ta share hawayenta sanan ta matsa ta rungume bilkisu Tana kuka take fadin "Yar uwata ko yanzun Allah ya dauki Raina naji dadi zan mutu da farin cikin nazo naganki Naga halin da kike ciki kisani a addua Domin Ina cikin mawuyacin Hali Allah ya fiddani idan Kuma ankasheni kiyimun addua Allah ya yafemun Kura kuraina" Sosai suke kuka Mai ban tausayi kusan minti goma suna rungume da juna sanan Fatima ta saketa tace"nagode bilkisu Allah ubangiji ya sadamu da alheri"Tana fadin haka ta juya da sauri ta nufi mota,Nan bilkisu ta durkushe Tana kuka harda shassheka haka ta dago Kai Tana gani yarima yaja mota suka fice Dan bazai iya hada ido da bilkisunba yadda zuciyarsa ta karaya mainakon ya lallashesu tayasu zaiyi..... Fatima tunda ta kifa kanta a tsakanin cinyoyinta take kuka jikinta har rawa takeyi haka yarima ke tukin mota minti minti ya dago kansa ya kalleta ya girgiza kansa idanuwansa sun canja kala zuwa launin ja.... ******* Dare ya tsala har misalin karfe daya Yana zaune Yana tunanin halin da Fatima ke ciki tabbas yarinyar abar tausayi ce ga mummunan kaddara data fada Mata Amma yasan cewa insha Allahu zata tsallaketa babban tashin hankalinsa be wuce yadda zaiyi da yakin da ke gabansaba gashi dik sacond da zuciyarsa ke bugawa da soyayyarta da kaunarta take bugawa......tun ranan da ya fara hada ido da yarinyar yakejin abubuwa da dama game da ita.....ga mummunar kaddara data fado akanta na kisan Dan uwansa,..ya zaayi ya inganta rayuwar wanan marainiyar Allah ?....runtse idanuwansa yayi take yaji bugun xuciyarsa ya tsananta idanuwansa sun kawo ruwa suna sauka a kumatunsa.....ga shiga kotu dake gabansa Wanda zai tsaya Akan Kare wadda itace ta kashe Dan uwanda da yafi so a rayuwarsa habib ....kuka sosai yakeyi Yana tunanin mafita a rayuwarsa..... *Muje zuwa🏃🏻‍♀.....kuyi hakuri da rashin jina akai akai insha Allahu zan rinka kokarin yin posting da interval na kwana daya idan nayi yau gobe bazanyiba sai jibi😍😍😍😍....mu hadu a next page Dan Jin ya zata kasance a kotu....* *SLIMZY🥰✍🏼*🌩 *ANYI WALK'IYA.....* 🌩 *HASKE WRITERS* *ASSOCIATION💡* *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* 16 Juyi kawai yakeyi Akan makeken gadonsa da tunani cunkushe a cikin ransa babban farin cikinsa shine wanan shiga kotun da zaayi zaayine iya judges da lawyers abinda hajiya babba ke tunani ba hakan bane,Kuma Yana da tabbacin insha Allahu sukeda nasara Dan dik wata hujja da zai gabatar ya Gama tattarata sanan shi kansa yasan tarko ya Dana Mata ta manta da cewa Yana daya daga cikin judges na supreme Court,kwakwakwarta ta toshe Akan manta cewa supreme Court ita ce kotun karshe dik fadin kasarnan matukar aka daukaka dik hukuncin da suka yanke shine dai dai....wani malalacin murmushi ya saki a cikin duhu Wanda shi kansa besan yayisa ba.....haka yayita tunani kala kala game da rayuwa gabaki daya har bacci barawo ya sacesa..... ******** Tunda garin Allah ya waye Fatima ke faman kuka a daki dik ta Gama tadawa barrister hauwa hankali,gefenta take zaune ta zuba Mata ido tana kallon yadda take kuka idanuwanta sun kumbura fuskarta ta kode saboda kuka, Cike da damuwa barrister hauwa ta dafa kafadar Fatima tace"wai Fatima kukan me kikeyi haka?so kikeyi ki janyowa kanki rashin lafiya ko?jiya Aysha tacemun haka kika kwana kina Kuka inaso insan kukan na meye ne" Cikin kuka Fatima ce "Abla(yadda taji Aysha na Kiran barrister hauwa) hankalina a tashe yake idan na tunada abinda Yaya yarima yace wai yau zaa mikani hannun hukuma gobe zaa Kara mikani kotu sai inji tamkar in hadiyi zuciya in mutu" Murmushi wanan karon barrister hauwa tayi sanan tace"to maida wukar ki kwantar da hankalinki babu me mikaki hannun hukuma shima kansa ne yayi zafi ya fada Miki hakan,wanan kotun ba irin wadda akaje bace wanan kotun badake zaa shiga shariah ba kina zaune a wani waje zai shiga su gabatar da komi ya fito saidai idan an nemi a gankine Amma babu inda zakije kinji kanwar ablah" Kuri da ido Fatima tayi Tana kallon barrister hauwa batare da ta gasgata maganarta ba gani takeyi kamar ta Fadi hakan ne Dan ta kwantar Mata da hankali,.. Murmushi barrister hauwa tayi sanan tace"baki yarda da maganata ba ko?kin manta Nima barrister ce Kuma nasan komi Akan shariah ki yarda da maganata babu inda zakije yau kina cikin gidan Nan kinji" Gyada Kai tayi tasa bayan hannunta ta share hawayenta ta durkusar da kanta kasa.... "Fatima ki dau breakfast dinki kici kafin ya huce Kinga babu kyau Zama da yunwa" Juyowa Fatima tayi ta dauki kofin da aka hado Mata tea Mai kaurin gaske ta janyo plate din soyayyen dankali da kwai tafaraci.... ********* Koda yarima ya shigo gida a shirye cikin manyan Kaya ya Sanya shadda Mai ruwan toka kansa babu hula ya nufi bangaren mahaifiyarsa a can ya tarada khausar zaune Tana ganin ya shigo ta Mike ta fita,dukkansu sai suka bita da kallon mamaki don Basu taba ganin hakan ba.... Gefen mama ya zauna ya kawo gaisuwa ta karba masa babu yabo babu fallasa sanan shiru ya biyo baya.... Mama ce ta katse shirun da cewa "sai Ina Kuma ranka ya dade"fuskarta a daure tayi maganar Murmushi yayi Jin abinda tace don yasan haushinsa takeji gyara Zama yayi sanan yace"zan fita zanje can Court of appeal ne inji yadda abun yake" Ajiyar zuciya mama tayi tace"kadaibi a hankali sanan Ina maka fatan alheri bazan taba hanaka abinda zakayi ya amfanar da Kai duniya da lahira ba Domin a hakikanin gaskiya nasan cewa abinda zakayin abune Mai kyau Amma hatsarinsa nake hango Masa dikda dai inayi maka adduar fatan alheri da nasarori a rayuwa" Wata irin sassanyar ajiyar zuciya yarima ya sauke a Fili yaji dadin kalaman mahaifiyarsa ba kadanba don yasan mahaifiyarsa macece Mai kawaici da rashin son fitina shiyasa take kakkaucewa badan wani abuba.... "Insha Allah mama akwai nasara sanan Allah Yana tare da Mai gaskiya naji dadin kalamanki a matsayinki na mahaifiya a gareni,sanan adduarki itace kariyata hade da kariyar Allah nagode sosai Allah ya Kara Miki lafiya da Nisan kwana" Murmushi kawai tayi sanan tace"Allah ya kiyaye" "Ameeen"kawai yace ya Mike ya fita... Koda ya fito har yayi bangaren hajiya babba don ya gaisheta sai Kuma ya fasa ya kalli agogo ya juya da sauri Ashe dik akan idanunsu..... Khausar ce ta yatsina fuska tace"mama wai kinsan yaya Kabir yanzun saboda maganar Nan ya daina zuwa bangarenki gaisheki sai bangaren mama karama?hmmm abin ya bani mamaki sai kace dama akwai wani Abu" Girgiza kafa hajiya babba keyi tace"khausar kenan ke yarinya ce ai ni tunda abun Nan ya faru nadade da fahimtar komi Kuma dagashi har uwar tasa Ina daidai dasu,anyimun sanadiyyar gudan jinina Aida Yana Nan bazai fitaba batare da yazo ya gaisheniba Kinga wanan ko da banina haifeshiba tun kafin aje ko Ina nafara ganin banbanci" "Ni mama rasa Mai suke cewa nakeyi Kuma da ya shiga sai bayin dake bangaren mama karama dik su watse su sukasan me suke cewa ni yaya yariman ma dik ya suremun a Rai" Kallon khausar hajiya babba tayi tace"ki kwantar da hankalinki lokaci na zuwa da zan Rama komi daya bayan daya....jiya rahina ta kirani Akan maganar deejamah ta fara cemin tunda habibu ya rasu Mai zai Hana khabir bazai nemi deejahmah ba ya maye gurbin Dan uwansa dikda deejahmah har yanzun Tana kukan rashin habibun sai nace Mata zanyi shawara,....to tunda ta haka suka bullo ni zanbada goyon baya Akan a aura Masa deejahmah ko yanaso ko bayaso sanan zanyi amfani da deejahmah wajen daukar fansa ta....yanzun babban burina shine a gabatar da shariar Nan a tozarta su a kotu" Murmushi khausar tayi tace"gaskiya mama idan deejahmah ta auri ya khabir akwai damuwa saboda tun farko kinsan ba shiri sukeba da wuya ya yarda da aurenta" "Dolensa ya yarda saboda ai rahina ba bare bace uwartata shima uwarsa ce baridai sarki ya dawo jibi" Jinjina Kai kawai khausar tayi ta janyo wayarta ta cigaba da dannawa.... ******* Yarima kuwa Yana fita babu inda ya zarce sai can Court of appeal, Yana zuwa aka gabatar Masa da takkadar da aka rubuta kamar haka: Kamar yadda hajiya babba wato mahaifiyar marigayi Kabir taso a yaune aka daukaka Kara Akan mutuwar yarima habib, lawyoyinda ta dauka sun daukaka Kara through d *Attorney general* Kuma zaa saurari karar gobe laraba 16 ga watan July ....Nan ya karasa karanta sauran bayanan da komi sanan ya maida takaddar aljihunsa saboda mallakinsa ne a matsayinsa na Wanda zai tsayawa wadda ake Kara, Mikawa masijan alkali hannu yayi suka gaisa yace"Masha Allahu,Allah ya kaimu goben lafiya....ya juya yayi ficewarsa.. ******* Bai zarce ko inaba sai gidan Barrister abdul lokacin karfe uku na Rana,direct ya shiga gidan yayi sallama Aysha ce da Fatima a parlor barrister hauwa Tana bedroom, Mikewa Aysha tayi tace"barka da zuwa Yaya " Murmushi yayi yace"sannunki aishatu uwar muminai",murmushi kawai tayi tace"Bari in Kira maka Ablah Tana ciki" "Ok"kawai yace ya karasa shigowa parlorn,inda Fatima ke zaune ya zauna a gefenta ta matsa lungun kujerar ya Kara matsawa Yana murmushi can kasa yayi da muryarsa yace"yadai cry cry yauma anyi kukan ne?" Dan turo baki tayi ta hararesa ta kasa batare da tace komiba, Barrister ce ta shigo parlorn Tana sanye da doguwar rigar jallabiya marroon colour ta yane kanta da gyale fuskarta dauke da faraa tace"yauwa ranka ya dade naji dadin zuwanka gidan Nan Dan tun dazun nake fama da Fatima Akan taci abinci taki,da safema dakyar nasamu ta karya dik ta tashi hankalinta Akan komawa kotu sai koke koke takeyi Kila Kai idan kace taci zataci" Dago Kai yayi Yana kallon Fatima Jin shiru yasa ta dago kanta daga dukar da kan datayi Aiko karaf suka hada ido ya zuba Mata shanyayyun idanuwan Nan Nasa wadanda Sam basa Kama Dana Mata,take taji wani Abu ya tsarga Mata cikin jikinta ta mayar da kanta ta sunkuyar, Murmushi barrister hauwa takeyi Tana kallonsu Dan ta Dade da fahimtar alakar dake tsakanin zuciyoyinsu dikda yarima na nunar musu da tausayin Fatima yakeji...."ranka ya dade Bari inkawo muku abincin tare kaci itama kasata taci Dole" Kallo Fatima tabi barrister hauwa dashi Tana murmushi ta maida kanta kasa,shiko yarima Yana gefe Yana aikin kallon Fatima wadda ta canja tayi kyau abinta dikda ramar data bayyana da damuwar dake tare da ita be hanasa ganin tsantsar kyau da Allah yayiwa yarinyar ba..... Kula da plates guda biyu Ablah ta gabatar musu sanan tasa Aysha ta kawo juice da ruwa Mai sanyi dukkansu suka bar musu parlorn.... Da kansa ya zuba abincin sosai fried rice ce taji kayan lambu da hanta da aka yanka kanana sai kamshi takeyi....cokali biyu yasa a plate din sanan ya kalleta fuska a daure yace"Bismillah" Rau Rau idanuwanta sukayi tamkar zatayi kuka tace" nifa na koshi"...ta turo baki gaba... Tsare gida yayi yace"Allah xan mareki idan baki matso munci abincin Nan ba to zanyi Miki dura" Da sauri ta dago Kai ta kallesa,Aiko ya kashe Mata ido daya ta dukar dakai kasa tace"Toni kadai nakeso inci" "Malama practice nakeso ki fara" "Na me?"tace da sauri... Sai ya basar yace"idan na kaiki gidan Miji Mana"....tura baki kawai tayi babu yadda ta iya haka ta matso sukaci abincin tare suka Gama.... Ablah ce ta fito daga daki tace cikin tsokana"iyyee Fatima dik kece kika cinye wanan abincin?Koda yake ai ranka ya dade ya iya lallashi" Dariya sukasa dukkansu Banda Fatima da murmushi kawai takeyi kanta a kasa,can cikin zuciyarta tunani kawai takeyi Akan makomarta.... Nan yarima ya zauna sunata Hira da barrister hauwa har yamma sanan yayi haramar tafiya ya kalli Fatima yace "bintu"gabantane ya yanke ya fadi ta dago Kai da sauri Tana jiran yace ta zo ya mikata gurin hukuma sai taji yace "kishirya da wuri zanzo gobe mutafi wajen daukaka karar Nan a wankemun ke dakyau a tabbatarwa da duniya kedin baiwar Allah ce.... Wata sassanyar ajiyar zuciya ta sauke Nan da Nan idanuwanta Suka kawo ruwa tace"toh" kanta a kasa.... Sallama yayi musu Ana Kiran magriba ya fita badan yaso ba don yau jinsa yake tamkar sabon ango haka kawai yake tsuntar kansa cikin farin ciki Yana driving Yana murmushi shikadai.....har ya iso gida,Yana ajiye motarsa ya wuce masallaci don yin sallah... ********* Bayan ishai can gidan galadima gwaggo rahi ce zaune cikin yaranta suna Hira sama sama, Deejahma ce tace"wai mama naji kinyi shiru da maganar da mukayi ranan nifa na kagara a fara kirana da matar Dan sarki Kuma sarki Mai jiran gado" Murmushi mahaifiyarta tayi tace"to rasa kunya beran tanka,wato kin kosa kitafi kibarni ko?har kike iya fadamun?to ai nakira hajiya babba na fada Mata shawarata Akan hadaki da khabir tace zatayi tunani gobe nakeso inje gidan da yamma in Kara tattaunawa da ita kafin sarki ya dawo,sanan inaso in jiyo ya takasance Akan maganar daukaka Kara inji yadda sukayi,inaso inji Mara kunyan ya tsayawa shegiyar ne Koko Dan uwansa Dan bansan me Kabir ke nufiba" "Mama dik duniya Babu Wanda nakejin haushinsa kamar shegiyar yarinyar Nan da tayi sanadiyyar rabani da habib dina,waini ya Kabir ma mamaki yabani har wani tausayinta yake mtsewwe" "Kyale banza shiyasa ai da yazomin da maganar na gwasaleshi zanyi maganinsa" Deejahma ta tabe baki tace"can ta matse Mai" ******** Washegari da sassafe ya shirya ya fita babu Wanda yasan fitarsa a gidan direct gidan barrister Abdul yaje Yana zuwa Fatima ta fito already a shirye take dama shi take jira,Tana ganinsa cikin bakaken Kaya saida gabanta ya fadi haka ta daure ta gaisheshi ta shiga gaban mota ta zauna,sama sama suka gaisa dasu barrister sukai mishi fatan alheri da nasara sanan sumabar gidan. karfe 10 na safe Kabir ya isa supreme Court a mota yabar Fatima a parking space ya fice ya tafi ciki, Yana cikin manya manyan judges da zasu tsaya game da karar Fatima Zahra,sanan shi kansa Yana matsayin Wanda zai kareta a wajen lawyoyin da haj babba ta dauka basuyi mamakiba ganin yarima Kabir cikin manya manya judges waanda zasu duba previous case da akayi a court of appeal ba...maana hukuncin da aka yanke a court of apeal..... Bayan duk sun zazzauna a cikin court din , (bcoz a kaida na supreme Court mutane basa zuwa kuma baa kawo Mai laifi).... Cikin kwarewa ta aiki yarima Kabir yagabatar da hukuncin da aka yanke a court of appeal da shedun da aka gabatar a can da komi,ya gabatarwa sauran judges, Tun daga Nan lawulyoyin Haj babba sukasan bazaasuyi succeeding ba,ko wannensu zare ido kawai yakeyi Yana kallon sauran judges dinn, Bayan dogon nazari da babban alkali yayi sanan yayi gyaran murya yace "yace abisa laakari da akayi da manya manyan shedu da aka gabatar, Kuma sannan a criminal case na kisa inde kan self defense ne accused person will be on d basis of liability,"saida gabansu duka ya fadi dikda dunsan dama hakan zata kasance,...alkali ya cigaba da cewa "abisa haka wannan decision na court of appeal yayi Kuma is valid, ......Kuma an wanke Fatima Zahra on d basis of self defense".... Abinda alkali yace kenan ya dauko file din takaddun da aka gabatar yasa hannu sanan ya mikawa kowa ciki yasa hannu na angama shariah ya Mike ya fice ya barsu zaune, Bakajin karar komi sai fanka,yarima ya mikawa sauran Barristers din hannu suka gaisa sanan ya fice Yana murmushin nasara, Ko cikakken minti arbain beyiba ta hangosa ya fito hannunsa dauke da takaddu Yana tafiyar Nan tasa ta takama da sarauta,bugun zuciyarta ne ya tsananta tunda ta hangosa tashin hankali ya bayyana karara a fuskarsa har ya bude motar ya shigo.... Idanu ya kafa Mata ganin yadda ta furgice sanan ya saki kayataccen murmushi yace "you are free".....ajiyar zuciya takeyi akai akai take hawayen farin ciki ya fara zarya a idanuwanta,hannunsa ya Sanya ya dago kanta Yana share Mata hawaye da hannunsa sanan yasa hannu yana shafa kanta cike da lallashi....juyawa tayi gefe Tana dariya ,shima gyara zamansa yayi yaja motar a guje...... **** Hajiya babba ce zaune Tana jiran feed back Dan already barrister Nasir ya sanar Mata da suna kotu, Ta kosa taji me yafaru Aiko wayarta dake gefenta ce tayi ringing da sauri ta dauka khausar ta kafa Mata ido.... Mikewa tayi tsaye daga zaunen datayi tace cikin kakkausar murya"barrister kana nufin bamuyi nasara ba?hukuncin da aka yanke kenan tabdijan nasan haka zata faru nagode"kawai tace ta kashe wayarta ta shiga kaiwa da komowa Tana fadin "fada da aljani babu Dadi,lallai khabir kayi kuskuren yin fada Dani Domin ka dauko balain da yafi karfinka saina tabbatarda na wulakanta rayuwarku dukanku" "Yanzun mama dik kudin da kika kashe a banza kenan" "Ba kudi bane a gabana khausar daukar fansa yanzun itace a gabana"..... ********* An shirya motoci daga gidan galadima zuwa masarauta inda gwaggo rahi ta fito cikin kayan alfarma irin na manyan masu kudi Kuma masuji da sarauta,har wajen mota yaranta suka rakota deejahmah tace"to mama saikin dawo a tattauna lafiya" "Ameeen"tace yayinda driver yaja mota su deejahma Suka koma cikin gida..... ********* Tafe suke daga court ko wannensu baya magana Fatima nata kalle kalle a gefen titi,juyowa tayi tace cikin sassanyar murya "yanzun Yaya yarima Ina zaka kaini gidan Ablah?" "Masarauta xamuje rikonki ya dawo hannuna yanzu" Dafe kirji tayi hado da zaro ido waje,Jin maganarsa tayi tamkar saukar aradu yayinda taji kamar an Sara Mata gatari a tsakiyar kanta...... Ko kallonta beyiba ya cigaba da driving dinsa....yashanyo kwanar gidansu ta Kara kwalalo ido waje...... Kofar gidan aka bude musu aikuwa Fatima ta fashe da kuka suna shiga wata mota ta wuce a guje cikin gidan da Yan rakiyata da tambarin sarauta a jiki an rubuta *GALADIMAR BARAYAR ZAKI* ..... *muje zuwa yanzun* *zaafara wasa*....... *wayyoo* *hajiya babba🤭* *SLIMZY😍✍🏼*🌩 *ANYI WALK'IYA.....* 🌩 *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 *NA:SLIMZY✍🏼* _wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* *HAPPY BIRTHDAY IN ADVANCE MOMMAH....*( *_Billy_* _*galadanci* )_ ~Shaku shaku don~ ~start from today~ 💃🏻😍😍 17 Kuka Mai sauti wanan karon Fatima ta fashe dashi a cikin motar ta riko hannunsa Tana kallonsa cikin ido,kauda kansa gefe yayi ya zura kafarsa daya waje yace "ummhmm Ina sauraronki akoke gwamnan kuka me kike nufi kika rikeni kina rusamun kuka kamar nayi Miki wani Abu" Kuka ta cigaba dayi batare da tace Masa uffan ba haushi ya Kara kulesa a zuciye yace"Kinga idan bakida abinda zakice ki sakarmun hannuna in shiga gida idan Kinga Zaki biyoni ki biyoni idan Kuma cikin mota Zaki kwana to Bismillah" Baki na rawa idanuwanta a rufe hawaye kawai ke gudu tace"Yaya yarima kayimun Rai ka rufamun asiri wallahi zamana a gidanku zai zamemun tamkar kabari,bazan tabajin dadin zaman gidan Nan ba bayan kowa ya Gama tsanata,ka rufamun asiri ka maidani gidansu Ablah ko ka maidani ainihin gidan mu" Wani haushine ya turnikesa ya kalleta fuska a daure yace"wato ni kike kallon tsabar idona kina cewa wai zaman gidanmu zai zame Miki tamkar kabari?wato baki shirya fuskantar dik wani kalubale akainaba ko?nine na shirya hakan ko?hmmmm to Fatima kisawa ranki bakida wajen Zama sai Nan gidan Dan wadanda kikeson Zama dasu babu abinda na hada Dasu sai soyayya da mutunci da sukemun Kuma koba hakaba wallahi bazan iya barinki kiyi Nisa Dani ba,idan Kuma kinga ke Zaki iya rayuwa babuni saki fadamun"....Yana fadin haka ya Juyo ya kafeta da idanuwansa da suka canja kala lokaci daya.... Girgiza Kai kawai takeyi Tana kuka zuciyarta na wani irin harbawa sauri da sauri lallai yarima so yakeyi a kasheta a cinye namanta Danye,ta kashe musu da' Kuma ya dakkota yace tazo cikinsu tayi rayuwa?sanan a matsayinta na tsintacciyar mage?yadai kawota kawai tayi bauta.....batada yadda zatayi ta bijire Masa don ita kanta bazata iya rayuwa a wani wajeba Babu shi.... Kukan kawai takeyi Babu kakkautawa hannu yasa ya cire makullim mota yace "share hawayenki ki biyoni"....fitowarsa yayi ya rufe bangarensa, Hakanan ta sako kafarta ta fito waje tasa hannu ta share hawayenta,shiko kulle motar yayi ya Kara hada ransa tamkar wani Zaki tamkar tunda yake be taba dariya ba yayi gaba,dakyar take cira kafa Tana binsa a baya. Babban gidane gidan sarauta dik inda suka wuce kallonsu akeyi daga maaikata har bayi da kuyangi kowa kallonsu yakeyi yadda take binsa tamkar tsomammiyar kaza ga uban hijabi har kasa..... Kuskus kawai ke tashi wajen bayi dik inda suka gifta har lekensu ake yayinda zuciyarta ta cigaba dayi Mata lugude ji takeyi tamkar ta hadiyi zuciya..... A haka har suka iso kofar da zata sadasu da babban sashi na gidan inda bayi ke tsattsaye masu tsaron kofar sashin take suka zube kasa suna kawo gaisuwa hannu kawai ya daga musu ya wuce Fatima na biye dashi..... Shi kansa uban gayyar cikin faduwar gaba yake saidai a fuskarsa ya tsare gida da jarumtaka irin tasa tun kafin su saka kafa a parlorn ya jiyo muryar gwaggo rahi....dammm gabansa ya yanke ya fadi haka kawai yaji zuciyarsa na bugawa sauri da sauri haka ya jajurce ya daga labulen dake zagaye a kofar yayi sallama"Assalamu alaikum"...fuskarsa a dake, Labewa Fatima tayi a bayansa taki shigowa dukkansu suka zuba Masa ido ganin yanayin yadda ya daura fuska Yana waige waige kamar Mai neman wani Abu a dake yace"Fatima shigo Mana ya kika tsaya a baya" Fatima da kafafuwanta da ilahirin jikinta ke rawa tamkar ta saki fitsari haka ta daga kafarta ta daga labule ta shigo da sallama a ciki..... Wani zabura da hajiya babba tayi nikaina saida na koma gefe a guje na labe a bayan labule Ina kallon ikon allah😂😂😂....gogan na hango ya dake fuskarsa babu annuri Hajiya babba da dik wani mahaluki dake dakin saida ya furgita tamkar sunga abin tsoro jikin hajiya babba Yana tsuma kamar anayi Mata gangi tace"lallai kabiru ka cika Dan halak ka nuna Mana cikakken Mara kunya ne kai fitsararee wato matsiyaciyar yarinyar Nan wulakantacciya ita ka dakko ka kawo Mana muma ta biyo dare ta kashemu?kamar yadda ta kashe habibu Kuma ka goyi bayanta to karyarka Tasha karya kayi kadan wallahi"bakinta har kumfa yakeyi.... Da sauri gwaggo rahi ta juya Tana kallon yarima dake tsaye kamar an dasashi Fatima a guje ta koma bayan yarima ta makale ganin yadda hajiya babba ke surfa balai, Dafe kirji gwaggo rahi tayi tace"kabiru tsintacciyar mage ka dauko ka kawo masarauta?kabiru Anya ka shirya gaskiya a lamarinka" Da sauri hajiya babba ta karbe zancen tace"Ina gaskiya a lamarinsa,aini tunanina gabaki daya ya canja akala Akan hada baki sukayi ta kashe habibu ya daukota ya kawota ta biyo dare ta kashe Mai martaba to kayi kadan wallahi kayi tsararo" Zuciyar yarima zuwa wannan lokacin ta Gama konewa tamkar zata Kama da wuta yakeji tunda yake be tabaganin mutane masu son Kai da son zuciya kamar mutanen masarautarsuba, Bude baki yayi zaiyi magana"hajiya...." Daga Masa hannu hajiya babba tayi tace dakata kabiru ai *ANYI WALK'IYA* asirinka ya tonu wanan abun da kayi Kai Mai tausayi Mai Jin Kai na maraya kaiga malam sarkin son lada da musulunci ya nunawa duniya inda ka dosa sanan hakan ya tabbatar munda da hadin bakinka aka kasheshi dana uwarka don dik abinda kuke kullawa Yana dawowa kunnena,yanzun Kun kulla makirci Akan a daukota a dawo da ita Nan saita karasa contract din daka Bata na kashe sarki da habibu Dan ka hau karagar mulki ko to kayi kadan wallahi kasake sabon shiri" Wasu irin zafafan hawayene ke gudu a idanuwan mama karama wadda ta kafe yarima da ido tun shigowarsa sai yanzun tasamu halin magana"burinka ya cika kabiru abinda nake guje maka gashi ka daukowa kanka Nima ka daukomi" Hankalin yarima ba karamin tashi yayiba ganin mahaifiyarsa na kuka,cillar da Curt dinsa yayi dake hannunsa ya ruga da sauri ya zube a gabanta ya fashe da kuka Yana fadin"Dan girman Allah ki daina zubar da hawayen Nan a gareni Domin hawayen uwa a wajen danta dafi ne daidai da second daya kikayi fushi Dani bazanga da kyau ba ban dauko Fatima na kawota gidan Nan Dan intozartaku intozarta martabarku ba nayi hakan ne Dan in nemawa masarautarmu kima da daraja a idon mutane duniya zatasan cewa ku masu adalcine tunda danku shi yayi kokarin lalatawa marainiyar Allah rayuwa ta kasheshi kuka daukota kuka inganta Mata rayuwa har a wajen Allah kunada lada Mai yawa wallahi summa tallahi bazan iya Bari rayuwar Fatima ta cigaba da wulakantaba" Dariya hajiya babba tayi maicin Rai tace"ai rayuwarta ta Gama wulakanta tunda uwarta cikin shegenta tayi ta haifeta ta Yar a bakin kwata gwamnati ta tsunta wulakanta ta karewa Dan kwararo Dan Fatima batada maraba da yayan kwararo" Runtse idanuwa Fatima tayi hawaye na gudu kamar an bude famfo a idanuwanta tunda Allah ya halicceta Bata taba tozarta irin na yauba dik wulakanci da cin kashin da hajiya halima keyi musu a gidan marayu be Kai wanan ba inama ace Allah ya dau ranta da wanan wulakanci da tozarci datake fuskanta a cikin wannan duniyar Mai cike da kalubale kala kala.....kuka Fatima ta fashe dashi Mai karfi.... Wani kallon tsana Mai hade da kyama hajiya babba ta wurgawa Fatima jitakeyi kamar ta shaketa a duniya batada makiyin da yakai Fatima bayan mutuwarta,takowa takeyi Tana wani girgiza tamkar giwa tazo har inda Fatima ke tsaye Tana rizgar kuka ta nuna Fatima da yatsa a wulakance tace"jibeta kamar ta Allah,har wani kuka kikeyi irin na munafukai tsofaffin kilaki masu shegen makirci ko kinzone ki yaudaremu kici amanarmu to kinyi kadan wallahi Ina Mai gargadinki da babbar murya tun wuri kisan inda dare yayi Miki ko ki koma can gantalin kwararon ko ki nemi wani wajen Amma ba gidan Nan ba shima Wanda kuka hada baki dashi aka kashemun gudan Jini kijira sakamakonsa"....takaiwa Fatima hankada jikin bango ji kake kummmmmm.....dafe Kai Fatima tayi juwa na dibarta ta zube a kasa ta saki kuka.... A zuciye Kabir ya kalli hajiya babba yace"menene aibun maraya?menene illar Dan da aka tsinta aka mikawa gwamnati ta Zama uwarsa da ubansa?shin kunada tabbacin Fatima tsintacciyace?bakwa tunanin iyayenta a tafarkin sunnah suka haifeta wata kaddarace ta rabasu?kunsan makomar Mai wulakanta maraya da cin zarafin maraya kuwa?Allah yayi alkawari dik Wanda ya zalunci maraya daidai da kwayar zarra sai Allah yayi masa sakayya bai kamata Fatima ta Zama abun kyama a wajenmuba mu masu gata Dan ita takasance Mara gata,Ina Mai tabbatar mukuda wallahi summa tallahi sai Fatima ta dawo gidan Nan" Jinjina Kai kawai gwaggo rahi keyi Tana tafa hannu cike da mamaki da al'ajabin yarima take fadin"lallai kabiru alamarinka yayi Nisa bakajin kira lallai ka tabbata Mara kunya fitsararee wanan maganar kake duban tsabar idonmu iyayenka kake fada mana saboda tsintacciyar mage kilaki daka tsunta Koda yake ba laifinka bane laifin uwarkane tinda a gabanta kakeyi takasa kwaba maka wai ita Mai kawaici da hakuri" "Bakinsu daya rahina wallahi uwarsa bazata iya ce Masa komiba kila ma ita tasashi ya kawota tasan komi karma kice wani Abu nidaidai nake dasu gobe Mai martaba zai dawo zaayita takare Amma wanan tsinanniyar Bata Zama a gidan Nan" Cikin daga murya mama karama ta na kallo yarima Rai a bace tace"dauketa kubar gidan Nan yanzun Nan tunban Bata maka Rai ba kabiru bazaka daukomin fitina ba kujecan kukarata idan mahaifinka ya dawo" Tana Gama fadin haka ta juya ta fice a parlorn tayi bangaren ta,kallonsu yayi daya bayan daya yace"Fatima batada wajen xama sai gidan Nan da yardar Allah insha Allah saita zauna a gidan Nan Bari Mai martaba ya dawo".... Da karfin gaske ya tako daga inda yake ya daga Fatima dake durkushe hannunta akanta ta dafe inda ta buge Tana famar kuka kamar numfashinta zai dauke.....janta yakeyi suka fice a dakin hajiya babba ta biyosu Tana yayyafa balai Tana fadin 'aida ka barta da yanzun nabada umarni sarkin baka ya soketa kowa ya huta shashasha mu zuba"...... Haka ta juyo parlorn Tana kumfar baki gwaggo rahi Tana tayata suna zagin yarima tasss.... Fitowa sukayi harabar masarautar suna tafiya a hanya sukai kicibis da khausar da affee andawo dasu daga gidan waziri masu tsaronsu suna take musu baya,...tun daga naisa affee ta kafe yayan nata da ido ganin yadda yakejan yarinya a hannu har sukazo zasu gifta su,kallo afee tabisu dashi hankalinta a tashe ganin yanayin yayan nata yayinda khausar ta tabe baki ta bisu da harara...... ********* Gudu kawai yake shararawa a mota kamar zai tashi sama,be taba tsintar kansa a mummunan bacin Rai irin na yau ba,sanan babban tashin hankalinsa mahaifiyarsa tayi fushi dashi harda zubar da Hawa akansa, It's kuwa Fatima kuka yin kansa yakeyi zuwa wanan lokacin kukan da takeyi ya dauke diff kamar anyi ruwa an dauke babu abinda takeyi sai ajiyar zuciya.....wani gida daban taga sun nufa da sauri ta waigo Tana kallonsa ko kallon inda take beyiba parking motarsa yayi ya fito har ya nufi hanyar shiga gidan sai ya hangi wata mota a can gefe tanayi Masa horn da alama mutum ne a ciki juyowa yayi da sauri ya nufi wajen motar.... Ahmad ne ciki abokinsa shima ganin yarima da sauri ya kashe motar da dama fita zaiyi ya fito.....Fatima ma fitowa tayi Tana takowa a hankali kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki, Cikin kidimewa Ahmad ya kalli yarima yace"ranka ya dade lafiya naganka a yamutse haka?" "Inafa lafiya Ahmad Ina cikin damuwa friend nida Fatima ne gatanan" Da sauri Ahmad ya juyo Yana kallon wadda aka Kira da Fatima,kallonta yake sosai daga sama har kasa a zuciyarsa yace"lallai babu karya wanan yarinya kyakkyawace"......irin kallon da Ahmad keyi Mata ya bawa yarima haushi a fusace yace "dalla malam wanan wani irin kallo ne saikace tsohon maye".....Dan Sosa Kai Ahmad yayi ya wayance ya juyo yace "yanzun meke faruwa" Nan yarima ya kwashe abinda ya faru ya fada Masa komi be boye Masa ba,jinjina Kai kawai yakeyi Yana jinjina irin wanan karfin Hali na yarima sanan yace"to Kai abokina Mai zai Hana ka maidata gidan Abdul zuwa wani lokaci"..... "Dakata malam ai nasan da gidan Abdul din nakaita gidanmu saboda ninasan abinda nake nufi da hakan,Kuma a gaskiya bazan iya bawa kowa rukontaba,bazan iya Bari Fatima tayi Nisa Dani ba saboda abinda na kudura araina akanta......nazo kabani shawara kanamun wata magana Mara dadi mtseww" Murmushi Ahmad yayi yace"to yanzun shawarar da zanbaka ka dauketa ka kaita gidan Abdul zuwa gobe,kafin Mai martaba ya dawo kamar yadda kafada" Ajiyar zuciya yarima ya sauke yace"to shikenan zanyi hakan,Kuma nasan Mai martaba baya kyamar talakawansa shi Mai tausayine Kuma Mai adalcine ga nakasa dashi nasan saidai idan ban bayyana Masa bukatataba da hujjojina zaiyi naam da maganata nagode Bari muje" Juyawa yayi inda Fatima ke tsaye a rakube ya kalleta Nan da Nan tausayinta ya kamashi "Fatima muje ko inkaiki wajen Ablah".... Gyada Masa Kai tayi ta juya ta nufi inda motar yarima take ya biyo bayanta...... ********* A can gida kuwa wajen hajiya babba da gwaggo rahi sungama tsara komi Akan auren na yareemah da deejahmah sanan tayiwa gwaggo rahi alkawarin da zarar Mai martaba ya diro masarauta zata gabatarasa da wanan shawarar da suka yanke insha allahu zatasan yadda tayi ta kullawa yarima makirci Akan auren deejahma kodan ta Rama Mata abinda yarimah yayi Mata,a haka sukai sallama gwaggo rahi ta baro masarauta..... ******* "Niko Ina mamakin wanan al'amari ranka ya dade ace wai mutane babu abinda suka sawa zuciyoyinsu sai son Kai da son zuciya,menene aibun Fatima?meye abun kyama a wajen wanna yarinya data kasance baiwar Allah ?"....kwalla ce ta ciko a idanuwan ablah Tana rungume da fatyma Tana kuka Mai ban tausayi.... "Niko ranka ya dade mazai Hana kabarmun rukon Fatima a wajena na harabada aure ya rabani da it's tunda kaga halin da ake ciki mutanen gidanku basa kaunarta idan ka kaita bakasan irin zaman da zatayi a can ba" Gwauron numfashi yarima ya sauke hade da furzo iska daga bakinsa sanan yace"kiyi hakuri barrister bazan iya bar Miki rukon Fatima ba alkawarin Dana daukarwa kaina akanta insha Allah ko Ana muzuru Ana shaho saina cikashi.....nafi so ta zauna a kusa Dani daidai da minti daya banaso Fatima tayi Nisa Dani,yau ma nakawotane ta kwana anan zuwa gobe idan Mai martaba ya sauka da safe idan mun tattauna da yamma zanzo in dauketa,akwai dalilin dayasa nakeson Fatima ta zauna a can din na gaba kadan zaku sani" Harga Allah Ablah bataso ba da wanan shawarar da yarima ya yanke Amma babu yadda ta iya ya fita iko da Fatima..... ******** Sai misalin karfe takwas na dare ya shiga gidansu direct bangaren mama karama yayi da sallamarsa ya shiga, a ciki ta amsa Masa sallama sanan ta juya baya....."mama...." Da sauri ta katsesa ta hanyar daga masa hannu sanan tace"tashi ka fita indai wanan maganar ce bana bukatarta yanzun"...kofa ta nuna Masa ya Mike jiki a sanyaye ya kalli afee yace"say dafamun ruwan zafi ki kawomin"...kallonsa tayi cike da tausayin Dan uwan nata tace"toh Yaya"....ya fice... Afnan ta biyo bayansa har bangarensa a kofar shiga side dinsa tayi kicibis da baiwarsa dake kula dashi hannunta dauke da fruits zata Kai mishi afnan tayi gyaran murya da sauri ta zube a kasa Tana kawo gaisuwa, batare da ta amsaba tacee"lantana koma ki fadawa saade ta dafowa yarima ruwan zafi akawo Masa" Kara durkusawa lantana tayi tace"angama ranki ya dade".....wucewa afnan tayi ta shige bakinta dauke da sallama lokacin Yana tsaye ya cire kayan jikinsa ya Sanya jallabiya cream colour Yana kokarin Zama a kujerar dake karamin parlornsa, Wuri ta nema itama ta zauna fuskarta dauke da alhini tace"Allah ya huci zuciyarka yaayah Ashe abinda ya faru kenan yau, a gaskiya na tausayawa Fatima irin cin zarafi da cin mutuncin da akayi Mata,Abu dayane nakeso Yaya ka kwantar da hankalinka ni na tabbatar da cewa abun Nan da kake shirinyi abune Mai kyau Kuma hakan zai jawowa masarautar mu kima da daraja a idon mutanen gari wadanda sukasan da abinda ya faru saidai fa gaskiya Fatima babu Wanda zai kaunaceta saitayi hakuri Dan gaskiya lamarin akwai sarkakiya" Tunda afee tafara magana ya kureta da ido tamkar Mai nazarin wani Abu harta karasa sanan yace"nasani little sis Kuma bazan taba canja kudirina ba Akan abinda nayi niyya" Girgiza Kai kurum afnan tayi Sarai tasan taurin Kai irin na yayanta bazai taba canja kudirinsa akan abinda yayi niyya ba inba yanzun bama da wanan Abu ya faru shi ko magana ma Bata damesaba balle shiga hurumin mutane.... Nisawa tayi ta sauke sassanyar ajiyar zuciya tace"Allah yasa mudace" "Ameen"kawai yace ta Mike tayi Masa saida safe lokacinda lantana ta shigo hannuta dauke da babban faranti da jug da cups akai.... ******* Gwaggo rahi ce can kuryar dakin yaranta yan Mata sunyi Shirin kwanciya dukkansu Amma xantawa sukeyi kus kus a kuryar daki... "Wai mama yanzun Yaya Kabir ne ya hakikance Akan wanan yarinyar da gaske?to meye hadinsa da ita?" Kasa da murya gwaggo rahi tayi tace"wayasani deejahmah aimu tunanin da muke ma yanada sa hannu a kisan habibu Kila shiyasa ya hakikance Akan sai yarinyar ta dawo gidan sarauta ni wanan kyakkyawar yarinyar ma zargin da nakeyi babu wata marainiya Kila budurwarsa ce yayi Mata alkawarin aure bayan ta kashe habibu" Zumbur deejahmah ta Mike ta dafe kirji tace"mama?yanzu kina nufin bayan ya goya Mata baya a kotu Kuma ya daukota ya kawota masarauta da Zama?meyake nufi da hakan?" "Shikadai yasan kudirinsa shida uwarsa,aini yanzun Raina fess tunda akai haka kan kowa zai rabu a gidan Kuma hajiya babba tayi naam da maganarki to nasan babu makawa aurenki da kabiru" Murmushi deejahmah ta sauke tace"aikuwa nice zan ramawa habibu duk abinda akayi Masa na sanaddiyar ransa da akayi na kuduri aniyar saina salwantar da rayuwar kabiru matukar Ina numfashi...." Zaro ido gwaggo rahi tayi tace"kina haukane?kinsan me kike fada kuwa deejahma?" Jinjina Kai deejahmah tayi ta kalli uwarta tace"nasan Shirin da zanyi akansa kafin in kasheshi saina haifi magajinsa sanan kafin in kasheshi saina nakasa rayuwarsa ya Zama tamkar mutum mutumi....." Jinjina Kai gwaggo rahi tayi Tana murmushi tasan niyyar yartata... "Aini gobe da yamma da gayya zanje gidan yiwa Dan uwana barka da zuwa inji mezai faru....." *Muje zuwa* *SLIMZY✍🏼🥰*🌩 *ANYI WALK'IYA.....* 🌩 *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 *NA:SLIMZY✍🏼* _wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* *HURRAY🎉* _it's d birthday party of my one in_ _millions,infacts billion's,sweet mommah...,u are spacial and morthan capable of achieving everything u put in ur mind,😍I want to hear lots of ur success stories dis new age and_ _always......I am so glad to have u🥰and u are such a_ _soul whom I will be loving through out_ _my entire life...._ *HAPPY BIRTHDAY WORLD CUTTEST MOMMAH* ...( *_Billy_* *_Galadanci_* )🍰🎂🎉 18 Tun sassafe maaikatan gidan suke kaiwa da komowa wajen shirye shiryen kayan abinci Wanda zaa tarbi Mai martaba dashi na girke girke da kayan ciye ciye...dik inda kabi sasan masu aiki kamshi ke tashi kasantuwar kowa yasan idan sarki yayi tafiya rangadi to da safe yake sauka.... Misalin karfe Tara da rabi ,gida ya kacame da hayaniya da busa irin na algaita kasantuwar masarautar barayar Zaki masarautace ta gargajiya Mai dumbin tarihi....dik Wanda yaji wanan busar yasan cewa sarki ne zai shigo ko zai fita.....yarima na kwance a dakinsa yaji hayaniya taki karewa gashi yanaso yadan runtsa saboda rashin samun isasshen bacci da beyiba Daren jiya ga matsanancin ciwon Kai days kwana dashi.....gyara kwanciya yayi ya janyo bargo ya lullube har tsakiyar kansa amma inaaa hayaniyar Yar rakiyan sarki dake shigowa da dawakai wasu da mota bazasu barshi yayi baccinba....kafarsa ya zura kasa ya Mike ya fada bathroom don yayi wanka..... Bangarensu mama karama da hajiya babba kuwa ko waccensu sanye take da hadaddiyar lafaya Mai tsadan gaske sun hallara a babbar fadar sarki inda dik jamaar gidan suke shigowa suna kawo gaisuwa suna fita,fuskar Mai martaba dauke da murmushi yake karba gaisuwa har kowa ya watse ya kasance dagashi sai iyamensa,inda afnan ke zaune ya kalla Tasha kwalliyrta tai kyau da ita murmushi ya sakar Mata yace"uwata ummul khair autar masarautar barayar Zaki ya akayi ne umm?" Rankwafawa afnan tayi cike da ladabi tace"nayi matukar farin cikin ganin abbahna cikin kosasshiyar lafiya Allah ya Kara maka lafiya da Nisan kwana"jinjina Kai Mai martaba yayi cike da Jin dadin kalaman afnan ya juya ga khausar wacce ta hade fuskarta babu yabo babu fallasa yace"nayi farin cikin ganinki zinariyar masarautar barayar Zaki ya ga Mai martaba"....murmushi Mai kayartarwa khausar tayi hade da Jin dadin wanan kirari da dukkaninsu kowa da irin Wanda yakeyi Masa cikin zolaya ,Dan rankwafawa tayi tace"barka da zuwa mahaifina fatan kana cikin koshin lafiya,Allah ya ja da ran Mai martaba"Tana murmushi ta karashe zancenta,jinjina Kai sarki yayi yace"lafiya kalau alkhausar" Juyawa yayi inda matansa ke zaune wuri daya jere ya kalli hajiya babba cikin murmushi yace"nayi matukar farin cikin ganin uwar gida sarautar Mata ta wanan masarauta ta barayar Zaki Ina fatan nasameku lafiya keda kanwarki sarauniyar masarautar barayar Zaki" Mama karama murmushi tayi ta dukar da kanta kasa alamar girmamawa da gaisuwa,...jinjina Kai sarki yayi ya amsa gaisuwarta sanan hajiya babba cikin faraa ta kawo Tata gaisuwar dukkansu ya karba musu cike da farin cikin ganin iyalen NASA.... Shiru ne ya gauraye fadar babu Wanda yace uffan sarki ne yayi gyaran murya yace"kowa yazo ya Miko gaisuwa a gareni Amma Banga Dan autan sarki ba Kuma sarki Mai jiran gado kabiru" Karaf hajiya babba tace cike da izza"yaushe zaizo Yana tashen rashin kunya da rashin mutunci".....murmushi kawai Mai martaba yayi batare da yace uffan ba Ana haka saiga Kabir yayi sallama cikin fadar cike da natsuwa Yana sanye da Riga da Wando na jamfa irin na yaran gidan sarauta bakake sun matukar amsar fatan jikinsa a matsayinsa na farin mutum...... Har kasa ya tsugunna a gaban mahaifinsa fuskarsa dake da tsadajjen murmushin Nan Nasa yace"barka da zuwa ranka ya dade fatan ka sauka lafiya?nayi matukar farin cikin ganin mahaifina cikin kosasshiyar lafiya,Allah ya karawa sarki lafiya da nisan kwana" Murmushi kawai Mai martaba yakeyi Yana jinjina Kai farin cikin ganin tilon Dan NASA yaki boyuwa a fuskarsa sai jinjina Kai yakeyi Yana kallon yarima Wanda ke tsugunne a gaban mahaifin nasa kansa a kasa cike da girmamawa..... ******** "Niko Fatima gani nakeyi zamanki a gidan sarauta zaifi Miki,Domin a fahimtana akwai wani kuduri da Yaya yarima yakeso ya cimma koma Dole saida hakan" Murmushin takaici Fatima tayi hawaye na sulalowa a idanuwanta tasa gefen hannunta ta share sanan ta Soma magana"Aysha kenan a naki tunanin Amma babu wani kudurin daya wuce alkawarin da yayimun na zamemun gata a wanan duniyar,Kuma indai haka ne to dik inda nake zai iya Zama gata na tunda Ablah tace yabarni a Nan gidan yace ah ah bankuma San me hakan ke nufiba" Murmushi Aysha tayi Wanda har saida side dimple dinta ya lotsa tace"Niko a tawa fahimtar kenan zamanki a gidansu shine zaibashi damar aurenki" Da sauri Fatima ta dafe kirji ta zaro idanuwa waje Tana girgiza Kai take fadin"Aysha kiyi shiru kada kiyi zunubi Domin wanan maganar da kike fada saidai a mafarki Dan abune da bazai taba yuwuwa ba ki dubani fa kiga koni wacece sanan ki tunada yadda yarima yake ni tunda mukema bai taba furtamun kalmar so ba nadaisan Yana tsananin tausayina" Hmmmm"Fatima kenan wallahi Yaya sonki yakeyi,koya fada miki Kobe fada mikiba sanan yayi hakan ne don yasamu damar aurenki" Jijjiga Kai Fatima keyi zuciyarta nayi mata zafi tace"Aysha ko giyar wake yarima yasha bazai taba aurenaba iyayensa da danginsa bazasu bariba sanan yarima yafi karfina ni wacece?waye gareni a duniyar Nan sai Allah mahaliccina" "Kuma Allah da kike dashi Fatima shike azurta bawansa a dik lokacin daya gadama saboda haka banaso kicire Rai daga rahmar Allah" "Mubar maganar Nan Aysha".... Dik maganar da sukeyi Ablah Tana tsaye a jikin kofa ta harde hannayenta a kirjinta Tana kallonsu musamman Fatima dake magana cikin karayar zuciya....gyaran murya Ablah tayi musu dukkansu suka juyo da sauri suka dubeta,...lallausan murmushi ta sauke sanan tace"hirar ta Isa azo muje a shiga kitchen muyi abincin Rana yanzun haka har azahar tayi" "Toh Ablah"dukansu suka hada baki suka Mike a tare ita tayi gaba suka bita a baya don shiga kitchen... ******* Bayan sallahr laasar tawagar gidansu gwaggo rahi data gidan waziri suka shigo gidan sarki Domin yiwa sarki barka da dawowa daga Yar tafiyar da yayi,.... Gida cike yake makil da jamaa ko Ina yarane samari da Yan Mata na masarautar wasu na Hira wasu na ciye ciye bayan ko wannensu ya je ya kaiwa sarki gaisuwa.... Dik suka dawo babban parlor na gidan suna zaune suna Hira sama sama ko wacce da abokiyar hirarta yayinda deejahmah ta koma gefe can ta kishingida da kilisa Tana daddana waya bakinta na taunar chewing gum a yangance fuskar Nan ta dau kwalliya.... Yarima ne ya fito daga bangarensa wanan karon yayi wanka ya canja Kaya zuwa wasu Riga da wandon na jamfa masu kwalliya kakarsu daban jajaye ,kansa sanye da hula baka tayi Masa kyau sosai fuskarnan babu walwala sosai ya fito ya bullo ta kofar baya wadda zata sadashi da main parlor na gidan ,kamshin turarensa shi ya fara karade parloyn gidan dukkann Yan matan dake parlorn saida suka waiga don ganin Wanda zai shigo Banda deejahma dake taunar chewing gum bakinta Yana kass kass a hankali....sallama yayi musu a ciki ya shigo parlorn dukkansu suka hada baki wajen gaisheshi hannu kawai ya daga musu har ya wuce ya dawo ya daura fuskarsa yace"Ina fatan dukkanku kunyi sallahr laasar"...mikewa suka shigayi daidai da daidai suna ficewa ,deejahmah ko dake kishingide zuciyarta nayi Mata bugu sauri da sauri tunda yarima ya shigo ta tsinci kanta a wanan yanayin Amma hakan besa ta daga Kai ta kallesaba,dago idonta tayi ta saci kallonsa sai ta ganshi a tsaye da sauri ta sauke kanta kasa Tana daddana wayarta, Dan waigowa yayi ya kalli inda take ya kauda Kai cikin wata iriyar murya yace"kefa bakiji abinda nafadawa sauranba kenan" Yatsuna fuska tayi ta dago daradaran idanuwanta ta saukesu akansa tace"banayi Ina hutu".... Dan taking ya saki sanan ya fice a dakin tabi bayansa da kallo hade da tabe baki.... ********** Gwaggo rahi ce durkushe a gaban Mai martaba suna Kara gaisawa yayinda hajiya babba data kasance itace da girki a wanan Rana Tana gefen Mai martaba,bayan sun Dan taba Hira da Mai martaba gwaggo rahi tayi Masa sallama ta fice a fadar ya rage daga hajiya babba sai Mai martaba, Shirune ya biyo baya na minti goma sanan hajiya babba tadan durkusar dakai kasa tace"Allah yaja da ran Mai martaba akwai maganar da nakeso mutattauna" Jinjina Kai sarki yayi yace"Ina sauraronki" "Nagode ranka ya dade,....dama wata maganace nakeso mu tattauna Kuma shawarace nake ganin ta Dace" "Ina sauraronki" "Dama a game da yaran Nan ne kabir da Khadija Yar wajen rahina wadda akayiwa marigayi habibu baiko da ita shine a ganina tunda haka takasance Kuma yarinyar batada manema dikta sallami kowa shine nace zan shawarceka Mai zai Hana kabiru ya maye gurbin Dan uwansa hakan shi zai cirewa yarinyar radadin rashin tsohon mijin nata" Shiru sarki yayi na wani lokaci Yana jinjina lamarin sanan yayi gyaran murya yace"wanan shawarar taking tayi"...washe baki hajiya babba tayi,sarki ya cigaba da magana"amma kina ganin hakan baa shiga hakkin ita yarinyar ba?" Kara durkusawa tayi cike da ladabi tace"ranka ya dade Khadija batada wani zabi daya wuce zabinmu kafin in zanta dakai saida nafara tuntubar yarinyar batare da kowa yasaniba Kuma ta amince da hakan" "To alhamdulillah naji dadin wanan shawarar Kuma tayi sanan shi kabirun zaizo ya sameni zan sanar Masa da hukuncin da muka yanke" Wani dadine ya lullube hajiya babba tamkar ta Mike ta taka rawa kudurinta ya cika saura na biyu na Hana Fatima zaman gidan sarauta.... "Assalamu alaikum"yarima yayi sallama cikin fadar shine ya katse hajiya babba daga tunanin data fada..... Takowa yayi cike da ladabi ya karaso Kan babbar daddumar dake cikin fadar ya nemi gefe ya zauna ya sunkuyar dakai hade da Mika gaisuwa wajen Mai martaba da hajiya babba,....cike da kulawa Mai martaba ya amsawa Dan nasa Banda hajiya babba dake gefe Tana jifansa da mugun kallo na tsantsar tsana da kiyayya.... Sarkine yayi gyaran murya yace"Dan halak yanzun muke maganarka da mamanka sai gaka ka shigo"...dammmm gaba yarima ya yanke ya fadi Nan da Nan zuciyarsa ta shiga yi Masa bugu Amma sai ya daure yayi murmushi kawai.... Sarki ya cigaba da magana cike da Kamala "mamanka ta gabatarmunda wata shawara data yanke gameda maida neman auran Dan uwanka akanka Wanda dama ko aurenta yayi ya mutu kanada damar da zaka kula da iyalinsa da yaransa balle Allah be kaddaro hakanba saboda haka mamanka ta kawomin shawarar hakan ni Kuma Naga dacewar hakan me magani" Jikin yarima rawa kawai yakeyi yayinda ilahirin network din jikinsa gaba daya ya dauke zuface kawai ke tsattsafowa a goshinsa dakyar ya iya motsa bakinsa yace"banida wani iko da zanja dashi Akan hukuncin iyayena dik hukuncin da suka yanke akaina daidaine,yanzun haka tafe nake da tawa bukatar zuwa gareka mahaifina" "Alhamdulillah Allah yayi maka albarka ka cika Dan halak wanan ya nuna lallai kaidin kaunar da kakewa Dan uwan naka ta hakikace,mecece taka bukatar Dana Fadi ko meye inhar inada halinta to zan biya maka ita" Gyara Zama yarima yayi yace"Ina neman agajin sarki Akan ya duba lamarin wanan marainiyar Allah wadda kaddarar kisan Dan uwana ya fado a hannunta bada niyyartaba inaso sarki Mai adalci Akan talakawansa ya duba lamarin yarinyar Nan rukonta ya dawo hannun wanan masarauta Mai cike da adalci" Wani mugun kallo hajiya babba ta wurgawa yareema sanan tace"ka canja bukatarka yarima Dan sarki wanan bukatar bame yuwuwa bace Dan bakada kwakkwaran dalili sanan babu yadda zaayi yarinya tayiwa Dan sarki kisan gilla a daukota a kawota masarauta a ajiyeta ni mahaifiyar marigayin Ina gani baayimun adalciba" Gyaran murya sarki yayi hajiya babba tayi shiru, "Yarima meye hujjarka da dalilinka nason rukon yarinya yadawo hannun masarauta?" Gyara Zama yarima yayi yakara gurfanawa dakyau a gaban sarki yace"yin hakan zai kauda zargin mutane Akan labarin da sukaji na Dan sarki na neman yin lalata da yarda batada galihu,sanan yin hakan zai karawa masarautarmu kima da mutunci da daraja a idon duniya Kuma yin hakan zai daukaka masarautarmu Akan ko wace masarauta,duniya zataga munyiwa yarinyar adalci da muka daukota muka kawota cikinmu Don muyi Mata rukon gaskiya da Amana ranka ya dade" Jinjina Kai kawai sarki keyi cike da gamsuwa da kalaman yarima "tabbas kabiru wanan tunanine Mai kyau kayi Kuma na karbi bukatarka na yarda na amince kaje ka dauko wanan marainiyar Allah ka kawota cikinmu mu riketa har muddin rayuwar mu...... Murmushi kawai yarima keyi na tsantsar farin ciki lokaci daya ya mance da din wani bakin ciki daya tsinci kansa Yan dakiku da suka gabata.... Durkusawa yakarayi yace"nagode ranka ya dade Allah ya Kara lafiya da nisan kwana, nagode ranka ya dade zan iya tafiya?" Daga Masa Kai yayi sanan ya Mike har ya Kai kofa Mai martaba ya tsaidashi ta hanyar cewa "ka kirawo Khadija "...Dan durkusawa yayi yace"to ranka ya dade"..... Hajiya babba kuwa Tana zaune tamkar gunki babu yadda zatayi tai bori a gaban sarki tasan hakinsa tasan yadda yakeson Kabir yakejin maganarsa tun kafin habib ya rasu a cewarsa yafi kowa hankali....lallai Kabir ya dauko ruwan dafa kansa da kansa ya dibi rushin wuta ya zuba a bakinsa saiyayi danasanin zuwansa duniya.... Yarima jikinsa har tsuma yake Yana fita yayi dialing number barrister Abdul....ringing biyu ya dauka yace"ranka ya dade" Murmushi yarima yayi yace"tare da naka kana gida ne?" "Ehh ganinan da iyalaina inbawa Fatima wayar ne?" "Ehh".... Barrister Abdul ya mikawa Fatima waya hannu na rawa ta karba ta Kara a kunne tace"assalamu alaikum".... "Waalaikumussalam ki shirya ganinan zuwa indaukoki sarki yace inzo intafi dake" Batasan lokacinda ta sumbular da wayarba a carpet ta Mike a guje tayi cikin daki Tana sakin kuka Mai karfi.....a guje Ablah tabi bayanta... *Muje zuwa*.... *Nima sauri nakeyi muna shirye shiryen birthday party na beloved mommah (Billy Galadanci)a can masarautar hankaka zaayi celebrating inda takawa yadau nauyin komi da* *komi shida meenal😍lol...(Happy birthday onece again *)**...... *Allah* *yasadai madam season seven tayi* *Mana cake kada TAFARU TAKARE MANA😆* *SLIMZY😍✍🏼*🌩 *ANYI WALK'IYA.....* 🌩 *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 *NA:SLIMZY✍🏼* _wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* 19 Lokacinda yarima ya Isa babban parlor inda dik Yan matan suke,ya tararda gwaggon sa rahi tsaye Tana magana da su deejahma Akan suyi haramar tafiya gida motocin daukarsu dunzo, Sallama yayi ganin kanwar mahaifiyarsa ya tsugunna har kasa ya gaisheta,a dakile ta amsa ta kauda Kai gefe sanan ya Mike tsaye ya kalli inda deejahmah ke ciccin magani yace"kije Mai martaba na kiranki"... Da sauri dukkansu suka juyo suna kallonsa cike da mamaki hada girar sama da kasa yayi ya juya zai wuce gwaggo rahi ta dakatar dashi da cewa"ai saika jirata kujera tare koh" Daga inda yake ya Bata amsa da "ya rigada ya sallameni,sauri nake inje indauki Fatima Dan yamma tayi"Yana fadin haka ya saki malalacin murmushi sanan ya fice Yana murmushin mugunta idan burunsu ya cika to shima burinsa ya cika Kuma komi Daren dadewa babban burinsa zai cika su cigaba da wasan donshi haka yakeso..... Kwafa gwaggo rahi tayi cike da takaici tace"maganinka abune Mai sauki a wajena kawai kayi kiskuren shigowa hannuna" Lokaci kankani wani Abu ya zo kirjin deejahma ya tokare Mata makoshi tunda taji furucin da yarima yayi na cewa zai dauko Fatima ta nemi farin cikin da takeciki ta rasa tamkar ta fasa ihu Dan bakin ciki,haka Nan ta Mike ta bukaci wata kuyanga da tayi Mata rakiya zuwa fadar sarki...... ******** Babu wani Bata lokaci yarima ya Isa gidan Ablah Koda ya shiga parlor wajen zamansu as usual kowa yayi jugum jugum kamar anyi mutuwa shiru kowa yayi sai TV dake aikinsa,sallamarsa ce ta dawo da kowa daga duniyar tunanin daya Lula, Cikin sanyin jiki Ablah tace"yanzun yarima daukar Fatima zakayi ka rabani da ita?ka dage Akan saita koma gidanku?gani kakeyi mu bazamu iya riketaba koh?kadai rabani da Fatima hankalinka ya kwanta"ta karashe maganar Tana hawaye hade da dafa Kan Fatima wadda ke famar shasshekar kuka, Murmushi yarima yayi sanan yace"haba Ablah Nima in Dana sunan,...babu Mai rabaki da Fatima sai Allah Dan a halin yanzun kece uwar Fatima ko Fatima tabar gidan Nan bazan rabakuba zan rinka kawota akai akai Tana duba ablarta kema Kuma nasan zakije ganinta Kinga ko baku rabuba ki kwantar da hankalinki har kwana zatazo yi" Gyada masa Kai kawai tayi Tana kallon Fatima Tana sharar hawaye, Aysha dake gefe ta hada fuskarta ta zunguro baki gaba saboda takaici,yarima ya kalleta shi dariya ma ta bashi saida yadanyi dariya sanan yace"haba Ashmah bakya kyau da kunci kisaki ranki kinji ban rabaki da kawarki Fatima ba Kuna Nan tare har kawota zanyi ta rinka Miki kwanaki,sanan makaranta ma nakeso in nema Mata Kila makarantarku zan kawota ko ai Kinga Kuna tare wannan bakin da aka turomin a maida" Harararsa aysha tayi ta Mike tabar parlorn dukansu suka bita da kallo, Kallon Ablah yarima yayi yace "magriba tayi banaso a Kira sallah Ina Nan Naga abokina bayanan Kuma naso mu hadu wallahi Amma bakomi zan dawo zamu tafi saboda tare da Mai martaba muke sallar magriba " "Badamuwa shima fitar ta gaggawace ta kamashi an kirashi daga gidansu shine ya tafi zan fada Masa,"....kallon Fatima tayi hade da mikewa tace"kindaiji maganganun Danayi Miki ko Fatima karki kuskura ki ketare shawarwarin Dana baki kinji Allah ya baku zaman lafiya" "Ameen".... Mikewa Fatima tai ta rungume Ablah ta fashe da kuka a haka suke tafiya har waje,yayinda Aysha ta biyota da Dan akwatin kayanta Wanda Ablah ta sissiya Mata da Wanda itama ta Bata har wajen mota suka rakasu dakyar Fatima ta saki Ablah ta shiga mota Aysha tasa akwatinta a bayan mota yarima ya shiga yaja suka wuce, ********* Deejahmah ce tsugunne a gaban Mai martaba fuskarta a lullube yake sanar da ita shawarar da suka yanke na hadata da yarima aure, Tambayarta yayi kamar haka "khadijatu kin amince da bukatarmu Koko kina ganin kinfiso kisamu wani miji can daban kiyi aure?" Shiru tayi na kimanin minti uku,kanta a Duke take motsa bakinta"babu bukatar amincewar yaro Akan shawarar iyayensa matukar sunga dacewar hakan aikin yarone yayi biyayya ga iyayensa Akan ko wace bukata,na amince ranka ya dade" Murmushi hajiya babba keyi dake gefenta don ita kanta Tana kaunar yarinyar haka kawai deejahmah ke burgeta cike da gamsuwa da maganarta sarki yace "Allah yayi Miki albarka" Kara rankwafawa tayi tace"ameen ranka ya dade Allah ya Kara maka lafiya da nisan kwana" "Ameen" Hajiya babba na murmushi ta bude baki zatayi magana sallamar yarima ta katseta ta juyo da sauri.....Mai martaba ne ya karba musu sallamar yayi musu umarni da shigowa..... Gefen deejahmah Fatima ta raba ta durkusa kanta a kasa yayinda yarima ya koma gefen hajiya babba ya zauna dikda hararar datake watso Masa besan tanayiba, Durkusawa yarima yayi yace"Allah ya taimaki Mai martaba na kawo Fatima fada in gabatar da ita gaareka " Zuciyar deejahmah ce ta shiga bugawa sauri da sauri babu dama ta dago Kai ta duba wadda aka Kira da Fatima gata a gaban sarki, Jinjina Kai sarki yayi cikin nishadi ya kalli Fatima da kanta ke sunkuye a kasa yace"barka da zuwa yata".... Nauyinsa Fatima taji tai murmushi ta Kara durkusawa cikin zazzakar muryata Mai dadin gaske tace"Allah ya karawa sarki lafiya,hakika banida isassun kalmomin da zanyi amfani wajen godiya gareka ,hakika Kai adalin sarki ne Mai kaunar talakawansa Wanda bayaso yaga wani nakasa dashi a cikin mawuyacin Hali nagode da amincewarka na shigowata wanan masarauta" Murmushi kawai Mai martaba yakeyi hakikanin gaskiya ko wani sarki yanaso a kodasa haka yadda Fatima tayi yaji dadin kalamanta da tayisu cikin natsuwa..... Shiko yarima mamakine da al'ajabin kalaman Fatima suka daskarar dashi a wajen,don be taba tunanin ta iya tsara magana hakaba dikda yasan cewa mafi yawancin kalaman yarinyar masu hukima ne..... Hajiya babba kuwa dake gefe jinjina Kai kawai takeyi a ranta Tana fadin yarinya kinyi kuskuren shigowa wanan gida harda wani iyayi takewa sarki bayan bada sarki Zaki zaunaba wata dabara ce ta fadowa hajiya babba da sauri tayi yak'e Wanda hausawa ke cewa yafi kuka ciwo tace"sannunki Fatima barka da zuwa masarautar barayar Zaki" Darammm kirjin Fatima ya bada baki na rawa Fatima ta amsada "yauwa hajiya....nagode da karamci Allah ya saka muku da alheri" Yak'e baki hajiya babba ta karayi tace"ameeen".....dan rankwafawa tayi alamar girmamawa ta kwantar da murya ga Mai martaba tace"ranka ya dade zanso ace rukon Fatima ni zan kasance uwar goyonta a wanan masarauta Mai albarka da nayi matukar farin ciki da hakan" "Da Fatima da Kabir duka mallakinki ne uwar gidan sarki saboda haka ki rike Fatima har muddin Rai"... Mutuwar zaune yarima yayi lallai hajiya babba ta shammacesa,.....zuciyarsa ce kawai ke harbawa maganar Mai martaba ce ta dawo dashi daga sumar wucin gadin da yayi "kabiru nayi magana da Khadija matarka itama ta amince da shawararmu,Kuma nayi matukar farin ciki da kuka kasance ya'ya masu biyayya ka riketa Amana tamkar dama Kaine ka nemi auren nata haka Allah ya kaddara Allah yayi Muku albarka" Cikin dasasshiyar murya yarima yace"ameen"...... Fatima kuwa kalaman hajiya babba na jiya a gareta suke yawo a kwakwalwarta lokacin da taji kalaman da take yiwa Mai martaba....shikenan tafaru takare Mata... Sallamarsu sarki yayi saboda Kiran sallah da akeyi dukkansu suka Mike tsaye suka fito..... Kuyangar data rako deejahma itace ke biye dasu itada hajiya babba da Fatima wadda ke bin bayansu kamar kwai ya fashe Mata a ciki batare da sanin inda zata dosaba a gidan saboda yarima sarki ya tsaidasa suje masallaci fada.... Binsu takeyi har cikin gidan inda suka tarar da gwaggo rahi zaune Tana karkada kafa da sauri ta dago Kai Jin shigowarsu,afnan dake gefen kawar deejahma baby da sukai ido hudu da Fatima.....saida ta firgita Dan daga ita har mahaifiyarsu basusan wainar da ake toyawa ba.... Gefen bango Fatima ta rabe a tsugunne ta tasa Dan akwatinta a gaba ta sunkuyar da Kai.... Kallon Tsana deejahmah ke watsawa Fatima yayinda ta tako cike da Isa da kasaita har gaban Fatima ta tsaya Tana Kare Mata kallo har zuciyarta tasan babu karya Fatima kyakkyawar yarinya ce ajin farko babu mahalukin da zai kalleta ko a kuskurene be juyo ya Kara kallontaba,..wata hassada ce ta tasowa deejahmah tace"kinyi kuskuren shigowa gidan sarauta Fatima kina tare da danasani Domin kin kawo kanki Ramin kura inda take zaune da yayanta fita daga ciki sai kin shirya,kin kawo kanki makabarta inda dakanki Zaki ginawa kanki kabari ki rufe kanki da ranki batare da kin mutuba wallahi summa tallahi saina shayar dake azaba tunda dake aka hada Kai wajen kashemun tsohon mijina,sanan yanzun sabon mijina kike bibiyarsa ke marainiya ko?shine ubanki to kinyi babban kuskure"..... Murmushi hajiya babba tayi ganin irin kallon tsanar da deejahmah ke watsawa Fatima wadda ke tsugunne jikinta na karkarwa,zufa ce ke tsattsafowa a jikinta tamkar an watsa Mata ruwa.... Takowa hajiya babba tayi tazo ta dafa kafadar deejahmah tace"ki kwantar da hankalinki daukar fansa ba naki bane ke kadai ta shigo hannun da bazata taba fitaba,idan anyi mak'isa a kotu an hada baki an wanketa Nan gidan babu Wanda zai wanketa saboda haka ki kwantar da hankalinki" A fusace deejahmah tace "wallahi mama ni ban yarda wannan yarinyar marainiya bace dubeta fa wallahi muna furci ne" Gwaggo rahi zatayi magana kenan yarima ya shigo parlorn Dan Allah Allah yakeyi su idar da sallah ya baro fadar dikda yasan sarki be barinsa sai anyi ishai Amma karya yayi Masa da yanaso ya watsa ruwa baijin dadin jikinsa.... Koda ya karaso parlorn suna tsattsaye akanta kamar wasu sojoji suna ganinsa dukkansu suka watsa Masa wani irin kallo Wanda shi baima San sunayi ba,.....ita dama afnan tunda taga shigowarsu ta ruga tayi bangaren mahaifiyarsu Dan sananr Mata abinda ke faruwa, Karasowa yayi ya sa hannu ya dago Fatima yace"haba bintu ya zakizo Nan ki tsugunna umm?saikace ba Yar gidaba?muje in nuna Miki dakinsu khausar Nan xaki zauna tare dasu" Murmushi Fatima tayi Masa ta dago daradaran idanuwanta ta saukesu Akan fuskarsa tace"kasan bakunta ya Zama Dole ai Amma zan Saba yaayaah kaji"ta kafesa da ido jinjina Kai yayi Yana murmushi tabi bayansa, Dukkansu galala sukai suna kallonsu,deejahmah wadda ta Gama fassara irin kallon da Fatima keyiwa yarima irin kallon masoya ji tayi kamar ta shaketa a haukace ta juyo tace da mamanta"mama kina kallo fa wallahi tallahi shegiyar yarinyar Nan budurwarsa ce ki duba irin kallon da tayi Masa fa" "Ki kwantar da hankalinki yarima mijinki ne ita kuwa saidai ta tsaya a iya kallon Dan wallahi mallakar Kare da hantar kura....harabada bazata cuwu masaba Kinga ko harabada saidai ta ganshi" Nannauyar ajiyar zuciya hajiya babba tayi tace"kuje abinku kubarmun komi a hannuna".... ******** Hawayen bakin ciki kawai mama karama keyi yayinda afnan ke famar kwantar Mata da hankali Dan bakaramim tashin hankali take cikiba.... Shigo da Fatima yayi bangaren mahaifiyarsa bayan sallamarsu Bata ko kalli inda suke ba saboda wani irin takaici da bakin ciki da take ciki haka suka Gama zamansu ya Mata jagora zuwa dakin baccinsu khausar da afnan...... ******* Gidan waziri kuwa wadanda sukaje gaisar da sarki yaran waziri Nan suka kwashe labarin komi suka fadawa iyayensu.....matar waziri dake zaune da kayan saki irin na mutanen da a jikinta tai murmushi ta kalli yan biyunta Yan Mata faizah da fauziyya tace"dik makircin rahina ne Amma idan tasan wata batasan wataba nice naso ace a cikin yaran gidan Nan cikinku wani ya auri daya daga cikin yaran sarki Amma hakan be yuwuba to tabbas sainasa Anyiwa deejahmah kisan mummuke zansa ayi Mata abinda zai nakasata ta kasa batare da tunanin wanine yayi mataba zata kasance da Rai da lafiya Amma saitayi hawaye ta dalilin abinda zanyi Mata" Murmushi fauziyya tayi wadda takasance itace hussaina tace"aikinki Yana kyau innarmu nasan ko kashe mutum ne zakiyi batare da kowa ya Gane kece kikai hakanba mugunta daya Zaki Dana Mata ya zame Mata babban bakin cikin a wanan duniyar" Faizah dake gefe Tana sauraronsu tace "aini innah deejahmah Bata dameniba tausayin Fatima nake Wai Kinga yadda sukayi Mata dazun kuwa harda uwar gidan sarki". Hmmmmm kawai Inna ta sauke gwauron numfashi tace"gaskiya Nima tausayinta nake dikda cewa ban taba tausayin wani mutum ba Dan babu abinda ya shafeni da sabgar kowa sai tawa data yarana zan shirya inje Inga yarinyar" Fauziyya cikin kosawa tace"innah me zakiyiwa anty deejahmah " "Sirrrim zuciyata ne sai abun ya fito Nan da shekara biyu bayan aure zan sanar daku nice sila" Gyadar da take ci a a gabanta ta Dina ta zuba a baki Tana taunawa Tana murmushi...... ******** Bacci ya gagari deejahma har kusan Sha daya na dare sai zazzaga masifa takeyi babu abinda ya tsaya Mata a Rai irin murmushin da yarima yayiwa Fatima.... Gwaggo rahi ta kalleta tayi murmushi tace"deejah banson kika tada hankalinki na keda kikace ba sonshi kikeba da kin Haifa Masa magaji Zaki ramawa habibu hakkin kisansa shine Zaki zauna kina tada hankalinki Akan sa kamar wadda ke kishinsa?alamar kishi fa soyayya ce" "Wallahi mama bana sonshi na tsanesa,sanan hassadar kyawun surar yarinyar kawai nakeyi Kuma wallahi saina kurbawa yarinyar Nan azaba....." "Kyau Mai saukine kinada damar da dazarar kika aureshi zakisa a Bata Mata fuska harabada fuskarta ta lalace" Ajiyar zuciya deejahma ta sauke tace "kin kawo shawara hakan zaayi" Dariya gwaggo rahi tayi tace"yanzun ki kwanta kiyi bacci dasafe zamu tattauna akwai wata Yar tafiya da zamuyi zuwa tudu" Takawa tayi ta Haye gadonta ta kwantar da kanta Akan pillow ta lumshe ido gwaggo rahi ta kashe musu globe ta fice ..... ******* "Khausar Wai menene nake fama dake kije ki kwanta kinki ke sai Nan xaki kwanta" Yatsina fuska khausar tayi hade da turo baki tace"ba Yaya bane yakai wanan yarinyar dakin kwanan mu waidamu zata zauna?" Dafe kirji hajiya babba tayi tace "mene?muje"ta Mike da sauri....sukayi dakin kwanansu khausar... Juye juye kawai Fatima keyi batare da tayi bacciba afnan na can karshen gado ta takure kamar zata hade da bango, "Tashi munafukar Allah ki nemi wajen kwana tun dare beyi mikiba Dan bazan iya barinki ki kwana da yaranaba kafin safiya Kin kashesu" Da sauri Fatima ta duro daga gadon jikinta har rawa yak'e....kofa hajiya ta nuna Mata tace"fita" Da sauri ta Soma tafiya Tana rawar sanyi saboda yadda garin ya dau sanyi kasantuwar lokacin tsagwaron sanyine haka ta fice a dakin idanuwanta cike da kwalla,...Tana tafe kwalla ta silalo Mata a kumatunta tasa hannu ta share, Wani Dan hanya ne dake sadaka da ko wani part din gidan Nan ta shimfida dankwalinta ta kwanta Tana rawar sanyi...... *Muje zuwa* *SLIMZY✍🏼🥰*🌩 *ANYI WALK'IYA.....* 🌩 *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 *NA:SLIMZY✍🏼* _wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* *SAKON GAISUWA DA FATAN ALHERI* *GAREKU SUMAYYA* *ADAM* ( _fauza house of_ _novels_ ) *TARE DA* *MOM SAYEED* *DA* *NOOR* ( _Haske_ _fans club_ ), *UMMU* *RAMLAT* ( _slimzy_ _novels_ )...... *SON* *SO FISABILILLAH* 😍👏🏼 20 Ilahirin jikin Fatima Babu inda baya rawar sanyi saboda hunturun da akeyi a wanan lokacin sanan a tantagaryar kasa take kwance ga sanyin tiles da ya dauka....baccin kansa ya gagareta saboda tsabar sanyin da takeji juyi kawai takeyi kafadunta sunayi Mata zafi gashi ganin Daren takeyi yayi Mata tsayi....cije lebenta tayi saboda tsabar sanyi har saida ya fashe jini ya fara fitowa,runtse idanuwanta tayi wata kwalla Mai zafi Tana gangaro mata a fuska a haka har wahalallen bacci ya dauketa,sai Kiran sallahr asuba ta farka da sauri ta kwashe Dan kwalin data shimfida da hijabinta da take lullube dashi ta say jikinta, Wata Yar kofa ta nufa batare da sanin inda zatajeba Tana shiga taga ta Kara karo da wata kofar a rufe ba tare da wani tunaniba ta tura kofar aikuwa tayi kicibis da wani katafaren bedroom Wanda yasha kayan more rayuwa da rantsatsen gado ta kunna Kai cikin dakin aikuwa furgigit wadda ke kwance a katafaren gadon ta Mike da sauri Tana kallon Fatima sanye da hijabi da sauri ta laluba hannunta zuwa gefen gadonta ta kunna globe ido hudu sukayi Fatima taja da baya da sauri , Wani durowa hajiya babba tayi daga gadon Tana fadin "dawo Nan dama bacci rabi da rabi nakeyi saboda tsoron Kar a kashemu ubanme ya kawoki dakina kinzo ne ki karasani?kamar yadda kika kashemun da'be ishekiba koh" Ko Ina a jikin Fatima rawa yakeyi ji takeyi tamkar ta saki fitsari har ga Allah Koda ta bude kofar batayi tunanin dakin wanan azzalumar matar bane tayi tunanin dakinsu khausar ne don dakunan gidan da kofofin gidan kamanceceniya suke da juna...... Wani mugun kallo hajiya babba ke jifar ta dashi ta Kara fadin "uban me ya kawoki Ina tambayarki?" Dago idanuwanta tayi sukayi ido hudu ta Kara saukesu kasa bakinta na rawa tace"kiyi hakuri wallahi bansan dakinki bane Nan wani dakin nake nema inaso in shiga bayi inyi alwala inyi sallah" "Dakin ubanki kike nema?ko dakin tsohon kwarton naki daya kawo ki kike nema kabiru?kinbiyo duhu kuyi karuwancin ne?to fitarmun a daki tun ban illatakiba cikin Daren nan" Da sauri Fatima ta juya har Tana hardewa kamar zata kife ta fice a dakin,hajiya babba ta bita da wani mugun kallo Mai cike da tsantsar tsana da kyama..... Tana fitowa taci Karo da wata kuyanga hannunta dauke da tsintsiyaye manya da kanana da alama itace Mai sharar gidan kallonta kuyangar tayi ta kauda Kai har zata wuce Fatima ta tsaidata da cewa"Dan Allah Ina zansamu bayi inyi alwala?" Hannu tasa ta nuna Mata wata hanya ba tare da tace komiba ta wuceta da sauri don kar ma wani ya ganta tanayiwa Fatima magana,kofar data nuna Mata ta shiga aikuwa saiga bayika a jere daga gani kasan na bayin dake bangaren ne ,ciki ta shiga ta Kama ruwa tayo alwala ta fito tazo parlor ta tada sallah....bayan ta idar da sallahr ne Tana zaune gari ya danyi Haske yarima ya shigo sanye da jallabiya daga gani masallaci ya dawo Yana shigowa yayi tozali da ita zaune Tana adduoi hannunta a sama juyowa yayi ya taho wajenta ya nemi gefe ya zauna har saida ta shafa, Sunkuyar da Kai tayi gefe tace"barka da tashi ranka ya dade ,fatan ka tashi cikin koshin lafiya" Murmushi yayi yace"na tashi lafiya ranki ya dade Dan kema yanzun kin Zama Yar gidan sarki Dole a ce Miki ranki ya dade" Harararsa tayi ta kauna Kai , Tambaya yarima ya wurgo Mata yace"cikinsu khausar din kika kwana kuwa ko a Ina?" Jimm kadan tayi ta tuno da nasihar Ablah da tayi Mata Akan dik abinda zaayi Mata a gidan kada ta sanar dashi tabari ya gani da idanuwansa,kada ta kasance Mai yawan korafi da kan Kara Akan Yan uwansa don watarana zai gaji da ita.....da sauri tace "Ina zan kwana Wanda ya wuce cikinsu khausar din?a dakinsu na kwana cikin sababbin Yan uwana" Murmushin Jin Dadi yayi yace "Bari in shiga ciki zan kwanta kema ki koma bacci" Yana Gama fadin haka ya Mike ya fuce........ Kallo ta bishi dashi Tana murmushi lokaci daya ta kauda kanta ta tuna da baccin da tayi rabi da rabi a Daren jiya..... ********* "Barka da tashi ranki ya dade uwar gidan Mai martaba sarki" "Barkanki"...hajiya babba tace Tana kokarin sakkowa daga gado "Ranki ya dade nasamo wani labari ne" "Ina sauraronki" Kara durkusawa kuyangar tayi tace"yanzun Nan ja dauko tsintsiya zan shigo bangarenki Domin tsabtace Miki Naga yarima Dan sarki da wanan bakuwar ya zauna a gefenta bansan me suke cewa ba" Kurriii da ido hajiya babba taiwa kuyangar Tata har takarasa abinda take fada sanan tace"naji dadin wanan labarin saade shiyasa nabaki wannan aiki na sawa wanan yarinya da kabiru ido dik motsin da zasuyi inaso kisa musu ido yadda yadda Dace kuma ki fadamun " "Insha allahu uwargijiyata zaayi yadda kikace" "Mike kije kiyi aikinki".... Durkusawa tayi tace "Allah ya taimaki uwar gidan sarki"...sanan ta Mike ta fara kakkabe kakkabe kafin ta fara shara.... ******** Kaiwa da komowa Fatima keyi kawai ta rasa dakin da zata shiga taji Dadi ma rayuwarta Dan batada wajen zuwa,gashi tanaso tayi wanka ta canja kayan dake jikinta saboda kaikayi da takeji, Wani waje can tasamu wani Dan dandamali a hanyar da zata sadaka da bangaren sarki ta zauna Tana kallon dawisu dake Kai komo cikin gidan suna baza jikinsu kwalliyar jikinsu na fitowa saita Samu kanta da shagaltuwa da kallonsu.... Tun daga nesa yake hangenta a hanyarsa ta zuwa gaida Mai martaba, murmushi kawai yakeyi Mata Wanda ita Sam batasan Yana yinsa ba ma har ya karaso inda take kamshin turarensa shi ya sanar Mata da isowarsa, Dago Kai tayi ta sauke idanuwanta cikin nasa lokaci daya ta rufesu ta Kara budewa sanan ta sauke Masa lallausan murmushin Nan nata,....kwarai ya shagaltu da kallonta muryarta ya tsikayo Tana fadin "barka da tashi ranka ya dade" Wata sassanyar ajiyar zuciya yarima ya sauke wadda saida ta fito a zahiri sanan shima ya maida Mata da martanin murmushin"barkanki da tashi ya bakunta?" "Ai yanzun niba bakuwa bace Domin na Zama Yar gida" Gyada kansa yayi yace "haka nakeso bintu zo muje mugaida Mai martaba sai mu dawo Nan bangaren mu gaidasu hajiya" Batayi Masa musu ba ta Mike tabi bayansa..... ******** Zazzaune suke a babban parlor Wanda dabiarsu ce zaman wanan parlor din kowace safiya Domin yin breakfast Wanda dokar Mai martaba ce hakan a cewarsa zasu Kara zumunci,tunda suka zauna Babu Wanda ya cewa wani uffan sai wani girgije girgije hajiya babba takeyi Tana cika Tana batsewa ita ga matar sarki.... Mama karama ce ta Dan kalleta ganin yanayin nata sai ta danyi murmushi tace"ni Kam hajiya wanna hukuncin da kika dauka akaina da yarana yayi tsauri a tunanina kome kabiru yayi Miki laifinsa bazai shafeniba saboda danki ne kinada damar yi Masa hukuncin daya Dace batare da hakan ya shafi zaman takewarmu ta yau da kullum ba" Wani kallo hajiya babba ta watsawa mama karama kafin ta bude baki tace "ai Dole kice hakan tunda kina gudun duniya ta zageki ba ?bayan dik abinda kabir yayimun na kuntatawa dik Dasa hannunki" "Dan kuka kenan Mai jawa uwarsa zunguri inda Kabir yaji maganata da bai aiwatar da abinda ya aiwatar ba hajiya har gargadi nayi masa bejiba musamman Akan dauko wanan yarinyar da baasan asalintaba ya kawota cikinmu " Tabe baki hajiya babba tayi tace"wanan keta shafa ni yanzun hukuncin Dana dauka shine tunda Mai martaba yabani ita to cikin kuyangina zan jefata Dole tasa uniform" Da sauri afnan ta kalli hajiya babba lokaci daya ta kauda kanta gefe batare da tace uffan ba.... Mama karamace ta sauke ajiyar zuciya ta bude baki zatayi magana shigowarsu yarima tasa ta hadiye maganarta dukkansu suka bisu da kallo Dan yadda suka jero suka shigo daka kallesu zakaga tamkar Miji da Mata ko saurayi da budurwa ko wanne fuskarsa dauke da murmushi.... Har kasa dukkansu suka zube a gabansu yarima ne ya fara magana "barkanku da tashi iyayena,fatan Kun tashi cikin koshin lafiya?" Babu Wanda ya tanka daga hajiya babba har mama karama,.....dago idanuwansa yayi ya sauke Akan mahaifiyarsa dake jifansa da wani irin kallo Mai dauke da maanoni kala kala, Itako hajiya babba kallon Tsana take jifansu dashi ji takeyi tamkar ta shakesu Dan wallahi ganinsu da tayi a haka saida gabanta ya fadi sanan Saida safiyar Nan ya Kara ganin tsantsar kyawun yarinyar.... Sunkuyar da Kai Fatima tayi gabanta ya tsananta faduwa cike da fargaba tace"Allah ya taimakeku,barkanku da tashi iyayen giji na" "To hanshakiya kinada bakin gaishemu saboda bakida kunya?Dan cikin gida Dan asali Wanda kowa yasan tsarkakakke ne Dan sunna ya gaishemu bamu amsaba saike kazanta uwar iyayi Zaki bude wanan shegen bakin naki Mai wari ki gaishemu saboda tsabar iyayi irin na yaran bariki?"to ku rike gaisuwarku Miji da Mata wato da sassafe kazo ka dauketa kukaje gaida sarki tunda ubanta ne ko?" Durkusar da Kai kawai yarima yayi ransa nayi Masa suya bashida yadda zaiyi Akan Fatima yasan Dole wadanan abubuwan su faru Amma alkawari ya daukarwa kansa kome zaayi Mata bazaisa baki ba bazai shigar mataba Domin hakan shine cikar burinsa...ba karamin zafi kalaman hajiya babba sukaiwa Fatima ba,wanan cin zarafi har Ina daga zuwanta?tun baaje ko Ina ba? Harara hajiya babba tabi Fatima dashi sanan tace "ke ga Yar gida ko harda tashi da sassafe ya daukeki ya kaiwa sarki ke neman suna ko?to Bari kiji infada Miki yaranmu sune yara a cikin gidan Nan dik Wanda ya shigo daga baya to bare ne Dan haka Ina Kara gargadinki da ki Kama kanki idan ba hakaba wallahi saina halakaki" Da sauri yarima ya kalli hajiya babba sukai Ido hudu "ko dukana zakayi na taba zuciyarka?wani shin kabiru yarinyar Nan asiri tayi maka ko?idan ba hakaba to menene Koko son zuciyane yasa kuka hada baki ta kashe maka Dan uwa Wanda kake ikirarin kana sonsa fiye da kowa a duniya?sai gashi ka nunawa duniya cewa ba son gaskiya bane tunda ka dauko wanan kajagar da tayi silar Kai Dan uwanka lahira cikinmu?to kasani ka fada Mata,idan akayi aurenka da deejahmah babukai babu ita Dan bazata illata Mana Suruka ba" Dik bala'in Nan da hajiya babba ke zazzagawa Babu Wanda yace uffan daga yarima har mahaifiyarsa,...sauraronta kawai sukeyi yadda take shiga batanan take fitaba.....zuciyar yarima tamkar ta Kama da wuta haka yakeji itakuwa Fatima dake durkushe a kasa hawayene ke diga a kasa wadanda ke gangarowa daga idanuwanta suna sauka Akan carpet din.... Mama karama ko haushin yarima kawai takeji Domin dik cin zarafin da hajiya babba tayi vataga laifintaba sai nashi Domin shi yajanyo komi da kyar ta ta daga kanta ta kalli inda Fatima ke durkushe kanta a kasa want haushi da takaicin yarinyar ya Kara lullubeta dik itace silar wargajewar gidan tace"tashi ki fita zamu karya da yaranmu" Kallon mahaifiyarsa yarima yayi Aiko ta wurga masa harara ya sadda kansa kasa,.... Mikewa Fatima tayi ta juya Tana tafiya hawaye ya gama wanke Mata idanuwa tabar parlorn..... Kallo ya bita dashi tamkar ya tashi ya bita yakeji zuciyarsa babu Dadi bashida yadda zaiyi wanan karon ba yakin wulakantata da zaayi zaiyiba yakin cikar burinsa Domin Fatima itace farin cikin rayuwarsa.....ko Fatima batai farin ciki yanzunba akwai lokacinda farin ciki dawamamme zaizo musu dagashi har ita....dikda har yanzun bai sanar Mata da kudurinsa na boye ba.... Abincin karyawa aka shiga shigowa dashi parlorn Mai Rai da lafiya aka shiga direwa a gabansu har aka Gama ,lantana itace ke serving din kowa a wajen....Koda tazo kansa tambayar Mai zaici ruwan zafi kawai ya Bata umarnin ta sa mishi....da sauri sauri ya kukkurba ya Mike ya fice.... ******* Nemanta yakeyi tunda ya fito zuciyarsa ke harbawa sauri da sauri Allah yasa Fatima ba gudu tayi ba lungu da sako na gidan babu inda bebi ba harya cira Rai da ganinta ya hangeta jikin wata bishiyar guava a durkushe kanta cikin gwiwoyinta,tun daga nesa yasan aikin kuka takeyi haka Nan ya tako jiki a sanyaye har wajen motsin tafiya ya Sanya ta dago kanta da sauri Tana ganinsa tasa hannu ta share hawayenta da sauri ta kirkiro murmushi.... A gabanta ya tsugunna Yana kallon kyakkyawar fuskarta da tayi jajir saboda kuka,...durkusar da kanta tayi kasa Tana murmushi.... Hannunsa yasa ya dago fuskarta Yana kallonta cike da tausayawa yasa hannu Yana share sauran hawayen dake gefen idonta ba tare da yabar kallon fuskata ba,runtse idanuwanta tayi tanajin wani bakon lamari a tattare da ita Wanda kallon da yakeyi Mata ne ya haifar da hakan sun kusa minti goma a haka harta fidda Rai zaice wani Abu saita tsinkayo muryarsa Yana magana cikin taushi da kasala, "Bintu Ina nemawa iyayena gafara a wajenki na cin zarafinki da sukayi Wanda hakan Sam bai daceba banji dadiba da inada Halin hanasu Danayi hakan saboda in nuna Miki babban muhimmanci da matsayin da kike dashi a rayuwata" Murmushi tayi sanan ta Dora idanuwanta cikin nasa Tana Masa wani kallo Wanda ita kanta batasan tanayinsa ba dakyar ta iya sauke ajiyar zuciya tace"dik muhimmancin Fatima a gareka baikai ga iyayen da suka kawoka duniyaba,iyaye daban suke a rayuwar ya'yayensu kome sukayi maka Dole ka daure kayi musu biyayya,saboda haka ka kwantar da hankalinka Babu abinda ya batamun Rai ciki don dik abinda suka fada akaina gaskiya ne sanan harabada sune iyayena da Allah ya bani koma menene watarana zai Zama tarihi yaayah saboda haka Ina rokonka Dan Allah kada kasamu sabani da iyayenka akaina"..... Shima kallonta yakeyi kamar yadda take kallonsa ya shagala da kallon yadda black lips dinta kanana ke motsawa Tana furta wadanan kalaman Wanda yasan dauriyace da tawakkali da karfin zuciya irin nata Babu Wanda zaaiyiwa wanan cin zarafin da wulakanci beji zafi da radadi a ransa ba Amma ita Sam ta nuna masa Babu komi....yayi nisa cikin tunani Yana kallonta besan harta karasa kalamantaba ....kallonta kawai yakeyi idanuwansa sun canja kala sun kankance,...hura Masa iska tayi a ido ya lumshe idanuwansa sanan yayi murmushi yace cikin dasasshiyar murya "Allah yayi Miki albarka Yar aljannah Allah kadai yasan tarin baiwar dake tattare dake bintu..." Murmushi tayi Masa sanan tadan tura baki tace"banason zugafa yaayaah"... Yatsansa yasa ya Dan bugi lips dinta yace "shagwabatu....komi sai kinyi shagwaba ni yanzun ki tashi kije kiyi wanka ki canja kayanki cikin wadanda kikazo dasu zan fita yanzun daganan zan suyo Miki sababbin Kaya da dik wani Abu da kike bukata" Kifta mishi ido tayi tai Farr da idanuwanta sanan ta Mike tace"Allah ya tsare ya kareka yaayaah saika dawo"...Tana karasa fadin haka ta juya abinta batare da jiran me xaice ba,kallo yabi bayanta dashi Yana murmushi hade da sauke sassanyar ajiyar zuciya....dakyar ya iya mikewa ya Kama hanyar parking space.... ******* Gidan Ahmad abokinsa yarima ya je ya daukesa suka fita yawo dagacan Basu dire kobinaba sai boutique Nan suka shiga yarima ya shigo jidan Kaya babuji Babu gani dik abinda ya daga sai ya siyawa Fatima shi musamman danginsu dogayen riguna ready made masu shegen kyau da tsada sanan ya shiga danginsu atamfofi ya jidar Mata Suma shidai Ahmad kallonsa yake kawai Yana mamakin yadda yaga yarima na kashewa Fatima kudi kamar hauka dikda dama yarima akwai kyauta, Bill akayi musu ya biya sanan da suka fito yarima ya roki Ahmad da su biya gidan barrister Abdul can zai bada wadanda zaa dunka Mata sukaiwa tela ba musu ya bisu..... ***** Matar waziri ce zaune a gaban hajiya babba Tana kawo gaisuwa bayan ta shiga ta sun gaisa da mahaifiyar yarima, "Ranki ya dade naji labarin abun farin ciki na shawarar da aka yanke na hada deejahma da kabiru gaskiya nayi farin ciki da hakan Allah ya Sanya alheri".. Washe baki hajiya babba tayi tace"ameen labari yakai Miki kenan" "Ehh kin Manta jiya su fauziyya sunzo Nan da suka koma ne suka sanarmun yaushene bikin?"...ta kalli hajiya babba a fakaice taga yanayin fuskarta, Murmushi hajiya babba tayi tace"yadda dai bikin yake tun farko baa canjaba Kinga Nan da Yan watanni kenan"....jinjina Kai matar waziri tayi har zuciyarta taji dadin wanan bayanin dama shine muhimmin abinda yakawota don ta shirya, "Allah ya nuna Mana wanan babban bidiri da shagali da zaayi a wanan masarauta bikin Dan sarki" "Aikuwa dai"... Waigawa matar waziri tayi tai tozali da wasu jajayen Kaya da ke gefen hajiya babba irin uniform din da kuyangi ke sawa tadan gyara Zama tace"ranki ya dade ankaro kuyanga ne Naga sabon uniform irin nasu" "Kinga na mance ma wallahi wadda zankira aba tasa nakeso in fada Mata aikinta" Murmushi matar waziri tayi Tana Yan dube dube don abinda ya kawota Taji daya saura daya ta bude baki zatayi magana kenan hajiya babba ta kwalawa saade Kira da sauri ta shigo ta zube a kasa kamar Tana jira tace"gani ranki ya dade" "Kiramun Fatima" Mikewa saade tayi da sauri ta tafi neman Fatima, Tana tsaye jikin wata Yar baranda kusa da toilets din maaikatan gidan a Nan ta sa kaya Tana tsaye ta yane kanta da wani Dan gyale Tana sanye da doguwar rigar material ja tayi matukar karbar fatar jikinta, Dafe habarta saade tayi Tana jijjiga Kai Tana kallon Fatima ta tabe baki tace"kizo hajiya nayi Miki Kiran gaggawa" Saida kirjinta ya buga Jin abinda saade tace,Bata tsaya neman hijabi ta ba tabi bayan saade jikinta na rawa faduwar gaba ta tsananta, A tare suka shigo dakin daga hajiya babba har matar waziri sakin baki sukai suna kallon Fatima da suturar dake jikinta ga wani annuri na kyau na fita a fuskarta durkusawa tayi har kasa tace"gani ranki ya dade" Jijjiga Kai hajiya babba tayi Tana karewa Fatima kallo tace "ehh lallai kin nuna Mana ainihin ke wacece marainiyar Allah itace sanye da tsadaddun Kaya na alfarma shiyasa ko kurani kabiru zai hadiya bazan yarda da cewa ke tsintacciyar mage bace,hakkinmu ne yasama aka tsundumo dake gidan Nan kika kawo kanki da kanki"....kayan dake gefenta ta watsawa Fatima ta cigaba da cewa "bakizo Nan gidan Dan ki zauna kiyi kwalliya ki saki jiki kiyi Mana karuwanciba bakida sutura a cikin gidan Nan data wuce wanan ta kuyangi daga yau kin tashi daga Fatima kin koma kuyanga"... Da sauri Fatima ta dago Kai saboda kalmar dataji hajiya babba ta fada sai tayi maza ta sadda kanta kasa, Hajiya babba ta bude baki zatayi magana taga bayi na shigowa da Kaya leda leda, sanan sallamar Ahmad da yarima ya dakatar da ita daga maganar da take shirinyi, Karasowa sukayi suka tsugunna suka hada baki wajen gaishesu itada matar waziri wadda ke faman raba idanuwa, Shiko yarima satar kallon Fatima yakeyi don bakaramin kyau tayi masaba idanuwansa yakai hannunta da ke rike da wasu jajayen Kaya irin na kuyangi kanta a kasa batamasan yanayi ba... "Mike kije ki canja wadanan kayan na jikinki kisa wadanda suka Dace da matsayinki kizo infada Miki aikinki"... Mikewa tayi jiki a sanyaye Tana tafiya dakyar take daga kafarta tabar parlorn... Kallon hajiya babba yarima yayi Yana neman Karin bayani... Murmushin mugunta tayi Masa sanan tace "daga yau Fatima ta koma kuyanga"...... Wani irin shock ne ya ziyarci ilajirin jikin yarima dake tsugunne baisan lokacin da ya zauna dirshan ba .... *Muje zuwa* *SLIMZY✍🏼🥰*🌩 *ANYI WALK'IYA.....* 🌩 *HASKE WRITERS* *ASSOCIATION* 💡 *NA:SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an* *maliki* *Tunda akayi walk'iya halin kowa ya bayyana na tabbatar Haske ya cancanci yabo wato Raina kama ne su kaga gayya....Tarayya sukai wurin ganin Tafaru takuma k'arewa me musu kallon raini* 21 Dafe kansa yayi Yana girgizawa wani irin bala'i ne wanan?yama zaayi ace Fatima ta fada cikin kuyangi?......girgiza Kai kawai yakeyi sallamar da tayi ce ta dawo dashi daga duniyar tunanin daya fada cikin seconds da sauri ya dago Kai ya kalleta karaf idanuwansu suka hadu waje daya wani shock ne ya tsargo Masa daga kwakwalwarsa har tafin kafarta kallonta kawai yakeyi cikin kayan kuyangi wadanda uniform dinsu ya kasance Jaja ye bayi Kuma koraye suke amfani dashi..... Har kasa ta tsugunna a gaban hajiya babba ta sunkuyar da kanta cikin sassanyar murya tace "gani ranki ya dade" Murmushin mugunta hajiya babba tayi tace "daga yanzun kin Zama kuyanga,Zaki Zama cikin jerin maaikatan gidan nan kin Gane ko?nayi Miki Mai sauki da ban jefaki cikin bayi ba yadda zan iya sawa a sokeki kibar duniyar gaba daya Amma hakan shi yafi cancanta dake Domin sai kin gwammace kida da karatu yanzun ki tashi kije ki nemi saade ta kaiki dakin tsohuwar ajiya ki gyarashi tsab kafin lokacin shiga kitchen ki shiga cikin maaikatan girki,sanan zan sa Miki masu tsaro yadda bazaki faki Ido kisa Mana guba a abinciba ki kashemu" Dan durkusawa Fatima ta karayi tace "to ranki ya dade" "Zaki iya tafiya ki nemi saade Dan aiwatar da abinda nasaki" "To ranki ya dade"....mikewa tayi jiki a sanyaye tabar parlorn matar waziri kallo tabi bayan Fatima dashi Tana jinjina Kai.... Dik jikin yarima a sanyaye yake bashida iko ko da ja da umarnin hajiya babba haka ya Mike Ahmad shima ya Mike har sun wuce ya dawo zai dauki kayan da ya siya Mata ya Kai hannu zai dauke yaji muryar hajiya babba na fadin "Ina kuma zakaje da kayan?ai wadanan Kaya bai Dace ka daukaba ka ajiyesu zan aikawa deejahmah" Da sauri ya dago Kai ya kalleta kallon data wurga Masa yasa ya juya ya fice a cikin gidan direct Ahmad ya samu a cikin mota.... Iska ya huro Mai zafi a bakinsa sanan ya dago rinannun idanuwansa ya saukesu Akan Ahmad bashida wani kuzari ya bude baki yace wani Abu ji yakeyi idan har ya bude bakinsa to tabbas zai iya fashewa da kuka.... Girgiza Kai Ahmad yayi ya dafa kafadar yarima yace "cool down gwarzon namiji bai kamata wanan Dan abun ya tada maka da hankali ba" Cikin dasasshiyar murya yarima ya bude baki yace "wanan ba karamin Abu bane friend marainiyar Allah na dauko na kawo sanan a jefata cikin kuyangi?kace wanan Dan abun?" "Da kayi shawara Dani tun farko da baka daukotaba Amma hakan yanada faidah,Domin yin hakan shine zaisa kasamu cikar burinka,sanan Kai kanka kasan Babu yadda zaayi ka dauko Fatima ka kawo batasha wanan wahalar ba friend Dole kaji kaki ji kagani kaki gani,...sanan inaso inyi maka wata tambaya" Kallonsa kawai yarima yayi ya gyada Masa Kai batare da yace uffan ba,Ahmad ya cigaba da magana "Ina fatan ka sanarwa da yarinyar Nan kudurinnka na sonta da kakeyi Dan ko baa fadaba dik Mai hankali yasan soyayya kukeyi" Ajiyar zuciya yarima ya sauke sanan yasa hannu ya share zufar da yakeyi dikda sanyin AC dake cikin motar "ban fada Mata ba" Girgiza Kai Ahmad yayi sanan yace "kayi babban kuskure,abinda ya kamata kayi yanzun Dan ka share Mata hawaye dik wahalar da zaasata da gallazawar da zaayi Mata zaisa ta samu sauki shine ka rikide mata ka rinka samun lokacinda zaka kebe da ita kana nuna Mata tsantsar soyayya da kulawa hade da kauna to tabbas zata shaku dakai Kuma zata saki jikinta damuwa bazatayi Mata yawa ba" "Haka ne friend zanyi hakan"... "Good.....sanan Abu na gaba kafin ka auri deejahmah to ya Zama Dole ka fadawa Mai martaba kudurinnka na auren Fatima" Da sauri yarima ya kalli Ahmad Ido waje yace "noo no friend ba yanzunba" "Abin nufi a Nan gara ka fara shiryawa yakin da zaka fuskanta tun yanzun kafin lokacin da yakin zai gagareka" Jinjina Kai yarima yayi kalaman Ahmad na neman juya Masa da kwakwalwa dakyar ya hadiye wani mugun miyau yace "friend Anya hakan zai yuwu?" Kallonsa Ahmad yayi Yana murmushi yace "ka kwantar da hankalinka ka natsu zamuyi maganar " Daga Masa Kai yarima yayi sanan yasa hannu ya dafe kansa dake Sara Masa kamar zai rabe biyu Ahmad yaja motar suka fice.... ******** "Bilkisu Niko ko wani Hali Fatima ke ciki oho?ko a raye ko a mace mudai tun bayan tafiyarsu hajiya bamu karajin duriyar komi ba ko wajensu uwaliya Mai kitchen"...Maryam ta karashe maganar cike da damuwa Gyara Zama bilkisu tayi tace "Fatima tazo kece dai baki gantaba Kuma Tana cikin koshin lafiya damuwace daya nake ciki Ina yawan mafarke mafarke akanta Allah yasadai Tana cikin Jin Dadi" "Ameeen Amma ni ai na cire Rai da Kara ganin Fatima Kuma saidai a darussalam" Hmmmmm"Maryam kenan bazan taba cire Rai da ganin fatimaba sai ranan da nadaina numfashi a wanan duniyar,nafi kowa tsananin kewar Yar uwata da Dadi babu Dadi muna tare Fatima mutum ce Mai hakuri ko a zamanmu muke cutar da ita muyita Mata abubuwa daban daban sai gashi lokaci kankani Allah ya tsameta a cikinmu"....wasu zafafan hawayene suka shiga gangarowa a kuncin bilkisu tasa hannu ta share sanan ta kifa kanta a tsakiyar kafafunta Tana kuka Mara sauti ... ****** Wani daki Mai duhun gaske can cikin gidan aka Kai Fatima da tsintsiya da tsumma na goge goge dakine da ya Sha kura da bola Wanda dik Wanda yayi tozali da dakin sai kayi tunanin yayi shekara sama da goma baa shareshiba an wanke, Kayan gargajiya ne irin na sarauta a ciki cike ga uban girma da dakin yakeda shi kallonsa Fatima kawai takeyi kanta na juyawa Domin batasan ta inda zata fara gyara wanan daki dake hargitse da karikitai na ajiya na tarihi ba.... Tari ne ya sarketa a tsaye saboda tsananin kurar dake ciki kalle kalle takeyi da kyat ta hangi wani Dan karamin window can sama a makale.... Takowa tayi a hankali ta iso wajen waige waige ta shigayi Domin tsawonta bazai Kai ba idonta ya hango Mata wani katon tum tum Wanda ya wanci gidan sarauta akafi amfani dashi ganin yanada tudu yasa Bata damu da kurar dake jikinsa ba tasa hannu ta kinkimeshi zuwa jikin windown ta taka dik da haka hannunta bai kaiba dage tayi tasa hannunta dakyar ya karasa taja sakatar windon aikuwa garin ja da karfi ya yanki hannunta azabar data ratsata ce yasa ta mance da abinda ta taka garin saurin sakin sakatar kafarta ta zame ta fado kummm ta buga kanta a jikin bangon wajen na siminti Mai karfi irin na da..... Yar Kara ta saki ta dafe kanta da hannunta biyu biyu kanta na juyawa jini na gangarowa ta hannunta zuwa fuskarta......hawayen azaba Suka shiga zurarowa a idanunta ta Dade a haka wajen minti biyar sanan ta Kai dubanta ga hannunta da tayi mugun yanka jini na tsurtuwa....mikewa tsaye tayi da sauri Tana waige waige hankalinta a matukar tashe Tana neman yadda zatayi da jinin hannunta.... Rigarta Yar doguwace har kasa tasa hannu ta yaga ta shiga kici kicin daure hannun Wanda jini ke zuba dik ya Bata Mata gaban rigarta haka ta daure batare da jinin ya tsayaba. Kuka sosai takeyi ganin yadda jini ke tsurtuwa a yatsanta hankalinta a matukar tashe ta kalli dakin da zata gyara har tayi abinci hannu takai n tsintsiyar ta dauka ta shiga shara babuji Babu gani ga kura data turnike ko Ina a cikin dakin harta kayan jikinta Saida yayi butu butu tayi nisa da sharar ne Taji motsin kamar Ana tahowa da sauri ta dago kanta ta kalli hanyar kofa saade ce kuyanga a tsaye Tana jijjiga Kai irin na muna fuka tace"sannu shafaffiya da Mai wato tun da ranki ya dade tasaki aiki bakiyiba kenan zamanki kikayi ko to hajiya na bukatar ganinki" Tana Gama fadin haka ta juya da sauri har Tana tuntube,....sakin tsintsiyar Fatima tayi ta Dora hannu akai ta ce a Fili "na shiga uku"...Nan da Nan hankalinta ya tashi hantar cikinta dik ta kada.... "Allah baki yawan Rai aikin da kikasa Fatima batayi shi ba" Da sauri hajiya babba ta dago Kai daga kishingidar da tayi ta lumshe idanuwa...."uban me to ta tsayayi" Saade ta bude baki zatayi magana kenan shigowar Fatima ta hadiye zancenta dukkansu kallonta suke yadda tayi biji biji da kura ga rigarta dik jini... Durkusawa tayi har kasa tai kasa da kanta tace "gani ranki ya dade" "Munafuncin ubanme kika tsaya yi bakiyi aikin Dana sanyaki ba?jinin uban meye a rigarki?wani kika kashe Mana a cikin gida" Da sauri Fatima ta girgiza Kai baki na rawa tace "yankewa nayi da..." "Da uban me kika yanke?da makami kikazo Mana gida dama ?makaryaciyar banza da wofi"...hajiya babba tasa kafa ta hambare Fatima a cikita fadi kasa warwas wani irin azaba Taji tamkar zaa dauki ranta yadda taji shigar hambarin.... Mikewa hajiya babba tayi tayo kanta da duka "tashi makira zakimun sharri daga Nasa kafa na tureki Zaki Fadi a kasa salon ace zan kasheki?to aniyarki ta biki" Mikewa Fatima tayi da kyar ta Kara durkusawa numfashinta na sauka cikinta da kyar ji takeyi tamkar numfashinta zai dauke.... "To Bari kiji badai nasaki aiki kinje kinyi shashancinki kinkiyi ba to Ina Mai tabbatar Miki da a cikin wanan dakin Zaki kwana yau kina aiki ki tabbatar kafin gari ya waye kin aikace dakin Nan idan ba hakaba na lahira sai tafiki Jin Dadi" Dakyar Fatima ta bude baki cikin sarkakkiyar murya a wahale tace "to ranki ya dade" "Tashi ki bacemun daga gani kije kisamu su lantana da Mami a kitchen ki Dora Mana abinci Kuma wallahi kika kuskura kikai gigin kashemu wallahi sai an kasheki" Kwallace ta ciko cikin idanuwanta ta taune lebenta da kyar tace "to ranki ya dade" "Bace mun daga gani mujiya".... Mikewa Fatima tayi jiri ya nemi daukarta dakyar ta take kafarta ta saita kanta ta cigaba da tafiya Tana takawa dakyar take sauke numfashi idanuwanta a lumshe take laluben hanya..... Kitchen ta shiga ta tarar da lantana da Mami sunata shirye shiryen girki da kyar ta karaso cikin kitchen din tasa hannu ta dafe bango dukansu kallo suka bita dashi Mami ta dauke kanta,ta cigaba da aikinta Tana tabe baki.....kallon tausayi lantana kewa Fatima Harga Allah Tana kaunar yarinyar tun ranan data fara ganinta Amma hajiya ta tarasu tayi musu gargadi da babbar murya..... Karasowa tayi tace "mezanyi muku?" Harara Mami ta wurga Mata sanan tace "taruugu Zaki gyara Mana kiyi Nika ki hada miyar burabusko" Kallon hannunta Fatima tayi sanan ta dago Kai tace "na yanke a hannuna kutaimakamun ku canjamun wani aiki" "Lallaima wanan yarinyar wato Dadi kikazoji kenan a gidan sarauta ko?muba mutane bane da muke tikar aiki Kuma bamuda ciwo a hannu saike Yar lelen Dan sarki to Dole kiyi idan ba hakaba in hadaki da hajiya" Murmushin takaici Fatima tayi tace"ba sai yakai Nan ba zam gyara" Hakanan Fatima ta warware daurin da taiwa hannunta ta wanke hannun ta tsomashi cikin kayan Miya tafara gyarawa dikda azabar dake ratsa ilahirin jikinta bai hanata gyaran kayan miyan Nan ba tass sanan ta nukashi suka cigaba da aiki tare.... ********* Sai wajen karfe uku na Rana yarima ya dawo gidan a gajiye ga uwar yunwa da yakeji bai zarce ko inaba sai dakin mahaifiyarsa Nan ya yada zango lokacin Tana zaune ita kadai a daki.... "Barka da Rana ranki ya dade"... Kallonsa tayi ta gefe Tana lura da yadda Dan nata ya rame yayi baki daka ganshi kasan Yana cikin damuwa Dan sakin fuska tayi ta amsa Masa a takaice Gyara Zama yayi ya Dan Bata fuska yace "inajin yunwa mama " "Ai abinci ya sauka kasa su kawo maka Mana?" Kararrawa ya Danna a dakin....ko cikakken minti biyu baayiba Mami ta shigo ta zube a kasa Tana kwasar gaisuwa batare da ya amsa mataba yace "Ina bukatar abinci"....da sauri ta Mike ta fice... Itada Fatima suka shigo a tare dauke da kulolin abinci kala kala tunda suka shigo idanuwansa suka sauka Akan Fatima wadda ko kallonsa batayiba ta dire kulolin ta fita yabi bayanta da kallo sanan ta dawo dauke da sauran plates da abubuwan bukata ta ajiye...idanuwansa kirrr akanta musamman jinin da ya gani a jikinta Wanda bakaramin tashin hankali ya shigaba, Itace tayi serving dinsa komi da komi sanan ta fice....kallo ya bita dashi sanan ya maida dubansa ga abincin da ta zuba Masa a gabansa.....ji yayi gabaki daya abincin ya fita akansa ko ganinsa bayayi da kyar yayi cokali biyu na burabusko ya ajiye ya fice batare da yayiwa mahaifiyarsa sallama ba..... ********* Kaiwa da komowa yakeyi a dakinsa Yana tunanin yadda zaayi ya ganta ya tambayeta meke damunta yaga jini a jikinta, Dabarace ta fado Masa ya leko bangarensa Yana waige waige wata baiwa dake sashensa ya hanga ya ya fitota da hannu da sauri ta zo ta zube a kasa "kiramun Fatima"... "Toh"....da sauri ta juya har ta fita ya kirata "saude" Ta dawo da sauri "banaso kowa yaga lokacinda Zaki kirata"....."insha Allah ranka ya dade"... Juyawa yayi ya shige abinsa ita Kuma ta tafi Kiran Fatima.... Tadan Jima Tana nemanta Bata gantaba harta juyo zata dawo ta koma,....dakin kwanan kuyangin gidan ta shiga da sallamarta aikuwa ta hangi Fatima can gefe ta shimfida dankwalinta a Kai Tana sallah Tana zaune Tana addua saudatu ta shiga ,gefe ta nema ta tsaya Tana waige waige har Fatima ta shafa "Fatima kizo inji yarima Dan sarki Mai jiran gado sanan baya bukatar kowa yasan da zuwanki bangarensa" Dammmm kirjin Fatima ya buga jikinta ya hau rawa,....saude juyawa tayi abinta da sauri hakanan Fatima tabi bayanta don batasan bangarensa ba.... Waige waige suke kamar marasa gaskiya har suka Isa... Kwankwasa kofar saude tayi daga ciki ya amsa da "waye" "Nice saude ranka ya dade tafe nake da Fatima" "Ta shigo".....gaban Fatima ya tsananta faduwa haka ta Murda kofar shiga dakin tayi sallama....Yana zaune a kujera gabansa Dan karamin table ne sai TV dake manne a dakin dake faman aiki... Kamar wacce kwai ya fashewa a ciki haka ta shigo parlorn ta tsugunna a Dan nesa dashi.... Kallonta yakeyi tausayinta da wata iriyar soyayyarta na ratsa dik wata kaba ta jikinsa, "Bintu"...maimakon ta amsa sai ta dago Kai suka hada ido kallon dataga yanayi Mata shi yasa Tai saurin sadda kanta kasa....murmushi takeyi Wanda shi kansa dake kallonta yasan karfin Hali take.... "Tasonan kusa Dani"....batayi mishi musuba ta Mike ta tako har inda yake ta tsugunna...idonsa na kanta haka ya zamo kasa gab da ita Yana kallon kyakkyawar fuskarta, "Bintu ko kowa ya gujeki bazan gujekiba ko kowa ya kyamaceki harabada bazan kyamaceki ba Allah shine gatanki ni zan zame Miki gata kinji?" Gyada Kai tayi Tana wasa da yatsunta,...hannunsa yakai hannunta ya rike ya dagosa Yana kallon zara zaran yatsunta ga yanka alamar ciwo a babban yatsanta...."bintu badai ciwo kikaji ba" Narai narai tayi da idanuwanta tamkar zatayi kuka ta kallesa cikin Ido tace "yankewa nayi yaayaah"hawaye ya sauko a kumatunta...."nooo banason kukanki yi hakuri kinji Yana Miki zafi ne umm?" Dan turo baki tayi tace "ehh Mana har kuka dazun nayi"tace cike da shagwaba....hannun yakai bakinta ya shiga hura ma ciwon iska a hankali kusan minti biyu sanan ya dago Kai yace "yadaina" Juya idanuwanta tayi sanan tace "ehh Mana ai ka hura mun,yadan daina ni sakar mun hannuna" Kara murza yatsunta yayi yace "ban saki saikince sun daina" "Ni wallahi zafi sukemun ka Bari yaayah😩" Wani irin Abu yakeji a jikinsa na yi Masa yawo ji yakeyi tamkar su kasance a hanka...dakyar ya saki hannunta ya Mike ya bude Dan ward drob dinda ke parlon ya Ciro wasu chocolate a hannunsa ya dawo gabanta ya tsugunna da kansa ya bare sanan ya kalleta ya kashe Mata ido "bude bakin' Kifta Masa Ido tayi sanan Babu musu ta bude ya saka Mata chocolate din "oya tauna".... Yadda take motsa bakinta Tana tsotsan chocolate din bakaramin Burgesa tayiba ya shagala da kallonta tamkar zai hadiyeta harta shanye ta kallesa taga idonsa na kanta ko kiftawa batayi "nidai kabar kallona" "Idan ban kallekiba wa zan kalla umm?baki hanani kallon matana".... Batare da tace komiba Dan bawai ta fahimci mgnrsa bane ta Mike da sauri data tuna da inda take Dan Harga Allah ta mance da komi "yaayah zantafi idan hajiya tasan nazonan na shiga uku" A kasalance ya Mike ya tsaya daf da ita Yana iya Jin saukar numfashinta yasa hannunsa ya dago fuskarta Yana kallo idanuwansa sun canja launi zuwa jajir saboda yadda yakeji a dik lokacinda yake tare da ita musamman da suka kebe yau, Dayan hannunsa yasa ya shafo fuskarta har lips dinsa da sauri ta juya zata wuce ya damkota ta Fado jikinsa ya riketa tsammmm. Kiciniyar kwacewa ta shigayi muryarta na rawa tace "ka sakeni Dan Allah yaayah wallahi inajin tsoron hajiya"ta karashe mgnr muryarta na rawa... Matseta yayi yace"Ina sonki fatima,banida farin cikin da ya wuce kasancewa tare dake wasu lokuta idan na zauna babu abinda nake tunawa sai rayuwarmu ta baya a gidan marayu.....yau gashi muna waje daya Amma inkasance tare dake Saida dabara....nikadai nasan abinda nakeji game dake" Kalamansa sun matukar sanyaya Mata jiki da kyar ta iya ture hannunsa ta fice da sauri.... Waige waige takeyi Tana duba hanya ko akwai Wanda ya ganta sauri sauri takeyi harda tuntube sukai kicibis da saade "daga Ina kike munafuka?" Jiki na rawa Fatima tace "na zauna can gefen ne" "Nazo bangankiba to sako hajiya ta bani ki koma dakin da aka saki ki gyara kicigaba da aiki idan baki gamaba ki kwana a can"..... Kallo Fatima Kebin saade dashi harta kule bayan tagama fada Mata tai tafiyarta....runtse idanuwanta tayi ta budesu sanan ta juya da sauri ta nufin sashen da aka turata dazun Dan ta gyara..... Aiki takeyi babuji Babu gani Amma Rabin abikin da takeyi Tana tunanin yarima ne Bata taba tsuntar kanta a yanayin data tsunci kantaba dazu wasu sababbin abubuwa ne takeji game dashi Wanda yasa taji tamkar su kasance a haka harabada.... Har dare Tana aikin a haka duhu ya risketa tsoro da fargaba dik suka ziyarceta ganin har duhu yayi Bata gamaba gashi ance a wurin Nan zata kwana ihunka banza,....can gefe ta rakube ga sauro dake faman Kai Mata cizo Tana bugesu ta ko Ina.....kukane ya kwace Mata Wanda ita kanta batasan tanayinsa ba,.....lokaci daya Yan uwanta suka Fado Mata su bilkisu da Maryam ko wani Hali suke ciki oho?kallon kanta tayi a cikin duhu ta tunada dik inda zasu shiga tare suke zuwa da bilkisu har bayi saboda yadda take da masifar tsoro sai gashi yau ita kadaice zaune cikin duhu sauro na Kai Mata cizo Babu Wanda ke debe Mata kewa......Tana Nan zaune tsoro Mai tsanani na karuwa Mata savoda yadda dare yafarayi gashi harta da tafin hannunta Bata gani saboda duhu dunkulewa tayi waje daya ta hada Kai da gwiwa sanyi na kadata sai adduoi take kamowa Tana saki.....haka dare ya tsala Tana Nan dunkule idanuwanta Gam ta rufesu Tana kamo adduoi kala kala har asuba batare da tayi bacciba..... ********** Washe gari da safe Misalin karfe goma na safe gwaggo rahi na zaune suna breakfast da yaranta kowa da abinda yakeci deejahmah ta ajiye cokali ta kalli mamanta tace "Wai nikam mama ko Yaya ake ciki da shegiyar yarinyar can ooho" "Ohon musu mudai ai burinmu ya cika tunda abinda muke bukata ya karbu a gidan sauran yakin dik Mai saukine" "Nifa mama na tsani yarinyar Nan wallahi hankalina bazai kwantaba idan har ban batawa yarinyar Nan wanan fuskar me kamada ta mayu ba" Kallonta gwaggo rahi tayi sanan ta kurbi ruwan tea Saida ya fada mata tace "ki aiwatarda dik abinda kikai niyya Yar lelen" Murmushin Jin Dadi deejahma tayi sanan tacee"zan kaiwa hajiya ziyara da yamma" "Hakan nada kyau" ********* Koda Fatima ta tashi dakyar ta iya mikewa saboda yadda jikinta yayi tsami tun asuba takarashe aikin wajen ta fito Tana tangal tangal har sashensu hajiya har kasa ta gaida su Amma Babu Wanda ya amsa Banda kallon kyama da khausar tabita dashi haka ta Mike jiki a sanyaye ta fice ta nufi wajen zamanta dake can baya kayanta sunyi dukun dukun jikinta dik cizon sauro yayi jajir hannuwanta ga yunwa dake kwakularta..... Sanin inda take Zama yasa yarima Yana fitowa bangarensa har ya nufi sashin iyayensa ta dawo da sauri ya canja hanya.....Aiko can ya hangeta da jajayen kaya zaune ta kurawa sashe daya Ido ko kiftawa batayi ta Lula cikin duniyar tunani....har ya iso wajen Bata saniba ya Dan tsaya akanta ganin batasan yanayiba yasa ya Sanya hannunsa ya shafi gefen wuyanta da sauri ta Mike a razane "Ke nine"....ajiyar zuciya ta sauke sanan ta turo baki gaba tace "shine zaka bani tsoro" "Yi hakuri bintu na fito saboda nasan wajen zamanki yasa ke nakeso infara gani nayo Nan ko bakiji dadiba"ya daga Mata gira daya Murmushi tayi tace "Nima ai Kai nakeson gani don inada wata bukata a wajenka"..da sauri ya gyara tsayuwa yace "Fadi bukatarki ko wace irice" Shagwabe fuska Fatima tayi har Tana shirinyin kuka cikin shagwaba tace"Ina maraicin Yan uwana" Matsowa yayi daf da ita yace "suwaye" "Su bilkisu....inaso sudawo Nan da Zama Dan Allah ka taimakeni ka hadani dasu ko zanji Dadi" Kallonta yakeyi cikeda tausayawa yasan Dole ta bukaci kasancewa da wani ko Dan tasamu sanyi ta wani bangaren to tayaya zai kawosu bilkisu gidan Nan?" "Kaji yaayaah"....firgigit ya dawo daga tunanin da yakeyi kallon fuskarta yayi yaga hawaye na sauka da sauri yasa hannu Yana share Mata ya riketa sosai yace "ya Isa zan kawosu Babu abinda Zaki nema a wajena ki rasa Amma da sharadi" Da sauri ta kallesa "Ina sauraronka,ko wani sharadine zanbi inhar zan kasance da Yan uwana ka taimaka ka cetomunsu Dan nasan baa lalata musu rayuwaba" "Shhhhhh naji sharadin shine zan kawosu bilkisu Amma daga ke harsu bazaku nuna kunsan juna ba saboda dabarar da zanyiwa su hajiya" Da sauri tace "na amince" "Oya share hawayenki banason kukan Nan a koke gwamnan kuka" Murmushi tayi Masa tasa hannu ta share hawayenta yabi hannunta da kallo Wanda dik cizon sauro yayi rudu rudu...ya girgiza Kai yace "zantafi wajensu hajiya insha Allah zankawo Miki Yan uwanki" Murmushi tai Masa ta gyada kanta ya juya tabishi da kallo Tana murmushi.... ******* Bayan sun gaisa dasu hajiya Sama sama yarima gabansa na faduwa ya gyara Zama yace "hajiya nikam bayin gidan Nan sunyi kadan ya kamata a karo wasu" Jinjina Masa Mai hajiya babba tayi tace"kayi yadda ya Dace" Murmushin nasara yayi batare da yasha wata wuyaba.... *Muje zuwa* *SLIMZY✍🏼😍*🌩 *ANYI WALK'IYA.....* 🌩 *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 *NA:SLIMZY✍🏼* _wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* *Wanan shafi kyautace zuwa gareki mommah* ( *_BILLY_* *_GALADANCI_* )... *kiyi yadda kikeso* *dashi, Ina yi Miki* *son so...* ❤😍 22 Kallon mahaifiyarsa yayi a fakaice,bama ta kallon inda yake don yadda ta nuna tamkar batasan da zamansa a wajenba, Yakai minti goma a zaune sanan ya Mike har ya juya hajiya babba ta tsaidashi ta hanyar yi mishi magana "A Ina zaka samo bayin kamar yadda kace"....batare da wata faduwar gaba ba yace "akwai wani kauye da Ahmad yacemun anyi rigima a wajen an zube mutane Kara zube wasu Ana dibarsu aikatau wasu Ana shigowa dasu cikin gari suna bara shine nace zanje in duba ko Yan Mata biyu ne asamo tunda Naga kuyangi sunfi yawa a gidan" "Hakan yanada kyau"....juyawa yayi batare da yace komi ba ya fice abinsa.... ******** Office yasamu Ahmad abokinsa Nan suka zauna yake bashi labarin shawarar da ya yanke.... "Yanzun kana ganin dakko yaran Nan ka kawo gidanku baka kinkimowa kanka wata rigima ba?" Dan Bata fuska yarima yayi yace "wace irin rigima" "Dik ranan da asiri ya tonu har sarki sai yayi fushi dakai Kuma zaka Kara jefa kanka cikin zargin da akeyi maka" Murmushi yayi yace "dik halin da zan shiga zan shiga matukar zansa Fatima farin ciki,sanan kafin insamu hajiya na gindaya Mata sharudda Akan hakan".....Nan yarima ya kwashe yadda sukai da Fatima ya fadawa Ahmad, "Allah ya baka ikon rikon maraya cikin gaskiya da Amana ya baka lada" "Ameen yanzun inaso in zauna a Nan ne zuwa ka tashi office dinka sai ka rakani muje can gidan marayu idan mun daukosu mukaisu gida tare da Kai Dan na fadawa su hajiya kauye zanje daukosu" Dariya Ahmad ya sheke da ita sanan yace "dadina dakai fasaha,ni wanan tunanin be shigomin a raiba,shiyasa ka zabi dik inda zakaje kaje batare da excort ba ko?" Murmushin gefen fuska yarima yayi ya shafa Dan sajen fuskarsa ya ce'ka cika sa ido" *********** A gidan Ablah kuwa tunda ta tashi take tunanin yadda zaayi taje taga Fatima,...aikace aikace takeyi itada Yar uwarta Aysha Saida suka Gama suna zaune a parlor suna hutawa ablah ta kalli Aysha tace"Niko Aysha inaso inje Inga yarinyar Nan Fatima Inga halin da take ciki" "Ablah kina ganin zaabarmu muganta?gidan sarauta fa?" Dan jinjina Kai Ablah tayi sanan ta jingina da jikin kujera tace "zaabarmu insha Allahu ai yarima Yana Nan ki shirya anjima zankira oga a waya in sanar Masa da inason zuwa ganin Fatima sai muje da yamma ko" "To Allah ya kaimu" "Ameen" ********* Tsaf deejahmah ta shirya ta dibi bayi da kuyangin gidansu Yan rakiya ta shiga mota Suma suka shiga tasu aka jata zuwa gidan sarki........ Tafiyar mintuna kadan ta kawosu gidan kasantuwar Babu wani tazara tsakanin gidan sarki da gidan galadima Wanda ya kasance shine mahaifin deejahmah..... A parking space sukayi parking deejahmah ta fito Tasha kwalliya ta kece raini Tana sanye da super English atamfa anyi Mata dinkin Riga da skirt ya zauna Mata dasss a jikinta ta kawo mayafi ta yane kanta dashi Wanda ya rufe har Rabin jikinta,fuskar Nan Babu annuri sai yatsina takeyi bayi da kuyangin ta suna biye da ita wasu a gabanta wasu a bayanta tamkar itace Yar sarkin yadda take taka kasa ma abin kallo ne dik inda ta gifta maaikatan gidan sarki zubewa kasa kawai sukeyi suna kawo gaisuwa,saidai kawai ta daga musu hannu,a haka har ta Isa babban sashin gidan.... Bayin dake tafiya a gabanta suna zuwa kofar babban parlor suka zube a gefe da gefen kofar ta shiga da sallamarta a ciki ciki...... Da faraa dauke a fuskar hajiya babba takeyiwa deejahma marhabun.... Gefen hajiya babba ta zauna inda khausar ke zaune ta kishingide Tana famar daddana waya, Fatima ce a gefen hajiya ta durkusar da Kai a lokacin hajiya na Bata umarni Akan wani aiki da zatayi.... Deejahmah Bata lura da Fatima ba Dan batada masaniya Akan komawarta kuyanga,....kallon hajiya tayi sanan ta sunkuyar da kanta kasa tace"barka da hutawa ranki ya dade uwar gida a wajen sarki Mai masarautar barayar Zaki" Murmushin Jin Dadi hajiya babba tayi sanan ta amsa da"barka da zuwa diyata deejahmah" "Barkadai hajiya na sameku lafiya?" "Lafiya kalau diyar albarka"..... Shiru ne ya Dan biyo baya kafin hajiya tasa kafa ta hankade Fatima cike da izzah tace "baki iya gaisuwa bane?Koko saarki ce ta shigo da kika kasa bude baki ki gaisheta isasshiya?ke komi sai an nuna Miki saboda dabbanci ki manta da matsayinki na kuyanga baiwar gidan sarki" Da sauri Fatima ta gyara durkuso tace "tuba nakeyi ranki ya dade" Wani kallon Tsana deejahmah ta jefawa Fatima Saida tayi magana sanan ta ganeta ta hanyar muryarta Dan bazata manta da shegiyar muryar yarinyar ba Mai kama da an hura usur.... Da sauri deejahmah ta tarbeta ganin Fatima ta Kara durkusawa Tana shirin gaisheta "dakata Yar matsiyata bana bukatar gaisuwarki a matsayinki na shegiya wadda batada iyaye.....gaisuwarki a matsayinki na kazanta Babu abinda zai karamun saboda haka ki rike gaisuwarki" Hajiya babba dake gefe Tana murmushin Jin Dadi da cin mutuncin da hajiya babba tayiwa Fatima tace"ya kamata ta gaisheki a matsayinki na matar Dan sarki,matar uban gidanta Mana Dan tafara girmamaki tun yanzun kafin tafara aiki a karkashinki" Murmushin kasaita deejahmah tayi batare da tace komiba ta gyara zamanta.... Kafafuwa hajiya babba ta Mike su sanan ta kalli Fatima tace "ke matsamun kafafuwana" "Toh ranki ya dade" Sallamar wata baiwa ce wadda ke bakin kofa ya juyo da hankalinsu duka,...zubewa tayi a kasa tace"Allah ya baki yawan Rai akwai baki dake neman iso a kofar fada..."Dan yatsina fuska hajiya babba tayi tace "wasu irin baki ne meke tafe dasu?" "Allah ya baki yawan Rai daya dai matashiyar macece,sanan dayar Kuma Yar budurwa ce sunce mun sunzo ganin Fatima ne" Wani irin faduwar gaba ne ya ziyarci Fatima lokacinda take matsawa hajiya kafa ji takeyi tamkar ta saki fitsari....tambayar kanta ta shigayi to suwaye wadan Nan?....maganar hajiya ce ta dawo da ita daga duniyar tunanin data fada "je ki shigo dasu" Wani mugun kallo hajiya babba ta watsawa Fatima sanan tace "asirinki ya tonu matsiyaciya" Tana rufe baki sukai sallama suka shigo parlorn Ablah ce da Aysha kanwarta sunsha kwalliya ta kece raini dik Wanda ya kallesu yasan cewa sunaji da kudi da aji da gayu......kallon kallo akeyi da hajiya babba da Barrister hauwa Domin Nan da Nan hajiya babba ta Gane fuskarta,dagowa tayi daga kwancen da take "sakarmun kafata "da sauri Fatima ta saki kafarta jikinta sai rawa yakeyi tamkar mazari.... Babu Wanda yace su zauna haka suke tsaye kikam mamaki da al'ajabin ganin Fatima da uniform din bayi shi ya lullube hauwa da Aysha ga yadda lokaci kankani tayi wata iriyar Rama sai farar fatar da har sheki takeyi, Yunkurawa hajiya babba tayi ta Mike a tsaye tamkar zakanya haka take zagaye su Ablah dake tsaye kikam kamar an dasasu tafa hannu hajiya babba keyi "lallai biri yayi kamada mutum sanan shi mutum Mara kunya dik abinda akace zaiyi zai aikata,yanzun rashin kunyar ki har ta Kai ki iya takowa ki shigo gidana?bayan iyayi da jarumtar da kika Gama nunawa a kotu a matsayinki ke lawyer?yanzun shine kikazo kikara nunamin jarumtar ki a karo na biyu Babu kunya Babu tsoron Allah kika Tako har cikin masarauta kinzo ganin fatima,.....koh?me kikazoyi?" Dariya ma maganar hajiya tabawa Ablah Dan Saida ta murmusa sanan tace "gidan sarauta inace gida ne Mai adalci da jin Kan talakawa?Babu Wanda akaiwa iko da shiga gidan sarauta matukar sarkin da magoya bayansa masu adalcine ga nakasa dasu" Mamakin amsar da Ablah ta Bata tayi Koda yake yarinyar akwai jarumta "da kinsani da fadar sarki kika nufa sai ayi Miki iso a matsayinki na Yar talakawa wacce tazo bara gidan sarauta sai sarki yayi Miki adalci a matsayinsa na maijin Kan talakawansa" Gyara tsayuwa Ablah tayi tace"dik wata masarauta wadda ta amsa sunanta masarauta to fa tabbas sunsan darajar Dan Adam sanan sunsan mutuncin bakonsu suna karramasa su bashi wajen Zama harma da abin motsa baki saidai Kash wanan masarautar Tasha banban da masarautun danasani wadanda sukafiku cikar mulki da izza,akwai wata masarauta danasani dik takamarsu dik nuna mulkinsu basa wulakanci ga bakinsu sukan sauraresu suji maike tafe dasu zanyi Miki misali da masarauta daya tamkar da dubu masarautar hankaka" Zuwa wanan lokacin hajiya babba takai kololuwa a bacin Rai jikinta har rawa yakeyi idan akwai abinda ta Tsana bai wuce ace akwai masarautar da tafi tasu mulki da izzah ba dikda tasan cewa karamar sarautace barayar Zaki Bata Kai wadda ake nufiba..... Cikin tsananin bacin Rai hajiya babba ta nunawa ablah Kofa da hannu"ficemun fice daganan tun kafin in zuciya insa dogarawa su jefaki a dakin duhu su azabtar mun dake,....kafin in bude idona ki tabbatar kin bacemun daga gani sharrin da kika kullo kika kawo Mata to asirinku ya tonu idanma kinzo ku hada bakine ta kashemu to ki sake sabon shiri"..... "Banji zafin wannan korarba dan na rigada nasan bakisan darajar Dan Adam ba saboda haka hajiya Ina Mai baki shawara da kiji tsoron Allah mulki da sarauta na Dan lokacine" Da sauri deejahmah ta Mike zatai magana hajiya babba ta dakatar da ita ta hanyar daga Mata hannu..... Juyawa Aysha da Ablah sukayi suka nufi hanyar fita a Nan sukai kicibis da yarima da Ahmad da Yan Mata biyu a tare dasu, Da sauri yarima ya fadada faraarsa yace "ranki ya dade Mrs Abdul wanan ziyarar bazata haka?" Dan yak'e Ablah tayi Masa tace "a gaggauce mukazo yanzunma banaso in Kara minti daya a gidan Nan idan kanason magana Dani zaka iya samuna a gida ranka ya dade"...Tana Gama fadin haka tayi gaba Aysha tabi bayanta....kallo ya bita dashi take ya hasaso akwai abinda ya faru... Dik wata huduba dama yarima ya Gama yiwa Maryam da bilkisu da sharrudan daya gindaya musu dik suka amsa da zasu kiyaye....tsaidasu yayi a kofar babban parlor yace sujirashi a Nan zaisa a shigo dasu..... Da sallamarsu suka shiga babban parlorn gidan inda hajiya babba ke kaiwa da komowa Tana nushin hannunta cikin tafin dayan hannun....Yana ganin haka saida ganansa ya fadi... Basarwa yayi ya maida dubansa ga Fatima dake durkushe hawaye na gudu a idanuwanta....kafeta yayi da ido yayinda deejahmah tunda Suka shigo ta Dora idanuwanta akansa ta kasa cirewa saboda yadda yayi Mata wani irin kyau da kwarjini....takaicin kallon da takeyiwa Fatima yasa deejahmah a hassale tace "ke fita".... Da sauri Fatima ta zabura ta Mike jiki na rawa ta bi hanyar fita"dakata Nan munafuka"...tsayawa tayi caka a wajen ta sunkuyar da kanta kasa kafafuwanta sai rawa sukeyi..... Kallon yarima hajiya babba tayi "Ina fatan ka hadu da wata Mara kunya yanzun da kanwarta sun fita?...Wai zuwa sukai wajen Fatima sanan suka karemun tanadi a matsayina na matar sarki Amma sai tayi datasani"... "Mistake akayi Amma ba wajen Fatima tazoba wajena tazo Domin abokiyar aikina ce yanzun haka akwai shariar da zan gabatar a wani gari sati Mai zuwa" "Ka sauya kalaman ka Domin Basu shigaba na rigada na fahimci komi yanzun kabiru asirinku ya tonu tunda har ta iya takowa cikin gidan Nan ta cimun zarafi to wallahi summa tallahi wanan shine kuskuren da tayi a rayuwarta ta Sha idan ta Kara nayi Mata alkawarin nadama ka fada Mata Kar insake ganin kafarta a gidan Nan" "Owk" Kawai yace a takaice....shiru na Yan mintuna sanan yarima yace"na iso da wadanan bayi da nace zan kawo yanzun muka daukosu nida Ahmad" Sai lokacin hajiya babba ta kalli Ahmad dake gefe tayi Masa murmushi suka gaisa sama sama... "A shigo dasu" Umarni yabawa sarkin kofa dake tsaye yace "ka shigo da wadanan bayi dake kofar shigowa" "Angama ranka ya dade"..... Mintuna kadan aka shigo dasu bilkisu kallo daya zakayi musu kasan suna cikin tsananin wahala duba da suturar dake jikinsu da daudar dake tattare dasu..... Fatima Dadi da farin cikine suka lullube Fatima dikda bakin cikin da ta tsinci kanta a wanan lokacin Jin shigowar Yan uwanta ta nemi bakin cikin da take ciki ta rasa... Zubewa sukai a gaban hajiya suka kawo gaisuwa sanan sukai Shiru.... "Ko wacce ta gabatarmun da kanta"shine abinda hajiya tace fuskarta a daure tamkar Bata taba dariya ba.... "Ranki ya dade sunana bilkisu" "Kefa"ta nuna Maryam dake tsugunne Tana Raba ido.... "Sunana Maryam" Jinjina Kai hajiya babba tayi ta nuna bilkisu tace "ke Zaki zauna a bangarena dik abinda nake bukata ke zakiyishi da komi nawa kina dakina"..... "Ke Kuma kina bangaren hajiya karama,zansa akaiki sashenta idan ta shigo daga Dan tattakin data fita dazu" "To ranki ya dade"suka hada baki.... "Kunfice a Nan zan nemeku anjima" Da sauri suka Mike suka fice... Fita yarima yayi shida Ahmad suka nufi sashinsa..... "Hajiya Wai Kinga kallon da yarima yakeyiwa waccen munafukar yarinyar tamkar zai hadiyeta" Kallon deejahmah hajiya babba tayi tace"ki kwantar da hankalinki wanan yarinyar azaba ce zatasa ta haka Rami ta bunne kanta da kanta kabiru nakine ke kadai ko yaki ko ya so akwai wasu Kaya da nasa ya siya Miki idan Zaki tafi zanbada asa Miki a mota"..... Murmushin Jin Dadi deejahmah tayi tace "toh ranki ya dade".... Hajiya ta waigo ta kalli Fatima dake jingine a jikin bango tace "tace kije wajen lantana ta kaiki wajen jakadiyyar sashin sarki kice a baki Kaya irin na bayi guda biyu ki nemi wadanan sababbin zuwan ki Kai musu su canja kizomin dasu" Durkusawa ta karayi tace "toh ranki ya dade"ta fice da sauri.... Can tasamu su bilkisu xaune sunyi jugum jugum a jikin bayi a tsattsaye Tana isowa ta sakar musu murmushi....lokaci daya wani farin ciki da Dadi ya lullubeta Wanda Saida ta zubar da kwalla... "Kefa Fatima kinada matsala yanzun kukan me kike so kikeyi a ganemu malama cikin dare xamu hadu mu tattauna yanzun meke tafe dake" "Kaya akace in karbo muku ku canja"..... ********** "Gaskiya abokina ka iya dabara abinda na lura wanan bilkisun shegen wayau zatayi inaga inhar suna tare da Fatima zata rinka Bata shawarwari Kuma wasu abubuwan ko anyi Mata bazata damuba Dan tanada abokanan debe kewa dikda dai ka gargadesu akan nuna sunsan juna" Murmushi yarima yayi yace "ni inaji a jikina inda bilkisu ce Fatima akwai abubuwanda saidai a kasheta Dan yarinyar akwai karfin Hali" "Shegen wayaune da ita kana ganin idanuwanta kuru kuru a tsaye xata gogar da Fatima,....kaikuwa inaso ka rike wuta ka koya Mata sonka sosai alhaji" Tafawa sukai yace "ni yanzunma wallahi ganinta nakesonyi Dan jiya yadda kasan in barta ta kwana wajena Ina ganinta inayi Mata Hira...." "Kardai ka zake mutumina" Sarai ya fahimci abinda Ahmad ke nufi murmushi kawai yayi ya shafa kansa....ya dauki juice ya Dan kurba ya lumshe idanuwansa" ********* Wajen magriba deejahmah ta iso gida Bata yada zango ba a ko Ina sai dakin mahaifiyarta Tana cika Tana batsewa "Yadai deejahmah sarauniya" "Mama wallahi bakiga wulakancin da yarima yayimunba ko kallon inda nake beyiba a matsayina na matar aurensa nunamin yakeyi tamkar besan da wata halittaba" "Ki kwantar da hankalinki zaisan da wata halitta Nan gaba kadan Domin Ina Nan Ina Shirina na boye a kansa burina be wuce Allah ya kaimu lokacinda zaki shiga gidan ya kusanceki a matsayin matarsa"..... Yatsina fuska deejahmah tayi cikin rashin fahimta tace"banganeba" "Zaki Gane Nan gaba kadan....Dan bakaramin shiri nakeyiba akanki matukar yarima ya aureki to shida wata mace saidai kallo" Dadine ya cikata tace"da zarar nasamu ciki na haihu ,zan cika borina akansa" Murmushin mugunta gwaggo rahi tayi tace "hakan nada kyau....mahaifinki nake jira ya dawo ya samu sarki Akan a matso da bikinki Nanda wata daya" "Yauwa mama Dan na kagara in shiga gidan in baza makaman yakina" Murmushi gwaggo rahi tayi tace"hakan nada kyau".... ********* "Faizah ni bana yaki saina shirya sanan ta karkashin kasa nake cizona Domin ni macijin kaikayi ce" Faizah da fauziyya suka jinjina Kai suna kallon innarsu dake wanna maganar wadda ita kadai tasan maanarta Dan Basu fahimceta ba.... "Bokana ya fadamun cewa Babu makawa sai yarima ya auri Fatima.....komi Daren dadewa" Da sauri fauziyya ta dafe kirji "wace fatimar tsintacciyar mage" Gyada Mata Kai matar waziri tayi tace "ita fa sanan dik Shirin da rahina keyi insane dashi Domin karkuzu ya sanarmun da komi,....Nima nayi nawa Shirin Dani dasu zamu zuba mugani..."..... ******* Kasa bacci Fatima tayi cikin dare sai juyi takeyi dago kanta tayi ta kalli sauran kuyangin dake kwakkwace suna sharbar baccinsu hankali kwance,....data rufe ido Babu Wanda take gani sai yarima tunaninsa ya dabaibayeta zuciyarta na harbawa dik lokacinda ta tuna dashi wani irin so da kaunarsa ke ratsa sassan jikinta,...runtse idanuwanta tayi ta budesu hawaye ya shiga gangarowa daga idanuwanta wanan wani irin balai ne zuciyarta ke Shirin jefata ciki?tabbas son yarima takeyi Amma tasan harabada kasancewa dashi saidai a cikin mafarki......kuka ta fashe dashi Mai ban tausayi Tana juyi a kasa ga sanyi Yana kadata ta ko Ina.....bacci ya gagareta kanta ne ya shigayi Sara Mata tamkar zai rabe biyu.... Bangaren yareemah shima hakan ne kaiwa da komowa kawai yakeyi daga parlornsa zuwa bedroom bacci ya gagaresa Fatima kawai yake bukatar gani Fatima kawai yake bukatar kasancewa da ita.....idanuwansa sun kankance bacci ya kaurace musu hannu yasa ya dafe kansa ya jingine da jikin bango hade da runtse idanuwansa,....kamar daga sama yaji Ana buga Masa kofa Dan bude idonsa yayi ya Kara saurare bugun kofane,daga kansa yayi ya kalli agogo Sha biyu na dare....to waye ke buga Masa kofa?... *Muje zuwa* *Zanje hutu da typing din nan☹* *SLIMZY😍✍🏼*🌩 *ANYI WALK'IYA.....* 🌩 *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 *NA:SLIMZY✍🏼* _wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* 23 Da sauri ya bude kofar shiru sai hasken pitilu da hasken farin wata,....mamakine da al'ajabi ya rufesa tabbas yaji bugun kofar daki Amma ya fito bega kowa ba to waye?.....kodai tunanin da yakeyi ne zuciyarsa keyi Masa gizo Akan bugun kofa?ajiyar zuciya ya sauke ya koma ciki maimakon ya kwanta sai ya dauro alwala ya fara sallah..... Biyu saura na dare bilkisu ta Mike ta shiga waige waige ganin dik bayin dake cikin gidan wadanda ke kwana daki daya sunyi bacci ita sai juye juye takeyi tanaso su kebe suyi maganar sirri da Fatima,....saye ta Mike cikin sand'a ta lallaba ta fice shiru cikin gidan ta zagayo ta kofar dakin da su Fatima ke kwana,tura kofar tayi cikin saa ta tarar da ita a bude, Zaune ta tarar da Fatima ta runtse idanuwanta kanta jingine da bango,Jin motsin shigowa yasa Fatima bude ido da sauri sukai Ido hudu da bilkisu wadda ke zare Ido cikin duhu... Hannu tasa ta ya fitota suka fita a tare ba tare da kowa ya gansuba ko tsoron duhun dare basayi wani kebabben waje suka samu Mai wadatar Haske suka zauna, Tagumi Fatima ta rafka idanuwanta sun kada sunyi jajir,....shirune ya biyo baya sanan bilkisu ta dafe kafadarta cikin kasa kasa da murya ta Soma magana, "Wai nikam Fatima meya hanaki bacci na tarar dake a zaune?" Harararta Fatima tayi ta gefe "ke meya hanaki bacci?" "Malama so nakeyi muyi magana don nasan ba lallai bane da Rana musamu halin kebewa mu zanta shiyasa nakeso inyi Miki wasu tambayoyi game da gidan Nan" "Umhmm Ina sauraronki" "Wai shin wani irin Zama kikeyi a cikin gidan Nan faty?Wai Kinga yadda kika rame kika lalace kuwa?ko mu da muke zaman ukubar gidan marayu munfiki kyan gani sanan abun mamaki ma Wai aka daukoki aka kawonan gidan a matsayin kuyanga Fatima banji dadin wanan lamariba" Hawayen da Fatima ke boyewa su suka sulalo Mata a kumatunta tasa bayan hannu ta share "bilkisu to kina tsammanin dama ki ganni cikin gata ne?bayan kin manta ni babbar Mai laifice a wajen wadanan mutanen?sanan kin manta da matsayina na rashin gata da galihu banida wani gatan daya wuce Allah da manzonsa sai yarima, ..Mai martaba ma ya nunamin kulawa ranan da aka kawoni,...wanan Hali da kikaga na shiga bai wuce mahaifiyar wadda na kashewa da ba itace ke azabtar Dani dik wata hanya wadda zata muzantani ta wulakantani shi takeyi saboda na fado a marainiya kallon shegiya kowa yakemun"....zuwa wanan lokacin kuka yaci karfin ta, "Kiyi shiru da wanan kukan yanzun ya kuke ciki keda yarima?kindaisan yareema sonki yakeyi ko?dikda kinfadamun a baya bai taba furta Miki kalmar so ba sai tausayi" "Bilkisu yareema Yana Sona yanzun abubuwan da yakemun ya wuce tunaninki ma ni tsoro nakeji ranan da zaa kamani nasan shi tashi Mai saukice nice ke cikin bala'i Domin na lahira sai ya fini Jin Dadi,...ai jiya Kinga matar da zai aura" Tabe baki bilkisu tayi ta harari Fatima "ni matsalata dake rashin jarumta wallahi,yo Dan zai auri waccen sai me?bayan kinsan yadda yake sonki mu shaidane?to Bari kiji sakin jiki zakiyi ku rinka soyayya Dan bazaa barki a baya ba" Zaro ido Fatima tayi hade da dafa kirji"Kinga bilki bazaki sani a masifa ba na tabbatar da yanzun sai kunfini mutunci a idon mutanen gidan Nan nida nake kamar mujiya" "Munafuka kinaso kina kaiwa kasuwa yanzun ubanme ya hanaki bacci?kike zaune kina runtse runtsen Ido?inba tunaninshiba ki zauna sonsa ya kasheki" Kamo hannun bilkisu Fatima tayi muryarta na rawa "wallahi bilkisu Ina Jin wani yanayi game dashi Amma abinda nake tsoro wutsiyar rakumi tayi nesa da kasa,ni ba Saar auren yarima bace idan zamuyi sara mu rinka duba bakin gatari,Wai kin manta da matsayina ne?ba gidan sarautabana Babu Wanda zaiso ya hada zuri'a da tsintacce Wanda baa San asalinsa ba" Tureta bilkisu tayi ta Mike tsaye "dalla malama tunda bazakibi shawarata ba ki tsaya dari dari tun Yana sonki Yana kulawa dake ya juya Miki baya sai ciwon so da na zuciya ya kasheki,wallahi keda halinmu daya da bakiyi wani abunba matsoraciya kawai Kinga tafiyata kafin a kamamu a ci ubanmu da safe" Fuuuuuu bilkisu ta wuce Fatima tabi bayanta da kallo Tana girgiza Kai,bilkisu sarkin fushi da fada abu kadan ke Bata Mata Rai sanan batason rainin wayau ko kadan Dan ko a gidan marayu ma rashin mutunci takeyiwa su hajiya halima dikda ubanta da sukeci..... Jiki a sanyaye Fatima ta Mike ta juya hanyar dakinsu,tafe take Tana tunani abubuwa dayawa sun taru sun cunkushe Mata a zuciya,....a hankali ta tura kofar dakinsu ta shiga,....tsulum saade wadda tun fitar Fatima ta Mike Tana kallonta Amma tsoron duhu ya hanata bin bayanta taga me tajeyi....kallon kallo akeyi da Fatima da saade wadda ke faman wurgawa Fatima harara "munafuka Ina kikaje?" Da sauri Fatima tace "fitsari najeyi" "Karya kike munafukar Allah fitsarin ne kika tafi kusan Awa nawa ai na leka ba hanyar bayi kikaje ba hanyar fita sasan Nan kikayi gobe zakiyiwa hajiya bayani wayasan ubanda kikaje kika shuka shiyasa nifa tun ranan da aka kawoki nakejin tsoronki saboda Jin labarin ke kika kashe yarima habibu" Kwanciya Fatima tayi batare da tacewa saade uffan ba dik balai da take zazzaga Mata Dan ta Dade da lura da yanayin saade tun ranan da suka fara haduwa ta tsaneta.... Juyi kawai Fatima keyi har asuba Bata runtsa ba Kiran sallar farko ta Mike ta fice a dakin ban daki taje tayi tsarki ta dauro alwala,...Yar barandar data Saba zuwa tayi ibadah yauma can taje ta shimfida dankwalinta ta fara nafilfili sanan ta zauna kafin a Kira sallar asuba tanata Yan adduointa..... ********* Kaiwa da komowa yakeyi tun safe besa Fatima a idonsa ba dik hankalinsa a tashe yake, Dik inda yasan zai sameta ya bi ta wajen bai gantaba har ya wuce ta kofar kitchen yaji alamar motsi dawowa yayi ya Dan leka,itace tsaye Tana faman aikin abincin Rana da sauran maaikatan kitchen din.....juyowa lantana tayi sukai Ido hudu dashi zubewa tayi a kasa "barka da warhaka ranka ya dade kanada bukatar wani Abu ne?" Basarwa yayi har ya juya ya dawo "ke" Da sauri dukkansu suka juyo Suka zube har Fatima,...."Fatima ki dafomin ruwan zafi ki kawomin bangarena".....bai jira komiba ya juya yayi bangarensa,...jikinta ne ya hau rawa ganin Mami ta bita da wani irin kallo na tuhuma yayinda lantana ta cigaba da ayyukanta, Ruwan zafi ta dafa ta zuba a flask ta dauko cups da spoons ta Dora Akan farantin Tana sanye da Dan karamin hijabi da take dorawa Akan uniform din nata fari ta fito dik jikinta Babu kuzari har ga Allah bataso haduwa dashi ba Dan haka yau wuni tayi cikin kitchen ko su bilkisu Bata hadu dasu ba,haka Nan ta nufi bangarensa, Ta Dade tsaye a kofar shiga sashinsa zuciyarta na harbawa sauri da sauri ta rasa dalilin da yasa ta tsinci kanta cikin wannan yanayin kusan minti uku Tana tsaye wajen dik jikinta rawa yakeyi dakyar ta bude baki tayi Masa sallama "assalamu alaikum"..... "Shigo"...kawai ya bada amsa a takaice tasa hannu ta Murda handle din kofar a hankali ta shiga kofar ta rufe Yana zaune Kan kujera ya rafka ta gumi hannu biyu biyu ta shigo hannunta sai rawa yakeyi dakyar ta iya durkusawa ta Dora farantin Akan centre table ta Mike da sauri zata fita,...."da kika ajiyemun waye zai serving Dina?"...mshine tambayar daya jefo Mata....cakk ta tsaya kusan second talatin sanan ta juye ta durkusa ta zuba Masa ruwan zafin ta hada Masa da Yar sugar kadan ta dauko kofin ta dago Kai tace"gashi" Hannunsa yakai zai amsa ya hade da hannunta Gam,....yakai cup din bakinsa a haka idonsa na kanta,...Dan kurba yayi ya lumshe idanuwansa ya ajiye cup din idanuwansa akanta....."Ina kika shiga dik yau bangankiba hankalina dik ya tashi Fatima?umm?so kikeyi in zauce ko?...idanuwansa akanta yake maganar Lumshe idanuwa tayi Wanda ita kanta batasan tayiba hade da Dan tura baki gaba "ni yaayah to mezanyi maka idan na ganka?" Bakinta ya Kama yasan Murda "ohhhh bakiso kiga yayanki?bakida bukatar ganina kenan?" Tsareta da Ido yayi yaji me zatace,....shiru tayi Tana kallonsa idanuwanta taff da hawaye ,da sauri ya saki bakin nata ya sauko daga kujerar daf da ita ya zauna"yi hakuri bintu nine ko?na Kama Miki baki?gasunan sunyi jajir kiyi hakuri kedince sai ayita zumburamun baki".....hawayene ya shiga saukowa a idanuwanta ganin haka yayi saurin dago fuskarta da hannunsa Yana Kare Mata kallo "Fatima meyasa dik lokacinda zan kasance dake sai kin zubar da hawaye bayan kinsan abinda nafi Tsana a rayuwata kenan Inga kinamun asarar hawaye?bakya bukatar kasancewa kusa Dani?ko bakyason ganina ne?" Da sauri ta shiga girgiza Masa Kai "ah ah niba haka bane Kaine ai ka rikemun baki Kuma yanamun zafi"....kallon cute lips dinta yakeyi hannunsa tallafe da fuskarta ....matsowa yayi daff da fuskarta har suna shakar numfashin juna....."toh kiyi hakuri nadaina kinji bintu?...Ina sonki kinji?...kina Sona?" Runtse idanuwa tayi fuskarta dauke da murmushi,...bakaramin kyau tayi Masa ba da wanan kayataccen murmushin nata.....besan lokacinda ya janyota jikinsa ba ya rungume zuciyoyinsu na bugawa sauri da sauri..kici kicin kwacewa Fatima ta shigayi Jin haka da sauri ya saketa Yana sauke numfashi.....hararsa ta danyi ta turo bakin Nan gaba "yaayah ni kabari Babu kyau fa?" Idanuwansa sun canja kala zuwa launin ja sunkankace murya a dashe yace "Fatima Wai kinajin menakeji akanki kuwa?Anya zan iya jure ganinki a haka batare da na mallakeki ba?" Kallon rashin fahimta tayi Masa,...daga Mata gira yayi "Fatima Ina sonki Ina kaunarki har cikin zuciyata tsakani da Allah nakeso in mallakeki inaso in aureki shine babban gata da zanyi Miki a wanan duniyar" Zumbur Fatima ta Mike tanaja da baya Tana girgiza Kai har takai jikin kofa ta jingina....batasan lokacinda hawaye suka kufce Mata ba tamkar an bude famfo..... Tsaye ya Mike Yana takowa a hankali har yazo daf da ita Yana kallon yadda take hawaye,...hannu yasa Yana share Mata hawayen,a raunane yayi kasa da murya daf da fuskarta yace"Fatima bazaki aureniba?bakya Sona?"....runtse idanuwanta tayi tanajin saukar numfashin sa a fuskarta,...kusan minti biyar a haka zuciyoyinsu na bugawa sauri da sauri ko wanne da radadin da yakeji a zuciyarsa,....karfin Hali tayi ta bude idanuwanta ta saukesu Akan fuskarsa da ya kafeta da idanuwa ko kiftawa bayayi, "Yaayah wanan kudirin naka ba Mai yuwuwa bane,banaso kasawa zuciyarka abinda bazaka sameshiba" "Meyasa bazan sameki ba Fatima?Babu wani dalili Wanda zai hanani aurenki sai ikon Allah " "Dan Allah yaayaah ka rufamun asiri ka nisanci kanka daga gareni kayi kokari kasawa zuciyarka son gimbiya deejahmah Dan itace ta Dace dakai bani Fatima ba Dana kasance Mara asali" Da sauri ya sa hannu ya toshe Mata baki"idan har kika Kara Kiran kanki da Mara asali to tabbas zanyi Miki hukunci Mai tsanani,...Babu ranan da zan sanyawa zuciyata son wata Diya mace bayanke bintu,bayan tunfarko zuciyata ta ginu Akan soyayyarki da kaunarki,....Kona auri deejahmah zan aureta ne don cika umarnin mahaifana Amma kisani gan gar jikina ta aura ba zuciyata ba,....kece nakeso Kuma komi runtsi saina mallakeki" Zuwa yanzun kukan Fatima ya tsananta don kalaman yarima suna barazanar tarwatsa Mata zuciya dikda ita kanta Tana Jin sonsa lullube da sassan jikinta.... "Zan gabatar da ke a matsayin matata ta biyu a wajen Mai martaba" Dafe kirji Fatima tayi jikinta ya hau rawa Nan da Nan zufa ta shiga karyowa a dik wata gaba ta jikinta ,zubewa a kasa tayi ta shiga rokon yareema Akan ya rufa Mata asiri kada wannan maganar ta fita.... Durkusawa yayi ya dagota daga tsugunnen da take suna fuskantar juna "Fatima idan ma ban fada yanzun ba Dole Nan gaba in fada saboda haka gara in sanarwa da iyayena kudurina akanki tun yanzun Domin itace tun Yana danye ake lankwasashi,....nasan halin mahaifina Mai adalcine adalin sarki nasan zai fahimceni Amma wallahi tallahi Babu abinda zai hanani sanar musu da kudirina na biyu bayan auren deejahmah.....inason in mallakeki a matsayin matar aurena" "Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun "kawai take furtawa a zuciyarta Tana kallonsa hawaye na gudu a idanuwanta.....juyawa tayi da sauri ta bude kofa ta fice w guje Tana kuka....kallo ya bita dashi zuciyarsa na Kara Masa karfin gwiwa Akan ya sanarwa da iyayensa kudurinsa na biyu, Zagaye parlonsa ya shigayi Yana tunani kala kala daga karshe zuciyarsa ta yanke Masa shawara akan idan an hadu a fada bayan sallahr isha.i ya fadi abinda ke zuciyarsa..... ****** Bilkisu ce gefe rakube a parlorn hajiya Tana sauraren labarinda Mami kuyanga take bawa hajiya Akan Fatima Tana dakin yarima kusan awanni biyu kenan.... Huci hajiya kawai takeyi tamkar zakanya "Mami kin tabbatar da maganar da kika fada?" "Allah ya taimakeki kin manta ke ce kika bamu umarni Akan dik wani shige da ficenta a cikin gidan Nan musanar Miki?...dazun saade take tsaiguntamim jiya cikin dare ma baa dakinsu ta kwana ba" Girgiza Kai kawai hajiya keyi "lallai yarinyar nan ta debowa kanta ruwan dafa kanta?wato karuwarsa ya dauko ya kawo Mana gida suke kebewa suke ashararamcinsu ?Aiko zan shayar da ita ruwan azaba".... Gumi ne ke karyowa bilkisu dake gefe a rabe tanajin tattaunawar hajiya da kuyangarta Mami....mutsu mutsu ta shigayi dabara ta fado Mata, Wani mugun kallo hajiya ta wurgawa bilkisu sanan ta daka Mata tsawa "mutsu mutsun ubanme kikeyi?" Jiki na rawa bilkisu tace"ranki ya dade fitsari nakeji"ta durkusar da kanta a natse ... Mtswww "shine bazaki iya mikewa ba sai kinyimun a carpet shashasha?tsoron uban me kikeji?" Girgiza Kai bilkisu tayi kanta a kasa "babukomi" "Zaki iya tafiya" "Nagode ranki ya dade".... Da sauri bilkisu ta Mike ta fice.... Kallon Mami dake gefe hajiya tayi tace"yarinyar Nan ta kwantamun a Rai tun zuwansu gidan Nan Domin tanada biyayya" Khausar dake gefe Tana latsa waya ta karbe zancen da "ga natsuwa" Jinjina Kai Mami tayi batare da tace komiba...... "Tashi kije kitahomin da Fatima"....durkusawa Mami tayi "angama ranki ya dade".... ******* Bilkisu Tana fitowa sashen hajiya ta shiganan ta fitanan Tana neman Fatima Amma Bata gantaba.....faduwar gaba kawai takeyi da sauri ta fito tayi hanyar cikin gida can nesa ta hangota wajen wata bishiya ta kifa kanta...... *Muje zuwa*...... *ya kamata in huta na Yan kwanaki....nagaji zan Dan huta kwana biyu*...... *SLIMZY✍🏼😍*🌩 *ANYI WALK'IYA.....* 🌩 *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 *NA:SLIMZY✍🏼* _wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* *_Assalamu alaikum zuwa ga masu neman anyi walkiya daga farko Dan Allah kuyi hakuri bazan ita yawaita turashi daga farkoba,kullum saina turashi daga farko Ina typing Ina turawa Dan Allah dik meso daga farko tayi cigiya zata samu Amma gaskiya na rufe turashi daga farko!!!_* 24 Da sauri sauri bikisu ta Isa inda Fatima ke zaune tanayi Tana waige waige kada wani ya ganta,....har bilkisu ta tsaya akanta batasaniba Tana faman sharbar kuka kamar anyi Mata mutuwa,wani kululun bakin cikine yazo ya tokare kirjin bilkisu ga takaicin kukan Fatima dake ci Mata zuciya kamar ta rufeta da duka komi akayi Mata saitayi kuka Dana kuka da bana kukaba ta kasa Zama jaruma,....takai seconds talatin tsaye Fatima batasan da itaba bakin cikine yasa bilkisu Jan dogon tsaki wanda yasa Fatima dagowa da sauri fuskarta sharkaf da hawaye.....harara ta watsa Mata Tana rike da kugu "to akoke gwamnan kuka kin Zama baure komi kuka shiyasa ko a gidan marayu uban kowa ya rainaki,wallahi ji nake kamar in shakeki Dan takaici yanzun dai ni banzo Dan inji wani baasiba nazone insanar dake balain dake tunkaroki" Daskarewa Fatima tayi Tana kallon bilkisu dake tsaye ta rike kugu,Nan da Nan kirjinta ya shiga bugawa sauri da sauri shikenan yarima ya cuceta ya fasa kwai "innalillahi wa Inna ilaihi rajiun" "Dalla malama kin kafe mutum da Ido tunda bazakiyi maganaba saiki tanadi kalaman da Zaki fadawa hajiya Dan wanan munafukar Mai kamar lagwani Mami taje ta fadawa hajiya babba ta ganki a dakin yarima" Zaro ido Fatima tayi hade da dafe kirji "nashiga uku" "Ki tsaya Kiran shiga uku,kinje soyayya ko?kin saki jiki bayan kinsan akwai idanuwa akanki kika Dade gashinan ai an kamaku har kamshin yarima kikeyi"....bilkisu ta karashe maganar da tuntsirewa da dariya.... Bakin cikin dariyar bilkisu yasa Fatima mikewa tsaye zata wuce,....dakatar da ita bilkisu tayi Tana gimtse dariyar dake taso Mata "malama ki fitittike kice ke bakije wajen yarima ba bake bace kice ko ganinsa ma bakiyiba ke idan Kinga zaaci ubanki ki hada da rantsuwar karya kice wallayi" Haushi yakara turnike Fatima murya na rawa tace"shine Zaki tasani kinamun dariya?haba bilkisu bayan kinsan azabar da zansha" "Idan banyi Miki hakaba bazaki jajirceba kin rinka kuka kenan kamar wata jaririya" Bilkisu na kaiwa aya ta hango mami Tana tafe Tana waige waige da alamun neman Fatima take Aida sauri ta makale bayan bishiya Tana numfarfashi har Mami ta karaso, Kallon tuhuma takewa Fatima wadda ke tsaye kikam kamar andasata sanan ta wurga Mata harara"kina Nan a makale bayan kin gamo iskancin kinzonan kina wani munafurcin to hajiya na kiranki" Kala Fatima batace mataba tayi gaba abinta Mami tabi bayanta,....bilkisu dake makale a bayan bishiya Tana cizar yatsa da Jin kalaman da Mami ke jifar Fatima dashi a matsayinta na kuyanga Amma Fatima ta kasa ramawa sai kace matsayi ta fita..... Durkushe Fatima tayi a gaban hajiya kanta a kasa zuciyarta na famar yi Mata lugude ga tsoro da ya lullubeta,....muryar hajiya ta tsinkayo Tana magana "Fatima " "Naam ranki ya dade"murya na rawa ta amsa , "Uban me kikajeyi dakin yarima me kuke kullawa?ko kinji marmarin namijine kikaje kuyi abinda kuka Saba?" Danne tsoro Fatima tayi ta shiga rantse rantse ita bataje ba ba ita bace wallahi..... Da sauri Mami dake gurfane ta karbe zancen da "ni zanyi Miki sharri ne?wallahi hajiya taje rantsuwar karya takeyi da idona na ganta har kitchen ya biyota yace tazo" Itadai hajiya babba tunda Fatima ta Musa taje ta kasa magana don tasan inhar Fatima taje to kukan munafurci zata farayi bazataki amsa laifintaba, Bilkisu kuwa na gefe Tana zare idanu bayan ta dawo fitsarin karya..... "Ki tashi ki bacemun daga gani domin ko ganinki banasonyi mujiya,idan ma kinje kikace bakije ba asirinki zai Tonu idan kere na yawo zabo na yawo watarana zaa hadu dik ranan Dana kamaki da shi wallahi saina shayar dake azaba,bacemun daga gani munafukar banza Kuma anjima kisani akwai aikin da zakiyimun " Sumi Sumi Fatima ta Mike ta fice,dikda haka tsoro be fita a zuciyarta ba yauce Rana ta farko da tayi jarumta a gaban hajiya lallai a gaida bilkisu da badan itaba yau bakaramin azaba zaa kurba Mata ba, Direct inda tasaba zuwa tayi ibadah na taje ganin ankira sallahr laasar tunda dadewa,alwala ta dauro tazo wajen ta shimfida dankwalinta ta tada sallah..... Hajiya karama ce tafe Maryam na biye da ita baiwarta sun fito daga fadar sarki har sunbiyo ta wata hanya sai hajiya karama ta fasabi ta canjo hanya suka bullo ta inda Fatima ta tada sallah.... Tundaga nesa mama karama ke kallon Fatima wadda yau shine Karo na uku da ta ganta Tana ibadah tunda take bayi da kuyangin gidan Nan Bata taba ganinsu suna ibadah ba Amma wanan yarinyar Tana yawan ganinta,sunkaraso daidai Fatima tayi sallama ta zauna Tana cikin yin tasbihi da yatsunta ta hango mama karama da sauri ta kwashe shimfidarta ta zube a kasa "barka da yamma ranki ya dade" Cikin sanyin murya irin na mama karama ta amsa da "barka"....ta wuce abinta Maryam na biye da ita suka hada Ido da Fatima sukaiwa juna murmushi.... Har cikin zuciyarta Fatima Taji dadin amsa Mata da mama karama tayi,Dan tunda tazo gidan Bata taba gaisheta ta amsaba sai yau alhamdulillah Koda hakan zata rinka amsa Mata zata gaisheta dikda a takaice ta amsa Mata..... ******** Zaune mama karama suke itada yar autarta afnan suna Hira sama sama anan ne mama karama ta jeho zancen Fatima "Niko afnan kin taba ganin bayi da kuyangin gidan Nan suna sallah Koda ta asuba ne?" Girgiza Kai afnan tayi "ah ah mama" "Akwai wani abin mamaki Wanda yau shine Karo na biyu Dana gani,wanan yarinyar Yar gidan marayu Ina yawan ganinta Tana ibadah sanan sallahr asuba ma baya wuceta,ranan da Mai martaba yayi zazzabi na kwana a bangarensa wajen hudun asuba na ganta zaune a kasa Tana nafila kafin ma ayi asuba" Murmushi afnan tayi "mama ai dik kuyangin gidan Nan Babu Mai kirkinta babu Mai hakurinta ga ibadah gata shiru shiru kamar magana bai dameta ba" "Umm dik kirkinta bazan sotaba saboda abinda ta aikata,dikda dai ance ba laifinta bane Amma dai idan batasaba bin mazanba bazaa kaitaba" Sallamar yarima ce ta dakatar dasu daga hirar da sukeyi,....a tare suka amsa Masa da afnan, Gefen mama ya takwashe kafarsa hade da durkusar da Kai kasa cike da ladabi yace "barka da yamma ranki ya dade" Dan juyowa tayi ta kallesa,take tausayin Dan nata ya lullubeta hade da soyayyarsa dake ratsa ko Ina a jikinta,horone takeyi Masa Akan rashin Jin maganarta Amma Harga Allah ita kanta kewar Dan nata takeyi....ajiyar zuciya ta sauke "barkanka baka fita bane?" "Ehh mama banje ko inaba Ina daki" Dan kauda Kai tayi gefe "hakan nada kyau,ka gaida mamanka ko?" "Yanzun na fito nakeson inje in gaisheta sai indan fita" "Badai nisa zakayiba ko?don kasan anjima zamu hallara a fadar Mai martaba" "Insha allahu" Jinjina Masa Kai tayi "zaka iya tafiya" Durkusawa ya karayi cikin girmamawa "nagode ranki ya dade"....kallon kanwarsa dake gefe yayi yadanyi Mata murmushi itama ta mayar Masa sanan ya Mike zuciyarsa fari tasss Domin adduarsa ta fara amsuwa mahaifiyarsa ta fara sakkowa daga fushin da takeyi..... ******* Sauri sauri yakeyi zashi sashin hajiya babba ita Kuma ta fito hannunta dauke da faranti da cups kanta a kasa take tafiyarta,....ta bullo wata Yar kwana sukai kicibis Yana ganinta yaja ya tsaya a hanya harta karaso, Batasan da mutum ba tai Karo dashi,da sauri taja da baya zata juya don har ga Allah Bata kalli fuskar ko wayeba hannunta ya janyo ta fado jikinsa ta saki farantin a kasa ta bude baki zatayi magana,..yasa hannu ya toshe Mata baki Yana kallon fuskarta Yana murmushi "sarkin tsoro.....yanzun kin kasa tantance kamshin jikin mijinki koh?" Zaro ido tayi ya sakar Mata baki da dayan hannunsa daya Yana rike da kwankwasonta "Dan Allah yaayah ka rufamun asiri ka sakeni kaga dazun an ganmu fa har hajiya aka fadawa" Kara matseta yayi a jikinsa yasa fuskarsa daf da Tata "nafiso aganmu a haka Kinga idan aka kaiwa Mai martaba karar anganni a jikinki ko muna wani Abu to tabbas zaice saina aureki" Hararsa tayi"nidai kasakeni" Kara rungumeta yayi a jikinsa Yana shafa bayanta "bazan sakekiba saikince kina Sona" Runtse idanuwanta tayi zuciyarta na harbawa ga tsoro da ya cikata Dan babu makawa dik Wanda ya bullo bangaren hajiya saiya gansu "naji Ina sonka"....ta kauda kanta gefe Murmushin mugunta yayi Mata ya Bata peck a kumatu"kece ruhina bintu" Motsin tahowa sukaji da sauri ya saketa ,jikinta na rawa ta shiga kwashe cups dinda ke yashe a kasa jikinta na tsananin rawa.... Bilkisu ce ta taho Tana murmushi, zubewa tayi a kasa fuskarta dauke da murmushi ta fara kawo gaisuwa "barka kadai ranka ya dade Yaya yarima" Murmushin shima yayi Mata "barkanki bilkisu ya bakunta?" "Alhamdulillah" Jinjina Kai kawai yayi ya wuce Yana murmushi hade da shafar fuskar bilkisu dake rabe a gefe..... Yana wucewa bilkisu ta Mike tsaye Tana dariya "sannu sarauniyar soyayya harda rungumeki akayi kika lafe Ina kallonku ai,...gadi na tsaya yi muku wallahi da saade ta ganku Dan hajiya ita ta aika nace nice zanje shinefa ta zauna da hajiya kafin indawo" Kunyar bilkisu ce ta lullube Fatima Tana murmushi kasa kasa "nidai banason sharri kindai tsaya Kinga gulma" "Ohh hakama zakice?danasani na Kira hajiya ta kamaku" Zaro ido Fatima tayi "da nashiga uku" Dariya bilkisu ta sheke dashi harda rike ciki "Amma gaskiya soyayyarku na burgeni fa?hmmm anaso Ana kaiwa kasuwa su wata" Wucewarta Fatima tayi Tana fadin "kedai kikasani"..... Kallo bilkisu tabi Fatima dashi ta saki sassanyar ajiyar zuciya a Fili ta furta "Fatima baiwar Allah kina bani tausayi dikda ni dake bamuda banbanci dukkanmu tsintattu ne Amma jarabawarki tafi ta kowa"....wasu kwalla masu zafi suka sulalowa bilkisu a kuncinta,tasa hannu ta share ta tafi Aiken da akayi Mata" ****** Yarima zaune gefen hajiya babba bayan sun gaisa Babu yabo babu fallasa dukkansu sukai shiru na Dan wani lokaci sanan hajiya ta kasa Shirun da cewa "ya kamata kaje wajen deejahmah ku daidaita kanku Domin inaga zaa dawo da aurenku Nanda wata daya" Gyara Zama yarima yayi Dan Harga Allah ya mance da wata deejahmah da wani zancen aurensu burinsa be wuce ya ga Fatima ba suyi Yar soyayyarsu ta boye Amma hakanan zai auri deejahma kafin yasamu farin cikinsa,....sassanyar ajiyar zuciya ya sauke yace "insha allahu anjima daddare zanje gidan nida Ahmad bayan ishai" Murmushi hajiya babba tadanyi irin na manya "Allah yayi albarka" Da sauri ya kalleta yaushe rabon yaji wanan kalmar a bakinta ?mamakinsa ya danne ya amsada "ameen" Yana zaune bilkisu ta shigo ta zube gaban hajiya cike da ladabi tace "Allah ya baki yawan Rai na aiwatar da umarninki" Murmushin kasaita tayi ta daga Mata hannu bilkisu ta koma can gefe ta rabe Kai a kasa, Kallon yarima hajiya babba tayi "inajin dadin wanan sabuwar baiwar da ka kawo Domin tanada hankali da natsuwa ga biyayya dik abinda zan sata tanayimunshi cikin gaggawa batare da Raina ya baciba inaga itace zata Zama baiwar fadata maana amintacciyata".. Murmushi yarima yayi "hakan nada kyau hajiya" "Zaka iya tafiya" "Nagode ranki ya dade"..ya Mike abinsa ya bar sashin..... ****** Waya hajiya babba tasa takira hajiya rahina lokacin suna zaune a part din yaran harda babban danta daya zo daga kasar waje Kiran hajiya babba ya shigo wayarta.... Kallon wayar tayi sanan ta kalli deejahmah tayi murmushi"hajiya babba ce" Gyatsine deejahma tayi "ki dauka Mana" Dauka gwaggo rahi tayi suga gaisa....take sanar Mata da deejahmah ta gyara yau yareemah zai kawo musu ziyara,....bakin hajiya rahina yaki rufuwa saboda murna haka sukai sallama ta kashe wayar...dukkansu kallonta suke suna jiran Karin bayani "Gyarawa zakiyi Domin yau yareemah zai kawo Miki ziyara" Tabe baki deejahmah tayi "me Kuma zai kawoshi?shida ko kallona bayayi ta wanan tsinanniyar yarinyar yake?shegiya Mara iyaye ni dama yayi zamansa" "Nasha fada Miki ki boye wanan kiyayyar da kishi da kikeyi akansa ki Bari ki mallakesa yadda Zaki juyasa son ranki Kuma ki azabtar da shegiyar yarinyar Mai kamada mayu" Tura baki deejahmah tayi batace komiba gwaggo rahi ta cigaba da lallashinta Tana faman zuba shagwaba.... ******** Shirinsa yayi tsaf zuwa fadar sarki bayan yayi sallahr magriba ya sha Riga da Wando na kaffani Ash colour da bakar hula akansa anyi Masa design Mai kyau irin na sarakai..... Yana tafe ya bullo ta parlor Babu kowa ciki kasantuwar dik sun tafu fadar sarki daga hajiya babba har mama karama khausar da afnan dik suna can sai maaikatane ke gilmawa sama sama.... Sauri sauri yakeyi yayi lattin zuwa fada Dan yasan shi suke jira a tattauna Akan matsalolin yau da kullum, Tana tsaye Tana kalle kalle ya hangeta murmushi yayi Saida yazo daidai gefenta zai wuce yasa baki daidai kunnenta ya rada Mata "zan tafi fada yanzun zanje neman aurenki wajen Mai martaba"...Yana Gama fadin haka yayi wucewarsa....zubewa tayi a kasa Tana ganin jiri na juyawa a duniyarta.... ******* Shiri kasariki akeyi a gidan galadima na tarbar yarima Wanda ya kasance yaune na farko da zaizo zance wajen deejahmah.... Uwarta ta saki jiki Tana faman gyara Yar Tata,bakaramin kyau deejahmah tayiba Domin it's kanta ba baya bace wajen kyau sai shiryata mamanta takeyi da taimakon kuyangi dake Miko wancan kawo wancen.... Murmushi kawai gwaggo rahi takeyi Tana kallon yadda yar Tata takai karshe wajen haduwa..... "Kinyi kyau harki gaji ya'ta....matar yarima Dan sarki....kwanan nan sunanki zai fito a cikin jerin sarauniyoyi na duniyar sarauta na tabbatar da babu wata wadda zata hada kanta dake wajen jerin kyawawan matan sarakan wannan duniyar tamu....Nan gaba kadan Zaki tashi daga matar Dan sarki zuwa matar sarki Kuma uwar Dan sarki Mai jiran gado" Murmushine ya subucewa deejahmah cike da zumudi tace"gaskiya mama kin iya kirari kinji Wai yadda kaina ke Kara girma?" "Nan gaba kadan kanki zaifi haka girma lokacinda magana ma zatayi Miki wuya saidai ki rinka bawa bayi da kuyangi umarni da hannu suna aikatawa ba saikinceba diyata" "Mama nikadaice matar Yaya yarima...nikadaice zan Haifa Masa magaji" "Ko a lahira bana fatan ayi Miki kishiya yadda nake nikadai wajen mahaifinki nake juyashi kamar waina haka kema Zaki juya kabiru sai yadda kikace don shi ma Yana sonki" "Dagaske mama Yaya Yana Sona?idan kuwa hakane nafi kowa saa a duniya sanan daukar fansan jinin habibu bazaimun wahala ba" "Ai alamu sun Gama nuna Yana sonki kedai kawai karki nuna Masa komi a fuskarki idan yazo ki saki jiki kuyi soyayya" Murmushi deejahmah takarayi ta gyadawa mahaifiyarta Kai...ta Dora kafa daya Kan daya Tana faman zuba kamshi.... ******** Zazzaune kowa yake a fadar Babu abinda kakeji sai tashin kamshin turare Wanda aka turare fadar dashi kowa Yana zaune wannan karon harda waziri da sarkin fada Suma sun kawowa sarki ziyara.... Matsaloli ake tattaunawa hade da maganar auren yarima Wanda hajiya babba ta Roka a maidashi Nanda wata daya sarki yayi naam da maganarta... Yarima na gefe sarki ya kallesa kansa na sunkuye,...Dan gyaran murya sarki yayi cike da sarauta da mulki yace "kabiru Babu wata damuwa ta kudi ko ta wani Abu dangane da bangarenka?" Dan rusunawa yarima yayi "akwai ranka ya dade" "Menene bukatarka" "Ina rokon adalin sarki Mai adalci da ya amincemun bayan nayi wanan auren na biyayya in gabatar da matar da nakeso in aura a matsayinta na zabina ta biyu" Da sauri kowa ya zubawa yarima idanuwa bakajin karar komi sai fanka da AC Dake aiki...kansa a kasa yayi maganar zuciyarsa na harbawa sauri da sauri... Gyaran murya sarki yayi hade da murmushin kasaita "na baka umarni ka gabatar Mana da wacece wanan yarinyar da kakeso ka aura a matsayin Mata ta biyu?Yar wace masarauta ce?sanan waye mahaifinta a wanan kasar" Dammmm gaban yarima ya fadi Nan da Nan zuciyarsa ta karye Jin abinda sarki ya ambata,...da kyar ya Tattaro jarumtarsa yace cikin hardewar murya "ba Yar kowa bace face baiwar Allah ce ita ranka ya dade nasan cewa mahaifina adalin sarki ne Wanda yasan adalci da cancanta sanan baya kyamar talakawansa a Koda yaushe burinsa be wuce ya kyautatawa na kasa dashiba,...shiyasa na yanke shawarar isarda bukatata zuwa gareka don nasan kaidin Mai adalcine" "Fadi wacece ita kanka tsaye zansa a nema maka aurenta matukar Kun Dace " "FATIMA CE Yar gidan marayu wadda rukonta yake a karkashinka yanzun haka"..... *Muje zuwa* *SLIMZY😍✍🏼*🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* 25 Da sauri hajiya babba ta tari numfashinsa "wace fatimar kabiru?Fatima tsintacciyar mage?wadda take a matsayin kuyanga baiwa itace zaka aura?ok yanzun muka ganoka yanzun nagama fahimtar dik inda ka dosa dama dalilin dayasa ka daukota ka kawota kenan?kunyi alkawarin zaka aureta bayan ta kashe Dan uwanka ko" Dakatar da ita Mai martaba yayi da sauri "dakata mun ba hayaniya na taraku kuyimun ba a Nan sanan ku baku Isa Ina magana kuna magana ba" "Allah ya huci zuciyar Mai martaba hakan bazai sake faruwaba"...cewar sarkin fada dake gefe Maida dubansa Mai martaba yayi ga yarima dake durkushe kirjinsa na tsananin harbawa gumi na karyo Masa ta ko Ina,...gyaran murya sarki yayi hade da yin shiru na Yan dakiku sanan ya nisa ya ce "bakada hujja ko dalilin da zaisa ka auri Fatima a matsayin Mata ta biyu kabir Domin ita ba Saar aurenka bace,mutuncinka da darajarka da kimarka sun wuce ka auri tsintacciya Kai ko Fatima ba tsintacciya bace bazaka auretaba saboda ba darajarku daya ba" Zuciyar yarima ce ta cigaba da bugawa yayinda duk wata gaba ta jikinsa Babu inda Bata rawa,daurewa yayi ya Tattaro dik wata natsuwa tasa da jarumta ya sawa zuciyarsa ya Kara rusunar da kansa kasa yace "Ina naiman agajin sarki Akan ya duba lamarin wanan yarinya,inaso sarki ya tunada cin zarafi da Dan uwana yayi niyyar yi Mata da keta haddi Allah be nufi hakan ba nakeso in huce Mata takaicin kallon kanta da takeyi a matsayin marainiya yasa akaso ayi Mata haka,...inaso sarki ya duba wannan lamarin ya ajiye matsayi ko cancanta ya duba dumbin ladan da zamu samu wajen killace rayuwar maraya sanan inaso Mai martaba ya tunada matsayin kowa a wajen Allah daya ne Babu Wanda yafi wani a wajen Allah sai Wanda yafi tsoronsa,zata iya yuwuwa idan Fatima ta fimu kusanci da Allah wajen bauta Masa da tsoronsa ya zamana tafimu babban mukami tafimu rabo ranan gobe kiyama,..Allah Babu ruwansa da mulki ko matsayin bawansa abinda Allah yakeso shine ka Zama maiyi Masa biyayya da zuciya daya ka Zama Mai bauta Masa danshi ba riyaba dik wadanan abubuwan idan Fatima ta fimusu ta fimu a wajen ubangijinmu ,sanan Allah Yana kaunar Wanda dik yake kyautatawa maraya ya rike maraya da zuciya daya har mutuwa Allah kadai yasan abinda ya tanadar Masa gobe kiyama.....mahaifina inaso adalcin da kakeyiwa talakawanka ya dawwama har zuwa mutuwarka ya kasance bayan gaskiya da Amana da ka rike na mulki ya zamana ka rike amanar maraya kasanyashi farin ciki Wanda Allah sanadiyyar hakan sai ya gafarta maka wani zunubi naka Kuma yayi maka rahma da mu baki daya...Ina rokon adalin sarki da ya duba wannan lamarin" Ba karamin sanyi jikin Mai martaba yayiba Domin tunda yarima ya Soma magana ya kafesa da idanuwa yake sauraronsa har ya Dasa Aya a zancesa, "Dik naji maganganunka Kabir kuma na gamsu dasu dik abinda kafada gaskiya ne Amma kasani akwai abinda komi cancantarsa Baya yuwuwa ga mutum domin akwai abubuwa da yawa da sun cancanta Amma abinda zai biyo baya a gaba shi ake kallo,da watace ba Fatima ba da gobe zansa a je a nema maka aurenta" Gwauron numfashi yarima ya sauke hade da hadiyar wani mugun miyau sanan ya Kara gurfanawa gaban mahaifin nasa ya nisa yace "bazan ja da hukuncin Mai martaba ba Amma inaso sarki yayi dogon nazari da bincike Akan wanan al'amarin" Jinjina Kai sarki yayi tare da fadin "zan duba lamarin sanan zan duba yuwuwar hakan a Zama na gaba zuwa jibi" Murmushi yarima yayi "nagode ranka ya dade Allah ya Kara maka lafiya da nisan kwana" Daga Masa Kai kawai Mai martaba yayi sanan ya juya ga matansa dake gefensa ko wacce yana kallonta Yana nazarinta sanan yace "Babu wadda takeda abin cewa?" Hajiya babba uffan bataceba sai yunkurawa da tayi ta Mike hade da Dan durkusawa "a tashi lafiya"shine kawai abinda tace ta fice Rai a bace,mama karama kuwa murmushi kawai tayiwa Mai martaba tace "babukomi ranka ya dade umarni kawai zaka bada ayi" Jinjina Mata Kai yayi shima murmushin yayi irin na manya,....babu wata tattaunawa data biyo baya Domin maganar yarima ita tai sanadiyyar wargaza dik wani maganganu da sukeyi da ta shafi masarautar......haka kowa ya watse jiki babu kwari waziri da sarkin fada da sauran fadawan fada kowa gulmace cike da cikinsa...... ******** Dama yarima ya sanar da excort dinsa da fadawa hade da bayi zasuyi Masa rakiya zuwa gidan galadima,Domin bashida wani zabi daya wuce cika umarnin hajiya babba matukar yanason zaman lafiya,Haka sukai kungiya da motoci na rakiyarsa suka fice daga gidan sarki misalin karfe takwas da minti arbain na dare.... Babu inda suka yada zango sai gidan galadima kasantuwar ansan da zuwan nasu akai musu iso zuwa babban parlor na tarbar baki Wanda yasha kayan alatu na more rayuwa hade da kayan ciye ciye Wanda aka ajiye su cike da babbar daddumar dake shimfide a tsakiyar parlorn gidan..... Ciki bayin gidan sukai Masa iso Yana tafe suna biye dashi wadansu na gabansa sunayi Masa jagora fuskar Nan tayi fess yayi kyau har ya gaji saidai ko faraa bayayi dik gaisuwar da bayin gidan da kuyangi da maaikatan gidan ke zubewa sunayi mishi ko daga Kai ya kallesu beyiba wajen Zama ya nema ya Dan kishingide da jikin kilisar dake parlorn..... Deejahmah ta kalli mahaifiyarta ta Dan Bata fuska "haka kawai na tsinci kaina da faduwar gaba,ji nakeyi tamkar haduwar farko zamuyi dashi" Murmushi gwaggo rahi tayi Wanda har hakoran ta suka bayyana ta dafa kafadar Yar Tata "wanan itace haduwar ku ta farko idan baki mantaba,itace zuwa ba musamman dayayi gidan Nan Domin ke Kuma zuwa yayi Dan ya tabbatar Miki da akwai wata kyakkyawar alaka a tsakaninku saboda haka ki dake ki cire faduwar gaba ki fuskanceshi Domin shine abokin rayuwarki Nan gaba kadan" Gyada Mata Kai deejahmah tayi hade da mikewa ta sakarwa mahaifiyarta murmushi "sai na dawo" "Da kyau Yar albarka".... Juyawa tayi Tana tafe bayi na binta a baya tamkar wadda kejin tausayin kasa haka take takawa cike da yanga da daukar hankali,...har cikin babban parlorn, Masauki tayiwa kanta a gefe Saida ta zauna sanan ta kalli kuyangin dake gefenta tayi musu alama da su fita,...da sauri suka watse daya bayan daya..... Tunda ta shigo take satar kallonsa,babu karya yarima kyakkyawa ne ajin farko gashi matashi Wanda keji da mulki da sarauta ga baiwar kwarjini Wanda Allah yayi Masa,...tunda ta shigo take satar kallonsa shiko idonsa na gefe daya yayi murtuk da fuskarsa tamkar tunda Allah ya haliccesa bai taba dariya ba....sun kusa minti goma babu Wanda yacewa Dan uwansa ko kala,...gajiya tayi da shirun ta bude baki cike da yanga da kasaita tace "barka da zuwa ranka ya dade" Shiru yayi Mata batare da yace komi ba,har tsawon minti biyar haushi da takaici suka lullube deejahmah tamkar ta fasa ihu takeji ga danasanin fara kulashi da tayi ya Raina Mata hankali,....ganin Shirun yayi yawa yasa ta Dan hararesa ta gefen Ido "kayi shiru bakace komiba Kuma har maraba nayi maka" "Da kin Mike kin fita kin koyo sallama kin dawo Dana amsa Miki tarbar da kikaimun" Wani kululun bakin ciki ya Kara turniketa Wanda ya fusatata ta kallesa cike da takaici"yanada kyau ka maidani makaranta a matsayina na matarka sai in koyo sallamar" "Akwai wadda nasani wadda ta taso ba a karkashin kulawar iyayentaba ba a karkashin kowaba tsintacciya Amma tasan muhimmancin sallama".. Da sauri ta kalli yarima zuwa wanan lokacin idanuwanta sun Gama rufewa wani masifar kishi ne ya taso Mata Domin tasan wadda yake nufi ba wata bace face shegiyar yarinyar Nan Mai kamada mayu ,takaicine ya lullubeta Amma saita dake "ya Zama wajibi a gareta da ta koyi sallama kodan kasancewarta kuyanga baiwa kaskantacciya sanan tsintacciya,matukar Bata koyi sallama ba to tabbas tasan zaayi Mata horo Mai tsanani so saboda haka inaso in fada maka da kadaina hadani da ita da take baiwa a wajenka da ni da nake a matsayin matarka" Ba karamin batawa yarima Rai kalaman deejahmah sukayiba Domin a duniyarsa Babu abinda ya Tsana ji fiye da Kiran Fatima kaskantacciya tsintacciya hakan na Sosa Masa Rai Domin shi kallonta yakeyi kamar kowa,idanuwansa sun canja kala zuwa launin ja Domin tunda yake Babu yarinyar da ya taba zuwa wajenta da sunan zance balle ta rainasa ta fada Masa maganganu,haushi da takaicin kansa ya kamasa meye ma dalilinsa na amsa zuwa wajenta ?danne zuciyarsa dake tafarfasa yayi yace "matukar Ina numfashi bazan taba daina hadaki da Fatima ba Domin keda Fatima matsayinku daya a wajena"...... A fusace deejahmah ta Mike tsaye ta rike kunta kadan ta juya Masa baya "kadaina mafarkin cewa matsayinmu guda da ita Domin ni matarka ce ita Kuma baiwarka ce wadda Nan gaba kadan zata Zama baiwata" "Yadda kike tunanin ke matatace to itama Fatima haka nakeyi Mata burin ta kasance daya daga cikin matana,idan baki sani ba kisani yau din Nan nakai maganar neman auren Fatima gaban Mai martaba" Da sauri deejahmah ta juyo ta kafesa da ido, Shima kallonta yakeyi Ido cikin ido take ya hango tsananin bacin Rai da tashin hankali hade da kishi cikin idanuwanta,murmushin mugunta yayi Mata Dan ya rigada ya Rama rashin kunyar da tayi Masa, Gira daya ya daga Mata da Dan murmushi dauke a fuskarsa yace "ki kwantar da hankalinki kece zakije a uwar gida ita Kuma amarya sanan saiki shirya yadda Zaki zauna Dani a matsayin mijinki yadda Zaki kwatarwa kanki yanci a wajena ki koyi ladabi da biyayya da iya kalamai masu dadi uwa uba tarbiyya" Hawayen bakin cikine suka fara sulalowa a idanuwan deejahmah wadda ke tsaye idonta cikin nasa tamkar an dasata,tsananin takaici yasa ta zubar hawayen da Bata shiryaba,Rabon da tayi kukan bakin ciki tun mutuwar habib yau gashi yarima yazo har gida ya ci Mata zarafi ya wulakantata,Babu wani namijin daya taba yi Mata wanan tozarcin sai shi, Murmushi yayi hade da takowa har gabanta Yana Kare Mata kallo fuskarsa har yanzun dauke da murmushin mugunta,....hannu yasa a aljihunsa ya Ciro farin kyalle Mai kamshi ya Mika Mata "amshi ki goge hawayenki sarauniya"ya kashe Mata ido , Juyar da kanta gefe tayi batare da ta kallesaba ta fara takawa a hankali ta nufi kofar fita,har ta Kai kofa ta tsinkayo muryarsa Yana fadin "ga kudin zancenan na ajiye miki da Wanda Zaki siya kyallen da Zaki share hawayen da nasaki,Ina Mai gargadinki Nan gaba sai kisan irin kalaman da Zaki furtamun Domin idan baki yasan abinda zai fada baisan amsar da aka tanadar masaba sai ki koyi kalami masu dadi,ki mikamun gaisuwa ga uwata".... Tsaye tayi a wajen a daskare Tana sauraron maganganun da yake jifanta dasu a tsanake cike da kasaita da gadara yake jifanta dasu da muryarsa Mai matukar dadin saurare..... Juyawa yayi ya ficewarsa ta kofar da ya shigo karar sautin futarsa taji ta waigo da sauri ta kalli kofar,durkushewa tayi a wajen Tana kukan bakin ciki ta dau kimanin minti talatin sanan ta Mike ta fice a guje ta nufi dakin mahaifiyarta..... Kuka takeyi harda shassheka a jikin mamanta,a kidime take tambayarta da "lafiya?me akayi Miki?waya tabaki?meyafaru?"....lokaci daya take jero Mata wadanan tambayoyin hannunta daysma rungume da deejahmah dake rizgar kuka,...cikin kuka take fadin "wallahi bazan yardaba bazan taba amincewa da maganganun da Yaya yarima ya fadamun na cewa Wai bayan ya aureni zai auri Fatima a matsayin Mata ta biyu"....da sauri gwaggo rahi ta ture deejahmah a Kan gado ta Mike tsaye "mekike fada?kinada hankali kuwa?kodai mafarki kikeyi?" Mikewa deejahmah tayi zaune Tana hawaye ta kwashe dik yadda sukayi da yareema daga farko har karshe da cin zarafin da yayi Mata ta fadawa mahaifiyarta" "Karya yakeyi wallahi,karyane be isaba wallahi yayi kadan yace zai hadaki kishi da kuyangarki baiwarki sanan shegiya Mara uba a matsayinki na sarauniya wadda aka haifeki a mulki kika tashi a mulki Yar asali Yar dangi wanan maganar shirmece,bazan taba yardaba idan kuwa haka ne to ya daukowa yarinyar balai ya jefata cikin masifa Dan saina tabbatar da na halakata ko insa a batar da ita" Cikin kuka deejahmah ke fadin "mama ki taimakeni yarima yanaso ya kaskantar Dani a wanan masarautar yanaso inzama abin kwatance a sauran masaratu wadda ke kishi da kuyanga baiwa"ta rushe da kuka.... Zama gwaggo rahi tayi hade da janyo deejahma jikinta ta rungume Tana bubbuga bayanta"ki kwantar da hankalinki lokaci yayi da zaayi yakin da baa tabayinsa ba a wanan masarautar Babu Wanda ya Isa yasamun gudan jinina kuka da hawaye a matsayinki na Yar gata gaba da baya gobe zanje gidan zan samu Mai martaba da maganar " Kara shigewa jikin mahaifiyarta tayi Tana ajiyar zuciya..... ********** Hankalinsa kwance ya shigo cikin gidan direct babban parkor ya shiga a Nan ya tarar da Fatima durkushe a gaban hajiya babba idanuwanta sunyi jajir fuskarta ta kumbura da alama Tasha mari....hawayene kawai yake gudu a idanuwanta kanta a kasa.... Jikinsa har rawa yakeyi ya karaso wajen ya kalleta ya kalli hajiya ya rasa inda zaisa kansa har ya karasa takowa wajen, Ganinsa yasa hajiya sa kafa ta hambare Fatima da sauri ya Mike zai riketa "idan ka taba ta sainayi mummunan Bata maka Rai kabiru maciya Amana wallahi munsa kafar Wando daya daku ku duka Kai banida hurumin da zan azabtar dakai Amma ita inada shi Domin baiwata ce sai yadda nayi da ita kayi kuskure daka bayyana asirinku da wuri ka gasgata zarginku da nakeyi sanan nakara gasgata labaran da nake samu game daku wannan dukan da nayi Mata somin tabi kenan azaba ita zatasa tabar gidan Nan da kafafuwanta kafin insa a hallakata.... Bilkisu dake rabe a gefe minti minti take kauda fuskarta ta share kwallar dake zubowa a idanuwanta na tausayin Yar uwarta Tana gani tun dawowar hajiya babba daga fada ake azabtar da ita kala Kala duka dai ta Shashi kamar jaka hajiya babba ta bugeta tasa an bugeta dik Dan yarima ya fadi zai aureta,...haushi yasa bilkisu furtawa a cikin ranta "insha Allahu sai ya auri Fatima saidai ku mutu"..... Takaicine yasa yarima barin wajen ya nufi sasansa cike da bacin Rai Yana zuwa ya cire kayan jikinsa ya zura jallabiya ,bayan minti talatin ya fito sashin hajiya babba ya shiga babu kowa a parlornta sai bilkisu da alama hajiya ta shiga bedroom don dare yayi hannu yasa ya yafito bilkisu yayi Mata alama da tazo ya juya abinsa , Gudun bacin Rai yasa bilkisu kwankwasa kofar hajiya,daga ciki ta amsa Mata da "lafiya?menene?" "Nice bilki ranki ya dade yarima ne ya nemi da in Kai Masa abinci bangaren sa ingyara masa shine nace Bari infadawa uwargijiyata" Murmushi hajiya babba tayi daga kwancen da take tanajin dadin girmamawar da bilkisu keyi Mata tace"Zaki iya zuwa ki rufomin kofa" "Nagode ranki ya dade".. daga waje ta watsawa kofar harara ta rufo kofar parlorn dama neman hanyar fita takeyi, ****** Sasan yarima ta buga daga ciki ya amsa Mata ya Bata umarnin shigowa ,Yana zaune a kujera ya Dora kafarsa daya Akan centre table din dakin idanuwansa a lumshe,...zubewa tayi akasa tace'gani ranka ya dade" "Jeki tahomin da Fatima" Dan jimm kadan tayi sanan ta bashi amsada "hajiya tasata aiki yanzun hakan Tana can kofar baya" Dakawa bilkisu tsawa yayi cikin bacin Rai "nace ki kiramun ita ko?aikin hajiya yafi kirana ne?" A tsorace ta girgiza Kai "ah ah ranka ya dade tuba nakeyi" Ficewa tayi hade da rufo kofar..... Can tasamu Fatima Tana famar aikin dibar Kaya masu uban nauyi Tana shigar dasu store na cikin gidan kayanda dogarawa ke shigar dasu karfafa Amma yau da kanta take Diba Tana shigarwa dasu Tana numfarfashi hawaye dik ya bushe a idanuwanta....bilkisu ta Dade a bayanta tsaye Tana kallonta cike da tausayawa dakyar ta bude baki tace"Fatima kizo bangaren yarima yanason magana dake" "Kije kice bazanzoba" "A dalilin me?" "Saboda shine silar jefani cikin wanan masifar na fada masa kada ya fadawa sarki zai aureni ya kafe sai ya fada ga balain daya jamun Nan idan suka kasheni ya huta" "Karkice haka Fatima ko yarima be fadawa sarki ba haka Allah ya rubuto zai faru dake banaso azabarsu tasa ki canja Masa ko kice Zaki tsanesa Dan shi ya janyo Miki aisu haka sukeso ni Kuma banaso ki sakar musu wanan wasan ya zamana kin rike wuta kina kyautata Masa Kuna soyayyarku hakan shi zai Kara bakanta ran makiyanki,Dan Allah kizo muje karkice bazakiba" Murmushi kawai Fatima tayi Wanda a iya fuskarta ya tsaya tabi bayan bilkisu har bangarensa,da sallamarsu suka shiga dukkansu suka durkusa, Kallon bilkisu yayi "bamu guri"...da sauri ta Mike ta rufo musu kofa.... Ruwa da towel din dake gabansa ya janyo ya Dora Akan centre table ya kalli inda Fatima ke durkushe a rabe ya girgiza Kai sanan yadan sassauta murya "taho Nan" Ko motsawa batayiba balle yasa ran zatazo,Kara shegewa jikin kujerar tayi , Tasowa yayi da kansa ya dagata cak ya dauketa yayi Jan kujerar dayake zaune dazun ya zauna ya dorata Kan cinyarsa ya rike hannunwanta biyu da hannunsa daya sanan yasa dayan Yana juko towel din Yana matsewa Yana shafa Mata a fuska Yana gargasa ida ya kumbura da ida jini ya kwanta a fuskarta,...haushi ne ya cikata batace masa komiba sai faman tura Baki takeyi Tana yatsina fuska Dan tanajin zafi,har ya Gama ya janye robar gefe hannunsa na rike da ita Akan cinyarsa, "Dan Allah kabari nidai kasakeni sai an samemu a haka ka Kara jamun ko?"idanuwanta suka kawo ruwa.. Kara rungumeta yayi zuciyarsa na bugawa sauri da sauri ita kanta zuciyarta bugawa takeyi Amma saita Samu kanta da kwantar da kanta a kafadarsa Tana hawaye, Kallon yadda hawaye yake gudu a idanuwanta yayi besan lokacin da shima hawayen tausayinta suka fara zubo masaba suna diga Akan fuskarta, Idonta ta dago ta kallesa Ido cikin ido "meyasa kake hawaye Ina tsammanin inji kasanya hannayenka masu albarka kana sharemun nawa hawayen sai Kuma ka tayani?Haba yarimana kaifa jarumine yayana kabar hawayen kaji?inhar akaina kakeyi azaba ko kyama ko kaskanci bazai taba canja matsayinka a cikin zuciyataba,nasan kana tunanin zan iya tsanarka saboda Dan Kai ake wulakantani,ko?babu wanan ranan harabada Kaine gatana Kaine farin cikina Kaine sirrin zuciyata" Kirrrr yayi da ido Yana kallonta ,tunda yake Bata taba fada Masa wadanan kalamaiba sai yau wani irin dadine ya ziyarci zuciyarsa Dan har cikin zuciyarsa Yana tsoron kada azaba tasa Fatima ta tsanesa.... Da kanta ta kamo gefen karamin hijabinta Tana share Masa hawaye lokaci daya murmushi kwance a fuskarta dikda itama hawayen takeyi.... Hannunsa yasa Yana share Mata hawaye shima Yana maida Mata da martanin murmushin ta,"hakika Fatima ke baiwar Allah ce ,Allah kadai yasan dumbin baiwar dake tattare dake Yar aljannah,babu abinda zai hanani cika burina akanki sai ikon Allah inama in bude idanuwana inga kin rikide kin Zama matata"..runtse idonsa yayi Yana murmushi, Dariya takamayi Masa Tana kallon idanuwansa a rufe tasa baki ta hura Masa iska a ido....ya shiga budesu a hankali Yana saukesu Akan kyakkyawar fuskarta dake faman yi Masa dariya,...mikewa tayi daga jikinsa da sauri ya janyota ya rike hannunwanta Yana murzawa a hankali..."inasonki bintu" Dan tura baki tayi sanan ta kashe Masa Ido tace"Niko banasonka Yaya" Da sauri ya kalleta ta sakar Masa murmushi "kaunarka nake" Yasa hannu ya lakuce Mata hanci sanan ya saukta a jikinsa ya Mike "kamar kada ki tafi" "To ko in kwana a Nan"...tayi Masa gwalo..."karki cika baki zan iya rikeku har safe" Sai lokacin Fatima ta zaro Ido "ashefa mu biyune nida masifatu,nasan tanacan ta cika tai famm" "Kin manceda ita kinata soyayya bintu ashedai kin iya soyayya"ya ruko kugunta Yana dariya kasa kasa Ture hannunsa tayi tai gaba har takai kofa ta juyo"Saida safe yarimana"ta kashe Masa Ido... Kallo ya bita dashi har ta rufo kofar Yana murmushi yasa hannu Yana shafa kansa,...ajiyar zuciya ya sauke a hankali "alhamdulillah burina ya cika nasanya marainiyar Allah farin ciki....bintu insha allahu sai kin Zama matata Domin kece burin Raina" Zama yayi da baya Akan kujera ya Dan kishingide da bayansa ya runtse idanuwansa Yana ganin fuskarta tanayi Masa murmushi... ******** Bacci barawo ya dauki gwaggo rahi da deejahma tun sassafe misalin karfe goma na safe hajiya rahina tayi shirinta tsaf Dan zuwa gidan sarki, A shirye deejahmah ta sameta a daki tace"inaso inbiki gidan sarki don in Rama takaicin da yarima ya kunsamun jiya" "Tayaya Zaki Rama?mezakiyi mishi ya bakanta ransa bayan shi kuka yasaki da hawayenki" Murmushi deejahmah tayi ta daga hannunta dauke da Yar karamar aska irinta wanzamai Tana murmushi tace "tunda safe nasa baiwata rahane taje gidan sarkin aska na bukaci da ta karbomin aska Mai kaifin gaske don inada abinda zanyi da ita" Kallonta uwarta keyi Baki bude da kyar ta saisata mamakinta tace"me Kuma zakiyi da aska?" "Wanan askar da kike gani da ita zanyi amfani wajen aske gashin Kan Fatima tass,sanan in zaunar da ita lungu da sako na fuskarta sainayi Mata tsage dashi na wulakanci,saina tabbatar da ko makaho bazaiso hada ido da fuskartaba,wanan kyawun da take dashi yau zai Zama tarhi"..... Dariya gwaggo rahi ta sheke dashi "lallai kinsan kan mugunta deejahmah shirya muje" "A shirye nake zamu iya tafiya".... *Muje zuwa* *SLIMZY✍🏼😍*🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* *SAKO DAGA KUNGIYAR HASKE WRITERS* *ASSOCIATION💡* *ZUWAGA DUMBIN MASOYAN MU MUKE SHAIDA MUKU WANI BAKON AL'AMARI DAGA MAHASSADA*, *AKWAI WANI SABON LITTAFI DA SUKA KIRKIRA ZAKUGA A SAMANSA AN AMBACI ...BILLY* *GALADANCI (MAGAJIYAR KARUWAI)....TO BA WRITE UP DINMU BANE BA RUBUTUNTA BANE ANYI HAKA NE DOMIN A BA'TA SUNAN TA, SHIYASA MUKA YANKE HUKUNCIN SANAR DAKU DA WURI KAFIN LITTAFIN YA FARA YAWO....* *BABU RUWAN BILLY GALADANCI DA WANAN RUBUTU BA NATA* *BANE....MAHASSADANE KAWAI...* 26 Motoci suka shirya tsaf da Yan rakiyarsu suka nufi gidan sarki cikin mintuna da Basu wuce arbain ba suka Isa.... Tun daga nesa Fatima ke hangen motoci na shigowa kasantuwar Tana can baya inda ake jibge Kaya idan ankawo Tana kwashewa Tana kaiwa dakin tsohuwar ajiya tun Daren jiya take aikin Abu daya har bacci ya kwasheta a wajen ta Dora daga inda ta tsaya da safe...... Hagensu takeyi suna tafe suna tunkaho Yan rakiyarsu na biye dasu haka dik inda suka wuce maaikata na zubewa a kasa suna kawo gaisuwa Babu Wanda suke kalla ballantana su amsa har suka shiga sashin cikin gidan.....haka kawai Fatima ta tsinci kanta cikin matsananciyar faduwar gaba.....ta Dade a tsaye Tana tunani kafin daga bisani ta cigaba da aikin da takeyi.... Bangaren hajiya babba suka yada zango tayi musu tarba Mai kyau Nan bilkisu ta shiga kawo musu kayan motsa baki Tana jerawa, Sai wani Shan kamshi deejahmah takeyi Tana yatsina fuska... "Hajiya barka da tashi Kinga nayi zuwan sassafe ko?" "Ehh wallahi kin rigani zuwa ne Amma nikaina yau nayi niyyar shirya zuwa gidan naki' "Muhimmiyar magana ta kawoni hajiya,wani mugun labari mukaji a bakin wanan jairin yaron kabiru har yasa deejahmah kuka" Girgiza Kai hajiya babba tayi hade da yin murmushi Mai ciwo ta cije bakinta sanan ta fuskanci hajiya rahina "wanan maganar ki dauketa a ruwan kwando Domin harabada kabiru bazai auri shegiya Mara iyayeba" "Cewafa yeyi yakai maganar gaban sarki....hmmm hankalinmu ba karamin tashi yayiba shiyasa na yanke shawarar zuwa gaban sarki infada Masa cin mutuncin da kabiru yazo har gida yayi Mana" Kurriii da ido bilkisu tayi Tana kallon bakin kowa a cikinsu karaf sukai Ido hudu da deejahma a hassale tace'ke ubanwa kike kallo haka munafuka?tashi ki fita waye ya baki izinin Zama muna magana kina kallon bakinmu!" Haushi ya Kama bilkisu Amma hakanan ta durkushe a gabanta Tana fadin "tuba nakeyi ranki ya dade waneni da shiga huruminku iyayen gidana" Harara deejahmah ta wurga Mata ta nuna Mata kofa "tashi ki fita" Sumi Sumi bilkisu ta Mike ta fita badan ranta yasoba..... Ajiyar zuciya hajiya babba ta sauke "deejahmah kada hankalinki ya tashi Domin Nina tanadar Mata azabar da dakafafuwanta zatabar gidan Nan Domin yanzun haka tana can baya wajen ingiricin Doki nasata kwasar kayan da sukafi karfinta ta Gama in cigaba da azabtar da ita' Askar dake boye cikin Jakarta deejahma ta Ciro Tana jujjuyaya "hajiya Kinga wanan askar?" Hajiya na fuskatar deejahma ta amsa Mata da Kai "ehh Ina sauraronki" "To da ita zanyi Mata azaba sanan zan aske kanta tsaf da ita Kuma in Zane Mata fuskarta da ita tamkar bayan kwarya" Dariyar mugunta hajiya babba tayi Wanda rabonta da yinta har ta mance "lallai yata kinsan kan mugunta,....sanan nayi Miki alkawarin bayan kinyi Mata wanan azabar nikuma yau zan turata dakin tsohuwar ajiya a can zata kwana zan hada baki da daya daga cikin dogaren gidan Nan ya shiga ya far Mata cikin dare yayi Mata fyade,ya tabbatar yayi Mata kaca kaca yadda bazata moruba" Sai wanan lokacin hajiya rahina tayi murmushi tasamu sassauci Akan takaicin da take ciki tun Daren jiya.....a gefenta ta ajiye askar sanan tacewa su hajiya tanaso sai tayi breakfast zata aiwatar da nufinta.... ******** Bilkisu ce ke faman kaiwa da komowa a bayan kitchen cikin tsananin tashin hankali Domin taso ace taji tattaunawar su hajiya har karshe Domin da alamu sharri ke tafe da wadanan mutanen ba alheriba.... Dafa bayanta taji anyi da sauri ta juyo sukai ido hudu da wata kuyanga wadda daga gani ba Yar gidan bace,...murmushi ta sakarwa bilkisu ta Mika Mata hannu alamar su gaisa,...murmushin yake bilkisu tayiwa wanan kuyangar, "Sunana rahane ni kunyanga ce a gidan galadima maana kuyangar sarauniya deejahmah ce tun dazun nake kallonki a Nan wajen shine Naga yanayinki kin burgeni nakeso muyi abota tunda Naga kema baiwar hajiya babba ce uwar gidan sarki Kinga abotarmu zatazo daya tunda iyayen gijinmu daya" Murmushi bilkisu tayi hade da Jin Dadi Domin koba komi zatasamu wani labari a bakin rahane...."ni sunana bilkisu bakuwace ni baadade da kawoni Nan ba gudun hijira mukayi daga kauyen takanda" "Ayya Allah sarki"... Shiru sukai ko wanne fuskarsa dauke da murmushi kafin bilkisu ta cije lebenta ta Dan kalleta ta gefe taga ita take kallo saita washe baki "Niko Yar uwa kinganni Nan inada son Jin labari tunda kuka shigo Naga alamar kamar iyayen gijinki suna cikin damuwa" "Kedai Bari Yar uwa "waigawa rahane tayi gefe da gefe sanan ta juyo ta cigaba da magana"wallahi uwargijiyata ce ke cikin damuwa jiya Dan sarki yazo wajenta shine yake shaida Mata da bayan ya aureta wai akwai wata kuyanga da zai aura,kinsan me itafa kuyangar ita ta kashe Dan uwansa Amma da yake butulune Wai aurenta zaiyi" Da sauri bilkisu ta dafe kirji tayi kasa da murya "turkashi Amma lallai anyi Mara tunani Allah sarki deejahmah tabani tausayi nice ita wallahi sai na dau fansa Akan shegiyar kuyangar" Waigawa raihane ta karayi tazo daf da kunnen bilkisu cike da tsaigumi tace"ai daukar fansar mukazo,Domin da safen Nan sarauniya tasa naje gidan sarkin aska na amso Mata aska wadda zatayiwa shegiyar aski sanan ta batawa shegiyar fuska" Wani irin faduwar gaba ne ya ziyarci bilkisu take taji tanajin fitsari jikinta ya dauki rawa dama abinda takeso taji kenan "tabdijan gaskiya ba karamin fansa zata daukaba don idan tayi Mata hakan ta Gama da ita....." "Sosaima aini nakosa a Kira shegiya a fara yi Mata aiki" "Kice zamusha kallo zamu kashe kwarkwatar Ido" Dariya rahane tayi tace"kedai Bari ai nakosa barima inje inji ko suna nemana suna bukatar wani Abu"....Tana Gama fadin haka ta dagawa bilkisu hannu da sauri ta wuce.....daskarewa bilkisu tayi tsaye a wajen Tana tunanin mafita.... ******** "Hajiya ya kamata mu aiwatar da komi kafin mubar gidan Nan yanzun zansa deejahmah a gaba muje fada insanarwa da Mai martaba abinda yarima yayi ta hada harda Kuka ke kuma yanzun kisa a Kira Miki daya daga cikin maaikatan gidan Nan kuyi maganar kafin mu dawo yasan da maganar tunda wuri Dan ya shaida" Jinjina Kai hajiya babba tayi tai murmushi ta kwalawa saade Kira... ********* Bayan yareema yayi breakfast daga bangarensa fada ya nufa wajen Mai martaba don ya tunasar dashi Akan maganar Fatima.... Bayan sun taba Hira sosai sanan yarima ya shigo da bukatarsa ,yauma Mai martaba fafur yaki yarda da maganar kamar jiya haka yarima bai gusheba Yana rokonsa Yana tunasar dashi game da maraya da dumbin ladan da zaisamu da rahmar da Allah zaiyi Masa sanadiyyar hakan.... Shiru yayi Mai martaba Yana tunani Akan wanan lamari sanan yayi Yar gyaran murya yace "dik na fahimceka kabiru Kuma na gamsu,Koda zan yarda da maganar aurenka da Fatima sai Akan sharadi daya" Da sauri yarima ya dago Kai cike da tsananin farin ciki yace "ko menene sharadi zan yisa matukar zaka amince mun mahaifina" Murmushi Mai martaba yayi ganin yadda yarima ya rude "sharadin shine bazaka auri Fatima yanzunba sai ka auri deejahmah har saita haihu" Damn kirjin yarima ya shiga lugude....shida ya yanke shawarar ko auren deejahmah yayi bazai taba hada shimfida da ita ba?yanzun Mai martaba yasa Masa sharadi akai Kuma matukar yanason Fatima Dole ya aikata hakan?..... Gumi ne ya shiga karyowa a fuskarsa ya gyara zamansa ya Kara durkusawa yace "na amince ranka ya dade" Murmushi irin na manyan sarki yayi ya Dan gyada kansa "shikenan na amince maka da aurenta Allah yasa ta Zama alheri a gareka da rayuwarmu baki daya Allah ya baka ikon rike Amana yasa ta zame Mana hanyar shiga aljannah' Wani irin farin cikine ya lullubesa bakinsa har baya rufuwa yace "ameen ranka ya dade Amma Dan Allah Ina neman alfarma daga gareka" "Fadi bukatarka kanka tsaye" "Allah ya taimakeka inaso ka fadawa kowa hukuncin daka yanke da kanka a Zama na gaba " "Idan na fahimceka iyayenka Mata kake tsoro" "Karkaji komi insha Allah komi zaizo da sauki Allah ya Kara maka hikima da kaunar na kasa da Kai Domin babu tantama Kaine ka biyo halina" Murmushi yarima yayi "nagode mahaifina Allah ya Kara maka lafiya da nisan kwana zan shiga cikin gida"... Daga Masa Kai kawai Mai martaba yayi.....ya Mike ya fice,...a hanyar sa ta komawa ya hadu da gwaggo rahi zasu shiga fada....da sauri ya tsugunna a gabanta ya gaisheta Amma ko kallonsa batayiba sai harara ta watsa Masa deejahma na biye da ita,....murmushi yayi ya waiga ya kallesu "nayi nasara"....shine abinda ya furta a Fili zuciyarsa fara tass fuskarsa dauke da walwala....Yana tafe Yana murmushi Wanda shi kadai yasan dalilin yin hakan burinsa be wuce yaga bintu ba sanyi idaniyarsa... ******** "Fatima dik yadda zaayi ki gudu ki boye Dan bazan iya ganin muguntar da ake Shirin yi Miki ba Domin kinji....."....Nan bilkisu ta kwashe abinda taji a wajen rahane ta fadawa Fatima tas Bata rage Mata komiba Ai dafe Kai Fatima tayi ta Fadi jagwaf ta zauna da duwawunta,tashin hankali Wanda baasa mishi Rana.... "Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun na shiga uku ni Fatima wanan wani irin balai ne nake fuskanta ciki rayuwata daga wanan sai wanan?dik wahalar Nan da nake ciki Bata ishesuba sai an hada da nakasani?"...ta fashe da kuka Mai ban tausayi, Itama bilkisun batasan lokacinda tasa kukaba sukayitayi har suka gaji bilkisuce ta tsagaita da kukanta tace "me zai Hana ki shiga dakin tsohuwar ajiya cikin Kaya ki boye ayita nemanki a rasa a cikin gidan ke idan kwana ya kamaki ma ki kwana a can kawai ninasan mezan fadawa yarima Amma bazan fada Masa abinda zaayi mikiba kika guducan zance mishi aiki aka sa ki" Da sauri Fatima ta Mike tsaye fuskarta sharkaf da hawaye ta rungume bilkisu "nagode Yar uwata hakika zuwanki gidan Nan alherine a gareni da babu ke da bansan yadda zan kasanceba".. Bubbuga Mata baya bilkisu tayi "ai ba surutu zamu tsayaba kitafi kawai muyi musayar Kaya inbaki nawa insaka naki inyita aiki anan tunda nasan hajiya bazata nemeniba tunda tanada baki Kuma akwai su saade".. "Haka zaayi"....da sauri bilkisu tayi gaba Fatima na binta a baya suka nufi dakin tsohuwar ajiya don suyi musayar Kaya har sun shiga bilkisu tai sauri tace"ke na tuna idan mukayi musaya zaazo nemanki tunda ansan inda kike aiki asirinmu zai tonu karmu canja kiyi zamanki kawai a Nan din" Shiru Fatima tayi Tana kallon bilkisu Tana mamakin yadda takeda masifar hikima da wayau koda yake ko dama can bilkisu akwai wayau ga basira.....Tana gani bilkisu ta fice da sauri Fatima ta bita da kallo hawaye na gangarowa a idanuwanta.... ******** "Isiyaku na tabbatar maka da inhar ka aikata abinda nasaka to zanbaka babbar kyauta Mai tsoka,....kayi yadda nace kada asamu matsala Domin yau dik runtsi can zata kwana kayi tafiyarka kayi aikinka daddare zakaje ka gudanar da abinda na saka don so nakeyi yarinyar Nan yadda ta kashemun gudan jini in nakasa rayuwarta sai tayi danasanin zuwanta duniya......" "Insha Allahu ranki ya dade zaa aikata yadda kikace idan kasheta kikace ayi ma zaayi ai kinfi karfin haka" Gyada Kai hajiya babba tayi "zaka iya tafiya bakin aikinka sai dare zaka gudanar da abinda nasaka" "Dakin tsohuwar ajiya kikace ko ranki ya dade?" "Ehh" Ya Kara durkusawa da har kasa "angama ranki ya dade" Ya mike ta fuce Yana murmushi,... A bakin kofar fita yayi kicibis da bilkisu zata shigo fuskarsa dauke da murmushi ya giftata ya wuce ta bishi da kallo har ya kule,....haka kawai jikinta bai bataba take taji jikinta yayi sanyi da kyar ta daga kafa tayi sallama ta shiga parlorn.... *Muje zuwa* *BONUS KUKASAMU YAU PAGE BIYU GASKIYA SAI NAN DA SATI BIYU ZAKUJINI😜* *SLIMZY✍🏼😍🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* _Wanan shafi kyautace zuwa gareki Yar uwata Rabin jiki bazan iya_ _musalta matsayinki da kimarki a idanuna da zuciyata_ _ba_ *SOPHIE GALADANCI* _Ina yi Miki son so Allah ya Kara Mana dankon zumunci....Allah ya barki da *N* dinki ya nuna mun bikinki in kwashi rawa harda shoki😹😹😹...._ 27 ******** Bangaren sarki kuwa tunda hajiya rahina da deejahmah suka gurfana a gabansa hajiya rahina ke koro Masa bayanin abinda ya faru Daren jiya na karya da gaskiya Wanda akayi da Wanda baayiba har cewa Mai martaba tayi yarima yace da gangan ya kawota gidan dama Dan ya aureta....shidai Mai martaba shiru yayi Yana saurarenta har ta Dasa Aya a zancenta, Gwauron numfashi ya sauke hade da Dan murmushi sanan yace "ai rahina be kamaceki ki kawo karar danki ba bayan kinada yancin da Zaki hukuntashi da kanki batare da kin fadamun ba,ni yanzun banida abin cewa da ya wuce kiyi hakuri da su duka Dan yarane kanana wani abun yaro yakan fadesa ne batare da tunanin mezaije ya dawoba ,to ke babba ce matsayin uwa Kuma suruka saboda haka kiyi hakuri kibarni da shi kabirun" Gyara Zama tayi "ranka ya dade yanzun maganar da kabiru yakeyi dik ya Gama zagaye gari Wai zai auri wannan tsintacciyar yarinyar Mara iyaye wadda baasan asalintaba,baasaniba ta hanyar aure aka haifeta?ko ba ta hanyar aure ba?".. Murmushi Mai martaba yayi irin na manyan sanan ya danyi gyaran murya,jimm kadan yace "yanzun dai a jira hukuncin da zan Yanke zuwa gobe" Dan shiru hajiya rahina tayi na Dan lokaci sanan ta Kara durkusawa"Allah ya taimakeka ya Kara maka lafiya ka duba yuwuwar wanan lamari ga Dan sarki jikan sarki" Daga Mata Kai kawai Mai martaba yayi batare da yace komiba..... Jiki a sanyaye tayiwa Mai martaba sallama suka baro fada jiki Babu kwari.... A hanyarsu ta komawa cikin gida suna tafe deejahmah na bambami tamkar zata Ari baki "wallahi tallahi sai yarinyar Nan tayi datasanin shigowa rayuwarmu,saina yi Mata abinda bazata taba mantawa daniba" "Kidaina Bata bakinki Domin na tanadi sabon makami Wanda zamuyi yaki dashi azabtarwa Mai sauki ne Allah dai ya Bata ikon yin kishi dake" Kwafa deejahma tayi ta gyada Kai lokacin sun shigo sashin hajiya babba, Tsayuwa deejahmah tayi rike da kugu sai hura hanci takeyi Tana huci,a fusace ta juyo inda bilkisu da Rahane ke tsugunne ta watsawa Rahane mugun kallo sanan tace "ke jeki kiramun Fatima" A kidime jiki na rawa Rahane ta Mike tayi hanyar ficewa harta Kai kofa ta tsinkayo muryar deejahma na fadin "ki tabbatar da kin kawota Nan kunzo tare" "Toh ranki ya dade Allah ya huci zuciyar sarauniya"....ta juya ta fice.... Zare ido kawai bilkisu takeyi a zaune tamkar zata saki fitsari Dan ta tsorata da ganin yanayin wadanan azzaluman,addua kawai takeyi a zuciyarta na Allah ya kar yasa aga Fatima... ********* "Mamana ki fahimceni wallahi auren Fatima a gareni tamkar jihadi ne a gareni daku baki daya,ke mahaifiyatace banaso kiyi wani mugun furuci Akan wanan lamarin Domin ke uwace a gareni yardarki itace bukatata kiyimun addua Allah ubangiji yasa sanaddiyar hakan Allah yayi Mana rahma Dani daku baki daya" Tunda ya fara magana tai shiru Tana fuskantar sa,Harga allah dik maganganun daya fad'a a fadar sarki gaskiya ce Amma yuwuwar hakan fa?shin me hakan ke nufi?idan wasu sun fahimci wanan lamari wadansu bazasu fahimtaba.... Ajiyar zuciya mama karama ta sauke,hade da Jan gwauron numfashi "kabiru na fahimceka na fahimci dik abinda kake nufi yanzun idan harni na amince ka aureta mahaifinka fa?" Murmushi ya yi kadan"mama nasan shima Mai martaba zai fahimceni insha allahu zan koma Masa da maganar tunda gobe yace zaa sake sabon zama bayan sallahr laasar" Jinjina Kai tayi "Allah ya zabi abinda yafi Zama alheri a garemu baki daya" Wani Dadi ne ke ratsa sassan jikin yarima,addua takobin mumini kullum yayi sallah sai ya roki Allah Akan wanan lamarin,idan mahaifiyarsa da mahaifinsa sun amince dik yakin da zai biyo baya Mai saukine Domin yasan cewa alheri yake Shirin yi ba sharri ba,....lumshe idanuwansa yayi sanan ya Kara durkusawa gaban mahaifiyarsa yace "nagode uwa tagari adduarki itace kariya a gareni " Murmushi kawai tayi batare da tace komiba.... Yunkurawa yayi zai Mike mama karama ta dakatar dashi "naji Mai martaba nacewa su hajiya zainab suna Nan dawowa gab da bikinka jikin Mai gidan nata ya fara samun sauki umarah zasuyi su dawo dasu zaayi biki" Dadi ne ya cika yarima da jin kanwar mahaifinsa wadda ke matukar kaunarsa zata dawo Nigeria gata da son mutane da kaunar talakawa,ya tabbatar hajiya zainab bazata bada goyon bayaba Akan wulakanta Fatima sanan Fatima zata samu sassauci.... "Allah ya dawo da ita lafiya" "Ameen".... ******** "Ranki ya dade na zagaye gidan Nan kaff ciki da kewaye Banga Fatima ba Domin har taimakon saade na nema Akan ta tayani nemanta bangantaba Babu ita Babu labarinta har inda take aiki mukaje bamu gantaba" Wani kallon wulakanci da tuhuma take watsawa Rahane wadda ke tsaye jikinta na faman rawa tamkar mazari..... "Rahane kina wasa da rayuwarki kina wasa da aikinki,idan har baki nemomin Fatima ba to hukuncin da zan Yanke Mata ke zan yakewa shi Domin Babu yadda zaayi kice ki karade gidan Nan kaff baki gantaba wanan maganar ruwan kwando ce" Zubewa Rahane tayi a kasa hade da fashewa da matsanancin kuka Tana fadin "kiyimin Rai ranki ya dade wallahi tallahi bansan inda Fatima takeba na rantse da Allah Babu inda ban dubaba a gidan Nan ban gantaba har cikin tsohuwar rijiyar tarihi nasa aka rakani mukaje muka Duba Babu ita".. Wata uwar tsawa deejahmah ta dakawa Rahane hade da nuna Mata kofa "bacemun daga gani munafuka idan ma hada baki kukayi kika fada Mata saina shayar dake azaba" Jiki na rawa Rahane ta fice Tana sharar hawaye,kirjinta na dukan uku uku.... Kaiwa da komowa deejahmah keyi hannunta rike da aska Tana jujjuyawa, Girgiza kafa kawai hajiya babba keyi dakyar ta sauke nannauyar ajiyar zuciya ta bakin ciki "ki kwantar da hankalinki diyata kila ta gudune azaba tasa tabar gidan,idan kuwa haka ne murna ya kamata kiyi ba bakin cikiba" "Banajin a jikina wanan bakar dagar xatabar gidan Nan saidai idan gudu tayi ta boye a wani waje saboda azaba dik inda ta boye ma zata fito" Murmushin keta hajiya babba tayi ta nisa tace "dik inda ta shiga tunda na hadata da isyaku magana ta Kare nasan cikin duhun dare zai shiga nemanta Kuma zai aiwatar da abinda nasashi" Sai yanzun gwaggo rahi tasa baki cikin maganar"bayan ya aiwatar da wanan kudirin ni Kuma akwai wani kuduri nawa na zuciyata Wanda sai hakan ya faru zan sanar daku".... Shigowa bilkisu tayi hannunta dauke da flask na abinci da aka Gama Allah Allah takeyi ta shigo Taji tattaunawarsu Amma lokacinda ta shigo ta tarar Dasu shiru tamkar ruwa ya cisu.... ******** "Innalillahi Ina Fatima ta shiga ne?me yarinyar Nan take nufi?badai ta gudu ba"...shi kadai yake tafe yana sambatunsa Yana zancen zuci.... Dik yau be gantaba ya rasa inda zai tsoma ransa yaji dadi,zuciyarsa Kara azalzalarsa takeyi da tsananin kaunarta Mai zafi.....daya zauna sai ya Mike ya fito tamkar wani sabon mahaukaci haka yaketa kaiwa da komowa har magaruba ta rufa be gantaba.... Haka ya hakura ya shige dakinsa ya rufe kansa ya shiga rera kuka Mai ban tausayi "shikenan Fatima kin tafi kinbarni da ciwon sonki cikin zuciyata Wanda nasan shine zai halakani,Ina tsananin kaunarki meyasa zakiyimun haka?"...dafe kansa yayi a bakin gado idanuwansa na fidda hawaye masu zafi..... Ciwon Kai ne Mai tsananin gaske ya rufesa Wanda ko masallaci sallahr magriba kasa zuwa yayi..... ********* Duhu ya rufa sosai bilkisu ta kasa zaune ta kasa tsaye,....ta rasa inda zatasa rayuwarta hakanan ta Mike ta fito daga wajen kwanciyarsu ta nufi dakin da Fatima ke ciki,Wanda ya gauraye da tsananin duhu sai Dan Haske kadan ta saman karamar window din dake ciki shima hasken farin wata ne, Motsi Fatima taji Wanda ya furgitata Saida ta saki fitsari a inda take zaune hantar cikinta ta kada,hade da yin suman gaske.... Cikin murya Mai kamada Rada kasa kasa bilkisu ta Soma magana"Fatima nice bilki kina Ina?nakasa sukuni nakasa kwanciya inbarki cikin wanan halin yasa na fito nazo Dan in tayaki Zama da asuba sai inkoma" Wasu hawayen farin ciki suka shiga gudu a idanuwan Fatima tasa hannu ta share hade da sauke ajiyar zuciya,Tana bayan wani buhun Kaya a boye ta fito a hankali take lalube harta hango inuwar bilkisu inda take tsaye Tana faman waige waige, Kafadarta ta dafa bilkisu ta juyo suka rungume juna suna kuka Mai ban tausayi,hannun juna suka rike suka koma can gefe suka zauna shiru Babu Mai cewa wani uffan, Suna Nan zaune suka hangi inuwar mutum biyu maza,suna Haske Haske da tar touch light wadda batada wadataccen Haske, Magana sukeji kasa kasa"kasha kuruminka hajiya ce tasani wannan aikin shiyasa na gayyatoka Dan Kai ma ka Dana" "Kamar kasan cewa Ina kwadayin wanan yarinyar tun ranan Dana fara ganinta komai yaji fa" Zabura bilkisu da Fatima sukayi jikinsu na matukar rawa ko wacce hanyar buya take nema, Cikin Kaya bilkisu ta shige hade da toshe bakinta saboda tsananin tsoro, Fatima lungun kofa ta shige ta baya ta tsugunna Tana hangensu suka shigo suna Haske Haske, Tana Nan tsugunne Tana Raba Ido cikin duhu taji wani mugun cizo gefen kafarta Wanda Saida ya ratsa har tsakiyar kwanyar kanta,take network din jikinta ya dauke......azaba da zugi da radadi suka dirar Mata lokaci daya.....zufa ce ke tsattsafowa a jikinta ta ko Ina cikin mintuna da Basu wuce uku ba jikinta ya shiga rawa, Haske Haske sukeyi da Yar touching daidai kasa ya haska touch light a karo na biyu Karaf Fatima idonta yakai Kan wani Abu Wanda ko baafadaba kunama ce ta harbeta tunda gashi ta daga k'arinta a karo na biyu..... *Muje zuwa*..... *Kuyi maneji da wanan sanan Ina rokon dik wani masoyina Mai karatun littafin Nan da yamun addua ta Allah ya kawomin farin ciki cikin rayuwata ya duba al'amarina🙏🏼* *SLIMZY😍✍🏼**🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* _Ina daukacin_ _jama'ar_ *KUNDIN* *HASKE?..* _wanan shafin kyautace ga dik wata member ta group din kundin_ _Haske,ku rarraba_ _Banda wawa😹_ 😹😹..... 28 Zaro ido Fatima tayi waje hade da sakin wani fitsari Mai zafi a tsugunne jikinta na faman karkarwa,a wanan yanayin da take ciki har gara Harbin kunama da balain dake Shirin samunsu, Zagaye dakin kawai sukeyi suna Haske Haske Amma basuga kowaba,kusan minti arbain basuji motsiba tsaki isyaku yayi "Kai Amma yarinyar Nan Bata kyautamunba dik na Gama Shirina dazun Dana fita har jiko Nasha yadda zansamu karfin cin uban shegiya Yar taadda Mai kisan Kai sai gashi ta gudu,komi Daren dadewa tunda hajiya tabani go a head saina aiwatar da nufina" Tsaki abokin yayi hade da kashe yar touch light dinsa yace "muje mu kwanta dare nayi dik Kai kasamun Rai wallahi"....Yana karasa fadin haka yayi gaba abinsa, Jiki a mace isyaku yabi bayansa yanata jera uban tsaki haka suka fita suna waigen dakin.... Jin takun fitarsu da kamar minti goma Fatima ta saki sassanyar ajiyar zuciya hade da fashewa da kuka ,rike da kafarta take fadin "na shiga uku shikenan ajalina yazo"..... A guje bilkisu ta fito daga mabuyarta jikinta jike sharkaf tayo hanyar kofa Tana lalube,waigawa takeyi gefen hagu da dama "kina ina Fatima meyasameki?meya faru?" Kuka Fatima ta Kara rushewa dashi hade da janyo jiki ta fito daga bayan kofar ta zube a kasa "ganinan bilkisu kunama ce ta harbeni" Dafe kirji bilkisu tayi hade da zaro ido cikin duhu "kunama fa kikace,munshiga uku a Ina ta harbeki" Cikin shasshekar kuka Fatima ta Bata amsa "a kafana" Ai bilkisu batayi wata wataba ta daga kasan rigarta tasa hakori ta yago dogon kyalle tayo Kan Fatima Tana lalube da hannu kasantuwar akwai duhu sosai,....Kama hannunta Fatima tayi hade da fadin "gani nan" Da sauri bilkisu ke zare Dara daran idanuwan Nan nata ta shiga nada Mata kyallen a kafar tanayi Tana daurewa tamau,yayinda azaba da radadi ke Dada ratsa sassan jikin Fatima ga karkarwa da jikinta keyi Nan da Nan zazzabi Mai tsanani ya rufeta.... Kallon bilkisu takeyi da rashin fahimtar wanan dauri da taiwa kafarta tamau "bilki kin dauremun kafa Tana karamun zugi da azaba Mai hakan ke nufi" "Kiyi hakuri Fatima hakan shine mafita kafin safiya Domin k'arinta bazai rinka Miki yawo a jikiba kinji ki daure zuwa safiya musan abunyi" Murmushi Fatima tayi hade da Jan majinar hancinta "abunyi kawai mu gudu na gaji da wanan azabar nagaji da wanan masifar"hawaye na Dada gangarowa a idanuwanta.... Cikin tausayawa bilkisu wadda itama zuwa yanzun ta karaya da wanan lamari Wanda tun kafin aje ko Ina masifa ta ishesu tace"ki kwantar da hankalinki Fatima wuya Bata kisa sai kwana ya Kare" "Idan wuyar Bata kasheni ba ai ta wahalar Dani ko bilki,gaskiya nagaji bazan iya jure wannan masifar ba tun Ina kubuta watarana zaayimun abinda zai nakastamun rayuwa" Hawayen da bilkisu ke boyewa su suka zubo Mata tasa hannu ta share "kece fa kike fadamana cewa bawa baya taba wuce kaddararsa,sanan bawa baya taba samun cigaba a rayuwa sai ya hadu da kalubale kala kala.....haba fati karki karaya Allah daya haliccemu Yana sane dake Wanda dik wuyar da kikasha kina jarinta zuwa yanzun ya rayaki kika girma da ranki da lafiyarki shi zai duba lamarinki"... Kuka Fatima takeyi Babu kakkautawa ga rawar sanyi da takeyi jikinta yayi zafi rau tamkar an hura wuta.....bilkisu ta nemi jikin bango ta jingina hade da lumshe idanuwanta wasu hawaye masu zafi suna gangarowa..... Kiran sallahr farko na asuba karfe hudu da rabi ya farkar da bilkisu wadda ke jingine tana baccin karfin hali....a firgice ta farka hasken farin wata ya wadata dakin,mikewa tsaye tayi Tana kakkabar kayan jikinta.... A gaggauce tazo daidai kunnen fatyma ta Rada Mata "Bari inje Kar a Gane baa daki na kwanaba idan na tabbatar kowa ya farka zan wayance zan dawo kinji?" Gyada Mata Kai kawai Fatima tayi Banda zugi da azaba Babu abinda kafarta keyi,bazata iya furta ko kalma dayaba sabodda yadda jikinta ya zuge da zazzabi.... ********* Tafe take Tana adduar Allah yasa Babu Wanda ya ganta,...kicibis sukayi da yarima ya fito daga bangarensa zaije masallaci ya rage lokaci saboda bacci daya gagaresa, Idan ba idonsa keyi Masa gizo ba to tabbas waccen yarinyar dake tahowa bilkisu ce daga wancan mugun dakin na tsohuwar ajiya,tafe yake Yana sake sake ita ko sai waige waige takeyi har suka hadu, Saida gabanta ya fadi ganin mutum da farar jallabiya a gabanta Dan batasan da dahowarsaba,....zubewa tayi a gabansa "barka da tashi ranka ya dade".... Kallon tuhuma yake binta da idanuwansa da suka canja kala zuwa launin ja saboda kukan da yaci a Daren jiya Yana rokon Allah... "Me ya fito dake daga can daki?me kikajeyi?" Jikinta na tsananin rawa tace"umm...ammm..dama aiki aka Sanya Fatima tun safiyar jiya muke kwasar Kaya tare to shine Bata gamaba har dare naje na zauna tare da ita" "Me kikace?bilkisu kinsan me kike fada kuwa a wancen dakin kuka kwana?dakin da manyan maza barada jarumai ke tsoron shiga saboda mugayen kunamu da macizai da iskoki dake ciki kike nufin kuka kwana" "Ehh Nan muka kwana yanzun haka ma faty Tana ciki kunama ta cije...." Ai kafin ta karasa ta.. din yarima yayi wani irin zabura ya juya a guje ya nufin dakin..... Kallo bilkisu tabisa dashi cikeda tausayi ta Mike ta nufi hanyar cikin gida Dan idan har ta koma tabi bayan yarima to tabbas asirinsu zai tonu batada zabin daya wuce ta lallaba ta shige ta kwanta.... Banko kofar yarima yayi Yana huci ,Tana ganin haka ta zabura hade da zaro ido tanajan jiki baya,ganin mutum da farar jallabiya ya Kara tsinkar Mata da zuciya..... Gadan gadan ya shigo yayo kanta Yana fadin "bintu?nine yarima ki kwantar da hankalinki?Babu abinda ya sameki?menene" Rushewa da kuka tayi tanayi Masa nuni da kafarsa Wanda sai lokacin idonsa ya sauka Akan kafarta wadda tafara kumbura "innalillahi wa Inna ilaihi rajiun"...shine abinda ya furta a Fili da sauri yasa hannunsa ya sunkuceta a kafadarsa ya fito....a guje a guje yayi bangaren sa da ita batare da kowa ya gansuba.... Bai sauketa a ko inaba sai Kan babban gadonsa,yasa hannu ya cire jallabiyar jikinsa data bacci da datti da kurar dake jikin Fatima yayi jifa da ita, Bathroom ya fada ya dibo ruwan zafi a Yar roba ya dauko towel yasa ciki ya zubo detol Dan kadan yazo bakin gadon,da hannunsa ya warware daurin da bilkisu tayiwa Fatima ga kafar Nan ta kumbura tayi jajir ya tsoma towel din ya shiga Danna Mata ai wata gigitacciyar Kara data saki yasa yayi watsi da robar ruwan zafin yayo kanta,ya janyota jikinsa ya rungumeta tsammm Yana shafa bayanta Tana kuka sosai "Dan Allah karka samun ruwan zafi ka taimakamun Dan Allah mutuwa zanyi Karin Nan Yana yawo a jikina" Tausayinta ne ya lullubesa ya Kara rungumeta sosai a jikinsa yajin sautin kukanta dake fita dakyar saboda wahala...baisan lokacinda shima hawaye ke dugowa a idanuwansa ba,ya Dan dago kanta ya sumbaceta a goshinta.....idanuwanta a lumshe hawaye na gudu Kallo ya kure fuskarta dashi yadda hawaye ke gudu a idanuwanta,fuskarta tayi jajir saboda tsabar kuka bakinta ya bushe kayau tamkar ta shekara bataci wani abuba....rungumeta ya karayi a jikinsa yasanya yatsansa Yana zagaye lips dinta dashi.... Ganin tayi shiru ya shimfideta Kan pillow,ya sauko ya shiga toilet ya dauko mopper da kansa ya goge inda ya barar da ruwan anata kiraye kirayen sallar asuba....ya dauro alwala ya kasa zuwa masallacin saboda tsabar tausayinta....dadduma ya shimfida ya tada sallah har ya idar idanuwanta na Nan a lumshe Amma yasan ba bacci takeyiba tsabar azaba ce.... Drawer jikin gado ya janyo ya Ciro paracetamol ya ballo ya dauko ruwan swan dake gefen gadonsa yazo da kansa ya tallabota jikinsa,...hannu tasa ta zagawo ta bayanshi ta kwantar da kanta a kirjinsa dik idanuwanta a rufe.... Daidai fuskarta ya sunkuyo yana Jin sautin futar numfashinta Mai zafi da alamar zazzabi takeyi ya furta a hankali "bintu Dan bude idonki kinji Kisha wannan maganin zai rage Miki radadi" Bude idanuwanta tayi ta saukesu Akan nasa idon ta Dade Dana kallonsa sanan ta turo baki ta makale kafada "nifa banason magani" Daidai fuskarta ya kusanto da bakinsa yana Mata Rada"sai allura?" Da sauri ta shiga girgiza Kai "ah ah banaso"....murmushi yayi ya shafa fuskarta "to me kikeso babyna?" "Ni bakomi" "Yi hakuri Kisha maganinki kinji zakiji Dan sauki kafin yanzun inkira doctor Ahmad ya dubamin ke" Dago Kai tayi ta Bata fuska tamkar zatayi kuka "Amma dai bazaimun allura ba ko" Kallonta kawai yakeyi yadda take shagwaba Tana shigewa jikinsa shikadai yasan me yakeji....zuciyarsa ke ayyana Masa inama matarsa ce?yau da har wanka zaiyi mata😨🙆🏻(kuji yarima da dangaga".... "Kisha ba abinda zaiyi Miki bazan bariba" Baki ta bude ya zuba Mata maganin hade da sa Mata bakin gorar a baki ta shiga Shan ruwan Nan babuji Babu gani dama kishi takeji...shiko kallonta kawai yakeyi cike da tausayawa....Saida Tasha Rabin gorar ya janye ya kashe Mata ido "karki shanye kiji fitsari Dan Babu Mai kaiki bayi" Turo baki tayi hade da Dan harararsa '"kaifa"....ta cije lebenta saboda azabar da takeji a kafarta.... Yana lura da yanayinta yasan tanajin jiki Domin cizon kunama Babu Dadi....Yana rungume da ita idanuwanta a rufe yaji saukar numfashinta ya canja alamar tayi bacci...a hankali yaja jikinsa daga nata yasa pillow ya kwantar da ita ya fada toilets Dan yayi wanka..... Har ya fito Tana bacci yadan kalleta yaga yadda minti minti take sauke ajiyar zuciya,wardrobe ya bude ya Ciro kananan kayansa ya sunyi matukar karbar jikinsa ya feshe jikinsa da turare ya fice ya janyo kofar... ********* Dik inda ya suce kuyangi da bayi na gidan ke famar tsegumi na baaga Fatima ba tun jiya,Kuma har wajen masu gadi anje sunce basuga fitarta ba.... Sashin mahaifiyarsa ya nufa Nan ya gaisheta bayan sun gaggaisa har ya Mike zai fita ta tsaidashi "Wai kasan abinda ke faruwa kuwa?" Da sauri yarima ya girgiza Kai Yana kallonta, "Wai wanan yarinyar ce baaganta ba Fatima,tun jiya da Rana naji su hajiya sun aika kiranta Babu ita to kowa ya dauka Tana bakin aikintane Amma har safe baagantaba kasan hakkinta na wuyanmu fa dole asan makama" Murmushi ya kubucewa yarima yace a ransa "Ashe dai kinasonta"...canja fuska yayi zuwa tsananin damuwa yace "Tana Nan mama Amma Babu Wanda yasan inda take" Wani kallo ta wurga Masa "kaika saceta kenan" Cikeda ladabi ya Soma magana "mama yarinyar Nan fa kunama ce ta harbeta" Da sauri mama karama ta ce "innalillahi yanzun Tana ina?,...sai Kuma ta wayance daga kidimewar da tayi tace"Allah ya kyauta saika kaita wajen malam ya'u ya dubata kasan anbashi daki gidan waziri" Sarai yarima ya lura da basarwar da mahaifiyarsa tayi yasan halinta Sarai yasa shima yace "to shikenan Amma mama kiyimun alfarmar Kar kowa yaji anganta har saina kaita an duba kafar na dawo da ita" Harararsa tayi hade da kada Kai kawai..... ********* A dakin hajiya babba ya tarar da ita cike da farin ciki,bayan sun gaisa sama sama ta amsa Masa gaisuwar.... "Algungumi to Yar daka kawo ta gudu inace kaji labari" "Naji hajiya Amma Ina kyautata zaton Tana cikin gidan Nan tunda masu gadi sun sanar Mana da cewa baaga fitarta ba sanan katangar gidan Nan tayiwa Fatima tsawon da zata haure" "Kaidai kasani yau saika tanadi karyar da zakayiwa Mai martaba,Domin yau yace zai Yankee hukunci Kuma Yana bukatar kowa da kowa daga Kai har deejahmar zakuzo fada har ita Fatima dazun ya fadawa sarkin fada yazo yake sanar mun" "Allah yasa a ganta"yarima yace hade da sunkuyar dakai.. "Ba Amin ba bakar jaraba Allah ya Kara kadata"... Murmushin gefen kumatu kawai yarima yayi batare da yace uffan ba ya Mike ya fice,hajiya babba ta bishi da harara... Yana fita ta sheke da dariyar mugunta,Allah yasa bayan fyade da isyaku yayi Mata ya kasheta uban kowa ma ya huta,....wayarta ta janyo ta Kira hajiya rahina ta sanar Mata da sakon Mai martaba da abinda ta faru sukai sallama..... ********* Murna a wajen deejahmah baa magana jin labarin Fatima ta bace baagantaba har rawa Saida tayi burinta ya cika a cikin ruwan sanyi..... Ji takeyi tamkar ta janyo bayan sallahr laasar suji Mai sarki zaice yake nemansu?minti minti take sauke murmushin Jin Dadi... ******** Yarima Yana fita direct gidan Ahmad yaje ya daukosa ya sanar Masa da abinda ya faru saboda haka a gaggauce suka dawo gidan ko sashinsu hajiya Ahmad be jeba direct sashin yarima sukaje.... A durkushe ya tarar da Fatima a kasa gefen bayi tayi zufa sharkaf Tana yarfe hannu da sauri yayi kanta "menene Fatima?" A wahale ta bude baki tace"bayi zan shiga cikina ke murdawa gashi kafata tamun nauyi" Kinkimarta yayi ya shigar da ita bayin ya fito ya janyo Mata kofa suka koma parlor shida Ahmad.... A furgice Fatima ka kallon cikin toilet din ganin zawon da tayi ya canja kala zuwa jini jikinta ya hau rawa tasa ruwa tayi flushing ta daddafa bango ta fito dik a tsorace take menene wanan ya fito a cikinta ?...kashin jini?....meyasameta? innalillahi shi kawai takeyi.... Jin karar fitowarta yasa yarima shigowa bedroom din da sauri yaganta zaune gefen gado tanata zufa ga kuka tanayi "menene Kuma bintu?kafarce?" A shagwabe tace"jini nagani kashin jini nakeyi"... Waigowa yarima yayi Yana fadin "friend zokaji Wai kashin jini tayi" Da sallamarsa Ahmad ya shigo Yana murmushi "ka kwantar da hankalinka sharrin cizon kunama ne Karin ne yake fita ta bayan gida tayi arziki already nazo da allurar da zanyi Mata takara samun sauki" Ai Fatima najin zancen allura ta fashe da kuka Tana fadin "wallahi na warke tunda k'arinta ya fita Dan Allah karkamun" Tausayinta ya lullube yarima ya riketa da kyau Yana fadin "Babu zafi nine zan rikeki a hannu zaiyi Miki ma daidai tsoka kinji" Kwantar da Kai tayi a kafadarsa Tana shasshekar kuka haka ya juyar da ita cikin dabara aka tsira Mata allurar,sai kuka takeyi Tana shagwabewa a jikinsa shiko Yana aikin lallashi... Fita yayi yakira bilkisu cikin gida ya Bata umarni da ta kawo musu abin karyawa.... Baafi minti gomaba saiga bilkisu dauke da tray hannunta daya rike da flask ta shigo sai zare Ido takeyi Ahmad Yana ta daddana waya yarima na gefensa, Darewa Ahmad ya sheke dashi Yana kallon bilkisu dake wurga idanuwa....da sauri yarima ya juyo yaga dariyar me Ahmad keyi shi kansa yadda bilkisu keyi da idanuwa ga uban datti tayi Saida yadan murmusa ta gefe... Daure fuskarta tayi ta gefe ta kalli Ahmad dake dariya,wani kululun bakin cikine ya tsaya Mata a kirji Tana ajiyewa ta yi hanyar kofa"ke bilki karki nisa kijirani kofar sashina zan nemeki" Takaicine ya lullubeta na dariyar wulakancin da Ahmad keyi Mata yasa dakyar ta bude baki ta amsa a ciki ta fita ta rufo kofa garammmm Kallon juna sukayi shida Ahmad sukai dariya "kasan Allah abokina kadainawa kanwata dariya Dan kaganta haka?jarumace" Dariya sosai Ahmad yayi sanan ya tsagaita "wallahi rigar jikinta ce tabani dariya kamar wata Mai daddawa ga idanuwanta Dara Dara sai zaresu takeyi" Shidai yarima bece komiba da kansa ya hada tea ya shige daki ya nemi gefen gado ya zauna ya ajiye cup din a gefe yasa hannu ya tallabota ya rike ta dakyau ya Mika hannu ya dauko kofin tea din da kansa yake Bata da cokali Yana hura Mata tanasha harta koshi,....sai zufa dake karyo Mata.... Ganin haka ya Sanya hannunsa ya shafo wuyanta yaji Babu zazzabi sanan ya kashe Mata ido "yanzun Kinga kin koshi saikiyi wanka ki shirya domin Mai martaba na nemanmu a fada" Da sauri ta kallesa ya daga Mata gira daya hade da murmushi ya kashe Mata ido daya..... "Nidai gaskiya bazanjeba" "sai a fadawa sarki sakonki na bazakijeba" "Nidai ah ah "ta makale kafada... Dariya yakeyi Yana kallonta,kwalla sun ciko a idanuwanta yasa hannu yaja hancinta ya ce "maza ki gasa jikinki Bari muje mudawo nida Ahmad" Ya Mike ya fice a binsa ta bishi da kallo.... ******** Isowarsu deejahmah yayi daidai da fitarsu Ahmad a mota daga gidan... Murna sosai deejahmah keyi na Jin labarin abinda ya faru ....tarasa inda xata tsoma kanta sai wani rawan Kai takeyi Tana nishadi.... Suna zaune suna Yar hirarsu da hajiya babba akayi sallar laasar,dukkansu babu Wanda ya Mike Domin yin sallah saima tattaunawa sukeyi Akan abinda deejahmah zata fadawa Mai martaba....haka sukai shiri tsab suna haramar zuwa fada..... Saida akayi sallah sanan yarima ya shigo masarautarsu a gaggauce yayi hanyar zuwa fadar sarki don yayi latti.... *Muje zuwa* *SLIMZY✍🏼😍*🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* 29 A gaggauce ya shigo fadar da sallamarsa a bakinsa ya karaso deejahmah dake gefe gabaki daya ta maida hankalinta akansa Dan ba karamin kyau yayi Mata ba da kwarjini,ta manta shaf a inda take har ya zauna Tana binsa da wanan mayen kallon Wanda har uwarta dake gefenta Saida ta Dan zungureta cikin rada tace Mata "ki natsu Mana karki bada kanki".....a hankali ta sunkuyar da kanta hade da wayancewa ta fara Wasa da yatsun hannunta,yayinda zuciyarta ke Kara azalzalarsa da ta dago kanta ta kalleshi ko Allah zaisa su hada ido Amma tabbas idan tayi hakan to kowa zai ga maitarta a Fili......ta rasa dalilin dayasa matukar kabir Yana waje to Tana neman natsuwarta ta rasa ta kasa gasgata abinda zuciyarta ke fada Mata na ta fada tarkon sonsa,....idan kuwa haka ne zuciyarta batayi Mata halarciba Domin Koda Tana sonsa bazata janye kudurinta na daukarwa habeeb fansa akansa ba.....ajiyar zuciya ta sauke sassanya wadda tayita ne a dalilin maganar Mai martaba data dawo da ita daga duniyar tunanin data afka na wucin gadi.... Gyaran murya Mai martaba yayi yau fuskarsa Babu yabo babu fallasa a bisa alamu yau din Nan sarki Yana Jin sarautar,kasaitar Yan maza ta motsa shi kansa dakyar ya motsa labbansa yayinda ya maida dubansa ga waziri dake gefe yace "waziri ka bude Mana taro da addua"....Nan take babu Bata lokaci waziri ya cika umarnin Mai martaba ta hanyar yin addua kamar yadda ya umarcesa hade da shafawa da salatin annabi (s.a.w)..... Shiru fada tayi kowa da sake saken da yakeyi a zuciyarsa gyaran murya Mai martaba yayi sanan yace "nataraku a Nan ne a bisa dalilai biyu zuwa uku Amma kafin in zartar da hukuncin sai na tabbatar da kowa Wanda keda hakki a taron Nan Yana wajen Nan" Shiru ne ya biyo baya Babu Wanda yace komi sanan Mai martaba ya cigaba da magana "kabiru Ashe abinda ya faru kenan?" Rasss gaban yarima ya yanke ya fadi Domin be fahimci inda maganar Mai martaba ta dosaba,Amma sai ya Dan gyara Zama cike da biyayya da ladabi yace "Allah ya baka yawan Rai ban fahimci maanar maganarka ba" Jinjina Kai Mai martaba yayi sanan yace"wani mugun labari ne yasameni dazun jakadiyyata ke sanar mun da cewa an nemi yar Amana an rasa ta gudu,maana Yar daka daukota ka kawota gidan Nan a matsayin Yar riko Wanda taron Nan musababbinsa saboda Kai da ita ne da Kuma Khadija" Wata xuface ta ke karyowa yarima Wanda ya Gama shiga rudani a maganar Mai martaba ta farko ,kansa a kasa ya Kara gurfanawa "Allah ya baka yawan Rai Babu inda Fatima taje Tana cikin gidan Nan yanzun haka".... Da sauri hajiya babba ta kallesa tayi maxa tace"maganar banza kakeyi bayan Babu inda baa dubana baaga yarinyar Nan ba har cikin tsohuwar rijiya an leka babu ita,karya kakeyi saidai idan nemanta zaka fitayi ka fakeda Tana Nan to idan gaskiya ne ai taron harda ita akace zaayi Tana Ina?" Shiru yarima yayi batare da yace komiba,kansa na sunkuye a kasa ya tsinkayo muryar Mai martaba na fadin , "Dakata hajiya dik maganar Bata fada ko hayaniya bace,Nasha fada Miki da banaso idan kinamun magana kinamun hayaniya" Jiki a sanyaye hajiya babba ta sunkuyar da Kai itama sanan tace "Allah ya huci xuciyar Mai martaba".... Juyawa yayi ga yarima ya cigaba da magana "kabiru kace Tana gidan Nan,gashi ance an duba Babu ita meye gaskiyar lamari" "Ranka ya dade kunama ce ta harbeta jiya daddare yau da asuba na fito zanje masallaci na gamu da ita zatayi alwala kafarta a daure shine na dauketa na kaita gidan waziri wajen malam ya'u ya yi Mata addua dagacan na kaita asibiti yanzun haka Tana waje nace tabari a Bata umarnin shigowa" Kallon juna hajiya babba da rahina sukayi sanan suka jinjina Kai ko wanne ya maida kansa kasa ya sunkuyar.... "Na baka umarni a shigo da Fatima".... Durkusawa yarima yayi 'nagode ranka ya dade"....sanan ya Mike a nutse yayi hanyar waje.....wani mugun kallo hajiya babba ta bishi dashi har ya fita, Fatima na tsaye jingine da jikin kofar shigowa kirjinta sai bugawa yakeyi ji takeyi tamkar ta gudu Bata kaunar abinda zai hadata da wadanan mutanen ,Bata ankaraba taga mutum a gefenta tsaye Yana binta da kallo don Harga Allah yayi tunanin ganinta a cikin muguwar Kama Sai ya ganta sanye da dogon hijabinta har kasa Babu wata alama da zata nuna Tana bauta a gidan ajiyar xuciyar daya sauke ita ta Sanya ta juyowa a furgice ai Tana ganinsa Taji tamkar ta saki fitsari, Ganin yadda ta tsorata yasashi daure fuskarsa tamkar be taba dariya ba ya Mika hannunsa ya damki kunnenta ta cikin hijabi a gaggauce yace "Saura idan kin shiga ki kasa cewa komi kiyi kuka wallahi saina Bata Miki Rai".....zafi ne ya isheta ta tura baki gaba batare da tace komiba ya saki kunnen yayi Mata wani kallo yace "muje ciki"....ya fadin haka ya juya tabishi a baya dakyar take taka kafafuwanta haka suka yi sallama a tare suka shigo Tana dingisa kafarta wadda ta kumbura tayi suntum..... Tunda ta shigo yadda take takawa kowa ya bita da kallo har deejahmah wanan karon haka take watsa Mata kallo Mai cike da tsantsar tsana da kyama, Jiki na rawa Fatima ta nemi can gefe ta tsugunna a hankali Tana cije kafa saboda yadda kafarta keyi Mata azaba, Kallonta Mai martaba yayi tausayin yarinyar da kaunarta ya darsu a zuciyarsa take tun rananda ya fara ganinta ya fahimci cewa yarinya ce Mai hankali da natsuwa,tunda aka fara wanan Zama Mai martaba baiyi murmushiba sai yanzun daya kalli Fatima wadda kanta a kasa yake yace "tahonan ya'ta ki zauna kusa da Yar uwarki Khadija"..yayi Mata nuni da gefen da deejahma ke zaune zuciyarta na harbawa sauri da sauri,....jiki a sanyaye Fatima ta Mike Babu musu ta dingiso kafarta ta dawo gefen deejahmah ta zauna Akan kafarta ta sunkuyar da kanta gabanta sai tsananin faduwa yakeyi,idanuwanta farare Tass ta dago ta kalli gefen da deejahma ke zaune Kai a sunkuye Aiko kamar hada baki suka hada ido,wani irin kallo deejahma ta watsa Mata kallon zamu hadu,Saida hantar cikin Fatima ta kada cikinta ya shiga murdawa tamkar ta saki zawo a inda take.....gyaran muryar Mai martaba itace ta saita tunanin kowa a wajen Wanda kowa ya maida hankalinsa Akan abinda Mai martaba zaice.... "Da farko dai ba wani abubane ya taramu a Nan face Akan magana muhimmiya wadda kabiru ya gabatar a zaman daya gabata Wanda na bada umarni Akan zan yanke shawara,.....kabiru ya gabatarmun da magana Mai muhimmanci Wanda a farko ban dauketa da muhimmanciba Saida na zauna nayi tunani na auna maganarsa da bukatarsa ta auren Fatima a karo na biyu,.....to nayi tunani na auna Naga cewa tabbas abinda yake shirinyi tabbas abune Mai kyau kuma jihadi ne gareshi damu baki daya,a bisa hakan ne yasa ya yanke hukuncin amince Masa da ya aureta a karo na biyu na yarda na amince dari bisa dari Domin nasan tabbas kabiru zaiyi adalci a tsakaninsu Domin nasan halin abinda na Haifa"...... Shiru tamkar anyi ruwa an dauke a wajen.....Babu Wanda ke iyayin motsin kirki tunda Mai martaba ya Soma magana.....bedamu da hakanba ya cigaba da maganarsa, "Saboda haka na yanke shawarar aurawa kabiru wanan marainiyar Allah bayan ya auri Khadija da Dan lokaci,yin hakan shine adalci ga ita khadijat Domin da badan haka ba hada auren zanyi,Amma bayan kabiru ya auri Khadija ni zan sa lokacin aurensa da Fatima,wanan hukuncin shine abinda na yanke akan bukatar da kabiru yazo da ita,sai abu na biyu shine daga gobe insha Allahu zan wakilta waziri akan sabon ginin da zaayi a babban filin dake can gefen gidan Nan Wanda zai Zama a Nan ne kabiru zai zauna da matansa ,irin ginin da kakeso kabiru zaka iya samun waziri kuyi magana bayan taro ya tashi" Bakin yarima yakasa rufuwa yakasa boye farin cikinsa,yanan durkusa "nagode ranka ya dade Allah ya Kara girma da daukaka,Allah ya Kara maka lafiya da nisan kwana" Jinjina Kai Mai martaba yayi sanan ya Dora da "Fatima Ina fatan hukuncin da muka yanke akanku keda kabiru kin gamsu Zaki amince da hakan?"...kallonta Mai martaba yakeyi cikeda tausayawa.... Dakyar ta iya farfadowa daga sumar zaunen da tayi ta motsa bakinta a hankali ta Soma magana"Allah ya baka yawan Rai banida iko da zan ja da hukuncinka Koda hukuncin kisa ka yanke mun,ballantana kasancewa ka adalin sarki uba a gareni kayimun zabi in iya bude baki ince bana son wanan zabin,hakika Kai adalin sarkine Mai kaunar al'ummarsa da ace duka sauran masu mulki haka suke da irin halayyarka da sai mu kirasu da Yan aljannah,....na daukeka tamkar uban daya tsugunna ya haifeni saboda haka dik hukuncin daka yanke akaina daidaine mahaifina"..... Hakika zancen Fatima ba karamin Dadi yasanya Mai martaba ba, yarinya ce Mai cike da ladabi da hikimar iya magana,wadanan kalamai datayi sunkara sa Mata tsantsar kaunarta a cikin zuciyarsa jinta yakeyi tamkarsu khausar da afnan,shi kansa Mai martaba murmushi yaki gushewa daga fuskarsa sai jinjina Kai yakeyi alamar Jin Dadi yace "Allah yayi miki albarka Yar aljannah" Ta Kara durkusawa cike da ladabi tace'ameen ranka ya dade nagode Allah ya Kara maka lafiya da nisan kwana".... Jinjina Kai kawai Mai martaba yakeyi Yana murmushin Jin Dadi sanan ya juya ga matansa dake gefe ko wacce kanta a kasa yake Tana sake sake... "Idan akwai wata Mai abin cewa zata iya magana kofa a bude take" Dago Kai hajiya babba tayi fuskarta a daure tamkar Bata taba dariya ba zuciyarta tafarfasa kawai takeyi wani kululun bakim cikine dankare cikin zuciyarta takasa boye hassadarta a Fili idanuwanta sun kankance dakyar ta bude baki tace"ka rigada ka yanke hukunci bamuda yadda zaayi muja da hukuncinka ranka ya dade Amma tabbas an cutar da Khadija da mahaifiyarta a wanan tafiya Amma Babu komi akwai Allah idan ma akwai wata makarkashiya da akeyi,to ko ba dade ko ba Jima zaayi walkiya asirin kowa saiya Tonu wallahi" Harta Dora Aya Akan xancenta Mai martaba idonsa na kanta Saida tayi shiru Sanan ya Bata amsa da "naji maganganunki hajiya Amma fa kisani ban taba yanke hukumci na warware wannan hukuncin ba Saida kwakkwaran dalili saboda haka maganar da kike fadin an cuci rahina da yarta,ita raheenar Naga Yar uwatace jinina ce kuma inada damar da zan Yankee hukuncin dik da nagadama akanta da di'yanta bata Isa tayi maganaba saike to dik abinda kikaga yadace kuyi keda raheenar" "Allahhh ya huci zuciyar Mai martaba"....cewar waziri dake gefen sarki Yana sauraron komi..... Shiru ne ya biyo baya na Dan lokaci ganin Babu Wanda zaice komi Mai martaba yabawa waziri izinin rufe taro da addua,Babu Bata lokaci waziri ya kawo Fatiha da salatin annabi taro ya tashi......kowa ya shiga mikewa jiki Babu kwari Ana fita daya bayan daya,Saida kowa ya watse sanan Fatima ta Mike Tana dingisa kafarta ta fice,tafe take jikinta a sanyaye zuciyarta ta karye,Bata taba tunanin hukuncin da Mai martaba zai yankeba kenan dik tunaninta ya Kare Akan zaisa a koreta a gidansa,sai gashi yayi bazata,yau itace Fatima zata auri Dan sarki?Kuma sarki a Nan gaba?Allah buwayi gagara misali kenan.....ajiyar zuciya ta sauke data tuno da babban bala'i dake tunkarota.....tabbas tasan akwai yaki babba a Nan gaba...tafe take Tana tunani har takaraso kofar shiga sashen cikin gida Wanda Dole ta babban parlor zata wuce jikinta na rawa zuciyarta na dar darr haka ta shigo bakinta dauke da sallama a zuciyarta Kuma Babu abinda take janyowa sai innalillahi wa Inna ilaihi rajiun..... Cirko cirko suke tsaye cikin parlorn deejahmah ce jingine Tana faman rusa kuka tamkar an Aiko Mata da mutuwa a haka Fatima ta shigo cikin parlon zata wuce Taji muryar hajiya babba cikin daga murya "keeee"....cakkk Fatima ta tsaya tsaye zuciyarta na harbawa sauri da sauri....Bata ankaraba Taji an fizgota da hijabin dake jikinta an nannadeta hade da shake Mata wuya deejahmah ce a haukace "wallahi baki Isa ki auremun mijiba kina baiwata,baki Isa ki shigo gidan Nan kice zakiyi kishi Dani ba a matsayinki na kucaka renon titi tsintacciya,wadda akayi cikinta a kwararo aka wurgar da ita a bakin hanya".....duka deejahmah take kaiwa Fatima ta ko Ina,a zuciye ta hankadeta kasa ta Fadi take idonta ya sauka Akan kafar Fatima dake kumbure tadanyi baki cikin zafin nama deejahmah tasa kafa ta take kafar..... wata gigitacciyar kara Fatima ta saki saboda tsananin azabar da ta ratso kwakwalwarta xuwa tafin kafarta.....ganin haka yasa deejahmah ta Kara take kafar......shiru Fatima tayi hade da lumshe idanuwanta azaba na ratsata ta ko Ina wani hawayene ya gangaro ta gefen idonta Tana ambatar sunan Allah a bakinta...... network din kanta gabaki daya ya dauke idanuwanta suna rufe hawaye na gudu.... Takowa hajiya babba tayi har inda Fatima ke kwance ta tsaya akanta....."wallahi tallahi sai kin gwammaci Harbin kunama dik second goma akan zamanki cikin wanan gidan,sai kin gwammaci haka kabari ki binne kanki da kanki zaifi Miki sauki Akan gigin auren kabiru da zakiyi.....azabar da kikasha a farko kadan ce akan wadda zakisha Nan gaba wallahi tallahi matukar kikace Zaki cigaba da zaman gidan Nan nayi Miki alkawarin nadama"... Juyawa hajiya babba tayi ta nufi sashinta yayinda hajiya rahina da deejahmah suka rufa Mata baya.... ******** "Wai malam yau Ina kajene bayan laasar na shigo dakinka na tarar bakanan na leka windon baya na hangeka Kanata sauri kayi Nadi sai nai tunanin ko fada kaje".... Ludayin furar da waziri ya dibo yakai baki Saida ya kurba sanan ya ajiye,ya canje kwanon silvar da yakeshan furar dashi gefe,Saida ya hadiye furar dake bakinsa sanan yasa hannu ya shafa gemunsa yayi shiru na Yan dakiku sanan yayi ajiyar zuciya yace "kaiii innar fauziya yau Mai martaba yayi wani abinda ko a mafarki bantaba tunanin hakan zai kasance ba" Gyara Zama matar waziri tayi Tana fuskantarshi sosai "malam fada kaje kenan meyafaru?wani Abu yasamu masaraunta ne?" "Rigima ce dai Nan gaba kadan zata balle Domin Mai martaba ya amincewa kabiru da ya auri yarinyar Nan data kashe habibu,wadda rukonta yanzun haka a gidan akeyi' Zaro ido Inna tayi waje Tana kirkida Kai "tabdijan lallai Mai martaba ya Dasa bomb dinda idan ya tashi fashewa hardashi zai fashe"ta cigaba da jinjina Kai take fuskarta ta sauya zuwa tsananin hassada da bakin ciki,Tana jujjuya Kai Tana jinjina lamarin sanan ta sauke ajiyar xiciya ta cigaba da magana "yanzun ya maganar auren deejahmah da kabiru " Sauke hularsa yayi gefe wadda yayi Nadi da ita sanan yace "ehh to maganar na Nan Domin Nanda sati uku zaayi bikin da Mai martaba ni yaba kwangilar ginin gidan da khadeejah zata zauna da ita kanta fatimar kinsan gidan nasa akwai girma da fadi Dan na tabbatar zaa iya Gina gidajen sama biyar ma zuwa bakwai Nan gaba" Murmushi kawai innah keyi na karfin Hali ita kadai tasan abinda yake boye cikin birnin zuciyarta,Domin dik maganganun da mijin nata yakeyi sauraronsa kawai takeyi zuciyarta na can wani waje daban..... Faizah da fauziyya wadanda kamaminsu suka baci da juna suke zaune cikin dakinsu suna zancensu na Yan Mata , "Nikam fauziyya kinsan wani Abu?" Dago Kai fauziyya tayi daga kwancen da take Tana faman chat ta kalli Yar uwar Tata tace"umhmm Ina sauraronki meye Kuma?" "Wallahi Harga Allah Ina kaunar wanan fatimar,ni Dan inajin tsorone da wallahi na rinka zuwa wajenta Ina Bata taimako don Allah ya hadata da kajaga,zan kulla kawance da ita" Wani malalacin murmushi fauziyya tayi sanan ta yunkura ta zauna ta watsawa Yar uwarta harara "to kwadayayya,kinji labarin zata auri Dan sarki kenan shiyasa zakije ki fara manne Mata tun yanzun?" Murmushi faizah tayi wadda ta kasance itace hassana tace"wanan ke ya dama ni bedameniba kece dama kike sonsa ni be taba burgenba ita Kuma da kikaji nace Tana burgeni Harga Allah Ina kaunarta ne" "Ki tattara kayanki ki koma gidan kuyi bauta tare karewar kauna kenan mtsww" Dik hirar da sukeyi mahaifiyarsu na tsaye Tana sauraronsu,Domin ita kanta abin ya dameta tunda waziri ya sanar Mata zuciyarta ke yi Mata saka da warwara Akan yakin biyu zai zame Mata Amma na Fatima me saukine Dan ba power garetaba kamarsu deejahmah saidai batasan hanyar da zatabi ba tayi yakin Fatima Dan Dole Saida Wanda Fatima ta yarda dashi,inko haka ne faizah na kaunar Fatima to ita da fauziyya zatayi amfani tunda kamarsu daya sakkk har maganarsu iri daya ne Kaya iri daya suke sawa Dole zatayi amfani da wanan damar wajen yiwa Fatima Wasa da hankali......ajiyar zuciya innah tayi ta shigo dakin da faraarta dauke da fuska wacce iya lebenta kawai ta tsaya, Gefen gadon faizah ta zauna Tana murmushi "Yan biyun innah zancen me akeyine Wai tun dazun ina sauraronku sama sama" Da sauri fauziyya ta karbe zancen "Wai faizah ce kecewa Tana kaunar Fatima tsintacciya"ta karasa maganar da harara... Murmushi Inna tayi "to ai Mai saukine fauziyya ki kyaleta suyi amincinsu ai kaunarta takeyi Kuma idan jininsu ya hadu ai shikenan" Murguda baki fauziyya tayi want kululun takaici ne ya tsaya Mata a wuya don me innah zatace haka?,ita kuwa faizah fuskarta ta fadada faraarta "nagode innah gobe zanje gidan"....jinjina Kai Inna tayi Tana faraa tace"hakan nada kyau,yanzun ki Mike ki hadamun dambu gashican yau malam yace shi yakesonci saura kuma fauziyya ki batamun girki in gamu dake Dan nasan halinki".... Kunkuni fauziyya ta shigayi yayinda faizah takai hannunta Kan wayarta ta janyo ta kunna karatun kur'ani ta fice ta nufi kitchen din.... Kallo innarta tabita dashi Tana murmushi,....mikewa tayi ta dawo gefen fauziyya ta janyota jikinta ta rungume Yar Tata Tana lallashinta,Saida ta tabbatar ta saukar da ita sanan ta shiga rada Mata maganganu kasa kasa,.....Nan da Nan fauziyya ta koma dariya harda kyalkyalewa......Niko Ina gefe sai zare Ido nake da kumburarren hannuna😜lol ******** "Yanzun tunda burinka ya cika friend zaka auri Fatima,to ya Zama wajibi ka cika umarnin Mai martaba nayin adalci a tsakaninsu Dan kaima da naka iskancin,Dan idan bera da sata daddawa nada wari" Dage girarsa yarima yayi sanan ya saki wani malalacin murmushi yace "wanan Mai saukine Amma kasani zuciyata kwaya daya ce tal da ruhina kuma Fatima suke kauna,wallahi bazan iya hada son wata Diya mace da son da nakewa bintu ba"....yanzun haka ita nakeson gani Domin nasan Tana can Tana kubar azaba,bedameniba tunda ko naji ciwon abun dole xan lallashi abuna" Kallon juna sukayi suka sheke da dariya hade da tafawa,dakyar Ahmad ya tsagaita da dariyarsa yace "angon Khadija da Fatima" Gira daya yarima ya daga "yason ranka dolema gobe inyi shigar burtu in burkice kamar baniba inje musha soyayya da deejahmah"ya karashe maganar da Dan murmushin mugunta... "Wallahi wanan yarinyar sonka takeyi,ta rigada takamu Domin dik haukar da takeyi Akan fati fa kishi ne bawai Dan kaddarar da ta aukawa faty bane kadai" Canje fuska yarima yayi "zata Soni nikuma zanyi amfani da wanan damar wajen ramawa Fatima takaicin da suke kunsa Mata na tanadar Mata manyan bokatai da zata cikasu da hawayen takaci a cikin gidana" Dariya Ahmad keyi Yana nuna yarima da yatsa "friend wallahi masarauta zata rikice" Dage kafadarsa yarima yayi batare da yace komiba ya janyo kofin da ya ajiye na ruwa ya kwalkwale sanan ya kalli Ahmad ta gefe "muje incigaba da jinyar amaryata".... ******** Kuka Fatima keyi Tana rike da kafarta yayinda bilkisu ke tsugunne gabanta Tana Danna Mata kafar da ruwan zafi Wanda ta dibo a kitchen batare da kowa ya gani ba... Cije labe takeyi Tana janye kafar bilkisu ta dago Kai a fusace "malama so kikeyi ki gurgunce kenan akaiwa yarima ke da kafa daya,ki tsaya a gasa Abu kina iskanci Aida gashin soyayya ne da bakiyi kuka ba"...ta watsa Mata harara... Cikin kuka Fatima ta dago Kai "ki sakarmun kafar Mana kibari yazo ya gasamun tunda dama ai aikinsa ne jinyar matarsa" Murmushi bilkisu tayi bayan ta tsomo tsumma ya Nadi ruwan zafi batayi wata wataba ta dorawa kafar....wani mugun duka Fatima takai Mata a baya "muguwa ki kyaleni wallahi kina sane kikemun wanan mugunta kibarni haka yazo ya gasamun"....takarashe maganar cike da shagwaba.. Harararta bilkisu tayi sanan ta kwashe da dariya"dama ai soyayya kece Kan Gama lailah da majnun"....ta saki tsumman a kasa "to Bari yazo yayi Miki"....ta juya tai tafiyarta,kallo Fatima ta bita dashi harta kule Bata ganinta sanan ta runtse idonta zuciyarta na bugawa sauri da sauri Babu Wanda take bukatar gani sama da yarima yayi Mata wanan lallashin da yakeyi mata.....murmushi ta sauke hade da dafe kirjinta Tana sauraren yadda zuciyarta ke harbawa.... ********* Zaune deejahmah take a gefen gadonta tana sanye da kayan bacci milki colour da bakar hula a kanta ta tura gashinta ciki,...hannuwanta duka biyu suna tallabe da habarta ta fada duniyar tunani,har mahaifiyarta da kanwarta suka shigo dakin batasaniba Saida uwar ta dafa kafadarta Tana kallonta sanan tayi waigo a furgice ta bisu da kallo.. "Deejahmah na fada Miki wanan Abu bamai yuwuwa bane ki kwantar da hankalinki wallahi tallahi Nina shiryawa wanna yaki...saboda haka karki damu kanki ki Hana kanki sukuni kisawa zuciyarki damuwa" Kallo tabi mamanta dashi fuskarta dauke da damuwa "kishi da baiwa kuyanga?,mama Dole hankalina ya tashi ki duba kigani fa yadda kawayena keyimun kamar xasu lashi tafin kafanta tunda na sanar musuda kabir zan aura ake girmamani sai Kuma a kawomin ziyara watarana aga wanan kucakar itace kishiyata wallahi na tsaneta"...ta karashe maganar hawaye na bin idanuwanta.... Gefenta uwar ta zauna ta janyota jikinta Tana shafa kanta "nayi matukar bakin cikin ganin hawaye a fuskar jarumar yata Khadija Wanda bantaba tunanin hakanba,Wai kin manta auren huce takaici xakiyi?kin manta da kudurinki Akan shi kansa yariman ne?kin manta da fansar jinin habibu da zakiyi akansa?Koko kinfara sonsa ne?"....."ba sonshi nakeyi ba bazan taba sonsa ba harabada Kuma bazan taba janye kudurina akansaba harabada,da zarar bukatata ta biya zan aiwatar da kudirina akansa"..... *Nagaji🤨....* *SLIMZY🥰✍🏼*🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* _nagode da kauna_ @ *ZAHRA MAI GARI*.... _son so_ _fisabilillahi_ 30 ******** A gurguje bayan kwanaki uku da faruwar haka kusan tunda Mai martaba ya yanke wanan hukunci Fatima ke cikin azaba dik ta rame tayi bakin Kirin, kwana uku kenan batasa yareemah a idanuwanta ba ta shiga matsananciyar damuwa wadda tunda take Bata taba shiga irintaba.... A bangaren yarima shima hakan ce ta kasance Domin kusan kullum cikin fakon Ido yakeyi ko zai ganta,saboda zamanta a gidan yasa ya mance da gidansa da yake bayan gari Wanda a al'asarsa ma can ne wajen zamansa zuciyarsa yauma sake sake kawai takeyi mishi Yana zaune ya rafka uban tagumi ya kurawa TV dake manne a bangon dakinsa Ido a zahirin gaskiya ba kallo yakeba ya fada duniyar tunanine... Yau kwana uku Fatima be gantaba ita Kuma Bata nemeshi ba me hakan ke nufi?yarinyar Nan kenan ba sonsa takeyiba dik abubuwan da takeyi mishi Tana yi Masa shine kawai bawai Tana sonsa bane ya shiga rigingimu kala kala daban daban akanta Amma ta juya Masa baya,bazai taba nemanta ba inhar Bata nemeshi ba tunda abin nata haka ne.... Mikewa yayi ya suri makullan motarsa da wayoyinsa ya zura a aljihunsa ya fice daga bangarensa har ya Miko hanyar parking space ya juya yabi side din da akeyi Masa gini... Sauri sauri ya keyi ya tsaya daga Dan nesa kadan abin ba karamin mamaki yabasa ba ganin yadda cikin kwana uku ansa foundation gini ya Mika,zuciyarsa cunkushe da takaici haka ya juya ya nufi motor park Sauri sauri bilkisu ke bin bayansa bai San da itaba ya shige motarsa yaja a guje ya bade wajen da kura....itama kallo ta bishi dashi haka ta juya jiki a sanyaye ta nufi cikin gida.... A daki ta tarar da Fatima kwance sai rawar sanyi takeyi dik jikinta Babu inda baya rawa a kwance take saman tiles Babu arzkin abinda zata shimfida ta kwanta ,gefenta bilkisu ta zauna fuskarta dauke da damuwa ta sa hannu ta taba wuyan Fatima Wanda yayi zafi rau "Fati nabi bayan Yaya besan Ina binsa ba ya shiga motarsa ya wuce dama tunda ya fito daga bangarensa Ina fakonsa inga inda zaije in sanar Masa da halin da kike ciki sai Naga yabi bangaren can da ake gini ya dade wajen tsaye sanan ya Mike wajen motoci Ina kiransa beji ba haka ya wuce" Runtse idanuwa Fatima tayi hawaye na gangarowa ta gefen hancinta masu zafi "ban taba tunanin yareemah zaimun haka ba,Saida ya samun soyayyarsa da kaunarsa sanan yake neman juyamin baya idan ko haka ne na shiga babban bala'i" Cikeda alhini bilkisu ta matso kusa da ita sosai ta kamo hannunta "kiyi hakuri ki kyautata zato akansa kila abubuwa ne suka Sha Masa Kai saboda aurensa Nanda sati biyu da Yan kwanaki ne Kinga kila akwai hidimomin da yakeyi kuma a kwanakin Nan Ina lura be shigowa sai dare kiyi hakuri" Kuka Fatima takeyi harda shassheka "tun kafin yayi aure kenan ya Soma canjamin inaga yayi aure ni danasani ma da ban jefa kaina cikin matsala ba Dan tabbas soyayya matsala ce bilki" Rufe Mata baki bilkisu tayi da hannunta "karki Kara cewa haka wallahi Yana sonki kidai kwantar da hankalinki kila yanada uzuri ne karki zargeshi kinji Yar uwata?....yanzun Bari inje Kar hajiya ta nemeni" Daga Mata Kai kawai Fatima tayi daga kwance yayinda bilkisu ta Mike ta fice a dakin Fatima ta bita da kallo har ta bace.... ******** Hajiya babba ce zaune a parlor gefenta lemon Zaki ne da ayaba Wanda bilkisu ke bare Mata Tana Mika Mata daya bangaren Kuma Mami ce kuyangarta Tana durkushe.... Kallon gefen da Mami take hajiya babba tayi "ke jeki kiramun Fatima tazo inji dalilin da yasa abinda nasata tamun batayimun shi ba " "Allah ya baki yawan Rai ai Fatima yau wuni tayi kwance a daki Tana jijjiga Wai sanyi takeji batada lafiya Kuma ninasan karya takeyi zannuwan gadon da kikasata wankewa ne Bata gada ma ba" A fusace hajiya ta dago Kai "yi sauri kiyimun kiranta" Da hanzari Mami ta Mike ta fice,....batafi minti biyar da fitaba sai gata ta shigo Fatima na biye da ita a baya dakyar take motsa idanuwanta saboda yadda sukai Mata nauyi....jikinta Babu kuzari kwata kwata ga yunwar dake kwakularta haka ta Tattaro dik wani karfinta tasa a kafarta Dan idan batayi wasaba zata iya zubewa a wajen "barka da hutawa ranki ya dade gani' Sarai hajiya babba ta lura da yadda jikin Fatima ke rawa ga uban Rama da tayi daga ganinta ko baa fada ba ansan akwai abinda yake damunta Amma saita Sha murr hade da Kara tamke fuskarta "Ina aikin da nasaki kiyimun?banace ki tattaramun zanuwan gado harda barguna ki wanke munba?sarkin gida kemun wanki Amma tunda gaki na hutar dashi maza ki Mike kije kiyi abinda nasaki cikin awannin da Basu wuce uku ba idan ba hakaba sai Nasa an lallasamun ke" Kwalla ce ta taro a idanuwan Fatima haka ta cije lebe hade da boyesu ta Dan rusuna"to ranki ya dade" Hanyar Kofa hajiya ta nuna da yatsa cikin tsawa ta ce "bacemun daga gani kinyi da shegun idanuwa kamar na tsofaffin mayu" Da kyar Fatima ta iya saisaita tsayuwarta ta fice da sauri saboda yadda jiri ke dibarta tamkar zata Fadi.... ******** Kwance yake rigingine a Kan doguwar kujerar parlorn ahmad ya kife fuskarsa da jarida Idanuwansa a rufe zuciyarsa keyi Masa tsananin suya tamkar an zuba Masa rushin wuta, Ahmad dake gefensa ya zuba Masa Ido tun shigowarsa ya Gama fadansa bece Masa komiba sai nazarin maganganun yarima yakeyi.... "Niko a ganina friend ka binciki yarinyar Nan kaji meyafaru da har baka gantaba tsawon wadanan kwanakin yadda takeyi maka shagwaba da soyayya ko baa fada ba Tana sonka" Dagowa yarima yayi daga kwanciyar hade da jefar da jaridar gefe ya saukewa Ahmad idanuwansa da suka canja kala suka kankance "Ahmad nasan Fatima Tana Sona Amma meyasa zatayimun wasa da so?meyasa zatayi mun wasa da zuciya?me hakan ke nufi guduna fa takeyi tunda har yau bankarasata cikin idona ba tun bayan haduwar da mukayi last a fadar sarki muke wasan buya da ita" Murmushi Ahmad yayi "kaga ne Mana friend kasani sanin kanka cewa Fatima batada yancin kanta a gidanku tazone a matsayin kuyanga baiwa kaga ko Dole ta bautawa iyayen gijinta da baka da masaniya Akan abinda takeyi da har ka kasa sata a Ido cikin wadanan kwanakin" Shiru yarima yayi Yana nazarin maganar Ahmad din Wanda wata zuciyar ta aminta da hakan yayinda wata ke ayyana Masa wani Abu daban..... Kusan minti talatin batare da yace komiba kamar Wanda aka tsikara ya Mike "Bari inje inaso inje wajen Khadija inji abinda suke bukata Dan ni daga yau tabar sake ganina" Dariya Ahmad keyi kasa kasa Dan Harga Allah wanan cika da batsewar da yarima keyi dariya abun yake bashi.... ******** Kuka sosai Fatima takeyi Babu kakkautawa haka takeyi Tana wanan wankin da ko zanin gado guda daya ta kasa wankewa kirjinta zugi yakeyi Mata Bata tabajin irin wanan ciwonba tunda take.... Tana murza kayan Tana hawaye haka amai ya taso Mata da sauri ta Mike daga wurin ta fice can wajen wata bishiya ta. Tsugunna ta rinka amai Wanda ruwane zalla babu abinci a cikinsa gashi yellow Shar da shi haka ta rinka yunkuri tamkar zata mutu tanayi Tana kuka haka ta juya ta koma wajen wankin Tana hada hanya.... ******** "Deejahmah Niko gani nakeyi tamkar kina son yariman Nan naki bazaki iya daukar fansa akansa ba kamar yadda kike fada" Murmushi deejahmah tayi hade da mikewa zaune daga kwancen da take Tana fuskantar kawarta dake gefe "teemah dollar a ganinki kenan Amma wallahi saina kamashi a hannuna sanan zan aikasa lahira Dan nariga na tanadi makaman yakina tsaf Kuma yanzun haka kwantar da kaina zanyi sai anyi auren zanfara yi Masa kisan mummuke a hankali a hankali zanyiwa rayuwarsa illar da kafin ya farga na rigada na kasheshi a tsaye...." Murmushin mugunta deejahmah keyi Tana kallon aminiyar Tata wadda rabonta da ita sunkai shekara daya Saida zancen aurenta ya tashi sanan ta nemeta... "Ni wallahi deejah Babu abinda nake jiye Miki kamar kishi da kuyanga baiwa haba da girmanki da ajinki da iliminki a kasashen duniya inane baki lekaba dik wani gata da wayewa a gurinki muka koya Amma ki bige da kishi da baiwa" Wani ma yaudarin murmushi deejahmah ta saki sanan ta gyara Zama ta riko hannun teemah dollar wadda ta zubawa deejahma Ido Tana jiran amsar da zata Bata, "Ba kishi da ita zanyiba teemah Yar aikina zata zama Dan azabata ce zata koreta da kafafuwanta kafin in kulla Mata abinda shi kansa yarima sai yaji ko sunanta bayason ji" Kyalkyalewa da dariya teemah tayi hade da tafa hannuwanta "lallai k'awata da shirinki kenan" Gyada Mata Kai kawai deejahmah tayi batare da tace komiba....suka cigaba da hirarsu...sai yamma sanan sukayi sallama teemah ta wuce gidansu... ****** Hangen shigowarsa gidan tayi ta kafe motarsa da Ido hade da sauke ajiyar zuciya, Kallon yadda yake tafe Yana amsa waya takeyi cike da kwanciyar hankali babu wani Abu daya nuna Mata cewar Yana cikin damuwa itace ya Dasa Mata sonsa ya juya Mata baya, Kuka ne Mai karfi ya taso Mata lokaci daya ta shiga rera kuka harda shassheka idanuwanta akansa har ya bace Mata.... Sauri sauri bilkisu ta fito daga sashen hajiya zuwa wajen Fatima sukai arangama da yarima da sauri taja da baya ta tsugunna "barka da dawowa ranka ya dade" A dakile ya amsa Mata da "barkadai".....Jin yadda ya amsa Mata ita kanta Saida gabanta ya fadi Amma ta daure ta bude baki cike da fargaba tace "dama dazon nazo nemanka infada...mak...a ne faty bata...da lafiya"dik a inda inda take maganar saboda yadda taga fuskarsa Babu walwala.... Gabansa ne ya yanke ya fadi Jin furucin da Bilkisu tayi sai jikinsa yayi sanyi lokaci daya yaji tausayinsu su duka biyun ya kamashi,...kallon yadda take a durkushe jikinta na rawa yakeyi da kyar ya saisaita kansa yace "ki shiryata bayan ishai zan fita daku cikin sirri zan kaita asibiti" Daga Masa Kai tayi "to ranka ya dade"..... Koda tasamu Fatima Tana kuka ta Dade tsaye kanta Tana kallonta cike da tausayi har saida Fatima ta tsagaita da kukan da kanta sanan bilkisu ta sauke ajiyar zuciya ta kwashe yadda sukayi da yarima ta fadawa Fatima.... Girgiza Kai ta shigayi "bilkisu saidai ke ya kaiki Amma ni bazanje ba bazanbishi ya Kara jefani cikin wani balain ba sanan bazan barshi wanan karon yayi nasara akainaba zanyi kokari in cire sonsa daga zuciyata,....ki koma ki fada Masa ba sai ya kaini ba zan warke Allah Yana sane Dani" Tasa hannu ta share kwallar dake gudu a idanuwanta...ita kanta bilkisu jikinta yayi matukar sanyi Fatima ta Bata tausayi matuka ji takeyi tamkar tayi Mata kuka,....rasa abinda zatace tayi haka ta tsaya akanta kamar an dasata.....Tana Nan tsaye Fatima ta karasa wankin ta tafi wajen shanya daga can ta nufi baya wajen alwala....cak Taji an dagata ta baya tamkar jariya hade da rufe Mata idanuwa.....ta shiga shilla kafafuwanta Tana ambatar sunayen Allah a zuciya..... *Muje zuwa* Kuyi hakuri da jina shiru kwana biyu uzurine ya rikeni Amma insha allahu zaku cigaba da jina....yanzun muka fara tafiyar insha Allah *SLIMZY😍*🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* 31 A mota ya jefata ya rufe murfin motar be jira cewarta ba yaja motar a guje.....Hagen fitarsu bilkisu tayi Tana murmushin mugunta....ta juya abinta, Saida suka hau Kan titi sanan ya waigo ya Dan kalleta har yanzun kuka takeyi kamar wadda akaiwa mutuwa gashi ta dunkule waje daya Tana rawar sanyi alamar zazzabi ne ke damunta.... Kada kansa kawai yakeyi minti minti Yana juyowa ya kalleta tausayinta ke ratsa sassan jikinsa, Be tsaya ko inaba sai asibitin su Ahmad,parking space yayi parking motarsa sanan ya Ciro wayarsa ya Kiran ahmda minti kadan sukai magana ya kashe.... Kallonta yakeyi yadda ta juyar da kanta gefe Tana hawaye yakai minti biyu a haka sai da ya gaji yace "muje ko?" "Bana bukatar taimakon kowa sai na Allah da ka maidani kawai ai Allah Yana sane Dani tunda mantawa Kayi Dani" Kamo hannunta yayi ta kwace "Fatima dama abinda ya janyo Miki zazzabi kenan?abinda yasamun ke rashin lafiya kenan?kika rame kikai baki tamkar wadda tayi ciwon shekara daya?....dafe kansa yayi take tausayinta ya Kara ratsa zuciyarsa cikin sanyin murya ya cigaba da magana "kiyi hakuri banyi hakan da ganganba sai Dan wani uzuri,Kuma Allah ya rubuto hakan zai faru insha allahu bazan sake barinki ba kinji?na tuba bintu"...ya karashe maganar cike da lallashi. Sai yanzun ta juyo da dubanta gareshi idanuwanta na fidda hawaye...."karka sake yimun haka idan ka barni bansan yadda zata kasance da rayuwata ba Kaine jigon rayuwata,idan ka nisanceni Yaya zanyi inyi rayuwa Babu Rabin rayuwata a tare Dani?"kafesa tayi da ido har yanzun hawaye ke zuba a idanuwanta Hannunsa yasa ya shiga share Mata hawaye cikin sigar lallashi yake fadin "ya Isa bintu Nima na shiga halin da kika shiga kanki kikasani juriyace kawai da jarumta irin ta da namiji Amma kiris ya rage in zubar da hawayena"...ya kashe Mata ido daya Cike da shagwaba ta langabar da kanta a jikin seat Tana jifansa da wani irin mayen kallo da idanuwanta ko kiftawa batayi yayinda yaji wani shaukin soyayyarta na dibarsa ji yakeyi tamkar ya rungumeta ya lallasheta,ji yakeyi tamkar ya dawo da kwanaki ukun da sukayi ba a tare ba....dakyar ya saita kansa ya matso daf da fuskarta Yana jiyo sautin futar numfashinta Mai zafin gaske "bintu Anya zan iya rayuwa da wata mace bayanki kuwa?" . Kada Masa idanuwanta tayi hade da murmushin karfin Hali "Dole zaka koyawa kanka rayuwa da wata mace bayan ni dikda naso ace nice kadai zan mallakeka" Hancinta ya ja cike da zolaya "matsoraciya keda kikace bakiso Mai martaba yasan da ke?cewa kikayi Kar infada Masa saboda kina tsoron Kar deejah ta zauneki ni bansan yadda zaayi ki koyi zama jaruma ba" Turo baki gaba tayi Tana Masa hararar wasa"nidai muje kaga ka kawoni a dubani ka cikani da surutu" "Malama kin fa warke dama ciwon soyayya ne Ashe dai haka akesona" Hannu tasa ta rufe idanuwanta Tana dariya,lokaci daya sukaji Ana kwankwasa glass din motar..... Da sauri yarima ya zuge glass din ya motar gaba daya,Ahmad ne tsaye sanye da labcutt wuyansa rataye da abin daukar numfashi irin na likitoci,hararar yarima ya shigayi "malam ka kirani tun daxun zaku shigo Kun kwashe kusan Awa daya bangankuba nagaji na harhado Mata magungunan zazzabi na biyoku dashi Dan nasan soyayya kukeyi.... Tabe baki yarima yayi hade da dage kafadarsa sama sanan ya Mika Masa hannu ya karbi ledar "zamuyi maneji Amma na rigada na Bata maganin ciwonta dama ciwon nawa ne ko bintu" Sadda kanta kasa tayi kunya ta lullubeta ganin yadda jikinta yayi dauda haka ta fito Babu kyaun gani wani ma sai yace ta shekara batayi wanka ba....murmushi kawai takeyi kasa kasa.... "Kaidai kasani sai nazo Mata allura" Da sauri ta dago ta kalleshi,dukansu suka kwashe Mata dariya ta sunkuyar da kanta da sauri.... Hannu yarima ya dagawa Ahmad hade da tayar da mota ya jasu a guje.... Tunda suka hau hanya gabanta ke tsananin faduwa Dan ta manta da shaff cewa wannan gidan zasu koma,idan Tana hare da yarima jinta takeyi a wata duniyar ta daban.... ****** "Ranki ya dade a idona ya dauketa suka fice Kuma motarsa yasata ya ja da kansa suka fita" Kaiwa da komowa kawai hajiya babba takeyi hannunta rungume a bayanta.....tsananin takaici ne ya hanata cewa komi tunda saade ta Soma magana, Kasa gasgata maganar saade tayi Saida tasa Mami ta binciko Mata ko Ina ta tabbatar Mata da Bata gidan, Iska Mai zafi ta furzar daga bakinta "lallai yaron Nan nema yakeyi ya nuna mun iyakata,lallai kabiru ya cika Mara kunya ya tabbatar mun da shi Dan halak ne ni Kuma zanyi maganinsu dukansu su biyun bawai na rasa yadda zanyi dasu bane...." ******** A parking space yayi parking motarsa ya kashe motar ya kunna fitilar cikin motar ya dan kalleta Yana nazarin yanayinta,ya lura da dik yadda take a tsorace a firgice,shi mamakinta yakeyi yadda takejin tsoron wadanan bayin Allah Jin shiru yasa tasa hannu zata bude kofar taji a rufe ta juyo da sauri suka hada ido ya sakar Mata murmushi kasa mayar Masa tayi sai kallonsa da takeyi cike da kosawa tace"yaayah Dan Allah ka budemin in fita kafin wani ya ganmu" "To meye idan anganmu nidin ba mijinki bane?Mai martaba ya mallakamin ke ya yarjemun da aurenki" Raurau tayi da idanuwanta Tana kallon yadda yake magana hankalinsa a kwance....ita ko dik inda hankalinta yake a tashe yake "haba mana yaayah Dan Allah ka budemin kofar Nan infita" Key yasa yayi unlocking motar da sauri ta bude kofar jiki na rawa tasa kafarta ta jiyo muryarsa "tunda kika tafi baki tsaya nagama kallon kyakkyawar fuskarki ba to tabbas wajen wata zanje yanzun Nan " Cakkk ta tsaya zuciyarta na harbawa sauri da sauri take wani Abu yazo ya tsaya Mata a kirji dakyar ta hadiye miyon bakinta ta karasa fita har zata rufe kofar ta leko da kanta Tana kallonsa cikin ido ya kashe Mata ido daya "idan har kaje to tabbas kasani kabar sake ganina sai Nan da sati biyu" Dage kafadarsa yayi Yana murmushin mugunta tarkon daya Dana Mata ya kamata Nan da Nan ta nuna Masa kishinta a Fili.... Juyawa tayi da sauri tabar ledar maganin cikin motar saboda kidimewar da tayi hantar cikinta dik a Kade take addua kawai takeyi Allah yasa Babu Wanda ya ganta.....ga takaicin maganar da yarima yake fada mata Wai zaije wajen wata ,to yaje Mana ai ko be fadaba tasan cewa Yana son deejahmah boye Mata kawai yakeyi.... Har ta doshi shiga ta babban parlor ta fasa dabara ce ta fado Mata tabi ta kofar baya da sauri ta kwaso shanyar da tayi ta nufo cikin gidan kirjinta na bugawa.... Sashen hajiya ta shiga da sallama sai Raba idanuwa takeyi dakyar ta Tattaro jarumtar ta tayi sallama cikin sassanyar murya... "Kin dawo daga yawon iskancin kenan?kin manta na baza idanuwana cikin gidan Nan Kuma dik akanki suke?...ya daukeki ya fita dake kunyi abinda zakuyi kundawo ko ?ai na dauka daga can wani waje zashi dake ya ajiyeki ya fiye Miki sauki Akan dawowa cikin gidan Nan"... Wani mugun miyau Fatima ta hadiye a fakaice"Babu inda naje Ina bayan can anan nayi sallah na zauna har akayi ishai sai yanzun na dawo ai bilkisu ta taganni lokacin " Da sauri hajiya ta juyo ga bilkisu wadda ke faman zare Ido "bilki Wai kinganta?" "Naganta ranki ya dade niba shiga sabgarta nakeyi ba shiyasa nayi wucewata Kuma bansan maganarta kukeyi ba Dan ni ko sunanta ma bansaniba".. Kwafa hajiya ta sauke ta wurgawa Fatima wata uwar harara "ficemun daga daki" Mikewa tayi ta fice abinta har yanzun gabanta be daina faduwa ba ta fito ta babban parlor, Hajiya karama ta gani zaune hannunta dauke da carbi Tana ja ta karaso ta tsugunna a gabanta ta gaidata ta amsa Mata Babu yabo Babu fallasa.... Dakinsu taje ta nemi waje ta zauna ta fada duniyar tunanin yarima....zuciyarta ke ayyana Mata yanacan tare da deejahmah suna Shan soyayya ke tsoro ya hanaki nuna Masa yadda kike sonsa,ki tsaya kallon ruwa kwado yayi Miki kafa, Yatsanta ta ciza hade da Jan tsaki lokaci daya, A gaggauce bilkisu ta shigo ta sameta daidai tanajan tsaki "ke kuma tsakin me kikeyi?angamo soyayya an dawo kinzo kina zare idon banza bayan ba tsoron da kikeji tunda kika iya awanni biyu tare dashi" Duka Fatima ta Kai Mata "ni ki kyaleni abinda ya dameni ya dameni Dan yanzun fa fushi yayi Wai zaije wajen wata" "Kadan kika gani wallahi inhar bazaki cire tsoroba kiyi yaki to watarana Zaki wayi gari ki nemesa ki rasa yanzun gogayya yakamata kuyi ta tsaya Jin Kai ke Kuma ki kwace miji dik kallon baiwa kuyanga da akeyi Miki ki barta a Tasha" Dariya Fatima tayi "ni Bilki idan kina magana kamar wata uwar Mata mamaki kike bani" Harararta bilkisu tayi "Dole inbaki mamaki ai tunda kin Gama koke koken kin warke yanzun ai Dole ki fadamun magana " Toshe baki Fatima tayi tanawa bilkisu dariya wadda ke magana cike da kulewa, "ni yanzun babban tashin hankalina be wuce ranan da zata kasance an rabamu da yarima ba maana ranan da zaa daura Masa aure" "Ki shirya kibishi gidan matar" Tsaki bilkisu tayi ta juya tai tafiyarta tabar Fatima Nan..... ********* Shiko yarima Yana ganin shigewar Fatima cikin gida ya fito ya rufe motarsa ya shige bangarensa Yana murmushi Domin Harga Allah dariya ma abin ya bashi.... ********** Bayan kwana shida, Ya kasance befi kwana takwas bikin yarima da deejah ba gida ya fara rikicewa da baki na cikin gida da waje saura kwana biyu a fara event kamar yadda deejahmah ta tsara itada aminiyarta teemah dollar..... Zaune Fatima take can bayan gida inda ya kasance Nan ne wajen zamanta Nan take makalewa taita kukanta dik ta fige ta rame ta shiga matsananciyar damuwa hakika sabo turken Wawa ne ta tabbatar da hakan Dan ta Saba dashi sosai fiye da tunanin Mai karatu, Durkusar da kanta tayi Tana kuka Mai ban tausayi Wanda batasan dalilinta na yinsa ba,.. Nemanta bilkisu takeyi tun safe Bata gantaba har ta cire Rai da ganinta saita tuna da inda suke Zama saboda mutane da suka fara yawa cikin gidan.... Yarima ta gani yanata dube dube tamkar me neman wani Abu can ya hangi bilkisu ta nufi bayan gidan su inda bishiyoyin mangwarori suke....bayanta yabi har suka Isa a tare wajen bishiyar da Fatima ke tsugunne Tana kuka Ganinsu ya sanyata saurin mikewa Tana share hawayenta hade da wayancewa, Kallon yadda ta canja yakeyi dik ta rame tayi bakin Kirin idanuwanta sunyi zuru zuru.... Tsugunnawa yayi a gabanta ya rike kunnuwansa alamar ban hakuri.....kuka ne ya taho Mata lokaci daya kawai ta durkushe a gabansa Tana kuka Mai ban tausayi.....besan lokacinda hawaye ya shiga fita a idanuwansa ba,....ita kanta bilkisu dake jingine jikin bishiya hawaye takeyi Domin dik Wanda ya kalli Fatima a wanan yanayin saita bashi tausayi..... Dakyar ta tsagaita da kukanta ta matso kusa dashi tasa gefen rigarta Tana share Masa hawaye hade da girgiza Masa Kai...."...banason ganin idon jarumin namiji Yana fitar da hawaye,....idan har bakayi shiru ba bazan gafartawa kainaba"tana maganar ne Tana kuka.... Hannu yasa ya share hawayensa sanan yasa hannunsa Yana share Mata hawaye "banason ganin kyakkyawar fuskar Nan cikin damuwa, kiyi shiru ki dainamun asarar hawayenki Fatima,hawayenki sunfi komi tsada da kima a idanuwana da inada Hali da na hanasu zuba har abada meyasa kike nisanta kanki Dani cikin kwanakin Nan".. Cikin shasshekar kuka taja hancinta "nafara koyawa kaina rayuwa batare da kaiba,kukan Nan da kaga inayinsa inayine saboda zan rasa farin cikina.....banida gatan daya wuceka a rayuwa,...ka manta Kaine inuwar dake zagaye Dani a cikin gidan Nan?babu wata inuwar da nake rabawa insamu farin ciki in samu sassauci daga zafin Rana sai inuwarka....banida uwa bani da uba sai Kai ya bazanyi kuka ba?ya bazanyi kukan rashin masoyi ba?"..... Tunda ta Soma magana hawaye ke gudu a idanuwansa tausayinta shine abinda ya mamaye ilahin sassan jikinsa.....hakika Fatima a bar tausayi ce Fatima batada gatan daya wuceshi cikin wanan duniyar..... Kammo hannunta yayi ya rike Yana murzawa yayinda take durkushe a kasa Tana kuka Mai ban tausayi..... "Ki dago kanki kidaina wanan kukan Domin idan kinayinsa ji nakeyi na tsani kaina a rayuwa ji nakeyi tamkar na cutar dake naci amanarki ki dago ki fadamun abinda kikeso inyi Miki nayi alkawarin yi Miki ko meyeshi a fadin duniyar Nan matukar Zaki daina zubar hawaye".... *Muje zuwa* *SLIMZY😍*🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* 32 Dago Kai tayi tana Kare Masa kallo har ya Kai karshen maganarsa,Kara damke hannuwansa tayi cikin nata,dayan hannunta ta Sanya ta share hawayenta "Kaima ka share hawayenka kaji ?kaga Nima na share nadaina kuka kaji?".. ta langabar da kanta Tana kallonsa, Hannu yasa ya share hawayensa ya maida dubansa gareta "Ina sauraronki fadamin bintu na mekikeso umm?" "Ni tsoro nakeji kada kayi aure ka mance Dani ka manta da wata Fatima na rayuwa a doron kasa,gashi ka sabamin da rayuwa da Kai ba lallai bane kullum inganka shiyasa na shiga damuwa" "Idan har zan mance dake faty to tabbas zan mance da kaina da rayuwata,kisawa zuciyarki ninakine ke kadai harabada bazan taba rabuwa dake ba numfashina" Kallon yadda yake motsa bakinsa takeyi soyayyarsa na yawo cikin jinin jikinta,ta shagala da kallonsa har ta mance da wani bacin Rai da take ciki a wanan lokacin, Duko da kansa yayi Yana kallon cikin idonta ,da sauri ta kauda Kai Tana murmushi "yaayah Dan Allah ka rinka zuwa wajena kaji?"ta marairaice fuska, Mikewa tsaye yayi Yana kakkabe jikinsa "rigimarki yawa ne da ita Fatima Allah Ina gab da fara zaneki don wanan kukan da kike yi wata rana hawayenki zasu Kare" Mikewa tayi tsaye tana murmushi "inhar kukan Nan ne bakaso to na Bari ".. Gira daya ya dage Mata "kin tabbata?" Daga Masa Kai tayi tana dariya. Aiko Dole inbaki chocolate,ya zura hannunsa cikin aljihunsa ya Ciro chocolate guda biyu ya bare da hannunsa "oya taho ki amshi kyautar soyayya" Tana dariya ta Miko fuskarta ta Dan bude baki ya tura mata chocolate baki ta hade da yatsansa ta rike Tana dariya... "Aushhhh da zafi Mana wallahi kinci bashi saina Rama" Kada Masa idanuwa tayi "yanzun sai ka Rama?"... "Ehh Mana kibari indawo daddare zan Rama zan siyo muku kayan da zaku canja kuci biki dashi keda bilkisu da Maryam" Gyada Masa Kai tayi "Allah ya tsare" Waige waige ya shigayi hade da leka bayan bishiyar sanan ya juyo Yana dubanta "Ina bilkisu?".. Sai lokacin Fatima ta tuno da wata bilkisu itama waige waige ta shigayi sanan ta juyo tace mishi "Ashe ta wuce" Jan hancinta yayi kadan "yaushe zakisan ta wuce kinatawa mijinki rigima?umm?"...yasa hannu ya zagayo kungunta ya riketa sosai Yana kallon fuskarta,itama shi take kallo Tana murmushin sannan taja da baya cikin dabara ta kwace daga rukon da yayi Mata "saika dawo" Gyada Mata Kai yayi ya juya cikin sauri Yana kallon agogo ya bar wajen,kallo ta bishi dashi hade da sauke ajiyar zuciya.... Ta Dade zaune wajen Tana tunani kala kala yadda zuciyarta batayi Mata Dadi kwata kwata..... ********** Yau ta kasance Ana gobe zaafara event din biki yayinda gida yake cike makil da jamaa na ciki Dana waje Kuma yau ne hajiya zainab da tawagarta suka sauka daga Saudi Arabia bangaren mama karama ta sauka Domin sunfi shiri da ita,.. Tunda garin Allah ya waye ake girke girke kala kala dik wata baiwa da ke cikin gidan Bata Samu tsugun ba saboda aikace aikace da suke famar yi yayinda deejahmah da tawagarta gabaki daya suka dawo gidan sarki Nan ake biki sosai.... Zaune da kawayenta can wani daki Wanda ya kasance Nan anyisa Domin masaukin baki dakine safe content da bayi biyu ciki a Nan suka sauka suke lalle itada kawayenta da kannenta ciki kuwa harda su khausar afnan,faizah da fauziyya sai wasu friends dinta guda uku,.. Taunar chewing gum takeyi cike da yanga da kasaita yayinda ake Zane Mata kafa da hadadden lalle Mai shegen kyau domin ita kanta me lallen daga wani gari aka daukota musamman don tayiwa Yan biki lalle,.. Gefen kawarta teemah ta kalla ta Dan yatsina fuska "ka'wata nake ganin kamar lallen Nan ya bushe ko?ya kamata a baremun na kafafuwan sanan akawo ruwa a wankemun kafar" Jinjina Kai teemah tayi tana kallon kafar "ya kamata Kam ai sai ayi Miki,...juyawa teemah tayi gefen da rahane kuyangar deejahmah take tsugunne ta Dan kalleta a wulakance "Rahane ki kawo Mana ruwa" Yunkurawa Rahane tayi zata Mike da sauri deejahmah ta dakatar da ita "Rahane wanan ba aikinki bane aikin tsintacciya ne,kije dik inda take ki kiramun ita tazo ta kankaremun lalle ta wanke kafar matar uban dakinta"...ta karashe maganar Tana murmushi hade da hada ido da teemah dollar ta daga Mata hannu hade da jinjina 👍🏼"yayi ranki ya dade ya kamata ta fara bautawa uwargijiyata kafin ta fara ainihin bauta Nan gaba" Kallon juna faizah sukai da fauziyya wadanda suke gefe waje daya idan ka kallesu zasu iya juyar maka da Kai saboda tsabar kamanninsu, Fatima na cikin kitchen suna hakilon aikin abinci dik tayi zufa tayi bakin Kirin ta gaji Domin aikin da takeyi yafi karfinta, Direct wajenta Rahane ta nufa ta tabota,da sauri ta juyo "uwar gijiyata nada bukatar ganinki yanzun a sashen baki"....Bata jira cewar Fatima ba ta juya abinta.... Dafe kirjinta tayi tana tambayar kanta a zuciya "wacece Kuma uwar gijiyarta?"...jiki a sanyaye tabi bayan rahane da sauri har tana tuntube gudun karta bace Mata,.. Sashen dataga Rahane tabi ne ya Sanya gabanta ya yanke ya fadi take taji wani Abu na Shirin tasowa a kirjinta tabbas yanzun ta Gane fuskar Rahane Dan ta taba ganinta tare da deejahmah, Dakewa tayi tabi bayanta har cikin dakin da sallama dauke a bakinta ta nemi gefe ta tsaya batare da tace komiba, Dukan wadanda ke cikin dakin suka zubowa Fatima na mujiya wasu nayi Mata kallon wulakanci wasu nayi Mata kallon ko in kula, A fusace deejahmah ta kalli Fatima dake tsaye kikam zuciyarta na tafasa "ke kinfi karfin ki tsugunna a gabana nasa a kiraki?ko kin manta matsayinki na kaskantacciyar baiwa ne?Koko ni saarkice da zankiraki ki tsayamim a Kai batare da kin rage tsawoba?" Batare da Fatima tace komiba ta rage tsawonta ta tsugunna Amma fuskarta a daure tamkar Bata taba dariya ba, Da yatsa deejahmah ke nunata Tana fadin "ba yanzun Zaki wannan iskancin ba kibari sai Kinga cikar burinki,..sanan ni ba kaunar kallon wanan mummunar fuskar Taki nakeyi ba infact ko ganinki banason yi yanzun ma dalili ne yasa nakiraki aiki zansaki ,kije kisamo ruwan zafi ki sirkashi kizo ki kankaremun lalle sanan kisa kafata ciki ki wankemun yanzun Nan idan ba hakaba kinsan sauran" Tsananin bacin Rai ya Hana Fatima cewa komi Banda idanuwanta da suka kada sukai jajir tamkar zata fashe da kuka haka ta Mike tsaye ta fice,....deejahmah tabita da uwar harara tamkar idonta zai fado kasa.... "Niko deejahmah Ina suka samo wanan kyakkyawar yarinyar tamkar ita tayi kanta kuma a matsayin kuyanga?gata yarinya karama wallahi"... Harara deejahma ta watsawa kawarta da tayi wanan maganar sanan tace"tsintacciya ce shegiya uwar ta da tai cikinta yarda ita tayi a bakin kwata Yan gidan marayu suka tsunceta suka sata cikinsu shine mijina ya daukota a matsayin baiwa Yar aikina" Daidai Nan Fatima ta shigo hannunta dauke da Dan karamin baho ta ajiye a gefe ta shiga kankarewa deejahmah kafa,....tanayi zuciyarta nayi Mata Kuna takaici da bakin ciki duka suka lullubeta a haka har ta Gama,ta sa hannu Tana Shirin tsoma kafar cikin ruwan zafin,...da sauri deejahmah ta dago Kai ta Kai Mata Mari cikin tsawa tace "kin taba kinji zafinsa ne da kike kokarin samun kafa cikin ruwan zafi?konani kikeson yi?kin kashemun tsoho mijina dik be ishekiba Nima sai kin konani kenan" Aikuwa idon kowa dake dakin ya dawo Kan Fatima wadda tayi tsumu hade da sunkuyar da kanta kasa,take kwallar bakin ciki suka shiga silalowa a kumatunta,....daurewa tayi tasa hannu cikin ruwan sanan ta dago Kai ta kalleta hawaye na zuba a idanuwanta "Babu zafi na surka kafin inzo" Murmushin nasara deejahmah tayi Domin burinta be wuce ta nuna mulki da Isa a gaban kawayenta ba burinta be wuce ta wulakanta Fatima taga Tana hawaye ba,...tabe baki tayi sanan ta watsa Mata harara "ki samun" Haka tasa kafar cikin ruwan Tana wankewa hawaye na gudu a idanuwanta har ta Gama ta Mike ta fice a dakin.... Tausayin Fatima ne ya lullube faizah dake zaune a gefe Tana ganin dik abinda ya faru,wayarta da Jakarta ta mikawa fauziyya ta Mike ta kalleta fuskarta Babu walwala tace"rikemun fauzy Ina zuwa".. Da sauri deejahmah ta kalli faizah cikin Isa tace"ke Kuma Ina Zaki?ko kin fasa lallen ne?bakiga k'awata ake mawa ba yanzu?shine kikai fushi Zaki futa kika canja fuska?" Girgiza Kai faizah tayi tana murmushi "ah ah wallahi anty deejah Ina Dan Jin yunwa ne zanje insa a zubomin abinci".. Murmushi deejahmah tayi tana kallon faizah "kiyi sauri fauziyya Dan idan tagama ku zaayiwa Dole ayiwa Yan biyun innah,...." Dariya sosai faizah tayi "anty deejah ga fauziyya Nan gefenki"...duka Yan dakin suka sa dariya...yayinda deejahmah ta tabe baki "ni ba ganeku nakeyiba kamanninku yayi yawa kiyi sauri dai" "Owk"shine abinda faizah tace a takaice ta fice.... ******* Kitchen ta shiga tanata dube dube Bata ganta ba ta fito ta kofar baya na kitchen sai ta ganta tsaye ta hada Kai da bango Tana hawaye hannunta daya dafe da jikin bango,...ta Dade tsaye a bayanta sanan dakyar ta karfin Hali ta ambaci sunanta cikin sanyin murya "Fatima"... Jimm kadan Fatima tayi sanan ta juyo fuskarta jike da hawaye da sauri tasa hannu ta share hawayen ta tsugunna gaban faizah "ranki ya dade me kike bukata?" Dukawa faizah tayi ta dagota ta mikar da ita tsaye fuskarta dauke da murmushi ,....kallo itadai Fatima ta bita dashi batare da tace komiba, Faizar ce ta fadada faraarta "sunana faizah,....na Dade inaso inzo in kebe dake inyi magana dake ta fahimta ni bazan cutar dake ba Domin Harga Allah ni Ina kaunarki tsakanina da Allah ne bansamu nazo ba saboda makaranta da muke zuwa nida Yar uwata,ni Yar waziri ce Nan bayanku kadan gidanmu yake kusan gida dayane Amma kofa CE ta rabamu" Murmushi Fatima ta kirkiro dikda bacin ran da take ciki a wanan lokacin ta mikawa faizah hannu su gaisa,babu kusu faizah ta mikawa Fatima hannu suka gaisa sanan faizah ta cigaba da magana "kiyi hakuri dik abinda ya sameki mukaddari ne daga Allah kinsan bawa baya wuce kaddararsa a rayuwa sanan kiris ya rage kema ki fara farin ciki kamar kowa,ki daure ki jure anzo karshe Domin kema Nan gaba kadan Zaki fara zuba mulki har mu da muke a matsayin kannen mijinki dole muyi Miki biyayya".... Murmushi Fatima takeyi Tana kallon faizah....ya fito ta kofar kitchen hannunsa dauke da leda yanata waige waige Dan sauri yakeyi zai fita sai yaji magana kasa kasa ya juya da sauri gefen da yakejin maganar take sukai Ido hudu da Fatima ta sakar Masa murmushi, Bayan faizah yakebi da kallo don besan ko wacece ba Saida ya karaso wajen ya bita da kallon mamaki,murmushi faizah tayi take yarima ya Gane itace ya maida Mata da murmushi hade da nunata da yatsa cikin wasa yace "idan banyi batan Kai ba faizah ce ko?Domin kece sarkin murmushi" Dariya faizah takeyi Tana gyada Masa Kai "nice Yaya barka da zuwa" Cikin kosawa ya Dan kalli Fatima ya kalleta "me kukeyi a Nan ne? injidai lafiya"...faizah zatayi magana Fatima ta rigata cike da shagwaba ta amsa da "nida faizah ne Yaya tazo Tana lallashina itace sabuwar k'awata Tana Sona" Dadine ya cika yarima Jin Fatima tasamu kawa me kaunarta bayan bilkisu koba komi zata samu sassauci..."gaskiya naji Dadi faizah Dan Allah ki rikemun amanarta ki rinka kulamin da ita kinji?Kinga ita zan aura Kuma marainiya ce batada kowa saini saike yanzun da kike kaunarta kinji' Gyada Masa Kai faizah tayi tana murmushi "insha allahu zaka sameni da rukon Amana yaayah Domin inason halin Fatima" Murmushi yayi ta mikawa Fatima ledar hannun sa "ankon wajen kamu ne da zaayi gobe Kuma a gidan Nan zaayi nasan sauran kuyangin ma sarki ya bada kudi a siya musu Kaya su sabinta saboda biki shine na siya muku keda bilki" Wani irin kallon soyayya take jifansa dashi Tana murmushi Wanda ganinsa ya mantar da ita bakin cikin da take ciki "mungode Allah ya saka da alheri Allah ya Kara girma" Dadi ne ya kamashi yayi murmushi "ki kawomin ruwan zafi daki zan Dan Sha in warware cikina tun safe banci komiba" "Angama ranka ya dade"... Hannu yasa ta Ciro wallet dinsa a aljihu ya Ciro kudi Yan dubu dubu ya kirga dubu goma ya mikawa faizah "ga wanan faizah kema ki siyi abinda baki siyaba na biki" Ta Dan durkusa "nagode Yaya Allah ya Kara girma" "Ameen"kawai yace ya wuce ya barsu Nan tsaye da Fatima, Kamo hannunta Fatima tayi ta hada "Allah ya barmu tare faizah nagode da kauna....Allah yasa ki rikeni Amana" Ta bayansu bilkisu tace "Fatima me kikeyi a Nan tun dazun hajiya na nemanki nazo kitchen bangankiba shine na biyo ta baya ko zan ganki" Karasowa bilkisu tayi tanabin faizah da kallo yayinda ta maida dubanta ga Fatima tanayi Mata kallon tuhuma,itadai faizah batasan tsakaninsu ba yasa tayiwa Fatima sallama tace Tana zuwa zata Kara dawowa ta wuce, Harara bilkisu ke jifan Fatima dashi "Mara zuciya wanan Kuma wacece tazo kika ruko hannunta kdmar wata Yar uwarki" "Ke da'alla faizah ce Yar waziri tanada kirki sosai yanzun aka Gama wulakantani a gabansu shine ta biyoni Tana bani hakuri take cemin ta Dade tanaso tazo wajena Domin Tana kaunata" Girgiza Kai bilkisu takeyi hade da rike kugu "kauna fa kikace Fatima?dama wadanan mutanen zasu kaunace ki?a tunaninki ba wani tuggun ake son hada Miki ba" "Ah ah bilkisu ka kyautata zatonka Akan kowa,kuma yadda tazomin ban kawo komi a rainaba Dan bakiga abinda deejahmah tayimun a gabansu ba"...Nan ta kwashe komi da ya faru tsakaninta da deejahmah ta fadawa bilkisu, Ajiyar zuciya bilkisu tayi murya a raunane tace"Allah yasa dagaskene " "Ameeen"... Ta kalli bilkisu Tana murmushi tace "Bari insa ruwan zafi inje inyi sallahr laasar kafin Nan ya tafasa yarima keso sai inzo mu zanta ko?" Jiki Babu kwari bilkisu ta amsada "toh shikenan ki sameni wajen magwarori" "Naga jikinki dik yayi sanyi ne ko akwai wani Abu ne Yar uwa?" Girgiza Kai kawai bilkisu tayi ta juya abinta.... ********** Sauri sauri tayo alwala ta zo inda ta Saba zuwa tayi ibada ta shimfida dankwalinta ta tada sallah cikin natsuwa take sallahr ta ta fuskanci alkibla Tafe suke Tana rike da hannun yaronta karami sun fito sashin Mai martaba yaron ya kalli mahaifiyarsa Yana nuna Mata Fatima dake sallah "ummu laa duba sallah takeyi ankira sallah ne?".. Juyawa hajiya zainab tayi tana kallon inda yaron ke nuna Mata tabi yarinyar da kallo wadda ke sanye da Kaya irin na kuyangin gidan "sadik ankira yanzun zamuje muyi muma kaji?".. "Toh ummu muyi sauri" Batace masa komiba takebin Fatima da kallo Tana jinjina Kai cike da mamaki ta furta a Fili "ikon Allah "...haka suke tafe Tana saka da warwara har suka shigo sashen hajiya karama ko Zama batayiba ta kalli hajiya cike da al'ajabi tace"hajiya dama maaikatan gidan Nan suna sallah ne?ni tunda nake bantaba ganin wata baiwa ko kuyanga na sallah ba a iya rayuwata a cikin gidan Nan sai yau Naga wata Yar farar yarinya bandai lura da fuskarta ba Tana sallah can baya" Fuska dauke da damuwa hajiya karama ta kalli hajiya zainab sanan ta kauda kanta gefe tace"wacece kika gani Banda Fatima?yarinyar da kikejin labarin ta kashe Miki d'a habibu ?itace wadda danki yake Shirin jajubowa a matsayin matar aure tsintacciya Mara asali itace surukarku" Zama hajiya zainab tayi gefen hajiya karama sanan ta nisa tace "hajiya insha Allah wanan yarinyar alheri ce a rayuwar kabiru Domin naji hakan a jikina,Koda ta kasance Mara asali tsintacciya ba yin kanta bane laifin iyayenta ne sanan ba ita ta halicci kanta ba Allah ne ya halicceta yasa kaddararta tazo a hakan....sanan maganar kisan Kai kusan gaskiya saidai ku take sani tunda kungani a video lalata danku yajeyi da ita Allah ya Aiko Masa da ajali,be Dace ku tsaneta ba Dan Babu Wanda yafi karfin kaddara ta fada Masa wallahi tunda ta kasance Mai ibadah ni Ina kaunarta Ina sonta a matsayin suruka kema Kuma inaso kada kibiyewa tsegumin mutane ki riketa amana bakisan me Allah ya boye a wajenba bakisan tarin baiwar da Allah yayi Mata ba" "Aike dama dik abinda kabir yakeso to fa kina sonsa,komi kabiru yayi daidaine a wajenki" Dariya wanan karon hajiya zainab tayi "saboda shi din yarone Mai biyayya da hankali da sanin ya kamata shiyasa,Kuma ninasan Dole yanada hujja da dalilinsa na yin hakan,nidai Ina kaunarta Kuma inayin suruka da ita" Ajiyar zuciya mama karama ta sauke "ai sai kiyitayi" Girgiza Kai kawai hajiya zainab tayi tana murmushi... ******* "Wai bintu sai wani sauri kikeyi kin hadamun tea ko ki tsaya kibani ma insha sanan kitafi" Dariya yabata Tana kallon yadda yayi maganar tamkar wani yaro karami "inbaka tea sai kace jariri".. "Toh ni ba jaririnki bane?ai mijinki tamkar jaririnki ne Domin kece keda hakkin kula dashi"... Mikewa tayi tana dariya"kaga tafiyata" Da sauri ya Kai Mata cafka zille cikin azama ya damkota da dayan hannunsa ya janyota Yana dariya itama dariyar takeyi "kaga bama saika rikeniba zauna da kyau inbaka,Amma kanaganin zaka iya Shan tea kana kallon wanan jikin nawa Mai dauda?"ta dage Masa gira daya hade da kyafta Masa Ido.. "Babu ruwana da dattinki ko cikin ruwan kwata kike kwana ke nakeso ba dattin ba" "Shikenan"ta dakko kofin tea din Tana juyawa Tana kallonsa ta dibo a cokali takai bakinsa Babu kunya yarima ya kurbe Yana dariya kasa kasa haka taita bashi har tea din yakai Rabin Kofi ta Mika hannu ya karba Yana fadin "oya Dole a ramawa kura aniyarta kema ki bude baki in baki naki" Rufe ido tayi yabita da kallo ya dibo tea din yace "oya ha baki"aikuwa Fatima ta bude Tana murmushi yasa Mata a baki yayita Bata harta shanye sanan ya ajiye kofin Yana kallonta Yana dariya, Turo baki gaba tayi hade da Dan canja fuska "yanzun da ka koyamin ciyar Dani idan katafi wajen matarka waye zai rinka bani abinci?bayan nasaba da yayana ke bani" Da sauri ya amsa da "nine Nan zan rinka zuwa Ina baki bintu,lokacin cin abinci nayi zanzo" Ta saki fuska Tana murmushi ta Mike ta dauke cup din ta juyo ta Dan kalleshi "ni natafi bakin aikina kaga bilkisu na can Tana jirana nasan ta cika tayi famm" Dage mata gira yayi batare da yace komiba ta juya tayi waje yabi bayanta da kallo,komi na Fatima na Burgesa... ****** Kicibis sukayi da bilkisu "malama nagaji da jiranki kintafi soyayya ko ?kunje satarwa sarauniya deejahmah hanya ko?Tana can tana kuri ku Kuna Nan Kuna soyewa".. Dariya Fatima tayi hade da yin kasa da murya "ai tunda ta bullo da hakan ni zata rinka tozartawa ni Kuma zan mantar da mijinta ita" Mamakine ya kashe bilkisu ta rike habarta Tana jinjina Kai Tana fadin "Allah ya kawomu Fatima tayi baki haka nakeso ta wajena jeki Kai kofin kidawo" Fatima ta shige Tana dariya.... ******* Maryam dake dakin hajiya karama Tana rabe a gefe hajiya zainab ta kalleta tace "ke,kinsan wata kuyanga Fatima?" Da sauri Maryam ta daga Mata Kai "ehh ranki ya dade" "Tashi ki kiramun ita"... Ta Mike da sauri, Hajiya karama tace dake gefe ta ce "hajiya lallai kinason surukar Nan Taki yanzun me zatayi Miki?".. "Inaso inganta ne sanan insata ta je bangarena ta bude ta gyaramun Kinga yamma tayi...." Jinjina Kai kawai hajiya karama tayi cike da gamsuwa... ******* A zabure deejahmah ta Mike daga kishingiden da take cikin tsananin tashin hankali take duban Rahane dake durkushe a gabanta tace"kikace takai awaya a dakin yarima? Kin tabbatar da maganar da kika fadamun ?" "Bana baki labari saina tabbatar ranki ya dade" Da sauri ta Mike tsaye tana zura flat shoes dinta, "Dakata princess ai martabarki da kimarki ta wuce kibita a matsayinta na baiwarki kece Zaki sa ai kiranta kici zarafinta yadda ya Dace" Huci kawai deejahmah takeyi Nan da Nan fuskarta ta canja kala ta dubi Rahane "kiramun ita"... Da sauri rahane ta Mike ta bar dakin ta barta Nan tsaye Tana huci hade da girgiza Tana furzar da iska a bakinta cike da bacin Rai... A parlor suka hade da Rahane Fatima na biye da Maryam Dan zuwa Kiran hajiya zainab Rahane ta tsaidasu "Fatima kizo inji uwargijiyata" Wani kallo Fatima tayiwa Rahane wanan karon sanan ta kauda Kai tace"zan fara zuwa Kiran hajiya zainab kafin inzo nata"....Tana Gama fadin haka ta wuce....Maryam tabi bayanta... Jinjina Kai Rahane tayi ta juya zuwa dakin da deejahma suke Tana shiga ta zube a gaban deejahmah "ranki ya dade tace ankirata saita Gama wancen uzurin zatazo naki" Cikin tsawa deejahmah ta ce"ita a wa?nidin inyi kiranta tacemun bazakazoba?lallai yarinyar Nan ta Kira Mai alewa batada kudin siye".....a fusace deejahmah ta wuce tamkar kububuwa har tana bangaje Rahane dake gurfane a gabanta ta fice a dakin.... Kallo suka bita dashi ko wanne da abinda yake rayawa a zuciyarsa..... *Muje zuwa* *SLIMZY😍*🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* *_Allah ya maimaita Mana ya Kara Mai maita* *Mana shekaru_ _masu yawa_* *EID MUBARAK* _Anty rabi sakonki ya iso gareni nagode sosai Allah ya saka da alheri..._ 33 Cike da natsuwa ta shiga dakin yayinda zuciyarta ta tsananta bugawa,fargabar abinda zai biyo baya takeyi Dan batasan laifin da tayiba ake Kiran nata... Gefe kadan ta tsugunna hade da sunkuyar da kanta kasa,..zuciyarta na tsananin bugawa ta bude baki a hankali tace "gani ranki ya dade ance kina nemana" Hajiya zainab wadda ke gefe ta kafe Fatima da Ido tunda suka shigo take binta da kallo har ta nemi waje ta tsugunna,...kallon yadda kayan jikinta sukai makal makal takeyi saboda datti sanan ta maida dubanta ga fuskarta wadda take a sunkuye ta kafeta da Ido.... Shigowa dakin yasa dukkansu suka daga Kai su kalli waye ya shigo Babu ko sallama bare neman izini, Deejahmah Bata damu da wadanda ke wajenba Dan batasu takeyi ba Fatima kawai takeso ta ciwa mutunci saboda yadda idonta ya rufe,....tsaye tayi Akan Fatima hade da rike kwankwaso jikinta har rawa yakeyi savida masifar dake cinta, "NA aika akiramun ke shine kika dawomin da Yar sakon kikace bazakizo ba saboda ninayi Kama da Saar ubanki?shegiya har ta Kai matsayin da Yar sunnah zata kirata tace bazatazo ba?ko kuwa aikin bautar da kikeyi an yantaki ne?"cikin tsawa take magana, Bude baki hajiya karama da hajiya zainab sukayi suna kallon ikon Allah, Dakyar Fatima ta hadiye wani mugun miyau na bakin ciki sanan tace cikin sanyin murya "kiyi hakuri lokacinda kika Aiko kirana,Nan anrigada an Aiko kirana ko kafin tazo shiyasa nace Mata tace Miki zanzo idan nazo Nan naji Kiran da akemun" Fincikota deejahmah tayi ta baya ta Fadi kasa,da sauri hajiya zainab ta Mike tsaye cike da masifa "dakata Mara kunya,kibari idan tazo saikiyi Mata cin mutuncin da zakiyi Mata Amma baa gabanmu ba wallahi tunda rashin kunyarki takai kishigo Mana daki Babu ko sallama,sanan ki rufe idonki kina kokarin ciwa Yar mutane mutunci to baki isaba kinyi kadan Khadija ai mafarkina be taba bani fitsararki ta Kai haka ba,Dan haka ki bacemun daga gani tun kafin nawa borin ya tashi insauke akanki".... Takaicine ya lullube deejahmah wani kululun bakin ciki yazo ya tokare Mata wuya Wanda yasa idanuwanta suka rufe ruf saboda tsananin bakin cikin abinda hajiya zainab tayi Mata gaban Fatima Amma dikda haka be hanata bude baki tayi magana ba "Ummu karya takeyi tun dazun na aike kiranta Taki zuwa saboda ni ta rainani shiyasa" "Da kika aika kiranta batazoba sai kika shigo Mana ko arzikin sallama bamu samuba ballantana gaisuwa dagani kuwa har uwar mijin Taki Anya Khadija wannan halin naki Zaki canjashi kuwa?rahina tayi Miki muguwar tarbiyyar da sai kinyi danasani Mara amfani a rayuwarki Nan gaba kadan,ki bacemun daga gani tunban gaggaura Miki Mari ba Mara kunyar banza" Jikin a sanyaye deejahmah ta juya batare da tace komiba zuciyarta nayi Mata suya,Bata da wani damar daukar hukunci a gaban ummu saboda sanin halinta Bata daukar raini haka ta fice cike da takaici,Mai makon tayi sashen da friends dinta suke sai tayi sashin hajiya babba..... Juyowa hajiya zainab tayi tana zazzaga masifa "wallahi wanan yarinyar da ake Shirin aurawa kabiru an hadashi da aiki,Domin batada tarbiyya ko kadan tun suna yara nasan halin deejahmah Bata laifi komi tayi daidaine a wajen rahina,banji Dadi ba ko da can da akace zata auri habibu balle yanzun da lamari ya juya Kan kabiru mutumin kirki" Tsaki taja ta juya ga Fatima wadda ke durkushe ko motsin kirki takasayi,zuciyarta cike da fargabar abinda zai biyo baya,muryar ummu ce tadawo da ita daga tunanin data fada "Makulli zan baki kije wancen sashin na can cikin gida ki bude ki gyaramun shi,tun shigowarmu nasa aka kaimun kayana can,Amma kafin kije kiyi aikin ki tabbatar kinje kinyi wanka kin cire wadanan kayan na jikinki kin wanke su dan bana kaunar datti ko kadan bazakije gyaran gidaba kema jikinki kaca kaca"...ta karashe maganar da kafe Fatima da idanuwa.... "Ranki ya dade kayana guda daya ne idan na cire wanan Babu Wanda zan canja sai Kuma kayan gida da nake dashi" Juyowa ummu tayi ta dubi Maryam dake durkushe a gefe "ke jaki kitchen kisamu lantana kice nice nace taje wajen jakadiyya tace a Bata Kaya irin na jikin faty ki kawomin yanzun Nan" "Toh ranki ya dade"..... Cikin mintuna da Basu wuce goma ba saiga Maryam ta shigo hannunta dauke da Kaya jajaye irin wadanda kuyangin gidan ke sawa ta shigo ta durkusa ta mikawa ummu "Mika Mata su" Hannun Fatima na rawa tasa ta amshi kayan,sanan hajiya zainab ta Miko Mata makulli ta Mike da sauri ta fice..... ********** Kuka sosai deejahmah keyi a jikin mahaifiyarta Tana fadin "kamar ni mama a wulakantani gaban baiwa kuyanga?baiwar ma kaskantacciya cikin sauran bayi?wallahi bazan yardaba sai na dauki fansa a wajen Fatima" Cikin tsananin bacin Rai da tashin hankali hajiya rahina ta ture deejahmah daga jikinta ta Mike Tana huci ta fice a dakin hajiya babba ta rufa Mata baya basu zarce ko inaba sai dakin hajiya karama,.. Koda suka shiga ummu na zaune da mama karama suna taba Yar hirarsu suka shigo dakin Babu ko sallama, Daga tsaye hajiya rahina ta juya baya cike da rashin mutunci tace "nazo inji baasin wulakanta Yar sunnah Akan shegiya" Murmushin kasaita ummu tayi ta dago Kai ta kalli rahina kadan sanan ta girgiza Kai "banyi mamaki ba da Khadija ta shigo Mana daki kerere babu ko sallama ta zuba rashin mutunci Ashe gado tayi a wajen uwarta,shiyasa masu iya magana ke cewa barewa bazatayi gudu ba danta yayi rarrafe yanzun kinzo ramawa yarki ne kenan rahina?to Bismillah"....ummu ta cigaba da kada kafa, Hajiya babba ce a fusace tafara magana "haba zainab wanan abin da kikayi kin dauka abune Mai kyau?a tunaninki bare yafi Dan uwanki ko?baren ma shegiya tsintacciyar mage?ke har kinada bakin wulakanta diyar Yar uwarki a gaban bayi?".... "Dakatamun hajiya,ke matar Dan uwana ce Kuma Dole in mutuntaki saboda haka ki rike bakinki wanan abinda ya shafi Yan uwa ne ki rike matsayin da Allah ya baki"... Takaicine ya lullube hajiya rahina jikinta har kyarma yakeyi ta juyo ga ummu Tana fadin "ai ni dama nasan cewa bakya kaunata baki kaunar abinda na Haifa,wayasani ma ko bakin ciki kikeyi da deejahmah kikai Mata wanan wulakancin a gaban wanan matsiyaciyar yarinyar" "Rahina matsiyaci shine Wanda zai tashi ranan tashin kiyama bashida komi na ladan ubangiji,ke baki Isa ki kalli wani kice Masa matsiyaci ba wallahi,sanan yarki gyara nayi Mata na dauka ta dauki gyaran Ashe wuta taje hasowa to tayi daidai Kuma zan gamu da ita,saboda haka ki bacemun daga gani tunban Bata Miki Rai ba kema Dan niba saarki bace "... Gyara tsayuwa hajiya rahina tayi tana tafa hannu Tana fadin "kome Zakice kice Amma a kiyayarmum yarinya Babu ruwanki"...Tana karasa magana ta fice Tana surfa balai ,hajiya babba juyawa tayi ta bi bayanta cike da takaici.... ******* Deejahmah kuwa ganin tijarar da iyayenta sukayi yasa tasamu sassaucin takaicin da takeji a zuciyarta dikda ta kudiri aniyar Rama abinda akayi Mata a Kan Fatima kota halin Yaya, Dakin kawayenta ta shiga dukkansu suka bita da kallo,saboda dik Wanda ya kalleta babu tantama sai ya fahimci Tasha kuka, Neman wajen zamanta tayi ta zauna,....teemah dollar ta Dan kalleta cike da tsaigumi tace "haba ranki ya dade,daga tafiya sai Muji shiru?kodai kinfara kukan rabuwa da momy ne Kinga yadda kyawawan idanuwanki suka canja kala?"....takaicine ya lullube deejahmah Jin abinda kawarta ke fada, Shiru tayi Tana girgiza kafa minti minti Tana sauke kwafa daga bakinta sanan ta juyo gefenta ta ruko hannun teemah tafara magana cike da bakin ciki muryarta a dishe"wallahi tallahi saina wulakanta yarinyar Nan saina tabbatar da ta Zama abar kwatance saitayi data sanin shiga Ramin damusa"... Cikin rashin fahimta teemah ke kallon deejahma yayinda ilahirin Yan dakin friends dinsu suka baza kunnuwa Dan Jin kanun labari,....cije lebe deejahmah tayi "Zaki fahimci abinda nake nufi Nan gaba kadan idan na aikata Mata abinda na kudura a zuciyata" Matse hannun deejahmah tayi tanadan girgizata"haba princess bai Dace ki tsaya furta Zaki dauki fansa akan baiwarkiba wadda kikeda yancin sawa a tsireta ma kowa ya huta fadin Zaki dauki fansa tamkar cewa tafi karfinki ne yasa kike wanan ikirarin,ai aiwatar da abinda kikeso a lokacin da kika gadama saboda ita mallakinki ce" Takaici ya Kara rufe deejahmah tamkar ta fashe da kuka,babban bakin cikinta be wuce tunanin abinda Fatima sukayi da yarima ba a dakin da akace ta shiga,....bisa alamu ta rigada ta fahimci Yana son yarinyar soyayya suka makale sunayi kenan?....Nan da Nan fuskarta tayi jajir saboda takaici da bakin ciki.... ********* Gyaran sosai Fatima keyi a bangaren hajiya zainab Wanda yasha Kura saboda dadewa da yayi baa budeshiba,...dakuna uku ne cikin sashin dik Saida tabi ko wani daki tayi gyara na musamman ta shimfida musu zannuwan gado tayi mopping dik inda wata kura ta makale ,sanan ta shiga ko wani toilet ta wankeshi tass suka fita, Har kitchen Saida ta fidda duka wanke wanken sashen ta wankesu Tass ko wanne ta jera shi a mazauninsa, Fadin yadda ta gyara parlorn hajiya zainab Bata lokacine dik uban kurar da dattin ciki Saida ta share tayi goge goge,..wajen drawer din gadonta taga burner da turaren wuta Nan da Nan ta hada ko Ina ya dauki kamshi cikin gidan Wanda tamkar be tabayin dattin da yayiba, Koda ta Gama aikin can barandar bayan dakin hajiya zainab ta nema ta zauna Tana maida numfashi,minti minti takan tsinci kanta cikin faduwar gaba Wanda batasan dalilinta na yin hakanba,har magriba ta risketa a Nan tayi sallar magriba sanan ta rufo gidan ta fito ta nufi sashen cikin gida.... ******** Suna zaune sun idar da sallah suna zazzaune da wasu kannen hajiya karama wadanda sukazo biki daga kasar Sudan ta shigo bakinta dauke da sallama, Ta zube a kasa ta gaida kowa a dakin,sanan ta juya inda hajiya zainab ke zaune tanajan carbi ta tsugunna hade da Mika Mata key din gidan tace cikin sanyin murya "na Gama ranki ya dade" Daga Mata hannu hajiya zainab tayi batare da ta amshi makkulinba Saida ta shafa adduar ta sanan tace "yauwa Fatima ko ki dauki wata daga cikin kuyangar gidan Nan kice nace kuje ki dafamin abinda zanci Dan bazanci abincin gidan Nan ba Kuma nawa nakeso a dafa min".. "Mai zaa dafa Miki ranki ya dade".. "Jeki min couscous da miyar hanta kije friege din gidan Nan ki dauki hanta Dan yau na dawo Babu komi a gidana kuje ki dafamin".. Fatima ta Mike Dan cika umarninta ta juya hajiya zainab ta dakatar da ita "kin ma iya abincin kuwa?karkije kimun shirme " Tsugunnawa Fatima tayi daga inda take sanan tace"na iya ranki ya dade a kitchen nake ai a Nan din " Daga Mata Kai tayi hade dayi Mata nuni da hannu da taje..... ********* Fridge Fatima taje ta bude ta ciri dik abinda take bukata sanan ta juya ta nufi sashen hajiya inda bilkisu ke Zama, Can ta taddata rakube gefe daya da sauri ta karaso cikin kasa da murya tace "kizo muje wancan sashin na waccen bakuwar tasani inyi girki Amma tacemun in nemi Dan rakiya saboda duhu ya farayi" Mikewa bilkisu tayi tana waige waige sanan tayi kasa da murya tace "jeki zanzo akwai abinda nake saurare a Nan"...batare da Fatima tayi musu ba ta juya tai tafiyarta, Daga can cikin dakin hajiya babba bilkisu ta kasa kunne Tana sauraronsu, "Inhar tayi amfani da wanan ya kwanta da ita to tabbas shida wata mace harabada,sanan babu makawa zata dauki ciki Kinga burinmu ya cika dan wata Fatima ma mantawa da ita zaiyi" "Amma hajiya Naga wanan abun tamkar ruwa beyi kamada magani ba"... "Ehh Mana bazakisan amfaninshiba sai deejahmah Tasha komi ya faru zakice nabaki labari tafiyayya aka kawoshi daga can a balaq garin buzaye nasa akayoshi ga Yar aminiyata Nan shiru a gidan miji Kuma infada Miki anayi tasamu ciki" "Kai hajiya nagode Allah ya saka Miki da alheri banida kamarki a rayuwata wallahi.....burina ya kusan cika kenan yata zata haifawa sarki jikan fari" Dariya Suka kwashe dashi sanan hajiya babba tace "bude drawer dincan kisa shi ciki gobe bayan sungama kamu sai tazo Tasha ta wanke fuska,to harshi tsoronta zai rinkaji" "Hajiya kin tabbatar idan ansaka a drawer din can bawani Abu?" "Babu karki damu Babu me shigomin daki sai bilkisu itama na amince da yarinyar ne don ko shiga shirgin sauran bayin gidan Nan batayi kullum muna tare da ita,itakadai yanzun nake Bari ta shigomin daki Kuma idan ta ganshi zata dauka zam zam ne,...yanzun ki tashi mune fada wajen sarki Dan ya Aiko jakadiyyarsa kiranmi inaji anfada mishi abinda ya faru ne dazun" "Owk".... Jin alamun zasu fito da sauri bilkisu ta koma can cikin parlor inda babu Wanda zaiyi zargin taji wani Abu... Zuciyarta ke tsabanin harbawa sauri da sauri tunanin yadda zatayi takeyi take mafita tazo Mata... A parlor suka taddata a rabe tayi shiru,hajiya babba ta kalleta tadanyi murmushi tace"bilki bakije cikin Yan uwanki ba tunda Babu abinda zakimun?" Cike da ladabi bilkisu ta kakalo yake tadan durkusa "ranki ya dade Ina Nan,nayi gyaran parlor ne nace Bari idan kinfito in tambayeki idan kinada bukatar a kakkabe Miki cikin daki saboda yau Naga gidan ya kacame ko Ina da Dan datti " Jim kadan hajiya babba tayi "kinyi tunani to a kakkabemun daki kafin mudawo idan kingama ki rufemin bedroom din da makulli ki bude waccan drawer din kisa makullin ciki sai kije abinki tunda dare yafarayi" "Toh ranki ya dade" Wani kallo hajiya rahina takewa bilkisu sanan ta rufawa hajiya babba baya suka fice, Kamar jira takeyi ta fada dakin a guje direct drawer ta bude ta shiga waige waigen neman abinda suka ajiye,daga idonta sama tayi ta sauke idonta Akan gorar swan Wanda bashi da maraba da ruwa,jikinta ne ya Kama rawa tunani kala kala ta shigayi sanan daga karshe ta yanke shawarar canja ruwan ciki, Da sauri ta nufi bayi ta bude ta shige ta rufo kofa jikinta sai kyarma yakeyi zufa na zuba a jikinta dakyar ta bude ta antayar da ruwan ciki,ta samu ruwan fanfo ta maida yadda ruwan yake ta goge gorar ruwan ta fice ta ajiye inda ta gani gabanta na tsananin faduwa.... A gaggauce ta kakkabe ko Ina ta gyera gadon ta rufo kofar yadda aka Bata umarni tayi ta fice,jikinta be bar rawaba tunanin tonuwar asirinta take.... ******* Kwankwasa kofar gidan tayi,da sauri Fatima tazo ta na kici kicin budewa sanin tasan bilkisu ce, Tana bude kofar sukai Ido hudu da yarima wani kallon tuhuma yake binta dashi hade da mamakin abinda ya kawota Nan gidan, Wucewarta tayi ciki ta nufi kitchen batare da tace Masa komiba kirjinta na tsananin bugawa, Ciki ya shigo Yana kwalawa hajiya zainab Kira "ummu"(yadda suke kiranta dashi)shiru yaji ya shiga leka dakunan dik Babu ita Amma komi a gyare, Mamakine ya kasheshi Tana tsaye ganan standing gas Tana juya miyar da takeyi kamshi ya karade ko Ina ya shigo ya tsaya a bayanta,gabanta ya tsananta faduwa saukar hannunsa taji a kafadarta ya juyo da ita Tana facing dinta Yana jifanta da wani irin kallo Wanda ita kanta taji ta kasa aiwatar da komi "bintu shine akayi banza Dani aka wuce aka barni bazaki tarbi mijinki ba ko "Yana Shirin janyota jikinsa taja da baya Tana fadin "Haba yaayah nidai kabari kada hajiya tazo Dan Tana gab da shigowa ta ganmu a Nan " Ta juya ta kashe gas din ta Mika hannunta Tana kokarin Ciro kuloli ya fizgota jikinsa ya rike ta sosai "to tazo Mana bakisan ni Dan ganta bane a wajen ummu?inda zata ganmu ma ba abinda zatace".. Turo baki tayi tana kunkunai hade da ture hannunsa'naji kabari inkwashe abincin Nan sai kace dik abinda zakace" Makale kafada yayi ya sauya murya cike da shagwaba "umm umm naqi" Dariya ta kamayi Masa Dan yadda yayi da muryarsa Dole ne ko waye yayi dariya, Batare da tace komiba ta shiga kwashe abincin fuskarta dauke da murmushi,Yana tsaye a gefenta ya kafeta da Ido yadda take aikin Yana gefenta sai zuciyarsa ke ayyana masa sundace da juna tamkar Miji da Mata, A bangarenta mamakinsa takeyi yadda yakeyin abubuwa tamkar ba Dan sarautaba,mafi yawancin masu mulki akwai kasaita da ji da Kai Amma Banda yariman ta ko dai itace yakewa haka oho a haka ta Gama gwashewa ta dibo kulolin tazo parlor ta jera dik inda tayi Yana biye da ita kamar bindi Tana faman kyalkyala Masa dariya a haka sukazo parlor ya jona tv ya kunna ya koma kujera ya zauna tazo ta bayansa ta durkusa da kanta daidai kunnensa cikin rada tace "yaayah barka a Nan ni zan wuce kafin hajiya tazo"....lumshe idanuwansa yayi Yana Jin wani Abu nayi Masa yawo a jiki yadda takeyi Masa rada a kunne hannunsa yakai daidai fuskarta ya shafa "kina nufin tafiya zakiyi?" Ta bude baki zata amsa aka kwankwasa kofa ....da sauri ta Mike daga durkuson da tayi jikinta har rawa yake Tana adduar Allah yasa dai ba hajiya bace... Tana budewa sukai Ido hudu da bilkisu ta sauke ajiyar zuciya, Kallon kallo suke yo da bilkisu "meye kikemun kallon rashin gaskiya" Murmushi Fatima tayi takai Mata duka a kafada "kema yau kinamun kamada marasa gaskiya"....dariya Suka sa su duka a tare suka shigo da bilkisu,.tsayawa tayi turus Tana kallon yarima da ya hade Rai Yana kallon tv Kallon Fatima tayi da tambaya a fuskarta ,....dage Mata gira tayi sanan ta rada Mata a kunne "tunda bakizo ba shi yazo jiran matarsa"ta kashe Mata ido daya Tana dariyar keta, Tabe baki bilkisu tayi "aikinku kenan kamar chewing gum"...dage Mata kafada Fatima tayi tana dariya kasa kasa Mikewa yarima yayi ya kalli Fatima ta gefe "Bari inje tunda kinsamu Yar Taya Hira dama na dauka ummu Tana Nan ne" Ido ta kifta Masa Tana dariya ya wuce, Waje suka samu suka zauna bilkisu na murmushi tacewa Fatima "wato yanzun kin Kuna bakijin tsoro ko?kin manta ke baiwace kaskantacciya inji su" Dariyar takaici Fatima tayi sanan ta fuskanci bilkisu da kyau tace "a zahiri ni baiwace kaskantacciya ,Amma a badini ni yace cikakkiya Mai yanci,bazasu fahimci hakanba sai Nan gaba kadan zasu fahimci hakan lokacin da deejahmah ta koma baiwa ni nakoma uwargijiyarta" Dariya sosai bilkisu keyi lokacinda sukaji karar zaa bude Kofa da sauri suka saisaita kansu, Hajiya zainab ce hannunta dauke da sadik da sauri Fatima ta Mike ta amsheshi Tana fadin "barka da zuwa hajiya" Kallon yadda Fatima ta gyara gidan hajiya zainab keyi Tana murmushi sanan ta nisa tace"Kar inkarajin kin kirani da hajiya ko ranki ya dade ki kirani da yadda kowa ke kirana ummu". Sunkuyar da Kai Fatima tayi ta juya taje kwantar da sadik,minti kadan ta fito ta tadda hajiya zainab ta baje a parlor bilkisu ta Mike Dan su wuce ta kallesu ta gefe "dare yayi bazaku iyabin hanyar Nan ku kadaiba Nima kabiru nasa ya dakko mota ya kawoni Kuma Koda zai dawo sai anjima Dan akwai maganar da zanyi dashi,yanzun dai kusamin abinci kuyi zamanku anan da sassafe kwa koma cen din" Kallon kallo bilkisu sukeyi da Fatima sumaiwa juna murmushi sanan Fatima ta tsugunna tafara serving ummu da abinci.... ******** Wajen Sha daya na dare yarima ya shigo sashen hajiya zainab Yana sanye da jallabiya don har yayi Shirin bacci takirasa tanason magana dashi... Suna zaune a parlor take shaida Masa Taji dik abinda ya faru tun daga farko har karshe har maganar aurensa da Fatima....shine ma yasa takeson magana dashi... Ajiyar zuciya ta sauke ta sanan ta dubesa ta Soma magana kasa kasa Dan bataso su Fatima su jiyo "a yadda Naga yarinyar tanada natsuwa ga ibadah sanan jikina ya bani aurenku alheri ne Amma naji Mai martaba yace Wai sai ansamu lokaci kafin ayi bikin" "Ehh ummu haka yace".... "Toh ni zanyi karambani Dan zansamu shi Mai martaba mu tattauna Akan ayi auren nan karshen shekara tunda yanzun muna watan biyu ko?" Dadine ya lullube yarima ya shiga faraa yace "ehh ummu da zaayi hakan da zaifi" Ta juyar da Kai fuskarta a daure "insha allahu zan nemi Mai martaba da maganar nasan zai saurareni Allah ya zabi abinda yafi Zama alheri Amma kayi shiru ko yarinyar karka fada Mata" Yarima ya sunkuyar da Kai Dadi na ratsashi "insha allahu".... "Tashi kaje dare yayi"....Dan Dadi dakyar yarima ke taka kafarsa ya fice.... ****** Washe gari da wuri wuri su bilkisu suka gyarawa ummu gidan ummu sukai Mata abin karyawa sukayiwa sadik wanka sanan sukai Mata sallama suka wuce..... Shirye shirye yau kawai akeyi na kamu har masu decorations aka Kira sukayi sukayi decorations a babban filin da aka ware Dan yin shagalin biki suka sassaka kujeru da runfuna sosai wuri ya tsaru tsayawa fadar yadda wurin yayi kyau Bata lokaci ne..... Tunda Fatima ta wayi gari take faduwar gaba haka kawai saidai ta ambaci innalillahi wa Inna ilaihi rajiun,hasbinallahu wa niimal wakil kawai takeyi..... ******* "Na Gama shirya dik yadda komi zai wakana a wajen Nan ranki ya dade yadda kika zubar da hawaye Akan shegiyar Nan itama saita zubar akanki saitayi danasanin shiga hurumin da ba nataba"cewar Rahane dake tsugunne gaban deejahmah wadda ke faman shiri Mai kwalliya zatayi Mata, Murmushi deejahmah tayi ta jinjina Kai alamar gamsuwa sanan tayi Mata nuni da ta fita.....ta Mike ta fice a dakin.... Shirye shirye kawai akeyi gida ya rikici da Yan uwa da manyan masu kudi wadanda akeji dasu su kawai ke shigowa gidan ana parking hadaddun motoci.... ***** "Fauziyya ki tabbatar kinyi abinda ya Dace yadda na fada Miki kada asamu matsala,Dan inaso ingama da karamar alhakin ne kafin inkoma Kan babbar dikda itama cikin sauki zanyi yadda yadace" Fauziyya tayi murmushi tace"insha allahu innah ai bazata ganeba" "Nasani shiyasa ma nasaki ki tabbatar kin Bata Kuma kinyi yadda nace" "Insha allahu" "Tashi kije faizah tun dazun ta shirya Tana jiranki "..... *Muje zuwa* *SLIMZY😍*🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* 34 Yan matan amarya uku ne tare da amarya a wani kebabben daki inda nan ne ake tsarawa amarya kwalliya wadda ta fito da ainihin kyawunta Domin ita kanta deejahmah ba baya ba wajen kyau da diri wadda fatarta ta kasance ita ba faraba ita ba baka ba fatarta tamkar mutanen Etopia ga manyan idanu da take dasu farare tas da yalwar Zara zaran gashin idanuwa sanan ita ba doguwa bace ba gajereba Tana cikin matsakaitan Mata Mai Dan jiki da shape dai dai ita....doguwar Riga ce jikinta kalar golden da kyalli kyalli na net da stones Wanda akai kwalliyar rigar dashi head dinta ma golden colour tayi matukar kyau na kece raini fuskar Nan Tata wadda ta kasance Koda yaushe a daure take yauma hkn ya kasance Amma hakan be tsantsar kyawunta bayyana ba... Mayafi aka kawo Mai tsadan gaske aka lulluba Mata akanta wayarta ce ta fara Haske da sauri ta cire pin din wayar Tex ne ya shigo kamar haka ... _HELLO IN D NEXT 5 MINUTE IDAN BAKI FITOBA WALLAHI BAZANJE WAJEN TARON BA WAYE YARONKI DA ZAKI SHANYA...MTSWW_. wani mugun takaicine ya rufeta wato yafi karfin ya kirata a waya ma saidai yayi Mata Tex,kwafa tayi hade da girgiza Kai cike da takaici a cikin ranta tace "zaka shigo hannu Dan rainin hankali"...a zahiri kuwa dago idanuwa tayi cikin mayafinta tana kallon su teemah dollar suna kashe selfi,haushi ne ya lullubeta dakyar ta bude baki cike da takaici tace "Sunita kubar daukar hoton Nan haka mu ake jira a wajen Nan yanzun haka prince ya turomin Tex suna waje" Dariya Sunita ta kamayi "soyayya wanan wani irin ango ne da baya Kira sai Tex" Teemah dollar ta karbe zancen "kedai Bari zee baby wanan amgon da abokanansa Yan Jin Kai ne domin Basu nemanmu sai amaryarsu zamu Rama wajen siyan baki"suka sheke da dariya suka tafa A k'ule deejahma tace"Kun fiye son magana muje da Allah" Saida suka kakkashe hoto da deejahmah sanan suka fito Tana tafe tamkar bazata taka kasaba ga wani uban takalmi me shegen tsini da kyau Wanda tasa Tana takawa a hankali mutum biyu suka tsaya gefe da gefenta daya na biye dasu a baya... A kofar harabar gidan sukaga motoci reras na abokanan ango cike da xumudi Sunita ta bude bakar mota zata shige Ahmad ya juyo da sauri ya dakatar da ita "motar amarya da ango ce wanan".turus tayi ta juya Tana kallon yarima Wanda ya hada girar sama da ta kasa tamkar be taba dariya ba haka ta juya ta wuce, Deejahmah na sako kafa cikin motar kamshi ya baibaye motar tamkar anyi barin turare,..ta gyara zamanta a baya kusa da yarima ta zauna Ahmad ya rufo kofar ya zagayo gefen driver ya zauna ta glass din mota yake kallonsu Yana dariya kasa kasa cike da zolaya yace "ranki ya dade,sarauniya deejamah amaryar sarki Mai jiran gado Allah ya Sanya alheri" Murmushi cike da kasaita Sanan ta amsa cikin sassanyar murya "nagode"... Fuska a daure yarima yace "Ahmad ka manta uwar gida ce?nan gaba kadan amaryarta zata shigo Wanda zataci girma ta barwa amarya Zama sarauniya tunda ita babba ce"...ya waigo ya kashe Mata ido... Takaicine ya lullubeta suna tafe a hankali a mota kusan second talatin tamkar bazatace komiba tsulum yaji tace"sai na so na bada kofa wata zata shigo gidan mijina,Domin mijina nawa ne ni kadai Kuma baayin sarauniyoyi saidai ace sarauniya,mulki da sarauta na ya'yan asaline ba tsintattu ba" Ta wurga Masa harara daidai lokacinda suka karaso wajen mota ta tsaya tayi parking .... ********* Da sauri sauri Fatima tayi wanka ta fito bayan sunkammala ayyukansu dikda ranta da yake abace Amma bazai hanata zuwa wajenba kodan farin cikin yarimanta, A dakinsu ta tararda bilkisu rike da Kaya Tana jujjuyawa,...turus Fatima tayi tana kallon kayan dake hannun bilkisu Tana juyawa Wanda akanbisu akayi musu sala Sala yankan wulakanci da almakashi, Dafe kirji Fatima tayi zuciyarta na tsananin bugu "innalillahi wa yayi wanan aikin?".. Girgiza Kai bilkisu tayi tace "ninasan zaa Rina Wai an Ari zanin mahaukaciya Domin dazun da safe Naga lokacinda rahane ta shigo dakin Nan Kuma zato zunubi Koda ya kasance gaskiya itace ta shigo tayi mugun aikin Nan" Hankalin Fatima ba karamin tashi yayiba ta karaso inda bilkisu ke zaune hannu rike da Kaya ta amshi kayan ta shiga jujjuyawa Tana girgiza Kai ,take hawayen bakin ciki suka shiga zubowa a idanuwanta tasa gefen dankwalinta ta goge sanan ta dago Kai ta dubi bilkisu wadda ta tsareta da idanuwa... "Wai dik wanan wulakancin da akemun saboda na fito a matsayin shegiya ne?ko ko saboda kaddara ta fadamun Akan habibu shiyasa ake kokarin aga bayana?shin Nina dorawa kaina rayuwar gidan marayu?ko ko ganin da sukamin a can sunada tabbacin nidin shegiya ce?kaddarar data fada mun Nina dorawa kaina?Koko Allah ya Riga ya kaddara cewa mutuwar habibu a hannuna take?menayi haka wani irin balai ne wanan?tsirara akeson a ganni a wajen kenan?"ta rushe da kukan ta kaici tayi jifa da rigar hannunta,hade da durkushewa a wajen Tana kukan bakin ciki... Janyo jiki bilkisu tayi ta matso kusa da ita ta shiga lallashinta"haba Fatima ai ya kamata zuwa yanzun kisaba da dik wani bakin ciki da takaici da ake kunsa Miki saboda kabiru,azabarki ta Karu ne saboda Kabir Yana sonki da badan haka ba da wani Abun zaa raga Miki,nasha fada Miki Akan ki Zama jaruma wanan koke koken dik ba naki bane ya kamata ki Zama idanuwanki sun bushe kema ki fara Rama wasu abubuwan" Dago Kai Fatima tayi tana jinjinawa idanuwanta manne da guntun hawaye "bilkisu lokacinda zan Rama wanan bakin cikin da nake kunsa Yana Nan tafe,lokacinda kowa na gidan Nan zai fara tunanin Anya nice kuwa Yana Nan zuwa Domin nayi alkawarin dik Wanda ya zalunceni ya cutar Dani bazan cuceshiba bazan zalunceshiba Amma inada hanya mafi sauki da kowa sai yaji a jikinsa wallahi zakice na fada Miki ko yanzun ma ba tsayawa zanyi a cigaba da cutar daniba abinda yake tauyeni be wuce kasantuwata a matsayin baiwa ba" Jinjina Kai bilkisu tayi cike da Jin dadin kalaman Fatima tace"Ina goyon bayanki dari bisa dari Yar uwata Allah ya cika Mana burinmu" "Ameen bilki"tasa hannu ta share hawayenta sanan ta Mike taje inda kayanta suke ta Ciro wata doguwar Riga baka Mai adon fulawas farare Yar kanti ce ta say a jikinta da Dan mayafinta Mai girma ta yane jikinta dashi ba karamin kyau tayi ba.... Itadai bilkisu sai bin Fatima da kallo kawai takeyi Tana girgiza Kai hade da guntun murmushi... Uniform dinta bilkisu ta mayar a jikinta ta shirya tsaf suka fito yare suka nufi wajen bikin.... ******** Isowarsu wajen wuri ya kacame anata famar ciye ciye da lashe lashe masu serving mutane abinci sai kaiwa da komowa sukeyi, Idanuwan rahane ne suka sauka Akan Fatima wadda take tsaye can gefe Tana karewa kowa kallo a cikin gidan Tana murmushin takaici, Yarima kuwa tunda ta kallesa sau daya Taji wani mugun kishi ya taso Mata ta Kauda kanta saboda Yar kwallar data ciko a idanuwanta, Durkusawa rahane tayi ta bayan deejahmah inda dama Nan ne wajen tsayuwarta kasancewarta baiwarta ,ta danyi kasa da murya kadan tace"ranki ya dade ga Fatima cen tsaye ta gefen hannun Daman mu a bangaren da aminanki suke" Da sauri deejahma ta dago Ido ta maida dubanta inda rahane ke fada Mata aikuwa direct idanuwanta suka sauka Akan Fatima wadda ke tsaye tamkar balarabiya tayi matukar kyau Wanda ita kanta deejahmar Saida ta shagala da kallonta sanan ta danyi tsaki ta kwanto da kanta cikin izzah tacewa Rahane "kiramun ita"... Rahane jiki na rawa ta kukkutsa cikin mutane ta karasa wajen da Fatima ke tsaye tasa hannu ta tabata hade da cewa "ke hawainiya Mai rikida?kije uwargijiyarki na kiranki" Murmushi ne ya subucewa Fatima Jin abinda Rahane tace"nakoyi rikida ne kafin lokacin rikidar tawa yayi Domin Nan gaba kadan zan rikida in koma hawainiya kamar yadda kikace"....galala Rahane tayi tana kallon Fatima wadda ta soko wadanan maganganun fuskarta dauke da murmushi, "Muje ko?"ta daga Mata gira daya,jiki a sukwane Rahane tayi gaba Fatima na biye da ita suna kukkusawa cikin mutane,take idon fauziyya ya sauka Akan Fatima wadda take ta Raba Ido tun tuni Tana nemanta dama, Har inda suke zaune Fatima da Rahane sukaje.... Dan durkusawa rahane tayi tace "gata ranki ya dade"... Dago Kai deejahmah tayi ta watsa Mata wani mugun kallo sanan ta bude baki cike da wulakanci da gadara ta Soma magana "waya baki umarnin canja Kaya daga kalar ja zuwa wani kala?....ko kinsamu yancine daga bauta zuwa cikakkiyar ya'" Daurewa Fatima tayi ta danne abinda takejin zuciyarta ta bada amsa da "ya kamata in sabunta kayan jikina ranar bikin iyayen gijina Domin intayasu farin ciki a wanan Rana data kasance ta farin ciki a garesu"... Amon sautin muryar Fatima ne ya sauka a kunnen yarima Wanda ke zaune a wajen kamar mutum mutumi,Jin muryar Fatima ya haddasa Masa faduwar gaba Wanda besan dalilinsa na hakanba,kasa jurewa yayi ya juyo gefen da yakejin wanan satin juyowarsa tayi daidai da dagowar idanuwan Fatima Wanda suka hadu Dana yarima take yaji wani Abu tamkar shocking na yawo cikin jikinsa tozali da kyakkyawar fuskar Fatima ya haifar Masa da hakan,...ajiyar zuciya ya sauke Yana Kare Mata kallo yayinda ita kanta fatimar dakyar ta Tattaro natsuwarta ta kawar da idanuwanta daga cikin nasa, Yan matan amarya dake gefe idanuwansu suna Kan yarima da Fatima da sauri Sunita ta zunguri teemah dollar "Wai Kinga kallon da prince yakewa waccen kyakkyawar yarinyar kuwa?Kuma a gaban deejahmah" Cikin kasa da murya teemah dollar ta Bata amsa "tsohuwar budurwarsa ce wadda take a matsayin baiwa a gidan yanzun haka,ni naji a majiya Mai karfi ma ita zai aura Nan da watanni kadan" Zaro ido Sunita tayi tana jinjina Kai "tabdijan Aiko deejah ta Gama yawo dik ranan da wanan yarinyar ta shigo gidan,Dan daga ganin yadda suke jifan juna da kallon soyayya kinsan Yana sonta" Dariya suka kamayi kasa kasa suna karewa deejahmah kallo wadda ta cika tayi famm tamkar zata fashe... Juyawa Fatima tayi da tafiyar Nan Tata Mai daukan hankali,yarima yabita da kallo hade da lumshe idanuwansa ya saki sassanyar ajiyar zuciya sanan ya juyo da kallonsa ga deejah wadda idanuwanta suka kankance saboda tsantsar kishi "ya kamata ki koyi yadda ake kallon soyayya kodan mijinki saboda gaba"....abinda ya rada Mata a kunne kenan ya koma ya jingina da jikin kujera... Can gefe Fatima ta nemi table ta zauna Tana sauke numfashi minti minti Tana sauke ajiyar zuciya wadda batasan dalilinta nayin hakanba murya tajiyo a gefenta Ana magana da sauri ta waiga cikin masu kawo abincine ya tsaya "ranki ya dade me xaa kawo Miki" Khausar dake tsaye a gefe ta karbe zancen da "waya ce maka bakuwa ce a wajen Nan?baiwa ce ta canja kamanni ta shigo Domin yin basaja saboda haka ba sai ka kawo Mata komiba matsayinka yafi nata a wajen Nan"ta karasa maganar da watsawa Fatima wata uwar harara hade da Jan tsaki tabar wajen....takaicine ya lullube Fatima batare da tace komiba ta cigaba da Zama wajen, Minti kadan fauziyya ta karaso table din Fatima taja kujera ta zauna hade da Mika Mata hannu Tana murmushi "assalamu alaikum" "Waalaikumussalam"Fatima tace hade da maida Mata da nata murmushin sanan tace"sai yanzun nake ganinki?haba faizah nadauka zakizo muzo tare?" Gyara Zama fauziyya tayi tana fadin "kiyi hakuri banzo wajen Nan da wuri bane wallahi Kuma sakonki shi ya zaunar Dani a gida wallahi " Cike da rashin. Fahimta Fatima tadan kalleta , "Ehh wallahi tsarabace aka kawowa mamanmu daga nijar shine na tsaya diba Miki kilishi da wani turare Dan agadaz Kya rinka shafawa idan kinyi wanka" Dadine ya cika Fatima "Kai Amma nagode wallahi inason kamshi banida yadda zaayine insamu turare inrinka shafawa kodan shiga mutane" Jinjina Kai fauziyya tayi tana kallon kyawun halitta da Allah yayiwa Fatima wani haushine ya turnuketa take taji tamkar ta shaketa,jinjina Kai kawai takeyi Tana kallonta Tana murmushi zuciyarta kawai ke Raya Mata "matukar kika shafa turaren Nan kin Gama yawo yarinya Domin jaba saita fiki mutunci a wajen Wanda kikewa rawan Kai" Dan kallonta Fatima tayi ganin yanayinta dik ya canja yasa tace "faizah kodai bakida lafiya ne yau?" "Mekika gani?" "Yanayinki ne Naga dik ya canja bakida annuri a fuskarki Babu faraa kamar jiya"ta tsareta da idanuwa Tana karantar yanayinta.... Girgiza Kai kawai fauziyya tayi "no bakomi yau hayaniya tasamun ciwon Kai wallahi" "Allah ya sauwake" Daga Mata Kai kawai tayi batare da tace komiba,dik yanayinta ya canja ba kamar jiyanba sanan yau tanayi Mata magana a takaice... Shagali kawai akeyi Yan matan amarya sai cashewa sukeyi yayinda hajiya babba da tawagar kawayenta suke zubar naira suna liki,fitowa dubu da amarya zatayi tai rawa yarima baya fitowa dik abinda sukeyi a zaune yake tamkar an dasashi... Haka akaita shagali wajen Nan Wanda dik inda Fatima tasa kafa fauziyya na biye da ita tanayi Mata basaja .....komai dake faruwa akan idon bilkisu ne tunaninta gabaki daya ya karkata wajen abinda ke hannun Fatima ne a jakar leda.... Baatashi taro ba sai karfe takwas na dare sanan jamaa suka fara watsewa suna tafiya gidajensu yayinda wasu ke shigewa cikin gida ciki kuwa harda baki wadanda dama yau suka sauka a gidan saboda biki.... ******** Hayaniya ce ta kacame sai surutu akeyi ta ko Ina saboda mutane dake cike a gidan ta ko wani bangare cike yake da mutane.... Sashen Yan matan amarya ne ya kacame da hayaniya ko wacce ta fiddo wayarta Tana kallon hotuna da videos din da akayi a wajen suna Hira suna dariya yayinda deejahmah zuciyarta take bakin Kirin Tana gefe a zaune Tana cika Tana batsewa da gudu kawarta tazo gefenta ta dafata Tana nuna Mata video dai dai inda yarima ya kafe Fatima da idanuwa wajen a slow yake tafiya "ranki ya dade kalli wani abu a wajen Nan wanan kawar mijin naki yadda suke jifan juna da wani kallo tamkar masoya" A fusace deejahmah ta juyo ta kalli Mai maganar Wanda dama a cike take famm tace "ba soyayya sukeyi ba Amma zan nuna Mata tayi gangancin hada Ido da idanuwa masu tsada a duniya saina shayar da ita mamaki ,sanan sai ta Zama baiwa a gareni Mai hidimar cikin gida na"...Tana Gama maganar ta fice a fusace dakin yayi tsitttt kowa ya bita da kallo.... Dakin hajiya babba ta shige a Nan ta taradda Fatima ansata aiki bayan ta tube Kaya sai mopping takeyi Tana hada zufa tana Ana kyararta hade da hantararta ai deejahma nayin tozali da Fatima tayi kanta Wanda hakan yayi daidai ta shigowar ummu dakin "Munafuka kin gamo karuwancin kindawo asalinki na baiwa?wallahi dik abinda kikeyi inasane dashi nasan cewa kin mallakeshi ne yasa yake kulaki Amma yafi karfinki" Rirriketa kawar mahaifiyarta tayi tana fadin "lafiya deejah meyafaru?meke tsakaninki da Yar aiki Kuma" Daga gefe hajiya babba ta sakarwa Fatima rankwashi a tsakiyar Kai ta shiga dukanta ta ko Ina Tana fadin "munafukar Allah kin zame Mana karfen kafa wallahi Dole ma ki hada kayanki kibar gidan Nan Dan ke balai ce annoba" A fusace hajiya zainab ta daka tsawa cikin dakin "meye haka kukeyi?Tara Mana mutane kukeso kuyi?Koko so kuke ku fallasawa duniya asirin da yake rufe a kasa kowa yaji?" "Wani asiri Banda Wanda itace tayi sanadiyyar mutuwar Dana daya tilo sanan saboda cin Amana aka dauko shegiya aka kawota cikin gidan Nan Wai ita marainiya bayan munji komi a gari cewa karuwa ce to wallahi saita bar gidan Nan tabar Mana zuriah yau din Nan ba sai gobe ba" Kuka sosai Fatima keyi yayinda hayaniya ta kacame cikin daki Wanda hakan yasa jamaar cikin gidan suka cika bangaren hajiya babba kowa na tofa albarkacin bakinsa,wadanda suka hayi maganar a sama suka shiga yiwa Fatima tofin Allah tsine, Jin hayaniya tayi yawa yasa yarima shigowa cikin gidan a guje yayo sashin hajiya babba Yana shigowa yayi tozali da Fatima Tana famar rizgar kuka,bece komiba yasa hannu yajata yayi waje da ita... A haukace hajiya babba ta Soma surfa balai Tana fadin "kamar yadda kakeson ganin karshena kabiru sai Naga karshenku a cikin gidan Nan daga Kai har ita matsiyaciyar yarinyar wallahi tallahi yau din Nan saita bar gidan Nan Kuma kaida aurenta saidai a kiyama" Yadda take kumfar baki kawai hajiya zainab ke kallo Tana watsa Mata wani irin kallo dakyar ta bude baki cike da takaici tace "Haba hajiya wanan wani irin Abu kikeyi haka kamar karamar yarinya sai a shigo cikin gidan Nan aga da yaran cikinki kike balai saboda waccen haddasanar ta kunno balai ko?to wanan rantse rantse da kikeyi na banza ne Domin Babu abinda zai yuwu a cikin maganar da kike fada,wanan yarinyar da kuka dau Karan Tsana kuka Dora Mata saboda Bata da gata ku kune masu gata Kuna ganin Allah ba zai saka Mata ba?to wallahi Allah zaiyi Mata mummunan sakayya sanan Ina Mai gargadinki Akan ki gaggauta canja tunaninki idan ba hakaba zan shayar dake mamaki"..... Dik jamaar dake wajen shiru akayi tamkar anyi ruwa an dauke sautin muryar ummu kawai ke tashi a wajen,.... Takaicin maganganun ummu ne ya lullube hajiya babba ta zaburo ta tsaya a gabanta Tana fadin "Akan kabiru da wanan tsinanniyar yarinyar kikeson yimun rashin kunya zainabu?kikeso ki nuna mun Isa?me kika Isa kiyi a wajen Nan Koko kece kikeda damar yanke hukunci Akan baiwata kutanga ta" Dariya kawai hajiya zainab keyi Tana tafa hannu Tana kallon hajiya babba ido cikin ido sanan ta nisa tace"zan nuna Miki isata kuwa,Domin Fatima baiwarki ce kuyangarki ce Amma yau cikin bainar jamaa kowa zai shaida cewa na ya'nta ta zuwa cikakkiyar ya'sanan rukonta kacokan zai dawo hannuna Kuma ko kinki ko kinso Dole kibi wanan umarni" "Karya kikeyi zainabu baki isaba wallahi kinyi kadan..... Bata karasa maganaba yarima ya shigo dakin fuskarsa Babu walwala dakyar ya iya bude baki yace "Mai martaba Yana kiran taron gaggawa yanzun a fadarsa".... Yana Gama fadin haka yayi ficewarsa kowa ya bishi da kallo yayinda hajiya zainab ta rufa mishi baya...... *Muje zuwa* *SLIMZY🥰*🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* 35 Hajiya zainab ita tafara Isa fada bayan yarima,a can ta iske fatima a gaban Mai martaba Tana faman zubar da hawaye tamkar an bude famfo kallo daya tayi mata ta kauda kanta saboda tsananin tausayin yarinyar da ya lullubeta take taji idanuwanta sun ciko da hawaye ta nemi gefen da Fatima ke zaune ta zauna da kyar ta bude baki tace "ya Isa haka Fatima kiyi Shiru insha allahu komi zaizo karshe Domin wannan cin zali yayi yawa na tabbatar da Mai martaba adalin sarki ne zai duba lamarinki kinji share hawayenki"ta kamo Fatima zuwa jikinta ta shiga goge Mata hawaye,a haka su hajiya babba suka shigo kowa ya hallara cikin fadar... Wanan karon sarki ransa yayi mummunan baci a fusace yake sai kaiwa da komowa yakeyi Saida kowa ya Gama zuwa sanan yanjuyo da kakkausar murya ya Soma magana "Kun bani mamaki kun zubarwa kanku da mutunci sanan Kun dauki wuka Kun dabawa cikinku yadda kuka taru waje daya Kuna hayaniya kuka kokarin fallasa asirin cikinku na tabbatar cikin gidan Nan ba zallar Yan uwa bane ciki harda na waje,yau Koda Yan uwane bai kamata kutaru ku nemi zubarwa da wanan masarautar mutunci ba " Gyara Zama ummu tayi ta ce cikeda ladabi "Allah ya huci zuciyar Mai martaba baa kyautaba sharrin shaidan ne" "Babu ruwan shaidan a wanan lamari sai sharrin zuciyoyinku wadanda gabaki daya Babu abinda kukasa a Rai sai son Kai da son zuciyane" Ya juyo inda hajiya babba ke zaune kanta a kasa Tana famar hura hanci "hajiya safiya kinbani mamaki ban taba tunanin ko kowa zaiyi rashin hankali ke zakiyi ba" Da sauri ta dago "ranka ya dade..." "Dakatamun hajiya Babu abinda kowa zaicemun a wajen Nan Domin ba yarda zanyi daku ba tunda kunci amanata kunci amanar marainiyar Allah Kuna neman aikata lahira to na yanke shawarar dauketa daga gidan Nan kafin ku kasheta" .. Jin haka yasa hajiya zainab saurin fadin "Allah ya huci zuciyarka ranka ya dade ai idan aka Bari har aka fita da yarinyar Nan zuwa wani waje Domin rukonta munyi asarar ladan da muke samu ta sanadiyyarta bazan taba bada goyon baya a fita da yarinyar Nan daga gidan nanba"... Harara kawai hajiya babba ke jifan ummu da shi,Jin furucin da tayi, "Yanzun ke zainabu nasan kinada hankali Kuma kin girmi rahina kinsan ya kamata inaso ki fadamun yau abinda ya faru a cikin gidan Nan a gaban kowa Dan banaso daga baya inji wani gutsiri tsoma Yana tashi... Murmushin Jin Dadi hajiya zainab tayi sanan ta gyara Zama murya kasa kasa ta kwashe kaf abinda yafaru Wanda tagani a idanuwanta ta fadawa Mai martaba sanan ta Kare maganarda "dama da Naga haka shine na yanke hukuncin yanta yarinyar ta dawo hannuna da Zama tunda ni dama Allah be bani haihuwar ya mace ba sai in riketa har zuwa lokacinda zaayi aurenta da shi kabirun,...shine nakeso a yanta ta" Ran Mai martaba ba karamin baci yayiba a fusace ya karbe zancen da "ai yarinya ya'ntacciya ce Domin yace kamar kowa tunda baa yaki aka siyota a kasuwar bayi ba balle a kirata da baiwa sanan maganar kikeso a yantata?aike kin Isa ki yanta kowa a gidan Nan Domin inda ke macece da idan na mutu banida da' namiji kece Zaki gaji mulki bayan ni Domin bayan yayana da Allah ya saukarwa kaddarer rashin lafiya ai saini saike sanan ita rahinar saboda haka ni da kaina na ya'nta Fatima na Kuma danka Miki amanarta halak malak harabada nabaki Fatima diyarkice" Juyowa hajiya zainab tayi ta kalli Fatima ta bude hannuwanta ta fada jikinta ta rungumeta Fatima ta fashe da kuka Mai ban tausayi, Mai martaba ya dubi Fatima wadda ke faman kuka yace "ke Fatima daga yau na mallaka Miki kanwata jinina ta Zama mahaifiyarki Niko dama a matsayin ubanki nake Kuma harabada a haka muke har karshen rayuwarmu idan Allah ya nufemu da ganin iyayenki shikenan idan bamu gansuba kina Nan a Yar amanarki kinji?ki share hawayenki inajin kaunarki cikin jinin jikina kamar khaussr da ummul khairi". Tsittt fadar tayi bakajin karar komi sai karar AC da fankar sama dake aiki a hankali..... Murmushi kawai ummu takeyi Tana jinjina Kai "nagode ranka ya dade Allah ya bani ikon rikon wanan Amana da aka bani"... "Ameen"..yarima ya amsa sanan Mai martaba ya shigayi musu nasiha Mai ratsa zukata Akan muhimmancin Amana da rikon maraya Wanda Saida jikin kowa yayi sanyi a wajen Banda hajiya babba da rahina wadanda inda zaasa takadda a zukatansu sai sun Kama da wuta.... Saida ya Gama nasiharsa sanan ya bawa kowa damar yin magana Amma kowa yace bashida abin cewa sanan yasa suka yafi juna gaba dayansu sanan akayi addua aka watse a wajen.... Ummu ce ta ruko hannun Fatima ta fito tare da ita daga fadar wajen goma na dare taron ya tashi.... ******** "Wanan makircin shiryayye ne yanzun na gano inda suka dosa Amma in Allah ya yarda bazasuyi nasara ba,idan zainab tayi nasara wanan karon to tabbas zamu hadu a Wasa na gaba"...cewar hajiya babba dake faman sunturi cikin dakin zuciyarta tamkar ta fashe Dan takaici, Kuka kawai deejahmah takeyi ta kifa kanta jikin mahaifiyarta Wanda Nan da Nan jikinta yayi zafi rau zazzabin Dole ya rufeta, Hannu hajiya rahina taka jikin deejahmah Taji yadda ya dau zafi tamkar wuta ga kuka da deejahmah keyi Wanda hakan ne ya haifar Mata da zazzabin tsabar kuka muryarta har dishewa tayi, Tunda Taji hukuncin da Mai martaba ya yanke tayi jifan bori a tsakar dakin hajiya babba tamkar Mai aljanu ta shiga rera kuka, Dago fuskarta tayi wadda tayi jajir saboda tsananin kuka ga hawaye ya wanke Mata fuska tace cikin dasasshiyar murya "mama da hajiya kuyi wani Abu Akan wanan lamarin,banaso Fatima ta shigo gidana a matsayin kishiya hakan babban ci bayane a wajena" Hajiya babba na tsaye hannayenta goye a bayanta ta sauke gwauron numfashi "ni saina haddasawa zainab da Fatima takaicin da har su mutu bazasu manta ba Domin wanan abun da zainab tayi ta farkar Dani daga gyangyadin da nakeyi da farko na farka Kuma din sainaci uban Yan iska".... "Hajiya yanzun me kike ganin zaayi"hajiya rahina tace cike da kosawa, "Akwai abinda na rigada na amso wanan ruwan wanda a lissafi gobe zatasha ta wanke fuskarta dashi,sanan akwai abinda zansa ayi, Wanda ba sai wani yayi amfani da shi ba, turen aljanu kawai zansa ayiwa shegiya ta haukace tabi bola uban kowa ma ya huta" Ruko kafar hajiya babba tayi tace"ki taimakeni hajiya Kar wanan auren ya yuwu"ta rushe da kuka durkusawa hajiya babba tayi ta zauna ta janyo deejahmah jikinta Tana lallashinta..... Ko wannensu sakawa kawai yakeyi Yana warwarewa yayinda ko wani sashe na cikin gidan Shiru kakeji kowa da gulmarsa cike da cikinsa,haka bayi da kuyangin gidan suka hade kansu suna famar gulma sai kuss kuss ke tashi cikin gidan,dik wata hayaniya da akeyi a cikin gidan biki ranan Babu ita daddare tamkar anyi mutuwa.... ******** Bayan sun shiga sashensu hajiya zainab ta umarci Fatima da taje ta dauko kayanta wadanda tace Mata tanadasu, Babu musu Fatima taje dauko kayanta dik inda ta gifta sai a bita da kallo tamkar wata sabuwar halitta,ita kanta sai takejin kanta wani iri haka ta ciccibo akwatinta tayo gidansu dashi ciki kuwa harda jakar ledar da fauziyya ta Bata ta dawo ... Wani daki Mai dauke da madubi da gado madaidaici da bayi a ciki hajiya zainab tacewa Fatima shine mallakinta Dan dadi Fatima batasan lokacin da ta rungume hajiya zainab Tana kukan farin cikiba"Allah ya bani ikon faranta Miki Rai kamar yadda kike faranta mun,Allah ya bani ikon yi Miki biyayya tamkar uwar data tsugunna ta haifeni nagode Allah ya saka Miki da mafificin alherinsa uwata"....ita kanta hajiya zainab Dan Dadi batasan lokacinda kwallar farin ciki ta taru a idanuwanta ba take kaunar yarinyar ta Kara shiga zuciyarta ta shiga bubbuga Mata baya Tana shafawa a hankali sunkai minti uku a haka kafin hajiya zainab ta zaunar da ita a gefen gado Tana murmushi tace "ke bakisan nauyi garekiba ai saiki yarda umman Taki" Murmushi Fatima tayi"Kai ummu ya zaayi in yardake bayan banida nauyi" Dariya sosai hajiya zainab keyi lokacinda Taji kwankwasa kofa ta tsagaita ta waigo ta kalli agogo Sha daya saura na dare tace "bintu tashi kije kiga wake buga Mana kofa" "Toh ummu"ta yunkura zata Mike ummu ta dakatar da ita da cewa "ko shiga kiyi wanka dare nayi ki tsaftace jikinki kicire wanan muguwar rigar idan kinfito ki duba waccen drawer akwai sababbin kayan bacci irin na Yan Mata kala kala ki duba ki dauka kisa Ina zuwa Bari inje" Ta fice daidai Ana kwankwasa kofar Tana fadin "waye wanan zai karyamun kofar gida"ta karasa ta sa key ta bude,tayi tozali da yarima tsaye Yana yatsina fuska ta watsa mishi wani kallo "me Kuma ya kawoka gidana daddaren Nan me kazoyi".. Ratsa gefenta yayi ya wuceta Saida ya shiga parlorn yake fadin "wallahi yinwa nakeji tun safe banci komiba".... "Saikace wani jariri dik bayi da kuyangin dake sashenku a rasa Wanda zai dafaa maka abinci sai kazo Nan da tsohon Daren nan?to uban wa zai dafa maka anan din badai niba ko?" Sosa keyarsa ya shigayi Yana dariya kasa kasa "Kai ummu ga Fatima a Nan?" "Au Yar aikinka ce ita?Koko ka aureta ne da zakazo kace tayi maka dahuwar abinci?" "Ummu Wai yau kadai kin canjamun saboda kinsamu Diya kin yaye yaronki?haba ummu nine fa kabiru autan ummu" "Kaidai kasani kaji da gulmarka diyata wanka take saita fito" Ta wuceshi ta shige dakinta,Jim kadan ta fito da Shirin bacci ta zo parlor ta zauna ta dauki remote ta canja Tasha sanan ta kwalawa Fatima Kira... "Bintu"....Jin sunan da ummu ta Kira yayi sauri ya kalleta Domin a iya saninsa shi kadai ke kiranta da hakan,Koda yake ba abin mamaki bane don yaji hk a bakin nata Domin kusan halayyarsu daya.... Fitowa tayi sanye da Wando da Riga na kayan bacci milk colour masu taushi da shegen kyau fuskarta fayau ko Mai Bata shafaba Amma hakan be hanata yin kyau ba, Sarai hancinta ya sanar Mata da kamshin turarensa Amma saita kauda kanta wajen da ummu take ta Dan durkusa cikin ladabi tace"gani ummu" "Wanan fitinannen ne Mai kamar Dan yaye yazo ya fitineni Wai yunwa yakeji shine nace ki dafa Masa ko indomie ne" "Akwai Miya a fridge wadda nayi shekaran jiya nasan batayi komiba Bari a dafa farar taliya".... Mikewa ummu tayi tana zabga hamma "to Bari inshiga ciki idan kin Gama Masa kisa mishi a flask ya tafi Dashi don dare yayi" "Owk".. kawai tace ta wuce ya bita da wani mayen kallo,ummu na kallonsa ta gefen ido ta girgiza Kai Tana murmushi ta shige dakinta.... Kusan minti uku da shigan Fatima kitchen ya kurawa kofar kitchen din Ido ko zata fito shiru tsulum ya Mike ya shigo kitchen din ya tokare hannunsa a kofa Tana fadin "Wai har yanzun baa Gama abicin bane?" Batace masa komiba ta cigaba da aikinta,ya karasa shigowa ciki ya tsaya daf da ita ya tsareta da idanuwa kamar zai cinyeta dik inda ta motsa sai ya kalleta,.. Gajiya yayi ya sauke ajiyar zuciya yace "malama sarautar ta motsa kenan yau baajin kulani?".. Harararsa tayi ta gefen ido batare da tace komiba ya ko Kai hannu ya rike hannunta ta kwace hannunta tace cike da tsiwa"kaje ka rike hannun matarka cikin mutane ni ka lallabo kazo zaka rikeni kayimun wayau bayan aure zakayi ka barni wayasani ma ka Gama tabani kazo baka aureniba" Da sauri yasa hannu ya toshe bakinta da hannunsa"idan nasakejin wanan kalmar a bakinki saina datse harshenki" Tasa hannu ta cire hannunsa daga bakinta ta turo baki gaba "ni kazo ka Hana mutum bacci kanasani aiki" Yar dariya yayi hade da gyara tsayuwa "Kuma Dole kiyimun ba Kuma ki bani abincin inba haka ba inje wajen wata tunda na fahimci kishi kikeyi"... Dago Kai tayi tana kallon fuskarsa tana sauraron abinda yace Wanda Nan da Nan ranta ya baci wani kishi ya turnuke ta da kyar ta janye idanuwanta daga fuskarsa Wanda yake jifanta da murmushi,ta kada Kai kawai ta kashe gas ta tsiyaye ruwan taliyar ta wanke Tass ta tsane a kwado ta ciro flask ta zuba Miya daban taliya da ban da Dan karamin flask na ruwan zafi Wanda yaji citta da kayan kamshi ta harhada Masa ta janyo basket ta sasu ciki ta ruko ta wucesa a bakin kofar kitchen ya bita da kallo ya dage kafadarsa sama ya biyota a tsakiyar parlor ta dire Masa ta dago jajayen idanuwanta ta jefesa da wani mugun kallo tace "Allah ya ta shemu lafiya"....Bata jira cewarsa ba tayi wucewarta ta shige dakinta ko kafin yayi wani yunkuri ta rufo kofar dakin garammmm Kamar wani Wawa haka yake kallon kofar dakin ya Dade tsaye sanan ya dauki basket dinsa ya fice ya rufo musu kofa.... Kwance take Tana juyi wasu hawaye masu dumi suna bin kumatunta saboda takaicin abinda yarima ya fada Mata,Aiko Dole t Rama Domin bazaici bagas ba,tun kafin ayi aure ya fara fada Mata idan Bata kula dashiba kenan yanada Mai kulawa dashi?yasan yanada ita yazo wajenta kenan?to meyasa beje deejahmar ta dafa Masa abincin yaciba yazo wajenta?....da tsaki tayi ta juya ta kifa kanta a pillow takaici ya hana bacci daukanta...."aikuwa zakasha mamakina Domin bazan yarda da hakan ba tun kafin a daura ko?"...Dole in Rama Dan ya kamata Nima kasan darajata kasan abinda zaka rinka fadamun Wanda bazai rinka batamun Rai ba....sai sambatu takeyi ita kadai bacci ya kauracewa idanuwanta sai maganganu takeyi ita kadai saboda tsabar takaicin yarima.... ******** Washe gari da safe bayan ta Gama ayyukanta ta hada musu breakfast itada ummu da sadik tayi Masa wanka ummu tayi wanka tacewa Fatima idan tayi wanka ta sameta cikin gida kasantuwar yau dinner zasuyi don gobe daurin aure ne kawai... Bayan tafiyar ummu Fatima ta fada bayi tayi wanka Mai Rai da lafiya ta fito tazo wajen kayanta ta Ciro wasu Riga da sket na atamfa jajaye da adon yellow yellow a jiki ta ajiye a gefen gado ta wawwaiga Babu kayan kwalliya dakin ta shiga dakin ummu taci Karo da body spray ta fesa sanan ta dauko powder da lip gloss ta fito ta shiga dakinta ta shirya tsaf tai kyau tamkar wata Yar baby har ta daura dankwalinta ta warware tayi parking din gashinta da dankwalinta ta nade ta shafa hodar tasa man baki ta zizara kwallin man da ta shafa a bakinta ya karawa bakinta kyau ya canja kala zuwa pink Wanda dama haka kalar bakinta yake...gyalenta ja medium size tayi rolling dashi Wanda ya tsaya iya kafadarta ta zura flat shoes jajaye ta fito tayi mugun kyau ....ta kukkule ko Ina sanan ta Miki hanyar cikin gidan... Tunda ta doso harabar cikin gidan kallo ya koma kanta wasu maaikatan gidan sun ganeta wasu Basu ganetaba haka take keta jamaa Tana tafe Tana kada makullin hannunta fuskarta a Dan daure haka ta shiga babban parlorn cikin gidan inda dik Yan matan gidan ke zaune suna breakfast ciki kuwa harda Yan matan amarya da amaryar ita kanta...kamshin turarenta da sallamarta yasa kowa juyowa ganin wacece, Deejahmah dake kishingide ta dago kanta suka hada ido da Fatima take ta kauda kanta gefe,ganin haka yasa Fatima karasowa wajensu ta zauna gefen kawar amarya tace cikin zazzakar muryarta "sannunku da hutawa Kun tashi lafiya" "Lafiya kalau"Sunita da farida suka hade baki suka amsa Mata Banda khausar da teemah dollar wadanda ke jifanta da kallon Tsana, Ko a jikin Fatima ta gyara zamanta Tana cigaba da wasa da makullin hannunta ta waiga Sukai arba da rahane,take tayi murmushin mugunta tacewa rahane "kawomin abin karyawa".. Rahane kallon inda deejahmah ke kishingide tayi wadda idanuwanta suke lumshe tamkar me bacci, Shiru rahane batace komiba Fatima ta Kara magana a karo na biyu "ki kawomin abin karyawa Nima don babu abinda naci na fito sauri nakeyi" Jiki Babu kwari rahane ta Mike Sumi Sumi ta shiga kitchen,Jim kadan sai gata da plate da cokali da cup a hannunta tazo inda flask din suke tasa mata siyayyen dankalin turawa say kwai da ketchup a gefe ta dire Mata a gabanta sanan ta hada Mata tea Mai kauri Rabin Kofi ta mikawa Fatima, Babu kunya Fatima ta amsa ta faracin dankalin a hankali Tana kurbar ruwan tae din Wanda tayi hakan ne Dan kawai ta muzanta rahane ... Ajiyewa tayi a gefenta ta kalli wadanda ke wajen kowa ita yake kallo sanan ta Mike tsaye ta Tana duban rahane da dik abin duniya ya isheta tace "ki kwashe kayan ya isheni haka idan kuma zakici to Bismillah Bari Inga ummu" "Aikin banza Kare da gudun layya,Wai samin yancin bawa yasa kwana daya kacal yake neman yiwa mutane iskanci bayan ba gidan ubansa bane"khausar tace cike da masifa da takaicin Fatima kamar ta shaketa... Bude idanuwa deejahmah tayi "bedace ace idan dabba yanayin Abu ki rinka kulasaba little Domin akwai banbanci tsakanin cikakken mutum da dabba,sanan akwai banbanci tsakanin bawa da Mai yanci,sanan akwai banbanci a tsakanin Dan asali da shege Kinga bedace ki tsaya kina maidawa shegiya martaniba" Har Fatima ta juya batace komiba ta juyo ya dawo ta Dan durkusa daidai kusa da deejahmah da khausar wadanda ke zaune waje daya tace"cikar Zama mutum ne yasa ya aikata dabbancin daya jefashi a cikin danasani Wanda awanni kadan da faruwar hakan yasa wanan cikakkem mutum din ramewa da fada babban tashin hankali,sanan Kuma shi Wanda ake Kira dabban shine akejin shakkar yin kishi dashi Domin a wajen mijinsa cikakken mutum ne kamar kowa,Ina Mai shawartarki da ya kamata ki zauna kiyi nazarin abinda wanan dabban yakeyi ake kaunarsa fiye da cikakken mutum yantacce Dan asali....idan har kin iya dabbancin to tabbas Zaki samu soyuwa a zuciyar mutum daya tamkar da dubu"Tana Gama fadin haka ta Mike tsaye tana faraa Wanda har hakoranta Saida suka bayyana, Cikin azama khausar ta Mike ta daga hannu zata wanke Fatima da Mari da sauri Fatima ta rike hannun khausar tace "kullll da taba kyakkyawar fuskar sarauniyar masarautar barayar Zaki?wanan fuskar tafi karfin Mari a wajenki Domin fuskar matar yayanki ce"ta yarfe hannun khausar kaasa ta juya tai tafiyarta ko waiwaye Babu.... Rike kugu khausar tayi Tana sauke numfashi cike da takaici "yau kadai yarinyar Nan ta canja salo?tabdijan zataci ubanta kuwa Domin wallahi tallahi saita Raina kanta"... Tsabar takaici ya hana deejahmah motsin kirki sai jinjina Kai kawai takeyi maganganun Fatima sunayi Mata yawo a tsakiyar Kai.... Bayan yarima yayi wanka ya shirya ya shigo cikin gida Domin gaida iyayensa,babu kunya ya wuce sashen hajiya babba da sallamarsa Tana zaune suna tattaunawa da mutanen dakinta ya shigo da sallamarsa,a ciki suka amsa Masa Koda ya gaishesu dakyar rahina ta amsa ita kuwa hajiya babba ko kallonsa batayiba ya mike har zai fita ya juyo muryar hajiya rahina Tana fadin "ya kamata kasa a kawowa Deejahmah magani Domin batada isasshiyar lafiya" Da sauri ya juyo ya durkusa Yana fadin "meyasameta?".. "Inaga gajiya ce kasai tasa Mata zazzabi da ciwon Kai jiya daddare" "Owk Bari indubata sai inkira waya akawo Mata magani"..harara ta bishi tashi batare da tace komiba ta saki kwafa ya fice.... ******** Suna zaune a parlor ya fito Yana tafe Yana takama har ya karaso inda suke zaune har zai wuce ya tunada cewar deejahmah batada lafiya ya dawo ta wajensu ta nemi gefe ya tsaya dukkansu suka shiga gaishesa daya bayan daya tanaji Taki bude ido, Kallonta yakeyi kawai yadda idanuwanta ke rufe sanan fuskarta kanta ta Dan fada jiya zuwa yau kadai wannan kadai ya shaida Masa da batada lafiya kamar yadda uwartata ta fada Masa, Ganin Taki bude ido yasashi Dan tsaki kadan yace "deejah ya jikin naki"....Saida yayi magana sanan ta bude jajayen idanuwanta ta sauke akansa Tana yatsina fuska da kyar ta bude baki tace"naji sauki".. "Allah ya Kara lafiya".... "Ameeen"tace a takaice.... Har ya juya zai tafi ya juyo ya dubeta kadan yace "zaa kawo Miki magani anjima kadan ki tabbatar da kinsha"...yayi wucewarsa... Sashen mahaifiyarsa ya nufa a can ne ya tararda gwaggwaninsa da ummu da Fatima dake gefenta Tana ganinsa ta kauda kanta gefe shima bai lura da itaba ya durkusa har kasa ya shiga gaida iyayen nasa wadanda ke amsa Masa cike da kulawa... Ummu ce tace "kabiru waye zakasa yakaimun diyata Fatima wajen telar ya gwadata dinkin lace na wajen dinnar Dan inaso itama ta shiga anko kamar kowa" "Sai in kaita ai wajen telan inace wajen inda nake Kai su afee ne ake musu dinki" "Ehh Nan ne" "Owk toh ta shirya sai muje "... Kallon Fatima ummu tayi tace Mata "ya kamata kije gida ki shirya kizo ya kaiki ko" Jimm kadan Fatima tayi sanan tace cikin sanyi murya "ummu ni banjin Dadi dama anyimun girma daya Dana afnan idan yaso sket din sai a Kara innci hudu Kinga ba sai munsha wahalar zuwaba ki kirashi kinji" Tunda ta Soma magana yaji wani Abu nayi Masa yawo a sassan jikinsa,cikin dabara ya dago idanuwansa ya sauke akanta.....Aiko idanuwansu suka hade waje dayata wurga Masa harara ta kauda kanta gefe,shi kuwa gogan mutuwar tsugunne yayi Dan tunda yake da Fatima bai taba ganinta da Koda Hoda ba ballantana kwalli da man baki kwalliyar ta amshi fuskarsa,take ya nemi dik wata natsuwa ta jikinsa ya rasa kokari yakeyi ya dago idanuwansa ya Dora Akan nata Amma Koda ya dago batashi takeyi ba juyar da kanta tayi Tana Wasa da sadik dake gefenta.... Dakyar ta yunkura ya Mike yaja kafarsa ya fice a dakin ya nufi sashinsa.... Koda ya shiga dakinsa ya nemi natsuwarsa gabaki daya ya rasa Fatima keyi Masa yawo a kwayar idanuwansa lokaci daya ya nemi natsuwarsa ya rasa babu abinda yake bukata kamar yayi tozali da ita a idanuwansa.... ******** "Ummu Bari inje gida inyi sallah in sake wanka in Dora Mana abinci ko?".. Jinjina Mata Kai ummu tayi tana murmushi,Fatima ta Mike tayiwa jamaar dakin sallama tayi ficewarta A hanyar fita suka hade da fauziyya da afnan sundawo daga cikin gari,dukkansu Saida sukai shock ganin Fatima a haka take hassadar fauziyya ta bayyana karara a fuskarta ta kasa boyewa tace"iyyeee k'awata an fita a kangin bauta gaskiya nayi Miki murna" Ruko hannunta Fatima tayi Tana murmushi "nagode k'awata"....itadai afnan wadda ta gaji murmushi kawai taiwa Fatima ta wuce yayinda fauziyya ta cigaba da jifan Fatima da wani irin kallo Wanda yasa Fatima yin mamakin hakan Amma sai batace komiba.... "Ashe haka kike da kyau?gaskiya kin hadu gashi kinsha kwalliyarki,Allah yasadai kinsa turare Dan cikon kwalliya Saida turare" "Laaa Kinga dazun inata neman turare na mance da Wanda kika bani gara da kika tunamin kuwa Dan anjima idan anyi Shirin dinner shi zan shafa" Takaicine ya lullube fauziyya najin har lokacin Fatima Bata shafa turaren ba saita danne tace "gaskiya ya kamata"... "Bari inje gida inyi sallah inyi wanka,ke inayin wankan ma shi zan shafa turaren aminiya".. "Yauwa gaskiya ki rinkasa turare kafin mamanki ta siya Miki"...fauziyya ta shige gida ta dagawa Fatima hannu... Fatima tayi nisa bilkisu ta biyota Tana kwala Mata Kira cakkk ta tsaya har bilkisu ta karaso "wallahi tun dazun ke nake nema Ina kika shiga ne?".. Dariya bilkisu ta kyalkyale dashi sanan tace "Ina makale Ina kallon dramarku a parlor gaskiya kinyimun daidai kinyi yadda nakeso Ashe kinsan Kan zance kika tsaya da anacin ubanku?" "Malama sun Gama cin ubana watan cin nasu ne ya tsaya Dan dik saina Rama abinda sukamun".. "Yayi daidai ta wajena haka nakesonki"... "Wai meye tsakaninkine da wadancan Yan biyun?Naga daya daga cikinsu Tana shige Miki nifa tsoron mutanen Nan nakeyi " Dafa kafadar bilkisu tayi tana jinjina Kai "karki damu wadanan basuda matsala sunada kirki babu abinda zai faru kinji?Bari inje inyi wanka sharp sharp" Ta kada Mata Kai kawai ta juya cikin gida itama ta wuce, Tana shiga dakinta t shiga cire kayan jikinta ta taciro wadanda zata canja kafin lokacin dinner ta Ciro turarenta ta Dora Kan kayanta ta fada toilet dinta don yin wanka.... Muje zuwa *SLIMZY 😍*🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* 36 Ta dauki kimanin minti goma cikin bayi Tana wanka sanan ta dauro alwala ta bude bayin ta fito Tana goge fuskarta Bata lura da ummu dake zaune gefen gado ba Saida ta juyo da nufin zuwa bakin gado ta dauki kayanta Sukai Ido hudu da ummu hannunta rike da turaren Tana jujjuyawa....ja da baya Fatima tayi hade da dafa kirji "ummu yaushe kika shigo?wallahi banji shigowarki ba" "In Banda abinki Fatima keda kike wanka ya zaayi kiji shigowata?bayan tahowarki sadik yasamun rigima shi indomie zaici to bansamu me kawoshiba shine nazo kawoshi nadade Ina sallama waje naji Shiru shine Dana turo kofar naji a bude,sai Kuma naji karar ruwa a bayi nasan wanka kikeyi".... Wucewa Fatima tayi wajen dressing mirrow ta dauki Mai Tana Shirin sharawa ummu ta watso Mata tambaya"Fatima me kikeyi da turaren Yan bori?turare Dan d'uri?" Da sauri Fatima ta juyo Tana kallon turaren hannun ummu,sai ta danyi murmushi tace "wayyoo ummu turarena ne na ajiyene idan na fito wanka Nasa Kaya in shafa" Takaicine ya lullube ummu tafara masifa Tana fadin "baki da hankali Amma,da ranki da lafiyarki Zaki shafa wanan turaren?Wanda idan kika shiga cikin jamaa na tabbatar da tushe hanci zaa rinkayi so kike ki janyowa kanki raini ma kenan cikin manyan mutane da ya'yan attajirai,to ki rufamin asiri ki rufawa kanki kar in kuskura inji kina kamshin wanan turaren Domin ni Zaki zubarwa da mutunci,ai kin wuce wanan lokacin Kuma Fatima,yanzun ke Yar gatace Yar ummu da abbah ko"...ta karashe maganar da sanyin murya yadda taga jikin Fatima na rawa, Gyada Mata Kai Fatima tayi baki na rawa tace "insha Allah bazan shafaba ummu dama banida turarene" Murmushi ummu ta sauke "nasani ai naji dazun kamshin turarena kikeyi koh?meyasa yanzun baki daukoshi kin Kara shafawa ba ai na mamanki ne koh" Ta sunkuyar da kanta kasa "toh ummu" "Kokefa yanzun gobe da wuri zansa akaiki kiyi siyayya hardasu turarruka da gyaluluwa da takalma da jakunkuna ko Yar ummu " Dadi ne ya Kama Fatima Wanda har saida murmushi ya subuce Mata sanan ta rufe fuskarta Tana dariya,itama ummun dariya ta shigayi Tana fadin "ja'irar yarinya Zaki sa magauta suyi Mana kallon banza" Itadai Fatima murmushi kawai take ta cigaba da shafa manta sannan ta dauki kayanta ta sanya, ta shimfida daddumarta ta tada sallahrta,bayan ta idar ne ta nade daddumar ta nufi kitchen sadik ya rufa Mata baya yayinda ummu ta Dan kishingida bacci ya dauketa.... ******** Sashen hajiya karama ya sake shiga Yana dube dube ko zai ganta Amma be ganta ba ya dade ciki a zaune har kanwar hajiya ta gaji ta tambayeshi wa yake nema?ko Yana bukatar wani abune Shafa keyarsa yayi sanan yace "dama ummu nake nema kuma bangantaba"....Nan ne ake sanar Masa da ta tafi gida, Yana fitowa sauri sauri ya nufi sashen ummu yayinda rahane ta ruga aguje ta sanarwa da deejahmah taga yarima yayi sashen hajiya zainab da alama wajen Fatima zaije....hankalinta ba karamin tashi yayi ba tunanin yadda zaayi taje taga me sukeyi takeyi..... Shikuwa yarima ya Dade tsaye Yana bugun kofa sanan sadik yazo ya bude Masa ya dauki sadik ya dagasa sama Yana fadin "oga sadik Kaine da bude kofa?rigima babu ko?"...ya karasa shigowa dakin Yana kalle kalle sanan ya dubi sadik yace "Ina ummu ne?" "Tana dakin anty Fatima Tana bacci"... "Owk Ina antyn naka?" "Kitchen ta shiga Tana dafamin abinci".... Jimm kadan yarima yayi sanan ya radawa sadik daidai kunnensa "jeka ce Ina kiranta"... Da gudu sadik ya shiga kitchen din Yana fadin "anty kizo inji uncle yarima"....gabanta ne ya yanke ya fadi,Jin abinda sadik yace,da kyar ta daure ta dubi yaron tace"tsaya ka tafi da abincinka idan kaje kace Ina zuwa"...ta karasa barewa sadik kwai tasa Masa a gefenn indomie dinsa ya fice parlorn, Saida ta Gama dauraye tukunyar da tayi amfani sanan ta fito fuskarta daure ta karaso gefen kujerar da yake zaune tadan zaune jikin kujerar,....shi kuwa yarima tunda ta zauna gefensa ya nemi natsuwarsa ya rasa,kasa jurewa yayi ganin batace masa komiba tsawon minti uku yadanyi gyaran murya yace "ranki ya dade dik fushin ne?menayi Miki kikeson yimun horo?" Dage kafadarta tayi tai Farr da idanuwanta sanan ta Dan dubesa ta kauda Kai ta turo baki gaba tace "oho Nima bansaniba" Murmushi yayi "sarautar Taki ta motsa kenan?shiyasa kike wani ciccin magani kina shamun kamshi" "Wayasani"shine amsar data bashi, Hannunta ya janyo ta fuzge hade da cewa "kaje wajen wadda kace kanada ita Mana?ai tanada hannu sai ka taba"ta murguda Masa baki Mikewa tsaye yayi ya damki hannunta da kyau ta saki Yar Kara Tana kici kicin kwacewa cikin Jin zafin rukon da yayi Mata tace 'ni ka sakeni?da zafi Allah hannuna zai karye'...kwalla ta ciko a idanuwanta yasa hannunsa daya ya dago habar ta Yana karewa fuskarta kallo sai ga hawaye sharrr sharrr Yana gangarowa a idanuwanta....sassauta rukon yayi ya matso da fuskarsa daff da Tata "kishi bintu?kishi be kamaceki ba Domin ke ya kamata ayi kishinki ba wata ba haba fatyna"...hawaye kawai ke zuba a idanuwanta Wanda batasan dalilinsuba, Hannu yasa Yana sharewa wasu na zubowa a idanuwanta ya matseta a jikin bango hade da shafa kanta Yana fadin "is ok banason kukan kinji?nayi laifi bazan sake cewa zanje wajen wata ba insha allahu" Dago idanuwanta tayi ta sauke Akan fuskarsa da sauri ya shiga girgiza Kai "ya Isa banason kukan kinji?" Kara shagwabe Masa tayi ta Dora kanta a kirjinsa cikin sigar shagwaba take fadin "Nima bansan dalilin da yasa naji wanan yanayin ba,kawai dai nasa tun daga ranan da kacemun kanada wata zuciyata tafara waswasin watarana zaka iya juyamin baya,Dan kawai nayi maka wasa sai kacemun kanada wata ni banaso kabari"...hannunsa yasa Yana shafa gefen fuskarta cikin sigar lallashi "ya Isa nadaina ai Nima wasa nayi Miki koh?"..... Turo kofar yasashi saurin juyawa kawai yayi Ido hudu da tawagar kawayenta deejahmah ciki kuwa hadda ita ko wacce da Jakar kayanta a hannunta, Shigowa parlorn sukayi da sallamarsu a bakunansu da sauri Fatima tasa hannu ta goggoge kwallar dake makale a idonta ta shiga faraar Dole "barkanku da zuwa,kune da laasar din Nan" Kallo kawai suke binsu dashi Dan ko wacce fuskarta dauke da mamaki,...dakyar Sunita taja numfashi cikin inda inda tace"ehh mune wallahi baki sunyi yawa can shine mukace Bari muzo Nan dik muyi wanka mu shirya a Nan idan lokacin dinner yayi ko?" Murmushi Fatima ta sauke tadan bugi yarima dake tsaye kamar statue "yaayah kaje zan kawo maka abincin,me kakeson ci ne?"ta kifta Masa Ido, "Nima naji shaawaer indomie din sadik Amma ni ki soyamun kwai" "Angama ranka ya dade,ango kasha kamshi"...hannunsa yasa yaja hancinta "sai kinsha duka" Ta Dan turo baki gaba ta juya yabi bayanta da kallo,sanan ya fakaici kallon side din deejahmah yaga ta kauda kanta tamkar batasan Yana Nan ba.... Juyawa tayi daki ta tashi ummu ganin lokacin laasar yayi Dan tayi sallah,bayan ummu ta tashi ne Fatima ke sanar Mata da tanada baki.... A parlor tagansu zazzaune Tasha mamaki Dan Bata taba tunanin deejahmah zata tako kafarta gidanta ba kila dai akwai wani dalili,.. Dan fad'ada faraarta ummu tayi tace "ah ah lallai gidana yayi albarka Yan matan amarya ne da amaryar kanta?to sannunku da hutawa" Suka hade baki suka gaidata ummu ta amsa cike da kulawa ta shige dakinta.... Tunda suka shigo Fatima ke kaiwa da komowa a kitchen Tana hidimar abinci, Fitowarta daga kitchen yayi daidai da Jan tsaki da deejahmah tayi tana fadin "ayi dai mugani idan tusa zata Hura wuta,ai mun rigada munsan komi munsan cewa karuwa ce".... Cakkk Fatima ta tsaya zuciyarta nayi Mata zafi Amma saita danne ta danyi yake hade da juyowa Tana fadin "ai karuwanci ma sai a gidan yaayah wayyoo masoyi"....tace Tana murmushi ta shige, Babu Wanda ya fahimci abinda Fatima ke nufi sai khausar da deejahmah wadanda sunsan komi su Yan matan amarya da ka kawai suke zaune, Shigowa faizah tayi baki dauke da sallama itada Yar uwarta hannunsu rike da jaka cikin faraa faizah tace"munje can akace Kuna Nan Ashe Nan kukayo Ina ummun?" Khausar ce tayiwa faizah nuni da Tana daki ta dire Jakarta ta shige dakin da sallamarta suka gaisa da ummu,bayan ta fito ne sukai Ido hudu da Fatima ta fito kitchen take suka sakarwa juna murmushi, Kallon mamakin ganin Fatima cikin wanan yanayin faizah takeyi Dan rabonta da ita tun ranan da suka gaisa da yarima, Karasawa tayi ta mikawa Fatima hannu suka gaisa suka shige kitchen din tare,kasa boye farin cikinta faizah tayi tace"kaiii k'awata haka kika koma?nayi matukar farin cikin samun yancinki Allah ubangiji ya Kara Haske a lamarinki" Farr da Ido Fatima tayi tace "bayan tun bayan rabuwarmu ranan biki bansake jinki ba" Murmushi faizah tayi Dan tasan ba itabace fauziyya ce kila fatimar Bata ganesuba ta bude baki da niyyar cewa ai ba ita bace aka kwalawa Fatima Kira ummu ce daga daki, Da sauri Fatima taje"yarima yace ki Kai mishi abinda yasaki"... Bata fuska tayi tace"ummu wlhy Yaya takuramun zaiyi nagama nasa a bascket Wai da bakin Nan nake nemawa abinda zasuci" "Kin iya wahala bintu keda zaakawo musu daga cikin gida kin Kama kin dora girki?,yanzun ba wanan ba waye zai kaiwa yarima abincin kike nufi" Jimm kadan tayi sanan tace"akwai Rahane" "Owk" Ta juya ta fita ta shiga kitchen da sauri Jim kadan ta shigo parlorn tsaye tayi Tana karewa kowa kallo sanan ta nuna Rahane da Mami tace cikin Isa "cikinku waye zai kaiwa ranka ya dade abinci?Domin ni naso in ciyar shi saidai hakan be samuba Dan inaso in karrama baki"... Dibbb parlorn yayi tamkar Babu kowa, Ta Kara nunasu da yatsa "ba saina maimaita kalamaina ba kunji abinda nace" Dan durkusawa Mami tayi tana jinjina Kai "munji ranki ya dade" "Shawara ya rage gareku nida bukatata a cika umarnina"...ta dire basket din a wajen, Ta juya abinta suka bita da kallon mamaki da al'ajabi,juyowa Fatima tayi tana jifansu da mugun kallo "inhar bakuje Kun cika umarnina ba to aikinku ya Kare" Da sauri Mami ta sunkuci basket har tana tuntube Rahane tabi bayanta a sukwane, "Dakata,ke haka zakije hannu Babu komi?tsaya inbaki ruwan zafinsa dan nasan Yana bukatarsa"....ta juya cike da yanga duka Ido yayi kanta har kitchen din haka ta dawo ta mikawa Rahane flask Tana binta da kallon raini da wulakanci, Babu wani musu ta amsa ta juya Tana kallon uwargijiyata,Tana Jin tsoron abinda zai biyo baya.... Jinjina Kai kawai fauziyya takeyi a ranta Tana fadin "zakici ubanki lallai kinsamu waje,a zahiri kuwa ajiyar zuciya ta sauke kawai.... Wayar khausar ce tayi Kara da sauri ta dauka ta Kara a kunnenta "ki tabbatar deejahmah ta shafa abinda na Bata a jikinta da tafin hannunta ki fada Mata sakona"hajiya rahina ke magana ta can bangaren, Kada Kai khausar keyi kamar Tana ganinta hade da cewa "toh in Sha Allah"ta kashe wayar Kasa tai da murya daidai kunnen deejahmah ta kitsa Mata sakon da aka Bata,tsabar takaici ya hanata amsawa da baki Kai kawai ta dagawa khausar din.... ******* Saida akayi magriba sanan ake haramar tafiya wajen dinner inda Mai kwalliya yauma tazo ta tsantsarawa amarya kwalliya a fuskarta tayi balain kyau tamkar ba itaba kamar wata sarauniyar kyau,haka Yan matan amarya ma ko wacce aka bita da kwalliya tayi musu casual ciki kuwa harda Fatima wadda tunda akafara daga girarta fuskarta tafara canja kala ko kafin agama Mata kyawun da tayi baya misaltuwa su kansu Yan matan amaryan Babu wadda Bata Yaba da kyawu irin na Fatima ba musamman da aka canja Mata halitta da kwalliya.... Ankonta dama afnan ta hada ta amso musu tare,tasa doguwar rigar fited gown na less seagreen Wanda shine ankon wajen dinner din tayi masifar kyau ya amshi fatar jikinta, Ita kanta deejahmah Saida ta daga Ido ta kalli Fatima data gifta ta gabanta hassada da bakin ciki hade da kishi suka tarun Mata a zuciya Wanda Taji tamkar ta shake Fatima ta huta, Deejahmah Bata manta da sakon mahaifiyarta ba tayi yadda akace,sai wani kamshi takeyi na musamman Domin Babu karya Tasha gyara..... Faizah kuwa dik inda Fatima tayi suna tare sai hotuna sukeyi a wayar faizar saboda yadda Fatima tayi Mata kyau, Yan matan amarya aka fara kwashewa zuwa wajen dinner inda abokanan ango gigaggun Yan boko kowa yazo da motarsa ta wanan Tana wane wanan,....tunda Fatima ta fito hannunta cikin na faizah su deejahmah na biye a bayansu da kawarta kwaya daya wadda ta rukota suka fito tare,kallo ya koma Kan Fatima dik wani Wanda yayi tozali da Fatima sai yace Masha Allah, Sai kuss kuss abokanan ango keyi yayinda yarima ya kafeta da idanuwa yaji kishi na taso Masa ganin idon kowa a wajen na kanta,...dakyar ya hadiyi mugun miyau ya radawa Ahmad a kunne "ga bintu can ta fito ka tabbatar Kai ka dauketa sanan karka Bari kowa ya rabeta....dik Wanda ka gani kusa da ita kafada Masa matar aurece"....dariya Ahmad ya hauyi Yana fadin "Kai abokina ga amaryarka Amma ta Fatima kakeyi?kasan Allah banganetaba gara da ka fadamun Dan Nima ita nake kallo" Wani mugun takaicine ya Kara lullube yarima ya bugi kafadar Ahmad.... Koda suka karaso Ahmad ya tarbesu ya nuna musu motarsa yace su shiga Nan ba musu Fatima ta shige fuskarta dauke da faraa... Motar wani abokinsu Nan aka tanadarwa amarya da ango suka shiga suka zauna....take kamshin turaren deejahmah ya daki hancin yarima.....yaji wani Abu nayi Masa yawo a cikin jikinsa,Wanda ya haifar Masa da tsantsar shaawarta cikin seconds wadanda basu wuce talatin ba.....hakan ne yasashi juyowa yadan kalleta,ya kauda kansa,din Tana lura dashi...Kara gyara hancinsa yayi ya Kara shakar kamshin turaren Wanda take network din jikinsa ya fara canjawa idanuwansa suka kankance....ya shiga Dan mutsu mutsu da jikinsa a haka suke tafe a motar Amma samm hankalinsa baya jikinsa wata matsananciyar shaaawace take fuzgarsa.... Ko kafin su karasa hall din idanuwansa sun Gama kankancewa haka suka Isa wajen,Wanda suka fito tare ya riko hannunta Dan shiga hall din,dakyar yake taka kafarsa savida yanayin da take ciki,ganin ya ruko hannunta yasa deejahmah yin Dan murmushi a haka suka shiga jamaa sukai caaa suna kashe musu hoto ta ko Ina,abokanan ango suka shiga barin naira na liki har wajen zamansu.... Fatima na zaune gefen faizah Taki an dafa kafadarta ta baya da sauri ta juya wacce ta gani ce yasata saurin mikewa ta rungumeta Tana fadin "ablahhhhh wayyoo Dadi kece" Bakin barrister hauwa yaki rufuwa Tasha leshinta me shegen tsada cikin tsananin farin ciki tace "Fatima kece haka?lallai nayi farin gani alhamdulillah"... Dakyar Fatima ta saketa ta juya ga Ashmah dake tsaye tana murmushi "Aysha Ashe zamu sake haduwa?"..suka rungume juna cike da farin ciki suka zauna table daya da Ablah wadda mamakin ganin Fatima a wanan yanayin ya cikata.... Yarima Yana high table Amma hankalinsa na wajen fatimarsa dikda mawuyacin halin daya tsinci kansa be hanasa kafeta da wani irin kallo ba Yana kallon yadda take faraa da jamaa zuciyarsa nayi Masa tsananin lugude.... Dinner sosai ake gudanarwa inda aka umarci amarya da ango da su sauko Dan nuna farin cikinsu deejahmah na gaba Yana biye da ita idanuwansa suka sauka akanta abinda yakeji ya sake karuwa a jikinsa fiye da dazun,Koda yazo daidai ita besan lokacinda ya rike kugunta ba suna rawa a haka a hankali Mai ban shaawa nanfa jamaa sukai caaa wajenyi musu liki,idanuwan Fatima kyarrr akan hannun yarima dake sagale da deejahmah....dakyar ta sauke numfashi ta Mike cike da yanga ta karasa daf dasu ta bude Yar pos dinta da ummu ta Bata da canjin Yan hamsin hamsin ciki, ta shiga yi musu liki, hajiya babba na gefe tanayi musu, batare da ta lura da Fatima dake gefenta ba,....kallonsa takeyi Ido cikin ido shima idonsa Yana kanta ya sakar Mata da lallausan murmushi,kasa mayar Masa tayi saboda abinda takeji cikin kirjinta.....daga inda yake Yana iya hango Yar kwallar data taru cikin idanuwanta...a haka takeyi musu liki Tana kallonsa Yana kallonta,ganin haka yasa deejahmah babu kunya ta kwantar da kanta gefen kafadarsa.... Saida kudinta ya Kare ,ta juya Tana taku daidai cike da yanga da izzah Wanda Saida ta dauke hankalin daukakin jamaar dake fuskantar wajen,....maimakon ta koma table dinta sai tayi hanyar fita hall din,a idon yarima,Wanda tunda ta juya yabita da kallo zuciyarsa tayi Masa nauyin gaske, gabansa ya shiga tsananin faduwa hade da firgici lokaci daya ya furta a zuciyarsa....."Ina Fatima zataje?"abinda ya tambayi kansa kenan..ya kasayin wani yunkuri sai dai gabaki daya ya rasa yanayin da ya tsinci kansa...Dan ba karamin furgici ya shigaba, Hankalinsa baya jikinsa deejahmah na lura da yanayinsa Amma sai ta share,... Ganin Fatima tayi wajen hall din yasa Ahmad dake gefensu Yana kallon dik abinda ya faru,yayi saurin juyawa ga abokinsa ya Mika Masa drink din dake hannunsa yabi bayanta.... Murmushin mugunta deejahmah tayi a fakaice hade da lumshe idanuwa ta budesu....wani farin ciki ke ratsata Domin tunawa da tayi da plan dinsu na gaba..... *Muje zuwa* *SLIMZY😍*🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* _Ku shaida na sadaukarwa_ *SUNITA* _wanan shafin _kyauta saboda tsananin kaunarta ga wanan littafi inayi Miki son so bae😍_ 37 Hanyar fita gate Ahmad yaga tayi da azama ya daga muryarsa yace "Fatima"....cakkkk ta tsaya hawaye na gudu a fuskarta wadanda ita kanta batasan dalilinsu ba a haka Ahmad ya taddata tsaye ko motsin kirki batayi sai hawaye dake gudu a fuskarta, "Meya faru kika fito Nan Ina zakije?Kuma?sokikeyi wani Abu ya sameki?"....dakyar ya karasa zancensa da yayi tozali da fuskarta wadda ta jike da hawayen bakin ciki, Shiru yayi hade da zura hannunsa cikin aljihun wandonsa batare da yace kokiba, Hajiya zainab ce ta fito daga hall din kunnenta manne da wayarta da alama waya takeyi Tana fadin "idan Kun shigo kuyo hannun damanku zakuga hall din akwai motoci wajen Ina kofar gate"...kamar a mafarki take ganin fatyma tsaye da wani tun daga Dan nesa dasu ta Gane itan ce harta karaso wajen Tana Taku daidai takalminta Yana Kara kwass kwass Wanda shine ya dauki hankalin Fatima ta juya da sauri Dan ganin waye,Aiko idanta ya hadu Dana ummu a guje ta fada jikinta ta fashe da kuka Tana fadin "muje ummu ni banason zaman wajen Nan tafiya zanyi"cikin kuka take maganar harda shassheka,...ba karamin tashin hankali ummu ta shiga saboda irin kukan da taga fatyma Tana rusawa ta Kara rungumeta Tana fadin "me akayi Miki wanene?fadamun ko waye shi sai na tabbatar ya zubar da hawaye kamar yadda kika zubar"....kuka kawai takeyi Tana Kara kankame hajiya zainab,.. Juyowa ummu tayi tanayiwa Ahmad kallon tambaya,da kyar ya sauke numfashi yace "ummu wallahi bansan meya faru ba kawai dai Naga Fatima ta fito hall a yanayin yadda ta fito nasan akwai wani Abu shine kika biyomu Kuma ni Bata ma yimun magana ba" Ajiyar zuciya ummu ta sauke daidai Nan babbar kawarta ta shigo da motarta,wajen da sauri ummu taja Fatima a hankali har sunfara tafiya ta juyo ta kalli Ahmad "jeka kawai Bari muje gida"... Wajen motar kawar Tata suka karasa daidai Nan ta sauke glass din motar Tasha kwalliya itada yaranta Yan Mata guda biyu cikin faraa tace "ranki ya dade muje ciki koh".. "Ah ah muje gida kawai ku saukeni yata Babu lafiya".... Dan leko da kanta tayi Tana kallon Fatima wadda ke faman shasshekar kuka kafin daga bisani ta budewa ummu kofar mota suka shige taja motar zuwa gida..... ********* Akan idon yarima Ahmad ya shigo cikin hall din shi kadai ba tare da Fatima ba wani irin kugi cikin yarima yayi lokaci daya fargaba da tsoro ya darsu cikin zuciyarsa.... Wasu irin yayan zufa ne Suka shiga karyo Masa ta ko Ina dikda sanyin ac dake cikin hall din saboda tsabar haduwarsa ta cikin dummm light din inda suke zaune kallo daya zakayiwa yarima kasan Yana cikin rudani,minti minti yake share zufar dake tsattsafowa a fuskarsa, Dan kallonsa deejahmah tayi hade da Dan darkewa a jikinsa Tana kallonsa cike da kissa tace"lafiya dai ranka ya dade?meke faruwa?Naga yanayinka tamkar kana cikin damuwa menene fadamin"...yadda tayi maganar kadai yasa jikinsa mutuwa take ya Kara nutsa cikin tsantsar shaawarta har baisan lokacinda yasa hannu yadan shafi gefen fuskarta ba take waje yadau sowa hasken camera kawai ke giftawa a wajen, Bakin hajiya rahina yaki rufuwa saboda Dadi Dan waigawa tayi gefen hajiya babba ta rada mata a kunne"turaren baba Sudan yayi aiki dan banza Kinga yadda yake lumshe Ido?" Girgiza Kai kawai hajiya babba tayi ta sauke murmushi cike da kasa tace"fada da aljani Babu Dadi rahina munyi da manyanshi balleshi karamin alhaki?hmmm hmm kadan kenan sai ya kusanceta yaji yadda take sanan idan har Tasha ruwan dadin Nan na baba Sudan angama sanan sauran hade haden a can zaiyi a binsa to daganan labari zai canja Domin shida wata mace harabada Kuma balle tsintacciyar mage shigiya Yar gaba da Fatima" Wani irin dariya hajiya rahina takeyi Tana jinjina Kai cike da nishadi "Kinga idan ta mallakeshi shikenan sai muga ta tsiya,sanan burina be wuce ta haifawa sarki magaji ba kafin ta sheka Dan banza lahira" Jinjina Kai hajiya babba tayi ta Kara kasa da kanta kadan "yadda Dana ya bakunci lahira wallahi sai kabiru ya bakunci lahira,....kisa Mai sauki deejahmah zatayi mishi Wanda harabada Babu Wanda zaisan cewa itace ta kasheshi" Dan murmushi kawai hajiya rahina tayi tana jinjina Kai Tana ayyana abubuwa da dama cikin ranta".... Dik wata natsuwa yarima baya cikinta ya rasa abinda keyi mishi Dadi Allah Allah kawai yakeyi a tashi a wajen party din .... ******** Kuka sosai Fatima keyi Tana mayarwa hajiya zainab abinda ke faruwa ta karashe maganar da fadin"na hakura da aurensa inhar hKan shi zai samamin farin ciki Domin a bisa alamu sun nuna Yana aurenta zai manta da alkawarina ,zai manta da wata Fatima marainiya wadda yayiwa alkawarin kasancewa da ita har karshen rayuwarta,gara in hakura ummu tunda ni banida sauran gata"ta karashe maganar hawaye na gudu a fuskarta "Babu ranan da zan huta kenan?tunda nataso nake cikin wahala har yanzun Ina cikin azaba daga wanan sai wanan shi kuma Wanda nakeso ya fara canjamun"ta rushe da kuka Mai ban tausayi... Ita kanta hajiya zainab Saida kwalla ta tarun Mata a idanuwa,Fatima na tsananin Bata tausayi,kalamanta suna caja Mata kwakwalwa Saidai dik ba wani Abu ya kawo hakan ba harda kishi data fahimci Yar tanadashi... Janyo Fatima tayi jikinta ta rungumeta ta shiga share Mata hawaye "kiyi Shiru ki kwantar da hankalinki kinji?Allah gatanki nice gatanki ko kabiru zai juya Miki baya ni bazan juya Miki ba kinji yarinyana?" Dago Kai tayi idanuwanta na zubda hawaye hajiya zainab tasa hannu ta share Mata hawaye zuciyarta tayi rauni gabaki daya dakyar ta bude baki tace "kiyi Shiru kidaina kuka Babu Wanda ya Isa ya rabaki da Kabir yadda Allah ya hadaku,idan sunsan wata basusan wata ba kinji ni zanyi musu abinda zan shayar dasu mamaki zan tabbatar musu da din sammakonsu wani a hanya ya kwana ki kwantar da hankalinki zan kwatar Miki yancinki sanan kema zanbaki damar da Zaki kwaci yancinki da hannunki dik abinda sukai Miki zan wargaza shirinsu a Daren yau zuwa gobe..... Kallon mamaki kawai Fatima take bin ummu dashi Tana tunanin yadda zaayi ta wargaza musu shirinsu bayan alamu sun nuna wasu abubuwan da yarima yakeyi yau kadai tamkar Mara hankali Wanda yasha wani Abu ya nuna an rigada an asirceshi....tayaya ummu zata warware asiri cikin awanni bayan washe gari da safe karfe Tara na safe sunan yarima ango?...wasu zafafan hawayene suka shiga gudu a idanuwanta tausayin kanta ya lullubeta,....ga wani irin soyayyarsa dake dawainiya da ita dik bugun da zuciyarta zatayi hade da numfashinta sonsa karuwa yakeyi cikin zuciyara.....ajiyar zuciya ta sauke yayinda hajiya zainab ta kafeta da idanuwa,tausayin yarinyar na Kara ratsa sassan jikinta jinta dafa ta tayi taji jikinta yayi zafi rau alamar zazzabi nason kamata "Fatima tashi kicire kayan jikinki ki wanke fuskarki kizo kiyi sallah kinji tunda baayi ishai ba muka tafi nasan bakiyiba,koh?" Jinjina mata Kai Fatima tayi sanan ta zare jikinta daga rukon da hajiya zainab tayi Mata ta Mike jiki Babu kwari ta nufi toilet ummu girgiza Kai kawai takeyi hade da tausayin karamar yarinya kamar Fatima wadda take fuskantar kaddarori kala kala.... Mikewa hajiya zainab tayi ganin Fatima ta shiga bayi yasa ta tuna da bakinta dake parlor da sauri ta Mike Tana fadin "asha assha hajiya nabarku a parlor nazo lallashin diyata ne".. Dariya kawar ummu kawai tayi tace "Babu damuwa hajiya aini ba bakuwa bace" Kallon abincin da aka ajiye musu hajiya zainab tayi "bakuci abincinba hajiya" "Wallahi munkoshi sallah zamuyi ma mutafi...." "To ku shiga wancan dakin akwai toilet sai kuyi alwalar,wallahi hankalina dik ba kwance yakeba an kunnowa Yar autata wuta ga autar tawa da shegen rigima" ********* Wajen karfe Tara su hajiya babba suka shigo gida hayaniya ta kacame cikin harabar gidan inda Yan matan amarya keta fitowa daga cikin mota suna yo hanyar gidan hajiya zainab inda suka ajiye kayansu, Ganin haka yasa Fatima saurin gyara fuskarta dikda kumburin da idanuwanta sukayi, Bubbuga kofa Suka shigayi,da sauri ta sakko daga Kan gadon lokacin ummu tabi kawarta tayi Mata rakiya ta fito ta bude musu kofa, Suka shigayi shisshigowa ciki,faizah ta dubi Fatima tace"malama saiki tafi Babu ko sallama?ganin fitarki kawai mukayi" Karbe zancen teemah dollar tayi da fadin "ai maki gani ya kauda idanuwansa Domin irin soyayyar da deejah suka nunawa duniya yau Dole dik wani makiyinsu yabar wajen Wanda bazai iya ganiba" "Ahayyeeeee yau munga soyaya har wani narkewa deejah take a jikin yarima gaskiya sun Dace sosai'cewar Sunita Tana wurgawa Fatima harara, Sororo Fatima tayi tsaye tana kallo da sauraren ikon Allah yadda suke zubo zance tamkar suna jiranta,zuciyarta babu Dadi Amma haka ta daure ta cije tace "ai soyayyar gaskiya itace soyayyar da ake kebewa anayinta ba don ganin idon mutaneba Dan su tafi da abin a baki suna Fadi yazama son asani kenan Domin ko ibadar Allah ce kayita don ganin idon mutane inda kayita anan zaka barta,saboda haka tafiyata tanada nasaba da kishina da mijina yakeyi gudun kada wani ya kulani kafin ya mallakeni in mallakesa a matsayin maaurata" "A mafarki Zaki mallakeshi Fatima Domin Dan asali sai Yar asali ba tsintacciya Yar kwararo Yar rukon gwamnati ba tsohuwar Yar taada wacce tayi kwana da kwanaki a kurkuku"cewar deejahmah Tana murmushi, Takaicine ya rufe Fatima Wanda take taji jiri na Shirin dibarta saboda cin mutuncin da deejahmah tayi Mata cikin mutane,Koda yake ba laifinta bane dama yarima munafuntarta yakeyi Yana xagayawa suna soyayyarsu tunda ya kasa controlling kansa cikin mutane....hawayene ya taru a Ramin idanuwanta Amma saita daure ta juya batare da tace komiba har ta shiga daki abun ya ciyoya ta fito fuskarta Babu walwala lokacin suna zazzaune suna kallo,har gefen deejahmah Fatima ta karasa ta zauna gefen kujera ta watsa Mata manya manyan jajayen idonta Wanda Saida gaban deejahmah ya fadi ta dago Kai Tana binta da kallo,daf da fuskarta Fatima tasa fuskarta ta Soma magana, "Ki tabbatar da dik ranan da aka dauramin aure da Kabir kashinki ya bushe da dik wani Wanda ya goya Miki baya kikeyi dik ku shirya ku daura dammarar fada Dani Domin kubar ganina haka abinda na kudura a Raina sai ya Dade Yana baku mamaki nidake sai min Zama tamkar damusa da ya'yan kura, ki kiyayi gamona dake Domin Yar karuwa saitayi Miki abinda baki taba tunani ba saina tabbatar Miki da tabbas ni Yar kwararoce a Nan ne zaa banbace mowa da Bora a wajen miji" Kallo kawai sukebin Fatima dashi kowa fuskarsa shaye da mamaki,...dagowa deejahmah tayi tadanyi murmushin karfin Hali "idan nabaki damar shiga gidana kenan dik kike wanan furucin" Mikewa Fatima tayi tana Taku daidai dik suka bita da Ido kamar wata tv gashin ganta na Lilo a bayanta yadda tayi parking dinsa da ribom... Tayi hanyar dakinta aka turo kofa bilkisu ce tayi satar hanya ganinsu deejahmah yasata tayi turus zuciyarta ta shiga bugawa da sauri ta zube a gaban Fatima Tana fadin "afuwan ranki ya dade kiranki ya iso gareni bansamu damar zuwa bane Saida na karasa aikin da nakewa hajiya a cikin gida" Kauda Kai Fatima tayi tamkar bazatace wani Abu ba dakyar ta bude baki tace"keta shafa Amma kisani bazaki bar gidan Nam ba sai kin karasa mun dik aikin da nake Shirin saki Dan Banga dalilin da zaisa nakiraki tun Rana kimun aiki kiki zuwa ba ,ki shiga kitchen akwai wanke wanke kiyi kafin inzo" Da sauri bilkisu ta Kara rusunawa "angama ranki ya dade na tuba".... Kallon takaici khausar kebin bilkisu dashi sanan ta taba deejahmah tace"Wai saboda tsabar raini irin na wanan shegiyar Wai har baiwar hajiyarmu take Kira tasata aiki tasamu wajene" Yunkurawa deejahmah tayi "kutashi muje bazan iya cigaba da ganin kayan takaici ba" Dukkansu suka Mike suka shiga fita daga gidan Fatima dake daki wajen goma saura tanajin sahun fitarsu ta fito da sauri ta kalli kofar dakin da suka Bari a bude ta rufe ta dawo tayi kitchen, A tsaye ta samu bilkisu kawai saita fashe da kuka ta rungumeta "Yar uwata Ina cikin matsala Domin kabir ya juyamin baya bakiga abubuwan da yakeyiba jiya har cemin yakeyi Wai dadin abun yanada wata"kuka sosai Fatima keyi a jikin bilkisu wadda itama hawayen ne ya wanke Mata fuska da kyar ta lallashi Fatima suka dawo parlor kasan carpet suka zube... Ruke da hannun juna suke bilkisu ta Kare matse hannun Fatima tace "ki kwantar da hankalinki na Dan lokaci ne Amma maganar gaskiya kece a zuciyarsa shi kawai sunyi hatsabibancine sun janyo raayinsa ki Mike da addua kinji?" Share hawaye Fatima tayi ta Kara duban bilkisu da kyau "karyane wallahi dama can Yana sonta munafurcine irin na da namiji Kuma zan bashi mamaki Domin zansamu miji inyi aure in shareshi Dan bazan yarda a nakasani ba shida yaji zai iya yaje can su daddatsa namansa" "Idan kikace haka kinyiwa Allah butulci kinyiwa yarima butulci Domin Babu Wanda zaiyi jihadi irin yadda yayi akanki,karki manta irin wahalar da yayi akanki yakici yaki Sha ya rabu da kowa ciki kuwa harda iyayensa,haba Fatima kiyi Masa uzuri baya cikin hayyacinsa" Take jikin Fatima yayi sanyi Amma can kasan zuciyarta tanajin haushi da takaicinsa ga wutar sonsa dake ruruwa a zuciyarta,.. "Ni Bari ummu ta dawo ma infada Mata ta nemi makaranta tasani kawai Kuma ni bazan sake bin ta kansa ba Dan nasan ba lallai ma ya Kara nemana ba' Murmushi kawai bilkisu takeyi Tana kallon yadda Fatima ke jaraba saboda tsabar kishi.... Dakyar bilkisu ta lallasheta da kalamai masu dadi A haka suka shiga Hira can ta daban... ***** "Wai hajiya Kinga yadda yarinyar Nan ke zuba mulki daga samun yancinta har ruwan iskanci takeyi Wai harda Kiran bilki baiwarki tasata aiki ?bakiga yadda bilki jikinta ke rawaba saboda tsabar tsoronta da takeji" "Dik wanan kafafar da takeyi da Jin Kai da sabon iskancin da takeyi Basu kamaceta ba saboda aransu tayi da Rana tsaka uwarta ba Mai sarautaba ubanta ba Mai sarautaba karewarta ma baasan danginta ko kiristoci bane dik take wanan iskancin to kashinta ya bushe tunda Kabir ya fara shigowa hannu,sanan tunda ta fara muamala da bilkisu to da ita zanyi amfani wajen hada Mata tuggu Dan watarana sai munyi abinda Mai martaba zaisa a ratayeta batare da Taji kamshin auren kabiru ba" Dukansu sukasa dariya kasa kasa,....mikewa hajiya babba tayi da takun takama ta bude drawer ta Ciro gorar ruwan da suka ajiye ta mikawa deejamah"karbi wanan ruwan baba Sudan ne ki shanye shi tas ki shafe fuskarki saidai wani ba kabiru ba Dan gobe iwar haka kin Zama sarauniya" Hannunta har rawa yake wajen karbar gorar ta bude ta zuciyarta fara Tass ta kwankwade ruwan ta shafe fuskarta dashi.... "Karfe Tara na safe zaa daura aurenki Wanda dagashi sai kuma auren khausar da afnan insha Allahu badai shegiya ba a gidan sarauta" Dadi ya Kara Kama hajiya rahina wadda tun dawowarsu wajen dinner bakinta yaki rufuwa... ******* Yarima Yana bangarensa dik minti biyar sai ya watsawa jikinsa ruwa saboda abinda yakeji take mararsa ta daure ko rufe idonsa yayi deejahmah ke tunanowa da kamshin turarenta,yayinda dayan bangaren zuciyarsa da ya tuna da baiga Fatima ba sai zuciyarsa tayi Masa nauyi,tunanin yadda zaayi ya fadawa ummu Fatima ta bace yakeyi Dan yasan akwai drama Amma tunanin da yakeyi yagansu da Ablah ko Tana gidanta,ya yi tunanin zuwa gidan ummu Amma yaganta lokacin data shiga fada wajen Mai martaba Allah yasa ba maganar batan Fatima taje yi Masa ba,yasa hannu ya sharce zufar goshinsa sanan ya janyo jallabiya yasa ya daga Kai ya kalli agogo karfe Sha daya da minti biyar na dare haka ya zura takalminsa ta nufo gidan ummu... ****** "Bilkisu dare yayi ki kwana a Nan kawai idan kika tafi tsoro nakeji ummu har yanzun Bata dawoba" "Baki gudun ummu tasan tsakaninmu?" "Zan sanar da ita idan lokaci yayi ki kwantar da hankalinki"buga kofar akayi da sauri fatima ta Mike Tana fadin "ga ma tanan"tayi hanyar kofar t bude da sauri taja da baya ganin yarima a hargitse yasata mannewa da bango,ta hade ranata tamkar Bata taba dariya ba kallon mamaki yakeyi Mata kawai ya karasa shigowa ciki Yana binta da kallo da kyar ya bude muryarsa a dishe yace "shine kika tafi ko?"... Cike da tsiwa tace "mezan tsaya inyi Kuna soyewarku kaida amaryarka Wai nabaka wurine kaji Dadi ka nunawa duniya yadda kakeson abarka" "Ke ni kikewa tsiwa da rashin kunya Ina Wasa dakene?" Ya daure fuskarsa Yana watsa Mata mugun kallo, Juyawa tayi tai wucewarta "Dan Kinga Ina sonki Zaki Raina ni ko?ya kamata kisan matsayinki a zuciyata be Dace ke nemi rainani ki wulakantani gaban kawarki ba" Takaicine ya rufeta kawai ta fashe da kuka wato ma yayi Mata laifi Amma yazo yanayi Mata masifa lallai ya nuna Mata tabbas shi Dan halak ne, Shigowa ummu tayi dauke da sadik a kafadarta da sauri bilkisu ta je ta amsheshi ta karbi jakar hannun ummu tayi daki yayinda ummu ta bi yarima da mugun kallo ta juya taga Fatima na shasshekar kuka, Hanyar fita ta nuna Masa "zoka fita mun a gida tunda abinda kayi Mata be ishekiba kazo ka Kara Akan nada koh?fitamun a gida kabiru kafin in sassaba maka" Shiru yayi Yana mamakin ummu yadda ta sauya lokaci daya take kaunar Fatima fiye da kowa takaicine ya lullubesa tayi masa rashin kunya Amma an bige da korarsa to tabbas idan ya tafi sai ya hora Fatima bazai sake dawowa garetaba Dan yafi karfin korar Kare...juyawa yayi cikin takaici yace "Saida safe"ya fita abinsa Fatima tabisa da kallo Tana hawaye... "Kiyi Shiru kidaina kuka dik sainayi maganin ko wani Dan iska a gidan Nan Dani suke zance ki kyaleshi idan ya gadama Kar yasake zuwa sai an kaiki dakinshi saime idan ankaiki ya koro min ke,sauran Yan iskan nagama dasu tunda nasamu Mai martaba zasuji result" Ta wucewarta daki bilkisu na Shirin fita ummu tace ta zauna suyi aiki da safe dare yayi hakanan ta zauna dakin Fatima ,har biyun dare Fatima batayi bacciba Tana kuka Abu goma da ashirin gobe Kabir zai agwance gashi yanzun bayasonta.... Sai wajen asuba bacci barawo ya saceta,haka ta tashi da safe jiki Babu kwari ga masifar ciwon Kai..... ******* Da sassafe aka shirya deejahmah akasa mata alkyabba tayi kyau da ita wajen karfe takwas gida ya rude da busar algaita ta ko Ina manyan mutane da sarakuna kawai ke shigowa yayinda aka bude babbar kofar fada inda anan ne zaayi daurin aure... Babbar Riga da Yar ciki Kabir yasa yayi kyau kamar wani babban mutum maroka dik inda yabi suna bnsa da kida da kirari..... Kuncin da yake ciki yasashi yake kawai yakeyi haka ya shiga gaisawa da mutane haka ya Raba ya shiga fadar yayi kicibis da mahaifin deejahmah yasha Nadi ya dawo daga Egypt har kasa ya tsugunna ya gaidashi ya amsa cike da faraa ....jamaa ne cike da wajen wadanda ya kallon mutum ne aminin sarki Wanda yazo tundaga wani gari sarki ya sashi ya zauna gefensa maimakon galadima dake Shirin Zama Dan ya Mika auren yarsa,damin kudi sarki ya mikawa aminin nasa Yana murmushi Yana fadin Allah yasa alheri Nan akafara gudanar da daurin aure inda aka sanar a loud speaker akwai wani daurin aure Wanda shi zaafara gabatarwa ,.. Take me sanarwa ya fadawa jamaa aka shiga gudanar da daurin aure yadda musulunci ya tanada Saida aka daura auren sanan Mai martaba yayi murmushi yace "alhamdulillah aminina babba na Mika Masa sadakin diyata Fatima marainiyar Allah Akan naira dubu dari biyar Wanda aka daura da Dana kabiru shine auren da muka fara daurawa jamaa ku shaida"take Mai shela ya shaidawa jamaa an daura auren kabiru da Fatima,kallon kallo mutane keyi dama Mata biyu zai aura?" Cikin minti biyar aka Kara yin shela ta daura auren deejahmah akaro na biyu da Dan sarki yarima"....Nan maroka da makida suka fara kidi tamkar jira suke a har gitse galadima ya mike yana fadin "ban yardaba ban amince da wanan auren ba,matukar kabiru zai auri shegiya bazai zauna da diyata ba Dole ya saketa"...Nan jamaa wuri ya dau hayaniya sarki bece komiba sai gaisawa da jamaa da ya cigaba da yi ya shiga bayarda kyauta ga wadanda Allah ya ciyar sukazo daurin aure.....yarima kuwa daskarewa yeyi a zaune dik jamaar dake Mika Masa hannu kasa dago hannunsa yayi ya Mika,yayinda waje ya kacame da hayaniyar galadima da tawagarsa.... Cire malum malum dinsa yayi yai cikin gida mutane Yan kallo suka rufa Masa baya..... *Muje zuwa 🙆🏻hajiya zainab ta hada gurmi....* *SLIMZY😍*🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* 38 Bankado labulen parlorn yayi a fusace "Ina khadijar take "...da sauri deejahma ta dago fuskarta a furgice Jin yadda aka Kira sunanta, "Tashi muje sai dai ya zaba ko ke ko Yar shegu Dan bazai yuwu da mutuncina da komi a wulakantani a tozartani cikin dubban jamaa ba wadanda sukazomin daurin aure" Kallon mahaifinta takeyi fuskarta dauke da furgici cikin rashin fahimta bakinta Yana rawa dakyar ta lalubo kalmomin ta hadasu tace "meya faru abbah?" "Au ku bakusan meke faruwa ba Kuna cikin gida ne?" Hajiya rahina wadda ta fito daga daki ta karbe zancen da "Wai meke faruwa ne naganka haka a furgice" Ya bude baki zaiyi magana yarima yayi sallama a parlorn take jakadiyya ta rangada gu'd'a... "Ga munafukin Nan ya shigo,wato dik kananan maganganun da akeyi da dik wata gutsuri tsoma na maganar aurenka da Yar gidan marayu Ashe dagaske ne ,tunda yau ta tabbata cewa Kai din Dan halas ne tunda ka hada baki da Mai martaba andaura aurenka da Mata biyu" Dafe kirji hajiya babba tayi "Mata biyu" 'kwarai da gaske Mata biyu sanan wani wulakanci ma Saida aka daura aurensa da waccan sanan aka daura da yata saboda tsabar cin fuska ban taba tunanin Mai martaba zaimun haka ba" Jikin deejahmah ne ya Kama rawa take kafafuwanta suka dauki rawa tamkar wadda akasawa shocking ta shiga ja da baya a hankali har ta jingina da jikin bango saboda yadda jiri ke dibarta, Takaicine ya rufe mahaifin deejahmah ganin yadda yarima ke faman raba idanuwa,cikin kumfar baki ya Soma zazzaga balai "cikin biyu zaayi daya, matukar kanason Zama da yata saidai a warware wannan auren munafurcin da aka kulla ko Kuma wallahi ka sakar min yata yanzun Nan Dan ba neman Kai nakeyi da ita ba" Zabura hajiya babba tayi tai Kan yarima ta cakumo malum malum dinta bakinta har rawa yakeyi "wallahi saika saki Fatima baka isaba kabiru nagaji da wanan cin Kashi da cin fuska da akemun uban waye yace kasa a daura ma aure da tsintacciyar mage?wanan auren be dauruba wallahi Dole a kwanceshi"....ta shiga jijjiga yarima tamkar wadda ta zare a guje tayi cikin dakinta ta dauko mayafinta ta yafa ta fito kafa babu takalmi ta nufi hanyar fita Tana fadin "wajen Mai martaba zani wanan munafurcin da aka kulla Dole a kwance shi Dan aga bayana anyi haka ne a nunawa duniya cewa kabiru shine Dan gata Dan so,an mance da shegiyar yarinyar itace tayi silar mutuwar dana daya tilo,....nayi hakuri dikda abubuwan da yaron Nan yakemun Dan ya bakantamin Rai Amma yau Dan a nuna Mana iyakarmu shine aka Mana wanan tozarci" Hajiya karama wadda ta fito sanye da lafaya Mai shegen kyau kqlar ja,itace ta rike hajiya babba Tana fadin "karkice zakije fada Akan wanan abinda Allah ya Riga ya kaddara kekinsan bamu Isa mujada hukuncin Mai martaba ba" Hankade hajiya karama tayi "karki kuskura kice Zaki gayamun maganar banaza Samira dan na Dade da sanin ke muna fuka ce kece kika kulla komi saboda anga banida da banida sauran gata banida da namiji shiyasa ake wulakantani a idon duniya"kawai sai hajiya babba ta rushe da kuka Tana fadin "wallahi koni ko ku a cikin gidan Nan" "Dakata safiya ba inda zakije karma kice Zaki bangaren Mai martaba Akan wanan maganar sakarmun yata kawai zaiyi" Yarima Wanda ke tsaye kamar an dasashi sai a sanan ya samu damar magana"mahaifina be bani damar sakin ko wace mace ba ya mun umarni da dik macen Dana aureta to na aureta ne sai mutuwa" Hajiya rahina dakyar take Tako kafafuwanta wadanda sukai Mata nauyi ta kasaro gaban yarima tana binsa da kallo Tana zagayesa "lallai ka cika Kai babban munafukine shiyasa kukai munafurcin da Saida aka yantata daga baiwa kaida hajiya zainab ko?to mu zuba wallahi summa tallahi saika gwammaci kida da karatu daga Kai har matsoraciyar yarinyar Kuma kasani ya'ta Yar halak ce ba shegiyaba alhamdulillah kowa yasan Yar asalice Dan haka Allah ya bada zaman lafiya kabiru Amma zakayi danasani" Juyawa hajiya rahina tayi taja hannun galadima kafarta ko takalmi Babu suka fice daga parlorn sukai waje, Fitarsu yayi daidai da faduwar deejahmah kasa sumammiya,a guje jamaaar gidan sukai kanta harda yarima Wanda ya cire malum malum dinsa yayi jifa da ita ya ciccibeta yayi waje da ita,bangarensa ya nufa da ita.... ********* Tunda ta daga Kai ta duba agogo taga karfe goma na safe ta tabbatar da an daura auren yarima da deejahma kifa Kai tayi a Kan pillow ta shiga kuka Mai cin Rai Wanda batasan dalilinsa ba,hajiya zainab ta Dade da shigowa dakin tai tsaye ta rike kugunta Tana kallon Fatima wadda ke kuka kamar wadda akayiwa mutuwa,murmushi tayi a hankali ta taka har wajen gadon ta dafa kafadar Fatima ta furta a hankali "kuka ya Kare diyata kin samu yanci a yau din Nan,tashi ki share hawayenki alkawarin Allah ya cika kedin dai da baaso kece uwar gida a wajen kabiru Domin aurenki aka fara daurawa kafin na Khadija" Cakkk Fatima ta tsaya da kuka gabanta ya tsananta faduwa,dakyar ta yunkura ta Mike a hankali ta zauna fuskarta sharkaf da hawaye ta kafe hajiya zainab da idanuwa ko kiftawa batayi, Dariya sosai ummu tayi "kiyi Shiru ki share hawayenki zakaran da Allah ya nufa da cara ko Ana muzuru Ana shaho sai yayi Fatima Allah ya daukaka daarajarki burina ya cika don nayi abinda nasan harabada safiya bazata mance da wanan bakin ciki ba kedin dai kece uwar gida Kuma matar so" Rungume hajiya zainab Fatima tayi Tana kuka Tana dariya lokaci daya,....ita kanta hajiya zainab din dariya takeyi Tana bubbuga bayan Fatima... Dago Fatima tayi tana dubanta Tana murmushi,take kunya ta lullube Fatima ta rufe fuskarta da tafin hannuwanta.... "Bude idanuwanki bakida wadda tafini nice uwarki nice ubanki Fatima sanan inaji a jikina kedin wata ce inaji a jikina iyayenki zasu bayyana kinji" Bude idanuwa tayi sababbin hawaye na sauka a idonta "ummu nacire Rai da ganin iyayena,zuciyata tafara mantawa da zancen iyayena tunda nasameki a matsayin uwa....nayi babban dace" Share Mata hawaye tayi ta mike tsaye ta fice dakinta,Jim kadan ta shigo da alkyabba baka Mai aikin golden colour Mai shegen kyau da tsada...ta karaso "taso kisa in kaiki fadar sarki sanan daganan mu shiga cikin gida koh" Gabanta ne ya fadi ta shiga girgiza Kai data tunada babban bala'i dake tunkarosu baki na rawa tace "ummu muje wajen Mai martaba kawai mudawo" "Tsoro ba naki bane Fatima dakewa zakiyi muje Mai martaba yasa Miki albarka mu shiga cikin gidan Kai tsaye gidan mijinki ne yanzun Babu shegiyar data Isa ta takaki Dan haka karki kuskura kibari suyi galaba akanki lokaci yayi da zanbaki dama ki Rama abinda dik akai Miki na karbar Miki yancinki na huce Miki takaici sauran yakin zan koma Baya ingani Yar tawa jaruma ce?".... Dago idanuwa tayi ta saukesu Akan ummu sai ta sunkuyar da kanta kasa Tana murmushi.... Canja Kaya tayi daga kayan dake jikinta xuwa hadaddiyar Riiga baka Mai shegen khyau ummu ta Bata ita kyauta daga saudiyya ta siyota,Saida tasa Mata ita sannan ta Dora Mata alkyabba wayyoo zokuga yadda alkyabba ta fito da Fatima tamkar Yar larabawa ta ummu da kanta ta gyara Mata fuska sanan suka fito gidan direct fadar sarki suka nufa.... Saida jakadiyya tayi musu iso sanan suka shiga,....har gaban sarki ummu ta zube ta kwashi gaisuwa dubban jamaa dake cikin fadar kowa sai Allah ya sanya alheri yakeyi fuskar hajiya zainab sai faraa takeyi.... A gaban Mai martaba ta ajiye Fatima wadda ta gaidashi cike da girmamawa ya amsa fuskarsa dauke da faraa Nan ya shiga yi Mata nasiha wadda batasan lokacinda hawaye ke gudu a idanuwanta ba....yasa Mata albarka sanan cikin jamaa ya shaidawa dik wani Wanda yake fadar yabawa Fatima kujerar makka da dawakai dari da rakuma dari da shanu dari sanan da kujera uku extra ta wadanda zasu rakata aikin hajji...da kyautar motoci uku Wanda natane mallakinta Dasu zata rinka fita Kuma ya Bata bayi goma masu kulawa da ita a matsayinta na uwargidan dansa daya tilo....kabbara ce kawai jamaa keyi a wajen Shesshekar kuka kawai Fatima takeyi Tana sauke ajiyar zuciya ganin komi takeyi tamkar a mafarki...yau itace keda wadanan niimomin gabaki daya?...godiya sosai ummu tayiwa Mai martaba harda Fatima wadda kalmomin godiya da tayi amfani dasu gani takeyi tamkar sunyi kadan....haka kawai Mai martaba ya kasa dauke idanuwansa daga gareta ya rasa dalilin dayasa yarinyar ta shiga ransa ga fuskarta da takeyi Masa gizo lokuta da dama... Sallama Sukai da fada suka nufo hanyar cikin gida....dakyar Fatima ke taka kafafuwanta a haka har suka Isa... ********* Da sallamarsu suka shigo cikin gidan inda kallo ya koma sama,jamaa sai tururuwar fitowa sukeyi Dan suyi kallo dik Wanda ya Dora idonsa Akan Fatima sai yace Masha Allahu saboda wani irin annuri na kyau da kwarjini dake fita a fuskarta, Dakin hajiya karama suka nufa inda maroka Mata Suka shiga wasa Fatima suna yi Mata kirari....faraa sosai Yan uwan hajiya karama suka shigayi suna fadin "Masha Allahu tubarkalla Allah ubangiji ya bada zaman lafiya Allah yasa ace gara da akayi,lallai yarinya kin shigo gidan sarauta da kafar dama hakika kin Zama tauraruwa wadda ke haska masarautar barayar Zaki da kewaye Allah ubangiji ya sa albarka" A gaban hajiya karama Fatima ta tsugunna ta sunkuyar da kanta kasa,...kallonta hajiya karama takeyi Tana murmushi ta dago hannunta ta Dora akanta Tana shafawa "Allah yayi Miki albarka Fatima Allah ubangiji yasa alkhairi a zamanki da danmu kinji?ikon Allah sai kallo dik abinda Allah ya kaddara mu bamu Isa mujada ikonsa ba saboda haka Ina farin ciki da kika kasance daya daga cikin surukaina" Murmushi kawai Fatima takeyi kanta a kasa batare da ta dago ba.... Sautin muryar hajiya babba yasa dakin yin tsit tun daga parlor kafin ta karaso take zazzaga balai "ayyiriri shegiya Mara uba itace surukar Mai martaba itace matar sabon sarki Mai jiran gado,...lallai wanan Abu yayi Amma is a tarihi ban tabajin wanan kwado ba ace Dan sarki ya auri shegiya Yar kwararo...wadda akai cikinta a titi iyayenta suka wofintar da ita...to meye sunan jikokin da Zata haifawa sarki? Shegu?"ta kece da wata iriyar dariyar rashin mutunci, Mikewa hajiya zainab tayi 'ke safiya ki Kama girmanki Domin Ina ganin mutuncinki a matsayinki na matar yayana yau da bakida wanan matsayi Dana kaskantar dake a idon duniya" "Zainabu kenan lallai kin cika kin aiwatar da mugun nufinki sanan kin shammacemu a wanan wasan saidai ki gyarawa shegiyar yarki waje Domin sati daya kacal na baki zai sakota Dan bata Isa tazo gidan sarauta a matsayinta na shegiya tayi kishi da yar asaliba sanan Kuma shekara ta zagayo tace zata haihu baa gidan Nan ba" Murmushin mugunta ummu tayi "burina ya cika na tabbatar da na shammaceku Dan na kulla muku abinda har ku mutu bazaku manta ba,kamar yadda Fatima ta auri kabiru cikin sauki Aka kawo muku albishir na aure haka zaa kawo muku albishir na ta Haifa muku jikoki" "Fatima bazata taba Haifa Mana jikoki cikin gidaba Dan bazamu hada jini da shegiya ba,..Kuma min rigada munsan kece kika hada komi batare da son kabiru ba saboda haka nabaki dama wanan karon Amma Ina gargadinki da karki Bari mu hadu a wasa na gaba Dan zakisha Kashi....yaro Yana can daki tare da matarsa Yana jinyar ta" Saida gaban Fatima ya fadi Amma saita danne kawai ta gyara zamanta a gaban mahaifiyar yarima.... Kanwar kakar yarima ce dattijuwa tayiwa ummu tsawa Akan Subar wanan fadan da sukeyi tonawa kansu asiri sukeyi cikin mutane....ummu batace komiba tai shiru yayinda hajiya babba ta shiga zazzaga balai...tagaji ta fuce a dakin... ********* Koda deejahmah ta farfado ta ganta a dakin yarima Yana gefen gado ya zabga tagumi Ahmad na gefe shima fuskarsa dauke da alhini sai kawai ta fashe da kuka Tana fadin "ka cuceni Allah ya Isa tsakanina da Kai Kuma wallahi bazan zauna a gidanka ba matukar da wanan karuwar zaka zauna" Dago jajayen idanuwansa yayi cike da balai ya fara magana "karki kuskura ki Kira fatima da karuwa a gabana kingane ko?yadda kike matata haka itama matata ce"...ya Mike a haukace ya fara masifa "waini ya kukeso inyi ne ke baa aure aka aureki?Koko kukadaine mutane?koba Fatima kina tunanin ke kadaice Zaki zauna a gidana?dama banida raayin Zama da mace daya wallahi saboda haka kisani ki bude kunnuwanki daga ke har Fatima Babu Wadda zata shigarmun gida Tana min iko baku isaba wallahi"...Yana nunata da yatsa,...mikewa Ahmad yayi ya kamosa ya zaunar da shi Akan kujera Yana fadin "cool down my friend ka kwantar da hankalinka please kayi hakuri zafin kishi ne irin na mata kawai,Kuma kaga batada lafiya kai meta a hankali" Hura hanci kawai yarima yakeyi zuciyarsa na tafarfasa,....ko Ina xafi Babu inda zaisa rayuwarsa ya huta ,yanzun ya Gama jiyo hayaniyar su cikin gida yasan dik Akan maganar ne ga babban bala'i dake damunsa Wanda ya rasa dalilinsa na fadawa wanan jarabar ta bukata...... Kuka sosai deejahmah takeyi harda shassheka ta dafe kanta kawai hawaye ke gudu a fuskarta,dago kansa yayi ya kalli yadda take kuka tamkar marainiya,wani irin tausayinta ne ya lullubesa,Dan tabbas yasan wanan abun da akayi Mata akwai ciwo Amma shi kansa yasan hikimace babba Mai martaba yayi Dan inba hakanba Babu yadda zaayi ya mallaki bintu,. Tasowa yayi ya dawo kusa da ita ya janyota jikinsa kawai saita fada kirjinsa Tana kuka da shassheka tausayinta ne ya lullubesa ya shiga babbuga bayanta a hankali... Mikewa Ahmad yayi ya fice zuwa parlor ya barsu ciki,.. Kasa cewa daita komi yayi sai lallashinta da yakeyi yayinda tsigar jikinsa ke tashi ta ko Ina,...ganin haka yasata yin shiru hade da lafewa kirjinsa Tana sauke ajiyar zuciya gabaki daya deejahmah kanta ya Gama daurewa babu abinda zatayi ta samu sassaci a cikin zuciyarta Sai kukan,tabbas tasamu Dan relief na zubda hawayenta da tayi ganin bece Da ita komiba yasata mikewa jiki babu kwari Tana takawa a hankali har parlornsa inda ta tadda Ahmad zaune ya rafka uban tagumi ya bita da kallo har ta fice.... Fitarta yasa shi fitowa parlor ya zauna gefen Ahmad...."ya kamata ka canja kayan Nan na jikinka Dan Kai ango ne tunda wadanan sun yamutse kasa wasu kasan dai karfe biyu akwai walima koh?..." Juyowa yayi ya dubi Ahmad fuskarsa dauke da damuwa yace "wallahi ganin komi nakeyi tamkar a mafarki,Amma kasan wani Abu kasan zuciyata farin ciki nakeyi da samun wanna baiwa da Allah yayi mun na amsar adduata cikin sauki na mallaki Fatima a matsayin matar aure Kuma bazan mutu ba sai na cika Mata burinta na mallaka Mata dik wani farin ciki....saidai wasu canje canje da nake gani a wajenta na kishi da ta dorawa kanta' "Nasani friend karka damu yau zaku angwance zaka Kuma lallashi abinka".... "Hmmmm"ajiyar zuciya kawai yarima ya sauke ya nufi Mike yace "Bari insake wanka" "Owk"..... ********** Koda deejahmah ta shiga gida direct dakin hajiya babba ta shiga ta taddasu zugum zugum a kuryar daki tamkar anyi mutuwa, Gefen gado ta nema ta kwanta wasu sababbin hawaye na gangarowa a gefen fuskarta, "Kidaina kukan Nan da kikeyi yanzun min rigada munyi sabon shiri....Kuma yau din Nan zamu aiwatar dashi ai wajen walima zamuje ko?to nasan abunyi wanan gida kece Zaki Soma shigarsa Kuma kece zai fara Tarawa da ita....nasan abunyi na tabayin wanan muguntar da dadewa wadda shine silar samuwar farin cikinmu kema Kuma abinda zanyi Miki kenan....zuciyata ta Gama bushewa nagama Shirina tsafff daga safe zuwa yanzun....ai hajiya zainab tabar shiri tun Rani ta mamayeni ne ta Kuma Sami saa Amma wanan karon bazatayi nasaraba Dan batasan Shirina ba..... ******** Tsaf Fatima ta kwashe labarin rayuwarsu na gidan marayu taba ummu a inda suke zaune a kuryar daki Tana kuka ta fayyace Mata komi dake tsakaninta da bilkisu... Sosai ummu ta jinjina lamarin ta ja dogon numfashi ta sauke..."bilkisu itace zata zame Mana babban makami Domin da nayi niyyar kwatarta ta karfin Hali tunda banida wata baiwa yanzun Amma zamanta a can din alheri ne...saboda Babu Wanda zai rinka samun information Akan abinda suke ciki Dan haka zanbarta a can sanan xan Bata damar Zama babbar aminiyar ta don ta hanyarce zamusan halin da suke ciki Domin yanzun dik yadda zaayi su dauki fansa shi sukeso Dan inada yakinin hajiya babba zata iya kisa tunda itace silar babban al'amari daya faru a masarautar Nan a baya Dan nadade Ina zarginta shiyasa nake tsoron mugun nufinta yasa na bullo Mata ta bayan gida...." Jinjina Kai Fatima tayi cike da gamsuwa sanan ta rusuna tace "nagode ummu Allah ya saka Miki da alheri" "Yauwa Fatima kece fa uwar gida Dan haka dakinki ya kamata yarima ya fara tarewa Dan haka nakeso in Miki wata tambaya " Sosai Fatima ta maida hankalinta Akan ummu "tambayar itace da dai nasan kinada tsarki Amma yanzun bansaniba ko kinyi bako" Kunyace ta lullube Fatima ta dukar da kanta kasa ta girgiza Kai alamar aa "Good jeki wanka ki fito inbaki wani sirri wadda na tabbata inhar hakan ta kasance to babu wadda zata wuce gabanki a wajen miji" Murmushi Fatima tayi ta Mike tayi Shirin wanka ta shige bayi,ta Dade Tana kuka a bayi Tana fargabar abinda ummu ke Shirin Bata umarnin yi Wanda batada agendarsa a yanzun....dikda itama akwai tarkon da tayi da tayi niyyar danawa yarima... Haka Nan tayi wanka jiki Babu kwari ta fito ko kafin tasa Kaya Saida ummu ta turare kayanta da turarruka kala kala sanan ta bita da wasu ta shafeta dasu Tass sai kamshi ke tashi Mai sihirtaccen Dadi... "Nasan yarima yayi Miki laifi Amma tabbas Dole ki bashi kanki yadda Zaki samu damar ramawa....ki kwantar da hankalinki kinji diyata yanzun lokacinki ne Dan haka kiyi abinda nace kawai" A furgice bilkisu ta shigo dakin Tana waige waige tayi zuru zuru daga ummu har Fatima kallonta sukeyi cike da fargaba..... *Yanzun aka fara Wasa dikda munzo gangara* *SLIMZY🥰*🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* 39 Cakk bilkisu ta tsaya Tana zazzare idanuwa Tana kallon ummu Dan batasan cewa Fatima ta bayyanawa ummu ko ita wacece ba, Dukkansu suka zura Mata idanuwa suna jiran suji meke tafe da ita Amma sai ta sauke murmushin karfin Hali ta juya da niyyar fita, Ummu ce tai maza tace "dakata bilkisu nasan komi dake tsakaninki da Fatima Bata boyemin komiba ta fada mun Dan haka ki kwantar da hankalinki kizo ki fadamun meya faru" Juyowa tayi jiki Babu kwari ta tsugunna a kasa,...ummu da kanta ta dago da ita ta zaunar da ita a kujerar dake jikin madubi tace"umhmm Ina sauraronki" Kasa tai da muryarta "hajiya ce naji tace Zata samu daya daga cikin bayin Fatima ta Basu magani da zasu sa Fatima bazata taba haihuwa ba harabada.....sanan cikinsu zatasamu wadanda zasu rinkayi Mata aiki Akan Fatima yadda zasu cutar da ita cikin ruwan sanyi....zasu nakasa rayuwarta batare da kowa ya fahimci sune ba,a yadda naji ma Ashe deejahmah ta auri Kabir ne don ta samu ciki ta haihu yadda zasu kashe shi"...... Daskarewa ummu tayi Bata Bari bilkisu ta Gama bayanintaba ta Soma salati Tana fadin "lallai dik abinda hajiya safiya tace zatayi zata aikatashi Koda kisan Kai ne kuwa karamin aikinta ne,...zamanki da hajiya ba karamin taimako bane ga wanan yarinyar Domin da badanke ba da bamuji wanan babban tuggun da suke Shirin yi ba.....Kai safiya anyi shedaniyar mace,Babu Allah a ranta kwata kwata,batada burin da ya wuce taga tafi kowa ,Babu abinda ke tattare da wanan baiwar Allah sai son zuciya".... Bilkisu ta sunkuya kadan sanan tace"a yadda naji sunce a al'adar ba haushe wadanda akai aurensu Rana daya dik wacce aka fara kaiwa gidan itace uwar gida saboda haka zasu dauki deejahmah su kaita gidan saboda maganin da suka Bata ya zamana itace uwar gida idan har yarima ya kwana a dakinta to Babu shi Babu Fatima" "Innalillahi wa Inna ilahi rajiun.....tabbas maganar haka take daura auren Fatima a farko bashi zai Bata damar Zama uwar gida ba a al'adar bahaushe sai wadda aka fara kaiwa dakin miji,wanan haka yake nagode sosai bilki tashi kije" Jiki Babu kwari bilkisu ta Mike tai hanyar kofa Tana waigen Fatima wadda ke jingine a jikin bango hawaye na gudu a idanuwanta, "Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun narasa dalilin da yasa mutanen Nan suka tsaneni bansan me hakan yake nufiba,Allah kana gani dik abinda na aikata banyi hakan da gangan ba nayi ne Domin Kare mutuncina,jarabawa da kaddara tasa na aikata kisan Kai Wanda dik wanan dalilin shi ya janyomin Tsana da kin jini,kodan nakasance Mara iyaye shegiya yasa ake kyamata ake tsanata"...toshe Mata baki ummu tayi 'kar insakejin wanan furucin daga gareki idan ba hakaba zan sassaba Miki" Bude drawer ummu tayi ta Ciro Mata sababbin Kaya wadanda zatasa zuwa wajen walima.... Lafaya ce Mai shegen kyau irin ta shuwa Arab Mai shegen tsada da kyau shi Fatima tasa sanan ta canja Mata wata akyabbar...ta shiryata tsaf ta Kara turare Mata jiki da turarruka masu shegen kamshi ta zaunar da ita a gefen gado, "Fatima kiyi hakuri da dik abinda ya sameki a rayuwa kinji? Babu Wanda yafi karfin kaddara irin wadda ta fada Miki ta fada mishi kinji?Kuma inhar iyayenki nada sauran rayuwa nasan zasu nemeki Kuma Zaki hadu dasu kinji?ki rike mijinki da kyau ki bashi kulawa wadda dik wata macen aure ya Dace ta bawa mijinta kinji?abinda nakeso dake shine yanzun gaskiya bazan baki damar zuwa wajen walima ba Domin mamayarsu zanyi a karo na biyu tunda har ga abinda suka bullo dashi zan bullo musu ta bayan gida" Wasu siraran hawaye ne Suka zubowa Fatima a kumatu tasa gefen hannunta ta share, "Toh ummu"....tausayi Fatima kawai take bawa ummu.... ******* Shiri sosai sukai na zuwa wajen walima ko wa yasha kayansa masu shegen kyau da tsada,na wanan Yana wane wanan haka waje ya cika da milliyoyin jamaa daga fanni daban daban....wajen da aka tanada Domin zaman amare da ango Nan deejamah da yarima suka zauna, Sai baza idanuwa yarima yakeyi yaga Fatima Amma shiru be gantaba,haushinta ne ya lullubesa ya Gama fahintar inda yarinyar Nan ta dosa Amma zai koya Mata hankali,. Be Gama Shan mamaki ba Saida yaga ummu a wajen walima da kowa na wajen Amma babu Fatima Babu dalilinta,...dikda irin fushin da yakeyi da ita hakan besa ya daina tunaninta ba,Rabon da ya ganta tun ranan dinner dinsu shima basuyi magana ba ko a wani Hali take ciki oho.... A daidai kunnensa ummu tazo ta rada Masa "zan sanarwa da iyayen deejahmah daga Nan akai amarya dakinta kawai tunda yamma tayi sanan jamaa sun fara tafiya gidajensu"....kallo ya bita dashi Yana so ya tambayeta ita Fatima fa?Amma sai ya kasa kawai ya maida kansa kasa batare da yace komiba, Deejahmah dake gefensa sai kallonsa takeyi ta gefen idonta,ta kasa dauke kanta daga gareshi haka kawai takasa daina kallonsa yayi Mata matukar kyau da kwarjini... Har inda su hajiya babba suke zaune suna tsaigumin baazo da Fatima wajen walima ba gudun kunya ace Dan sarki ya auri shegiya yasa aka kulleta a gida,to sun rigada sun Dana tarko Akan daga wajen idan andau deejahmah a mota ayi can cikin gida inda akai musu gini.... Sallama hajiya zainab tayi Amma babu Wanda ya ansa Mata sai rahina....wadda itama tsoron kada Mai martaba yaji labarin halin da suke ciki takeyi yasa ta amsa, "Nazo ne in shaida muku maganar Kai amare gidajensu inaga zai kyautu idan an tashi Nan sai muje a kaisu ko?"....yatsina fuska rahina tayi sanan tace"umm"...ummu ta juya abinta cikin jamaa suka bita da harara, Zare jikinta ummu tayi ta koma gidanta inda dama ta Gama shirya komi tunda dama ta rigada ta kaiwa Mai martaba ita yayi Mata fada, Can ta dibi tawagar Yan rakiya ciki harda jakadiyyar sarki da babbar kawar ummu wadda tazo Mata biki,..ummu tasa motoci sukai layi a kofar gidanta sanan bayi Suka fara fitowa sanan ummu da aminiyarta sai Fatima wadda ke tsakiyarsu suna rike da hannunta,wadda gaba daya komi ganinsa takeyi tamkar a mafarki haka ummu tasata a mota saura suka hahhau tasu akaja su zuwa gidan amarya, Farin ciki ne ya lullube ummu ganin burinta ya cika na sharewa marainiyar Allah hawaye,....gida ne tsararre ginin zamani Mai sashi hudu a ko wanne sama da kasa ne,...gate guda daya ne na shiga gidan Wanda shine ainihin main entrance na shiga ,....rike hannunta ummu tayi suka nufi sashen gate din gidan,... maaikata da dogarawa gidan suna ganin zuwansu suka bude musu gate din gidan hade da zubewa kasa suna kawo gaisuwa, Addua ummu tabawa Fatima umarnin yi kamar yarda al'adar malam bahaushe take anaso ko wace amarya idan ankaita gidanta tayi addua hade da Bismillah ta shiga da kafar dama..haka Fatima tayi sanan suka shiga cikin gidan Wanda harabar gidan kansa abin kallo ne tamkar baa kasar hausa ba haka ummu tayi musu jagora har sashen da ta zabawa Fatima Dan dama tazo gidan taga komi..... Sama suka hau da ita inda Nan ne dakunan kwanan bangarenta suke, Wani daki ummu ta bude suka shiga da ita Basu direta ko inaba sai Kan makeke hadadden gado Dan kasar waje suka direta... "Masha Allahu" shine kawai abinda kawar ummu ke Fadi "tubar kallah Fatima lallai kinzo duniya a saa Domin samin irin wanan daular sai Wanda Allah ya zaba,saboda haka ki Zama Mai biyayya Kuma ki rike Miji Allah ya bada zaman lafiya"... Nan sukaita Mata nasiha Mai ratsa zuciya sanan ummu sukai sallama ta bi bayan kawartata suka fice..... Bayi biyu ne ke cikin dakin Fatima ko wacce na tsaye gefe da gefe yayinda wasu ke kasa a parlornta mutum hudu Wanda dik nata ne...su zasu rinka kulawa da ita, ********** Sai magriba aka tashi walima inda tawagar jamaa sukayi caaaa a hanyar gidan amarya wadanda sukayo wa deejahmah rakiya da kawayenta da baki wadanda suka zo biki.... Jamaa kowa sai sambarka yakeyi da wanan makeken gida Wanda yasha kayan more rayuwar duniya, Dayan part din aka nufa da deejahmah inda sukai meta rakiya har cikin bedroom itama aka ajiyeta,..too fa Nan kawayen amarya su Sunita Suka shiga kashe selfie a bedroom din deejahmah saboda tsabar haduwarsa .... Dai dai kunnenta hajiya babba ta rada Mata "ki kwantar da hankalinki karki nuna Masa komi Domin dakinki zai Soma zuwa tunda ke aka fara kawowa Kinga kece uwar gida sai yayi Miki kwana bakwai sanan zai koma sashenta lokacin kin mantar dashi wata halitta".... Deejahmah ta jinjina Kai batare da tace komiba,haka suka Gama surutansu sukai Mata sallama harda Yan matan amarya wadanda dama Ahmad ya sallamensu da makudan kudi tun a wajen walima,,,,, Sakkowa kasa hajiya babba keyi cike da Isa da mulki kawai tai Karo da bayi wadanda suna ganinta suka zube ...tabisu da kallon tuhuma Tana kallonsu daya bayan daya "ku Kuma daga Ina" A tare suka hada baki wajen Bata amsa "mune maaikatan sarauniya Fatima wadda aka kawo Nan dazun kafin maraice".....dibbbb network din Kan hajiya babba ya dauke saita juya da sauri zuwa dayar matakalar ta shiga takawa sauri da sauri har ta shige ciki ta nufi kofar da take hangen hasken lantarki tasa hannu ta tura kofar daki, Fatima wadda ke zaune Kan dadduma ta idar da sallah ta dago Kai da sauri,ganin ko wacece yasata sauke lallausan murmushi hade da mikewa ta nade daddumar Tana fadin "Bismillah ranki ya dade,ai ya kamata kishigo kiga yadda Allah yayi da Yar shegiya Yar kwararo"...tai maganar fuskarta dauke da murmushi, "Bismillah ga waje Kun kawo amaryata ne?"ta jefa Mata tambaya dikda zuciyarta na tsananin bugawa.... Kallon takaici hajiya babba keyi Mata "yarinya kinyi kuskuren shigowa hurumin da ba naki ba a guje zakibar gidan Nan da kafafuwanki,idan baki fita da hankali ba Zaki fita da tsananin hauka" "Kinyi babban kuskure hajiya wajen bani damar shigowa gidan Nan Domin kafin infita sai shegiya ta tabbatar da ta Haifa muku jikokin shegu Domin tabar muku tarihi Wanda bazaku taba mantawa ba" Idanuwa kawai hajiya babba kebin Fatima dashi wadda take jifanta da mugayen kalamai a cikin hikima...."lallai kin dakko ruwan dafa kanki tunda daga kawoki ko cikakkun awanni goma bakiyiba kinfara Zama tantiriyar Mara kunya" Yar dariya Fatima tayi ta dago Kai Ido cikin idon take kallon hajiya babba "hajiya dama bakisan dik Dan kwararo bashida kunya ba sai yau?....dik azabar da kikaimun dik a tunaninki biyayyr da nayi Miki tsoro ne yasa nayi Miki su?nayi Miki ne kawai don kedin uwargijiyata ce a wanan lokacin,sanan jira nakeyi insamu damar da Nima zanci nawa duniyar Domin kaf dinku saina baku mamaki,nayi matukar farin ciki da ya kasance ke da kanki kika Tako inda nake har nasamu damar amayar da abinda ke cikina a cikin sauki.... alhamdulillah Allah ya cika mun burina na Zama matar kabiru sanan wani abin farin ciki ma uwargida a wajensa wanan ne ya bani damar Zama sarauniyar sarki Mai jiran gado.....hajiya Dan Allah ga hanya Nan mijina na gab da shigowa"....Fatima ta nuna Mata hanyar Kofa Tana murmushi.... Kalaman Fatima kawai keyi mata yawo akai tamkar a mafarki.....kallon Dan bakin Fatima kawai takeyi yadda take zaro maganganu tamkar Tana jiranta.....batasan lokacin da gumi ya jikata ba sharkaf.....a tarihin rayuwarta Babu Wanda ya taba tararta ga da ga ya mayar Mata da martanin maganganu marasa dadiba Koda kishiyarta ce balle Fatima dake matsayin surukarta..... Jinjina Kai kawai tayi ta nuna Fatima "lallai kin Kira ruwa bakida laima kinzama kiyashi Mai jawo abinda yafi karfinsa.....lallai kin nunamin ke din cikakkiyar Yar bariki ce Amma da sannu zanyi maganinki Zaki hada kayanki da kanki ki koma gidan marayu...idan nayi Miki me sauki kenan idan baki fita gidan Nan da hauka ba" "Yan rakiyarku suna jiranki hajiya".... A fusace ta fice a dakin Fatima ta bita da malalacin murmushi hade da dafa kirjinta ta furta a Fili "banso na Miki hakan ba tun yanzun Amma gara in shayar dake mamaki ki kwana kina tunanina"... Runtse idanuwanta tayi tana sauke numfashi a hankalinki a hankali harta samu natsuwa a zuciyarta..... Jikinsa a sanyaye ya shigo gidan,direct side din dake facing dinsa ya nufa....Wanda shine na Fatima... Babu kowa a parlorn kafa ta dauke haka ya nufi hanyar matakala Yana takawa a hankali a hankali har ya Haye sama.... A hankali ya tura kofar dakin bakinsa dauke da sallama...ya maida dakin ya rufe, Tsaye yayi gabansa na faduwa Yana tunanin wacece a side din da akace Nan zai shiga ya kwana?....kallo yake binta dashi tun daga kasa har sama inda ya sauke idonsa Akan fuskarta dake sunkuye.....ya kafeta da idanuwansa wadanda yake Kara budesu Yana kallonta saboda gani yakeyi tamkar gizo take yi mishi ita dince kuwa?....ya Kare Mata kallo sanan ya tako a sanyaye ya karaso har inda take ya zauna a gefen gado....zuciyarsa ce ta tsananta bugawa Amma hakan be hanasa Kiran sunanta ba a sanyaye "bintu"...shine abinda ya furta a hankali.... "Allah ya cikamun burina na mallakeki a matsayin matar aurena"...besan lokacin da hawayen farin ciki suka Soma gudu a idanuwansa ba.... Ya matso daf da ita ya dago kanta ya kura Mata ido,....ita kuwa Fatima idonta a rufe suke sai zuciyarta dakeyi Mata lugude.... "Ki bude idanuwanki ki kalleni bintu yau na Zama mallakinki kema kin Zama mallakina....dare da Rana banida burin da ya wuce hakan,kullum adduata shine Allah ya cikamun burina na karshe shine aurenki,sai Allah ya dubi kyakkyawar niyyata ya mallakamin ke cikin sauki....hawayen Dadi ke diga a idonsa suna sauka a fuskarta...itama su ta shigayi suna gudu a fuskarta kawai yasa hannu ya shiga share Mata su Amma tamkar karuwa suke.....tausayinta da soyayyarta suka shiga yawo a jinin jikinsa,...ntake jikinsa ya hau rawa ta rungumeta tsammm a jikinsa da karfin gaske..... ******** Kaiwa da komowa kawai hajiya babba keyi a cikin bedroom dinta Tana tunani kala kala....kalaman Fatima kawai ke yawo a kunnuwanta sunayi Mata amsa kuwwa....."tabbas kinyi kuskure Fatima Wanda bazaki tabayin irinsa ba a rayuwa.....lallai kin dakkowa kanki dala Babu gammo Amma nidake zamuga Wanda zaici riba.....sainayi sanadiyyar zamanki a gidan yari na harabada.... *Muje zuwa* *SLIMZY😍*🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* 40 Sundade rungume da juna suna sharar kwalla,dayar yasamu ya saketa kadan ya juyo da fuskarta daidai saitin tasa ya rada Mata "tashi kiyo alwala kafin indawo kinji?"... Shafff Fatima ta saki jiki ta share zancen wata deejahmah sai da yadan kashe Mata ido "minti goma zuwa Sha biyar da kikajiki a jikina har kin manta kinada kishiya"...kauda kanta tayi gefe Tana murmushi kasa kasa cike da kunya batare da tace komiba,...ganin hakan yasashi janye jikinsa daga nata ya fice a dakin, Da sallama dauke a bakinsa ya shiga dakin deejah dake zaune ta kafe kofa da Ido Tana sauraron shigowarsa ta bisa da kallo tun daga sama har kasa sanan ta sauke idonta Akan bugaggiyar shaddar dake jikinsa wadda ta dan yamutse kadan botir din rigarsa daya a balle take jifansa da kallo, Zuciyarta ce ta shiga saka Mata cewar lallai yarima daga dakin Fatima yake,...Bata Gama tunani ba ta tsunkayi sautin muryarsa Yana Mata magana,hade da gyara tsayuwarsa a gefen gadonta hade da watsa Mata manyan idanuwansa "na shigo dare ya rigada yayi naso ace nasamu cikakken lokacinda zan hadaku da Fatima in yi muku nasiha,insha Allahu zuwa gobe zan hadaku gabaki daya in tattauna Daku"....shiru tayi tana Mai sauraronsa batare da tace komiba kusan minti biyar har ya gaji Dan kansa ya huro iska a bakinsa "bakice Dani komi ba kindaisan banason sarauta ko" Jinjina Kai kawai deejahmah tayi zuciyarta na cigaba da tafarfasa.... "Saida safe"...shine abinda ya ce Mata ya nufi hanyar fita ta bishi da kallon takaici ,lallai yarima wato ko arzikin Zama a dakinta ma batasamu ba yaje sun Gama iskancinsu sanan zaizo ya tsaya Mata akai yace yazo sallama ko?kwafa tayi tace a ranta "zaka shigo hannu"karar rufe kofarsa yasata dawowa daga duniyar tunanin data fada....ta Mike ta cire alkyabbar jikinta ta nufi wardrobe din jikin bango ta bude inda kayanta suke jere ta shiga zakudo rigar bacci wadda zatasam.. ******** Yana shigowa dakin ya nufi toilet yayi wanka sanan ya fito ya fice jimm kadan ya dawo sanye da jallabiya ya shimfida dadduma da kansa ya ja kusu sallah rakaa biyu sanan suka sallame, ya juyo gareta ya kakama kanta yanayi Mata addua kusan minti goma sanan ya shafa yayi Mata tambayoyi game da addini alhamdulillah wadanda tasani ta amsa, Da kansa ya mikar da ita ya nade daddumar ya ajiye ta gefe wajen switch din globe yasa hannu ya kashe ya ruko hannunta zuwa gado.... Turesa kadan tayi ya rada Mata a kunne "ke meye haka Wai Hira fa zamuyi"...a shagwabe tamkar zatayi kuka tace"nifa banajin yin hirar bacci nakeji".... Murmushi yayi cikin duhu ya Kara janyota jikinsa ra rungumeta sosai yanajin sautin bugun zuciyarta wadda ke cike da fargaba,...yasani Sarai tsorone cike falll zuciyarta kawai sai ya Dora bakinsa daidai kunnenta ya rada Mata "to Bari insaki bacci ai babyna ce ko?rainonki yabar hannun ummu ya dawo wajena"yadan hura Mata iska a kunne yadda yake maganar kadai yasa jikinta yin sanyi tai lamo a jikinsa ya shiga shafo wuyanta Yana hura Mata iska a kunne....dik da yadda jikinta ya mutu bai hanata tsoro da fargabar Jin hannuwansa na yawo a kirjinta da sassan jikinta.... Saida ya tabbatar ya Gama kashe Mata jiki sanan.....😬labari ya canja Dan gabaki dayansa a furgice yake jikinsa rawa yakeyi tamkar ansa Masa shocking Babu abinda yake bukata sama da ita Babu inda baya lasa a jikinta hawaye ke gudu a idanuwanta ganin dik yadda ya koma tamkar mayuwacin Zaki....kasa hanasa tayi dikda fargabar da takeci data tuna da alkawarinta da ummu kawai saita sakar Masa linzami.... Ko kafin asuba yarima yayi round yakai hudu...bai taba tsintar kansa a cikin wanan yanayi ba irin na yau,da yasamu gamsuwa zaiji sabuwar shaawa na taso Masa,ita kuwa shame shame kawai tayi tamkar gawa Tana Jin yadda yake aiki a jikinta,sai wajen asuba ya dagata ya rungumeta jikinsa kawai ya saki kukan farin ciki ya shiga Kai Mata kiss ta ko Ina.... Hannu yasa ya kunna dumm light yaga yadda hawaye ke gudu a idanuwanta yasa bakinsa Yana lashewa hannunwansa na yawo a jikinta..... Kacokan ya dauketa yayi toilet da ita Nan da Nan ya hada musu ruwa Mai zafi yayi Mata wanka ya gasa Mata jiki sosai sanan ya fito da ita ya kwantar yaja bargo ya rufeta...shima ya shiga yayi NASA wankan Da kanshi ya Ciro Mata doguwar jallabiya a drawer ya sa Mata sanan ya fita Yana Jin Kiran sallah a masallaci ya rufo Mata kofar.... Sakkowa tayi a hankali ta koma bayi tayo alwala tazo ta tada sallah,tanayi jiri na dibarta saboda rashin karfi a haka ta idar da sallar taja jiki ta Haye gado.... Misalin karfe shida ya shigo gidan direct dakin deejahmah ya nufa Yana tura kofar yaganta Tana bacci,..tsaki yayi sanan ya shiga tashinta da tayi sallah dakyar yasamu ta amsa Masa ya fita ya rufo Mata kofar.... Ganin hijabi jikinta Kuma gata a kwance ya bashi amsada tayi sallah sai kawai ya Haye gado ya janyota jikinsa ya rungumeta tsam Yana laluben bakinta Nan ya shiga tsotsar bakinta a haka bacci ya daukesa Mai dadin gaske... ******** Sai goma na safe deejahmah ta farka da sauri ta tunada batayi asuba ba Nan da Nan ta shiga bayi tayo alwala ta tada sallah sharp sharp gudun kada ya shigo.... Tana idarwa ta fada toilet ta tsala wanka ta fito ta Dade zaune Tana kwalliya sanan ta shirya tsaf da tsaddun material Dan India maroon Wanda yayi masifar amsar fatar jikinta.... Lekowa tayi taji shiru ko Ina a haka ta sakko daga sama kwass kwassss da takalminta har babban parlonnsu Nan taga Yar kararrawa ta Danna saiga bayin gidan dukkansu suna rige rigen shigowa dukkansu ko wacce ta zube... Kallonsu takeyi daya bayan daya tamkar bazata ce komiba cann ta nisa tace "Ina bukatar abun karyawa"... "Toh ranki ya dade"...suka hada baki suka fice a tare... Cikin minti biyar suka shiga shigowa da kayan breakfast kala kala wadanda aka turo wasu daga gidan sarki wasu a Nan sukayi shi....sukai serving dinta da kunun gyada da soyayyar doya da kwai tanaci tamkar Tana taunar magani... Karar fitowa yasata tsayawa da taunar da takeyi ta maida dubanta daga inda take jiyo sawun takalmin, Yarima ne yasha shadda baka da hularsa ja Mai shegen kyau gefensa Fatima ce da red less dinkin sket da Riga fuskarta Babu make up Amma hakan be hana kyawunta na usuli bayyana ba.... A tare suka shigo parlon inda Fatima ta zauna Nan shima ya zauna gefenta hannunsa rike da kwankwasonta... harararsa ta danyi "dik ka Hana mutum sukuni dik inda nabi kana manne Dani Nika cikani" Dan tsungulunta yayi ta zabura Tana fadin "mugunta ko mugunta ko Allah saina fadaka da ummu"yadda tayi maganar a shagwabe yasashi kafeta da idanuwansa Yana murmushi.. Kararrawa Fatima ta Danna saiga bayi sun Kara shigowa "Ina bukatar abinci Amma ba kalar wanan ba Dan ni banajin Shan kunun gyada,a dafomin ruwan zafi a soya min cheefs"...tace cike da Isa... Mikewa deejahmah tayi tana Shirin barin wajen yarima yayi saurin cewa "na cancanci gaisuwa Amma bansamuba deejahmah ko Mulkin ne ya motsa irin na yaran masarautar barayar Zaki?"yace cike da zolaya, Kayataccen murmushi tayi tai farr da idanuwanta "gaisuwarka ta musammance ranka ya dade a daki ya Dace asameka a gaisheka ba cikin mutane ba".... Tabe baki yarima yayi ya dage kafadarsa "yadda kikaga ya Dace"....ta juya abinta Tana juya kwankwasonta... ******** Cikin kwana biyu soyayya Mai karfi hade da shakuwa ce ta Kara shiga tsakaninta da yarima wadda takejinta a sabuwar duniyar da Bata taba tunanin zata tsinci kanta ciki ba.... Tunda safe sarki ya Aiko neman yarima ya fita Dan Kiran nasa Dan haka Koda Fatima ta shirya sai Bata nemeshi ba tayi fitowarta Dan ta Sha iska... Sallama tayi a parlorn ganin deejahmah zaune Rahane baiwarta da aka kawota Tana famar matsa Mata kafa hannunta dauke da waya Tana chat... Harara ta watsawa Fatima hade da sakin tsaki tace "nibansan dalilin dayasa kike son ki rinka shiga gonata ba bayan kinsan danida ke din ba saanin juna bane babu Hadi hanyar jirgi daban ta mota da ban sai shegen naci da maita yarinya sai kace kaska".. Mikewa Fatima tayi daga inda take ta Tako har gaban deejahmah ta tsaya fuskarta dauke da murmushi "nidake tabbas ba saanin juna bane Domin akwai banbanci tsakanin uwar gida da amarya,sanan akwai banbanci a tsakanin sarauniyar asali da wadda take amsa sunan sarauniya Amma Bata cancaci a kirata sarauniyar sarki ba saidai a kirata da matar sarki Kinga kuwa akwai banbanci,naji Dadi da kika sanar Dani cewa indaina zubar da girmana wajen gaisheda kanwata,saidai hakan bazai yuwu bane saboda kasancewar ni din Mai ilimin addini ce nasan muhimmancin sallama ko a musulunce"...ta juya Tana takawa dai dai deejahmah na Kare Mata kallo, "Samun ilimin addini a gidan marayu bai amfana Miki komiba tunda garin karuwanci kikayi sanadiyyar Rai Wanda ya rataya a wuyanki,sanan ke har kinada wani tunkaho da kikedashi bayan kinsan asalinki?kin manta cewar tsintarki akayi aka Mika ki gidan marayu?kin manta cewa itayayenki wofintar dake sukayi gwamnati ta tsunceki tayi Miki suturar daurawa?....gaskiya bakida Hadi Dani da akayi cikina a sunnah aka haifeni akaimun hakika"...ta kece da dariya Tana karkada kafa Tana bin Fatima da kallon wulakanci .... Ba karamin zafi kalaman deejahmah sukaiwa Fatima ba wadanda sukasa fararen idanuwanta suka canja kala Nan da Nan zuwa naauin ja wata Yar kwalla ta taru a Ramin idanuwanta, "Dikda kasancewata tsintacciyar mage shegiya wadda aka tsinta a gidan marayu hakan be hanani Zama cikakkiyar yarinya Mai tarbiyya da sanin ya kamata ba....hakan yasa mijina yake alfahari Dani a ko Ina sanan kisani nidin ba shegiya bace Sunnah ce ta haifeni" "Idan Sunnah ce ta haifeni Fatima inada bukatar ganin uwa da ubanki sai in tabbatar" A fusace yarima ya shigo parlorm Yana Mai daka tsawa "ya Isa haka Khadija,...dik naji abubuwan da kike fada kedin da kikeda iyayen wace tarbiyyace suka baki ita wadda Zaki fito da ita kiyi alfahari da ita a idon duniya?inace ibadah ma wanan Bata Gama cika a wajenki ba ballantana sanin darajar Dan Adam?karki kuskura insake Jin kin zagarmin Mata wallahi saina sassaba Miki" Hawayene suke gudu a idanuwan Fatima kirjinta na tafarfasa tamkar ta fasa ihu haka takeji cakkk take tsaye ko motsin kirki batayi....yau kwananta shida a gidan miji tun kafin aje ko Ina anfara goranta Mata maganar iyaye?yanzun inda yara gareta fa akeyi Mata wanan gorin?harda yaranta zaa hada kenan....rungumota yayi jikinsa Yana shafa bayanta a hankali..... deejah wadda ke zaune tamkar mutum mutumi ta Mike tayi sama a guje Tana fadin "wallahi bazan yarda ba bazan taba yarda ku hada Kai da matarka ku wulakantani ba".....ta shige dakinta ta bugo kofa... Daukar Fatima yayi tamkar baby ya nufi bangarensa da ita can ya shige daki da ita ya rage rigar jikinsa ya ajiye sanan ya hauro saman gadon ya rungumeta Yana kallon fuskarta wadda har yanzun akwai sauran hawaye a makale... Hannu yasa ya share hawayenta yace "banason kina Kuka a gabanta don anyi Miki gorin iyaye kinji?kidaina kuka ki cire zuciyarki Akan hakan dan kisamu farin ciki dawamamme"... Sababbin hawayene suka gangaro a fuskarta tasa gefen hannunta ta share sanan ta langabar da kanta a kirjinsa Tana sauke a jiyar zuciya....hannunsa ya tura cikin kirjinta ta dago Kai Tana harararsa ya kashe Mata ido "abuna ne fa abarni inyi yadda nakeso ".. Ta Dan turo baki "ni gaskiya zafi sukemun fa kabari "..tace a shagwabe.... Dariya ya kamayi yasa kansa a gefen wuyanta Yana lasar wuyanta da harshensa ya shigayi Mata wasanni masu zafi wadanda yasa Nan da Nan tafara sauke numfashi...ganin haka ya dago kansa ya Dora bakinsa a nata ya shiga aika Mata da hot kiss hannunsa yasa a bayan rigarta ya zuge zip din rigarta Nan da Nan ta bashi hadin Kai suka shiga farantawa juna.. Sanye take da alkyabba tayo hanyar sashensa a fusace ta nufi kofar Taji saukar numfashinsu....cakkkk ta tsaya Tana Mai Kara sauraren abinda takeji....Nan da Nan idanuwanta suka kawo ruwa ta juya hawaye nabin kuncinta ta nufi sama jiki a sanyaye ta shige dakinta ta kwabe alkyabbar ta fada gado ta saki kuka Mai karfin gaske Tana juyi....lallai ma yarima..tsabar jaraba har da Rana ya hayeta yanayi Mata soyayya ita kuwa ko dakinta ya shigo saidai ya nemi gefen gado ya tsaya ko arzikin Hawa gadonta ya zauna beta samu ballantana abinda ya shafi soyayya...kuka sosai takeyi Mai ban tausayi Wanda takai awa biyu Tana yinsa sanan ta nemi tsakiyar gado ta zauna..... ******** Saida yasamu natsuwa sosai sanan ya shiga bayi ya watsa ruwa ya fito ya rufo kofar yabar Fatima ciki Tana wanka... Karfe hudu da kwata ya shigo dakin deejahmah Tana zaune ta rafka tagumi fuskarta ta kumbura saboda kuka,...kallo daya yayi Mata ya kauda kansa ganin yanayinta dikda ta bashi tausayi Amma be hanasa daure fuska Akan abinda tayiwa Fatima ba, "Ke kinci abinci?"...ji wata tambayar rainin wayau da yayi Mata tun karfe suke daki be fitoba sai yanzun Yana tambayarta kotaci wani Abu, Haushi ne ya lullubeta yasa kwalla cikowa idanuwanta ta girgiza Masa Kai kawai...kwallar da take boyewa ta sulalo a idanuwanta masu zafi ta dago Kai da niyyar Gaya Masa magana yadda taga fuskarsa yasata saurin sunkuyar dakai Tana sharar hawaye... Tausayinta ne ya kamasa jikinsa yayi sanyi,jiki Babu kwari ya karaso har inda take ya hayo saman gadon ya dago fuskarta sai kawai ta fashe da kuka.....da sauri ya rukota "ya Isa haka yi shiru ki fadamin abinda kedamunki kinji deejah"..yadda yayi maganar cike da lallashi yasata kwantar da kanta jikinsa Tana shasshekar kuka "haba Yaya yarima bansan menayi maka ba ni ka tsaneni ko shigowa dakin Nan kayi baka Zama kake ficewarka baka damu da lamarinaba yanzun Kuma a gaban kuyangata Rahane ka dizgani ka wulakantani Akan Fatima"... Jikinsa ne ya karayin sanyi ya shiga shafa kanta"ya Isa nabari Amma kema kidaina wulakantamin Mata deejah matukar bazaki Bari ba to tabbas bazan daina saba Miki ba Dan itama bazan Bari ta wulakantamin Yar uwaba kinji" Haushi maganarsa ta Bata Amma ba yadda ta iya batace masa komiba ta janye jikinta daga nashi ta share hawayenta ta shige toilet...kallo ya bita dashi Yana kada Kai kawai.... Koda ta fito Bata sameshi ba hakan be Bata mamaki ba Dan tasan dama yagadama ne ma ya zauna yanayi Mata lallashin karya bayan ya Gama sauke numfashi wajen wata, Murmushin takaici tayi hade da mugunta ta sauke numfashi "daga gobe kinyi bankwana dashi Yar matsiyata saina tabbatar da na juya masa hankali zuwa gareni...ya Gama shaawarki daga gobe kedashi saidai kallo badai kwanciya ba"...zuciyarta na cigaba da yi Mata tukuki ********** Rass ya ya tadda Fatima tayi shirinta tsaf har tayi wanka,shiga yayi da sallama Yana fadin "baby har kin tashi?".. Juya Masa Kai kawai tayi hade da zumburo baki gaba "Ina kaje?wato tafiya ma kayi wajen matarka kabarni wankan daka savamin ma yau bansamuba kanacan kana lallashi?" Wani kishi ne ya taso Mata Nan da Nan idonta ya kawo ruwa,...jikinsa na rawa ya zauna gefenta ya ruko kuguntd "yi hakuri nayi laifi yanzun tashi muje a sake wanka"...makale kafada tayi ta Kara juya Masa baya Da karfinsa ya rungumota ta fada jikinsa ya matseta tsammm Yana kallon kwayar idanuwanta da yake hango kishi karara..."baby kiyi hakuri kinsan dai hakkina ne insan taci ko bataci ba shine naje na tambayeta ko taci wani Abu" Ta kwantar da kanta jikinsa kawai taji wani irin kamshi da sauri ta turesa ta Mike tsaye tana dire dire "ni bazan yarda ba zuwa kayi ka rungumeta kayi Mata irin abinda kakemun"ta fashe da kukan shagwaba, Dariya ya shigayi ya Mike ya dauketa cakk yayi waje da ita Koda suka fito kicibis sukayi da deejahmah tayi wankan yamma tsoron Allah ne ya kamata ganin da tayi musu hannunsa daya yanayi Mata cakulkuli Tana shura kafafuwa Tana dariya shima dariyar yakeyi suka gifta ta gefenta sukai sama....tabisu da kallo... ********* "Fauziyya gobe nakeso ayi aikin Nan fa?zakije kuwa ?" "Zanje Mana innah karki damu komi zai tafi yadda kikeso" Murmushi innah tayi "dakyau" ********* Daddare suna kwance shida Fatima Tana rungume jikinsa kanta a kafadarsa ta yatsina fuska tace cike da shagwabarta data Saba "habeeby inaso kayimun wani Abu guda daya Wanda dagashi idan kayimun har abada ka gamamin komi" Maida hankalinsa yayi sosai gareta ya gyara Mata kwanciya jikinsa yace "kome kikeso ki fadeshi kanki tsaye bakida wani hijabi tsakaninki da mijinki kinji?wa kikedashi Wanda ya fini?umm? fadamin?ya Kara matseta a jikinsa, A sanyaye tace"so nakeyi ka bani hadin Kai wajen neman iyayena,inaso insan kosu din suwaye,inaso in tabbatar da niba shegiya bace,idan ma ni shegiyace inaso insamu labarin yadda akayi nazo gidan marayu"...tai kwalkwal tamkar zatayi kuka, Ajiyar zuciya ya sauke "nayi Miki alkawarin baki gudun mawa wajen binciken iyayenki a din lokacinda kika shirya" A shagwabe tace "ni ko yanzun ma na shirya"....ya lakuce hancinta "to rigimatu kibari gobe zan bincika inji?".. "Ni ah ah muje tare gidan marayu muyi bincike inaso inje dama".... Ya dade Yana nazarin fuskarta wadda ke dauke da tsananin damuwa yasan cewa gorin da akai Mata ne yasa dik ta shiga damuwar Nan....ita kuwa kafesa tayi da Ido Tana jiran amsarsa,...iska ya hura Mata a idanuwanta ta lumshesu Tana murmushin karfin Hali... "Dik yadda kikace haka zaayi yanzun dai nidai nidai" Dariya ta kyalkyale dashi Tana turesa "Kai baka gajiya ne?umm?' Ya kashe Mata ido yasa fuskarsa daidai Tata Yana kallonta,hannunsa daya yasa ya kawar da gashin daya rufe Mata Rabin fuska Yana Kare ma fuskarta kallo sai kawai taji saukar bakinsa Akan nata ya shiga sarrafashi tamkar sweet... ******** Da wurauri Fatima ta tashi ta kimtsa sanan ta tashesa,bacci be ishesaba haka ya juya yana murza Ido Yana kallon yadda ta dauki kwalliya tamkar wata zinariya ya mance da maganar fitarsu yana Shirin gyara kwanciya tace "Haba habeeb katashi Kar muyi latti " Dago Kai yayi cikin rashin fahimta yace "Ina" "Gidan marayu Mana"ta shagwabe fuska .... *Muje zuwa* *SLIMZY😍*🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* _Sakon gaisuwa da fatan alheri gareku mutanen_ *KUNDIN HASKE* , _uoum sadeek,hussy luv, hauwa isah ibrahim,bawa subee,fulani ummu Ahmad,asmaul husnan mom,Maryam sabiu....._ *da dik Wanda ban Kira sunansuba Kuna raina* _Mutanen gidan uwata Kuma ban manta daku ba_ *TASKAR BILLY GALADANCI*.. _Hindu,teemah imran,maman_ _ameena,Fatima Hassan,mama faruk,...babbar_ _antyna_ *meenath kt*, _Nana Khadija,da'iman,shamsiyya_ _bilyaminu_ ......🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀ *bazaku fadu dukaba dik Wanda beji sunansa ba register batazo kansaba Amma Ina mishi sonso😍* 41 Mikewa zaune yayi Yana mutsittsika Ido sanan ya dire daga hannunsa sama ya kashe murya "ni a daukeni nima ayimun wankan"yadda yayi maganar tamkar karamin yaro ba karamin dariya ya Bata ba....dariya ta shiga shekawa Tana nunasa da yatsa yadda ya makale hannu da kafada, "Hebeeb ka ganka kuwa saikace jariri?tabdijan walleh ban iya daukarka" takara kwashewa dariya Tana tsalle, Mikewa yayi yayo kanta suka shiga zagaye dakin Yana biye da ita Tana gudu har tagaji ta fada Kan gado rigingine ya Haye kanta Yana maida numfashi....kallon fuskarta yakeyi yadda Tasha kwalliya tamkar ba itaba ya sumbaci lips dinta "babyna kinyi kyau kin ganki kuwa?" Dage Masa gira tayi "kamar?" "Kamar sarauniyar barayar Zaki".....wani kayataccen murmushi tayi itama tayi kissing dinsa a lips dinsa sanan tace "itace"... Kwantar da kansa yayi a kirjinta Yana sauke numfashi yanajin sautin bugun zuciyarta kussn mintuna hudu,...gajiya tayi tasa bakinta daidai kunnensa"ranka ya dade zamuyi latti fa"tasa hannunta Tana shafa sumar kansa Wanda yasashi lumshe idanuwa Yana budewa,a hankali ya shiga dagata har ya Mike tsaye Yana binta da mayen kallo Wanda yasata saurin mikewa Domin Sarai ta fahimci abinda yakeso Dan tagani a kwayar idonsa, Jallabiyar jikinsa ya cire ya nufi bathroom dinta,har ya kai kofa ya tsaya sanan ya juyo yace "jeki daukomin kayana a dakina" "Owk ranka ya dade".... Murmushi ta sauke ganin shigarsa bayi ta Mike da sauri ta bude kofa ta fice,ta rufo koferta.... Cike da nishadi take takunta harta karashe sauka kasa,...tasha mamakin ganin deejahmah zaune da kayan bacci a wanan lokacin da yake safiya Dan batai tunanin Tana tashi da wuri ba, Har ta wuce ta dawo "barka da tashi"...."barkanki dai uwar gida sarautar mata yaudai zakiyi ritire daga dakin Mai gida mannewar haka ta Isa da jaraba sai aba masu waje wuri".... "Gaskiya na tayaki murna kasancewar Zaki dandana niimar dana da'ndaneta na rage....ba haka Rai yaso ba kanin miji yafi miji kyau"ta saki wani malalacin murmushi tai wucewarta side dinsa zuciyarta fesss cike da nishadi haka ta fito hannunta rike da kayansa har Zata wuce deejahmah ta dakatar da ita da fadin "idan kin shiga kicewa mijina inada bukatar ganinsa" Murmushi Fatima ta sauke "karki damu zan fada Masa Amma saidai bazaki samu ganinsa yanzun ba Domin wanka yakeyi sai ya shirya matarsa Zata sanar Masada amaryarta nason ganin Mai gida".... "Karya kikeyi baki isaba wallahi a dik lokacinda naso ganin mijina zan ganshi ba sai kinbasa umarni ba" Dage kafadarta Fatima tayi hade dayi Mata gwalo tayi sama a guje Tana dariya..... Ta tura kofar a hankali bakinta dauke da sallama Yana tsaye Yana goge jikinsa "mekika tsaya yi?naji kamrr hayaniya a kasa" Farrr tayi da idanuwanta sanan tace "wayyoo Ina magana da su zaituna ne Akan bazamu samu damar yin breakfast ba sai mun dawo"... "Ok"kawai yace ya cigaba da shiryawa ita ta taimaka Masa ya shirya tsaf.... Ta zura alkyabbarta ta Kara feshe jekinta da turaruka masu sanyin kamshi.... Sanan suka fito a tare daka kallesu Dole ka Kara kallonsu saboda tsabar kyawu da daukan hankali da sukayi... Kallo deejahmah ta bisu dashi baki galala....dakyar ta hadiye miyon bakin ciki tace "barka da tashi ranka ya dade" "Barkanki da tashi deejah,Yaya kika kwana?" "Lafiya"kawai tace a takaice ta juyar da Kai.... "Naga yau kin tashi da wuri" "Umm"shine abinda tace still Tana kallon tv .... Rahane da zaituna suna zaune a kasan carpet fatima tai gyaran murya "ammm zaituna kije sama ki gyaramin dakuna na inada bukatar a caccajamin zannuwan gado sanan ki shiga kitchen ki fada musu burabusko da miyar kwai sa farfesun kifi danye mukeda bukata idan mun dawo dan fita zamuyi" "Angama ranki ya dade"....Jin abinda Fatima tace yasa deejahmah saurin juyowa Tana binsu da kallo cikin karfin Hali ta bude baki tace"matarka Bata fada maka inason ganinka bane naji zaka fita" "Laaa kaga habeeb na mance amarya ta murda kambunta nason ganin mijinta"tai maganar Tana dariya Dariya yarima yayi "to deejah ya akayi kinada bukatar wani Abu ne?" Ganin Fatima ta kalli agogo yasa deejahmah mikewa cike da yanga da Isa Tana Taku dai dai "inason ganawa da mijina Amma a dakina" Tai gaba abinta,...ya dauki seconds kafin ya dubi Fatima a gaggauce yace "ina zuwa"....ta kaicine ya lullube Fatima ganin lokaci na tafiya sai batace komiba ta gyada Masa Kai.... ******* A gefen gado ya sameta zaune Yana shigowa cikin gaggawa yace "gani mekikeda bukata?mekikeso kice" Kawai sai deejahmah ta shiga rera kukan kissa hawaye na gudu a idanuwanta ta shiga fadin "ni yanzun banida yancin da zantashi bacci mijina ya shigo dakina yaji ko inada damuwa?banida yancin da kwanciya bacci mijina zai shigo yayimin sallama Saida safe?banida yancin da darana mijina zai zauna a dakina yabani lokacinsa ya kula Dani Koda na minti talatin ne?dik banidashi yayah?saboda ni din ba matar so bace?Koko bakasona ne aka daura makani Dole zaka kula Dani ka duba lamarina....niba kanwarka bace?ko wani yayimun haka a gidan mijina nadauka Kai Mai zuwa ka amsarmin yancina ne sai gashi da kanka kakemun haka?...yanzun banida hakkin da zaa fadamin zaa fita saidai kawai inganku?ko ka manta inada hakki akanka ne?"....ta karashe maganar da rushewa say kuka Mai karfi.... Sandarewa yarima yayi a tsaye saboda yadda maganganunta Suma shiga jikinsa....tabbas maganganunta dik gaskiya ce Babu karya tabbas be kyauta Mata ba, Dakyar ya motsa jikinsa ya karaso gabanta ya dagota zuwa jikinsa ya rungumeta tsammm....shafa Mata jiki kawai yakeyi zuwa gashin kanta Wanda hakan ya Bata damar manna Masa albarkatun kirjinta Wanda take yaji wani Abu nayi Masa yawo a jiki Jamar Ta'na....ya shiga rada Mata a kunne "kiyi hakuri kinji nadaina insha Allahu zan rinka kulawa dake Kuma Ina sonki kema kinji".. Ta dago kanta Tana manne a jikinsa yasa hannu ya shiga share Mata hawaye "ya Isa kinji?nabari banason kukanki" Dora kanta tayi a kafadarsa "Amma kasan nice keda Kai koh?ta shagwabe murya, "Yi hakuri nasani ai zamu dawo da wuri yau Ina tare dake ko"...yadda yaji Tana sakin ajiyar zuciya tausayinta ya Kara kamashi ya dagata cakkk Yana juyata a daki kawai saigata Tana dariya sanan ya direta kasa ya ja hancinta "zamuje saimun dawo ko?" "Ka kukamin da kanka"tace idonta kirrr Akan nasa fuskarta dauke da murmushi,shima murmushin ya mayar Mata sanan ya fita a gaggauce ta bishi a baya, Fatima na tsaye babu abinda zuciyarta keyi sai tafarfasa bakin ciki ya lullubeta tamkar ta fasa ihu ta sani sarai deejahmah tayi hakan ne don ta tozarta ta ta Bata Mata Rai ta Kuma Bata tayi nasara saidai ta tsokalowa kanta tsuliyar dodi inhar wanan wasan ne Bismillah.... Shigowarsu parlon ya Bata damar kirkiro faraa ta Dora a saman fuskarta "har Kun Gama?amarya saida lallashi dama muje koh?" Kallo yabi Fatima dashi Dan ya hango tsantsar kishi da bacin Rai a fuskarta dauriyace kawai da jarumta irin Tata... Tsabar mugunta yasa deejahmah sakin Yar dariya kasa kasa ta Haye kujera ta Dora kafarta daya Kan daya. Ficewa sukayi ko kafin su fita dama Fatima ta aika a shirts motoci haka kuwa akayi da Yan rakiyarsu dasu kansu motoci uku suka dauka.... Tunda suka shiga motar yake kokarin aika mata da sakwannin soyayya Amma ko kallon inda yake batayiba savida takaicinsa daya lullubeta data kalleshi sai Taji haushinsa ya kamata ya gamo soyayya da lallashi da rungume wata yazo zai Mata barazana...ta kauda kanta gefe ganin haka ya sashi tabe bakinsa ya maida nasa Kan gefe batare da yace komiba...... Tafiyar minti arbain ta daukesu zuwa gidan marayu,....karya kwanar da zata sadasu da gate din shiga gidan driver yayi take Fatima hankalinta yayi mummunan tashi tunda tai tozali da wanan gate din,abubuwa da dama suka shiga dawo Mata da yawo a cikin kwakwakwar kanta..... Koda suka shiga ciki runtse idanuwanta tayi ganin yadda yara ke famar fitowa daga wajen karbar abincin safe dayawa daga cikinsu kafafuwansu Babu takalmi wasu suturar jikinsu dik a yage wasu Kuma tsabar dattin da sukayi ko miyau bazaka iya hadiyewa ba idan ka kallesu.... Ganin motoci sunyi parking yayi matukar daukar hankalin yaran inda dayawansu Sukai wajen motocin wasu Kuma suka tsaitsaya suna kallonsu, Bangarenta diriver ya bude Mata mota ta sako kafafuwanta ta Dade ciki kafin ta fito gabaki daya wata Yar karamar yarinya ce da bazata wuce shekara biyar ba ta shiga ihu tana murna Tana fadin "yeeehhh ankawo taimako yau zamuci shinkafa".....sai duka yaran wajen suka dauki ihu da sowa na murna Tsaye tayi Tana kallonsu yadda suke murna suna farin ciki Wanda ita ma a lokacin baya Bata wuce yin hakan ba Domin da zarar aka zo dubasu ji suke tamkar ansasu a aljannah.... Kwallace ta taro a cikin idanuwanta ta mikawa wannan yarinyar hannu alamar tazo Aiko a guje tayo wajenta Tana fadin "Kun kawo Mana abinci ne?harda shinkafa?....tuwo aketayi Mana kullum kullum"...Yar ta canja fuska tamkar zatayi kuka, Fatima ta share hawayen daya gangaro Mata batare da yarinyar tagani ba,ta shafa kanta "insha allahu yau zamuci shinkafa kinji?" Sai kawai ta saki hannun Fatima tai cikin yara tana murna duka yaran suka shiga murna suna shigewa bangarensu a guje, Ta dau Yan mintuna Tana sharar hawaye abubuwa da dama na dawo Mata na Baya....tabbas rashin iyaye da gata babban gibi ne a rayuwa dik ranan daka rasa iyayenka idan kanada damaryin kuka kayi Domin dik maraya Yana tare da wani ciwo a cikin zuciyarsa Wanda me iyaye bazai taba fahintar wanan ciwon ba....😭(ya ilahi Allah ka jikan iyayenmu).... Kallonta yarima yake hannuwansa rungume a kirjinsa,shi kansa ganin yanayinta ya sashi karajin tausayin nata Domin dik Wanda ya kalli fuskar Fatima a wanan lokacin sai ya zubda hawaye... Tana tsaye tamkar an dasata,batasan yazo bayanta ba sai Jin sautin raunanniyar muryarsa tayi "haba ranki ya dade yanzun kin tashi daga marainiya fa kin koma uwar marayu,be Dace uwar marayu ta tsaya gaban yatanta Tana zubar da hawaye ba" Hannu tasa ta share kwallar data zubo Mata Tana kallonsa lokaci daya "Ina tayasu jimamin abinda sukeji ne Domin dagajin kalaman yarinyar Nan kasan cewa basa samun cikakkiyar kulawa daga wajen gwamnati sai lokacinda Allah yasa suka tuna dasu sanan su kawo musu dauki,...bana manta lokacinda mukai yunwa a makarantar Nan harta da ruwan Sha bamu dashi abincin da zamuci babu Saida mukai kwana uku Babu ci Babu Sha Wanda sanadiyyar hakan dayawa daga cikinmu sukaita ciwo suna rasa rayukansu saboda yunwa da kishin ruwa.....masu kudi suna mancewa da taimakon marayu ko fidda dukiyarsu sukayi saidai su nemi me karfi su Kara mishi karfi ga inda ya kamata su kawo dauki su ciyar da maraya Domin su samu babban rabo ranan gobe kiyama Amma sun manta da hakan" Shi kansa yarima Saida yaji hawaye na Shirin zubo Masa ganin yadda Fatima ta rikice,Amma gudun Kar ya Kara karya Mata zuciya yasashi ruko hannunta batare da yace komiba suka nufi record office na gidan... ******* Bincike sosai akeyi a cikin record office baaga file din Fatima ba,Wanda ya Kara sata cikin mummunan tashin hankali dik ta fada damuwa ta furgice, Sai manager na wajen ya shiga cikin store din wajen inda tsofaffin files suke da wadanda suka gudu baagansuba Nan ya shiga ya Soma duddubawa,ya dauki lokaci kafin ya fito wajen zufa dik ta Gama wanke Masa fuska ga kura da jikinsa yayi, Kakkabe file din yayi sanan ya Ciro medical glass dinsa dake makale a aljihun gaban rigarsa ya Sanya ya bude ciki ya shiga karantawa Yana girgiza Kai....ya dau lokaci kafin ya dago kansa ya maida hankalinsa garesu, "Toh a bisa alamu da bincike da abinda file dinki ke kunshe dashi na record dinki Wanda ya kawoki gidan Nan namijine Kuma babban mutum Domin ko a lokacin shekararsa hamsin da takwas ke kuma an kawoki gidan Nan ne a shekara hudu da watanni" Kallon juna sukai da yarima a tare ko wanne gabansa na tsananin faduwa, A hargitse Fatima tace"shekara hudu da Yan Kai?....Kuma namiji ne ya kawoni gidan Nan?" Jijiina Mata Kai maaikacin yayi "Kenan hakan na nufin tsuntata yayi kenan?" "Bazan iya saniba Domin nidin sabon maaikaci nee wajen Nan wanan tambayar Taki amsarta Naga tsohon maaikacin gidan Nan Wanda shine yasa hannu aka karbeki ga sunansa a kasa MALAK SANI SULEMAN...ni bazan San wani abuba dangane dake Domin dik Wanda ya kawo yaro sai ya fadi dalilinsa na kqwosa din kodai tsintarsa yayi ko Kuma iyayensa sun mutu Babu Wanda zai iya rikesa ko Kuma baasan danginsa baz Bude takaddar kasan file din yayi ya Ciro wani hoto na Yar yarinya Mai tsananin Kama da Fatima sak ya Mika Mata Kallon hoton takeyi Tana jinjina Kai tabbas wanan itace lokacin Tana Yar shekara hudu to,...kallon hoton takeyi daga sama har kasa suturar dake jikinta masu kyau ne Domin blous ne na yara kanta sanye da hular blous din Tana dariya akai Mata hoton....yarima dake gefenta ya karbi hoton Yana dubawa shima mamakin ganin suturar dake jikinta yakeyi kuma aka kawota gidan marayu? Gauron numfashi yarima ya sauke "yanzun sir ya zamuyi muga wanan tsohon maaikacin na gidan Nan?".. "Tabdijan ni bansanshi ba da dai akwai wani tsohon maaikacin ne a gidan kila zai iya saninsa" Jinjina Kai yarima yayi "owk badamuwa zan bincika insha allahu mungode" Ya kamo hannun Fatima ta mikar da ita "muje koh?" Jiki Babu kwari ta mikawa manager wanan hoton ya maida cikin file din sanan ya ajiyesa a gefe sukai Masa sallama hade da bashi sakon cewa zasuyi aike na kayan abinci abqwa marayu... Dakyar Fatima ke take kafarta suka fito excort dinsu suka rufa musu baya har mota... ********* Fauziyya ke rike da hannun deejahmah suna tattaunawa "yanzun kenan tun safe suka fita gashi yanzun sun Kai karfe uku Basu shigo gidan ba kamata yayi muyi aikin da zamuyi kafin su dawo koya kikace?Dan ni na Matsu da Inga karshenta" Khausar wadda ke gefensu itama tazo ba dadewa fauziyya tazo tace "ai hajiya tace wanan auren Babu inda zaije sanan sabon maganin Nan Dana kawo Miki matukar kikai amfani dashi an wuce wajen" Dadine ya lullube deejahmah "ai ya Gama Mata kwanakinta daga jiya Kuma Ina Mai ji a jikina tayi bankwana dashi" "Yanzun dai wannan abun a dakinta zaasashi a tabbatar ta diga ko yayane q dakin kwanansu to tabbas bazai taba iya Zama cikin dakinta ba ko ya shiga zaiji tamkar Ana Hura Masa wuta a jikinsa zai tsani dakin,...ita kanta da take cikin dakin kwana uku kacal zaiji tsanarta..." Tafawa sukai dykkansu suka Mike a tare suka nufi sama bangaren Fatima... ******** Tunda suka shigo motar da nufin dawowa gida Fatima ta kasa ce Masa komi saidai kwantar da kanta da tayi a kafadarsa minti minti takan ja numfashinta ta sauke Babu abinda keyi Mata yawo a kwayar idanuwanta sai wanan hoton nata Tana yarinya da kalaman mutumin Nan na cewa "tun kina Yar shekara hudu da watanni aka kawoki gidan marayu kuma Wanda ya kawokin namiji ne"...da wanan farucin yazo Mata kunne gabanta sai ya yanke ya fadi tunaninta dik ya tafi ne a yadda zata gano bakin zaren?.....shin ta Ina zata fara?ya zaayi ta gano itadin ko wacece? Muryar mijinta ta jiyo Yana fadin "idan har samun tsofaffin maaikata a gidan Nan shi zai bamu damar sanin iyayenki to tabbas zamu ganosu" Dago kanta tayi ta kallesa fuskarta cike da damuwa tace"yaayah ta Yaya?zaka taimakamin?ka taimakeni Dan Allah kayimun wanan gatan"tai maganar a raunane "Zan taimaka Miki Fatima harabada Babu abinda Zaki nema ki rasa a wajena akwai wani da nasani da dadewa nida Ahmad zan binciki Ahmad din ko yasan inda yake shi maaikaci ne a gidan marayu munsaba dashi tun bamukai hakanba muna zuwa Kai taimako gidan marayu shike taimaka Mana to nasan bazai rasa sanin malam sani SULEMAN din ba,zan bincika inji saimuje indayaken koh?" Ta jinjina Masa Kai Tana murmushin karfin Hali Wanda iyakarsa fuskarta bai Kai zuciyarta ba,....ji takeyi tamkar ta bude Ido taga iyayenta.... Maimakon taga sun karya hanyar gidansu sai taga driver ya juya Kan mota zuwa hanyar masarauta.... *Muje zuwa* *SLIMZY😍*🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* 42 Tsayawar motocinsu yayi daidai da fitowar bilkisu da niyyar zuwa bayan gida hannunta dauke da mopper ganin motoci sababbi yasata tsayawa kallon motocin cike da kosawa da bukatar ganin kosu waye.... Murmushi Fatima ta sauke ganin Yar uwar Tata tsaye tana kallon motocin tamkar Yar kauye ta juyo ta kalli yarima shima murmushin yakeyi ya daga Mata gira sama "Ali yaga Ali ko?" Jinjina Masa Kai tayi tana mai maida dubanta ga bilkisu wadda har yanzun tana tsaye motocin take kallo sanan ta juyoga yarima ta ruko hannuwansa "Lokaci nake jira a yanta Yar uwata daga kangin bauta," "Kefa kin fiye rigima tayaya hakan zai kasance?bayan kinsan baiwar hajiya babba ce" "Bedameniba inhar baa yantata ba zansa a daukemun ita Nan gaba kadan" Lakuce Mata hanci yayi "rigimarki yawace da ita yanzun mubar wanan maganar" Ta Bata fuska Tana kallonsa "to zan roki Mai martaba da ya nemamin alfarmar a bani ita a matsayin baiwata idan yaso a dawowa da hajiya bayi guda biyu Nan" Bata Rai yayi "nibanason rigima bintu Kinga kibar wannan maganar ba yanzun ba" "Shikenan tunda haka ka zaba ganin Yar uwata a kangin bauta ni Kuma Ina ya'ntacciya tunda ka rigada ka mallakeni Dole kace hakan"..ta bude mota ta fito Bata jira cewarsa ba bayin dake zagaye da motocinsu suka rufa Mata baya, Zubewa bilkisu tayi fuskarta dauke da faraa "Allah ya taimaki sarauniya Fatima....barka da zuwa' Dagota Fatima tayi cikin kasa da murya tace "harabada Yar uwata bazata taba durkusaminba,kiris nake jira in daukeki daga kangin bauta"Tana fadin haka tai wucewarta sauran kuyangin suka Mara Mata baya, Shiko yarima dage kafadunsa yayi yai hanyar fadar sarki tunda yaga cikin gida tayi..... ******** Sashen mama karama ta nufa Tana tafe Tana takama dik inda ta gifta maaikatan gidan na zubewa suna kawo gaisuwa Bakinta dauke da sallama ta shiga parlorn hajiya karama a nan ta tararda ummu zaune da afnan suna zaune sun idar da sallahr laasar "Lale marhabun da zuwan diyata daya tamkar da dubu yanzun nake cewa kewarki ta isheni mijinku yaki kawoku ki gaida Mai martaba yanata fada" Kunyace ta lullube Fatima ta zube a kasa a gaban ummu hade da kamo hannayenta "Ina kewarki uwa ta gari na durkusa a gabanki Ina me neman afuwarki na rashin ganina da bakiyiba" Jinjina Kai ummu takeyi cike da farin ciki "ai idan kaji danka shiru a gidan miji to lafiyar kenan karki damu a dik inda kike inayi Miki addua" Gyada Kai Fatima tayi sanan ta juya gaban hajiya karama wadda tunda Fatima ta shigo take binta da kallon shaawa fuskarta dauke da murmushi Tana gyada Kai.....kwana bakwai kacal yarinya ta canja ta Zama tamkar balarabiya ga wani kyau da tayi sanan babban abinda ya karawa fuskarta kyau shine ladanin sallah dake manne a saman goshinta Dan karami yayi bakin Kirin dashi, "Allah yaja da ranki ya kareki ya Kara daukaka barka da warhaka ranki ya dade" Daga Mata hannu hajiya karama tayi "barka dai Fatima ya gida?ya abokiyar zaman naki?" "Lafiya Lau tace a gaisheku itama zatazo ko zamuzo tare " "Masha Allahu,kinje kin gaida hajiya babba ko?"...gaban Fatima ne ya fadi Dan shaff ta mance da wata hajiya babba Domin Bata ita takeyi ba "Yanzun zanje insha allahu" "Tashi kije ki gaidata".... Cike da ladabi Fatima ta Mike dukkansu suka bita da kallo suna Mai tausayawa rayuwarta ********** Hajiya babba na kishingide a jikin kilisarta Tana kada kafafuwa gefe da gefenta dik kuyanginta ne zaune sun gurfana a gabanta, "Nakejin kamar hayaniya cikin gidan Nan koh?sautin gaishe gaishe nakeji a waje" Dada gurfanawa mami tayi "sarauniya fatimace da yarima sukazo" Mikewa tayi zaune "tazo?shine Bata fara shigowa Nan ta gaisheniba sai taje sashin uwar mijinta kenan koh?niba uwarta bace" Shigowar Fatima ya dakatar da Mami da yin maganar datai niyyar yi,....kaff hirar da sukeyi Fatima ta sauraresu wannan ne ya Bata damar sakin Yar dariya.... Gaida Fatima suka shigayi daya bayan daya Tana tsaye kerere takai mintuna tsaye Tana karewa hajiya babba kallo yadda take cika Tana batsewa Tana faman hura hanci "Ku tashi ku ficemun da gani inason zantawa da uwata"...shine abinda Fatima tacewa kuyangin hajiya babba ciki kuwa harda bilkisu suka Mike Sumi Sumi suka fice, Gefen hajita ta zauna ta janyo plate din da takecin soyayyar gyada ta diba ta watsa a bakinta Tana taunawa Tana lumshe idanuwa yayinda hajiya babba kebinta da kallon mamaki "Waya baki damar samun hannu a cikin kwanon da nakecin abinci?bayan kin manta da kedin kazanta ce?" Saida Fatima ta hadiye abinda ke bakinta sanan ta dubi hajiya babba Tana watsa Mata kallon raini tace "ehh na dibi gyada na zuba a bakina ne na tauna saboda shaawar da naji gyadar ta bani Dan bansaniba ko shegiya Tana dauke da cikin jikanki ko jikarki shiyasa kada tazo da rowa.....Domin a kwana bakwai din Nan danki yayi jarumta wajen bani hakkina a matsayina na matarsa ta Sunnah ba karuwarsa ba" Wani zabura hajiya babba tayi tamkar zata kaiwa Fatima duka tace"keni nayi Kama da Saar wasanki ce da zakizo har dakina kiyimun rashin kunya?ki fadamun maganganu marasa Dadi Wanda ko saarkice ya Dace kiji kunyarta bawai ki fada Mata wadanan maganganun Kai tsaye ba" Yar shewa Fatima tayi "hajiya kenan,kin manta yayan karuwai basuda kunya?ko kin manta dik Dan da akace Dan kwararone to tabbas Zaki sameshi bashida kunya ko kadan a kwayar idonsa....ai bedace in Ari Hali na ya'yan Sunnah insawa kainaba Ina matsayin shegiya" Sakin baki hajiya babba tayi kawai tanabin Dan bakin Fatima da kallo yadda take zaro maganganu Tana watso Mata su, "Surukarki ce ta turo ki kiyimun rashin kunya ko uwar goyonki?wadda tagama zaman saudiyya ta dawo?Saida kikaje kuka Gama munafuncinku sanan kika kwaso kafa kikazo gaisheni koh?" "Surukata surukar arziki ce wadda tasan yakamata tasan darajar Dan Adam sanan ta daukaka addininta ta tsaida sallah sanan take nunawa na kasa da ita kauna Bata fifita kantaba Akan Wanda ke kasanta shiyasa Koda nace Mata banzo gaishekiba tabani umarnin Nan da Nan inzo ingaisheki shiyasa na shigo sanan inyi Miki godiya Akan bawa danki maganin karfin shaawa Wanda hakan ya bashi damar barje amarcinsa a wajen matar so ba matar da aka lika Masa doleba,....naso ace ita ya saukewa gajiyarsa kamar yadda kukaso sai reshe ya juye da mujiya" A gigice hajiya babba ta Mike zaune jikinta har rawa yakeyi Tana kokarin saukewa Fatima tafi a fuskarta da sauri Fatima ta guce "ai wata fuskar tafi gaban Mari,hajiya kayya fuskar sarauniya tafi karfin Mari a wajenki yanzun ,a da datake baiwarki kin mareta kin duketa yanzun lokaci ne na maida martani....." "Kinyi kadan kice zakizo in rinka hada numfashi dake yarinya,ban hada numfashi da manyan mutaneba cikakkun Yan asali saikece kadangaruwar bariki zan tsaya musayar miyau dake?yarinya kinyi ganganci Amma ki tabbatar Nan gaba kadan zaki rasa hankalin da zakizo kice zakimun rashin kunya ".. "Da Allah na dogara hajiya ban dogara da boka ko malam ba nazo inyi Miki bangajiya ne Akan Wasafa yayi kyau sosai yanzun aka fara bugashi,Ina fatan kin Kira diyar Taki kinji halin da take ciki?"ta kashewa hajiya babba idanuwa wadda gabaki daya take kallon komi tamkar a film ganin komi takeyi tamkar a mafarki.... Girgiza kafa takeyi Tana girgiza kai idanuwanta sun kankance cike da tsananin bacin Rai...ta bude baki zatayi magana yarima yayi sallama, "Barka da zuwa ranka ya dade,kajini shiru ko?hajiya ce ta rikeni da Hira wallahi" Kallon rashin yarda yake binta dashi take ta kashe Masa Ido daya sai kawai yayi murmushi ya gurfana a gaban hajiya babba "barka da yamma ranki ya dade"... Kallon kallo sukeyi da Fatima sanan ta kauda kanta kadan "barkadai"....murmushi dauke a fuskarsa yace "inbarki Nan ko?" "Dau matarka kutafi Domin ko ganinta banasonyi".... Bece kokiba ya Mike jiki a sanyaye cike da rashin Jin dadin abinda hajiya babba tace, Itakuwa Fatima ko a jikinta Koda yayi gaba tsayawa tayi kadan ta dubi hajiya yadda bakin ciki da tsananin takaici ya bayyana karara a fuskarta "hajiya bakida yadda zakiyi Dani Domin yanzun kika fara ganina yanzun kikafara rayuwa Dani Domin Ina Nan daram a cikin gidan Nan....rashin ganina yanada nasabane da ranan da dik kika wayi gari kikaga kin makance shine kawai Zaki daina ganina'...ta karashe maganar cike da tsiwa ta juya abinta Tana girgiza tai tafiyarta wani kululun bakin ciki da takaicine suka taru suka cunkushewa hajiya babba a zuciyarta.... ********** Babu yadda deejahmah batayiba da zaituna Akan ta bude Mata dakin Fatima ta shiga Amma fafir zaituna Taki yarda ta watsawa idanuwanta toka tace ita baa bar Mata makulliba,.. Takaicine ya lullubesu dukkansu suka shiga jibgar zaituna tamkar an aikosu deejahmah Tana haki take fadin "yau zakibar aiki a gidan Nan tunda kin nunamin cewa shegiya tafini mutunci da daraja a idanuwanki Bari Mai gidan ya dawo" Fauziyya ce tace "ko a harabar dakin shegiya mu watsa yadda da ya nufo dakinta zaiji takaici da bakin cikin da zai hanashi shiga" "Kin kawo shawara"cewar khausar, "Muna fuka bacemun daga gani"...Sumi Sumi zaituna ta juya zuciyarta cike da tausayin Fatima da alhinin abinda ake Shirin yi Mata.... ******** Ana kiraye kirayen sallahr magriba Fatima ta shigo a gajiye,ta baro yarima cikin mota daganan zai wuce masallaci, Da sallamarta ta shigo Amma deejahmah dake zaune dasu fauziyya Babu Wanda ya tanka mata,ganin faizah a tare dasu yasa Fatima cin birki Tana bin fauziyya wadda takewa faizah kallo, "Danki ya dade faizah abun naki ma yau Babu magana Yar shariya ce?" Yatsina fuska fauziyya tayi cike da takaici "kedai kikasani tun yaushe nazo kin fita da miji ance tun safe kuka fita Kuma ba girkinki bane" Mamakine ya lullube Fatima sai Bata kawo komiba tace"wayyoo ai girkin be fita a hannuna ba sai daddare tukunna zan shirya angon nawa yaje wajen amaryarsa fatana dai Kar yaje dakin amarya Yana baccin gajiya"ta kashewa deejahmah Ido wadda suka hada Ido lokaci daya hade da dariyar mugunta, "Faizah kisameni a sama zan rage kayan jikina"Tana fadin haka ta Haye benenta, Kallon juna sukayi dukkansu dake falon khausar ce wadda takaici ya Gama kasheta "tashi kije dama tasamu da zarar shegiyar ta shiga alwala kiyi yadda yadda Dace,idan yaso kice Mata haushi kikaji na jiranta da kikayi Bata dawoba yasa kikai Mata bakar magana" Rage murya fauziyya tayi cike da munafurci "Allah koh".. "Sauri sauri" Fatima a daki kuwa zaituna ta tutsiye Tana famar zazzaga Mata masifa "saboda kin rainani yasa nace ki canjamin zannuwan gado nadawo na tadda dakina yadda yake ko" Girgiza Kai zaituna tayi gabanta na tsananin faduwa tsoro da fargaba suka cikata lokaci daya taji Tana son Fatima tun ranan da aka ce tana daga cikin bayinta savoda haka Mai martaba a manar Fatima ya Basu bazataciba... Bakina rawa tace"ranki ya dade ba laifina bane nayi hakan ne Domin Kare lafiyarki da igiyar aurenki" Cikin Rashin fahimta Fatima ta watso Mata tambaya "banganeba" Nan zaituna ta kwashe komi abinda ya faru cike da tsoro ta fadawa Fatima,wadda tun kafin ta karasa tai mutuwar tsaye saidai ya zaayi ta gasgata zancen zaituna?Bata kai karshen tunaninta ba ta tsunkayi muryar zaituna Tana fadin "Ranki ya dade akwai abinda na fahinta guda daya shine Wanda shima ya kamata in fargar dake" "Umhmm Ina sauraronki" "Faizah da fauziyya Yan biyu ne yaran wazirine suna son suyi Miki Wasa da hankali,wanan wasan abinda na fahinta shine faizah itace me kirki ita kikasani yayinda fauziyya ke amfani da wanan damar tanaso ta cutar dake" "Zaituna kema nafarajin tsoronki banason Mina furci karki hadani da mutane" "Ba munafurci bane ranki ya dade gaskiya ce Bari kiji abinda naji".....Nan ta kwashe labarin da Taji fauziyya Tana fadawa deejahmah na har turaren jaba ta kawowa Fatima a boye.....Jin haka yasa Fatima gasgata zaituna tunda Babu Wanda yasan anbata turare Kuma turaren na Nan cikin Jakarta idan haka ne kuwa tasan maganinta, Zufa ta share,jiki Babu kwari ta zauna gefen gado ta rafka uban tagumi Tana fuskantar zaituna,...buga kofar dakin akayi Wanda shine ya tabbatar Mata da kila fauziyya ce,sai kawai ta sallami zaituna tace "bude kofar,kije abunki idan nagama zan nemeki" "Toh Allah ya taimakeki"....zaituna ce ta bude kofar ta ratsa ta gefen fauziyya tai tafiyarta, Shigowa fauziyya tayi, fuskarta dauke da faraa "ranki ya dade guda dakinki a hargitse" Wani irin kallo Fatima Kebin fauziyya dashi Wanda yasata tsarguwa ita kanta fauziyya dakyar ta zauna a gefen gadonta tana waige waige, "Lafiya Naga kina waige waige?Koda yake shi Mara gaskiya haka lamarinsa yake" "Bangane Mara gaskiya ba Fatima mekike nufi?" "Wayyoo bansan bakida fahinta ba yasa na Fadi hakan Amma Nan gaba kadan kwakwalwarki zata bude ranan da kika nemi manemanki kika rasa kin Soma warin jaba saboda rashin wayau irin naki" Kan fauziyya ba karamin daurewa yayiba Nan da Nan jikinta ya Soma rawa "mekike nufine".. Fatima ta janyo Jakarta dake rataye a jikin abun rataye jaka "Bari inbaki babbar kyauta"...hannunta na cikin Jakarta ta bude turaren ta fito dashi batai wata wataba ta watsawa fauziyya dik turaren a jallabiyarta"idan kinje gida kifadawa babarki naji dadin turaren gashi kema na tsan Miki Wanda kika kawomin ne ranan kamun bikin mijina" Turo kofar yarima yayi ganin fauziyya yasashi sauke faraa a dik tunaninsa faizah ce yasashi cewa "faizah Yar innah " "Ba faizah bace fauziyya ce wallahi muke wani game Nan a wayarta Wanda ya burgeni na mage da bera Dan Allah habeeby ka siyamun waya"ta shagwabe fuska, NA bada order wayarki gobe zaa kawo, Jikin fauziyya sai rawa yakeyi tanabin Fatima da kallon ikon Allah da al'ajabi dama yarinyar Nan haka take?Ashe ba kyalle bace turmin zani ce?" "Fauziyya Ashe kema kuna shiri da Fatima kenan" Jinjina Masa Kai tayi "umm Yaya zan wuce".... Fatima ce ta Mike muje inyi Miki rakiya koh?"ta bi bayan fauziyya suka saukko bene a tare,dik deejagmah ta dokanta,ganinsu dare yabata tabbacin komi ya auko....ta sauke wani malalacin murmushi, Tsayawa tayi a tsakiyar parlorn ta rike kugu kanta babu dankwalin sai fanka dake kada gashin kanta "Wasa yayi kyau saidai an Kara rashin saa Domin tsintacciyar dai a dik inda take da saaarta take da kuma Allah na tare da ita,saimu Tara a Wasa na gaba ko fauziyya?Kya basu labari"....ta juya abinya har takai wajen matakala ta tsaya ta juyo "ranki ya dade ki shirya dakyau Domin angonki xaiyi Shirin zuwa dakin matarsa"ta Haye sama abinta, Inda ta barshi na ta taddashi Tana shiga ya rungumeta Yana shinshinar wuyanta ta Shiga shafa sumar kansa zuwa kunnuwansa,a hankali ta rada Masa a kunne "ba aikina bane aikin amarya ne yau zaka dandana zumarta itama" Jiki Babu kwari ya saketa daga rukon da yayi Mata ya juya ya fice daga dakin kawai.... Kallo ta bishi dashi Tana sauke numfashi a hankali,ga gabanta da ya tsananta faduwa na tunawa da tayi yau ce Rana ta farko da zasu raba wajen kwanciya itada masoyinta,tsaki tayi kadan ta zauna jagwab Akan gado ta dafe kanta zuciyarta nayi Mata zugi da tsananin radadi,...ta Dade zaune Tana tunani dakyar ta Mike tsaye ta rage kayan jikinta ta fada toilet a can toilet din ma kuka ta zauna tanayi wiwi saboda tsananin kishi da yake taso Mata,dakyar tasamu tayi wankan ta fito ta shafa Mai sama sama ta feshe jikinta da turare saban ta bude drawer dinta ta Ciro Yar doguwar Riga Mai siririn hannu yellow har kasa take ta zura sanan ta daura zani tasa hijabi ta tada sallah, Tana zaune Tana adduointa Akan dadduma Tana rokon Allah Akan Allah ya cigaba da kareta da mijinta Akan dik sharrin da zasu nufeta dashi Allah kuma ya rage mata wanna mummunan kishin dake dawainiya da ita, Tana Nan zaune da hisnul Muslim a hannunta zaituna tayi knocking,...kallon kofar tayi sanan tace"umhmm,waye" "Nice zaituna ranki ya dade" "Shigo" Ta bude kofar ta shigo ta zube a gaban Fatima "ranki ya dade yarima ne yake kiranki a parlorn kasa" "Meyafaru?" "Nima bansaniba"tace a takaice ta sunkuyar da kanta kasa, "Jekice Ina zuwa" Zaituna ta Mike Sumi Sumi ta fice, Kusan minti goma Sha biyar da Kiran Fatima Bata fitoba shiko gogan ya kafe Akan saita fito zasuci abinci tare deejahmah wadda ke gefe ta cika tayi famm tamkar ta fashe, Karar takun sahunta ya ankarar dasu da saukowarta daga sama,haka ta shigo parlorn fuskarta babu yabo Babu fallasa ta nemi gefen kujerar da yake zaune ta zauna,....binta yayi da kallo daga sama har kasa sanan ya kauda kansa gefen hagunsa inda ya ajiye kwalayen wayoyi guda biyu ya Kai hannunsa ya daukosu,Fatima ya fara mikawa sanan ya juyo ga deejahmah itama ya Mika Mata Tata wayoyin iri daya ne product daya ne harta kalar jikinsu iri daya ne golden,iPhone 8 ya sissiya musu Sarai yasan ita deejahmah ke rikewa Amma gudun rigima yasa shi siya Mata Dan Kar ya nuna banbancii, Zamowa Fatima tayi kadan daga kujera"mungode Allah ya saka da alheri Allah ubangiji ya Kara budi" Yaji dadin adduarta sosai yace "ameen bintu" Deejahmah ce ta dubi rahane da zaituna a wulakance tace "sai ance kuyi serving dinmu abincin zakuyi kenan" A hanzarce suka shiga bubbude kulolin abincin suka shigayi serving dinsu daya bayan daya, Tsakurar abincin Fatima tayi ta ajiye ta sunkuci wayarta ta dubi yarima "asuba ta gari ranka ya dade"Bata jira me zaice ba ta juya tai tafiyerta yabita da wani arnen kallo,take ya hadiye miyon takaici ga tsananin bukata Yana ciki Koda yake itama deejahmah Dole ya sauke mata hakkinta tunda yayiwa Mai martaba alkawarin hakan, Mikewa yayi yayi hanyar dakin dakin Fatima sauri sauri yake hada matakala Amma ko kafin yaje ta rufe kofarta,bugun duniya yayi Taki budewa Tana zaune a tsakiyar gado hawaye na gudu a fuskarta,ta dafe kanta tunanin yau abinda yayi Mata shi zaiyiwa wata yassta wanan kukan na takaici, Ganin Bata budeba yasashi Jin haushi ya juya abinsa,....tsaye yayi Akan deejahma ya Mika Mata hannunsa "taso muje"...sai sanan tai murmushi ta Mike tsaye ta ruko hannunsa yayi hanyar side dinsa da ita,mamakine ya lullubeta na ganin ita baa dakinta zai kwanaba bangarensa ya nufa da ita me hakan ke nufi? Gefen gado ta zauna itama kamar yadda ya umarci Fatima da yin alwala hakan ta kasance a wajenta ,haka ta Mike tayo alwala jiki babu kwari sukai sallah tare sai bayan ya Gama adduoi ta tunada batayi amfani da abubuwanta ba Saida gabanta ya fadi,baki na rawa tace a hankali "zanje side Dina in dakko kayan bacci" "Bakya bukatarsu ki rage kayan jikinki ga towel cen ki daura ai zafi akeyi Kuma ma bedace kije daki mun rigada munyi adduar kwanciya bacci ba" Bakin ciki ne ya lullubeta tabbas tayi wauwta maimakon tunda tasan cewa babu makawa da ita zai kwana tayi dik yadda aka umarceta,gashi kadarin maganin farkon saduwarka da mijinka zakayi amfani dashi idan bakayiba ko kayi daga baya bazaiyiba.....wasu kananan gumi ne suke karyo Mata a Kan hancinta.....hakanan badan tasoba tayi yadda yace, Dik zumudinta da yarima tajishi a tare da ita Saida ta furgita tun farkon days cire towel din dake jikinta hankalinta ya tashi,ya shiga sarrafa Mata jiki yadda ya Dace, Kuka sosai takeyi Amma yarima bai sarara mataba don be tsaya shigarta a hankaliba haka ya kwashi gara a wanan Daren sai wajen uku ya sarara Mata ya murgina gefe Yana sauke numfashi.... ******** Da wuri Fatima ta tsala wanka tasa kayana alfarma ta fito parlor ta zauna tanata daddana wayarta Tana shige shige don ta Gane abubuwan wayar.... Ta Dade zaune sanan yarima da amarya suka fito wadda idanuwanta suke a kumbure tun Daren jiya dakyar take taka kafarta Kishi ne ya tasowa Fatima Amma take ta ambaci hasbinallahu wa niimal wakil cikin zuciyarta,ta danne komi ta kirkiri faraar Dole, "Barkanku da tashi" Yarima ne ya ansa Mata Amma deejahma sai yatsine yatsinen fuska takeyi ga idanuwa sun Kara girma lol "Bintu da sassafe haka kika sheka wanka?kin ganki kuwa ?" "Kwalliyar tarbar mijina ce,yanada kyau ko wace matar aure kafin mijinta ya tashi bacci tayi wanka ta sheka kwalliya yadda idan ya tashi zai ganta da kyau".. Yarima Yana Yar dariya yace "really bintu?dik way koya Miki".. Saida ta kada eyeballs dinta sanan ta bashi amsa da "ummu Mana" "Lallai ummu ta iya huduba gaskiya kin yakeni".. Dariya sosai Fatima tayi "bakada dama sweet" Harara deejahmah ke watsawa Fatima sanan tace"iyayi" Daure fuska yarima yayi "wake Miki iyayi anan wajen?Dan ta Fadi gaskiya sai kice iyayi?ita abinda aka koya Mata kenan saboda haka kowa yayi tarbiyyar gidansu,ban yarda wani yaci zarafin Dan uwansa ba wajen magana" Ya maida dubansa ga Fatima wadda ta sakar Masa murmushi alamun bataji haushiba dikda can kasan zuciyarta tasan deejshmah bashi taci, Sallamar ahmad ce ta kauda komi Nan da Nan suka shiga raha Ahmad na tsokananr yarima Yana tsokanan deejahmah da Fatima,itadai Fatima dariya kawai takeyi yayinda deejahmah tai kicin kicin da fuska sai Harare Harare takeyi, Saida Ahmad ya zauna sosai yarima ya dubeshi cike da zolaya "wayace kazomin gida da sassafe Ina soyayya da matana" "Toh rumeo banazo kaimun iskanci bane,Nima Ina gab da yin nawa auren" Dariya Fatima da yarima sukeyi, Ahmad yayi gyaran murya "malam ba wani Abu ya kqwoni gidanka ba maganar jiya ce da kace in bincika maka tsohon maaikacin gidan marayu to na bincika Kuma Yana Nan nasan inda yake,sanan na tuntube sa da maganar ko yasan malam sani suleman ya tabbatar mun da yasanshi" Gyara Zama Fatima tayi cike da faduwar gaba da zumudi tace "toh ai sai muje ko ranka ya dade?" Kallo yarima ya bita dashi dik yadda ta furgice Jin zaasamu labarin Wanda ya kawota gidan marayu,...tausayinta ya lullubesa yasan rashin iyaye da ciwo, Deejahmah wadda ta cika famm a gefe take binsu da kallo wato yau ma fita zasuyi kenan Aiko Basu isaba idan fitan ne ayi da ita itama, "Ranka ya dade zamuje ne?"Fatima ta Kara cewa cike da kosawa, Jinjina Mata Kai yarima yayi "ehh zamuje Mana bintu" Sauke ajiyar zuciya tayi gabanta na tsananin faduwa, *Muje zuwa* *SLIMZY😍*[8/26, 20:00] 🥰slimzy🥰: 🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* *Anty Aisha(sultana)...wanan shafin nakine ke kadai Ina sonki kamar yadda kikeso na Allah ya bar kauna...son so fisabilillahi😍💜* 💚 43 Cike da zumudi Fatima ta Mike ta haye sama a guje, Mikewa yarima yayi da nufin barin parlorn dan ya dubi Ahmad Yana Shirin magana kenan deejahmah ta dakatar dashi ta hanyar watso mishi tambaya hade da kafesa da idanuwa lokaci daya,.. "Ranka ya dade Wai fita zakuyi ne?"yadda tayi Masa maganar murya a raunane yasashi jin wani iri a ransa, Dawowa yayi ya zauna Kan hannun kujerar da take zaune ya tallabota jikinsa "fita zamuyi dear,kina bukatar wani Abu ne?" Jimm kadan tayi sanan ta nisa tace "ehh inaso muje gaidasu mama da hajiya tunda dai girkina ne yau"tai maganar a takaice,.. Shiru yayi Yana wani tunani,tabbas be Dace ace ya fita jiya da Fatima ba yau ma ya Kara fita da ita batare da deejahma ba yin hakan Sam baayi Mata adalci ba, Shi kuwa Ahmad dake gefe yayi bakan da kunnuwa Yana sauraren amsar da yarima zai bada, "Yadda kikeso haka zaayi,da naso mu fita da Fatima ne zuwa wani uzuri Amma tunda kinkawo naki bukatar zaa jingine waccan din zuwa gobe ko?".. Ta jinjina Masa Kai Tana murmushi,....shima murmushin ya maida Mata hade da shafa kanta, Tasowa yayi ya dawo gefen Ahmad ya zauna,...."inaga zamu daga tafiyar Nan zuwa gobe koh friend!" "Yadda dik ka gani hakan zaayi ranka ya dade Mai Mata biyu"ya fada Yana dariya kasa kasa, "Banson iskanci kanajina koh?" Dariya sosai Ahmad yayi hade da dafe kansa batare da yace komiba, Fatima ce ta fito cikin shiri Nan da Nan harta canjo Kaya ta sauya alkyabbar jikinta tasaka wata Mai shegen kyau ja da golden,kamshin turarenta ne ya gauraye ko Ina Wanda yasa dukkansu suka maida hankali wajenta, "Habeeby ya naganka a Nan bakaje kayi wanka ka shirya ba?" Da sauri deejahmah ta tarbeta da cewa 'inada bukatar fita da mijina yau in gaida iyayena shiyasa bazai samu fita dake ba" Kallo Fatima Kebin deejahmah dashi wadda take magana Tana daga manyan idanuwanta Tana yatsina fuska tamkar Dole akace sai tayi maganar, Jikin Fatima mutuwa yayi Amma hakan besa ta kasa Bata amsaba "wayyoo amarya na mance fa kin angwace jiya,gaskiya ya kamata yau miji ya zauna tare dake ya tarairayeki,....Koda yake kince fita zakiyi gaidasu mama koh?ai yadace kije ki fada musu yadda komi ya wakana".... Daure fuska sosai yarima yayi ganin deejahmah na Shirin yabo wata maganar ga Kuma Ahmad a zaune "banason iskanci kunji koh?Akan me zaku zauna Kuna sakarwa juna magana?Kuma a gaban Ahmad yanzun da wani bakon ne haka zaku kunyatani kenan?" Shiru Fatima tayi zuciyarta nayi Mata tafarfasa ta juya abinta batare da tace masa komiba tayi hanyar bangarenta, Ganin Fatima batace komiba yasa deejahmah karyar da murya cike da kissa tace "kayi hakuri yaayah baxaa sakeba" Kwafa kawai yayi abinsa batare da yace komiba Amma can kasan zuciyarsa haushin Fatima ne dankare,wato ma tafi karfin tsayawa tace wani Abu yasa ta juya abinta Tai tafiyarta, ya lura Dan ganin Yana sonta yasa takeyin wasu abubuwan, Mikewa deejahmah tayi Sumi Sumi ta nufi nata bangaren zuciyarta fall farin ciki Dan tayi nasarar kuntatawa Fatima koba komi tasa anfasa fitar, "Friend Bari in shirya inyi wanka mu fita kaji? bazasu ganni a gidan bama balle wata taimun iskanci " "Haba yarima karkace haka Mana,kishi ne kawai irin na Mata kq rabu dasu Kuma dukkansu ba isasshen hankali garesu ba tunda ba wasu shekaru ne dasu ba har gara Khadija" "Owk ita Fatima savoda taga na damu da ita inajin tausayinta yasa ta bude shafin iskanci?Dan me Zata Fadi maganar data fada a gabanka?idan ni sun rainani Kai Kuma bakon Ido fa?sanan tafi karfin ta tsaya ta bani hakuri Tai zuciya Tai tafiyarta koh?Zata gani idan zankara bin ta kanta "mtswwww Dafa kafadarsa Ahmad yayi "kayi hakuri ka kwantar da hankalinka please banaso kana daukan zafi Akan al'amarin Mata bayan kasan rauni garesu,sanan ba hankalinsu daya da namiji ba Koda karamin yaro ne,su sunada karamar kwakwalwa sanan halittarsu kansu bakaji ance a lankwashe suke ba?idan aka takura musu sai su karye,Dan haka kayi hakuri pls" Numfashi yarima ya sauke a hankali sanan ya furta cikin sanyin murya "shikenan Amma gaskiya saina koyawa Fatima hankali"... "Bance idan mutum yayi laifi Kar a hukuntasa ba Amma a rinka Sara ana duban bakin gatari,....yanzun abinda zaayi ni Bari inje tunda dama inada office karfe Sha daya gashi yanzun har karfe goma gone idan Allah ya kaimu sai muje koh?"ya karashe maganar hade da mikewa Yana duban agogon hannunsa, Mikewa yarima yayi ya bi bayan Ahmad har kofar gate ya rakashi inda yayi parking motarsa,....Fatima na hangensu ta sama a tsaye a jikin window,Tana kallo har Ahmad ya tada mota yarima ya juyo da nufin shiga gida,da sauri ya daga kansa sama setin windown Fatima Nan da Nan ta saki labule ta koma jikin bango tsaye ta dafe gefen zuciyarta dake bugawa sauri da sauri,....tsaki yayi don ya hangeta Sarai lokacin data saki labulen yayi cikin gida abunsa cike da bacin Rai.... ********* Koda ya shigo gidan ba kowa a parlor sai TV dake faman aiki ya je ya kashe tv din yayi shigewarsa bangaren deejahmah dikda yadda zuciyarsa ke axalzalarsa da soyayyar Fatima Amma hakan be hanasa zuwa inda zai huce haushin takaicinsa ba, . Tana zaune Kan kujerar madubinta Tana tsara kwalliya ya tura kofar ya shigo da sallama ciki ciki ya maida kofar ya rufe,.. Binsa tayi da kallo har Kan gado inda ya nemi waje ya zauna ya dafe kansa zuciyarsa cunkushe da takaici da bakin ciki, Murmushi ta sauke ta Mike tsaye ta gyara daurin towel dinta dake makale jikinta iya saman cinyarta sai tashin kamshi takeyi ta taso Tana kwarkwasa har inda yake zaune,sai kawai tasa hannu ta cire Masa tagumin Wanda yasa shi dago jajayen idonsa ya sauke Mata su ,wani killer smile ta sakar Masa hade da nadewa saman cinyarsa ta zagayo da hannunta ta bayan wuyansa Tana kallon fuskarsa,cikin shagwaba tace"Haba yaayah dik fushin ne?ummM?kayi hakuri nidai nadaina insha Allahu kaji?"tayi Rau Rau da idanuwanta Tana kallonsa , Jinjina Kai yayi hade da sauke ajiyar zuciya yasa hannu ya tallabo kanta ya hada bakinta da nashi ya shiga tsotsa cikin wani irin salo Yana shafa wuyanta Tana Kara narkewa a jikinsa,ganin haka ya sashi Jan towel din jikinta ya shiga warwareshi tsaf....sai kawai ya jata suka fada Kan gado still bakinsa Yana Kan lips dinta Yana kissing hade da shafa ko Ina a jikinta,.....tun Bata maida Masa martani ta Soma Jin hannuwansa a Kan kirjinta Yana Mata wasanni Nan da Nan ta Soma sauke numfashi sama sama.....shiko yarima baa cewa komi jikinsa har rawa yakeyi saboda tsananin shaawar data taso Masa gadan gadan.....take Saida ya biya bukatarsa sanan ya kankameta a jikinsa Yana sauke numfashi....lumshe idanuwansa yayi lokaci guda Fatima ta fado Masa....tun jiya ya banbance tsakanin Fatima da deejahmah ko wacce da baiwar da Allah yayi Mata ,Abu daya ne jiya ya kasa gasgatawa sai yau da ya Kara kebewa da deejahmah ya tabbatar ba dadinsu daya da Fatima ba,....baya taba gajiya da Fatima har bayaso ya kawo idan Yana tarayya da ita saboda tsananin Dadi da niima da baiwar da Allah yayi Mata Amma deejahmah minti Sha biyar yayi yawa yayi realising a tare da ita to me hakan ke nufi?....bayajin dadin muamalar aure da ita kamar Fatima dikda itama deejahmah tanada nata niimar Amma ba kamar Fatima ba,....runtse idanuwansa yayi lokaci daya Dan tunanin Fatima da yayi wata sabuwar shaawarta ce ta bijiro Masa... Sauke numfashi. Da yakeyi yasa deejahmah saurin dago kanta Tana karewa fuskarsa kallo wadda idanuwansa yake a rufe Yana numfarfashi,..hannu tasa Tana shafa sajen fuskarsa a hankali tanayi Masa waiwayi....hakan da takeyi Kara tada Masa da hankali takeyi saidai bejin zai Kara maimaita wani Abu a yanzu Kuma,sai kawai ya bude idonsa ya saukesu Kan fuskarta Yana kallonta Tana kallonshi fuskarta ta shigayi Masa gizo data fatima wadda idan Yana kallonta take runtse Ido Tana murmushi Mai kayatarwa saboda kunyarsa Amma ita Sam deejahmah Kara kallonsa ma takeyi.... Gira daya ya daga Mata ya janyota saman kirjinsa ya tura hannunsa a Kan kirjinta Yana shafawa Tana lumshe Ido haka bacci ya dauketa....Saida yaga tayi bacci sanan ya sauketa ya kwantar ya rufa Mata bargo....ya fice a daki,... ********* Tsaye yayi a kofar dakin Fatima Yana sauraren saukar numfashinta dagaji ko baa fada ba kuka takeyi... Sauka yayi kasa ransa Babu Dadi dakyar yake daga kafarsa haka ya nufi side dinsa Yana shiga ya fada toilet yayi wanka ya fito ya shafa Mai sama sama ya dare gadonsa ya lumshe idanuwansa abubuwa da yawa sunayi Masa yawo akai... ******** Bacci ne ya dauke Fatima Akan daddumarta bayan ta idar da sallah,Tana baccin ne Amma ajiyar zuciya take saukewa dikda sama sama yake figarta sai wajen karfe biyu ta tashi baccin sanan ta fada toilet tayo wanka ta zo gaban madubi ta zauna dikda yadda fuskarta ta canja saboda tsananin kuka Amma hakan be hanata Zama ta gyara fuskarta da powder ba ta canja kayanta ta sauya wasu hadaddiyar doguwar Riga ce a jikinta maroon Mai ado da stones masu kyakkyali da Haske ta dauko kwalli ta zizara a idanuwanta Wanda suke farare tassss tamkar Madara,kwalin ba karamin kyau yayi mataba (kwalli sirri ne na musamman da yake karawa Mata kyau) Yane kanta da bakin gyale tayi ta dauko wayarta ta fito ta rufo koferta, Waje tasamu ta zauna a parlo,gefenta zaituna ta zauna ta shiga matsa Mata kafafuwanta Tana game a wayarta, Tsaf deejahmah ta shirya ta fito Tai shegen kyau rahane na biye da ita ta tsaya a parlorn Jin karar rufe kofar yarima Wanda shima a shirye ya fito yayi matukar kyau, Fatima na zaune Tana game a wayarta,ko ta kansu batayi ba tanajin lokacin da deejahma ta kashe murya tace "ranka ya dade na fito" "Owk"kawai yace a takaice har ya juya ya dawo ya wuce deejahmah ya shige parlon,har lokacin Kan Fatima a Kan wayarta yake,ya dade a tsaye a kanta sanan yayi gyaran murya fuskarsa a daure "kitashi muje gaida gwaggo rahi dake" Dago eyeballs dinta tayi ta kallesa sanan ta kauda kanta tace "kuje kawai Allah ya tsare" "Karki Bari in Kara magana ki Mike mutafi kawai ko daki ban baki umarnin shiga ba"yadda yayi maganar fada fada sai ya Bata mamaki da tsoro yasa ta Mike tacewa zaituna "muje koh?" "Toh ranki ya dade" Bakin ciki ne ya lullube deejahmah Jin yadda yarima yayi da Fatima har tana cewa bazata zo ba Yana wani cewa sai taje sai kace gidan ubanta....gaba tayi abinta cike da takaici ******** Horn driver yayi masu gadin gidan galadima suka bude gate motoci suka shiga cikin gidan guda uku,daya nasu yarima da matansa daya na kuyanginsu daya na excort dinsu dogarawa.... Gaba abinta deejahmah tayi Bata tsaya jerawa dasu ba a babban parlor ta tadda mahaifiyarta da kanwarta baby da murnar ta take fadin "yeee mama gani nazo ganinki" "Lake marhabun da zuwan sarauniyar masarautar barayar Zaki....barkanki da zuwa diyata" Fatima dake bayansu ta amshe da "yauwa ranki ya dade naji Dadi da wanan tarbar" A fusace hajiya rahina tace "ke Kuma asuwa?uban waye ya baki damar zuwa mun gida ma tukunna?" Murmushi cike da kasaita Fatima tayi ta nemi daya daga cikin kujerun gidan ta zauna ta Dora kafarta daya Kan daya fuskarta dauke da murmushi "nazo gaida uwa a gareni ne tunda ai matsayin surukata kike Kinga kuwa inda mutunci kedin uwata ce".. Tana rufe baki yarima yayi sallama cikin parlorn Wanda yasa hajiya rahina yin Yar dariyar yake dikda kasan zuciyarta mamakin Fatima da al"ajabinta ne kwance... "Barkanki da yamma ranki ya dade"....yarima ya katse Mata tunani, A wayance ta juya bakinta na rawa hade da inda inda tace"umm ammm barkanka dai kabiru ya Iyali?" 'alhandulillahi"yace kansa a kasa..... Hada Ido rahina tayi da Fatima take ta sakar mata wani malalacin murmushi Tana kada kafafuwanta... Samm yarima ko kallon Fatima beyi ba Dan be lura da irin zaman da tayiba saboda yadda ya dau fushi da ita... "Zauna Mana kabiru?ko kaje parlon babanku" "To"kawai yace a takaice ya Mike ya fice.... Cikin daki deejahmah tayi mahaifiyarta ta rufa Mata baya...kallo Fatima ta bisu dashi ta tabe baki Tana Kade kafa, A can cikin daki gwaggo rahi ce suke tattaunawa da diyar Tata Tana Bata labarin irin zaman da sukeyi... "Kina nufin kenan abinda muka kashe kudi akayi be yuwuba?Kuma beyi aiki ba?" Dan Bata fuska deejahmah tayi "be yuwuba wallahi mama Amma yanzun abinda na fahinta shine yarima besan kissa ba to da ita zanyi amfani inyita hadasu fada Dan yanzun haka ba shiri sukeyi ba" Yar dariya gwaggo rahi tayi "yauwa deejahmah ai nasan Babu inda kika Bari a halayena,Dan haka karki kuskura kibari ta kwace Miki miji kicimun uban shegiya...Koda yake ba uba gareta bama" Dariya suka kwashe dashi har parlor Fatima na jiyosu, Sun kusan Awa daya tare ciki sanan suka fito fuskokinsu dauke da farin ciki, "Ni bansan wace irin mayya bace wanna yarinyar,yanzun ke da kikeda gidan uba ma sai an biyoni Dan zakije gidan ubanki?meyasa ita bazataje gidan ubanta ba" Dariya deejahmah ta sheke dashi Tana tafa hannuwanta "kin manta Wai batada uba?iyayen ma tanadasu ne?kaji mama da wata magana" Harara hajiya rahina ta Kara watsawa Fatima "af na manta fa shegiya ce Yar gaba da fatiha" Ran Fatima ba karamin baci yayi ba zuciyarta na tsananin yi Mata suya Nan da Nan idanuwanta suka kawo ruwa ta Mike ta kallesu tamkar zatace wani Abu sai ta fasa ta fice zaituna ta rufa Mata baya, Dariya dukkansu sukeyi sanan suka zauna Kan kujera suna Kara tattaunawa inda hajiya rahina ta dauko wani Dan kulli tabawa deejahmah ta rada Mata a kunne... Yarima ne yayi sallama a dakin ya shigo"ku fito mutafi" Waigowa yayi inda yasan Fatima ta zauna saidai be ganta ba, "Ina fatimar?" Ya tambaya Yana kallon deejahmah,....Saida ta kauda kanta sanan tace "ai ta tafi mota tun tuni Wai bazata iya zamana don Kai ka matsa Mata ma tazo tunda ba gidan ubanta bane" Shiru yayi Yana nazarin maganarta,can ya Mike tsaye yayiwa hajiya rahina sallama ya fice, deejahmah ta sauke wani malalacin murmushi sanan ta juyo tayi hugging din mamanta "saina Kara dawowa ki gaida abbah"ta dagawa mamanta hannu sanan ta fice, hajiya rahina ta bita da kallo cike da so da kauna ta sauke ajiyar zuciya tace a fili"ya'daya tamkar da dubu uwar magajin sarki"....Tai murmushi ta shige daki... ***** Takaicin Fatima yasa yarima kasa cewa komi tunda suka shigo motar yake wurga mata harara ta gefe gashi ya rasa dalilin da yasa ko motsi tayi idanuwansa sai sun kalleta, Itama Tana kallonsa ta gefen idonta yadda yake watsa Mata harara,...sai kawai taji kwalla ta ciko a idanuwanta ta kwantar da kanta jikin window tasa hannu a fakaice ta cire kwallar dake taruwa a idanuwanta... Driver ne ya karya kan mota da nufin zuwa gidan Mai martaba,take yarima ya dakatar dashi ta hanyar daka Masa tsawa "kaiii Ina zaka Kuma".... Burki yaja sanan ya juyo cike da girmamawa yace "ranka ya dade na dauka zamuje gidan sarki ne" "Juya ka kaimu gida kawai"ya kauda kansa gefe ransa a bace, Ko karasa parking driver beyi ba Fatima ta bude side dinta ta fice a motar tayi cikin gida, Dakinta ta shiga ta rufo kofar ta danne bayanta da kofar ta saki wani irin kuka Mai ban tausayi "ya ilahi...Allah kana gani Kaine gatana ban dogara da kowa ba sai Kai,Allah ka bayyana mun iyayena Koda sun mutu ne"...hawaye ke gudu a idanuwanta ta durkushe a jikin kofer Tana rusa kuka Mai ban tausayi.....sosai take kuka ba wani Abu bane ya tada Mata hankali kamar gorin iyaye da akeyi mata...tabbas rashin iyaye masifa ne, Runtse idanuwanta tayi tasa hannu ta cire gyalen data yane kanta dashi tayi jifa dashi a kasa ta zauna Tana kuka durshan....shikenan tun kafin akai ko Ina yarima ya fara wulakantata Akan Yar uwarsa?....ta dafe kirjinta yadda zuciyarta ke bugawa sauri da sauri....Nan da Nan kanta ya shiga Sara Mata ta kwanta a kasa a wajen ta rufe idanuwanta.... ********* Har karfe Tara saura na dare Bata fito parlor inda suka Saba Zama ba deejahmah na kwance gefensa kanta na kan cinyarsa Yana shafa Mata gashin kanta, A zahiri gangan jikinsa ke zaune a wajen Amma ruhinsa da tunaninsa gaba daya suna wajen Fatima...minti minti yakan daga Kai ya kalli sama ko zaiga gilmawarta Amma shiru.... Sai wajen goma saura na dare ta fito sanye da kayan bacci kanta Babu dankwali Riga dav wando ne na bacci purple a jikinta,wandon iya cinyarta ne ya Dan Kama Mata jiki sanan rigar Mai siririn hannu ce Mai gidan breziya sun masifar yi Mata kyauz Hannunta dauke da plate da sauran Apple a Kai tazo center table ta ajiye ta kauda kanta dikda taga a yanayin data samesu sai Tai wucewarta ya bita da kallo ta gefen ido... Dago Kai deejahmah tayi "nafarajin bacci muje mu kwanta"tace a shagwabe Tana kallonsa,.. "Owk muje" Saita Mike shima ya Mike... Maimakon yabi dakinta sai ya juya yayi sashin Fatima Saida yakai wajen matakala ya Dan tsaya taji muryarsa Yana fadin "Bari inje inyi sallama da yarinyar Nan" "Ok"kawai tace ta Haye sama ******* Tana kwance cikin duhu hawaye na gudu a idanuwanta tajiyo karar bude kofarsa da sauri ta rufe ido Dan Tana iya ganin inuwarsa ta jikin kofa, Hannunsa yasa ya laluba jikin switch ya kunna globe Haske ya kauraye dakim... Ya Dade tsaye Yana kallon fuskarta wadda idanuwanta ke rufe tankar me bacci Amma hawaye na gudu a fuskarta. Jikinsa ne yayi sanyi ya tako a hankali ya Haye saman gadon har inda take ya sunkuyo da fuskarsa daidai fuskarta Amma Bata bude idanuwanta ba dikda kirjinta dakeyi Mata lugude Bakinsa ya Dora Kan nata ya shiga kissing dinta Amma ko motsi batayiba....ya dade a haka sanan ya dago kansa still yana kallonta idanuwansa jajir ya maida idonsa Kan kirjinta wadanda suke a tsaye tsaye...take yaji wani Abu na tsarga Masa yakai hannunsa ya shafasu....dikda haka Bata motsabba sai hawaye dake Kara gudu a fuskarta, Tausayinta ne ya lullubesa ya ja jiki ya sauko daga gadon yaje ya kashe globe yadan juiyo ya kalleta jin ta motsa,Amma sai ya fice kawai zuciyarsa Babu Dadi... ******** Da asuba bayan tayi sallah kanta keyi Mata ciwo Tana zaune Kan dadduma wayarta tayi Haske , Tasa hannu ta duba wayar Tex ne ya shigo kamar haka "fatan kin tashi lafiya bintu,...ki shirya da wuri zamuje gidan mutumin Nan da Ahmad" Tana Gama karantawa ta ajiye a gefe ta Mike ta fada toilet tayo wanka ta fito ta shirya,... *******. Wajen karfe Tara Ahmad yazo kofar gidan be shiga ba ya Kira wayar yarima ya sanar Masa da Yana kofar gida,.. Sauri sauri ya shigo dakin Fatima Tana zaune ta shirya fuskarta jajir saboda kukan data kwana tanayi "ki fito ga Ahmad a waje shi zai daukemu" Batace komiba ta Mike ta biyo bayansa,....kusan a tare suka sakko kasa "Allah ya kiyaye ranka ya dade"deejahmah dake tsaye gefe tace, Daga Mata hannu yarima yayi ya fice,Fatima tabi bayansa ******* A mota ahmad ne kawai suke Hira da yarima ita kuwa Fatima tamkar kurma haka take a motar tafe suke zuciyarta na tunani kala kala yadda zata Rama abinda deejahma tayi Mata,...shi kansa yariman ba kyalesa zatayiba saita horasa.... Zuciyarta ke kudura Mata irin abinda zatayiwa Deejahmah na ramuwa....... Tafiya Mai nisa sukayi tamkar zasu bar garin har suka shigo cikin wani Dan karamin gari inda Nan ne Ahmad yayi parking ya fita ya shiga wani gida Jim kadan suka fito da wani tsoho sai kawai Ahmad ya bude gaban motar ya cewa yarima "koma Baya zai shigo zamuje gidan mutumin da ya kawo Fatima gidan marayu ne" Fita yayi ya bude baya ya shiga mutumin ya shiga gaba Ahmad ya tada motar...m Ta glass Fatima ke kallon tsohon mutumin Wanda Babu tantama tasanshi a gidan marayu da dadewa shine tsohon me Zama a store wajen ajiye record. ****** Wani tsohon gida wanan tsohon ya nunawa Ahmad Nan sukayi parking Ahmad ya kashe motar kowa ya fito...yara ne suka zagaye motar suna kallon tamkar Basu taba ganin mota ba, Wani yaro Ahmad ya Kira ya aika cikin gidan ya nema musu izinin shiga , Jim kadan ya fito "baabah kuluwa tace ku shiga".... Ahmad na gaba tsohon Nan na biye dashi yarima da Fatima na biye dasu, "Lale marhabun da zuwan baki"wata tsohuwa dake zaune a babbar tabarma a tsakar gida tace.... "Yauwa"cewar wanan tsohon maaikacin gidan marayu sanan suka zazzauna a tabarma.... Tsohuwar kebinsu da kallo daya bayan daya sanan tace "bangane Kuna,suwayeku?daga Ina kuke?" Tsohom maaikacin gidan marayu ne ya Soma magana "sunana isyaku yakubu,ni tsohon maaikacin gidan marayu ne sanan ni abokin me wanan gidan ne malam sani suleman" Shiru tadanyi sanan tace "to meke tafe daku?" Nan malam isyaku yayi Mata bayanin komi da dalilin zuwansu, Ta Dade sunkuye da kanta kasa batare da tace komiba Tana faman jinjina Kai,..yayinda kowa ya watsa Mata Ido Yana jiran me zatace, Fatima wadda ke gefe gabanta ya tsananta faduwa Babu abinda take ambata a zuciyarta sai innalillahi wa Inna ilaihi rajiun....fatanta Bai wuce Allah ya cika Mata burinta ba, Sun Kai minti goma Sha biyar sanan tsohuwar Nan ta dago fuskarta jike da hawaye Tana bin Fatima da kallo "tabbas Nan ne gidan malam sani suleman Amma ya rasu shekaru da dadewa saidai inada wata sheda guda daya Wanda ya barmun yace saboda wata Rana"...Tana Gama fadin haka ta Mike ta shige daki, Suna Nan zaune na Yan mintoci sanan ta fito hannunta rike da hotuna guda biyu ta mikawa Fatima "amshi yarinya ki duba hotonki ne keda uwarki domin a Nan aka haifeki dikda uwar Taki ba Yar Nan bace Amma a bayan hoton tayi wani rubutu" Hannun Fatima har rawa yakeyi ta amsa ta kafe hoton da idanuwa...itace Tana Yar shekara uku Akan cinyar mahaifiyarta dukkansu suna dariya akai musu hoton....juya bayan hoton tayi ta duba wani rubutu haka...M.B.Z...shine abinda aka rubuta a jiki sanan kasan anyi wasu rubutu kanana masu yawa... Muryar tsohuwar sukaji "kuje da wanan hoton akwai adreshi a kasa na mahaifarsu ne idan har baku samuba baa yardaba kuzo kusameni inada sauran Karin bayani"....ta Mike ta shige daki, Itadai Fatima hawaye kawai ke gudu a idanuwanta yayinda ta kafe dayan hoton da Ido shine na mahaifiyarta ita kadai Tana murmushi.... Hannunta Yana rawa kanta a kasa ta mikawa yarima Wanda jikinsa har tsuma yakeyi Yana duban hoton da sauri ya juya bayan hoton idonsa suka sauka Akan bakin da ya gani kamar haka M.B.Z...wani irin faduwar gaba ne ya ziyarceshi ya Mike a zabure ya tsaya Yana Kara ware idanuwansa.....Yana maimaita bakin a bakinsa.... Kallon yadda jikinsa yake rawa takeyi idanuwanta taf da hawaye take binsa da kallo.... *Muje zuwa* *SLIMZY😍* [8/28, 20:00] 🥰slimzy🥰: 🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* 44 Kallon hoton yarima yakeyi Babu ko kifta idanuwa....hannuwansa ne kawai yake rawa yayinda zuciyarsa ke bugawa tamkar zata fasa kirjinsa ta fito, Ahmad ne ya Mike Yana duban yarima yadda dik tashin hankali ya bayyana a fuskarsa yace "ranka ya Dade lafiya kuwa?meke faruwa ne"....still yarima Yana tsaye idonsa Akan hoton bema San Ahmad Yana magana ba Saida ya gaji ya bugi kafadarsa "malam da Kai nake magana fa meye ya faru ne?ko kasan wani Abu dangane da wanan hoton ne?" Murmushi kawai yarima ya sauke yayinda ya cije lebensa kwalla ce cike a Ramin idanuwansa sai kawai ya kada kansa dakyar ya iya juya kansa ya kalli Fatima wadda ke durkushe da daya hoton Tana kallo Tana kuka, "Tashi muje gida" Wanan tsohon ne ya sauke ajiyar zuciya "iko sai Allah wanan al'amarin akwai boyayyen lamari cikinsa Allah ya warware muku yara" Ahmad ne yayi karfin halin cewa "ameen"... yayi gaba yarima na biye dashi hannunsa rike da hoton, Fatima ce karshen fitowa daga gidan Tana kuka Mai ban tausayi tanayi Tana waigen kofar gidan,....dakyar ta shiga mota suka tafi, Gidan tsohon maaikacin gidan marayu suka fara zuwa suka saukesa, Yarima da kansa ya fito yayi Masa godiya sosai ya Ciro kudi masu yawa a aljihunsa ya Mika Masa sukai sallama sanan ya juya ya shiga gidan gaba ya zauna, Ta gefen ido Ahmad ya kallesa "Ina muka nufa?" "Gidana zamuje" Jin amsar da yarima ya bawa ahmad yasa Fatima saurin dago kanta Tana duban bangaren da yarima yake,....sai ta sunkuyar da kanta zuciyarta nayi Mata tsananin Kuna da zugi...ga tsantsar takaicin yarima dake kwance a zuciyar Fatima...dik yadda taso da suje gidan sarki taga ummunta Amma yarima ya Hana sai kawai ta kauda kanta ta cigaba da zubar hawaye, A kofar gida ya saukesu ya juya abinsa suko a tare suka shiga gidan, Deejahmah na tsaye tana Shirin Hawa sama suka shigo dik tabisu da kallo ganin yanayin da suka shigo.... Sama Fatima ta Haye a guje Tana hada matakala Yarima dake Shirin bin bayanta deejahmah ta dakatar dashi "barka da dawowa" "Barka dai"....ya Haye sama abinsa...tabishi da kallo hade da tabe baki, ****** Kan gadonta ta fada ta fashe da kuka harda majinu Tana juyi a haka ya sameta a dakin, Bece Mata komiba ya jingina kansa da jikin bangon dakin shima ya runtse idanuwansa saiga wasu hawaye masu zafi na sauka a fuskarsa,.. Zuro kafafuwanta tayi kasa ta Tako gabansa ta tsaya "ka Tai makeni Kabir ka kaini inda iyayena suke Domin yanayinka gabaki daya ya nuna kanada masaniya game da inda iyayena suke...ka taimaki rayuwata ka kaini inda iyayena suke a daina kirana da shegiya"ta karashe maganar idonta kyar akansa, Hannuwansa yasa ya tallabota lokaci daya ya saki lallausan murmushi dikda hawayen da suka wanke Masa fuska "tabbas Fatima nasan inda iyayenki suke ko Ince inada masaniya da su saboda kedin jinina ce"... "Ta Yaya na Zama jininka?ko ka manta a inda ka sameni ne?ko ka mance a inda aka tsinceni ne sanan kaga a irin gidan da uwata ta haifeni".. Hannu yasa ya share Mata hawayen idanuwanta "ke jinin masarautar barayar Zaki ce fatima" Wani irin gigicewa da tayi ne yasata ja da baya Tana girgiza Kai "karkacemun ni jininka ce saboda bakason tayani neman iyayena,ni banida wani Abu daya danganci masarauta" "Karki karyatani Fatima Domin rubutun dake makale a jikin hotonki Babu Wanda zai rubuta hakan sai Dan masarautar mu Kuma complete din rubutun Yana nufin masarautar barayar Zaki,sanan hoton wadda ta kasance mahaifiyarkice inayi Mata kallon sani".. "Ban fahimci inda maganar ka ta dosa ba kana nufin cewa rubutun dake bayan hoton na masarautar ku ne?".. "Ke jinina ce Fatima Domin kedin da namijice babu abinda zai Hana mahaifina yin murabus ya baki sarautar garin Nan" Kan Fatima ya Kara daurewa ta kasa kauda idonta daga gareshi "yarima ka fahimtar Dani yadda zangane" "Fatima Babu yadda zaayi inyi Miki fashin baki ki gani Domin Nima kaina a cikin duhu yake,saidai rubutun dake bayan hotonki ya nuna cewa mahaifinki shike da sarautar masarautar barayar Zaki Domin ainihin sarautar Bata mahaifina bace".. Wani irin farin ciki ne ya lullube Fatima lokaci daya ta fada jikin yarima suka rungume juna suna kuka a tare..... Sun Dade rungume da juna suna kukan farin ciki Wanda dakyar Fatima ta kwaci kanta daga rukon da yarima yayi Mata "tsarki ya tabbata ga Allah ubangijin sammai da kassai....hakika Allah shine Kun fayakun....nagodewa Allah daya kasance Kaine miji a gareni....ba abun mamaki bane idan Dan uwa ya kaunaci Dan uwansa a ko wani Hali....tabbas soyayya ta dakai daga Allah ne...Kuma hakan yanada nasaba da Kai din jinina ne" "Nadade inayi Miki kallon jinina Fatima saboda abubuwa da dama Dana Gama fahinta dangane dake saidai banida wata kwakkwaran hujja da zn iya fitowa in bayyana hakan" Ruko hannunsa tayi suka nemi gefen gado suka zauna ta Dora kanta a Kan kafadarsa wasu sababbin hawaye na Kara sauka daga idanuwanta suna diga a kafadarsa.... "Ba kuka ya kamata kiyi ba farin ciki ya kamata kiyi Fatima sanan ki godewa Allah da yasa kika Fado a hannun iyayenki" Jinjina Masa Kai kawai tayi batare da tace komiba.... Hannunsa yasa ya zagayo kugunta ya rukota jikinsa sosai ya sumbaci bakinta "tashi kiyi wanka ki canja kayan jikinki muje gidan sarki"... "Amma inajin tsoron zuwa mu tunkari Mai martaba da wanan maganar bamuda kwakkwaran hujja" "Karki damu nasan zamusha fama kafin kowa ya yarda da hakan dikda akwai hoto Wanda dolene ma su yarda".. Ta Mike tsaye a gabansa ta shiga cire kayan jikinta tsaf sanan ta nufi toilet shima ya Mike ya fuce a dakin.... ******** Tunda suka nufo gidan Mai martaba gaban Fatima yake faduwa zuciyarta na cike da tsananin zullumi har suka iso Bata daina faduwar gaba ba... Dukkansu suka fito daga motar yarima yayi musu nuni da su shiga ciki shi zai je bangaren Mai martaba, Ganin deejahmah tayi bangaren hajiya babba yasa Dole Fatima tabi bayanta Dan bataso su shiga daban dabn hannuwanta na sake da hotonta a cikin alkyabbarta suka shiga, Da faraa hajiya babba ta amshi deejahmah Tana fadin "lalw marhabun da zuwan Amar..." Kasa karasawa tayi ganin Fatima biye da ita yasa hajiya babba saurin cewa "me kika zoyi bangarena?yau ma kinzo ne kiyimun rashin kunya kamar yadda kikaimun ranan irin naku na ya'yan shegu?".. Deejahmah ta karbe zancen "au rashin kunya tayi Miki hajiya?....hmmmm Koda yake kinsan dik Dan da akace shege ne shi bashida uba Dole ya Zama Mara kunya" Yar dariya hajiya babba tayi "kinsan wani Abu kuwa?ni mamaki ma ranan ta bani yadda tazo tanamun zakewa Akan Wai itadin da take shegiya zata haifamun jikokin shegu kiji fa?Wai Mara asali ke fadin wanan maganar har yasamu damar tsula iskanci".. Dariya sosai Fatima tayi tana musu kallon mahaukata ganin yadda suka takarkare suna sakin maganganu tamkar suna jiranta ko Zama basuyi ba, "Tunda baa bani wajen Zama ba Bari in zauna ni"Fatima tayi maganar tana gyara inda zata zauna,suka bita da kallon yadda take sauke murmushi fuskarta cike da annuri, "Ya kamata ki zauna hajiya Domin yau nazo Miki da babban albishir Wanda inada tabbacin har goro Zaki bani idan kikaji wanan albishir din sanan inaso ya Zama sirri tsakanin nidake uwata da kishiyata Kuma Yar uwata".. A tsiwace deejahmah tace"karki kuskura kiyi gigin kirana da Yar uwarki Dan Babu abinda muka hada Dan nidin ba shegiya bace da ubana,Abu daya muka hada Miji,shima Kuma kaddarace ta Riga fata da ko a hanya bazakiga me Kama damiba".. "Uhmm kayya deejahmah banaso kina furta kalaman da minti kadan ya rage kiyi danasani Domin nidin ba shegiya bace da iyayena....sanan ba wasu bane iyayena face jininku" A zabure hajiya babba ta Soma balai "karki kuskura kice Zaki hada kanki damu shegiya tsintacciyar mage" Yunkurawa Fatima tayi zuciyarta cike da fargaba da tsananin bacin Rai ta shiga zagaye parlorn sanan ta tsaya cakkk a tsakiya "banso ace kunji ko nidin wacece ba daga bakina saidai kalamanku sun tunzurani da Dole in sanar muku da ni din ba kowa bace face Yar asalin masarautar Nan....dikda ba lallai bane ku yarda da maganata Amma nasan idan mijina ya sanar da Mai martaba hakan Dole ya sanar daku"... Wats iriyar dariyar rainin wayau deejahmah keyi itada hajiya babba sun nuna Fatima take hajiya babba ta tsagaita "au tanan kuka bullo keda mijin naki?Mana kisar da kuka bullo da ita kenan?to wanan karyar Bata shiga ba sanan Ina me Miki albishir da sarki shirye shiryen barin kasar yakeyi zaije Domin duba lafiyarsa...ba lallai bane wanan karyar Taku ta shiga".... A fusace Fatima ta wurgawa hajiya babba hoton dake hannunta "nasan Zaki iya sanin hoton wadda ke jikin wanan hoton inma bakisan yarinyar ba ki duba da kyau" Daidai Nan yarima yayi sallama a dakin,.. "Yauwa alhamdulillah nagode Allah daka shigo kabiru ka fitar mun da wanan shegiyar yarinyar tsintacciyar matar Nan taka Dan ko ganinta banasonyi,nace ta firarmun a daki tunda bada ubanta aka hada kudi aka Gina Mana gida ba,kaidai da kaji ka gani sai ka auri shegiya Bismillah" Mummunan bacin Rai ne ya darsu a zuciyar yarima Jin mugun furucin da hajita babba ke jifan Fatima dashi jikinsa har rawa yakeyi "lokaci yayi da zaku daina Kiran Fatima da shegiya savoda ita din ba shegiya bace da iyayenta....Dan asalin Fatima ma Yar masarautar Nan ce" "Kabiru rashin kunya kazo kayimunkenan?wato kun hado baki kaida ita kunzo kuce ita Yar sarauta ce saboda kana gudun ta haihu ace uwarsu shegiya ce diyanka a zagesu a idon duniya" "Da Zaki kalli hoton da ta baki da kin tabbatar da abinda nake fada din karyane ko gaskiya?".. A fusace hajiya ta durkusa ta dauki hoton ta Dora idanuwanta akan hoton.....take gabanta ya yanke ya fadi...ta dago da sauri Tana duban Fatima....wadda Nan da Nan kamannin Fatima suka juye Mata tamkar ta jikin hoton... Miyaun bakinta ne ya kafe ta shiga tsananin furgici da tsantsar tsoro....a zahiri saita dake ta Tattaro dik wata jarumtatata "wannn hoton karya ne hadasa akaje akayi wanan hoton ba gaskiya bane cuta ce da hainci akeson hada baki da Kai saboda ka samawa Fatima gurbi a gidan sarauta" Idanuwan Kabir ne suka kankance sukai jajir dasu "bedace kiyi wanan furuciba Domin gabaki daya yananinki ya nuna kinsan gaskiya kikeso ki take sani" Deejahmah ta karbe "wallahi Fatima ba jininmu bace baka Isa ku kirkiro karya kuce ita jinin mu bace"... "Dakatamun Khadija bansa bakinki a wanan maganar ba kin Gane ?Domin nidin ba saanki bane" Farin ciki ne ya lullube Fatima ta Tako a hankali ta ruko hannun yarima "ka kwantar da hankalinka mijina Domin hajiya tasan gaskiya take ta kawai takeso tayi,lokacin data dauki hoton Tana kallo zan iya kirga iya bugun zuciyarta daga inda nake tsaye....jarumtace irin tamu ta Mata irinta masu sarauta ainihin jinin sarauta shiyasa kaga ta dage Akan hakan.....Amma lokaci yayi da ya kamata kisan cewa nidin ba tsintacciyar mage bace"...Tana Gama fadin haka taja hannun yarima sukai hanyar fita Aiko hajiya babba ta biyo bayansu Tana surfa ashar har dakin mama karama suna zaune ita da ummu.... Mikewa tsaye sukai a tare ganin hajiya ta shigo Tana hayaniya bayanta deejahmah ke biye yayinda yarima da Fatima suke ruke da hannun juna... Tsananin bacin Rai yasa idanuwan yarima rufewa take ya mikawa hajiya karama hoton hannunsa "hajiya Dan Allah Dan annabi ki duba hoton Nan bazaki rasa sanin wacece a jikin hotonba wadda a yanzun take itace uwar Fatima".. Hannu Mama karama tasa ta karbi hoton ta maida idonta a Kan hoton......ta Dade Tana kallon hoton ko kafin ta dago kanta idanuwanta sun cika da hawaye fuskarta ta jike da zufa ta ko Ina...."wanan hoton sarauniya zahrau ne a gefen ta kuwa diyarta ce tunda ga kamanninsu Nan sak da juna".... "Alhamdulillah mama wacece sarauniya zahrau?"yarima ya jehowa mama karama tambaya yayinda wajen yayi tsitttt "Sarauniya zahrau itace matar sarki abdallah yayan mahaifinka....wanda shine asalin Mai sarautar garin Nan....sarauta ta koma hannun mahaifinka ne ta silar saifiya".... Hajiya karama ta nuna hajiya babba Tana hawaye...dukkansu sukabi hajiya babba da kallo... "Me kike shirinso kice?koko kema kin yarda da wanan bakin hoton da aka kawo akace zahrau ce matar sarki abdallah?wallahi wanan ba zahrau bace karya ne "Tana karashen zamcenta ta juya da sauri Tana jaraba deejamah wadda tayi mutuwar tsaye dakyar ta taka kafarta tabi bayan hajiya babba... Zama yarima yayi ya tankwashe kafa Fatima ta zauna gefensa jiki a sanyaye "Mama banso kukasan maganar Nan ba nasone infara samun sarki da maganar kafinku sai Kuma naje banaameshi ba ance yaje gaisuwar mutuwa gidan sanata shine na shigo Nan naje gaida hajiya na tarar da ita tasa Fatima gaba Tana hayaniya shegiya ce tsintacciyar mage shine abinda yasani tsananin takaici na fallasa Kwan" Kuka sosai ummu takeyi Tana fadin "Fatima Ashe yata ce ke?Ashe Yar wana ce uwa daya uba daya?banyi mamakiba da nakejin tsananin kaunarki.... alhamdulillah Ashe zahrau ta haife cikin dake jikinta?Ashe zahrau ba mutuwa tayi ba?".. Kuka sosai mama karama keyi dakyar ta tsagaita ta dubi Fatima na Yan mintoci ta sauke ajiyar zuciya sanan ta dubi yarima Wanda dik ya kosa yaji yadda akayi hakan ta faru...."da Fatima ta kasance da' namiji da Babu abinda zai Hana mahaifinka beyi murabus ya Bata sarautar garin Nan ba....Domin sarautar ta mahaifinta ce,...." Cikin kosawa yarima yace "mama ta Yaya hakan ta kasance?".. "Dole in sanar dakai abubuwan da muka aikata a baya Koda zamu samu sassauci da kwanciyar hankali a duniya da Kuma lahirar mu....Domin munada sa hannu a komi"..... "Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun"...shine abinda yarima ya ambata a Fili Yana share zufar fuskarsa ... *Muje zuwa* *SLIMZY😍* [8/29, 14:50] 🥰slimzy🥰: 🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* _Wanan shafin sadaukarwa ne ga dik wani maraya dake fadin duniyar Nan....._ 👏🏼😊 45 "Tun bayan rasuwar kakanka,ya kasance sarki abdallah shine babban danshi sai mahaifinka Sanan sai zainab sai rahina itace autarsu, Mahaifinka ya Riga yayansa aure Dan ko lokacin da kakanka ya rasu dukkanmu babu Wanda baa auraba Dan lokacin ma habibu yanada shekara kusan goma Sha takwas a duniya,shiyasa Koda kakanku ya rasu nida safiya muka shiga farin ciki Akan mahaifinka shi zai gaji sarauta saboda shine yake da iyali shi ya cancanci abashi sarauta ba sarki abdallah ba, Kwatsam bayan anyi sadakar bakwai na kqkanku sai mukaji labarin babban aminin kakanku ya aikowa abdallah da yazo zai bashi diyarsa zahrau ya aura tunda bashida Mata ya Kuma manyanta a lokacin,.. Jin haka yasa abdallah beyi musuba ya amshi auren wanan yarinya da akayi Masa tayi zahrau ranan da aka daura musu aure ranan aka nadashi sarautar garin Nan mahaifinka yayi matukar farin ciki da aka nada Wanda sarautar garin Nan sabanin mu matansa da mukayi bakin cikin hakan, Tunda aka wanke zahrau aka kawota gidan Nan muka hade Mata Kai nida hajiya babba Kuma hakan dik yasamu asaline da tsananin kishinta da safiya takeyi itace ta kawo shawarar mu hade Mata Kai Babu wata muamala da take shiga tsakaninmu da ita saboda dik mun girmeta ko a wanan lokacin batafi shekara ashirin zuwa da dayaba sukai aure.... Babban burin safiya be wuce zahrau ya Zama Bata haihuwa ba saboda mijinmu ya gaji sarauta idan har zahrau Bata haihuwa to Babu makawa mijinmu ne zai hau sarauta.... Shiyasa safiya ta hada baki da dik wata baiwa dake cikin gidan Nan maaikata masu girkin abinci take Basu abubuwa suna sawa zahrau cikin abinci na Hana daukar ciki,wani lokacin ma har kwayoyi muke tasata nida safiya mu Bata dikda ni Ina baya baya saboda gudun kamuwar da Allah zaiyi Mana, Dik wadanan abubuwan da mukeyiwa zahrau na tsangwama da tsananin tsana mazajenmu basu sani ba saboda bama taba nunawa a gabansu Dan su kansu a hade yake, Rahina dama ta kasance ita Yar dakin safiyace tun Tana kqrama dik abinda safiya takeso shi takeyi Bata tsallake umarminta wasu abubuwan dayawa Tare da rahina suke yinsu dikda Nima Ina Taya safiya kishi Amma bana taba yarda in muzgunawa zahrau ko nayi daga baya zan koma in nemi gafararta,.. Samm zahrau Bata fitowa Tana bangarenta Koda yaushe cikin kuka take saboda yadda mukabi muka sawa kowa tsanarta cikin gidan Nan harda bayi da kuyangi basa ganinta da mutunci dikda kasantuwarta matar sarki a wanan lokacin Amma samun waje da fuska da sukayi a wajenmu yasa kowa ke tsula iskancinsa, Kwatsam bayan shekaru biyu da aurensu zahrau tasamu ciki Wanda bamu San dashi ba saboda yadda muka saki jiki Akan mahaifarta ta lalace saboda mugayen abubuwan da safiya ke amsowa Ana Bata yasa ta rame ta koma tamkar me wani mummunan ciwo,Dan haka Koda tasamu ciki bamu saniba Saida ya Kai wata biyar Amma shi mijinta da mijinmu sunsani dik a tunaninsu muma munsani, Ranan muna zaune a parlor da mijinmu nida safiya ya Dan kishingida kadan idanuwansa a lumshe yace "Kuna dai kula da zahrau koh?kunsan yarinya ce wani Abu sai an rinka sa Mata idanuwa dikda gabaki daya ta canja ta rame tamkar me wani mummunan ciwo" Gyara Zama safiya tayi cike da kissa tace"ranka ya dade ai kulawa da zahrau ya zame Mana Dole tunda Yar Amana ce ko jiya na shiga bangarenta mun Dade tare Mina Hira Ina tambayarta yadda zaman nasu yake da maigidan nata" "Ai kullum ya kamata ku rinka shiga yanzun saboda sauraren haihuwar Tata tunda cikinta yanzun zai Kai wata shida ko biyar".. Kamar hadin baki muka hada baki wajen fadin "ciki fa kace ranka ya dade" Sai yadan bude idonsa Yana binmu da kallo cike da mamaki ganim yadda ko wacce a cikinmu ta furgice "au bakusan tanada ciki ba kenan?koko baku lura bane?" Wayancewa mukai a tare muke fadin "yo ranka ya dade aimu bamusan da wanan labarin farin cikin ba,kasan fa matar wan naka akwai kunya Sanan kullum cikin alkyabbar take babu Wanda zaaiyi ka fahimci akwai ciki a jikin nata" Yar dariya yayi "aikuwa abdallah ya kusa samun magaji insha allahu,Allah dai ya sauketa lafiya" Dakyar safiya ta bude baki ta amsa saboda yadda gabaki daya ta furgice da lamarin,Allah Allah mukeyi ya fita zuwa fada muje bangaren nata,aikuwa Yana fita muka zari gyalenmu muka nufi sashin zahrau, Tana zaune Akan daddumar sallarta gefenta Kaine zaune dama tun kana karami jininka ya hadu da ita Koda yaushe kana tare da ita Nan ne wajen hirarka,.. Babu ko sallama muka shiga a tare,Tana ganin mu yadda ta furgita a wanan lokacin kaidin da Mai hankali ne saika fahimci wani Abu sai ta baka tausayi savoda tsananin tashin hankali daya bayyana karara a fuskarta,.. Harararka nayi nace "rasa kunya ka tsaya ne kaji me zamuce?"...sai kawai kabi zahrau da kallo batare da kace komiba ka fice a dakin,... Safiyace ta gyara tsayuwa "zahrau dama ciki gareki?dayake ke munafuka ce kinsan abinda kika kulla yasa kika kasa sanar Mana?saboda dama kudurinki kizo ki haifi magajin sarki koh?shiyasa ubanki ya daukeki sadaka ya mikawa abdullahi ke Dan yasamu jika sarki koh?to wallahi baki isaba yayanmu su zasuyi gadon sarautar barayar Zaki ba Dan Yar sadaka ba".. Kuka zahrau ta shiga rerawa Mai ban tausayi ni kaina da nake gefe Saida jikina yayi sanyi ganin yadda dik ta furgice ta gigice Tana bamu hakuri.... "Ciremun hijabin dake jikinki mugani muna fuka?"cewar hajiya babba,.. Jikin zahrau Yana rawa ta cire hijabin jikinta saiga ciki ya fito sosai..... Nan muka saka salati muna tafa hannuwa,....safiya batai wata wata ba ta shararawa zahrau Mari "wallahi baki Isa ki haifi abinda ke cikin Nan nakiba Dole ma a cireshi kodai ki yarda a cire cikin Nan ko Kuma ko ki haifeshi babu Rai"... Nai saurin cewa "safiya bedace ace mu kashe Mai Rai bafa?mu kyale cikin kawai ta haifi abinta".. "Idan ke wawuya ce niba wawuya bace wallahi ai Dole ma kice haka tunda Kinga ai Koda sarki ya mutu ba danki bane zai gaji mulki saboda bashi bane babba shiyasa kikace haka to wallahi yanzun ba sai anjima ba Dole ta haifeshi".. Zaro idanuwa nayi waje inabin safiya da kallon mamaki, Wata kuyanga ta kwalawa Kira Ana ce Mata uwaliya,Babu dadewa uwale ta shigo ta tura uwale dakinta ta Kira Mata rahina,Nan da Nan sai gasu tare da rahina,.. Fuska babu walwala safiya ke duban rahina "Ina tsumin madacin Nan da nace ki jikashi saboda wanan shegiyar?to amfaninsa yazo " Juyawa rahina tayi jimm kadan sai gata da Koko cike da ruwan magani Kore sharrr safiya ta amsa ta mikawa zahrau dake tsaye jikinta na rawa Tana shasshekar kuka fuskarta tayi jajir, "Dan Allah kiyi hakuri hajiya karki kashemun abinda ke cikina inason Dana idan zamana ne bakuso zanbar muku garin" Wata tsawa safiya ta dakawa zahrau Nan da Nan ta amshi maganin Nan jikinta na rawa ta kafa Kai,tasss ta Sha kusan rabi idanuwanta suka canja kala savoda tsananin azaba da dacin maganin..... Minti kadan muna Nan tsaye zahrau tafara murkususun ciwon ciki ta durkushe a wajen Tana kukan azaba Tana Kiran mutaimaketa Babu Wanda yabi ta kanta tunda mukaga jini ya fara bin kafarta muka fice muka rufo Mata kofar Sanan safiya tabawa bayin bangarenta doka Akan Kar Wanda ya shiga wajen da zahrau take,.. Har wajen laasar Ina jimami da tunanin yadda muka baro Yar mutane,tsananin furgici da tsoron Allah ya sa na Mike nayi sashinta Koda na shiga tasamu sauki Tana zaune Tana faman sharar hawaye dik ta Bata ko Ina da jini,.. Ganina yasa ta furgita ta Mike tsaye na shiga girgiza Mata Kai "banazo Dan in cutar dake bane zahrau nazo ne in nemi gafararki Akan abubuwan da mukayi Miki kiyafemun nidai na cire hannuna".. Kuka sosai takeyi Tana fadin "na yafe Miki mama karama har duniya ta nade na yafe Miki Dan Allah ki taimakeni kubarni in haifi abinda ke cikina"Tana kuka take fadin hakan,.. Saboda tsananin tausayinta bansan lokacinda hawaye ya Soma zuba a idanuwana ba Nan da Nan da kaina na gyara bangarenta nasa Mata turaren wuta na rufo Mata kofar na tafi sashena cike da zullumi da tunanin halin da Yar mutane ke ciki.... Tun daga ranan kullum nakan leka inganta yayinda Koda yaushe Ina turaka ka dubata Kaine abokin hiranta lokacin Nima inada cikin afnan wata uku a jikina, Shirye shirye sosai Mai martaba yakeyi da kaninsa na haihuwar zahrau inda ya shirya zahrau a saudiyya zata haihu lokacin cikin nata nada wata takwas ranan da safiya Taji wanan labarin batayi bacci ba Dan dik a tunaninta zahrau ta haifi abinda ke cikinta matacce tunda bataji wata duriya daga gareta ba uwaliya ke kawo Mata rahoton karya cewa zahrau batada ciki. Ranan safiya ta tasa rahina da wani tsohon maaikacin gidan Nan zubairu suka shiga sashin zahrau suka firgitata a gabanta safiya tabawa zubairu umarni da yazo sashen cikin dare ya farde cikinta ya Ciro abinda ke cikin nata ya kashe batare da kowa ya saniba saboda ranan Mai martaba da kaninsa sunje ran gadi wata masarauta kusa damu.... Tsagaitawa mama karama tayi tana kuka harda shassheka ta maida dubanta ga Fatima wadda ta kifa Kai Tana kuka tamkar ranta zai fita,shi kansa yarima kuka yakeyi saboda tsananin tausayi... "Tun bayan barinsu sashin zahrau suka nufo sashen mu zahrau ta shiga furgici da tsananin tashin hankali Nan ta nemi taimakon uwaliya Akan tanaso ta gudu ta taimaka Mata uwaliya batai musuba ganin gwalagwalan da zahrau ta mallaka Mata dik Dan savida ta taimaketa aikuwa ta taimaketa ,Dan uwaliya itace Tai Mata hanyar data gudu cikin dare batare da kowa ya saniba.... Washe gari muka tashi da mummunan tashin hankali na batan matar sarkin masarautar barayar Zaki...Nan da Nan aka baza a ko Ina Akan an save matar sarki fadin mummunan tashin hankalin da abdallah ya shiga Bata baki ne a sanadiyyar hakan ne ya kamu da tsananin cutar barin jiki saboda faduwar da yayi lokacin da labarin batan matarsa ya ruskesa, Hankula da yawa sun tashi a wanan lokacin ko Ina labarin abinda ya faru a masarauta ake ciki ko harda ciwon sarki abdallah.... Safiya da rahina kuwa dik alhinin da akeyi be damesuba Dan su farin ciki ma sukeyi na batan nata Dan rahina dama bayan ta haifi deejah ta dawo gida saboda aiki da galadima ya samu a Egypt , Kusan kwana arbain da faruwar lamarin mugun labari ya riskemu daga zubairu cewa ai matar sarki data bace yaji labarin mota ta bigeta ta rasu da ciki motar data bigeta ne Suka dauki gawar suka tafi da ita baasan inda suka kaitaba,...Nan sabon tashin hankali ya samemu Dan Babu Wanda be firgitaba da Jin wanan labarin jikin sarki abdallah ya Kara rikicewa gashi yaki yarda akaisa asibiti ayi Masa magani na bature yafison na gargajiya,Nan aka tattara shi aka maidashi garin iyayen su Dan ayi Masa magani,... Koda labarin rasuwar xahrau ya riski Yan uwanta sunyi matukar bakin ciki da rasuwar Yar uwar tasu yayinda wasu Basu yarda da cewa ta rasunba, Bayan shudewar lokuta abubuwan sun faru ciki kuwa harda nadin sarautar da akayiwa mahaifinku a matsayin sabon sarki lokacin na haifi afnan babu dadewa Dan dama khausar ita kusan saanni suke da deejahmah.... Kuka sosai Fatima takeyi lokacin da ta dago fuskarta a rikice tace "yanzu a Ina mahaifina yake?"shine tambayar data jefo Wanda ya Kara razana hajiya karama, Take yarima ya ruko hannunta Yan girgiza Kai hawaye na gudu a fuskarsa,.. "Fatima mahaifinki Allah yayi Masa rasuwa kwanakin baya Dan lokacin da abun ya faru ma kina gidan Nan" Mikewa Fatima tayi tsaye cike da tashin hankali Tana fadin "innalillahi wa Inna ilahi rajiun" Rukota ummu tayi ta fada jikin ummu ta rungumeta Tana kuka "Ina saudiyya dik wadanan abubuwan suka faru lokacin Dana dawo sarki yayi Yar tafiya lokacin mahaifinki ya rasu yaje can garin....abinda yasa baa sanarba kuwa shine saboda tun da dadewa jamaa sukai tunanin ya mutu Dan haka shiyasa akai shiru da maganar".. Rungumeta sosai Fatima tayi tana kuka harda shassheka,.. Sallamar hajiya rahina ce ta shigo gidan direct sashin hajiya karama ta nufa hajiya babba da tajiyo muryarta itama ta fito tare da deejahmah suka shigo,.. "Wani sabon labari ne ya riskeni yanzu yanzun Nan na karyar da naji Ana Shirin shiryawa".. A zabure Fatima ta Mike daga jikin ummu jikinta har rawa yake tasa hannu ta share hawayenta "ba karya bane ba Kuma sharri akai muku ba abinda kuka binne cikin duhu shekaru ashirin da suka wuce yau *ANYI WALK'IYA* asirinku ya tonu.....Kunyi sanadiyyar korar uwata daga garin gabaki daya saboda karta haifi abinda ke cikinta ya gaji sarauta sai Allah yasa da hannunku kuka reni abinda ke cikin nata tunda gashi na dawo cikinku na dawo cikin dangina......shegiya tsintacciyar mage Ashe yar Sunnah ce cikakkiyar Yar dangi uwa uba Yar saarkice dakanta Dan haka ku shirya daukar fansa da zanyi akanku daya bayan daya" Mamakine ya lullube kowa dake wajen na furucin Fatima da takeyi tamkar wata babba Babu alamar tsoro ko fargaba take fadan magana kanta tsaye... "Karya kikeyi Fatima baki Isa kice kindauki fansa akanmu ba saboda labarin karya da aka zauna aka shirya Miki shine Zaki Mike kina fuffukar banza?idan kikace Zaki shiga shirginmu wallahi saina halakaki".. "Idan kin halaka uwata kinci riba ni bazan halaku Miki ba Domin ni din Nan kainuwa ce dasheb Allah badai mutum ba kwayoyi da dacin madaciya Basu kasheniba sai tuggunki Wanda gabaki dayanku a tafin hannuna kuke?" Yarima ne ya Mike tsaye ya ruko Fatima ta fada jikinsa ya rungumeta matarsa ya fice a dakin ya barsu suna faman jaraba da kumfar baki.... ******** Cikin tsananinn tashin hankali hajiya babba ke magana "lallai na tafka babban kuskure tunda na kashe macijine bansare kansa ba,barin xahrau gidanmu shine babban tashin hankalin da yanzun yake Shirin tunkaroni....hanya Mafi sauki itace yadda zaayi in kauda Fatima daga wannan masarautar idan ba hakaba yarinyar Nan sai ta kaskantar Dani ta wulakantani a idon duniya".. Gauron numfashi rahina ta sauke dik a firgice take "wallahi hajiya tun ranan Dana fara ganin shegiyar yarinyar Nan fuskarta keyimun Kama da uwarta Dan Babu inda tabar mahaifiyarta sakkk Abu daya ya banbantasu mahaifiyarta tanada Dan fadin fuska kadan ita Kuma doguwar fuska gareta,ni a ganina hajiya musawa yarinyar Nan Ido tayi dik haukar da zatayi"... "Bazansa Mata Ido ta wulakantani ba cikin wanan masarautar inda nake abinda nakeso nake juya Wanda na gadama"... A gadarance Fatima ta shigo sashin ta tsaya a kansu duka ta rike kwankwasonta hade da kauda kanta gefe "naji Dadi da yakasance diyar da ake Kira shegiya itace Yar asalin sarauta ba wadda take ikirari da ita din Yar asali bace,.... deejahmah kenan ya kikaga abinda ya faru?Ashe Aron mulki kikayi ba naki bane tunda ubanki be gaji mulki ko sarauta ba,uwarki itace Yar sarki tayi karfa karfar da Saida aka mallakawq ubanki galadiman garin Nan to ki tabbatar indai inada Rai sai nayi sanadiyyar da aka sauke galadima" Mikewa Deejahmah tayi tana Shirin. Wankawa Fatima Mari ta rike hannunta Tana sakin murmushi "fuskar sarauniya tafi karfin Mari a yanzun....idan kikayi gigin Marina wallahi tallahi saina shayar dake mamakin da baki taba tunani ba....albishir nazo muku dashi na sarki yaji labarin *ANYI WALK'IYA* a masarautar sa sirrin dake boye cikin duhu hasken walkiya ya bayyanashi a Fili....zaku iya zuwa ku amsa Kiran Mai martaba"....Tana gama fadin hakan ta juya abinta suka bita da kallo, Kukan takaici deejahmah ta rushe dashi "nashiga uku na lalace meke Shirin faruwa Dani?meyasa wadanan mugayen abubuwan suke samuna ta ko wani bangare?yanzun Ashe dama Fatima kanwatace nake kishi da ita?" Dafata rahina tayi wadda take cike da furgicin halin da suke ciki da irin tunanin hukuncin da Mai martaba zai yanke musu.... Dakyar hajiya babba ta yunkura ta Mike ta janyo gyalen ta ta yafa "muje fadar sarki" Idanuwan rahina ne kawai suke yawo ta ko Ina a cikin fadar lokacin da suka shigo ta tararda fuskoki dayawa cikin fadar ciki kuwa harda mijinta galadima....waziri da iyalensa kaff sun hallara...dik wani Mai ruwa da tsaki a wanan masarautar ya hallara saboda yadda Kiran sarki yake yawo a ko Ina na masu ruwa da tsaki a sarautar... Dakyar rahina ke taka kafafuwanta wadanda suka kasa daukarta saboda furgici ta nemi gefen hajiya babba ta zauna..... . *Muje zuwa* *SLIMZY😍* [8/31, 19:38] 🥰slimzy🥰: 🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* _Sakon gaisuwa da fatan alheri a gareku_ *FARIDA KAKANGI,ASMAU IBRAHIM* *BELLO(MA'U),AISHA USMAN(DADA),FAEEZAH* *ISYAKU(FA'EEH)...* __son so fisabilillahi_💙💜 _ 46 Gyaran murya Mai martaba yayi hannunsa rike da hoton da yarima ya gabatar Masa ya dago kansa ya dubi kowa dake cikin fadar Sanan ya maida dubansa ga hoton dake hannunsa lokaci daya ya sauke ajiyar zuciya Sanan ya fara magana a nutse, "Dukkan yabo da godiya ta tabbata ga Allah subhanahu wataala da ya bayyanar Mana da wani bakon al"amari Wanda bamusan dashi ba tun bayan shekaru da suka gabata,watakila ma mun cire Rai da cewa wata Rana wani bakon al'amari zai faru,hakika kabiru ya gabatarmun da wani hoto dazun dazun da wasu bayanai dangane da hoton da Kuma wani rubutu a bayan hoton dikda bamu da tabbas Akan hakan" Murmushi hajiya babba tayi tana kada kai, "Saidai dik wani Mai hankali Wanda yasan marigayi abdallah yasan zahrau to tabbas wanan yarinya batada banbaci da iyayenta ko wajen kamanni,...na Dade Ina zargin wani Abu dangane da Fatima tun ranan da Allah ya jehota gidan Nan nagasa samun natsuwata narasa hankalina saboda tsananin Kama da itakeyi da ubanta ta wani bangare Kuma jini Yana nuna kamaninta da uwarta Dan haka yanzun da kabiru ya gabatar mun da abinda ya faru ban tsaya wani waswasiba na yanke shawara Akan Fatima diyar abdallah ce marigayi" Wani irin faduwar gaba ne ya ziyarci hajiya babba da rahina suka dago a lokaci daya suka kalli juna Sanan suka maida kansu suka sunkuyar, Juyowa Mai martaba yayi ya dubi waziri Wanda ke gurfane Yana jiniina Kai "waziri me kake gani dangane da abinda ya faru?maana ga Fatima Nan diyata ta bayyana kasan ubanta tun Yana Raye kakeyi Masa waziri to yanzun menene shawararka?" Gyaran murya waziri yayi "ni a ganina anawa tunanin ranka ya dade bazai yiwu ace daga ganin hoto da kamanni ace an amince da wanan yarinya a matsayin Yar marigayiba ya Dace ayi bincike kafin a tabbatar da hakan,abinda yasa nace haka shine hoto da kamanni suna iya yuwuwa ta ko wani yanayi,Sanan zamanine yanzun na computer zaa iya hada hoton Fatima da sarauniya zahrau data bace,gaskiya be kamata sarki yayi saurin karbar wanan maganar ba".. Wani mugun kallo yarima yake watsawa waziri lokacin da yake maganar,Sanan take ya juya ya maida dubansa ga hajiya rahina da hajiya babba wadanda suke faman jinjina Kai tunda waziri ya Soma magana, Shiru Mai martaba yayi Yana nazarin kalaman waziri wadanda yanada nashi point din a wanan lokacin,sai Mai martaba ya gyara zamansa kqdan yace "hakika kanada taka hujjar waziri duba da Babu wata kwakkwaran hujja da ya nuna cewa Fatima din diyar Mai martaba marigayi ce sai kamanni sai Kuma hoton da ya bayyana surar marigayiya zahrsu da ita Yar Tata zaa duba maganarka,.. Ummu ce dake gefe bude baki muryarta a sarke "Niko a ganina tunda bayanai da hujjar hoto ya bayyana be kamata a tsaya jainja Akan yarda da maganar Fatima din diyarmu ce saboda idan akace bazaa yardabd da wanan hoto da bayanin da zahrau ta rubuta a baya to a Ina zaa samu ita zahraun ta bayyana abinda ya faru?...Niko xanso ace hajiya karama ta fito a gabanka ta fasa Kwan abinda ya faru tsakaninsu da zahrau da safiya da rahina"a tausashe ummu ta karasa bayanin ta Wanda hakan ne yayi sanadiyyar gigicewar hajiya babba da rahina ..... "Hajiya karama menene boyayyen Al'amari daya faru a baya Wanda ni din bansan da zamansa ba?" Gurfanawa mama karama tayi "Allah ya taimaki Mai martaba,.....Nan ta kwashe dik abinda ya faru Wanda tabawa su Fatima labari ta Kara bayyanawa a gaban Mai martaba harda abinda ta boye da Bata fadaba dik ta fada na Hari da aka kaiwa zahrau Dan akasheta Wanda shine musababbin barinta gidan sarauta baasan inda take ba har yanzun, Tunda Mama karama ta Soma koro bayani jikin Mai martaba Babu inda beyi sanyi ba Nan da Nan jikinsa ya jike da zufa sharkaf tamkar an jijasa da ruwa harta karasa bayaninta... "Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun "shine abinda Mai martaba yake fadi Yana jinjina Kai A fusace ya bude baki yace "lallai Kun cuceni Kun zalunceni Kun hada Kai Kun hainci masarauta Dan haka dukkansu zaku fuskanci mummunan hukunci" Da sauri Fatima taja jiki ta karasa gaban Mai martaba ta ruko kafafuwansa "Ina neman agajin sarki Mai adalci Akan hukuncin da yake Shirin yankewa batare da yin shawara ko bincike ba Akan lamarin,....inaso sarki yayi watsi da wanan lamari na hukunci da yake Shirin yankewa zuwa Nan gaba kadan idan an tabbatar da nidin jinin sarauta ce,Koda an tabbatar da hakan ni nayafewa su hajiya cutar da mahaifiyarta da sukayi...Dan haka nake gurfane a gaban Mai martaba Akan ya janye wanan hukunci na Roki arziki a karo na farko"...hawaye ne ke diga a idanuwanta lokacinda take gurfane a gaban Mai martaba Tana ratabbo wadanan kalaman... Sosai jikin sarki yayi sanyi ya durkusa da kanshi ya dagota ya zaunar da ita a gabansa "hakika nayi dacen samun suruka ta gari Kuma ya'ta gari a gareni da masarauta baki daya,babu wani arziki Wanda Zaki nema a wajena Wanda banyi Miki shi ba Fatima nayi Miki wanan arzikin na bar maganar hukunci harabada saidai idan ke dince kika bukaci hakan" Fatima tasa hannu ta share hawayen dake gangarowa a idanuwanta "Abu na gaba ranka ya dade shine maganar da waziri yayi Akan hanya take na cewa ayi bincike sosai Sanan a aminta Dani din jininku ce,.... banida zabi Wanda ya wuce Mai martaba yasamun hannu wajen neman mahaifiyata" Wani irin tausayin Fatima ne ya lullube dattijon sarkin Wanda har saida kwalla ta cika a idanuwansa,....tabbas Fatima jininsa ce shi yanaji a jikinsa tunda dadewa Babu Kuma wani Abu da zaisa ya kasa gasgata wanan hoto daya gani baro baro na zahrau da Fatima saidai Dan Cece kuce da zai biyo a cikin garin da masarautar, "Na yarda na amince da kedin jinina ce Kuma diyata ce fatima ki kwantar da hankalinki inada yadda zaayi asamu labarin mahaifiyarki Amma sai mun koma can inda akasamu wannan hoton naki munji bayani cikakke daga garesu" Jinjina Kai Fatima tayi cike da gamsuwa "nagode ranka ya dade Allah ya Kara lafiya da nisan kwana,Allah yasa kafi haka",... Mahaifin deejahmah Wanda ke gefe ya cika famm da tsananin takaicin ganin dik abinda ke faruwa yasashi cewa "ranka ya dade a gaskiya wanan lamari karyane tsantsa da makirci Wanda aka hada ciki harda matarka mahaifiyar kabiru,anyi haka ne saboda a tozarta diyata da mahaifiyarta wanan makircin shiryayyene wallahi,haba dik shekarun da suka wuce baasamu labarin wata zahrau ba sai yanzun?labarin ma Wai a hoto Dan tsabar an rainawa mutane hankali?" Dubansa Mai martaba yakeyi cike da mamaki da al'ajabin wadan kalaman da yake jefowa batare da wani tunani ko tauna magana ba,.. "Shin ka manta a gaban Mai martaba Kuma sarki kake jeho irin wadanan kalaman galadima?kanada hankalinka kake fadan irin haka?" "Ranka ya dade wanan maganafa abun dubawa ce ya zaayi kabiru da matarsa subi dare subi Rana su hada makirci da karya Rana tsaka su fito da hoto suce Wai Fatima Yar gidan sarauta ce?harda wani rubutu na karya a bayan hoto?saboda yanajin tsoron irin zagi da tozarci da yayansu zasu fuskanta Nan gaba idan aka gano uwarsu shegiya ce batada iyaye?" "Dakata galadima bazan dauki dik wani wulakanci da cin Kashi ba a cikin fada ta bazai yuwu ka rinka shegantamun y'a a gabana ba bazai yuwuba idan kanada hujjar da zakuce ku baku yarda da fatimaba zaku iya cewa sai an fidda hujja kwakkwara,Amma ba kazo kana jifanta da mummunan lafazi ba" "Gaskiya bamu yarda ba da wanan hoto da wani labarin kanzon kurege da aka bada dangane da wanan yarinyar sanan Nan wajen nasan da yawa Basu yarda da hakan ba"...Nan da Nan fada ta dauki hayaniya magana kasa kasa kowa Yana fadin albarkacin bakinsa,.. Tsawa Mai martaba yayi "ya Isa,dik wani Wanda yake da ja Akan wanan yarinyar kofa a bude take ya fadi raayinsa dikda Ina Nan Akan bakata" Tsulum hajiya babba ta tsoma baki "magana ta gaskiya Fatima ba jinin mu bace ba Kuma tsatson masarautar Nan bace makirci ne kawai aka hada Wai hoto Fatima Yar sarki abdallah ce ta Ina?".. "Dakatamun safiya banso kice komi Akan wanan lamarin saboda ke banida magana dake da rahina"yace a kausashe, Juyowa yayi gefensa na dama "waye yake da ja a wanan lamarin Kuma?"sarki ya watso musu tambaya Yana dubansu daya bayan daya, Waziri da matarsa da sarkin fada tare da galadima dik sukace Basu aminceba Basu yarda ba da sauran jamaar dake wajen Yan rakiyar sarki dik sukace Basu aminceba, "Dik naji bayaninku Sanan ku din Kun rinjayi wadanda sukace sun amince Dan haka,bazan fasa aminta da din Fatima diyata bace,diyar Dan uwana Dan haka yanzun bincike zai tashi Dan Gane da haka,yanzun Ina umartar kabiru da Fatima da su gabatar mun da matar da suka samu wanan hoton a wajenta me kunshe da wadanan bayanai, Sanan zanyi bincike dangane da gidan mahaifiyar Fatima dikda banida tabbacin samunsu a cikin garin Nan Dan haka zan tsaida tafiyar da nayi niyyar yi zuwa wani lokaci sai gaskiya ta bayyana".. Harara hajiya babba ta watsowa Fatima da yarima wadanda ke zaune gefen Mai martaba,wani murmushi Fatima ta maidawa hajiya babba Sanan ta sunkuyar da kanta, "Fatima"Mai martaba ya Kira sunan Fatima wadda ke zaune a gefensa,.. "Allah ya taimaki Mai martaba".... "Ki kwantar da hankalinki karkice Zaki tada hankalinki Akan wanan batu kinji?insha allahu gaskiya zatayi halinta Kuma inaji a jikina kedin diyatace jinina ce,...naji Dadi nagode da halarcin da kikayi Allah yayi Miki albarka ya baku zaman lafiya" Sunkuyar da kanta kawai tayi cike da kunya batare da tace komiba, Haka Mai martaba yasa akatashi taro kowa ya watse, ******** Can dakinsa nada yarima ya shiga ya zauna a parlor ya kunna tv zuciyarsa Babu Dadi,saude kuyangarsa yayi Mata umarni da ta Kira Masa fatima a dakin hajiya karama, Fatima na tare da bilkisu a bangaren ummu tasa aka Kira Mata ita suka hadu a can, "Nayi matukar farin ciki daya kasance kedin ba shegiya bace da iyayenki Yar uwata Fatima naji Dadi saidai wani hanzari ba gudu ba,dazun da kuka baro fadar sarki naji wasu kananun maganganu suna tashi wajen hajiya babba da rahina cewa Wai karyane makirci kuka hada" Murmushin takaici Fatima tayi "ki kwantar da hankalinki dik suna tunanin cewa karyane ba hotona bane Dana mahaifiyata,gaskiya zatayi halinta lokacin zanyi maganinsu daya bayan daya don har ke zansa a y'antamunke Yar uwata?" "Nayi matukar farin ciki da Jin hakan daga gareki Fatima,Koda bansamu iyayena ba a rayuwa inada ke nasan bazaki gujeniba".. "Ki tayani adduar samun mahaifiyata a raye,idan hakan ya kasance to karki Kuma Kiran kanki marainiya don itace uwa a garemu nidake"... Bilkisu zatayi magana wayar Fatima ta hau ringing,da sauri ta duba number yarima ce baro baro a fuskar wayar, "Ranka ya dade nawan nikadai?"tace cike da kissa, A kausashe yayi magana "Ina kika shiga?na aika saude nemanki a sashin hajiya Wai bakya Nan?".. "Ina zanje mijina?Wanda ya wuce sashen uwata?umm?me kakeda bukata ne!" "Kizo kawai inason magana dake kafin mutafi gida"... "Angama ranka ya dade?"Tai murmushi ta datse wayar ta juyo ga bilkisu wadda ke binta da kallo cike da shaawa da burgewa, "Yar uwata Mai gida yayi Kira Bari inje inji wace rigimar ce kuma?Dan Naga hakan a idanuwansa tunda muka fito fada" Murmushi bilkisu tayi "to me Miji?wato kin Zama Mara kunya ko? hmmm aje a lallasheshi"... Sukai sallama fatima ta fice a gaggauce ta nufi sashen yarima zaituna na biye da ita, ******** "Wani daliline yasa kika cewa Mai martaba ya sassauta hukuncin da yayi niyyar dauka akan azzaluman?"yace a fusace, Rungumesa tayi jikinta Tana shafa fuskarsa a hankali idanuwanta kirrr akansa "bazanso ace ta sanadiyyata an yakewa surukata hukunci Mai tsauriba saboda hajiya karama uwace a gareni uwa ta gari,batada wasu laifi cikin abinda ya faru Amma nasan Babu yadda zaayi sarki ya yanke hukunci batare da itaba nikuma bazan iya juran hakan ba shiyasa kawai na sadaukar da farin cikina don surukata"ta karashe maganar tana kallon kwayar idonsa Wanda shima ya kafeta da Ido, Jikinsa ne yayi sanyi da Jin furucin Fatima Wanda tabbas yasan maganarta a Kan hanya take,idan kuwa hakane Fatima tayi Masa halarci dikda irin wulakanci da cin kashin da akayi Mata, Muryarsa a sanyaye yace "gaskiya samun irinki a wanan zamanin abune Mai matukar wuya bintu,dikda irin rashin adalcin da akayi Miki akayiwa mahaifiyatki dama tasameki Wanda Zaki iya samun farin ciki idan Mai martaba ya yanke hukunci Amma kika gwammaci ki yafe don mahaifiyata....nagode..." Shhhhhhhhh tasa yatsanta Akan bakinsa "karkace komi habeeby,don Nima kayimun abinda harabada banida abinda zan biyaka dashi,don haka banida riba idan na Bari an wulakanta mahaifiyarka a matsayinta na matar sarki"Tana karashe maganar ta kankamesa ta hade bakinsa da nata ta shiga aika Masa da sakwannin wadanda suka gigitashi a wanan lokaci,Nan da Nan jikinsa ya saki abubuwa suka shiga yawo a dik sassan jikinsa, Sun dauki lokaci a haka kafin ta zare bakinta daga NASA Tana dubansa yadda dik jikinsa ya saki idanuwansa suka kankance,Shirin kwacewa takeyi ya janyota, "Dakata malam ka manta?bafa girkina bane umm?Kar muzo mu aikata Haram kayi hakuri kaji?"ta kashe Masa Ido ta janye jikinta Tai waje abinta Tana dariya kasa kasa ya fadi jagwaf Akan kujera Yana maida numfashi.. ******** "Hmmm tsuguni Bata Kare Mana ba hajiya nikam na tsorata da wanan lamari Domin tabbas inada yakini akan gaskiya zata bayyana Dan wanan hoto fa ba hadashi akayi ba?" "Idan gaskiya ta bayyana an gabatar da matar da sukace din shin kinada tabbacin zaasamu ita zahraun ne?ai inhar baasamu dangin zahrau ba baasanetaba to Dole sarki yayi watsi da lamarin" Gauron numfashi hajiya rahina ta sauke "nikam hajiya inada tabbacin sarki ya watsar da maganar ne yayi bakan saboda jin munada yawa wadanda bamu yardaba Amma ya rigada ya amince da zancen Fatima diyar zahrau ce Dan kinjifa abinda ya fada" "Naji sai me?Wai har yanzun rahina bakisan abinda duniya ke cikiba koh?wallahi wallahi makirci suka hada Babu wata Mata da tabasu hoto da rubutu a ciki,tunda kikaga shegiyar ta janye da wuri harda cewa kqda ayi Mana hukunci" Fatima har zatayi hanyar dakin mama karama ta juya ta nufi sashin hajiya babba,batare da wata fargaba ko tsoroba ta daure fuskarta tamkar Bata taba dariya ba ta tura kofar bakinta dauke da sallama ta shiga, Deejahmah wadda ke gefe ta rafka tagumi ganin fatima yasata saurin gyara zamanta Tana binta da kallo cike da faduwar gaba, Tsaye tayi tana binsu da kallo daya bayan daya batare da tace uffan ba, Hajiya babba wadda ke faman kada kafa Tana girgiza hade da yamutsa fuska ta dubi Fatima shekeke tace "rasa kunya beran tanka?kinzo ne kiyi Mana Rashin kunya savida Rashin samun saa da kikayi?".. "Ke kike ganin haka a Rashin samun saa hajiya safiya?" Yadda ta Kira sunan a gadarance yasa dukkansu suka dubeta cike da tsananin mamaki, "Saa Tana gareni hajiya safiya,bakomi bane kake samunsa a take batare da kasamu kalubale ko Shan wahala ba,Dan haka ki fara shirya cin kashinki da hannunki Dan saina shayar dake mamaki" . "Bakida wani karfi da Zaki iya shayar Dani mamaki fatima,saboda nidin ba Saar wasanki bace ba tsararki bace,ita uwar takima Bata iya daniba balle ke da Rana daya zan kulla abinda zan Gama dake....tsoro ne yasa kika dakatar da Mai martaba wajen daukar hukuncin da yayi niyya,saboda ke kanki kina gudun makircin da kuka kulla Kar asirinki ya tonu a Gane cewa hada hoto kukayi" Dariya sosai maganar hajiya babba tabawa Fatima ta shiga kyalkyala mata dariya cike da shakiyanci Tana nunata da yatsa, "Yanzun gashi kince uwata ta gagara zaman gidan Nan saboda azabarki yanzun kuma kince makirci muka hada to kinsan cewa kenan uwar tawa Dana gabatar ita ta haifeni kenan Amma kike fadin makirci?".. Zuface take karyowa hajiya rahina sai faman zare Ido takeyi cike da rashin gaskiya "ke Fatima me kikazo kiyi Mana anan?rashin kunya ko cin mutuncin? "Wanan zufar da kikeyi da zare Ido ya nuna alamar kina cikin tashin hankali Domin tun a fada kike yinsu,shiyasa ma no banida lokacin tsayawa sainsa dake rahina".. Fatima na Gama fadin hakan ta juya ga hajiya babba wadda ko motsi Fatima tayi sai taji gabanta na faduwa Amma saboda jarumta irin Tata takasa gasgata cewa tsoron yarinyar takeyi, "Hajiya safiya na dawo gareki ba tsoro bane yasa na janye Akan hukuncin da Mai martaba yayi niyyar yi muku,arzikin surukata kukaci Dan bazan iya Bari ta tozarta a idon duniya ba yin hakan da nayi na siya Mata mutunci da kima ne Amma indanku ne baki sarki ya watsaku a kurkuku ba ya azabtar daku har ku mutu,....Sanan Ina meyi muku albishir da nidakaina zan hukuntaku ni zan wulakantaku kamar yadda kuka wulakanta mun mahaifiyar sai kunyi danasanin aikata hakan"....Tana karashe maganarta Bata jira cewarsu ba ta fice zuciyarta na yi Mata tsananin zafi, Karo sukai da yarima lokacinda ta fito sashen hajiya babba don dik abinda ya faru Yana sauraronsu kuma yaji Dadi da take maida musu da martani, Ruko hannunta yayi ganin zata wuceshi batare da tace komiba "Ina zakije?"cakk ta tsaya batare da tace komiba, "Yamma tayi kuzo mu wuce gida".. "Zanyi sallama da ummu da hajiya" "Ok kitura zaituna ta Kira mun deejahmah mu wuce".... Ta gyada Masa Kai batare da tace komiba Tai gaba abinta, Kuka sosai deejahmah keyi saboda tsananin takaicin abinda ya faru dik jikinta yayi sanyi ga tsoron Fatima daya darsu cikin zuciyarta, "Banaso ki karaya khadeejah kisawa zuciyarki jarumta zakici ribar rayuwa,karki kuskura yarinya karama taci galaba akanki".. Ta jinjina Kai hade da share hawayenta,...zaituna ce tayi sallama ta isar Mata da sakon yarima ta fice...itama bada jimawa ba ta kimtsa ta gyara fuskarta ta fito suka tafi... ******** Da dawowarsu gida Fatima ta fada sashenta ta rufo kofa kowa bangarensa ya nufa,.. Wanka tayi ta fito ta bude wardrobe dinta ta Shiga dube duben kayan da takeso ta Sanya,.... Shiru tayi tsaye tana daure da towel lokacinda wasu Kaya suka Fado Mata Wanda ummu ta Aiko Mata dasu bayan abkawota da kwana biyu, Da sauri ta bude side drawer dinta na gefen gado ta Ciro katuwar jakar ledar da tunda aka kawo Bata budeba ta Shiga zazzage kayan ciki,abinda taganine ya Bata mamaki da dariya savoda kananan Kaya ummu ta siya Mata masu shegen kyau da tsada ta Shiga budesu daya bayan daya harta Kai hannunta Kan wata Yar doguwar Rigar da bazata wuce Mata iya cinyoyinta ba ta ajiyeta a gefe, Ta maida sauran kayan ta ajiye a gefen gadonta ta dauki rigar tasa dakyar ta kugata a jikinta ta shige saboda robace, Rigace Mai shegen kyau da rubutu I love u a gaban rigar wadanda akayi su da kalar baki,.. juyi sosai tayi tana kallon kanta,lokaci daya tasa hannunta ta rufe fuskarta Tana dariya Dan ita kanta tabawa kanta kunya, Ta Dade gaban madubi Tana shafe shafen turarruka kala kala a jikinta ciki harda Wanda ummu ta Aiko Mata dashi ta baza gashinta a bayanta Tai masifar kyau tamkar wata baturiya, Wayar ta tadauka da earpiece dinta ta makala a kunnenta wayar na rike a hannunta ta fito ta rufo kofarta, Dakyar take taka kafarta ta sauka cike da yanga ta karasa parlorn lokacin deejahmah na zaune gefen yarima ta Dora kanta a kafadarsa, Kamshin turarenta ne ya kauraye wajen shi yaja hankalinsu gabaki daya suka maida dubansu gareta, Wani irin kallo take jifan yarima dashi Sanan ta sauke Masa Kaya taccen murmushi tayi mishi throwing kiss ummuaahhhh ta kashe Masa Ido ta juya cike da kwankwasa ta zauna a kujerar dake kusa da tasu ta Dora kafa daya Kan daya, Dakyar yaja numfashinsa dake kokarin kwace Masa saboda wanan sako da Fatima ta aika Masa ya nemi natsuwarsa ya rasa, Wayarta ta rike Tana tattabawa Sanan ta dago Kai a karo na biyu,..."ranka ya dade nifa banason kallo ga matarka a jikinka Amma idonka na kaina?"a shagwabe tati maganar ta turo babki, Sosai abubuwan da Fatima keyi yakeba yarima mamaki saboda gabaki daya ta sauya a yadda yasanta, Wayancewa yayi ya Dan kalli deejshmah yaga itama shi take kallo, "Bintu ke dawani Ido kika kalleni zakice na kalleki?" "Abin ne da mamaki bayan ga matarka a jikinka kana Bina da kallo ,in gaskiya ne ka kalleta Mana" Shan murrr yayi ganin Fatima nayin maganar cike da gayya ga yadda deejahmah ta cika ta batse, Hararta yayi hade dayi Mata kallon zamu hadu, Makale kafada tayi "nidai ah ah banso dik ka Gama luguiguitani bayan kasan wanna abun bazai yuwuba tunda ba girkina bane shiyasa ma yau bazakamun rakiya daki ba"da gayya tayi maganar, Kasa boye kishinta Deejahmaj tayi Tai saurin cire kanta daga kafadarsa Tana kallonsu daya bayan daya zuciyarta na tafarfasa ,wato dama munafuntarta sukeyi a kwananta suke makalewa suna soyayya?idanuwanta suka kawo ruwa ta kallesa Ido cikin ido Yana hango Yar kwallar dake Shirin zubo Mata Tai tafiyarta a fusace, Toshe bakinta Fatima tayi tana Yar dariya cike da mugunta da gayya, Tasowa yayi yayo kanta a guje ya Mike suka Shiga zagaye parlon Tana kyalkyala dariya tun baya dariya shima ya Shiga yin dariyar ta bullo ta bayan kujera Tana Shirin Hawa sama ya cafketa ta fada jikinsa Tana dariya sosai, "Haba bintu meyasa kikeyin irin haka umm?so kikeyi kisawa diyar mutane hawan jini?Babu kyau fa Kinga yanzun kin hadamu"ya kashe Mata ido, Turo baki tayi kadan ta hararesa "to tunda bakason bacin ranta sai kaje ka lallasheta ai ramawa nayi"ta Dan hararesa Tana ture hannunsa daga jikinta, Ya Kara rungumota jikinsa Yana shinshina wuyanta zuwa kirjinta Yana shafata,sanan ya dago kansa Yana dubanta,"ya kikeso inyi umm?Wai kinsan menakeji kuwa?".. Kashe Masa Ido daya tayi "mekakeji?".. "Ina muradin zumarki bintu" Rufe idanuwanta tayi cike da kunya Tana murmushi,shima murmushin yakeyi ya dagata cakkk Yana juyi da ita a cikin parlon tanata famar dariya sanan ya sauketa a kujera Yana maida numfashi, ******* Jingina tayi da jikin kofar dakinta ta rufe idanuwanta hawaye na ambaliya a idanuwanta, Dafe kirji deejahmah tayi saboda yadda take Jin zuciyarta nayi Mata suka tamkar Ana tsira Mata allura a kirji,..kuka sosai takeyi me ban tausayi data rufe idanuwanta yarima take gani lokacinda yake wurgawa Fatima kallon soyayya, Wani irin abune yake Shirin samunta a rayuwa ya zatayi da sonsa bayan zuciyarsa na can wani waje daban? Kuka sosai takeyi meban tausayi taji kamar Ana kwankwasa Mata kofa, Da sauri ta share hawayenta ta say hannu ta murda key din ta bude, Ganinsa ya sata saurin bashi hanya ya wuce ta gefenta ta rufo kofar, Kallonta kawai yakeyi yadda dik ta sauya Sanan daga ganin idanuwanta tayi kuka sai tabashi tausayi, "Deejah" "Naam"ta amsa hade da kallonsa lokaci daya ta kauda kanta gefe gabanta na faduwa,.. "Meke damunki ne?" "Meka gani?babukomi kawai na shigo nadan kwantane" Sai kawai ta kauda kanta ta Haye gado,ya juya a sanyaye ya Haye gadon ya janyota jikinsa ya rungumeta yaana shafa kanta... ****** Da ruwan sama aka wayi gari Dan haka basu tashi da wuriba har karfe daya saura na Rana Sanan Suka hadu a wajen breakfast, "Ki gaggautafa bintu banso muyi yamma Dan inaso muje gidan matar Nan don muga yadda zaayi" Sauri sauri sukai breakfast suka shirya suka fice a gidan.. ****** Basu Bata lokaciba wajen Isa gidan inda yarima yake directing driver har unguwar, Bayan sun gabatar Mata da kansu ne ta jinjina kanta Tana Dan murmushi "ai naganeku yara karku damu meke tafe daku?" Yarima ne yayi magana "dama Mai martaba ne yakeda bukatar Karin bayani akan wanan hoton da baiwar allahr Nan da kikace a gidan Nan ta haihu shine mukazo,gashi Kuma kince Wanda ya kawota ya rasu" "Tohhhh nidai banida wani cikakken Karin bayani saidai a bisa alamu da bayaninku ya nuna cewa baa gamsu da maganar Ku ba koh?to Waqa a bakin me ita yafi Dadi dikda cewa akwai alkawari a tsakanina da malam sani suleman shi Wanda yasan komi dangane da yarinyar" Kuri sukai suna kallonta hade da saurarenta dik zuciyoyinsu cike suke da tsoron abinda zata fada, "A gaskiya yara malam sani ba mutuwa yayi ba tashi yayi daganan yabar garin gabaki daya,kafin yabar garin ne yabarmun sallahu Akan yasan koba Dade koba Jima zaazo nemansa tunda da hannunsa ya dauketa yakai gidan marayu shiyasa saboda bayaso wani Abu ya faru yasa yace dik Wanda yazo ince mutuwa yayi Amma hakikanim gaskiya be mutuba Yana Nan da ransa Yana can wani kauye gabanmu".. Bakin yarima har rawa yakeyi wajen fadin "mama ki tabbatar da abinda kike fada?kin tabbatar da cewa shi ya Riki mahaifiyar yarinyar Nan?" "Kwarai dagaske yaro".. "Yanzun ya zaayi musameshi Sanan idan munsameshi akwai hujjoji da zasu nuna cewa shidin ya riketa?".. "Zaku iya samu yaro Sanan ni zan taimaka muku kusameshi din" Jikin Fatima a sanyaye tace "mungode mama" Mikewa tsohuwar Nan tayi ta Shiga ciki ta dauko hijabinta ta fito tasa Sanan ta dauki takalmin a slipas tasa a kafarta "muje" Shine abinda tace musu dukkansu suka Mike a tare suna gaba Tana binsu a baya,... ******** Mai martaba ne zaune a parlonsa gabansa jakadiyarsa ce gefensa Kuma wani Dan matashin yaro ne sanye da jajayen Kaya irin na dogarawan gidan Yana gurfane, Kofi sarki ya dauka ya kurbi ruwa ya ajiye a gefensa Sanan yayi Dan gyaran murya, "Maga takadda kace kaje can gidan tsohon limamin garin Nan kayi bincike Akan abinda nasaka?" "Ehh ranka ya Dade nayi bincike abinda nasamo shine sunbar garin Nan tun shekarun baya saidai inada labari Akan dik wata suna zuwa Kuma suna sauka a wanan gidan nasu " "Yanzun rabonsu da garin kwana nawa kenan a binciken ka?" "Kwana goma Sha hudu kenan kaga a lissafi saura kwana goma Sha hudu Nan gaba".. Jimmm kadan Mai martaba yayi "sati biyu kamar yau ne idan Allah ya kaimu".... ****** "Yanzun meke tafe daku me kukeso a wajena da kuka kwaso jiki kukazo?" "Taimakon mu mukeso kayi yadda Allah ya taimakeka" Dan dattijon ya sauya fuskarsa "nifa banason ku kaini inda zaa hallakani a banza gara ku fadamun gaskiyar lamari Dan ni inajin tsoron Kar ace wanan baiwar Allah laifi tayo dama daga garinsu tazo wajena na amsheta ya zamemun matsala" "Babu wata matsala sai alheri baba ka taimaka Mana kazo muje a warware wannan matsalar Dan Allah".... Shiru yayi Yana Dan tunani ,Fatima kuwa dik hankalinta ya Gama tashi, "Injidai idan nakawo bayani shikenan zaa kyaleni indawo?".. "Insha Allahu"cewar yarima cike da kosawa Yana duban yadda garin ya hade da hadari... "Muje to Allah ya bamu saa" "Ameen"suka hada bakinsu , a tare suka yunkura harda wanan tsohuwa suka nufi motar su yarima.... *Muje zuwa* *SLIMZY😍* [9/2, 20:09] 🥰slimzy🥰: 🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* 47 Basu iso gidan Mai martaba ba sai bayan sallar magriba, Sai bayan an idar da sallah Sanan Mai martaba ya umarci sarkin fada da yayi Masa Kiran iyalansa dake cikin gidan,haka kuwa akayi hajiya babba da mama karama da afnan da khausar tare da yarima sai Fatima dake wajen dik suna zazzaune, Gyaran murya Mai martaba yayi ya dubi malam sani dake gurfane Yana faman hada zufa saboda tsananin furgici da yake ciki a wanan lokacin, Gyaran murya Mai martaba yayi Sanan yace "malam sani sunanka bawan Allah?" Gabansa ya fadi ya Kara rusunawa "ehh ranka ya Dade sunana kenan"ya fada a furgice, Ganin yadda dik ya tsure yasa sarki sassauta murya "ka kwantar da hankalinka bawan Allah Nan masarautace Mai cike da adalci da kaunar talakawa Dan haka Babu abinda kayi Babu abinda zaayi maka cikakken bayani mukeso kawai kayi Mana game da wanan baiwar allahr dake cikin hoton Nan"ya mikawa malam sani hoto,....jiki na rawa ya karbi hoton ya Kara dubawa, Sarkin fada dake gefe yace "ka natsu kayiwa sarki bayani kadaina rawar jiki a gaban Mai martaba kake" Shiru yayi na Dan wani lokaci yayinda parlon yayi tsit bakajin karar komi sai fanka, Wata Rana, "Na fito gabanin sallah asuba ta lungun dake jikin gidana dan zuwa masallaci sallah kawai cikin duhu na hangi mace tsaye ta raba hanya da tsohon ciki a jikinta farko na tsorata Dan tunani nayi ko gamo nayi Ina rike da carbina sai na Soma Kiran sunan Allah Ina kokarin karasawa inda take, Tsayawa nayi daf da ita dikda tsananin tsoron da nake ciki be hanani yin jarumtar bude baki inyi Mata magana ba, "Assalamu alaikum"...shine abinda na ce Mata sai Naga yadda ta waigo gareni a furgice tamkar wadda ta samu tabin hankali Tana neman hanyar gudu yayinda lokaci daya take fadin, "Dan Allah kada ka kasheni ka taimakeni sun biyoni abinda ke cikina sukeso su cire su kasheshi ni Kuma Ina son abuna bawan Allah ka taimakeni Kila Allah ne ya jehoka cikin rayuwata Dan ka Taimakeni"....Tana maganar ne Tana waige waige ta furgice tamkar me neman wani Abu, "Ina fatan mutum ce ke ba aljanah ba"....da sauri ta amsa da , "Ni mutum ce kamarka ka taimakeni bawan Allah " "Ki kwantar da hankalinki zan taimakeki Amma da sharadi Akan bazan taimakekiba daga baya ni kizo ki saka mun da sharrri daga taimako Dan duniyar yanzun abin tsoroce"sai kawai ta fashe mun da kuka harda durkusawa kasa Tana fadin "wallahi bazan saka maka da sharrri ba sai alheri bawan Allah ka rufamin asiri" Jinjina Mata Kai nayi dikda zuciyata dake waswasi akanta Amma hakan be hanani samun karfin gwiwar Taimaka Mata ba nan nayi Mata umarni da ta tashi muje gidana inkaita Dan anata kiraye kirayen sallahr asuba ta Mike Babu musu ta bini muna tafe Tana sharar hawaye har gidana na kaita wajen matata shaawa, "Shaawa!" Da sauri matata ta fito daga daki Tana fadin "malam ko kayi mantuwa ne gashi anata Kiran sallahr asuba"...Bata karasa zamcenta ba ganina da mace yasa Tai shiru Tana Bina da kallon tuhuma da tambayea, "Ki ajiyeta har indawo masallaci"shine abinda nace Mata na juya abuna inda ta Kama hannun wanan baiwar allahr suka Shiga ciki, Bayan na dawo sallahr asuba ne na taddata Kan dadduma itama tayi sallahr suna zaune da matata Tana Bata labari Akan ita din matar sarki ce tsangwama da azaba ya korota daga masarautar su take bamu labarin irin azabar da Tasha na baaso ta haifi cikin jikinta,mun matukar tausaya Mata nida matata inda mukai Mata alkawarin riketa har ta haihu tunda muma ba karfi garemuba,ni lebura ne matata Kuma Tana kitso Tana wanki da guga dashi muke ci da kanmu tunda ba yara Allah ya bamu ba, Malama zahrau tunda taga sanaar da matata keyi dikda cikin dake jikinta ta zage Tana wanki da gugar Nan itama saboda zaman haka har cikinta ya Shiga watan haihuwa, Wata ranan alhamis da asuba ta wayi gari da ciwon nakuda Mai tsanani gashi bamuda yadda zamuyi mukaita asibiti muna tsoron mu kaita mu hadu da wani nata Dan haka sai muka yanke shawarar ajiyeta a gida ta haihu kawai sai Mai dakina ta Kira wata makociyarmu da tayi karatun likitanci cikin ikon Allah Bata dauki lokaciba Tana nakuda ta haifi yarta mace kyakkyawa kamar ta farin ciki wajen wannan baiwar Allah baa magana, Bayan an gyarata komi ya Lafa suna zaune Yar na nade cikin tsumman zani wasu Yan riguna ta siya Wanda su akasawa yar dagasu batada wasu kayan saita yanke shawarar Ciro Dan kunnen zinari na kunnenta ta mikawa Mai dakina "amshi wanan a Saida idan yaso sai a sissiyi abinda bamu dashi harda kayan abinci dik mu siya Naga zaifi koh?" Shiru Mai dakina tayi Sanan ta sauke ajiyar zuciya "Niko zahrau da kinbar dan kunneki ko saboda gaba Kila Zaki bukaci wani taimako" Hawaye ke gudu a fuskarta cikin kuka tace"Babu wani Abu da nakeda bukata a yanzun sama da mijina Amma ya rigada yayimun nisa banida wani Abu da zanyi yanzun Dan idan nakoma kasheni zaayi da Yar Dana Haifa Dan haka kada kidamu a Saida akwai Allah " Shaawa Mai dakina ta Dade Tana jinjina lamarin kafin daga baya ta hakura ta shirya ta je kasuwa ta Saida wanan dankunnen da ta Saida da kudi masu yawan gaske, Sosai tayo siyayya ta dawo Mata da Yan canjin Wanda shi muke kashewa muke cefane har ranan suna inda tace tanaso yarta taci sunanta haka yarinya ta amsa sunan Fatima tun daganan rayuwa ta cigaba Mana yau fari gobe baki har ta shekara uku da watanni a hannun mu zuwa wannan lokacin zahrau ta saba da jamaa tasamu Dan aaikinta Tana zuwa wani waje inda Nan ne take samu ta ciyar da kanta da Dan abinda baa rasaba na rayuwa, Bayan watanni zahrau ta bukaci tanaso taje wajen iyayenta ta gansu ta sheda musu Tana da Rai ta roki me dakina Akan ta rike Mata Fatima zuwa sati daya zatayi ta dawo Babu musu shaawa ta amince tunda sun Saba sosai kuma Yar Tata akwai hakuri batada kyuya Dan ko aiki zataje gida take barinta, Tun bayan tafiyar zahrau abubuwa suka rikice Mana ciki kuwa har da rashin lafiyar da Mai dakina tayi inda bamuda wani hanyar samun kudi saidai idan na fita na roro abinda nasamu indawo muci abinci Babu wani Wanda ke kula da Fatima kullum yarinyar saidai ta rinka ambatar maamah yadda take Kiran mahaifiyarta sai ta bani tausayi komi nikeyi musu har takai ta kawo ko fita banayi Ina gida ga dawainiyar matata gata Fatima gashi zahrau kusan wata biyu da tafiyarta Bata dawoba haka muke rayuwa yau fari gobe baki har matata tasamu lafiya muka cigaba da rukon Fatima har kusan wata takwas zahrau Bata dawoba sai abun duniya ya fara damunmu Domin kanwar Mai dakina da tazo cewa tayi zahrau Kila cikin shege tayi tazo ta haife Mana ta gudu tunda baa shedar mutum Sanan abinda ya Kara sawa muka gasgata hakan kafin tafiyar xahrau sunyi hoto da Yar Tata Tai rubutu a jiki tabawa Mai dakina tace saboda halin rayuwa Dan haka Koda kanwar shaawa ta Fadi hakan sai muka gasgata hankalinmu ba karamin tashi yayi ba a wanan lokacin musamman ni Dan Saida mukaso samun matsala da matata da halinsu na Mata cewa tayi wayasani ko hada baki mukayi ta gudu tabar Mata yarta Dan haka Dole cikin biyu inyi daya kodai indauki yarinyar Nan inkaita wajen uwarta tunda nasanta ko Kuma ta hada kayanta tabar gari idan taje garinmu zatace ai ciki nayiwa wata na shege ta haifamun ya Dan haka Dole in San nayi da Yar Dan Saida yakai ko taba Yar Mai dakina ta dainayi tunda Taji wanan zance Fatima saita wuni da yunwa bataci komiba saidai Shan hannu da takeyi idan tasa yatsanta a kofar daki Tana tsotso saitayi bacci sau uku gashi dik yunwar da takeji Bata kuka, Na Shiga tsananin tashin hankali Wanda shine dalilin da yasa na shirya yarinyar na nufi wajen abokina malam isyaku maaikacin gidan marayu na nemi shawararsa yace a Mika yarinyar gidan marayu kawai tunda Nan zata samu kulawa Dan Ina gudun indauki yarinyar imba wani tazo ta Shiga wani Hali, Har hoto na dauka da Fatima lokacin da nakaita ta Dade a jikina Ina jimami Ina sharar kwalla Dana kalleta Tana Shan hannu saita cire tace baba sai infashe da kuka saboda tsananin tausayinta....Koda na kaita nasa hannu nabada adreshina Amma banfadi cewar nasan mahaifiyarta ba, Dakyar muka rabu da yata Fatima Tana kuka inayi nabarota can Ina zuwa gida na shaidawa matata sai Kuma Taji dik Babu Dadi Dan tasaba da yarinyar gudun abinda zaije ya dawo takeyi Dan haka bamu dadeba aka Aiko inkoma kauyenmu inda Nan ne suka daukoni, Sai na sa gidana a kasuwa tunda karamine dama shine wanan baiwar allahr ta siya kafin mubar garin na damka Mata hoton Fatima da mahaifiyarta Sanan na gargadeta Akan karta kuskura tace tasan inda nake dam cewa nayi tace mutuwa nayi..... Yana kaiwa Nan ya tsagaita da labarinsa ya sunkuyar da kansa kasa inda yakeji tamkar zaiyi kwalla da ya tuno da abinda ya faru baya, Kowa a wajen jikinsa yayi sanyi harda Mai martaba saida ya jinjina lamarin, "Malam sani kayi namijin kokari wajen ajiye mace a gidanka har ta haife abinda ke cikinta tayi shekaru tare da Kai batare da kasan wani nata ba,da badan kaddara data gifta zahrau tabar gidanba Kila da ka cigaba da rayuwa da ita.....lallai abin a jinjina maka ne a yaba maka mungode allah ya saka da alheri" Dukkansu suka amsa da "ameen"... Shiru na Dan wani lokaci Sanan Mai martaba ya cigaba da magana "malam sani zaka koma garinku dama abinda muke bukata muji komi daga bakinka munkumaji mungode Sanan Ina Mai sheda maka a bisa wannan halarcin da kayi Mana Mai martaba sarki ya baka kyautar wajen xama a cikin gari tare da kayan abinci da Kuma tsabar kudi dubu dari biyar" Dan murna malam sani fashewa yayi da kuka Yana xubawa Mai martaba godiya,itama tsohuwar data kaisu gidan malam sani sarki yayi Mata kyautar makudan kudi...Sanan ya bada mota yace a maidasu kauyensu..... Bayan tafiyarsu ne Mai martaba yace "na aika a bincikamum dangin malam liman wato dangin mahaifiyar Fatima dazu".... Da sauri Fatima ta dago kanta Tana kallon Mai martaba ko kiftawa batayi sai faduwar gaba da take faman yi, "A bisa binciken da akayi shine iyayen zahrau Allah ya axurtasu yanzun basa Zama a Nan kasar suna can wata kasa Dan haka basa zuwa Nan sai karshen ko wani wata suke zuwa suyi kwana uku,Dan aikena ya sanarmun da cewar satinsu biyu kenan da barin garin kunga kenam sai ndn da sati biyu zasu dawo Dan haka sai mu cigaba da addua Allah yasa asamu labarin zahrau ko a wajensu" Wani irin numfashi Fatima ta sauke yayinda ta sunkuyar da kanta jiki a sanyaye kwalla cike da idanuwanta da tunani kala kala..... Basu sukabar gidan Mai martaba ba sai Sha daya saura na dare suna tare da ummu, ******* Tafe suke a mota yarima ya ruko hannunta kamm ya janyota jikinsa Yana shafa fuskarta yasa bakinsa daidai bakinta ya furta a hankali "kinsan fa yau zandawo dakinki koh?me kika shiryamun?....tura Masa baki tayi idonta akansa batare da tace komiba, "Sarauta kikejine?umm?bintu kiyimun magana Mana"ya karashe maganar Yana tallabo kanta da Kai Mata light kiss a lips dinta,dai dai Nan mota tayi parking alamar sun iso, Kaiwa da komowa kawai deejahmah keyi Tana leken hanya Dan ganin ta inda xasu bullo Amma Basu dawoba yanzun ma tsaye take a window a sama Tana hango lokacin da mota ta shigo gate din gidansu teyi parking a parking space, Koda suka fito Fatima tsaye tayi batare da ta motsa ba Tana Bata fuskarta, Sassauto da muryarsa yayi ya rada Mata "menene sarauniya Fatima"... Kauda kanta gefe tayi "ni da'ukata zakayi"tace Tana hada Rai tamkar zatayi kuka, Dariya kawai yayi "toh babyna muje"cakkk ya dauketa ya rungumeta a jikinsa hannunsa na rike da wayarsa suka shigo gidan, Da sallamarsa suka shigo lokacin ta sauko Tana zaune a parlor fuskarta ta Dan kumbura tamkar wadda ta wuni Tana kuka, A shagwabe Fatima tace"saukeni a Nan yunwa nakeji kmr zanci Babu"Dan kallonta yayi ya kashe Mata ido sanan ya sauketa a kujera ya zauna a kujerar "Gaskiya baby kin Kara nauyi Wai kinji nauyinki kuwa?" "Kai habeeby Nan har wani nauyi gareni?"tace hade da hararsa ta dubi zaituna dake zaune ta takwashe kafa "Ke me kuka dafa ne?"Tana yatsina fuska Tai maganar, "Ranki ya dade shinkafa da Miya ce da farfesun Naman kaza sai juice din lemo da saratu ta hada" "Jeki hadomin" Deejahmah na zaune tamkar an dasata dik abinda sukeyi Tana satar kallonsu saidai ta maida idonta akan tv tamkar Tana fahimtar wani Abu, Yarima ne ya taso daga kujerarsa ya dawo gefenta ya zauna ya Dan tabata da hannunsa "bakiga mindawo bane Babu ko sannu da hanya?"ya tsareta da idanuwansa, Kallon da yakeyi Mata ya saukar Mata da kasala dakyar ta bude baki Tana wurga Masa wani kallo Mai cike da sakwanni tace "jira nakeyi kugama sai inyi muku barka da zuwa ranka ya dade na tuba"a sanyaye tayi maganar tana rike kunnuwanta, Itadai Fatima na gefe Tana faman aika abinci a cikinta tamkar Bata San dasu ba, "Deejah kinsan kinfita girki yau ko?to Dan haka yanzun zaku fara exchanging ranan girki Dan haka nace dama San sanar daku ba neman izininku nakeyiba na yanke shawarar kowa kwana biyu biyu zata rinkayi Dan haka Naga ya Dace" Murmushi deejahmah tayi hade da jinjina Masa Kai"toh shikenan"..kallon yanayinta yakeyi itama kallonsa takeyi haka kawai a Yan kwanakin nan ta canja dikda basa shiri da Fatima Amma tausayi take bashi, Tabe baki Fatima tayi lokacin data dubesu taga yanayinsu take taji wani kishi ya taso Mata saita danne ta ajiye plate din abincin, ta jingina kanta da jikin kujera, Mikewa yarima yayi ya nufi sashensa, Su biyu ne a parlon lokacinda Fatima ta Soma gyangyadi saboda gajiya, Dan tsaki deejahmah tayi Wanda shine ya farkar da Fatima daga baccin daya kwasheta sukai Ido hudu deejahmah ta watsa Mata harara, Dagowa Fatima tayi tana mutsika Ido sanan ta gyara zama "Ina fatan bani kikayiwa tsaki ba"...ta tsare deejahmah da Ido, "Idan ke nayiwa fa Zaki bugenine?diyar matsiyata?" "Karki kuskura kice Zaki zageni Dan wanan lokacin ya wuce na zagina Dan zuwa yanzun kinsan ubana kinsan waye matsiyaci tsakanin ubana da galadima" "Fatima ni kike zagi?ubana kike zagi?" Kallonta Fatima keyi Ido cikin ido "bancikaso Ina hada numfashi dake ba deejahmah Dan akwai banbanci tskanim Yar sarki Yar na gada da Yar galadima masu karfa karfa,da kin kwantar da hankalinki kinyi biyayya kinbini a hankali Dan kada inyi sanadiyyar da zaa tsige tsohonki daga rawani" "Ke har kin Isa kisa a tsige mahaifina a mulki?" Kasa Fatima tayi da murya Tana murmushin mugunta "kin manta mulki gabaki daya a gidanmu yake? kefa uwarki CE gidan Niko gabaki daya ubana keda sarautar garin Kinga akwai banbanci inada damar da zan roki Mai martaba ya tsige galadima cikin sauki kugewa Allah vanzo a namijiba Dan Allah banason hayaniya daddaren Nan".... Yarima ne ya shigo sanye da kayan bacci "baby Hira kukeyi ne?"... "Ehh wallahi habeeby tambayarta nakeyi " Kallon yanayin deejahmah yarima yayi yasan akwai magana Amma sai ya basar kawai ya mikawa Fatima hannu ta rukoshi ya dagata yasa a kafadarsa,Tana dariya kasa kasa "idan kintashi ki kashe kayan wutan zan kwanta ne Saida safe"Yana karasa maganarsa ya wuce, Lallai Kabir ya Raina Mata wayau wanan wani irin cin Kashi ne sukeyi Mata a gabanta batare da ko damuwa da ita ba,....Dole ta dauki mataki Akan hakan,sanan babban bala'i yadda fatima takeyi Mata gadara tanayi Mata ruwan rashin mutunci.... ******** Bayan kwana uku da faruwar haha, Hajiya babba da rahina suka shirya sukazo wajen deejahmah ganin daki don rabonsu da gidan ita hajiya babba tunda aka kawo deejahmah, Zazzaune suke a parlor suna Yar hirarsu harda su fauziyya sukazo da khausar, Hajiya babba ce ta dubi Deejama "Wai lafiya Naga dik kin rame Kim susuce aure wata daya da kwanaki tamkar Ana dibarki Ana Miya kodai munsamu Dan jika ne?" Murmushi deejahmah tayi "hajiya wallahi babukomi yanzun haka ma period nakeyi wallahi" "To Allah ya kawo kinji?Dan na Matsu ace kece kikafara kawo Mana jika ba waccen shegiyar yarinyar ba rasa kunya".... Ddga bayansu suka jiyo sautin muryar Fatima Tana fadin "idan Allah ya bani sai ku amshe ko Kuma idan kune ke badawa ku hanani"ta cigaba da tsotsa lemon Zaki dake hannunta tazo ta nemi kujera ta zauna ta Dora kafarta daya Kan daya ta dauki remote ta canja Tasha, Dukkansu tamkar anyi ruwa an dauke Babu Wanda ya sake magana Domin zuwa yanzun hajiya babba cike take da fargabar abinda zaije ya dawo ranan da uwar Fatima ta dawo Dan tasan ba karamin rashin mutunci Fatima zatayi misu ba, Zaituna Fatima ta kwalawa Kira tazo da sauri "yi sauri ki kawomin abinci wata sabuwar yunwar nakeji wallahi kamar inci Babu" Yar dariya tayi zaituna "to uwargijiyata angama"ta fice, Koda aka kawowa Fatima yadda takecin abincin ne dukkansu dake gurin yabasu mamaki hannu baka hannu kwarya haka ta share abincin plate daya ta ajiye a Nan ta Dan jingina da kujera ta runtse idanuwanta sai bacci, ********* "Narasa Gane kanki bintu a Yan kwanakin Nan baki samun lokacina kwata kwata,ga yawan fushi da kikeyi wani lokaci har mamaki kike bani banyi Miki komiba zakidau fushin duniya ki dauka Dani haba babyna" Kwantar da kanta tayi a kafadarsa "habeeby Nima bansan meyasa nake hakanba wallahi kayi hakuri kaji?baa son Raina bane kawaidai ni yanzun Babu abinda na hada da abinci" Lakuce hancinta yayi "to acici ai gashinan kinyi kumatu suku suku mazaunanki sum Kara Zama da kyau"ya shafi gefen fuskarta, "Nidai kabari nidai kabari banaso"😩 Toshe bakinsa yayi Yana Mata dariya hade da Kara rungumeta a jikinsa.... ******** Da sassafe sarkin fada ya nufi gidan da a alkawari yau ya cika sati biyu zaije Dan jiya akesa Ran suna dawowa tunda yau biyu ga wata, Kwankwasa kofar gidan yayi da sauri Mai gadi ya bude kofa hade da leko da Kai,ganin sa da rawani da malulmalum irin na masu sarauta yasashi saurin fitowa ya tsaya a kofar gidan, "Kai ranka ya dade wallahi banji dadiba saboda dai ranan da kazo katafi da kwana uku sukazo gidan Nan kamar daga sama sanan sunkai kwana takwas a gari sanan suka tafi Dan yanzun haka kwanansu uku kenan da tafiya Amma abinda nake gani kamar lokacin dawowarsu ya canja ne tunda kamar Mai gidan beda koshin lafiya" Shiru yayi sarkin fada sanan ya sauke numfashi "gaskiya banji dadiba wallahi da kazo ai ka sanar min da dawowar tasu" "Malam bansankabafa a Ina zanyi tunanin ganinka nida nake gadi ko kofar gida bana zuwa" "Daga masarautar barayar Zaki nake" Jinjina Kai dattijon Mai gadi yayi Yana dubansa cike da nazari sanan ya nisa yace "gaskiya kasha wahala Dan zuwanka na biyu kenan Allah beyi haduwarku da masu gidan ba,yanzun taimakon da zanyi maka daya ne" Da sauri sarkin fada ya ruko hannunsa "Ina jinka malam ka taimakeni Dan Allah" "Ka kwantar da hankalinka yamzun ka rubutamin number wayarka dik lokacin da suka duro garin Nam zan nemeka" Da sauri sarkin fada ya Ciro biro a aljihun gaban rigarsa ya zaro ta karda a aljihunsa ya rubuta Masa number waya ya Mika Masa sukai sallama ... ******** Zazzabin da Fatima keyi ba karamin tadawa yarima yayi da hankaliba saboda yadda take tsananin galabaita saboda zafin zazzabi har surutai takeyi Tana ambatar sunan mahaifiyarta Tana fadin a taimaketa a hadata da ita, Hakan ne yasa yarima ya tsorata ya daukota ya kawowa ummu ita ya ajiye, Ahmad ya Kira abokinsa ya dubata yayi Mata Yan gwaje gwaje hade da dibar jininta ya tafi Dashi ya barsu Nan zaune da ummu wadda ke rungume da Fatima a jikinta Tana sauke numfashin wahala dik ta fita hayyacinta, "Niko kabiru gami nake wanan zazzabin kamar ciki Fatima ke dauke dashi Dan gabaki daya yanayinta ya sauya ta koma sakk masu ciki" A sanyaye yarima ya dubi ummu sanan ya kalli Fatima dake sauke numfashi Tana bacci lakadan yace "to nidai ummu banida masaniya Akan hakan sai abinda gwaji ya bamu".... "Allah yasa muji alheri"... "Ameeen" ******"" "Nifa na furgita da kikace Wai Fatima batada lafiya Tana fama da masassara Anya ba ciki ta rigaki yiba?" Gaban deejahmah ya fadi ta Shiga girgiza Kai Tana duban mahaifiyarta "ah ah mama batada ciki insha Allah Fatima bazatayi cikibama kawai dai zazzabi ne" Hmmmm kawai hajiya rahina tayi "to Allah yasa Amma ni Ina tsoron hakan Dan idan Fatima ta rigaki haihuwa mun Shiga uku" Yatsina fuska deejahmah tayi "matar dake wasiyya zata mutu?ai Bata amai balle ace cikine zazzabina me zafi takeyi Tana Kiran sunan uwarta wadda nasan ita da ita sai a kiyamah kila" "Allah yasa kedai Dan wanan yarinyar idan tasamu ciki ai kashinmu ya bushe".. Shiru deejahmah tayi batare da ta Kara cewa komiba ta dauki kofin ruwa ta Sha sanan ta sauya maganar zuwa wata ******** Cikin tsananin farin ciki yarima ya ruko Ahmad "kana nufin Fatima Tana dauke da ciki har na tsawon sati hudu?" Jinjina Masa Kai Ahmad yayi Yana dariya "kwarai dagaske abinda gwajina ya nunamin kenan shine ma ya haifar Mata da wanan zazzabin me zafi Amma ga magunguna Nan Nazo dasu Wanda zasu Dan Sanya jikinta tasamu sauki Taki karfi Kuma" Rungume Ahmad yarima yayi cike da tsananin farin ciki, Ummu dake gefensa sai faraa takeyi bakinta yaki rufuwa tashafa fuskar Fatima ta furta a Fili "lallai kainuwa dashen Allah Bata mutum ba Allah ya inganta Miki wanan ciki" Ta gyara Mata kwanciya ta sa zaituna ta Shiga kitchen ta dafa abinci kafin Fatima ta tashi... ***** Tun safe wayarsa ke ringing Amma yaki daukar wayar ganin bakuwar number ce ya share , A karo na hudu kenan wayarsa na ringing Yana zaune a kofar fada gefensa wani dogari ne sarki suna Dan tattaunawa "Wai sarkin fada ba wayarka bane ake Kira Tim dazu?" "Mtsww Ina ganin kamfanin Zain ne shegu sun Saba kirana in dauka su kwashe kudi to bazan daukaba" "Wanan yafi karfin kamfani tunda tun dazun ake kiranka muna zaune yanzun gashi har yamma tayi suna Kira?kana ganin ba wani bane ke kiranka?".. Yana Gama maganar wayat ta tsinke ,sarki fada ya bude baki zaiyi magana kenan Kira ya shigo a fusace ya zaro wayar a aljihunsa ya Danna dauka ya Kara a kunnensa hade da yin shiru.... "Ranka ya dade dama nine nakeso in shaida maka me gida yadawo tare da iyalensa gabaki daya Kuma naji kamar suna fadin umara zasu tafi gobe da yamma"... Yatsina fuska sarkin fada yayi "wake magana?" "Nine mutumin da nayi maka alkawari Akan idan me gida ya dawo zan sanar da Kai"... Dibb wayar ta tsinke,wata zabura sarkin fada yayi ya Mike tsaye Yana sake dialing number wayar..... *Muje zuwa* *SLIMZY😍* [9/4, 16:50] 🥰slimzy🥰: 🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* 48 Tallafe yake da Fatima a jikinsa Yana faman riritata sai zuba Masa shagwaba takeyi Tana kakkaucewa saboda ummu dake kaiwa da komowa daga daki zuwa kitchen dinta,..wayarsa dake gefensa ce ta hau ringing be dubi wayarba ya Kara rungumota jikinsa Yana famar shafa kanta,wayar ta tsinke a karo na biyu ta Kara shigowa Dan tsaki yayi "mtsww Wai waye ne kuma?"ya janyo wayar Yana kallon me Kiran, Receive ya Danna ya Kara a kunnensa "umhmm ya akayi sarkin fada?" Daga can bangaren aka bashi amsa da "ranka ya dade iyalan gidan malam liman ne yanzun Mai gadin gidan da yake nabashi number ta ya kirani yake sanarmun sun shigo gari tun jiya gobe Wai zasu tafi umara".... "Ganinan zuwa sarkin fada ka kirani a kofar fada"ya datse wayar ya dubi Fatima da tunda ya fara wayar ta kafesa da ido dikda batasan me akeyi ba, Gyarata yayi ya janyo pillow ya Dora kanta akai Sanan ya durkuso daidai fuskarta "zanje indawo kinji babyna ki kulamin da kanki kina bukatar wani Abu ne?" Girgiza Masa Kai tayi tana binsa da kallo har ya Kai kofa ta tsaidashi "habeeby"....cakkk ya tsaya ya juyo a gaggauce "ya akayi Fatima?mekikeso ?" "Ka fadamun inda zaka dik ka kidime sai kace wani Abu ya faru"....jimm kadan yayi Yana Dan tunani bayason sanar da ita koma menene Dan saboda yasan rigima zatasa mishi sai taje gashi ba lafiya gareta ba, "Mai martaba ne yakeson ganina shine zanje bada dadewa zandawo kinji?" Yatsina fuska tayi hade da tabe baki ta juyar da kanta gefe cike da kishi tace"kodai me martabiya ba,Kila ma wajen matarka zakaje"... Agogo ya kalla 'koma menene sai na dawo "be jira cewarta ba ya fice, Idonta yayi kwalkwal,Kila wajen matarsa zaije suci soyayyarsu ita Tana Nan shine zaiyi Mata wayau yace Wai me martaba ke kiransa,....janyo bargo tayi ta rufe har kanta ta shige Tana sharar hawaye saboda tsabar kishi da ya taso Mata.... ********** Bacci sosai Fatima takeyi lokacinda hajiya karama ta shigo sashen ummu Domin ta duba jikin surukar Tata ,dikda kunya hakan be hanata zuwa ba, Bayan sun gaisa da ummu mama karama ta dubi sashin da Fatima ke kwance fuskarta tayi fayau ta Dan rame hancin Nan ya fito zirr, "Wai hajiya zainab meke damun surukar Taki ne?umm?" Yar dariya ummu tayi "diyar tawa karuwa muka samu" Da sauri mama karama ta dubi hajiya zainab fuskarta dauke da murmushi "Masha Allah alhamdulillah Allah ya inganta " "Ameeen ameeen"...ummu ta amsa fuskarta dauke da faraa.... ******** Cikin parlorn baki akayiwa yarima ma sauki shida sarkin fada da Ahmad Wanda ya samesu a can, Sosai dattijom yasha mamakin Jin daga inda suke ya dade Yana nanata masarautar barayar Zaki a ransa...lokaci daya abinda ya faru a baya ya dawo Masa Wanda hakan ya haifar Masa da tsananin tashin hankali...m "Kaidin waye a masarautar barayar Zaki?"....Saida gaban yarima ya fadi Jin tambayar da dattijon ya jefo Masa, Da kyar ya hadiye mugun miyau ya Dan rusuna "nine kabiru da na biyu ga sarki Muhammad Wanda ke mulki yanzun a masarautar barayar Zaki"... Shiru yayi Yana jinjina kansa "Masha Allahu kabiru Dan wajen matar sarki ta biyu kenan koh?" "Ehh"ya amsa ya sunkuyar da kansa, "Me kuke bukata yanzun menene asalin dalilin zuwanku gidan Nan Dan nayi mamakin hakan , Shiru yarima yayi gabansa ya tsananta faduwa Dan besan ainihin yadda zaiyi Masa bayanin dalilin zuwan nasu ba,shin tayaya zai fara bayani? Kallonsa dattijon yayi Yana me nazarin ysnayin NASA kafin ya furzar da iska a bakinsa "Ina sauraronka kabiru"... "Umm..umm..dama baba munzo ne binciken ko zahrau Tana Raye"...yadda yayi maganar Yana inda inda shi kansa ya tsorata da Jin amsar da zai biyo baya, "Shekara nawa kenan kabiru rabonku da zahrau?dikda nasan cewa bakada wasu shekaru lokacin Amma kanada wayon da zakasan komi"a kausashe yayi Masa maganar wanda hakan ya haifarwa da yarima kugin ciki xufa ta Shiga digo Masa, "Bazan iya tuna yawan shekarunba" "Ai nayi tunanin sarki da ahalin gidansa sun manta da wata zahrau a wanan duniyar da dadewa tunda labarin mutuwarta ya iskeku dakyar akasamu wadanda sukazo mun gaisuwa tun daga Nan baa Kara waiwayata da iyalina saboda a lokacin na kasance fakiri banida komi ooh?" Sosai yarima ya furgita da yanayin yadda malam liman yake maganar a kausashe, Shiru yayi ba tare da yace komiba malam liman ganin haka yasashi mikewa ya fice a fusace, Wani kayataccen parlor ya Shiga inda ya tarar da iyalan gidan nasa a zazzaune suna kallon film wata Yar dattijuwa ke zaune gefe hannunta rike da alkurani fuskarta dauke da medicated glass ,kallo daya zakayi Mata ka fahimci ita din asalin bafullatana ce kuma buzuwa saboda kyau da Allah yayi Mata dikda manyata da tayi, "Inna wuro"shine abinda malam liman ya ambata Kai tsaye Yana tsaye a tsakiyar parlorn, Dagowa tayi ta dubesa da idanuwanta dake farin glass "malam ya akayi kana bukatar wani Abu ne?" "Wani abun al'ajabi ne ya samemu yanzu yanzun nan" "Injidai ba maganar tafiyar umarar su zuhra da zahrau bane da halimatu" "Wai kabiru ne yazo daga waccen masarautar barayar Zaki" Dukkansu suka dago kawunansu a tare harda matan dake zaune a parlon suka zuba masa idanuwa..... "Wai meyafaru Kuma?me sukace?" "Wai sunzone bincikar ko zahrau tanada rai" Mikewa Inna wuro tayi tsaye cike da masifa da murya irin Tata ta fulani "yau sukasan da zahrau Tana da Rai ?Koko sanadiyyar da sukayi ta yartata suke so suji?tun shekaru goma Sha Tara da suka wuce Basu nemeta ba sai yanzun" "Zo muje kiji komi daga bakinsa"... Kallon gefenta Inna wuro tayi tace "zuhra muje" Wadda aka Kira da zuhra itace ta Mike Yar babba ce zatakai shekaru arbain a duniya Amma dayake jiki iirin na fulani Tana sanye da tsadadden lace Riga da sket Babu Wanda zai ganta yace takai wadanan shekarun ta bi bayansu,.. Yarima Yana Nan zaune ya hada zufa ta ko Ina Yana jiran abinda zai biyo baya dikda faduwar gabar daya tsinci kansa be hanasa Tattaro dik wata jarumta tashiba,.. Dattijon ne kawai yayi sallama Amma sauran shigowarsu sukayi Kai tsaye, "Kai yaro wani sharrin kuke Shirin kullawa yasa kukazo kuji zahrau tanada rai ko batadashi?" Kansa a kasa ya Soma magana "Babu sharri a wanan lamarin sai alheri inada bukatar ganawa da sarauniya zahrau matukar Tana da Rai Domin akwai muhimmin abinda yasa nazo Nan din" "Ai bakuda sauran mutunci da wata martaba a idanunmu,wanan masarauta Taku Babu abinda ke tattare cikinta sai zalunci da son zuciya,ai nayi tunanin Kun manta damu a rayuwa tunda kukasamu mulki abinda kukeso" Mikewa yarima yayi yasa hannunsa cikin aljihunsa ya Ciro hoton Fatima da mahaifiyarta Wanda suka samu, "Dalilin wanan hoton yasa mukazo gidan Nan" Inna wuro ta Mika hannu ta amshi hoton hannunsa ta kafesa da idanuwanta wadanda ke killace cikin glass, Takai minti biyar Tana kallo Sanan ta mikawa zuhra ta amsa ,zuhra na tozali da hoton ta dubi mahaifiyarsu "wanan hoton shine babban burin zahrau a duniyar Nan Wanda tasa a ranta ko bataga yarta ba tasamu hoton Nan shikenan tasamu dukkan farin cikin rayuwa,bakaramin nishadi zahrau zatayiba idan tayi tozali da wanan hoton"Tana maganar ne Tana duban Inna wuro, Dattijon ne yayi gyaran murya "yanzun kabiru bayan bukatar ganin zahrau zaka iya fada Mana kwakkwarae hujja wadda tasa kazo nemanmu ba sharri ko wani mugun Abu ya kawoka ba?" Girgiza kansa yayi yabisu da kallo yadda dukkansu suka maida hankulansu gareshi ko wanne da abinda yake sakawa a ransa, "Fatima itace dalilin da yasa nazo Nan" Cikin hada baki zuhra da Inna wuro sukace a tare "wacece Kuma Fatima?" "Kanwata,diyar zahrau sanan matata a yanzun haka" "Karya kakeyi kabiru wace Fatima Kuma bayan inda zahrau ta barta ma mutanen baasamesu ba balle wata Fatima" "Wallahi Fatima na Nan da ranta,yanzun haka Nike aurenta....dalilin zuwana Nan kuwa shine dalilin neman itayenta da muka Shigayi yasa muka samu hoton Nan,a bayan hoton mukai tozali da rubutun da yake jikin hoton ya tabbatar Mana da ita din jinin mu ce" "A Ina kasamu Fatima kabiru"Inna wuro tace Tana zare glass din dake idonta, "A gidan marayu ta girma,dalilin kashe habibu marigayi da tayi yasa muka Santa".. Dukkansu sukai shock suna binsa da kallo batare da sunce komi ba sai mamaki da ya bayyana karara a fuskokinsu, Ya cigaba da magana "babban burina a rayuwa ya kasance mahaifiyar Fatima Bata rasuba tanada rai in hakan ya kasance nasamu babban farin ciki a rayuwata kasantuwar banida wani buri a rayuwata Wanda ya wuce Inga matata cikin farin ciki musamman yanzun da ya kasance Tana dauke da cikina a jikinta" Hawaye zuhra takeyi lokaci daya fuskarta ta wadata da kayataccen murmushi tasa hannu ta share hawayenta, "Alhamdulillah daya kasance zahrau tanada sauran farin ciki a rayuwarta....batada burin daya wuce ta bude Ido Taji Koda labarin Fatima ne Wanda ravonta da ita shekara goma Sha shida kenan" Ita kanta Inna wuro farin ciki ne ya lullubeta Jin sunada sauran numfashi a duniya Basu mutuba Allah ya bayyana jikarsu kwaya daya tall a duniya....hannu ta daga sama Tana fadin "alhamdulillahillazi biniimatihi tatimussalihat" Ta juyo ga malam liman Wanda sukai Ido hudu ya fadada faraarsa Yana dubanta cike da farin ciki, Mikewa yayi ya taso ya tsaya kusa da yarima Wanda ya sunkuyar da kansa Yana sauraren Amon maganganunsu a kunnuwansa tamkar sunayi Masa busa yasa hannu ya dafa kafadar yarima "kabiru ka kwantar da hankalinka zahrau Tana Nan da ranta yanzun haka Tana cikin gidan Nan" Tsabar farin ciki besan lokacin da ya rungume dattijon ba cike da farin ciki shigo liman sai bubbuga bayan yarima yake "jairi Ashe Kai kasacemun Mata ka aureta ni kabarni da Mata daya...." Dariya sosai yarima yakeyi yakasa magana Yana duban fuskokinsu fauke da farin ciki, Zuhra ce ta juya ta fice a guje Tana kukan farin ciki hade da dariya.... Zahrau ce zaune Tana dauke da laptop a hannunta Tana sauraren karatun alkurani lokacinda zuhra ta shigo,...a guje ta kamo hannun zahrau Tana fadin "zomuje inji baba" Fuskarta Babu faraa ta amsa da "inhar zanyi tozali da ahalin gidan sarki to tabbas zan iya hadiyar zuciya in mutu saboda tsabar bakin ciki Wanda sune sanadiyyar haddasamun shi harabada" "Bakin ciki ya Kare kanwata ki kwantar da hankalinki kibini Muni umarnin baba kije kawai" Batada wani zabi Wanda ya wuce bin umarnin mahaifin nata...ta Mike jiki Babu kwari xuhra ta ruko hannun zahrau suka nufi parlon baki, Karar turo kofar dakin yasa yarima saurin dago kansa ya dubi kofar...kamar hadin baki suka hada Ido da zahrau wadda ta Tsaya cakkkk Tana bin yarima da Ido,shima ita yake kallo ya kasa mantawa da kamaminta dikda ta manyanta yanzun Amma yanzun take ganiyar kuruciya tunda bazata wuce shekara talatin da bakwai ba, Ahmad dake gefe jikinsa a sanyaye yakebinsu da Ido tamkar me kallon tv, Takawa tayi yarima a hankali Yana fuskantar ta har ya karasa gabanta, Kafarsa yasa a kasa ya dure gwiwoyinsa a kasa Yana binta da kallo ya kasa dauke Ido daga gareta, "Alhamdulillah Da Allah be amshi numfashina ba Saida na Kara tozali da uwata a duniya....momy nine kabiru danki" Kauda kanta tayi gefe hawaye na sauka a idanuwanta tamkar ambude famfo, "Ki dago idonki ki kalleni in baki wani babban albishir Wanda shine mafarkin ki a wancen lokacin" Runtse idanuwanta tayi zuciyarta na bugawa sauri da sauri ji takeyi tamkar zuciyarta zata fasa kirjinta ta fito, "Burinki ya cika uwata,kin manta lokacin da kike da cikin Fatima kin sanarmun idan har kika haifi Diya mace Zaki bani kyautarta a matsayin Mata?kin manta kince idan da namijine kin haifamun babban aboki?...ki bude idanuwanki Ina Mai tabbatar Miki da Allah ya cika Miki burinki Domin Fatima itace matar da nake Aure yanzun hak" Bude idanuwanta tayi ta saukesu Akan yarima Wanda tsananin tausayinta yasashi zubar da hawaye shima.....hannu tasa ta dagosa daga durkuson da yayi a gabanta ,dakyar ta iya bude bakinta "kabiru banaso ka rude ni da dadin baki in mance da tsanar da ke kwance a cikin zuciyata dangane da family dinku" Girgiza Mata Kai ya Shigayi 'bakya bukatar in tsaya rantse Miki Akan wanan al'amarin uwata" Kuka ta fashe da shi harda shassheka ta juyo suka hada Ido da zuhra wadda itama kukan takeyi da gudu suka hade suka rungume juna suna kuka.... ********** Kuka sosai deejahmah takeyi Tana fadin "hajiya nagaji da wanan rayuwar ace ni banida yanci a gidan mijina?shikenan ni bayasona Fatima yakeso raboda da yarima Tim jiya da safe Haba ai ciwo ba hauka bane"ta karashe maganar tana shasshekar kuka, Shiru hajiya babba da hajiya rahina sukayi suna duban Yar tasu wadda gabaki daya ta canja ta rame tamkar ba deejahma me Isa da izza ba tamkar ba Deejahma me mulki da sarauta ba dik ta susuce, "Deejahmah be kamata ki tada hankalinki Akan kabiru ba bayan kinsan auren yarjejeniya akayi" Da sauri deejahmah ta juyo ta dubi hajiya babba, "Ehh Khadija kin manta kin auresa ne saboda ki ramamin abinda akayiwa Dana marigayi?kin manta ba sonsa kikeyiba kin aure shine Dan ki kasheshi ki samamun farin ciki?banida wani buri a duniya Wanda ya wuce Inga gawar kabiru a kwance kamar yadda Naga ta d'ana habibu" Shiru deejahmah tayi tana nazarin kalaman hajiya babba,shin Anya zata iya kashe kabiru yanzun bayan bakin abubuwa da takeji game dashi?idan akwai Wanda ta tsana takeso ta kashe be wuce ta kashe Fatima ba ta hutawa rayuwarta ta zauna daga ita sai kabiru,.... Yama zaayi ta kashe kabiru yanzun bayan batada burin da ya wuce a duniya ta ganta dauke da ciki.....gashi yanzun wata biyu da aurensu batada ciki, Hajiya rahina ta kafe Yar Tata da Ido ganin yadda ta fada duniyar tunani gabaki daya, "Deejahmah kinyi shiru kiyi magana Mana" Mgnr mahaifiyarta ce ta dawo da ita daga duniyar tunanin data fada, "Hajiya kin manta da cewa kisan kabiru ba yanzun zaayishiba sai nasamu cikin magajin sarki?idan na kashe kabiru yanzun menene ribata to ta aurensa" "Inaji a jikina kece zakisamu ciki ki haifama sarki jika ba Fatima ba".... Rahane dake durkushe a gefe tayi tsulum tace "Allah ya taimakeku da badan karkice nayi muku shisshigi a lamarin ba da na sanar daku wani Abu da nake hasashe kuma nake hange" Dukkansu suka maida hankalinsu ga Rahane wadda ke magana kasa kasa Tana jinjina Kai, "Umhmm meye kike hange?me Kuma kika gani Rahane" "Hajiya bana fada muku labari saina tabbatar dashi" "Rahane kiyi maganarki kin Tsaya kina Mana kwana kwana ni banson iskanci" Jiki na rawa Rahane tace"Ina Mai tabbatar muku da Fatima matar kabiru Tana dauke da ciki yanzun haka" "Karya kikeyi Rahane,waya Gaya miki Fatima Tana dauke da ciki?Fatima bazata taba samun ciki ba nice xansamu ciki" "Hajiya wallahi Fatima ciki gareta".... A zabure hajiya babba ta Mike tsaye tana dafa kirji..... ******** "Ka tabbatar da ka kawomin matata har gida Dan ni ya kamata tazo ta gani ba ni zanje ganinta ba tunda ka kwaceta"....liman yace cike da tsokana, "Insha Allah zaakawota ta ganka Amma karfa ka ganta ka rude kace saina sakar maka ita" Dukkansu dariya sukeyi a parlon Banda mahaifiyar Fatima wadda murmushi kawai takeyi cike da kunya.... ********* Tunda Fatima ta tashi take kallon agogon bango Tana dubawa har wajen karfe shida na yamma yarima be dawo ba?Yana can Yana soyayya da matarsa....haushi ya sake lullubeta, Bilkisu ta dubeta "yadai ranki ya dade" Galla Mata harara Fatima tayi idonta taf da hawaye "kina ganin yarima Yana can wajen matarsa ni ya barni anan suna Shan soyayya saboda ni banida lafiya,lallai namiji wato yaci moriyar ganga" Toshe bakinta bilkisu tayi tana Yar dariya,yadda Fatima tayi maganar ba karamin dariya ta Bata ba Amma gudun kada tayi fushi yasa bilkisu shanye Yar dariyarta, Kwantar da kanta tayi a pillow hawaye ya Shiga gangarowa a gefen idonta, Sallama yarima yayi da Ahmad suka shigo ciki, Jin hakan yasa Fatima saurin Jan bargo ta lullube kanta...... *Muje zuwa* *SLIMZY😍* [9/6, 19:54] 🥰slimzy🥰: 🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* 49 Da sauri ya karasa inda Fatima ke kwance a bargo ya ja bargon sai kawai ta runtse idanuwanta zuciyarta na cigaba da bugawa, Tallabota yayi yakai idonsa fuskarta yaga yadda hawaye ke kwance a fuskarta sai ta bashi tausayi ga yadda jikinta yayi xafi Rau alamar zazxabi, A raunane ya dubi Ahmad "Anya doctor zazzabin Nan zai barta kuwa?kaji yadda jikinta yake da tsananin zafi?" "Wai meyasa kake haka ne friend bayan kasan fa dik inda akace ciki Yana karami musamman nata Dole ne sai anyi hakuri da kanana kananan ciwon da zatayi tayi saidai kawai a Bata drugs Wanda zata Dan samu saukin jikinta Amma bawai ya Bari ba sai cikinta yayi kwari" Beso jin wanan amsar daga bakin Ahmad ba Amma sanin shi din doctor ne yasashi Dole amincewa da hakan dikda yadda yakejin tausayin nata, Fatima kuwa a zahiri wani haushin yarima takeji tamkar ta shake shi yazo Yana wani kuri yanajin tausayinta bayan Yana can wajen matarsa ya biya bukatarsa ita tunda yayi Mata ciki ai shikenan... Bude idanuwanta tayi ta saukesu akansa ,"yadai Fatima ya jikin" Bata amsa masaba sai kokarin kwacewa da takeyi daga rukon da yayi mata,....mikewa Ahmad yayi ya dubi bilkisu Wadda ke zaune a gefe a takure yace "zo muje ki dakkowa Fatima sako a mota,..." Ba musu ta Mike ta fice,...juyawa yayi ga yarima "to malamin soyayya malamin Mata biyu Allah ya sauwake ni nayi Nan"...ya fice abinsa, Yana fita Fatima ta kwace jikinta ta jingina daga jikin kujera watsa Mai harara, "Baby Wai lafiya kike wanan Harare hararen haka?meya faru?ko kina bukatar wani Abu ne?" "Ko Ina bukata ya zanyi tunda mijina bani kadai ke dashi ba ya tafi saukewa wata bukatarta...Koda yake Kila kaima kana bukatar ne"ta karashe maganar hade da Shan murrrr Shiko mamaki da tsoron Allah ne suka Kara lullubesa yana binta da kallon takaici,lallai ma wanan yarinyar wato Yana can Yana nema Mata farin ciki ita Tana Nan Tana zarginsa,ya rasa dalilin da yasa Fatima ke irin wanan mugun kishin hakax Haushi ne ya Kara kamasa ya Mike daga tsugunnon da yayi ya fice abinsa,sai kawai ta sa kuka a zaune wiwi tamkar karamar yarinya.... ********* "Wanan cikin bazata taba haihuwarsa a gidan nan ba inhar Ina numfashi deejahmah kidaina wanan kukan da kikeyi Domin wanan karon na shiryawa lamarin zakisha mamaki" Kukan deejahmah ne ya tsananta Babu abinda take da buri a duniya sama ta ganta da jikan Dan sarki a hannunta,ya zamana itace ta Soma bawa sarki jikan fari.....batada hope Akan abinda hajiya babba ke Fadi Domin zuwa yanzun ta Gama sarewa da lamarin gabaki daya musamman data fahimci dik abinda suka sa gaba basa nasara akai sai wani Abu ya gifta Wanda zaisa basuyi nasara ba,....hawaye be daina gudu a idanuwanta ba,....Anya wanan tafiyar da hajiya babba ke tunani zata yuwu na su Bata cikin Fatima?shin idan Sukai kokarin hakan akwai nasara kuwa?menene basuyiba Akan shi aurem gabaki daya, Zuwa yanzun zuciyarta ta karaya batada wani hope Wanda ya rage Wanda ya wuce ta nemi zuciyar mijinta ta yada makaman yaki ta zauna lafiya,dama ita batada burin cutar da kowa a rayuwarta iyayenta sune suke sata a hanya....jikinta yayi sanyi dakyar ta motsa ta goge idanuwanta ta maida dubanta ga mahaifiyarta tace a raunane "Babu ruwana da zancen cikin Fatima,babban burina be wuce Nima in ganni dauke da juna biyu ba,....idan har zanyi wani Abu be wuce inyi abinda zansamu ciki ba"ta karashe maganar da share hawaye, "Sakarya kafin kisamu cikin naki ya kamata ki lalata cikin shegiya" Girgiza kanta tayi tana cigaba da sharar hawaye sai kawai ta Mike tsaye "ni zansa a maidani gidana sai na sake dawowa"Tana gama fadin haka ta Mike Rahane tabi bayanta, Tsananin tausayin yarta ya hanata motsi jinjina Kai kawai takeyi zuciyarta cunkushe da tsananin bakin ciki da takaici dakyar ta dauke wani gawuron numfashi ta dubi hajiya babba wadda ke faman jijjiga kafa, "Bansan meyasamu deejahmah ba hajiya,Kinga dik yadda yarinya ta Kare ta lalace anason nema Mata mafita Amma Tana ki?to gaskiya idan ita bazatayi ba ni zan tsaya Mata tunda ita batada hankali mahaukaciya ce" Tabe baki hajiya babba tayi ta dago daga kishingidar da tayi "rahina kenan aini na Dade da fahintar deejahmah son Kabir takeyi Sanan matacciyar zuciya gareta" "Hmmmm hajiya nidai ki taimakeni ki duba lamarin Nan ayi wani Abu akai" Jinjina Kai hajiya babba tayi batare da tace komiba ta maida dubanta gefe daya..... ********* Tun barinsa wajen Fatima gidansa ya nufa Koda yaje babukowa ya manta da deejahmah Tana gidansu dikda tare sukaje takaicin Fatima ya mantar dashi ita, Yana zaune Yana kallon news din yamma deejahmah tayi sallama a parlorn baiwarta na biye da ita, A ciki ya amsa saboda tsananin takaici da ya tsunta kanshi ga wani sonta da yake yawo a sassan jijiyoyim jikinsa, Gefensa ta zauna Tana duban yanayin nasa hade da karantar halin da yake ciki, "Sweet heart"shine sunan data kirashi dashi yaune farkon da yaji ta ambaceshi da wani suna Wanda mamakin hakan yasashi juyowa da sauri Yana dubanta batare da yace uffanba, Juyowa tayi gefenta na dama taga Babu kowa a parlorn sanan ta matso daff dashi tasa hannu ta dago habarsa ta hada bakinta da nashi ta Shiga kissing dinsa cikin wani irin salo Wanda tasashi suman zaune,....ta Dade Tana kissing dinsa kafin ya fara mayar mata da martani ya rukota sosai Yana tsotsar bakinta hade da sauke numfashi sama sama, A hankali ta zare bakinta daga NASA Tana fuskantarsa Tana kallonsa cike da salon soyayya, "Sweet heart kafadamun menene yake damunka umm?akwai wani Abu ne?" Girgiza Mata Kai kawai yayi da rinannun idanuwansa,batare da yace komiba.... Rungumesa tayi ta Dora kanta a kirjinsa ta Soma magana cike da natsuwa "hmmm nasan ni ban cancanta insan matsalar mijina ba saboda bani bace a zuciyarsa...naso ace inada matsayin da zansan abinda ke damun mijina kodan in faranta Masa Rai ta wata hanya davan,saidai Kash nidin ba kowa bace a gidansa face matar kallo ".... Hannu yakai Yana shafa gefen fuskarta zuciyarsa nayi Masa sanyi a hankali a hankali....ya zaayi ya sanar da ita matsalarsa Fatima ce bayan yasan ba shiri sukeyi ba?sanan be cancanci ya kwashe sirrin Fatima ya sanar Mata ba.... Dago fuskarta tayi tasa hannunta Tana shafa sajen fuskarsa tanayi Masa yawo a fuskarsa Wanda hakan ya haifar Masa da tsananin kasala.... "Mijina ka fadamun matsalarka in magamce maka ita karka damu,ka kwantar da hankalinka I am ready in sama maka farin ciki inhar xaka sanar Dani damuwarka" Dakyar ya hadiyi wani mugun miyau ya numfasa yace "Fatima ce"... Wani irin faduwar gaba ta tsinci kanta ciki,...Fatima Kuma?yanzun saboda Fatima yake fushi?wato soyayyar da yakeyi Mata ta tsananta da har in sun samu matsala zai tsinci kansa cikin tsananin damuwa,dikda kishin da ya taso Mata be hanata numfasawa ba ta nisa tace, "Kayi hakuri yaayah ai kasan Fatima yarinya ce sanan Kuma kaga halin da take ciki na rashin lafiya Dole ne ayi Mata uzuri koh?bedace ka rinka fushi da bintu ba" Mamaki da al'ajabin maganarta ne ya lullubesa Dan be taba tunanin deejahmah zatayi wanan comment din Akan Fatima ba Domin dik sainsar da sukeyi yasani ,wani lokaci kyalesu yakeyi saboda Fatima ta tsinci kanta....shin me kalaman deejahmah yake nufi,ta Soma sonta ne?Koko ta daina rigima da itane....shin waye ya sanarwa da deejahmah Fatima na cikin wani Hali kenan tasan tanada ciki....tsoronsa Kar suyi Mata abinda zaisa cikin Nan ya lalace.... Hannunsa yasa ya dago fuskarta Yana karantar yanayinta,yadda take kallonsa hawaye kwance a fuskarta yasashi karaya yasa yatsansa Yana goge Mata, "Kukan na menene?" "Ina kuka ne saboda nasan bana cikin zuciyar mijina ko kadan saboda abubuwan da nayi a baya...koba haka bama zuciyarka gabaki daya Tana wajen Fatima" Girgiza Mata Kai yayi "Ina sonki Deejahmah,ko Babu komi kedin fa Yar uwata ce,Sanan itama Fatima haka Kinga Baku da banbanci a wajena" Hawayen da take boyewa ne suka sulalo Mata "naso ace nice a zuciyarka kamar yadda Fatima take,saidai hakan bazai yuwuba Domin zuciya so daya ne Kuma Fatima kakeyiwa shi,bazan ga laifinka ba Dan ka sota Domin ta cancanta ne....Nima yanzun burina be wuce mijina ya Soni Koda kwatankwacinta ba dikda yanzun Fatima tayimun nisa......koba komi yanzun dauke take da cikinka a jikinta kaga matsayinta da martabarta ta Karu a idanuwanka" Tausayinta ne ya lullubesa saidai ya kasa gasgata kalamansa Domin zuciyarsa nayi Masa waswasi akanta,ya kasa yarda da itadin ya yada makaman yaki xaman lafiya take nema.... "Fatima Yar uwata ce....Ina sonta yanzun haka banida wani kudiri a zuciyata dangane da ita Wanda ya wuce alheri".... Zuwa yanzun kalamanta sun Gama Shiga jikinsa dik jikinsa yayi sanyi dikda bawai ya gasgatata bane Amma ta bashi tausayi Amma zaisata on trial... Rungumeta sosai yayi ya sumbaci goshinta ya cigaba da shafa bayanta Yana lallashinta..... Zuwa dare yarima ya saki jiki ya mance da wani bacin Rai na Fatima dikda gangan jikinsa ne ke gidan Amman zuciyarsa da ruhinsa sunaga farin cikin rayuwarsa bintu.... ********* Kuka sosai Fatima keyi na Rashin yarima a kusa da ita daddare,....gabaki daya hankalinta ya tashi saboda yadda ya fita daga gidan ummu a fusace ya nuna alamar yayi fushi da ita.... Shin meye laifinta Dan tayi kishinsa?kishin miji halak ne ga ko wace matar aure....yarima bazai taba fahintar yadda takeji ba ko deejahmah ce ta amshi girki ya kwana a dakinta ji takeyi tamkar ta kashe kanta saboda tsananin bakin ciki da takaici.... Kifa kanta tayi a pillow Tana kuka harda shassheka,dakyar ta motsa hannunta ta janyo wayarta tayi dialing numbersa.... Ta Dade wayar na ringing be daukaba Jin hakan yasa wani sabon zazzabi ya Kara rufeta... Texx ta tura mishi kamar haka... _Habeeby bazan iya bacci ba,bacci ya kauracewa idanuwana....banida farin ciki Wanda ya wuce inganka yanzun a gefena kaimun mayafi da faffadan kirjinka....Ina sonka mijina...._ Yana sama tare da deejahmah ya sauko kasa daukar wayarsa da ya manta a kujera yasa hannu ya dauka ya taba yaga Miss calls dayawa ya duba ciki harda na Fatima...be Gama dubawa ba Tex dinta ya shigo wayar, Tex dinta ya karya Masa zuciya...girgiza Kai kawai yayi ya kashe wayar ya juya ya Haye sama wajen deejahmah.... ******"" Tare suka shirya da safe da deejahmah suka nufi gidan Mai martaba... Bayan driver yayi parking hannunsa na cikin na deejahmah ya dubeta "Zaki Shiga cikin wajen hajiya ne?" "Umm umm inaso inje induba Fatima"....yadda tayi maganar ba karamin mamaki ta bashiba sai kawai ya sauke ajiyar zuciya ya ruko hannunta suka fito...maimakon su Shiga sashen su hajiya sai suka nufi sashen ummu, Tana zaune a parlor saboda zazzabi da takeji Tana sanye da katuwar rigar sanyi da safa,hannunta dauke da tea da takesha kadan kadan sukai sallama... Kallo tabisu dashi cike da mamaki, Gefe ya zauna dik yadda yaso ya kauda kansa daga gareta kasawa yayi besan lokacinda ya kafeta da idanuwansa ba tamkar ranan ya Soma ganinta, Deejahmah dake gefe kishi na neman taso Mata ganin Fatima da yayi lokaci daya ya manta da ita a wajen sai kawai ta daure tayi gyaran murya Wanda hakan ne yasashi saurin wayancewa ya sa hannu a aljihun rigarsa ya Ciro wayarsa ya maida kansa ga wayar tasa, "Ya jiki Fatima?" Tambayar ce tazowa Fatima a banbarakwai don Bata taba tunanin haka ba, Dakyar ta motsa lanbanta ta amsa da "da sauki"a takaice tayi maganar, Murmushi deejahmah tayi "to Allah ya Kara lafiya ya rabaku lafiya"Tai maganar hade da kauda kanta gefe, Ummu ce ta fito daga dakinta Tana fadin "waye ne yazo yakesa patient Dina magana" ..turus ta tsaya tanabin deejahmah da kallon mamaki,ta daure fuskarta tamau ta karasa shigowa parlorn ta nemi kujera ta zauna Tana bin deejahmah da kallo, Ganin irin kallon da ummu keyi Mata yasata sunkuyar da kanta kasa "barka da tashi ummu" "Kema barkanki,Ashe kinsan hanyar gida na" "Kiyi hakuri ummu wallahi.... "Wallahi me?yau ma mijinki ne nasan ya tilastaki kikazo sashin nawa saboda ki gaida kishiyarki Amma da badan haka ba banida wanan arzikin a wajenki,yanzun ma tashi zakiyi kibarmun gida Dan ban yarda dake ba" Da sauri yarima ya amshe zancen "Haba ummu ya zakice haka?" "Da katamun kabiru karka kawomin iskanci kanajina koh?idan Kai ta kanainayeka da kissa ni Bata isaba Dan Nima macece sanan wani rawan jiki yasa ka fada Mata halin da Fatima ke ciki?to kasani idan wani Abu yasami cikin Nan bazan yardaba" Kunyar deejahmah hade da tausayinta ya lullube yarima yadda Tai tsumu a zaune ummu na zazzaga Mata cin fuska ba karamin tausayi ta bashiba dikda shima bawai ya Gama yarda da ita bane, Kwalla ce ta jika idanuwanta a hankali tasa hannunta ta cire hade da mikewa jiki a sanyaye tabi ta gaban Fatima ta gifta,kamshin turaren jikin deejahmah ne ya daki hancin Fatima Wanda tajishi a hancinta sakkk na yarima aikuwa take amai ya taso Mata ta Mike a guje tayi cikin daki ko kafin ta Kai ta amaye jikinta....cakkkk deejahmah ta tsaya hade da juyowa zata Shiga dakin, "Dakatamun deejahmah wuce kawai zan gyara yata Dan bansan wani mugun Abu kikazo dashi ba Wanda ta Shaka ta Soma amai tunda tafara ciwo batayi amai ba ko sau daya sai yau da zuwanki....bansan mugun nufin ki ba" Zuwa yanzun ranta ya Gama baci haka ta taka kafarta ta fice jiki Babu kwari...Tana tafe Tana sharar hawaye zuciyarta na Raya Mata Allah ubangiji yasa itama tasamu ciki kodan wanna abun da ummu tayi mata itama a kula da ita kamar yadda Fatima take ganin gata.....gashi Allah ya jarabceta da son ciki... ******** Saida Fatima ta numfasa sanan yarima ya dubeta kadan ya kauda kansa, "Naga bakida lafiya gashi inaso muje wata Yar unguwa bansaniba ko Zaki iyayin karfi da jikinki daganan sai mu biya asibiti a Kara dubaki"... Shiru tayi kamar bazata ce komiba sai can tace"zan iya Nima inaso infitan kodan Inga gari tunda na kwana biyu ban leka wajeba" "Shiga ki shirya" Mikewa tayi ta Shiga bedroom inda nan ne wajen zamanta ta bude karamin akwatinta ta Ciro bakar doguwar Riga Mai stones jajaye Mai shegen kyau ta cire kayan jikinta ta zurata kawai ta shafa Hoda a fuskarta da man baki sanan tasa Jan gyale tayi rolling tayi masifar kyau dikda ramarta data fito da wani irin fari da ta Kara Tai mugun kyau... Ko alkyabbar batasakaba ta cire Jakarta ta rataya side bag red da flat shoes jajaye masu Dan flowers a sama ta fito, Kallonsa tayi kamar bazatace komiba ta sunkuyar da kanta kasa "na fito" "Ok"kawai yace ya Mike yayi gaba a abunsa tabishi a baya, Tasha mamakin ganin shine zaiyi driving dinsu Dan haka kawai saita Shiga gabam motar ta bude Jakarta ta Ciro wayarta ta Shiga buga game suka dau hanya Babu mecewa wani uffan... ****** Tankakemem gidan sama Wanda ya tsaru taga sun nufa yarima ya Shiga horn da gudu Mai gadi ya bude Masa kofa hade da fadin "barka da zuwa ranka ya dade" hannu kawai ya daga Masa ya nufi parking space yayi parking motarsa.... Kashe motar yayi ya dubeta "muje koh?" Turo bakinta tayi gaba "Ina ne Nan Kuma?" "Idan muka Shiga zakiga ko inane na kawoki wajen sabuwar budurwata ne Inna wuro"... Tabe baki tayi ta bude mota ta zuro kafarta kasa take Taji wani irin faduwar gaba ya ziyarcewata Wanda hakan ya haifar Mata da rawar jiki... Har yayi gaba yaga Tana takowa a hankali ya Mika Mata hannu sai kawai ta Mika mishi ya rike Mata hannu Yana lura da yanayin yadda jikinta ke rawa bece Mata komiba haka suka nufi cikin gida.... Suna zazzaune a parlor har malam liman lokacinda yarima yayi sallama, "Assalamu alaikum"...shine abinda yace hade da Shiga fuskarsa dauke da faraa, Dukkansu faraa dauke da fuskarsu suka amsa harda xahrau dake gefe a zaune ta sunkuyar da kanta, A sanyaye Fatima ta shigo parlorn hade da sallama dauke da bakinta kanta a kasa, A tare suka Mike malam liman zuhra da Inna wuro suka hada baki "Allahu akhbar"sukace a tare fuskokinsu dauke da tsananin farin ciki, Fatima na dago Kai suka hada Ido da zuhra Yar mamanta Taji jikinta ya Kama rawa ganin yadda hawaye ke sauka a idanuwanta...kirrrr tayi da Ido Tana kallon zuhra, Inna wuro ce ta zare farin glashin fuskarta tasa hannu ta cire kwallar data cika a idanuwanta..... Xahrau wadda ke zaune kwalla na sauka a jikinta yadda ta sunkuyar da Kai ko motsi ta kasa....a hankali Fatima ta taka gaban zuhra bakinta na tasbihi saboda tsananin kamar da ta gani da hotonta Dana mamanta Tana karama.... A gaban zuhra ta tsaya idanuwanta ko kiftasu batayi sai kawai zuhra ta bude Mata hannuwanta alamar ta taho Bata tsaya wata wataba ta fada jikinta ta fashe da kuka dukkansu kuka sukeyi sosai Tana kissing din gefen fuskar Fatima... Karfin Hali Fatima tayi ta dago kanta daga jikinta ta bude baki dakyar tace"mahhh"....girgiza Mata Kai zuhra tayi "umminki ce ni Fatima ga mahaifiyarki Nan zahrau"ta nuna Mata inda zahrau ke zaune ta sunkuyar da Kai hawaye na diga.... A hankali ta juya ta dubi mahaifiyarta...a hankali ta Shiga takawa har gaban mahaifiyarta ta ta dire Jakarta kasa tasa hannu ta cire gyalen dake kanta ta jefar ta tsugunna ta dafa kafafuwanta"maamah.."....kuka yaci karfin zahrau Koda ta dago suka hada Ido da yarta numfashinta ne ya tafi saboda tsananin yadda taga kamaninta da Yar Tata.....mikewa tayi tsaye bakinta na rawa...ta ambaci "bintu".... Cikin shasshekar kuka Fatima ta amsa da "naam".... Kawai numfashinta ne ya tafi ta Fadi.. da sauri zuhra ta rukota jikinta Tana kuka, Halima ce ta shigo daga waje taga halin da suke ciki itama tayi joining wajen kukan farin ciki.... ********* Bayan komi ya Lafa zahrau ta farfado daga suman da tayi hannunta na cikin na Fatima take bin diyar Tata da kallo yadda Tai masifar Kama da ita Babu abinda ya Rana kamanninsu sai shekaru dikda itama zahraun Bata tsufaba tunda Bata wuce 37 ba lokacin.... Yarima na zaune a gefe Fatima ta kallesa suka hada Ido ta sakar Masa murmushi wani soyayyar mijinta ne ya lullubeta Wanda Bata tabajin irinsa ba,Anya akwai mazaje irin kabiru kuwa?tabbas ya cika Dan halak tunda ya cika Mata alkawarin da yayi Mata na sama Mata farin ciki har karshen rayuwarta.... Memakon ya maida Mata da murmushi sai ya harareta...turo Masa baki tayi Sarai ta fahimci fushi ya dauka da ita Dole ma ta lallashi mijinta Domin yarima ya Gama Mata komiba a rayuwarta.... *Muje xuwa* SLIMZY❤ [9/9, 19:57] 🥰slimzy🥰: 🌩 *ANYI WALK'IYA.....🌩* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 💡 *NA: SLIMZY✍🏼* _Wattpad@slimzy33_ *Sadaukarwa ga k'awata faty D'an maliki* 50 A Daren ranan yarima ya sanarwa da Mai martaba samun mahaifiyar Fatima Wanda yayi tsananin farin ciki da Jin hakan....Nan da Nan yasa aka sanar da akwai kwarya kwaryar liyafa washe gari ta taryar mahaifiyar Fatima zuwa masarautar barayar Zaki Kuma matar tsohon sarki Marigayi.... ******** Washe gari yarima ya sanarwa da deejahmah samun mahaifiyar Fatima....saboda tsananin farin ciki har kuka tayi na Taya Fatima samun mahaifiyarta dikda Fatima a gidan kakaninta ya barota Dan zasu taho dasu zuwa masarauta... Duban deejahmah yayi ya shafa kanta saboda tsananin tausayinta da yakeji yadda lokaci daya ta canja daga yadda take dik jikinta ya mutu tayi wani sanyi... "Ki shirya dakyau kiyi Shiga ta alfarma saboda Mai martaba yace zaayi biki ne sosai na taryar mahaifiyar Fatima" Kashe Masa Ido tayi hade da lallausan murmushi "yadda kace haka zaayi ranka ya dade"...rungumeta yayi Yana jujjuyata a sama Tana kyalkyala dariya... ******** Wasu tsadaddun Kaya ummu tabawa bilkisu ta Sanya masu shegen kyau tayi kwalliyarta ta alfarma tamkar ba ita ba dik inda ta gifta ummu sai ta kalleta tausayin yarinyar takeji yadda take rayuwa Babu iyaye Kuma Bata damu ba tasawa zuciyarta hakuri da dangana... "Bilkisu Niko idan bazaki damuba zanyi Miki wata Yar tambaya"ummu taiwa bilkisu maganar cike da kulawa, Murmushi tayi ta sunkuyar da kanta kasa Tana Wasa da Yan yatsunta, "Shekaran jiya na ganku keda Dana Ahmad a jikin mota yadda kuke magana sai Naga tamkar akwai wata alaka a tsakaninku kedashi" Murmushi kawai bilkisu takeyi batare da tace komiba,....ummu ma Yar dariya tayi "to kodai tuwona Mai na zaayi ne keda Dan nawa?Dan gaskiya Kun matukar dacewa da juna" Mikewa bilkisu tayi tsulum batare da tacewa ummu komiba ta shige tsohon dakin Fatima na da,.... ******** Da yareema da deejahmah suka tafi gidan kakannin Fatima, Deejahmah Tasha mamakin ganin yadda suka tarbeta hannu biyu biyu tamkar Yar da suka Haifa haka mahaifiyar Fatima ta rungume deejahmah a jikinta, Fuskar Fatima dauke da murmushi take duban deejahmah dik yadda ta sauya tamkar ba itaba da abin mamaki yake Bata da Bata yarda da deejahmah ba dik tunaninta kissa ce kawai takeso tayi Mata Amma yadda taga deejahmah na shisshigowa lamarin nata yasa ta Dan saki jiki da ita, Wani irin kallo Mai cike da shauki da tsananin soyayya yarima ke jifan Fatima dashi ya kasa dauke idanuwansa daga gareta ya rasa dalilin da yasa Fatima ta Shiga ransa fiye da kowa a rayuwarsa....ga wani sabon sonta da yake ji a dik jijiyoyim jikinsa musamman yanzun da take dauke da gudan jininsa a jikinsa.... Wucesa tazo yi ya ruko hannunta Yana murzawa hade da sauke ajiyar zuciya Yana Shirin janyota jikinsa deejahmah tayi Dan gyaran murya "malam ka Bari dai kuje gida tukunna ni banaso kasa Yar uwata Jin kunya....Dan yanzun da zarar aka shigo aka ganta a jikinka Kai ba kunyar da zakaji itace zataji kunya"...Tai maganar cike da zolaya.... Turo baki Fatima tayi cike da shagwaba ta dubi Deejama "kina ganin ko tausayina bayaji so yakeyi yamun mugunta ma" "Yi hakuri rabu dashi zamu Rama Bari muje gida yau ai a gidanmu zamu kwana koh?injidai Zaki bimu" Gyada Mata Kai Fatima tayi tana murmushi, Kallonsu yakeyi cike da shaawarsu lokaci daya ya tsunci kansa cikin tsananin farin ciki.... Motoci ne nagani na fada aka shirya zuwa gidan Mai martaba wadanda kaf dangin Fatima da mahaifiyarta zahrau suka hallara Dan zuwa gidan sarki kowa cike yake da tsananin farin ciki Mara misaltuwa.... ******* Fada ta cika tayi dankam dangi na kusa Dana waje kowa ya hallara sai Sam barka akeyi da zuwan zahrau masarautar barayar Zaki kusan kowa da yake wajen cike yake da farin ciki Banda hajiya babba wadda fuskarta kadai zaka duba kasan Tana cikin tsananin tashin hankali Mara misaltuwa....ita kuwa rahina gabaki daya yanayinta ya nuna tayi give up hukunci kawai take jira... Shiru kowa yayi lokacin da Mai martaba yayi gyaran murya... "Dukkan yabo da godiya ta tabbata ga Allah daya nuna Mana wanan Rana Mai cike da tarihi....ranace wadda bazamu taba mantawa da itaba a rayuwarmu kasantuwar dawowar iyalan Dan uwana sarki abdallah na biyu a masarautar barayar Zaki Marigayi....hakika lokacin da ya shude abubuwa da dama na bakin ciki sun samemu misali kamar batar matar Dan uwana da ciki Sanan kuma mutuwarsa shi Dan uwan nawa a karshe Kuma rasa Dana babba habibu da mukayi mun tsunci kanmu a cikin damuwa sai gashi Allah ya kawo Mana waraka ta sanadiyyar mutuwar habibu daya kasance Yar uwarsa ce tayi sanadiyyarsa bada son ranta ba Allah ya jikansu da rahma" Fada ta hada baki da "ameeen" "Abu na gaba shine lokaci yayi da ya Dace indauki mulki in mikawa masushi Amma saidai hakan bazaiyuwuba sanadiyyar abinda sarki abdallah ya Haifa din macece saidai zan dauki tamanim cikin dari na mukami a mikawa Yar marigayi wato fatima" Murmushi yarima yayi hade da dubam inda fatima ke zaune gefen deejahmah dukkansu murmushi suka saukewa juna, Mai martaba ya cigaba da magana"Allah ya nuna min ranan da ya Dace Inyake mummunan hukunci Wanda ya Dace da masu laifi guda biyu a cikin fadar Nan".... Gaban hajiya babba ya yanke ya fadi Nan da Nan zufa ta Shiga karyo Mata a ta ko Ina a sassan jikinta, "Safiya kinbani mamaki ,ban taba tunanin kedin azzaluma bace Saida wanan lamari ya faru,Ashe ba tsakani da Allah kike zaune Dani ba...kina zaune danine saboda mulki da dukiya Wanda hakan ya tabbatar mun da dik ranan da na rasasu Zaki guje ni,to tunkafin hakan ya faru Ina Mai tabbatar Miki da na tanadar Miki hukunci me tsanani daga ke kuwa har Yar uwata rahina.... "Hukuncin Dana yanke Miki kuwa shine na sauwake Miki igiyar aurena guda daya.....Sanan na yanke Miki hukuncin xama a kurkukun masarautar Nan na shekara biyar sakamakon yunkurin kisan Kai da kikayi".... Murmushi Fatima tayi lokaci daya ta dago kanta ta dubi hajiya babba idanuwansu suka hadu da juna ta sauke Mata kayataccen murmushi hade da kafeta da idanuwa..... "Ke Kuma rahina ba wani hukunci zan yanke mikiba face na yanke dik wata alaka Taki da cikin masarautar Nan na tsameki a cikin Yan uwana har zuwa lokacin da Zaki shiryu ki tsarkake zuciyarki Sanan gidan da nabaku kuke xaune keda mijinki na dauki mukamin galadiman gari gabaki daya na kwace su daka hannunku zan mikasu ga sarkin fada a bisa namijin kokarin dayayi wajen nemawa Fatima diyata farin cikinta" Sunkuyar da kanta Deejahmah tayi kwalla cike da idanuwanta Jin hukuncin da Mai martaba ya yakewa iyayenta.... Hannu Fatima tasa ta ruko hannun deejahmah lokaci daya ta dago kanta suka hada idanuwa,take tausayin deejahmah ya lullube Fatima Wanda hakan yasata girgiza Mata Kai alamar kada tayi kuka..... Kuka sosai hajiya rahina takeyi me cike da danasani Wanda Bata taba tunanin zata wayi gari ta tsunci kanta a kaskantacciyar rayuwa ba,...Rana daya dik abinda take takama dashi an kwaceshi daga gareta sakamakon son zuciya da rudim shedan da tabi na zugar hajiya babba gashi ta kaita ta baro.... Itadai zahrau tunda ta sunkuyar da kanta Bata dago ba saboda kwata kwata Bata taba tunanin saboda ita Mai martaba zai iya sakin uwargidansa ba a dalilin mugun aikin da tayi na yunkurin kisan Kai.... "Fatima Allah yayi Miki albarka keda abokiyar zamanki Allah ya hada kawunanku ku zauna lafiya kunji?" Jinjina Kai Fatima tayi "ameen ranka ya dade Ina godiya" "Ina neman wata alfarma guda daya ranka ya dade" Fada tayi tsit kowa na kallon Fatima yayinda zuciyoyin wasu daga ciki suka Shiga tsananin rudani... "Bakida alfarma a masarautar barayar Zaki Fatima saboda sarautar dungurungum Taki ce da badan xuwanki a matsayin mace ba da yau sarki zaiyi mirabus ya Mika Miki sarautarki Dan haka kome kikeso umarni kawai Zaki bada ayi Miki shi" Murmushin Jin Dadi Fatima tayi "akwai Yan uwana guda biyu a cikin gidan Nan Maryam da bilkisu wadanda suka kasance marayu babu uwa Babu uba suna Nan suna bauta inaso Mai martaba ya yantasu daga bayi zuwa cikakkun ya'ya ranka ya dade" "Kinada damar da Zaki yanta ko wani bawa daga cikin gidan Nan Fatima Dan haka bilkisu da Maryam sun yantu Sanan nayi alkawarin rikesu a matsayin Yaya harabada".... Wani irin farin cikine ya lullube Fatima Wanda Saida hawaye ya sakko daga idanuwanta....abinda Bata taba tunanin samuba ko a mafarki yau gashi itace a daular mulki sarautar gabaki daya tatace Dik ta sanadiyyar yarimanta kabiru Wanda ya zame Mata kyautar Allah.... Bayan Yan jawabai da Mai martaba ya Kara Nan aka Shiga gudanar da liyafa Wanda sarki ya shirya Domin murnar dawowar mahaifiyar Fatima Sanan ya roki iyayen zahrau da Subar zahrau ta zauna a masarautar a sashen da zaa Gina Mata nata daban da masu hidimarta kasantuwar tanada gado a gidan nata Dana yarta da Wanda sarki abdallah ya bada wasiyyar Bata Koda ansameta a raye... Bayan komi ya Lafa wajen yamma Fatima ta baro sashin ummu ta nufo sashin cikin gida direct bangaren hajiya babba ta Shiga, Zaune ta sameta a kasan carpet Babu kowa a bangaren ta tayi shiru, Tsaye Fatima tayi a kanta Tana dubanta shekeke, "Ranki ya dade sarauniyar sarkin masarautar barayar Zaki,yau Ina sarautar?Ina mulkin?sanan Ina jiji da Kai?Ina cikar asalin Taki?Ina hadimanki da bayinki hade da kuyanginki wadanda kike sawa ki Hana dik Ina suke?shi kanshi auren naki Ina yake?....." Ta sunkuyo ta dago fuskar hajiya babba Tana Kare Mata kallo cike da faraa "naso ace kin dawwama a cikin farin ciki a cikin daular mulki saidai son zuciya da rudin duniya da kururuwar shedan ya janyo Miki babbar asarar da na tabbata cikin awannin da suka shude kinyi Dana sani yafi sau million hajiya.....yau Ina asalin naki?na tabbatar da son zuciya irin naki yasa kin guji danginki saboda daukar mulki yau gashi an wayi gari Babu ko daya Zaki Kare a zaman kurkuku kurkukun ma na masarautar da kika zuba mulki a da.....yau Fatima wadda ta kasance shegiya Mara asali Yar kwararo itace Mai mulkin da kike takama dashi...mshiyasa idan zaka Gina Ramin mugunta ka ginasa daidai kwaurunka wata Kila ya rufta da kai to gashi ke Ramin miguntar naki ya rufta dake ya zame Miki kabari....a karshe inaso in sanar dake cewa ni saina shayar dake azaba fiye da wadda kika shayar Dani....a dakin da Zaki zauna a kurkuku nasa an cikasa da kunamu masu harbi saboda inaso in dandana Miki irin azabar Harbin kunama".... A fusace Fatima ta juya saboda tsananin bakin cikin da takeyi idan ta dubi hajiya babba,da sauri ta ruko kafafuwan Fatima "ranki ya dade ki taimakeni karki mun azaba ki tallafi rayuwata wallahi summa tallahi nayi danasanin abinda na aikata"ta karashe maganar tare da kukan nadama, "Au har na Zama ranki ya dade kenan?tun kafin aje ko ina?yau Fatima baiwarki da kike wulakantata a idon jamaa yau ita kika Rika kafafuwanta kina neman gafararta koh?hmmmm bakiga komiba sai bayan shekara biyar kin Zama baiwata nida yayana in aikeki daga kitchen zuwa dakina insaki kiyimun abinda na gadama Ina zaune na harde kafafuwa Ina tare da mijina da yayana da kishiyata zakisha mamaki Amma yau tabbas kwana Zaki kunamu suna harbinki"... Rukota hajiya babba ta karayi tasa kafarta ta take hannun hajiya babba Wanda Saida ta saki Yar Kara.... ******** A kurguje bayan watanni biyar da faruwar hakan komi ya Lafa, Fatima na zaune da cikinta Dan wata takwas Wanda ya girma haihuwa ko yau ko gobe itada deejahmah ne zaune a parlor suna kallon wani series film, Yatsina fuska Fatima tayi tana Dan cijewa, "Yadai Fatima?mekike bukata?ko abun yazo ne" Girgiza Kai kawai fatima tayi ta saki kukan shagwaba ....Nan da Nan hankalin Deejahma ya tashi ta dauki wayarta ta Kira yarima, Yarima Yana tare da Ahmad sunje siyayyar kayan aure na Ahmad da bilkisu wadanda tuni suka daidaita kansu sanan rukon bilkisu gaba daya ya koma hannun mahaifiyar Fatima zahrau tamkar itace ta haifi bilkisu haka takeji, Daukar wayar yarima yayi Yana fadin "menene kuma?badama in fita Kun rinka kirana kenan" "Uwargida keda bukatar mijinta a kusa da ita Dan yanzun haka kuka tasamun narasa yadda zanyi da ita shine na kiraka" Dafe kansa yayi "shikenan gamunan zuwa"...ya datse wayar "Yadai abokina?"Ahmad ya tambayi yarima "Rigimar Fatima ce ta motsa Wai kuka takeyi so takeyi inje gidan kawai tasamun rigima Wai incire Mata cikin da nayi Mata kaji fa?Haka tamun jiya wallahi dakyar na lallasheta" Dariya sosai Ahmad keyi "to Kai waye yace ka Mata cikin?"ya tambayesa cike da zolaya....dariya dukkansu sukasa... ******** Bayan wata daya a yau ya kasance jumaa yau ne Kuma alkawarin Allah ya cika Fatima ta haifi yaranta biyu dik maza kyawawan gaske masu kamanni sakk da ubansu identical twins wadanda tsabar kamanninsu yasa akayi musu sheda, Fatima taga tsananin gata wajen wanan family din gabaki daya ba karamin hidima akayiba tun daga haihuwar Fatima har ranan daya kasance ranan bikin suna...komi da akayi a wajen deejahmah ce ta shiryashi itada kawarta Sunita wadda dama tun yarinta suke tare Dan haka tare da ita akai hidimar suna....sosai jamaa suka hallara wadanda basu samu damar zuwa bikin Fatima ba saboda yadda akayi bikinta Babu shiri,....masoyan Fatima Basu faduwa Dan hussy luv tun ana jibi suna ta dira a gidan Fatima itada Hindu dasu akai komi Naga wasila getso (waseey)ta halarci bikim suna da yawa ma masoyan Fatima Basu faduwa a wajen sunan Nan inda yarima yayita barin kudi da kyaututtuka kakannin Fatima ma baabarsu a bayaba Dan Inna wuro shanu dari ta bawa Hasan da hussaini wadanda sukaci sunan Umar da aliyu..... ********* Hajiya babbace ke zaune dik ta fita hayaccinta tayi bakinkirin ta rame gabanta robar abinci ce Wanda ake Bata shi Babu Dadi haka takeci maganin yunwa Turo kofar akayi da kafa Fatima ce ta shigo Hassan da hussaini na sagale a kafadarta gabanta da bayanta dik hadimanta ne da escort dinta, Tsayawa tayi tanabin hajiya babba da Ido sai cannn ta nisa tace"nakawo Miki jikokin sarki ne wadanda suka fito daga cikin shegiya kigansu magada mulkin ubansu" Hawaye hajiya babba ta Shiga matsowa a idanuwanta hade da shasshekar kuka Wanda baya fitowa saboda tsabar wahalar da take ciki, Dik jikinta yayi rudu rudu tamkar me borin jini ga wari da takeyi na rashin wanka, "Kukanki da kwallarki Basu zasu sa inyafe Miki laifin da kikamunba Domin kukanki ma Kara tunzurani yakeyi Dan kece sanadiyyar da narasa ubana....inda bakisa anbi uwata akashe ba da ubana be Shiga matsanancin Hali ba Wanda ya saukar Masa da mummunan ciwon da yayi ajalinsa Dan haka ki shirya kuka Dan vaki Gama kukaba tukunna ma,Dan Mai martaba ya mance da wata halitta safita...."...Tana Gama fadin hakan ta juya abinta hade da tsirtar da miyau... ******** Bayan shekara uku Fatima na dauke da wani cikin yayinda Hassan da hussaini sunyi girma sunyi wayau Kuma rukonsu gabaki daya Yana wajen deejahmah Dan tsakaninsu da uwarsu saidai idan sunje gaisheta, A wanan shekarun ko batan wata deejahmah batayiba balle asa ran zata haihu Wanda hakan ba karamin damuwa ya haifarwa da Fatima ba kullum cikin yi Mata addua take na Allah ya Bata tunda ga bilkisu Nan Dan yarta surayya Tana goyo... Fatima Babu dadewa ta Kara haihuwar mace inda yarinyar taci sunan deejahmah wato Khadija akai Mata takwara tayi tsananin farin ciki da hakan Taji dadin karar da yarima da Fatima sukai Mata Kuma ta gode musu, ******* Bayan wata biyar da haihuwar Mimi wato deejahmah karama itama Deejahmah Allah ya Bata nata Rabon murna a wajen wanan family din baa magana tuni labari ya Isa ko Ina cewar deejahmah na dauke da ciki kowa yayi farin ciki da wanan labari. Anata shirye shiryen bikim khausar da afnan da Maryam da faizah da fauziyya deejamah ta haifi yarta mace Nan itama ta roki yarima yasawa Yar Fatima suke kiranta da Noor...... Zaman lafiya da kwanciyar hankali ne ya wanzu a cikin wanan masarautar inda dik wata Fatima sai ta kaiwa gidan marayu taimako ta dubasu ta tallafawa rayuwar yaran dake cikin wanan gidan Wanda ya zame Mata gidan tarihi..... *ALHAMDULILLAH* DUKKAN GODIYA TA TABBATA GA ALLAH DAYA BANI DAMAR YIN WANAN RUBUTU ALLAH YASA MU AMFANA DA DARASIN DAKE CIKI KURAKURAN DAKE CIKI KUMA ALLAH YA YAFE....NA SADAUKAR DA WANAN LITTAFIN GABAKI DAYA GAREKI FATI DAN MALIKI KAUNARKI A CIKIN ZUCIYATA TAKE HARABADA KEDIN MASOYIYATA CE TA HAKIKA MEENARKI NA KAUNARKI DAN ALLAH ALLAH YA BARMU TARE.... INA MIKA GODIYATA GA DUMBIN MASOYA WANAN LITTAFI NASAN BAZAKU KIRGU BA SHIYASA BAZAN IYA LISSSFA SUNANKU BA AMMA KUSANI A DIK INDA KUKE INA KAUNARKU SOSAI..... GODIYA TA MUSAMMAN GAREKI UWA TA GARI ABAR ALFAHARIN KO WACE DIYA DIK WADDA TASAMEKI A MATSAYIN UWA HAKIKA TA MORE....BANIDA KAMARKI A KULLUM INA FADA BILKISU MUSA GALADANCI ...SLIMZY DIYARKI CE HARABADA.... NAGODE SOSAI HAUWAU MUAZU AMIR (UMMU AFEE)MASOYIYA TA HAKIKA TUN YARINTA INA KAUNARKI.....ALLAH YA RAYAMUM ADNAN YAR AMMIEY SLIMZY.... NAGODE SLIMZY😍