[7/3, 9:54 AM] Aysha Galadima: *_Typing📲_* *_Haske writer's asso...._*💡 *_♦RAINA KAMA......♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻 ____________________________ *_Dolene page d'in farko yazama sadaukarwa agareki MAMAN JUNIOR😭, ALLAH ya gafarta miki, ya raya abinda kika bari, ALLAH ya k'addara bazakiga k'arshen wannan littafiba. (Masoyan Raina kama kusaka wannan baiwa a addu'arku, ta rasu cikin azumi, kusanma k'arshe, member ce a group d'in raina kama, ALLAY ya yafe mata🙏🏻😭._* _INA fata kunyi salla lafiya gaba d'ayanku, ALLAH ya kar6i ibadunmu. Ya yafe mana, yasa kar6a66iyar ibada mukayi🙏🏻😭._ Sai dai banci naman salla ba sosai, gashi banida d'inkin dallah🤦🏻‍♀🤥. ______________________________ ~Book 2~ 👉🏻1⃣ .............Tunda mukayi maganar nan dashi banyi k'asa a gyuwa ba wajen dagewa da addu'oi wa mahaifinsa, ina buk'atar ruwan zam-zam, dan haka yau nashirya fad'a masa ya nemomin. tunda safe ya fice, dan haka bamuga juna ba. Yauma dai haka Na tashi banida wata isashshiyar lafiya, Na tak'ark'ara nayi gyaran d'akin har zuwa falo, sannan Na had'a ruwa mai zafi nayi wanka dashi. Ina cikin shiri najiyo sallamar Samha a k'ofar falon, rigar dana fara sakawa Na k'arasa, sannan nace ta shigo. “humm Aunty gimbiya kina kallon kanki a mirror kuwa?”. Cikeda mamaki Na kalleta sannan Na kalli jikina, nace, “kamarya?”. Zama tayi a sofa tana 'yar dariya, sannan tace, “wlhy kinyi k'iba, sati uku kacal da zuwanmu India kin koma wata madam”. Nad'an fiddo idanu waje, sannan Na harareta, “lallai Samha nagode da zagi to”. “tab wlhy babu wani zagi gaskiya Na fad'a, halan Uncle Sam bai ta6a fad'a mi ki ba........” Ta k'arasa Maganarta da d'ai-d'ai saboda shigowarasa d'akin da sallama ciki-ciki. Suna had'a idanu ya watsa mata harara, hakan ya tabbatar mana da yaji maganar tata, da sauri tamik'e ta fita, Nikuma najawo gyalena na yafa sannan Na kallesa. Saman sofar ya zauna ya dafe kai, kallo d'aya zaka masa ka karanci damuwar dake shimfid'e bisa fuskarsa. “yalla6ai lafiya kuwa?”. ‘nafad'a cikin tausayawa’. Shiru bai amsaniba, banyi zuciyaba nataka a hankali zuwa gabansa, durk'usawa nayi a gaban nasa, a d'arare nasa hannu Na najanye nasa dayay tagumi dashi. Ya d'ago idanunsa da sukai jaa yana kallona. kasa jurar kallon cikin idonsa nayi, Na janye nawa gefe, cikin dakiyar zuciya nakuma fad'in “bakada lafiya yalla6ai?”. Yanda nayi maganar a marairaice saiyaji yakamata ya fad'amin, kodan nuna damuwar danayi akansa...... Ganin yamin shiru nikuma saina yink'ura natashi ina fad'in “kayi hak'uri idan nashiga hurumin daba nawab......” Bankai k'arshen maganarba naji tattausan tafin hannunsa cikin nawa. Rintse idanuna nayi, saboda wani yarrr da tsigar jikina tayi, shima agaresa saiya lumshe idanu kawai. najuyo danufin zare hannun kawai ya fisgoni na fad'a saman kujerar, rabin jikinna duk yana a jikinsa, yayinda sauran rabin nake a kan kujera. Bansan nawani lumshe idanuba saboda daddad'an k'amshin turarensa d'aya ratsa hancina zuwa magudanar jinina. shikuma ya sauk'e 6oyayyiyar ajiyar zuciya. Ya karkato da fuskarsa inda tawa take a gefen kafad'arsa har inajin saukar numfashinsa saman face d'ina, mayun idanun nan nasa suka kuma shiga cikin nawa, na janye da sauri, sannan nafara k'ok'arin cire kannawa daga kafad'arsa. Hannunsa na dama da nake jiki ya sak'alo ta bayana, ya maida kai na ya kwantar a kafad'ar tasa, cikin muryarnan tasa mai kama da anmasa tilas yace, “jikin Abie ne ya motsa, Ashe tun jiya basuyi barciba gaba d'aya, da safennan Akash yakirani yake sanarmin, nakasa kallon halin da mahaifina yake ciki Munaaya! Abie na yana cikin mawuyacin hali..” ‘yak'are maganar cikin zirarowar kwallar data cika masa idanu tunda yafara maganar’. Wani matsanancin tausayinsa ne ya ratsani, duk jarumtar Galadima kaga yana kuka ai kasan lamari ya 6aci gaskiya, nima hawayen suka fara gudun fanfalak'e a kumatuna, tashi nayi zaune sosai, cikin wata jarumtar da bansan inada itaba nasaka hannu Na kamo hannunsa cikin nawa. Sai kawai naga ya zame sosai ya kwantar da Kansa bisa cinyata, tareda hard'e hannayensa a k'irji. duk da kujerar tama tsawonsa kad'an, dan ma Love's chair ce. Kansa nafara shafawa a hankali, hawaye na zirara daga idona har yanzun. Shikam idanunsa a lumshe suke. Cikin tausasa harshe da tsantsar Nuna kulawa da tausayawa nace, “Yalla6ai kayi hak'uri, Abie d'inmu yana buk'ar addu'armu ne fiye da kukanmu, sannan itace jarabawarsa, wad'anda suka aikata masa hakan summa kansune, domin ALLAH bazai barsuba. idan ka amince akwai wasu addu'oi Dana Sani, Nina kakanmu ne yabama innarmu kafin yarasu, shine ta koya mana, mizai hana ka samo mana zam-zam muma mu farayima Abie su, Ubangiji gafurun rahimunne, babu abinda ya gagaresa, kuma shine yace mu rok'esa zai amsa mana”. Tunda nafara maganar bai bud'e idonsa ba, nikuma ban fasa shafa masa kaiba. Saida nakai k'arshen zancen sannan ya bud'e lumsassun idanunsa dasuka koma launin jaa a kaina. yamotsa baki kamar zaiyi magana saikuma yayi shiru. Nima shirun nayi ban sake yink'urin yin magana ba, nadai cigaba da shafa kan nasa a hankali. ba akai 3minutes ba barci ya d'aukesa, sai numfashinsa danaji yakoma sauka a hankali. Ajiyar zuciya na sauke kawai, na tsurama fuskarsa ido, yaune ranar farko dana ta6a nutsuwa namasa kallon tsaff, sosai yake kamanni da dukkan iyayensa, Abie da Momma, amma yafi tsananin kama da Momma gsky, duniyar tunani nafad'a batare dana fargaba, tausayin Galadima da families nashi yana cukurkud'ar ruhina, insha ALLAH nayi alk'awarin bada gudun mawa a duniyarsu har zuwa lokacin da aurenmu zai k'are. kaina na jingina da jikin kujera, nima sai barcin ya kwasheni, dama bajin dad'in jikina nakeyiba. ******** Bayan anma Abie allurar datake temaka masa yin barci mai nauyi idan jikinsa yamotsa irin haka su Momma suka sami nutsuwa, dan yayi barci. Sai alokacin hankalin Momma yadawo kan Neman Galadima, tabbas taga yafita hankali a tashe lokacin da Abie ke fidda numfashi a wahale, amma hankalinta bai koma kan Galadiman ba. Aunty Mimi ta kalla tace, “Mimi ina d'an uwanki?”. Itama aunty Mimi sai yanzu hankalinta yadawo ta farga babu Galadima d'in, hankalinta a tashe tace, “Momma inagafa ya fita, bara na duba”. Bata jira cewar Momma ba tafito daga d'akin da sauri. ganin babu Galadima a wajen hankalinta yak'ara tashi, fitowa tayi harabar asibitin tana tambayar securitys d'in wajen. d'aya ya sanar mata ya fita a rikice gaskiya, dan suma sun nemi su taimaka masa amma baima tanka musuba. Innalillahi tashiga ambata. Bata koma wajen Momma ba tashiga mota tanufo gidan. Ta iske Samha a falo kwance, ko sauraren sannun datake mata batayiba tace, “k ina Uncle d'inku?”. Samha tace, “yana sama Mummy”. Da sassarfa ta haye step's d'in, itadai Samha da mamaki taringa binta da kallo. Ko knocking bata tsaya musuba ta turo k'ofar ta shigo. Ajiyar zuciya ta sauke dan ganin Galadima kwance, kansa bisa cinyar Munaya, hannunta d'aya na bisa Kansa, yayinda shikuma yarik'o d'ayan hannun munaya ya had'e da nasa ya d'ora kan kirjinsa, suduka barci ya kwashesu a haka. cikin sand'a ta juya ta fita taja musu k'ofar tana share hawaye dayima ALLAH godiya d'aya bama d'an uwanta mace tagari wadda take kulawa dashi. inda dane kafin yayi aure shima sai ciwonsa yatashi saboda damuwar dazai saka Kansa akan motsawar jikin Abie, amma gashi yanzun yasamu mai kwantar masa da hankali, suma kuma nasu ya kwanta suji da Abie kawai. Momma ta kira ta fad'amawa dan hankalinta itama ya kwanta. Momma harda hawayen farinciki, tana godema ALLAH. Aunty Mimi bata zaunaba suka koma asibitin itada Samha da tace zata bita, itama sai yanzu takejin jikin Abie ya motsa. ************* A k'alla munyi barcin 47minute's, Galadima ne yafara farkawa, ya bud'e idanunsa a hankali, hannuna dake rik'e a nasa yafara kallo, kafin yad'ago ido zuwa kaina, yamin kallo kusan na 2minutes sannan yad'an motsa da nufin gyara kwanciya, saina bud'e idona, ido muka had'a, kowa yay saurin janyewa cikin basarwa, hannuna dake kansa na cire, sannan nazame Wanda yarik'e d'in, dan wata matsananciyar kunya ce kuma takamani. Shima sai ya tashi zaune sosai, a hankali yacemin “thanks”. Daba kusa dashi nakeba ma bazanjiba. Bance komaiba, shima bai sake cewa komaiba yamik'e tsaye. takalmansa kawai yacire ya d'auki jallabiya a wardrobe d'insa yashige bayi. A hankali na sauke ajiyar zuciya, tareda janye idona daga k'ofar bayin, komai banceba nakuma zamewa saman kujerar na kwanta. Ya d'auki adadin wasu mintuna masu tsawo kafin yafito sanye da jallabiya ruwan toka, da alama wanka yayi, kallona yayi batareda yayi magana ba ya nunamin agogon dake ajiye a drowan gefen gadon alamar time d'in salla yayi. Kaina kawai na girgiza na mik'e, zuciya ta na mamakin hali irinna Galadima. Shikam turare kawai ya d'auka ya fesa yafice salla. ★★★ ((★))(())((★)) ★★★ A gidanmu kam hankalin mamansu yaa hameed da Zarah a tashe yake, dan babu Sa'eed babu labarinsa, kira Zarah tamasa yafi 50 amma yak'i d'agawa, ta tura massages babu reply, bata aikin komai sai kuka, ga ciki. Abbanmu kuma jin sanadin sawowar tata gida yace bazai kira Alhaji halliru ba har sai Zarah tafad'i ainahin gaskiya, danshi bai yarda ba itace ta d'auki kud'inba.. Innarmu dai dasuke zagi suna kallonta mak'iyarsu batakai komaiba itace tashiga lalla6a Abba damasa magiya. Itama da farko buris yay da ita, saida yaga tanace sannan yace, “wai kekam Ai'sha miyasa kika damu kankine? kinbi kin damu da lamarin wad'anda basu damu dakeba, na tabbatar da Munaya ko Munubiya ke cikin wannan halin su murna zasuyi a gidannan”. Murmushi innarmu tayi, cikin kwantar da murya tace, “Alhaji ai daga Zarah harsu munubiya duk d'ayane a wajena, domin kaine mahaifin Zarah, dukkan abinda kuma yakasance naka ina kaunarsa fiye da zatonka, a duba lamarin yarinyar kodan abinda ke gabanta, ba'a son mace mai ciki da shiga tashin hankali, muyima tufk'ar hanci tun munada sauran dama, basai Abu yayi tsamariba kuma muce zamu nemo mafita, hannunka baya ru6ewa ka yanke kayar alhaji, dan ALLAH kayi hak'uri kaji”. Jawota yayi jikinsa ya rungume yanamai saka mata albarka da aminta da buk'atarta na kiran senator halluru da safe insha ALLAH. Innarmu tamasa godiya itama. ********** “Babyna wai mike faruwane haka?”. Da gyar Munubiya ta d'ago ido daga kwancen datake a kujera ta kalli yaa Marwan dake mata tambayar. Ta shagwa6e fuska tace, “wlhy Yaya jikinne babu dad'i, kamar jiya sai kwankwatsa kasusuwane keyi”. Zama yay kusada ita, yad'ago kanta ya jinginata a jikinsa yana ta6a wuyanta, “please ki yarda muje asibiti adubaki mana?”. “a'a dan ALLAH Yaya, wlhy banason zuwa, kabari muga kwana biyu idan bai dainaba saimuje d'in”. “Amma kuma k'ya zauna da ciwo, ki daure dai, kinga ko abinci kin kasa mana fa”. “babu damuwa Yaya, yanzu zan tashi na d'ora, dan zazza6inma ya sauka ALLAH”. “Ana dai so aima Yaya wayo kawai”. Murmushi tayi tana tashi daga jikinsa,, takama hannunsa ta sumbata sannan tatashi tafice daga falon. Binta kawai yay da kallo yana murmushi, yana k'aunar matarsa kuma 'Yar uwarsa, gaba d'aya Munubiya ta canjashi, dukda bawai miskilancinsa yabariba, itace kawai yanzu baya iyama miskilancin nasa, komai a d'auren da fuskarsa take da zarar ya tunkaro gida zakiga yafara sakin murmushi, balle yay tozali da fuskar tauraruwar nan tashi mai haske da kawalwalniya a zuciyarsa. Mik'ewa yayi yabi bayanta zuwa kitchen d'in danya taimaka mata da aikin, dan yau d'in weekend ne baije aikiba. dan yayi resume tun last week. ((★))*((★))*((★))*((★)) Tunda na idar da sallar nazame a wajen na kwanta, bawai barcin nakeba, jikinane kawai da baya min dad'i, jinake kamar ana kwankwatsamin kashin jiki, sallamarsa tasakani d'ago ido na kallesa, sannan na amsa ciki-ciki nima. Frigate ya bud'e ya d'auki ruwa yakoma saman sofar ya zauna, murfin kawai ya 6alle ya hau kwankwad'a, saida ya shanyeshi tas sannan ya ajiye goran yana sauke tagwayen ajiyar zuciya. nikam na k'ura masa idanu nakasa janyewa. saida yad'ago muka had'a idanu sannan nayi saurin yin k'asa da nawa. Shi bai janyeba yana kallona yace, “tashi muje hospital d'in, daga nan saimu samo zam-zam d'in”. Tunkan yakai k'arshen maganarma na mik'e tsaye, hijjab kawai nasaka nad'an gyara fuskata, shikuma ya d'auki kaya yashiga bayi ya canjo sannan muka fice. Jin gidan shiru yasashi d'aukar waya yakira sashen bayin gidan, babu dad'ewa saiga d'aya acikinsu tazo. Zubewa tayi tana gaishemu, ya d'aga mata hannu yayinda nikuma na amsa. yace, “ina Samha?”. “Ranka ya dad'e sunfita suda mummy”. Yasan aunty Mimi take nufi, dan haka bai sake cewa uffan ba yafice abinsa. sai nice nace tatashi taje, sannan nabiyoshi abaya. Sai da yasakama k'ofar security sannan muka nufi wajen motarsa, bayin dake zaune a harabar gidan maza sukazo da sauri suna gaishemu, hannu kawai suma ya d'aga musu muka shiga motar, suka bud'e mana gate d'in muka fice. Tunda muka fita babu Wanda yay magana tsakanin ni da shi, yana aikin tuk'insa da sauraren redio daya kunna a motar, nikam ina lafe a kujera ciwo ya isheni, dan bana fahimtar yaren dasukeyi a redio d'in, tunda ba English baneba gaskiya. Mun Isa wani babban shagon Islamic camix, komai zaka iya samunsa daya shafi maganin muslinci. Abinda ya kaimu muka shigayi, yad'ebo zam-zam dayawa, sannan ya kalleni yana fad'in “saikuma mi?”? Shiru nayi ina nazari. Dame yakamata muk'ara?, zuwa can nad'an hau duddubawa ina karanta sunayen magungunan ajikin kwalin, duk maganin danaga zai iya shafar jinnu ko sihiri, saida na d'akkoshi, (a tunanina idan mun dawo gidan zan d'auki hotunansu na turama Munubiya ta bincikamin yanda yadace ayi amfani dasu. Duk abinda nake yana a tsaye yana kallona, saida na kammala sannan nasanar masa na gama. Mun k'arasa wajen biyan kud'i, bayan yabiya yaran shagon d'aya ya d'aukar mana zuwa mota. Daga nan asibitin muka nufa, mun tarar har lokacin Abie yana barci, sai gaisawa nukayi da momma da aunty Mimi, duk sunji dad'in yanda sukaga Galadima cikin nutsuwarsa. Zama yay kusada Abie yana mai tsurama masa idanu da masa addu'oi samun lafiya a zuciya, da kuma kudirar binne Wanda ya cutar masa da mahaifi da ransa idan ya kamashi a hannu. Momma tayi farinciki da yanayin Galadima d'in cikin k'oshin lafiyarsa, dan da a dane da yanzu shima yana gadon asibitin, amma Alhmdllh yanzu gashi normal. Mukam ni da Samha muna gefe zaune muma, ba hira mukeba, kowa yayi shirune yana tunanin duniya. Sauban ma yana dawowa daga school shida Khaleel nan suka taho. Bamu bar asibitinba sai dare, harda Momma muka wuce, dan yau suna buk'atar Abie ya kwana tare da ma'aikatansu. Koda muka shigo Galadima sama ya wuce abinsa, ganin haka Momma tace natashi na naje nima na kwanta na huta hakanan. A kunyace na mik'e domin cika umarninta. Na iske yana cire kaya, dan haka nakoma da baya zuwa falo, saida na kintaci yagama sannan na shigo, na iskeshi yashiga wanka, nima natu6e nawa na d'aura zani nasaka hijjab tareda d'aukar kayan barcina ina jiran fitowarsa. Bai dad'eba sosai kuwa yafito, sanye yake da bathtub fara tas, ban yarda na kalleshi ba natashi nashige nima. Mai makon yayi shirin barci saiya kwanta a bakin gadon a haka, k'afafunsa na k'asa, ya tsurama rufin d'akin idanu alamar yatafi duniyar tunani. Nikam ruwa mai zafi na had'a nashiga koda zanji dad'in jikina, na dad'e acikin ruwan kwance, jinakema kamar karna fito. shikansa yafara tunanin lafiya kuwa?, lokaci-lokaci yakan kalli k'ofar bayin, Amma babuni babu dalilina. Yana shirin zuwa yamin knocking sai gani nafito kuma, janye idonsa yayi daga saitin k'ofar cikeda basarwa. Ni bammasan yanayiba, dama nayi shirin barcina tun aciki, saina d'auki zani na d'ora a saman kayan nasaka hijjab nayi sallar shafa'i da wutiri, bayan na idar nad'akko roban zam-zam d'in d'aya na zauna nafara karatu Qur'an acikin ruwan zam-zam d'in. a hankali nake karatun cikin nutsuwa, dukda barcin dakecin idona. Har cikin 6argonsa da jini yakejin sautin karatuna, ya lumshe idanu yanamaijin kamar mu kwana a haka inayi. mik'ewa yayi shima yayo alwala yazo yay shafa'i da witiri yay joining d'ina muka cigaba da karatun a tare. Bamu kwanta ba saida mukayi sallar asubahi. (da yake sai zuwa 1 zasu bari ashiga wajen Abie, yau kuma babu aiki). ____((()))((*((()))*))((()))____ Yauma dai haka innarmu tadagema abbanmu saida yakira Senator Halluru agabanta, dan Zarah tana kwance babuma lafiya, ga mamansu Yaa Hameed ita kanta kallo d'aya xaka mata kagane abirkice take. Innarmu duksai suka bata tausayi, matan gidanmu kuwa abin magana yasamu, sai gulma da dariyar gatsatsa, ita kanta Momy Hadiza ta hannun damar mamansu yaa Hameed d'in dad'i takeji, tanadai nuna damuwarta agaban mamansu Yaa hameed d'inne. Bayan Abba sun gaisa da Senator halluri sukad'anyi barkwancinsu na abokai sannan yasakko xancen Zarah. Hankalin Senator halluru yatashi, danshi koda wasana baisan Zarah bata nanba, yadai lura kullum Sa'eed saiyaje gida yaci abinci, shi duk zatonsa Zaran bata iya girkine saboda ciki. Hak'uri yashiga bama Abbanmu yace wlhy shi baima saniba, amma insha ALLAH zai bincika, zuwa dare sa'eed d'in zaizo ya d'auki matarsa. Dahaka sukai sallana da Abba kowa nakuma bama d'an uwansa hak'uri akan lamarin. Innarmu bata buk'atar jin k'arin bayani dantaji komai, takumaji dad'i sosai. ()-()-()-()-()-()-()-()-()-()-()-()-()-() Jikin Abie dai kam yayi tsanani a tsakaninnan, yau kwana biyar kenan lamarin sai addu'a, dan baisanma Wanda yake a kansa ba, mai martaba Sarki Abdul'fatah ma yazo shida inno matarsa, (wannan ne karon farko dana gansu ido da ido), mutanen kirki masu d'aukar kowa nasu, duk da d'ar-d'ar danai tayi haka sukaita jana ajikinsu. yanda Galadima yake zubama inno da papi shagwa6a sai abin yaso bani dariya, amma dai sun birgeni, mu a gidanmu wazaima innaro wannan ta6arar bata k'arema uwarsa tanadiba, ba kamarma mu 'yan d'akinmu. hakama sarki jalalludden shida uwargidansa sunzo da mama Fulani. Ranar momma har tausayi tabani, kai mama Fulani batada kirki wlhy, idan kunga yanda take shinfid'a mulki a asibitin nan. Hummm🤦🏻‍♀. Galadima ne kawai maganinta, tamasa magana ya dage ya ya6a mata bak'a shikuma. Ba gidan suka saukaba, a hotel suka sauka, dan haka yau mun iskesu a asibitin sun rigamu zuwa. Tunda muka shigo mama Fulani ta zubamin ido, Galadima ya gaida mai martaba da matarsa yakoma kusada Abie ya zaina. Nima k'asa na durk'usa na gaidasu su dukansu har Momma da aunty Mimi. Momma ta nunamin kusada ita alamar nazo na zauna kusada. banyi musuba naje na zauna, dan kallon k'urillar da Mama Fulani kemin duk sai na takura. Tad'an ta6e baki sannan ta gyara zama idonta na kaina, tace “toke amarya halan saikin tashi haihuwa zaki koma mana? daga zuwa dubiya kuna Neman share wata 1 a india”. Gaba nane yafad'i, dan nafahimci dani take, saina rasa amsar dazan bata.. 'Yan d'akin kam kowa ido ya zuba ma mama Fulani har Galadima. Aunty Mimi ce tace, “Ranki yadad'e Kodai kina Kishine haka? Amarya ta kwance Miki fada wajen mai gidanki?”. Ajiyar zuciya Momma ta sauke a hankali, taji dad'in yanda aunty Mimi ta mayar da maganar wasa, ko nad'an batason abinda zai munana Munaya ko muzantata, dan bataso yarinyar taji kamar ita dabance a cikinsu......... Wani munafukin murmushi mama Fulani tayi, ta kalli Galadima da zuciyarsa tafara hasala akan tsohuwar, kamar daga sama sukaji tace, “cikin namu wata nawane Galadima?”............✍🏼 E me🙆🏻 mama Fulani mai gani har hanji🤦🏻‍♀. *_ALLAH ya gafarta na iyayrnmu😭🙏🏻_* [7/3, 9:54 AM] Aysha Galadima: *_Typing📲_* *_Haske writer's asso...._*💡 *_♦RAINA KAMA......♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻 ~Book 2~ 👉🏻2⃣ ..............Shiru Galadima ya mata, da ace babu Momma daya ya6a mata maganar da har tabar India tana mata zafi kuwa. amma duk da haka maganar ta daki zuciyarsa, bai saniba ko zancen tsohuwarnan gaskiyane. Momma da Aunty Mimi da matar sarki kuwa kallona duk sukayi, nayi k'asa da kaina gabana Na luguden duka, saboda zancen tsohuwarnan yana son tsoratani. Shigowar Sarki Abdul'fatah (papi) da inno matarsa da mai martaba Sarki Jalaluddeen ce ta tak'aita zancen. dan daganan kowa yasaki maganar, saidai munata juyata a zukata ni da Galadima, yayinda aunty Mimi da Momma ke fatan ALLAH yasa hakane. _____________________________ Misalin 8:pm saiga Sa'eed yazo gidanmu, a time d'in gwaggon Haleematu da mamansu yaa Hameed suna ta hayaniyar fad'a, wai mamansu yaa Hameed ce takama gwaggon Haleematu tana kallon Zarah dake alwala a fanfo tana dariya. Shinefa mamansu yaa Hameed tace gwaggon Haleematu taci kanta tasha bak'in ruwa, karta lashe mata jika tun yana a ciki. Wannan kalma ta mamansu yaa Hameed itace tajawo fad'a, Dan gwaggon Haleematu tace mamansu yaa Hameed tace mata mayya bazata yardaba. Fad'a sosai sukeyi suna cin zarafin juna da gori, dama kowa kishi Na cinta a zuciya. Matan gidanmu duk sunyo waje anrasa masu dakatar dasu sai innarmu dake cewa suyi hak'uri Dan ALLAH, darene fa. Amma Sam sunk'i saurarenta. Innaro dataji hayaniyar tundaga gidanta yasata d'akko fayafi tafito, kamar anjehota haka tashigo gidan. Sa'eed da Sulaiman suna awaje a mota, duk badak'alar da akeyi daga cikin gidanmu suna jiyowa, har shigar innaro kuwa suna kallo. Dayake su Abbanmu suna masallaci. Innaro tanata magana sunk'i saurarenta, saiyi sukema kamar zasu fara danbe. Mamansu yaa Hameed Na k'ok'arin kwalama gwaggon Haleematu ludayin miya dake hannunta innaro takawo jiki zata kare sai a goshinta, jikake kwarrrr!. Tako dafe goshi tafasa k'ara.. Hakan kuma yay dai-dai da shigowar su Abba gidan, su duka ukun, tunkan sushigo sukejiyo hayaniyar dama, dukansu rai a 6ace suka shigo. Dan iskancin matan nasu ya ishesu hakanan, idonsu yarufe ko ganin motar su Sa'eed basuyiba. Ran Abba yakuma 6aci, Dan ganin duk matansa ne ma masu hayaniyar, ga abinda sukaima mahaifiyarsa akan idonsa. batareda yabi ba'asiba yace duk sufice su bar masa gida. Ananne kowa yay tsitt, yadaka musu tsawa yana fad'in wlhy idan basu fitaba zaisa a fiddasu, ko d'akunansu bai yarda wata takomaba kuma. Dole sai 'ya'yansu suka d'akko musu hijjabai suna kuka da bama Abban hak'uri. Amma yak'i sauraren kowa, daddy da baba k'arami kuwa babu Wanda yay yunk'urin hanashi. Innarmu tamatsa kusadashi tana rok'onsa karyayi haka, yazauna ya sauraresu tukunna, Hararar daya zuba matace yasata jada baya tai 6am da bakinta. Innaro kuwa maman safara'u ce takamata ta zaunar, goshi harya fara kumbura🙆🏻. (((+)))***(((+)))***(((+))) Kafin mu baro asibitin nama manta da maganar mama Fulani, saboda murnar bud'e ido da Abie yayi ta d'aukema kowa hankali kuma, gaskiya ina tausayin bawan ALLAHn nan sosai. yauma bamuyi k'asa a guywa ba wajen cigaba da addu'oin damukeyi cikin zam-zam ni da Galadima, somuke muyi na 1week sannan afara bashi. Washe gari Alhmdllh jikin Abie yayi k'yau sosai, Dan inka gaidashi yakan maka murmushin sa Na dattako, hakan ya sanya su papi sukayi shirin tafiya da yamma. Ni da Galadima da Sauban muka musu rakkiya, sainaji tamkar nabisu. Harda 'yar kwallata kuwa. Inno tanata tsokanata, Dan tsohuwar tashiga raina sosai. Tunda muka d'akko hanyar dawowa asibitin nakife kaina a cinya inata hawaye, sauban ne kawai ke tsokanata, amma Galadima tamkarma baya cikin motar. hakan saiya k'ara tunzura zuciyata, nakuma k'ara k'arfin kukan nawa. Sauban yasamu guri yay parking, da hannu Galadima yamasa alamar yaje. Fita yay yana k'uk'uni da k'umshe dariya, wai “su boss za'ayi lallashi shine aka koroni”. Saida yay nisa da motar sannan yasami damar dariyar, har yashiga wajensu Momma. Daga Momma har Aunty Mimi kalli onsa sukeyi,, aunty Mimi tace, “Auta lafiyarka kuwa?”. Saida ya zauna sannan yashiga kora musu bayani, dariya kawai sukayi, sunsan Sauban babu sauk'i wajen taso mutum agaba. Tunda Sauban ya fita sai Galadima ya gyara zamansa kawai ya zubamin ido, mutum ne shi dabaya son shiga hak'in wani, ko kad'an baiso ace wane yana cikin damuwa ta dalilinsa...... Wayarsa aka kira, ya kalli wayar kafin yakai hannu ya d'auka, salamar da akayi daga can ya amsa suka gaisa. Jin ya ambaci Nuren nagane da Wanda suka ta6a yin waya kwanakine, nad'an tsagaita da kukan ina sauraren mizasu tattauna. Galadima naji yace, “miya farune kakeson nazo Nigeria haka da gaggawa Nuren”. “no babu wani damuwa, driver da yarinyar nanfa suna hannu, so yakamata ka shigo muyi abinda yadace ko?”. “ok babu damuwa, insha ALLAH zuwa Wednesday idan jikin Abie ya kuma lafawa zan shigo”. “O right, ALLAH ya k'ara masa lafiya, a gaishesu”. “zasuji insha ALLAH, bye”. Wayar ya ajiye a tsakkiyarmu ya maida hankalinsa kaina. Cikin wani salo yace, “Munaaya!”. Wani Yarr naji a jikina, karo na biyu kenan danaji sunana a bakinsa, sainaji sunan nawa ya canja kamar ba shiba, danya iya sarrafa sunan a harshensa..... ganin ban d'agoba yakuma kiran sunan. Kasa jurewa nayi nad'ago idona na kallesa, ganin ya tsareni da idanu saina janye nawa. yad'an lumshe nasa ya bud'e a kaina ya furzar da huci “kina ganin haka abokai yakamata su kasance? ni friend nakine, miyasa bazaki iya fad'amin damuwarki ba? kiyi hak'uri nasan kina buk'atar zuwa gida, last week naso maidaki Nigeria, amma sai jikin Abie Daya motsa ya dakatar dani”. Tausayi yabani, nad'ago na kallesa, mutumne shi mai sauk'in kai, saidai idan baka fahimceshi ba zaka sameshi a amurd'e, domin yanada wahalar sha'ani, hawayen dasuka ziraromin na goge, muryata na rasa nace, “kayi hak'uri ina kewar su Munubiya ne, insha ALLAH bazan sake yin kukanba amma”. Murmushi yaymin yana jinjina kai, yad'an shafa girarsa zuwa kai sannan yace, “kinada tsiwa, amma wani time d'in kinada kirki”. Bansan lokaci da dariya tazominba, nad'an dara sannan nace kaima ai hakan kake, kanada tsauri kanada sauk'i”. Yawani k'ank'ance idanu cikin wani salon kallon yace, “really?”. Gira d'aya na d'aga masa nima nace, “yaah”. Murmushi mai k'ayatarwa yayi yakwashi wayoyinsa yabud'e motar yafita batare data sake cewa komaiba. Ganin haka nima saina fito fuskata washe da murmushi, kamar banice nagama kukan shagwa6a ba😉. Tunda muka shigo aunty Mimi da Momma suka zubo mana ido, Sauban kam dariyar shak'iyanci yafara k'asa-k'asa. Momma tace, “ina kuka mak'ale haka?”. Murmushi yayi yana zama kujerar dake kusada Abie yace, “ba ko ina Momma”.. Momma tayi 'yar dariya tace, “shikenan tunda ba'aso muji”. Sauban da Aunty Mimi ma dariya sukayi, nikam kunya tasani k'asa da kaina inad'an murmushi. __((*))__((*))__((*))__((*))__ Abba dai bai yarda su maman yaa Hameed su kwana a gidanba, a daren kowacce tanufi gidansu, yayinda baba k'arami ya d'auki innaro zuwa asibiti. Su Sa'eed kam zare jiki sukai suka koma gida, zukatansu tab da mamakin wannan lamari. A ranar zarah sai sashenmu ta kwana a tsohon d'akinmu ni da munubiya, saboda Aminu ya sanar mata yaga Sa'eed da mijin Siyama a k'ofar gidanmu. Gaba d'aya saitaji yau tanajin haushin mamansu, dan daba ta tanka dariyar da gwaggon Haleematu tamata ba ai dabasuyi rigima har Abba ya korasu gidaba, dayanzu gidanta zata kwana jikin mijinta itama, wane irin abin kunyane wannan kai kana gida uwarka na gidansu itama🤦🏻‍♀. %%%%%%%%%%%%%%% Dawowarmu kenan ni da Sauban da Samha daga zagaya gari, nagaji ovar, jikina sai ciwo yakemin, dama Yaya lafiyar giwa, saman sofa na zube Ina sauk'i numfashin wahala, wani zazza6ima nakejin yana neman rufeni, harna rufe idanu naji wayata na wringing, lalubowa nayi na duba mai kirana, nasan dai duk Wanda zai kirani to daga Nigeria ne, dan su Samha duk suna gida, Galadima kam bai ta6a kirana a wayaba, banmayi tunanin yanada number ba duk da shine ya sayi layin. Sunan munubiya dana gani yasani fad'ad'a murmushina, saida nabari ya katse sannan na kirata. Bugu biyu ta d'aga, jin muryarta can k'asa sai hankalina ya tashi, nashiga tambayarta ko lafiya. “sweetheart wlhy banajin dad'i, ko school nakai sati banjeba, ya kuke?”. “ayya sorry sweetheart, mike damunki?”. “wlhy zazza6i, kema naji muryarki wata iri ai?”. “nima lafiyar sai a slow wlhy, ina yaa marwan?”. “tofa, ciwo a time d'aya mu duka? ALLAH yabamu lafiya to, yaa marwan yafita gaida su mama, ya jikin Abie da Galadima?”. “everything Alhmdllh dear, jikin Abie ma yanata sauk'i, sun fara masa amfani da addu'oin, amma naji kamar doctors d'inshi suna complain wai abar shafa masa abinda ake shafa masa”. “karku wani sauraresu, Ku cigaba kawai, ALLAH yasa muji alkairi”. “insha ALLAH dear, dama haka Galadima yace shima”. “ALLAH ubangiji yabashi lafiya, bara na barki ki huta, a gaida minsu”. “ok sweetheart bye”. Ina ajiye wayar na mik'e, bayi nashiga nahad'a ruwa mai zafi nagasa jikina kozanji dad'i, haka nake kusan yini wanka da ruwan zafi, wai ko zan dainajin ciwon jiki, amma a banza, danayi wanka bana wuce mintuna talatin ciwon yake dawowa sabo. Wani ash d'in wando da Riga na jawo na saka, kayan basuda nauyi sosai, wandon kad'an yawuce guywata, rigar kam hannunta iya kafad'a ya tsaya, kamardai vest d'in maza take, saidai daga gaba tanada banbanci data maza. nasan Galadima bazai dawo gidan yanzuba saboda koya tashi aiki saiya biya ta asibiti kafin yazo gida, yanzu kuma akayi isha'i nasan sai zuwa irin 11, shiyyasa nayi tunanin sakasu ko zan ragema kaina nauyin jikin. komawa nayi saman sofa data zama gadona na kwanta, amma sai naji dukna takura, najujjuya naji babu dad'i kwanciyar, tsaki nayi namik'e nakoma saman gadon na kwanta, insha ALLAH kafin maishi yadawo dai natashi😏. Banfi 5minutes ba da kwanciya barci ya d'aukeni. ***** Kansa daya fara matsa masa da ciwone yasashi tattara kayansa yabaro office, Dan yau sunyi overwork ne, suna shirin fidda laptop sabon k'ira, saida yashiga office d'in vijeey da Alexander yamusu sallama sannan yanufo gida, ko asibiti bai biyaba, Dan har wani jiri-jiri yake gani a idonsa, yasan barcin dabasa samun yine ya haddasa masa ciwon kan, bama kamarshi, Dan gara ni idan yafita nakan kwanta nayi barcin. Da k'yar ALLAH yabashi Damar isowa gidan. Ko rufe motar baiyiba sai a cikin bayin ne wani yataso yarufe, a falo ya wuce Samha na barci itama, tunda muka shigo ta zube a wajen, tun yana taka steps d'in yafara cire bottom d'in Indian suit d'in dake jikinsa white color, burinsa yana shiga d'akin yagansa a gado kawai. Ganina baje a gadon yasashi yin turus yana kallona, yay saurin kauda idonsa gefe saboda kayan jikina sun kamani sosai, sun mugun fito da surar jikina d'as, gashi sun bala'in min k'yau, yau da ace matar dayake soce babu abinda zai hanashi yabawa harma yabata tukuycin wannan kwalliyar, tsigar jikinsa sai tashi takeyi, gashin jikinsa duk ya mimmik'e, rigarma yakasa k'arasa cireta, ya dafe kansa yanajan guntun tsaki, miya kawo yarinyarnan gadonsa?. Yayi maganar cikin zuciyarsa. Jin jiri na neman zubdashi a k'asa yay saurin zama bakin gadon, samu yay ya lalla6a ya ida cire kayan, duk da yafi buk'atar kwanciyar haka ya daure yad'an watso ruwa, sannan yafito yasha magani, koma shafa'i da wutiri baiyiba, a nufinsa sai zuwa anjima zai farka yayi. Abin dariya, saiya jawo dogayen filullukan gadon yajerasu a tsakkiyar gadon sannan ya kwanta can k'arshe, shima babu dad'ewa barcin yay gaba dashi. (Wlhy kafad'o babu ruwana fad'ama fans zanyi Galadima ya tik'o k'asa ehe😏🤨🤣🤣) Can cikin barci Galadima yafara juye-juye, yasaba shi kad'ai yake kwana abinsa, jin fillos a gabansa yasa hannu ya d'aukesu yayta wurgawa k'asa cikin barci, sannan yay juyi zuwa tsakkiyar gadon. Munaya kam tasaba da kwanciyar mutum biyu. dan haka ko juyin zatayi bata barin inda take kwance, duk da ma batasan da Galadima a gadon ba, tunda batasan ya shigoba. Barci yay barci saiga su yalla6ai Galadima masu jera fillos a jikin munaya😂, d'umin jikinta yasashi kuma nanik'e mata, saboda zazza6in daya rufeta, kasancewar yanajin sanyi-sanyi sai jikinta yamasa dad'i. Itama saita kuma lafe masa a jiki saboda jin sanyi-sanyi da k'amshin turarensa kuma, sunbi sun k'adandane juna kaikace ana shirin rabasune, kowa yana amfanuwa da yanayin jikin d'an uwansa. Humm, bara na lek'o su innaro 'yan Nigeria suma🤗, mai tuk'ulluma a goshi ba🤭🤫, ni nama godema mamansu yaa Hameed🤣 dama k'afar suka karya😝. _____________________________ Anbama innaro magani a wani camix suka dawo gida, gidanta aka kaita, innarmu tad'an dafa ruwa tazauna kusada ita tasaka k'aramin towel danta gasa mata goshin koza'a samu yarage tukullumar dayayi. Innaro ta 6ata fusaka zatama innarmu tijara. Baba k'arami yay saurin tareta da fad'in “haba inna, Dan ALLAH kibari tamiki, naga wad'anda suka miki abunma ko kallo baki ishesuba balle su nuna damuwarsu akai, wai shin minene laifin Ai'sha agarekine?”. Abbanmu da daddy suna zaune basuce uffanba sudai. Harara innaro tazuba ma baba k'arami kawai amma batace komaiba, itakuma innarmu ta saka towel aruwan tafara gasa mata. Tanama innarmu masifa dai har akad'an gasa mata, aikam saigashi wajen yad'an saki, baba k'arami yamik'a mata kofin tea d'in da maman fauziyya ta had'a. Kar6a tayi tana yatsine Baki, amma saigashi ta shanye tas, aka bata magani shima tasha ta kwanta. Basu bar gidanba saida tasamu barci, da innarmu tace zata kwana annan, sanin halin innaro Abba yace a'a tatashi suje gida tunda ga habiba d'iyar gwaggo safiyya dabata komaba. Badan innarmu tasoba tahak'ura, Dan aganinta innaro itama uwace agareta, kodan hallacin da mijinta yama iyayensu da darajar abbanmu, amma takula ran Abba a 6ace yake, kad'an yake jira a ta6ashi ya fashe, shiyyasa bataja zancen yay tsawoba ma. Koda suka shiga gida kowa sashensa yayi, innarmu harta kwanta saiga Abba yashigo d'akinta, abinda bayayi kenan, yakan shiga sashen matansa amma baya kwana, saidai mace tabishi nasa d'akin. Tana yunk'urin tashi zaune zata tambayesa lafiya? ya d'aga mata hannu kawai ya hawo gadon tareda janta a jikinsa suka kwanta. Bai bata damar maganaba Dan haka tayi shiru kawai kamar mai barci. Kamar yanda Abba bai isashen barciba hakama innarmu batayiba, Zarah ma kwana tayi kuka akan rashin shigowarsu Sa'eed. Hakama mamansu yaa Hameed da Gwaggon Haleematu basu rintsaba dasukaje gida. Kwana biyu da faruwar lamarin Abba yak'i cewa komai, yakuma k'i sauraren wayar da ake masa daga gidan matan nasa. Innaro harta fara samun sauk'i itama. Sa'eed kam dadynsa ya taso k'eyarsa washe gari gidanmu, an tattauna akan maganar, yafad'i dukkan abinda zarah ke masa, wani ta amsa laifinta wani kuma ta musa ba ita tayiba, sai wani cikin iyayenmu ya harareta take shiru. Nandai aka musu fad'a bayan itaba dad d'insa yace tafad'i abinda yake mata, saboda kar ahanata komawa saitace ita baya mata komai, wannan yasa aka musu fad'a da nasiha kawai akace yad'auki matarsa su tafi. Dad'i tamkar zai kar zarah kuwa, saitaji zuciyarta wasai, bata tareda damuwar komai, (kota manta uwarta bata gidansu itama a dalilinta kuma🤕?). Washe garin rana ta uku tunda safe saiga mamansu yaa Hameed tareda yayanta ya maidota, (dayake babanta ya tsufa sosai, komai nasu yanzu sai yayan nata, ko kud'inma dashi suke tak'ama yanzun, duk da mahaifinsu ya tara musu). Abba dai k'in saurarensa yayi, saida yaje ya kama k'afa da baba mai kanwa aminin marigayi mal. faruku, daddyne yamasu jagora zuwa gidan innaro dake kwance tana jiyyar goshi, damma kullum sai innarmu ta gasa mata safe da yamma, duk da masifar innaro da take sha batayin zuciyar ko nuna gazawa. Ansha fama akan Abba kafin ya sauraresu, danma akwai baba mai kanwa ne a zancen, amma ya tabbatar musu da Cewar shifa yagaji da iskancin dasuke masa a gida, tun zamanin k'uruciya har girma yafara kamasu sun k'asa canjawa, yabama kowaccensu damar k'arshe inhar suka kuma Tayar masa da rikici agida kowacce zata nemi hanyar gidansune, kuma tatafi kenan har abada, Dan bazai duba 'ya'yan dake tsakaninsuba ma. Tunda ga ranar mamansu yaa Hameed tadawo gidan, Gwaggon Haleematu kam bata dawoba, itada iyayenta sunce sai Abba yazo da Kansa koya turo anbasu hak'uri. Shikuma ya rantse saidai tayita zama inhar saiyaje bikonta. Gidanmu dai kam kwana biyu tsit kakeji, Dan baba k'arami da daddy ma summa matansu kashedi da sharad'in barin gidan gaduk wacce tasake fad'a da wata, wannan dalilin yasaka gidan yin lafiya, 'yan anguwa da makwafta sukaji kasiririt. Innaro ma ta warke abinta, saidai kam sun k'ulla da mamansu yaa Hameed, Dan yanzu ko 'ya'yanta basuda farinjini wajen innaro, ko Naziru autansu yamata Abu saita makeshi (ho innaronmu ta mutunci🤣😝). *************** Zazza6i dai yahana Munubiya sakat, yaa marwan yagaji da lalla6ata ga ciwo na cinta, yau dai yakwasheta zuwa asibiti tana kukan batason zuwa, amma yak'i saurarenta. Haka dai sukaje, bayan yankar kati dabin layi suka sami ganin doctor, gwajin farko doctor yabasu albishir d'in samun rabo na wata d'aya kacal (yaa marwan sharpshooter🤭, Munubiya dai inaga tuntu6e akayi🤫🤣). Wayyo zokuga murna wajen ogan miskilanci, babu kunya yakira Abbansa ya sanar masa, shima murna yaytayi ata cikin waya, kafin kace mi zance yabaje dangi, har innarmu labari yakai kunnenta. Harda kukan dad'i tayi, ikon ALLAH kenan, ita saida ta jera shekara 20 tana kuka da shan gori kafin ta samesu, amma ga Munubiya wata 1 da sati d'aya da aure har ALLAH ya kawo rabo. Saura munaya, k'ila itama d'indai an samu, tunda shekaran jiya dasukai waya take mata complain batajin dad'i. haka innarmu taita murnarta a d'aki ita kad'ai, babu Wanda ta sanarmawa tabarma cikinta, a cewarta idan yafita ko Munubiya tazo gidan sagani. Abin nema yasamu fa, yaa marwan tamkar zai maida Munubiya ciki, kokuma ya maido cikin nata jikinsa yarage mata wahalar laulayi haka yakeji, Dan tana d'an shan wahala gaskiya. ko girki yanzu bata iyayi balle gyaran gida. Hakanne yasaka mama rabi'a cewa yadawo da Munubiya wajenta harta samu sauk'i. Saiya fara fushi da rok'on tabarta Dan ALLAH shima zai kula da ita ai, abasu Ayusher ko feena takoma wajensu saita taimakawa Munubiya da aikin gidan. Mama Rabi'a tace a'a, Ayusher itake taimaka mata itama, feena kuwa ba cikakkiyar lafiyace da itaba, ba kowanne aiki take iya yiba ko agida (kunsan masu sikila dai🤦🏻‍♀, ubangiji ALLAH yabama dukkan masu irin wannan ciwo lafiya, ALLAH yasa yazamema rayuwarku kaffara kuda iyayenku da kullum suma hankulansu ba a kwance sukeba😢, duk mai wannan ciwon ina tsananin tausayinsa wlhy😭). Babu Wanda yaa marwan ya iya, dole ya tattaro kayansa shida Munubiya suka dawo gidan kawai, ai ko su Ayusher sunci dariya, danma fadeel bayanan, saidai a waya suka bashi labari. Munubiya tacigaba dasamu kulawa wajen mama Rabi'a, bata aikin komai saidai amata, sai idan boss nason rage nauyi ya janyeta d'akinsa da wayo ya kashe arna😉😎. Mama Rabi'a duk tana kula da su, amma saitayi kamar batasan bikin dasukeyiba, Dan taga idon yaa marwan a tsakar goshi yake😂😜. 🤥kai jama'a mu koma India.🛫⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀ .................................................... ______________________________ .................................................... Zafin jikinane yafara masa yawa, dan yafara shiga sosai jikinsa, cikin barci ya laluba danson jin minene mai zafi ya rungume haka? jin kamar mutum yasashi k'ok'arin bud'e idonsa dasukai masa nauyi saboda barci, dishi-dishi yafara ganin fuskar munaya, hardai yasamu nasarar bud'e idon gaba d'aya a kanta🤫.................✍🏼 _ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🤚🏻✋🏻_ [7/3, 9:54 AM] Aysha Galadima: *_Typing📲_* *_Haske writer's asso...._*💡 *_♦RAINA KAMA......♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻 ~Book 2~ 👉🏻4⃣ .............Cikeda tsantsar mamaki Galadima ya jujjuya wayar a hannunsa, kai kace itace zata fassara masa ma'anar sak'on, kuma komawa yay yana karanta sak'on a karo na biyu, a fili yace, *“SURIKI! SURIKI!.* to nikam wanenen sirikina?”. A take zuciyarsa tabashi amsa da *Baban matarka ta contract*. wata fad'uwar gabace ta samesa lokaci guda, wadda ALLAH ya tak'aita bata buga da bugun zuciyarsa ba, cikin tsitstsinkewar tunani dana zuciya yashiga bitar message d'in kamar mai haddar karatu, idan ya fahimci sak'onan dai akwai mummunan al'amari daya faru akan mahaifin munaya kenan? “ya salam”. ‘ya furta a fili, cikin dafe kansa yakuma fad'in “to adalilin mi wani abu zai samesa kuma yazam kamar yashafeni?”. gabansa yakuma fad'uwa, mutuwar Alhaji Abdussalam Abba mahaifinsu Samha ta dawo masa a rai, (mijin aunty Mimi). dafe kansa dake shirin sara masa yayi, to mizai kawo Abban munaya cikin case d'insa kuma? Sam bazai yuwuba ma, koma dai by mistake wani yaturo masa sak'on ne?. “mtoww! K'ilama hakane”. ‘yay maganar a fili yanajan guntun tsaki, tareda jefa wayar kan gado yacigaba da shirinsa. Shiri yake amma yakasa fidda abin a ransa, koyayi k'ok'arin ture tunanin gefe sai yakasa, dukda zuciyarsa tak'i yarda ta gaskata sak'on nasane. shiri ya kammala cikin Ash color d'in shadda gizna dakakkiya, tamasa k'yau ainun, komai nasa saiya saka Ash, Takalminsa helf cover, agogo da hula duk ash, ya kwashi phones nashi a hannu, ya fesa turare da gyara zaman hularsa sannan ya ciro wayarsa d'aya a aljihu, dan yakasa daurewa, number yaa marwan ya lalubo ya kirasa. A time d'in yaa marwan nata lallashin Munubiya tasha shayi sutafi asibitin amma tak'i, ta gardame akan ta k'oshi itadai su tafi kawai, mama Rabi'a dasu Ayusher sunyi lallashi amma tak'i yin shiru tasha, sai kuka take, hakan yasaka feena zuwa d'akin yaa marwan takirasa, shine yaketa lalla6ata amma tak'i kar6a, sai kawai ya had'e fuska ya koma mata ainahin marwan da bai d'aukar raini, cikin daka tsawa da hargagi yamik'a mata shayin, jiki na rawa takar6a tafara sha, tayi nisa dashan tafara amai kuma, mama Rabi'a tarik'eta, sukuma suka shiga mata sannu, yaa marwan na dafe da kansa cikin damuwa kiran Galadima ya shigo masa, kamar bazai d'aukaba saikuma yaciro wayar a aljihu ya diba. Mamakine ya kamashi dayaga sunan Galadima ta Nigeria, (ko sunzo k'asarne?), da hanzari ya d'auka tana gab da katsewa. Yanda Galadima yaji muryar yaa marwan yayinda yake amsa masa sallama sai hankalinsa ya tashi, ko gaisuwar kirki basuyiba Galadima ya hau masa tambaya akan Abba. Yaa marwan yace “gaskiyane ranka ya dad'e, jiya misalin 12pm Abba yayi accident, sunyi taho mu gama da wata thriller, yanzu hakama yana general hospital”. Zufar dake tsatstsafowa a fuskarsa yasa handkerchief ya share, muryarsa na rawa yace, “Marwan da gaske?”. Kula yaa marwan yayi Galadima kamar ba a hayyacinsa yakeba, shima muryarsa na rawa yace, “da gaskene ranka ya dad'e”. “hasbinallahu wani'imal'wakil” Galadima yafara maimaitawa akan la66ansa, ya sauke wayar a hankali zuciyarsa na wani irin suya, yama rasa wane kalar tunani yakamata ace yayi? Yaya zai fassara wannan lamarin? Kenan akwai wani Abu dabai saniba, kodai Abban munaya yanada wata masaniya akan lamarinsa, kokuma bai saniba yafad'a tarko, tabbas yakamata ma akan kansa yay wannan tunanin kodan abinda yayta faruwa tsakaninsa da Munaya, cikin k'araji yace “MUFTAHU!! kasan komai, dolenema kasan komai muftahu!!!, tabbas duk da kasancewarka d'an uwana, jinina, saina binneka da ranka a tsakkiyar masarautarnan inhar mahaifin matata ya rasa ransa wlhy, wannan ALWASHI NANE!!. ya k'are maganar yana buga table glass dake gabansa da masifar k'arfi, aiko ya tarwatse a wajen, kwalba ta yanka masa hannu. baibi takan ciwon dayaji ba yamik'e a harzuk'e ya d'auki wayar ya fice. A yanda yafito sai hankali hadimansa ya tashi, ga hannunsa yana d'igar da mini kad'an-kad'an, kuma suna gaisheshi yak'i amsama kowa gaisuwarsa, ko hannun daya saba d'aga musu inbaya buk'atar maganar yau basu samuba, da kansa yabud'e motar yashiga, hakan yasaka sarkin Mora Shiga da hanzari shima shida sauran dogaran dakan bisa in zai fita. Ko takan zuwa fada yay gaisuwa baibiba, suna fita daga masarautar kiran Nuren yashigo wayarsa. Yana d'agawa yace, “kajiramu a plaza”. ‘abinda yace kenan kawai ya Yanke wayar'. Nuren yabi wayar da kallo, inhar kunnensa yajiye masa dai-dai to ran Galadima a matsanancin 6ace yake, to mi aka masa? kokuma shida mutuniyar tasane mama Fulani? Nuren ya girgiza kai kawai yana murmushi, mama Fulani da Galadima sai addu'a kawai, dan tamkar suna ganin hanjin junane. Tafiyar mintuna 30 takawosu plaza, amma basu shigoba, dan haka Nuren yana hangosu yataso yafito. Matashin Saurayine shima, mai kama da Galadima sosai, dan wandama bai saniba saiya d'auka tagwayene, abubuwa kad'anne suka banbantasu, dan a shekaruma zasu iya zuwa d'aya, shima Nuren dagani yana cikin Hutu sosai, gashi d'an gaye ajin farko cikin nutsatstsun matasa masu ji da kai. Da sauri dogari d'aya yafito ya rissina yana gaisheshi, hannu ya d'aga masa cikin sarauta (hakan ya tabbatar min shima jinin sarautar ne) dogarin yabud'e masa inda Galadima yake ya shiga. Kallo d'aya yayma Galadima ya tabbatar akwai Matsala, hannu yabashi sukayi musabaha, cikin tsantsar kulawa yace, “brother mike faruwa ne?”. Galadima ya kalli Nuren da idanunsa da suka koma jajaye, cikin matsanancin d'acin zuciya yace, “bansan alak'ar data sashi cikin tawa ba”. Nuren yace, “waye?”. Kauda idonsa Galadima yayi daga kallon Nuren, ya maida ga window yana kallon mutane daketa harkokinsu, wani murmushin takaici yayi, sanan yafurta *“SIRIKI!”* Nuren yazaro idanunsa waje, a zabure yace, “yanzu haka yana ina?”. “general hospital ”. Nuren yay hanzarin fad'ama sarkin mota “muje general hospital na garinnan”. “to ranka ya dad'e”. ‘sarkin mota yafad'a a ladabce. Hannun Galadima dake d'igar jini har yanzu Nuren ya kamo, ya kalli Galadima da alamar tambayar miya damesa? amma shi galadiman sai yamak'i kallonsa, Nuren ya girgiza kai kawai Dan yasan hakan dayayi bazai fad'aba ne, handkerchief d'insa ya Ciro ya d'aure hannun Na Galadima Dan jinin a samu ya tsaya daga zubar, dukya d'an 6ata seat d'in mortar kad'an, da yake a nan ya ajiye hannun daga gefe. ran Nuren a 6ace yace “brother dolene muyi bincike akan Surukinka, dan duk ta yanda zamu fassara a yanzu, zukatanmu bazasu d'aukaba. zamu iya zargin akwaima hannunsa a ciki, zamu iya zargin sunnemi wani Abu daga garesa yak'i basu had'in kai, zamu iya zargin abubuwa da dama”. Iska Galadima ya furzar daga bakinsa, yasaka hannu ya tura hularsa baya, kansa ya jingina da kujerar tareda lumshe idanu. zuciyarsa tana tunani yaushene zai kawo k'arshen mak'iyan mahaifinsa? Sai yaushene za'ayi walk'iya yagansu? yana buk'atar sanin dalilinsu Na za6ar maida masa mahaifi haka, miyayi musu?. Wannan tambayoyin yakema kansa kullu yaumin ta kowacce rana. Hannunsa Nuren yakamo yad'an matsa, Galadima yabud'e idonsa dasuka fara komawa kalar jaa. “brother a wannan karon bana buk'atar 6acin ranka, dan duk sanda ranka ya6aci baka iya Controlling d'in fushinka, fushinka Na saka aikinmu tafiyar wahainiya, lokaci yayi dazaka saba da irin wad'annan abubuwan fa, karinga saka nutsuwa a zuciyarka aduk lokacin da irin haka tafaru, kamarfa yanda takawa (papi) yake fad'a mana ne a kullum, sufa sunayin wad'annan abubuwanne dan kawai su fusata ka, a haukansu zasu iya samun nasara a kankan saboda ciwon da ALLAH ya jarabceka dashi, waynote kaikuma ka karya wannan kwarin guywar tasu OK?”. Ajiyar zuciya Galadima ya sauke, shima ya dafa hannun Nuren d'in yana lumshe idanu, a hankali yace “Okey it's better”. Daga nan motar ta d'auki shiru, ahaka suka isa asibitin. Zuwa lokacin jama'ar gidanmu sun kuma cika asibitin, harsu Munubiya duk sunzo suma. Tunda motocin Galadima uku suka shigo asibitin kallo ya koma Kansu, kowa son ganin mai fitowa yakeyi. Dogaraine suka fara fitowa, kafin abud'ema su Galadima. 'Yan gidanmu sun fahimci daga masarautane, amma babu Wanda yay tunanin ganin Galadima d'in. Tunda yafito kwarjininsa da cikar haibarsa ta kasancewarsa jinin sarauta ta cika idanun jama'ar wajen, dogarensa sun tsare ko ina babu mai damar ra6arsa, Nuren na gefen hannun damarsa. Wayyo, nanfa ido yaymasa caa, baya son kallo ko kad'an, amma yaya zaiyi, tunda jama'a sunga abin kallon.🤦🏻‍♀ Tunkan ya k'araso su yaa Hameed suka mik'e suka nufoshi. Munubiya kam bayansa kawai take lek'awa, azatonta harda 'Yar uwarta. amma ganin babu alamar mace ma acikinsu sai jikinta yay sanyi. Hannu Galadima ya d'agama dogaransa alamar su dakata, baya suka ja, yayinda shikuma yamik'ama yaa Shafi'u daya fara k'arasowa hannu, sun gaisa da yayuna cikin girmama juna, kafin sumasa jagora zuwa ciki inda Abba yake. Dayake su Munubiya suna daga gefene, shiyyasa basu gaisa da Galadima ba, sai k'amshin turarensa daya cika hancinansu. Dukda halin da ake ciki, saida 'yan gidanmu sukaji Hassada, kowa jitake inama mijin 'yartane🤕🥴. Humm doctor daya hana kowa ganin Abba saigashi jikinsa Na rawa ya tarbi Galadima, daddy da baba k'arami sunje gida suyo wanka, bayan dawowar su yaa Naseer sai sukuma suka tafi. Doctor yama Galadima jagora har d'akin da Abba yake kwance. “Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un” kawa Galadima ke iya fad'a a la66ansa, maganar gaskiya jikin Abba babu k'yawun gani, yaa Shafi'u ma mai ragguwar zuciya kasa daurewa yayi yafice da sauri yana hawaye, yaa Hameed kam runshe ido yayi zuciyarsa Na suya kamar zata fad'o k'asa. Galadima ya dafe bango tareda rik'e kansa dayaji ya sara masa, halin da Abba yake ciki exactly dana Alhaji Abdus'salam Abba. Da sauri Nuren yaruk'o hannunsa, a hankali yake fad'in “Control yourself please”. Doctor yajawo kujera biyu yabama Galadima da Nuren dansu zauna. Ina kasa zaman sukayi, dole suka fito. Galadima yabuk'aci ganin doctor d'in. 'Yan gidanmu kuwa fitowar yaa Shafi'u yana share hawaye yasaka zukatansu kuma tashi, caa sukayo kansa da tambayar lafiya. Kasa magana yayi, ahaka su Dady suka samesu, sukansu jiki a sanyaye suka k'araso wajen, kardai ace d'an uwansu yatafi ya barsune. muryoyinsu har rawa sukeyi wajen tambayar lafiya?. Sai alokacin yaa shafi'u yasamu bakin maganar cemusu bafa rasuwa yayiba, jikinnasane sai babu dad'in kallo. Baba k'arami yace, “sun bari kun gansane?”. “Eh baba, Galadima ne mijin Munaya yazo”. Dady da baba k'arami ciki suka shiga, sukabar 'yan gidanmu dake kuka abin gwanin tausayi. Doctor bai 6oyema Galadima komaiba, yafad'a masa gaskiya jikin Abban yayi tsanani, dan yaji raunuka Na tashin hankali, ga karaya a jikinsa takai hud'u. Galadima ya cije lips d'insa, kafin yace, “ina police d'in dasuka kawoshi nan?”. “ai wlhy yalla6ai basu kwana ba, tun jiya around 11pm suka tafi abinsu, kuma har yau basu dawoba”. Amatuk'ar fusace Galadima yace “Why!!?”. Doctor yagama rikicewa, jiki Na rawa yace “ban saniba wlhy ranka ya dad'e”. Harara Galadima ya watsa masa, yace “saboda kaima bakasan aikinka ba? wai......”. Nuren yay sarin fad'i “Cool down Sameer!”. “haba Nuren, kajifa wani zancen banza, saboda jami'an tsaron k'asarnan basu san aikinsuba, su kawo mutum cikin irin wannan mawuyacin halin amma bazasu dakata suji wani issues akansaba su tafi, bazama su iya zama zuwa washe gariba ko za'a iya buk'atarsu”. “sorry ranka ya dad'e”. ‘cewar doctor a tsorace’. Dady da baba k'arami dake tsaye abakin k'ofa tun d'azun suka k'arasa shigowa, sune suka kwantarma Galadima hankali da nuna masa yayi hak'uri. A girmame ya risina ya gaidasu da tambayar mai jiki. Suka amsa masa da Alhmdllh. Cikin mintuna 30 Galadima yasa aka canjama Abba d'aki Na musamman, sannan aka kawo police 5 suka zagaye d'akin. Hakan yama familyna dad'i sosai, dansu baba k'arami tun a daren jiya sukaga wasu sunata zagaye-zagaye a k'ofar d'akin da Abban ke kwance, ba k'aramin tsoro abin yabasuba, amma basuda mai taimakonsu, sai addu'a dasukai tayi da Neman tsarin ALLAH akan mutanen. Amma gashi yanzu ALLAH ya kawo musu Galadima. Galadima yasaka doctor yayi shirye-shirye daduk tattara bayanan Abba. Da k'yar Nuren ya lalla6a Galadima ya amince aka masa treatment d'in hannunsa shima, sai da Dady yasa baki ma, amma da ya dage akan abarsa shifa baya masa ciwo, saigashi hardasu d'inki akayi masa a wajen. Daga nan suka fito daga office d'in doctor d'in, sunason zuwa inda Accident d'in yafarune. Harsun kusa fita Galadima yatuna, ya buk'aci abashi wayar Abba idan babu damuwa. Baba k'arami yace, “ai bama azo da wayarsa asibitin ba gaskiya, maybe ma tana can inda abun yafarune”. Galadima ya jinjina kai kawai suka tafi. Su innarmu sunji dad'in abinda Galadima yayi, innaro sai kwararo masa addu'oi takeyi tana kuka. ____(((★)))____ Zuwa yanzu hankalina yakai k'ololuwar tashi, saboda mafarkin Abba na danayi da daddare, abin mamaki a barcin safema dana koma hakance ta faru, nakuma mafarkin Abba yana cikin mawuyacin hali, a firgice na farka jikina sharkaf da zufa, wayata na lalubo nashiga neman wayar Abbana, amma Switch up, nakira Innarmu network yahanata wucewa, hakama Munubiya, hankalina fa ya tashi, haka naitabin Number's d'in 'yan gidanmu ina kira. Amma daga Wanda zaik'i amsamin sai wadda zan kira switch up, saikuma marasa tafiya. kuka nazauna rerawa babu mai lallashina. A wannan halin Samha tashigo ta sameni, itama hankalinta tashi yayi, takira Momma a waya ta sanar mata gani inata kuka. Babu shiri Momma tabaro jakadiya da aunty Mimi a hospital tanufo gida, dan itama a cikin damuwa take, na rashinjin Galadima. dan bai sanar da ita ina zaijeba, itakuma bata kawo yana Nigeria bane, tunda bai ta6a tafiya bai sanar mataba, tazata tafiyar kota shafi company d'insu ne. Ta iso ta iske Samha nata lallashina, jikinta a sanyaye tazo bakin gadon ta zauna, hannuna ta kamo ta jawoni jikinta, batayi maganaba tashiga shafa kaina da bubbuga bayana, munkai kusan 10minutes a haka, harna bar kukan sai ajiyar zuciya kawai. A tausashe tace, “kiyi hak'uri kinji Munaya, ni kaina hankalina a tashe yake da rashin kiran, dan baita6a hakaba”. (ALLAH Sarki momma ita ta zata saboda rashin kiran Galadima ne, shima rashin jinsa na damuna kam, amma yanzu na Abba ya danne komai). Samha tace, “Momma amma an gwada Number sa ta Nigeria?”. “Samha banyi tunanin can yajeba, amma bara na gwada na gani”. Wayarta ta d'auka ta kira number Galadima ta Nigeria, a mamakinta kuwa saita shiga, cikeda al'ajabi taciro wayar a kunnenta takuma kallon number d'in, tabbas itace dai da gaske. Harta katse bai d'aukaba, takuma kira a karo na biyu. Lokacin Galadima suna mota zasuje inda Accident d'in Abba yafaru. ganin momma saida gabansa ya fad'i, harta tsinke yakasa d'auka, sai da aka kuma kira Nuren ya d'aga yasaka masa a kunne. muryarsa a sanyaye yay sallama, daga can Momma tace, “lallai Muh'd, yanzu nan dan zakaje Nigeria shine ka 6oyemin? kabi ka tada mana hankali muda matarka, maimakon ma ka sauka kakiramu hankalinmu ya kwanta”. Runtse idanunsa yayi, muryarsa a sark'e yace, “ki gafarceni Momma, wlhy banason ki hanani zuwanne, nazo kuma na iske wani tashin hankali, shiyyasa ban kirakuba”. Mik'ewa Momma tayi tafice daga d'akin, ni da Samha muka bita da kallo, tace “innalillahi.. miya farune Muh'd? ”. Zuciyarsa na suya ya zayyane mata komai daya faru, dukta rikice, “kodai wani yafad'ama Munaya Muh'd?”. “banajin hakan gaskiya Momma, dan mutanen gidansu basuda Nutsuwar ma sanar da ita, amma miya faru?”. “hankalinta gaskiya a tashe yake, dan ina asibiti Samha takirani tana sanarmin Munaya nata kuka, babu shiri nabaro asibitin nazo gida, da k'yar na lallasheta, ni na zatama ko rashin kiran dabaka yi baneba”. “to maybe rashin kiran nawane gaskiya. Amma batasan komaiba, Momma kuma banason tasani harsai yafara samun sauk'i kin...........” Da sauri Momma ta katseshi “bazai yuwuba Muh'd, dolene anema mata ticket ta taho ko itada Sauban ne, mahaifi yawuce gaban wasa, ko kai baka sanar da itaba dolene wani a cikin 'yan uwanta ya sanar mata, bakuma zata ta6a samun kwanciyar hankaliba, mukuma saita mana wani kallo daban na 6oye matan da mukayi”. “to shikenan Momma, Sauban yaje ya bincika ko'akwai jirgin dazaizo Nigeria, saiya nema musu tickets, yanzu muna kan hanyar zuwa inda Accident d'in yafaru, idan na koma gida zan kiraki”. “to shikenan saina jika”. Momma ta kwantarmin da hankali sosai, sannan takoma asibiti da alk'awarin indai gida nakeso zatasa Sauban ya nema min ticket natafi, amma bata fito ta nunamin ainahin abinda ya faru zanje gidanba. Dukda inason tafiya gida sainaji kamar akwai abinda ake 6oyemin, saboda wannan tafiya ta gaggawa, sai dai ban tambaya ba nabarma zuciyata kawai. Sauban kuma yashiga mana shirin tafiya. ______________________________ Tunda Galadima ya ajiye wayar babu Wanda yayi magana a cikinsu, daga Nuren har Galadima kowa damuwar ganin halin da Abba ke ciki tanacin zuciyarsa. Su Dady ma suna mota kowa shiru, tausayin d'an uwansu da addu'ar samun lafiyarsa kawai kowa keyi. Police d'in dasuka musu jagora inda Accident d'in yafaru ne suka samu hanya da k'yar, dan motar Abba da thriller d'in data hau kan motar Abban sun tsare rabin hanyar, hakanne ya haddasa go slow sosai, Galadima kam yakasa koda motsi, saima tsirama motar idanu da yayi tacikin glass d'in motar zuciyarsa Na matuk'ar suya. Saida Nuren ya taimaka masa sannan yafito. glasses d'insa yad'auka yasaka, Wanda ya 6oye jajayen idanunsa. thriller d'in data hau kan motar Abbanmu Na gefe itama a kife take, duk Wanda yaga motar ta abbanmu zaiyi zaton mai motar bazai rayuba, saboda fita hayyacinta da tayi. Jingina da mota kawai Galadima yayi ya hard'e hannayensa a k'irji ya zuba musu idanu. Nuren kam yanacan jikin motar sosai tare da police d'in dasu Dady ana laluben wayar Abba acikin motar. Harsun fidda rai da samunta ma, da k'yar aka sami wayar, amma tayi rutsu-rutsu, ga jini dukya bushe a jikinta, cikin Leda aka Sanya, Nuren ya kar6a yabama sarkin mota. Sund'an k'ara bincikawa kozasu samu wasu muhimman abubuwa, takardune kawai sai abinda ba'a rasaba. Nuren ya kalli police d'in yana fad'in “amma kamarma wasu sun d'ebi wasu abubuwa a motarnan?”. “zata iya yuwuwa ranka ya dad'e, Kasan mutane da anyi accident maimakon taimako dasuke bayarwa sai wasu su 6ige da sace-sace kuma”. Nuren ya jinjina kai kawai, danshi ba mutane yake zargiba. Yafi zargin wad'anda sukaso kashe abbanne kawai. Dady da baba k'armi da suke gefe kam harda kwallan su, Dan kallon motarma kawai ya ishi bawa shiga tsantsar tashin hankali. Sund'an jima a wajen kafin su tafi, Galadima dai yayi d'if, ko magana yakasayi. Su baba k'arami asibiti suka wuce, sukuma birnin gayu plaza. Tunda suka shigo ma'aikatan wajen suka zube suna kwasar gaisuwa, Nuren ne kawai ke iya amsa musu, galadima kam hannu kawai yake d'agawa. Kai tsaye Office d'insa Na plaza d'in ya shiga, saima yazo k'asar sau nawa bai shiga Office d'inba kwata-kwata. Ya zauna tareda zame hular Kansa da glasses d'in, sannan ya jingina kansa da kujera yana mai lumshe idanu. Nuren ma zama yayi kawai ya zuba masa ido, kusan minti 2 da zamansu Manager d'in plaza yashigo, gaisuwa yakumayi ga uban gidan nasa cikin girmamawa, Galadima ya d'aga masa hannu batare da ya bud'e idonsa ba. hakan yakuma tabbatarma manager babu lafiya kenan. Kirane yashigo a wayar Galadima, yad'an bud'e ido kad'an ya kalli phone d'in, Harun ne, tun d'azun yake faman kiransa amma bai d'agaba, yasan labarin zuwansa k'asar yazo musune. Yanzunma bai d'aga ba, ya share, saima kwanciya daya kuma gyarawa a jikin kujerar, da hannu Nuren yayma Manager nuni da yaje. Manager ya gyad'a kai sannan yafice yana mamakin miya ta6a yalla6ai hakane?. Idon Galadima a rufe yace, “Nuren wane layine akan wayarnan?”. Wayar Abba da sarkin mota ya goge fes, duk babu jinin yanzu Nuren ya d'auka ya bud'e, Mtn ne da glo aciki. ya kalli Galadima sannan yace, “glo and mtn ne”. Galadima ya bud'e idanunsa akan wayar shima, ya d'an yamutsa fuska sannan yace, “dolene muje office d'insu kenan, dan zanso sanin dawa yake mu'amulla, k'ilama zamu iya samun wani abidance”. “o right, hakan yayi, amma waynote mu fara zuwa kaci abinci kasha maganinka, dan bazai yuwu muyita yawo bakaci komaiba, ni gamma ni nayi breakfast a hotel kafin na fito, kaiko nasan bakaci komaiba, gashi har time d'in lunch yayi”. “karka damu, banajin wani yunwa ni kam, muje dai muyi salla muje”.. “ina, bazai yuwuba, bara nasa amana oder a wancan restaurant d'in naga suma sun iya abinci”. Galadima bai sake cewa komaiba, Nuren ya d'auki waya yakira cikin ma'aikatan plaza d'in, saiga Saleem, dan Nuren yasan Galadima ya yarda da Saleem sosai, bayan ya gaishesu Nuren yabashi kud'in. Amma sai Saleem yak'i amsa, ya fita kawai. Kusan 30minutes saigashi da yaran restaurant d'in su uku, kowanne d'auke da babban tire, shiya dunga kar6a yana shigarwa office d'in. Da k'yar Galadima yad'anci abincin, danma tuwone, yanason tuwo sosai, maganin Nuren ya 6alla yabashi yasha, sannan suka nufi massallaci dan gabatar da sallar azhur. '*****'*********'*******'*******' Sauban ya sama musu tickets d'in tahowa Nigeria, Momma bata bari Munaya ta d'ebo wasu kayaba, tunda tanada kayanta anan, d'an abinda ba'a rasaba kawai ta d'akko, sunje asibiti sukaima Abie sallama sannan khumar yakawosu airport shida Samha da Khaleel dasuka musu rakkiya. Sunyi zama nakusan 1hour sannan jirginsu yasamu tasowa......................✍🏼 *_ALLAH ya gafartama mahaifanmu😭🤚🏻✋🏻_* [7/3, 9:54 AM] Aysha Galadima: *_Typing📲_* *_Haske writer's asso...._*💡 *_♦RAINA KAMA......♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻 ~Book 2~ 👉🏻3⃣ ............Shiru kawai yayi yana kallon fuskarta ta cikin d'an hasken mai kalar jaa, sai fuskar tabada wata kala data k'ara mata k'yau. yaune ranar farko dazaice yamata kallon k'urilla irin haka, yadad'e yana kallonta kafin ya janye idanunsa dake cike da barci. hannu ya mik'a ya kunna ainahin fitilar, haske ya gauraye d'akin, cikin dabara yafara yunk'urin janye jikinsa, amma tak'i yarda, saima farkawa datayi, tabud'e idanunta dasukai nauyin barci a hankali, kad'an take kallon face nashi, ta lumshe idon tasake bud'ewa. “wannan d'aurin goronfa?”. ‘galadima yay maganar a hankali cikin muryar barci, yanabin hannun munaya da ta zagaye cikinsa da kallo’. Sosai Munaya ta waro idonta yanzun, ganinta a jikinsa kwance, gashi tawani dabaibayesa saita sakeshi da sauri tana matsawa baya da waige-waigen inda take kwance. gabanta ne ya fad'i, dan ita harga ALLAH tama mance ta hau masa gado, tayi saurin rik'e kanta dake sara mata tana tashi zaune. Shima saiya tashi yana binta da kallo, a mugun sanyin murya yace “bakida lafiya ne?”. Hawaye suka wanke mata fuska, muryarta na rawa tace “kaina kamar zai tsage”. Saida yaja 1minute kafin yad'an matso kad'an, yatsunsa biyu ya d'ora gefen wuyanta, saiyaji jikin zau da zafi, ya janye ya d'aura zuwa gefen kanta, jijiyar wajen sai motsi takeyi d'ass d'ass d'ass d'ass, alamaun kan namata ciwo sosai. hannun ya janye tareda sakkowa daga gadon gaba d'aya. Ya zagayo 6ari da take, hannu yasa ya zame nata hannun data tallafe kanta dashi, ta tad'ago idanunta dake cike da barci, sunyi d'anja sun k'ara girma, idonsa a kanta, Dan haka ta janye nata ta maida k'asa tana cigaba da hawayenta. Kad'an yad'an furzo iskar bakinsa, kafin a hankali yace “mike miki ciwo bayan kan?”. Saida takuma matso wasu hawayen sannan tace, “duk jikina”. “kin fad'ine?”. Kanta kawai ta iya girgiza masa, ya cigaba da tsura mata idanu batare da yace komaiba, ganin tana hawaye duk sai yaji babu dad'i, koba komai itad'in Friend nashice ai, kamar yanda yafad'a tun farko. yad'an sauke ajiyar zuciya mai sauti kafin ya mik'e, bayi yashiga, mintuna kad'an yafito, tana a inda ya barta dafe da kanta, yace “taso kid'an watsa ruwa, ko jikin zai huce”. d'agowa tayi ta kallesa, sai taga ya tsatstsareta da mayun idanun nan nasa, tayi saurin janye nata, amma takasa tashi. matsowa yayi kusada ita, ya mik'a mata hannunsa, alamar takama ta tashi, ta d'ago ta kallesa ya d'aga mata kansa yana mai lumshe idanunsa alamun tabbatarwa. Hannunta ta saka a cikin nasa, ya had'e waje guda sannan ya taimaka mata ta tashi tsaye, kallo d'aya yamata ya kauda kai, dukda kayan nata masu kaurine saida yaji wani Abu daban, dansu fidda surarta sosai. Har wajen wankan yakaita, sannan yafito batare da ya ce uffanba. da kallo tabi bayansa, a ranta tana mamakin sauk'in kai irin nasa, ada kallon mutum mai girman kai take masa, amma tunda suka fara rayuwa a tare saita fara fahimtar ba haka baneba, kawai dai shi mutumne dabai cika hayaniya da surutu ba, shiyyasa inbaka gama saninsaba saika dunga masa kallon mai girman kai. Koda ya fito saiya had'a mata tea, shi dama baya rabo dasu a d'akinsa, magani ya d'akko shima ya ajiye, yakoma bakin gadon ya zauna yana tsumayen fitowarta. Kusan mituna 10 tagama watsama jikinta ruwan, lallai naji dad'i sosai, saidai kuma bazan iya maida kayan dana cireba, inajin kunyarsa, kuma jinsu nake sun d'auki zafi, towel naja Na d'aura, saidai bashida girma, bazan iya fita a haka dashiba Galadima yana d'akin, kad'an nabud'e k'ofar Na lek'oda kaina, yad'an juyama k'ofar bathroom d'in baya kad'an, a hankali cikin muryata mai nuna alamun banida lafiya nace “please yalla6ai ka taimakeni da hijjab”. Waiwayowa yayi ya kalleni, alamun baijiba sosai, Na turo baki kad'an sannan nace “please yalla6ai hijjab”. Baice komaiba ya mik'e, inda nake ajiye hijjab d'in yaje ya d'ako, yazo inda nake ya d'oramin akan hannuna dana mik'o, kallon ido cikin ido mukaima juna, kowa ya janye cikeda basarwa. Bayan nasaka hijjab d'in nafito kamar wata muna fuka, sai k'asa nakeyi da idanu nakasa kallonsa, shima idonsa a lumshe ya jingina da fuskar gadon, wucewa nayi wajen akwatina Na d'akko wasu kayan barcin, bayi nakoma Na saka, saina yafo k'aramin Vail Na cire hijjab d'in. Yabud'e idanu kad'an a kaina, batare da yayi magana ba ya nunamin mug d'in daya had'a tea a ciki. nad'an yatsine fuska da marairaice murya tamkar xanyi kuka, “ALLAH yalla6ai banajin yunwa”. Shiru yay kamar bazai tankaba, saida yaja kusan 2minutes sannan yatashi zaune sosai, batare da yayi magana ba ya d'auki mug d'in da drug's d'in ya taso inda nake zaune a kan sofa, saman k'aramin table d'in gaban kujerar ya zauna yana fuskantata, d'an gaf d'in daya bari tsakanina dashi bai wuce tafin hannuba, Dan har inajin saukar numfashinsa, baya nad'anja kad'an Na jingina da jikin kujerar, amma hakan bai hana kusanci sosai tsakanina da shiba. babu magana babu komai naji dirar cup a bakina, d'ago ido nayi tamkar zan fasa kuka, danni wlhy banajin shan shayinan, yamin hararar data saka 'yan cikina harmutsawa, babu shiri nabud'e baki na kar6a, ya had'e girar sama da k'asa, baibar ko k'aramar k'ofar dazan kawo masa wargiba, haka naita kar6a ina hawaye, saida yaga Na shanye tas sannan ya barni yana hararata, nidai yau babu k'arfin mayarwa, yabani maganin, shikam babu musu Na kar6a nasha. ganin yanda naketa hawaye saiya zubamin ido kawai yana kallon ikon ALLAH, nikam banida niyyar daina kukan nawa, kuma nima bansan dalilin kukanba, kawai dai jinake hawayen Na tahowa. Ya zuba tagumi abunsa yana kallona kamar yasamu television. kallon dayake min saiya k'ara tunzurani, nafara kuka mai sauti harda shashsheka. Tagumin yacire yana wani k'asaitaccen murmushi, ya mik'e tseye yakoma kan gadon, filolin dasuke k'asa ya d'auka ya jera a tsakkiyar gadon kamar d'azun. nidai duk ina kallonsa, saida ya lullu6ama k'afafunsa bargo zuwa cikinsa sannan yace, “taso ki kwanta sarkin arhan hawaye”. Harara Na zuba masa batare da Na shiryaba, sai kawai ya ta6e bakinsa yay kwanciyarsa ya barni, tareda kashe fitilar ya maida ta barci. Kusan mintuna 4 Na zame Na kwanta a kujerar, amma sainaji duk babu dad'i, saboda maganin bai fara tasirin da jikina zai bar ciwonba, tashi nayi nakuma zama, kusan 5munutes sannan natashi sad'af-sad'af tamkar munafuka na haye gadon. Ni duk tunanina yayi barci. Ashe duk abinda nake yanajina da kallona. murmushi yayi kawai yana lumshe idonsa, a ransa yana jinjina irin rashin wayona. Ajiyar zuciya Na sauke a hankali, sannan naja bargon dayake babbane Na lullu6a, mintuna kad'an nafara zufa, alamar zazza6in ya sauka. Bargon na janye don insha isaka, bansan sanda barci ya saceni ba. Juyowa yayi ya kalleni, yaga ina sauke numfashi a hankali alamar nasamu barci, k'aramar ajiyar zuciya ya sauke kafin yasake addu'a shima ya gyara kwanciyar sa. ★★★★★★★ Yau gidanmu sun tashi cikin tashin hankali, Abbah yay Accident yayin dawowa gida daga wajen aikinsa, innarmu Na kwance ciwon kai dukya isheta, tunda ta tashi da safe dashi ta tashi, gasu Aryaan sun isheta da ihun fad'ansu, sai mugun wasa sukeyi suna guje-guje a falon, amma takasa d'aga kai ta tsawatar musu. Zuciyarta cike da kewar su Munubiya, inda suna nan da yanzu suke bata taimako, koyaya tace batajin dad'i zasu rud'e, amma gashi yau ko wanke-wanke tama rasa mai matashi, sai Zainab maman fauziyya tasaka tayi mata, amma 6angarenta ko shara bai samuba yau, kuma tun d'azun tafara jin mamansu yaa hameed tana k'ananun magana akan tak'i fitowa ta aza musu girki, maimakon sunga shiru su lek'o suji ko lafiya? A'a su babu ruwansu, kawai a dafa abasu suci da 'ya'yansu... Wayarta dake ring ta katse mata tunani, ta kalli su Aiyaan dake danbe Aryaan Na kuka saboda dukansa da Aiyaan yayi a baki. “wani cikinku ya d'akkomin wayata saman freight”. Cikin kuka Aryaan yace “Innarmu kingafa ya dokarmin baki”. “kukuka Sani, nidai nace wani ya d'akkon waya acikinku, idan kuma kuka bari Na tashi sai jikinku yagaya muku”. Aryaan ya d'akko mata wayar ya kawo mata, lokacin harta tsinke, ganin Abbanmu ne yasata bin kiran, bugu biyu aka d'aga, ko gaisuwa bai bari sunyiba, yace mai wayarne yayi Accident, yanzu haka suna general hospital. “innalillahi wa'inna'illaihirraji'un” innarmu tafad'a tana mik'ewa zumbur, ga wata zufa Na karyo mata, batasan tayo waje tana kwalama matan gidan kiraba. Kowacce tafito jiki Na 6ari, azatonsu wata acikinmu aka sako, musamman ma ni dasuke kiran aurena auren d'ori d'afini. tana hawaye ta sanar musu da abinda yafaru. Nanfa gidan ya rikice, yara suka garzaya suka sanarma innaro. Ko takalmi babu haka tanufo gidanmu tana shar6ar majinar kuka da kiran tashiga uku, Awwalu zai mutu ya barta. wannan kwakwazon natane ya ankarar da jama'ar anguwarmu. A rikice baba k'arami da Dady suka nufi asibitin, Dan matan gidanmu sun kira suma sun sanar musu abinda ke faruwa. Kafin wani lokaci jama'ar gidanmu sun gama cika asibitin, sai koke-koke sukeyi suna son ganin Abba, amma an hanasu, Dan bak'aramin buguwa yayiba. ______________________________ Alhmdllh natashi jikina da sauk'i, Dan kuwa babu zazza6in da ciwon jikin, hakama ciwon kan babu, bai tadani ba saida yadawo massalaci, lokacin har gari yafara haske ma. Na idar da salla ina zaune ina addu'a yafito daga bathroom, da alama wanka yayo, Dan sanye yake da bathrobe sky blue, yana rik'e da k'aramin towel a hannu yana goge ruwan fuskarsa. Kallo d'aya namasa Na d'auke kaina, shikoma bai kalleni ba ya wuce gaban mirror ya zauna, saida yafara shafa mai sannan Na tsinkayo muryarsa yana fad'in “ya jikin naki?”. Yanda yay maganar a cinkushe yasakani d'agowa Na kallesa, ganin hidimarsa kawai yakeyi saina d'auke kaina, nace “da sauk'i”. Bai sake magana ba, harya kammala yabar gaban mirror d'in, wajen wardrobe yakoma, nidai kaina Na k'asa bansan hidimar dayakeba. Koda ya d'auki kayan saiya koma bayi ya saka tamkar yanda ya saba, ya fito ya iskeni ina gyaran gadon, ta gefen ido Na kallesa, yayi k'yau cikin wani bak'in lallausan yadi, Wanda akaima ado da jan style, nakula yanason kayan al'adarsa, dukda baitashi ya girma cikin k'abilar tasaba, sock's ya d'akko da bak'ak'en takalma sau ciki ya zauna saman sofa, yana sakawa yana magana, “uhm Zanyi wata 'yar tafiya Na kwana 2 kacal, mikike da buk'ata?”. Tsayawa nayi daga gyaran gadon danake, Na d'ago ina kallonsa kawai, jin nayi shiru kuma yanajin alamun ana kallonsa ya d'ago shima. Ido muka had'a saina janye nawa. “kallon fa?”. ‘yafad'a yana k'ok'arin saka d'ayan takalmin’. Cikin la6e baki nace “yoni yalla6ai mizan kalla anan?”. Banza yamin, saida yagama saka takalminsa sannan yamik'e tsaye yana fad'in “hakanefa, Ashe babu abin kallo anan”. Nima shiru namasa ban tankaba, ya saka laptop d'insa dawasu 'yan abubuwa a k'aramar briefcase d'insa, ya zuge zip d'in yana fad'in “ki shirya muje kiga likita kafin Na wuce”. Da sauri nace “a'a kaje abinka, Indai nice Na warke”. Idanu ya tsuramin alamun tuhuma, nikuma nak'i kallonsa, ya girgiza kansa kawai sannan ya ajiye min kud'i akan gadon, “ni Na tafi, a yafi juna”. 'Dagowa nayi ina kallonsa da mamakin kalmarsa ta k'arshe, bansan sanda bakina ya su6uce nace “ALLAH ya tsare hanya, ya dawo dakai la fi ya”. ‘na k'are maganar da d'aid'aya’. Cak ya tsaya abakin k'ofar, saboda yanda addu'ar tawa tazo masa a bazata, dan bai tunanin hakan daga gareniba, yajuyo a hankali tamkar maison gaskata abinda yaji, kallona yayi muka had'a ido, amamakina saiya sakarmin wani tsadajjen murmushi, irin Wanda zan iya rantsuwa ban ta6a gani daga garesaba. Baice komaiba yajuya yafice da sauri. Yabar zuciyata da luguden dabansan dalilinsa ba. Wata ajiyar zuciya Na sauke, tare da zama jagwaf a bakin gadon na dafe kaina da mamakin murmushin da Galadima yamin. Bai dad'eba sosai a hospital yamusu sallama yafito, dama tun a daren jiya ya sanar musu zaiyi tafiya, ga jirgi kuma ya kusa tashi. yafito sunata binsa da addu'oin dawowa lafiya, yayinda shikuma yake amsawa cikeda murmushi. Saida yafara xuwa sukayi magana da doctors d'in dake kula da Abie, yaji babu wata Matsala sannan yafito. Dama Khumar ne ya kawoshi, Dan haka yanzu ma shine yatafi kaisa airport d'in. Zaman da baifi 30minutes ba jirginsu yataso zuwa 9ja. Zaune yake kusa da window, yayinda wata matashiyar budurwa ke gefensa, tunda tazo da nufin zama yawani kuma had'e fuska, a d'age ma ya amsa mata sallamar data masa, yasaka belt tareda bud'e Newspaper yahau karatu. Budurwar sai satar kallonsa takeyi, tanason masa magana amma bataga fuska ba. Sai da akazo tambayar misuke buk'ata?, yace Coffee. Itama da sauri tace Coffee d'in. juyowa yayi ya kalleta, ta sakar masa wani tsadajjen murmushi. Janye idonsa yayi yanajan tsaki a zuciyarsa. duk yanda taso yamata magana ko sau d'ayane Galadima yak'i yayi, ya had'e gabas da yamma abinsa. Haka kawai sai tunanin tahowarsu da Munaya ya fad'o masa a rai, yatuna yanda tadinga wani dakewa irin itafa ta saba da hawan jirgi. jaridar yasaka ya rufe fuskarsa yana murmushi da jinjina jan aji irinnan yarinyar, ita bata yarda aga marenarta ba. ya tuna diramarsu ta daren jiya, wani murmushin yakuma saki...... haka abubuwa da yawa sukaita dawo masa akan Matar tasa ta auren Contract. wani abun nata abin dariya, wani Na mamaki, ita bata yardaba adole big girl Ce. Koda suka sauka baiko kalli inda yarinyar nan takeba, da sauri tabi bayansa tana fad'in “haba yayana babu sallama? Ai kodan darajar makwaftaka mayi sallama”. Yana sauka daga step d'in k'arshe Na jirgin ya juyo ya kalleta, aransa yace yarinya sai nacin jaraba. Ta kuma fad'in “kozaka bani Number ka muke zuminci”. Yanzu kam wata uwar harara ya zuba mata kafin yay gaba abinsa. tsaye tayi tana binsa da kallo, jitake kamar ta tsala ihu, harma tafara tunanin ko shid'in kurmane?. cikin matuk'ar mamaki ta hango wasu masu kaya iri d'aya sunyo wajensa, daka gansu kaga jama'ar masarauta. da k'yar ta had'e yawun bakinta, kenan shid'in jinin sarautane?. Batada mai bata wannan amsar, Dan haka taci gaba dabin motocin Galadima da kallo har suka fice abinsu. Driver d'in da yazo d'aukarta yak'araso inda take, gaisheta yafarayi kafin ya k'ar6i handbag d'in hannunta. amota take tambayarsa koya San wanene Wanda masu kaya iri d'aya sukazo d'auka?. Yace, “ma'am Galadima Sameer kenan, d'an tsohon Sarki, kusan 1month kenan da aurensa ai”. Hararsa tayi cikin daka tsawa tace “ina ruwana dawani aurensa, bashi Na tambayeka ba. Punishment d'inka Na fad'amin abinda ban tambayeka ba shine ka nemomin number sa”. “ALLAH ya huci zuciyarki Ma'am”. Banza tamasa, yayinda shikuma zufa keta karyo masa dukda AC n dake motar, tunaninsa a ina shikuma zai Samo number babban mutum irin Galadima Sameer shikam? yasan idan bai samo d'inba yashiga uku, dan yarinyar nan ba mutunci gareta ba. ********************* Tun bayan tafiyar Galadima saina zama wata sukuku, abin mamaki saigani da kewar Galadima wai, gaba d'aya yinin sai nayishi wani babu dad'i, ga gabana yanata yawan fad'uwa, jinake kamar wani al'amari yana shirin faruwa da rayuwata. Sauban ma sarkin tsokana kasa shiru yayi saida yay magana. Bayan ya dawo school sai muka tafi asibiti, tunda Na gaida Abie da Momma da Aunty Mimi saina koma gefe nayi shiru abina, ciwon jikine kawai ke nuk'urk'usata, dan ga6o6ina masifar ciwo sukemin, narasa wannan dalili? zazza6inma banaji yanzun, ga yawan fad'uwar gaban dana yini inayi, sai kasa kunne nake naji ko Galadima zai kira wani a 'yan uwansa yace ya sauka lafiya, dan zuciyata tafi karkata da fargaba a kansa. Shirun da Sauban yaga nayi shine ya kalleni yana dariya k'asa-k'asa. “Aunty gimbiyarmu har kin fara kewar Hubbin naki halan?”. Idanu nad'an waro ina kallonsa, ganin su Momma Na dariya saina 6oye face d'ina cikin veil d'ina ina fad'in “kai yaa Sauban ALLAH a'a”. Dariya suka kuma sanyamin, Abie nata murmushi shidai, Momma tace, “A'a Mrs Galadima kifad'a gaskiya dai?”. Kunya takuma lullu6eni, saina k'udundune kaina gaba d'ayama a gyalen saboda. ina k'aunar wannan family sosai a raina, saboda nima suna nunamin tsantsar k'auna, ko yau nabar cikinsu auren contract d'inmu yak'are bazan manta da alkairinsuba a gareni. Haka nagama shirin barci Na kwanta a gadonsa ina shak'ar k'amshin turarensa danakejin dad'insa fiye da da. nadad'e ina juye-juye banyi barciba saboda damuwace cinkushe da raina, ga zazza6i mai zafi ya rufeni, bansan ina Galadima yajeba balle nayi tunanin samun number na kirashi, Na gwada number shi ta nan India tak'i wucewa, dama a wayar Samha Na d'auki number bama ta saniba, yau babu mai kulawa dani, sainaji wata kewar innarmu da Munubiyata sun dawomin sabo fil a zuciya. Sai da dare yakusa rabawa kafin barci mai nauyi ya d'aukeni. _____ .★. _____ .★. _____ Har yamma ba'abari kowa yaga Abba ba, 'yan gidanmu sunci kuka harsun gode ALLAH, Su Munubiya da dukkan yaran gidanmu Na ma'auri tuni labari ya iso musu, kuma duk sun tattara a asibitin suma. Doctor d'in dayake kan Abbanmu ne yafito yana basu hak'uri akan suje gida hakanan, dan gaskiya baza'a bari suga Abba ba a yau. Sabon kukane yatashi, musamman ga innaro, idan ka kalleta dolene tabaka tausayi wlhy, yau babu jarabarnan da rashin mutunci, kuka take da fad'in Auwalu karya tafi ya barta.......... Sambatunta yakuma raunana zukatan mutane da yawa a wajen. Munubiya tayi yunk'urin kirana amma network yahana, da Yaa marwan yakula da hakan kuma ya hanata, yace karta sake ta sanarmin yanzu. Wannan dalilin yahana a sanar min d'in. Kowa zuciya babu dad'i suka tattara suka tattafi gida, dady da baba k'arami, yaa hameed yaa shafi'u da ya Naseer aka bari a asibitin zasu kwana. Ranar duk Wanda yasan gidanmu yasan babu lafiya, Dan gidan yayi tsitt, kowa tashi ta isheshi a zuciya, barcima k'alilanne daga cikinsu suka yisa. ___________________________ Sosai hadimansa sukayi farincikin ganinsa, kamar yanda shima yay farin cikin ganin Nasu, sud'in mutanene masu muhimmanci a rayuwarsa, sunzama wasu 6angare na duniyarsa. Kwance yake a bayan motar idonsa a lumshe, ya saki guntun murmushi saboda tinano yanda zata k'are masa a wajen Momma, koda wasa bai sanar mata Nigeria zai zoba, yayi hakane kuma dan kartayi yunk'urin dakatar dashi ma. jin alamar motar ta tsaya ya bud'e lumsassun idanunsa tareda furzo k'aramar iska, duk da isowar dare yayi hakan baisa sauran hadimansa sun kwanta ba, ya iskesu zazzune a k'ofar sashensa suna jiran isowarsa. Dogarin daya bud'e masa k'ofar yafara k'ok'arin d'aukar briefcase d'insa domin shigar masa. Shima ziro k'afarsa d'aya yayi ta inda aka bud'e masan, ya zuk'i iskar masarautarsa tareda fesota tabaki yana lumshe idanunsa, ko ina kwanyar yake da hasken lantarki tamkar rana, duk lokacin daya zo cikin masarautarsa, mahaifarsa, yakan tsinci kansa cikin tunano abubuwa masu d'aci da rad'ad'i a zuciyarsa, yakanji inama ace shid'in ba kowa baneba, inama ace shid'in talakane fitik mai tarin kwanciyar hankali, da za'ace yaza6i rayuwar dazaiyi, da zai za6ama kansa zama talakane, dan babu Wanda yakai talaka kwanciyar hankali inhar yanada k'yak'yk'yawar zuciya da wadatar zuci, amma babu komai a cikin dukiya da mulki sai damuwa darashin kwanciyar hankali, kai kenan kullum cikin rashin nutsuwa, idan kayi wasama ibadar da ubangiji ya halicceka dominta bazakayiba, ya had'iye wani Abu mai d'acin gaske a mak'oshinsa. sannan yashiga k'ak'aro murmushin dole ga sauran hadimansa dake gida basuje tarbarsaba. daka kallesu kasan suna cikin tsantsar farincikin ganinsa, dan sunyi kewarsa, shima hakance agaresa. bayan sun gama gaggaisawa ya tambayesu lafiyarsu sannan yashige ciki. Ko ina k'al yake tamkar yanda yake buk'atar ganinsa, (hadimansa nada k'ok'arin tsaftace sashensa koda baya k'asar). Zama yay bisa kujera yana fad'in “ya ALLAH! Alhmdllh”. Dogarin daya shigo masa da jakka yakuma masa sannu da zuwa sannan yafice. Yakai mintuna 5 a wajen zaune, sai k'ullawa da kwancewa kawai yakeyi, ga gajiyar zaman jirgi na nuk'urk'usarsa data rashin isashen barci dabasa samu shida Munaya. da k'yar dai yamik'e zuwa bedroom d'in, komai need sai k'amshin mayen turarensa da air fresheners mai sanyin dad'i ke tashi, ya ajiye jikkarsa a kan gadon sannan yafara zame kayansa danya samu ya watsa ruwa. Ya d'an jima a bayin sannan ya fito d'aure da towel, yana tsane fuskarsa zuwa kai dawani. wardrobe yabud'e ya d'akko boxes kawai yasaka, sannan ya saka jallabiya, sallolin da suka riskesa a hanya ya rama, yana idarwa yacire jallabiyar, matsawa yay jikin mirror ya fesa turare kad'an ya hau gadonsa da yay missing. harya kwanta yatashi zaune, briefcase d'in dayazo da ita ya bud'e, ya Ciro wayoyinsa tareda layinkansa na Nigeria duk ya saka, sannan ya ijiye wayoyin, insha ALLAH zuwa lokacin da zai tashi yana fata komai ya dai-daita. Addu'ar barci yayi ya gyara kwanciya, amma sai barci yace bai gadaba, tunanin ahalinsa daya baro wata k'asa ya dabaibaye zuciyarsa, wata kewarsu ke tsikarar zuciyarsa, yanzu yasan Abie yayi barci, hakama Momma watak'il ta kwanta, dan macece mai yawan k'iyamull laili, duk da a asibiti takan kwana hakan baya hanata kusanta kanta ga mahaliccinta, Aunty Mimi da Samha ma yasan sunyu barci, Sauban ne dai dakamar wahala ace ya kwanta, ya juya kwanciyar sa yana murmushi, zuciyarsa tace “to matar contract fa?”. ya d'age kafad'a da ta6e bakinsa kad'an, saikuma yasaki k'aramar dariya, daren jiyane kawai ya fad'o masa a rai, yau kuma koyaya ta yini ta kwana? (danba time d'inmu d'aya da India ba), a fili yace, “ALLAH yasa yau dai babu zazza6in, my Friend kin cika taurin kai, dakin yarda nakaiki asibiti zanfi samun nutsuwa, oh god🤦🏼‍♂”. ‘ya k'are maganar da dafe kai’. Shima yajima baiyi barciba, sai can dare yaja da nisa sannan ya saceshi. Da asubahi da k'yar ya iya tashi, alwala yay yafita massalaci, bayan an idar da salla yafito suka had'u da Sarki da jama'a keta zubewa suna kwasar gaisuwa. Sarki yayi mamakin ganinsa, dan har saida fuskarsa ta nuna hakan, murmushi kawai Galadima yayi yana rissinar da kansa k'asa. Sarki baice masa komaiba yanufi sashensa, sai Galadima yabi bayansa, dogarai kuma suka take musu baya, bayan sun gaida Galadima d'in. A hamshak'in falon mai martaba na farko suka yada zango, Sarki na zaune bisa kujera mai zaman mutum biyu, Galadima na k'asa kusada k'afafunsa. Kukun Sarki ne suka shigo shida jakadiyya bayan sunyi sallama.. K'aramin tire suka ajiye dake d'auke da butar shayi, sai mug da wani k'aramin bowl mai k'yau anzuba sukari, sai jug k'arami shima an zuba tataccen lemon tsami, saikuma Zuma shima a k'aramin bowl. Kuku da jakadiyya suka zube gaban mai martaba suna kwasar gaisuwa, sannan suka gaida Galadima shima da masa barka da zuwa. Cikeda kulawa ya masa musu, har kuku ya durk'usa zai had'ama mai martaba shayin Galadima ya dakatar dashi, tareda masa nuni dayaje abinsa. Kuku ya rissinar da kai alamar girmamawa sannan suka fice shida jakadiyya suka basu waje. Galadima ya had'ama Mai martaba shayi da ruwan lemon tsami kamar yanda yasan yana sha a kowacce Safiya, (ada mahaifinsa yasani da wannan al'adar, dan awajensa Sarki jalaludden ya koya). cikeda girmamawa ya mik'ama mai martaba mug d'in, kar6a yayi yana masa murmushi, sannan yace “kaifa?”. Girgiza kai Galadima yayi, yace “a'a Abba, wannan sai ku”. Mai martaba yay murmushinsu na manya sannan yace “Saukar yaushe Sameer?”. Galadima yad'an shafa wuyansa, cikin tsantseni yace, “da daddare Abbah, wani business ne ya kawoni, inaga insha ALLAH zamu bud'e company anan Nigeria saboda muma matasanmu su Mora daga guminmu”. Murmushi mai martaba yayi, ya kur6i shayinsa sannan yace “tunani mai k'yau yarona, ALLAH yasaka hannu a lamarin. ya jikin d'an uwana dasu auntyna Zeenah?”. “jikin Abie Alhmdllh Abba, dan bayan tahowarku sauk'i yakuma samuwa gaskiya, Momma kam suma lafiyarsu lau”. “to Masha ALLAH, tareda iyalin naka kazo kenan?”. “a'a Abba, ni kad'ai nazo, saina kammala abinda nazoyi itama idan zan dawo zamu dawo tare”. “to ALLAH ya tabbatar”. “Amin Abba, bara naje nad'an kimtsa mu gaisa da jama'a, dan zan d'an fita”. “ok, ALLAH yayi Albarka”. “amin Abba, a huta lafiya”. Hannu kawai mai martaba ya d'aga masa, Galadima kuma yafita. Babu inda ya Shiga, ya koma sashensa domin yayi shiri. saida ya had'a coffee da kansa kamar yanda ya saba idan yazo k'asar, ya zauna yasha danba abincin kowa yakeci a masarautarba, ko Ummu hasheem bayacin abincinta kota kawo, duk da kuma kulawa datake nuna masa fiye da kowa a gidan, gimbiya zulfah uwargidan sarkima tanada k'ok'arin aika masa abincin inhar yazo, amma ko kallon kulolin ma bayayi, saidai bayinsa su cinye. Yafito wanka yana tsane jikinsa wayarsa tayi k'ara alamar shigowar sak'o, wayar ya d'auka danya duba ko company ne, dan yana fatan ace komai ya daidaita ne, yanason kiran su Momma yaji Yaya jikin mahaifinsa. Ganin number ce sai abin yabashi mamaki, bud'e sak'on yayi kawai azatonsa ko Nuren ne. _Gargad'i!! tabbas sirikinka ya tsira a wanan karon, amma ka tabbatar masa next time bazamu barsaba, saimun raba ruhinsa da gangar jikinsa!!!!.................._✍🏼 *_ALLAH ya gafartama mahaifanmu😭🤚🏻✋🏻_* [7/3, 9:54 AM] Aysha Galadima: *_Typing📲_* *_Haske writer's asso...._*💡 *_♦RAINA KAMA......♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻 ~Book 2~ 👉🏻5⃣ ..............Bayan an idar da salla Galadima yace wanne office yakamata su fara zuwa?, mtn ko glo?. Shiru Nuren yay yana tunani, zuwa can ya kalli Galadima “Sameer mizai hana mubari sai zuwa gobe, kasamu kaje kad'an kwanta ka huta, kaga yanda idonka yay jazur kuwa, ga jijiyan dukta tashi”. Lumshe idanu Galadima yayi yana furzar da huci mai zafi a bakinsa, “Nuren muje kawai, kona kwanta bazan samu nutsuwa ba, kaga fa yanda suka jigata bawan ALLAHn nan”. “hakane, amma karka damu muje kai dai kawai”. Galadima bai musaba, suka jera shida Nuren zuwa wajen mota, bayan anbud'e musu sun shiga sai Nuren yacema Sarkin mota suje hotel d'in daya sauka. Galadima yanajinsu amma baice uffanba, yayi shiru kawai yana kallon jama'a ta glass. Koda suka isa hotel d'in sai Nuren yace su sarkin mota suje abinsu, zuwa anjima zai kirasu su maida Galadima d'in gida. Cikin girmamawa sarkin mota ya amsa da to, yamusu sallama suka tafi. Koda suka isa d'akin da Nuren ya sauka Galadima cire rigar shaddar yayi ya kwanta dagashi sai dogon wandon da vest, kwanciyar mintuna 5 kacal barci yay gaba dashi. Sosai tausayinsa yakama Nuren, yanason d'an 'yar uwar mahaifinsa sosai, (Nuriddeen d'ane ga Abubakar yayan Momma, babban d'an Sarki Abdul'fatah daya gaji sunan Sarki Abubakar kakansu Galadima, mahaifin Nuren ayanzu haka shine mai jiran gado a masarautar su momma, Nuren d'ansane na biyu, akwai yayansa Ballo, shid'in sa'an Galadima ne, kusanma tare akayi goyonsu, amma Galadima ya girmesa da watanni 7 a duniya, kunga d'an uwansane na jini kenan, ta 6angaren mahaifiya👌🏻). Galadima ya jima yana barci, dan kiran sallar la'asarne ya tadashi ma, wanka yasake yi, ya kar6i kayan Nuren ya sanya, k'ananun kayane amma sun masa k'yau sosai, Nuren nata tsokanarsa, wai kayan sun masa k'yau, inhar Munaya ta gansa bazata ganeshi ba. Harara ya zubama Nuren, sannan yanemi hanyar fita, “malam idan kagama surutun saika taho muje”. “sorry sarkin gagara badau mai jiran gado”. tsaki Galadima yayi kawai yafice abinsa, shifa haushin mai jiran gado d'innan yakeji idan aka ambata masa, sadai nemi mai jiran gadonsu amma bashiba, mtsoww!!. Wata mota dake fake a harabar hotel d'in suka nufa, Nuren ya zauna a mazaunin driver, yayinda Galadima ya zauna gefensa. A hankali Nuren ke tuk'in suna 'yar hirarsu jefi-jefi, dayake kowanne akwai nutsuwa basuda yawan hayaniya, dan shima Nuren d'in bashida surutu. Tafiya mai d'an nisa ta kaisu wani k'auye, bawani babban gari baneba can. Galadima ya kalli Nuren yana hararsa, “wai Nuren bazaka saida gidannan ba dai ko?”. Murmushi Nuren yayi, yad'an gyara zamansa yana kallon Galadima, saikuma ya maida ga hanya. “brother kenan, ai yanzu ba abinda kuke tunanin nake aikatawa ba a gidan, wlhy babu ruwana da 'yar kowa yanzun”. “Humm Nuridden! nasan inhar kana tareda Muzaffar bazaka ta6a daina neman mataba, nidai bazan gaji da gaya maka gaskiya ba, inhar aure kakeso kawai kayi aure, bazaka gane llar zina ba saika auri yarinyar da wani yagama Sani, saika haifi yara kuma, Nuren! Ba cika baki nakeba, bakuma nafi k'arfin ALLAH ya jarabceniba, amma dana aikata zina ka ganni nan gamma a d'auramin aure da mata hud'u a rana d'aya, please and please d'an uwana, ka canja tun Kannada damar hakan, dukkanin ahalinmu basa son wannan d'abi'ar taka wlhy”. Nuren ya jinjina masa kai yana cije la66a, “na gode d'an uwana, insha ALLAH nabari har abada, kuma kwannan zakaji maganar aurena ta tashi, wlhy tun wancan lokacin da abunnan yafaru ban sake mu'amulla da kowacce maceba, idan najima zan takura saina fara azumi”. “tom ALLAH yacigaba da gadinmu muda zuciyoyinmu, amma Auren shine tafi cancanta dakai, dan wani lokacin da mutum yakai azumin ma zakaga komai yadawo, kaga Auren shine cikakkiyar mafita kawai”. “gaskiyane wlhy, ALLAH dai ya k'ara shiryamu”. ‘Nuren yafad'a yana horn a k'ofar gate d'in katafaren gidan gonarsa dayake kiwo’. An bud'e musu gate d'in suka shiga, ma'aikatan sai murnar ganinsa sukeyi, tsayawa yay da motar batare da sun fitoba, sukaita zuwa gaishesu, bawani Sanin Galadima sukayi sosaiba, tunda bawani zuwa wajen ya keyiba, Nuren zai fad'a musu wanene, amma Galadima yamasa nuni da karya fad'a, hakkane yasakashi 6ame bakinsa. ****************************** Ran mama Fulani a 6ace yake kallon manyan jikokin nata maza guda uku tayi, cikin isarta da k'asaitarta tafara kiran sunayensu, “Talba! Wanbai! Matawalle!, kunsan dalilina Na taraku anan kuwa?”. A tare suka girgiza mata kai kawai. Takuma gyara zamanta cikin tsantsar mulki da izza, tace, “nakula mahaifinku har zuwa yanzu baison ciwonku ba, shi dole yanaso ace masa adalin Sarki, shiyyasa kullum yake fifita d'an wani bisa Ku da ALLAH ya bashi, Matawalle shekarunka dana Galadima kusan d'ayane, amma mahaifinku nagani Galadima yay aure bai ta6a nuna damuwarsa akan kai kayiba balle sauran 'yan uwanka, to yanzu matar Galadima cikine da ita, kuma tabbas ta haifi namiji kuda sarautar gagara badau saidai kallo”. A razane Talba da wambai suka zaro idanu waje a zabure, matawalle kuwa murmushi kawai yayi yana girgiza kai da mamakin wannan kakar tasu mai shegen son kanta. Wambai yace, “haba Granny miyasa kike fad'ar wannan maganar, yakamata bakinki ya fad'i alkairi mana, shi dan uban cikin basai mun bari an haifesa ba, koshi uban cikin dayake tak'ama yana jiran gado bai isa yayi mulkiba balle cikin da babu tabbas d'in haifosa, ni wlhy kinma 6atamin rai”. Talba yaja tsuka shima yana harare-harare, “Granny ya akayi kikasan tanama da cikin to? wannan sarkin girman kai d'inne zai iyama mace ciki?”. Harara mama Fulani ta zubama Talba, “to uban matanbaya, azatonka zai zuba mata idone yana kallonta kamar hoto ko television a gida? ince kwana nan 4 kenan dabaro inda suke”. Wambai yace “amma shine bakiyi maganarba sai yau Granny?”. “to ubana koyamin yanda zanyi”. “ALLAH yabaki hak'uri”. ‘cewar wambai yana k'unk'uni k'asa-k'asa’. Matawalle dabaice uffanba tunda aka fara maganar yay guntun murmushi, muryarsa a tausashe yace, “Ranki ya dad'e ni banga amfanin wannan maganarba, ALLAH shine ya azurta Galadima da samun ciki a jikin matarsa, wannan kuma abun farin cikinmu ne amatsayinmu Na 'yan uwansa, shi dai mulki Na ALLAH ne, shike badawa ga Wanda yaso akuma lokacin da yaso, bamuda tabbacin tsawancin ran ganin gobenmu ma balle maganar gadar sarautar cikinma daba'a San miza a haifaba, please musama zukatanmu sallama kodan mutuwa, nifa banga wani dalili dazamu ke saka kammu a wahala akan mulkin da ubangijine kawai madawwami a mulkinsa, nikam kunga tafiyata, ki gafarceni inada uzuri”. Tunda matawalle yafara maganar Mama Fulani da Talba da wambai ido suka zuba masa, harya fice ba'a samu mai iya tanka masaba. haka yake shi, babu ruwansa da bak'in mugun abun masarautar, da zuciya d'aya yakeson d'an uwansa, shi bama wani zaman k'asar ma yakeba sosai. Wani wawan tsaki Talba yaja, yabi bayan Matawalle da harara yana fad'in “lusari kawai, inkai bakason sarautar mu ai munaso, shifa wannan ko sarautar ya gada wlhy lusarin Sarki mai lasisi za'ayi anan, duk wannan wahalar akansa akeyinta danya zama magajin Abba amma shashashan nan baya gani”. “mtsoww!! bar banza d'an uwa, idan zai bamu matsala kai basai ka zama magajin Abban ba, nifa harma tunani nake, anya matawalle jinin gidannan ne?..........” “kai ya isa haka, banason rashin tauna magana, Ku k'yalesa zaima dawo hanyane, miye mafita yanzun?”. “mafita d'ayace Granny a 6arar da shegen cikin kawai, kuma ma ai Galadiman yazo jiya”. Da sauri mama Fulani ta tashi zaune daga kishin gid'ar datayi, “wambai kana nufin Sameer na a masarautar nan?”. “kwarai ma kuwa, da safe nagansa zaishiga mota a k'ofar sashensa, yanata faman d'aurema mutane wannan shegiyar fuskar tashi da yakejin tafi ta kowa k'yawun gani”. Wani k'asaitaccen murmushi mama Fulani tayi tana fad'in “lallai yaronnan ya isa, kuje kawai, bayan nagama tsara komai zan nemeku”. atare suka mik'e suna fad'in “ahuta lafiya ranki ya dad'e sarauniyar gagara badau”. Murmushi tama jikokin nata tana gyad'a musu kai. ____((____(((★)))____))____ Galadima da Nuren sun shiga ainahin matsakaicin gidan Nuren dake a gidan gonarsa Na kiwo, sosai ya tsara cikin gidan, dan ananne yake holewa da 'yammatansa a watannin baya, sai dai yanzu kam alhmdllh yabari gaskiya, dan sai lokaci-lokaci yake d'an ta6awa, fatansa ma yabari gaba d'aya, dama ta silar abokai ya koya🤦🏻‍♀. Galadima ya zauna saman kujerar guda d'aya yana sauke numfashi, har yanzu zuciyarsa tak'i nutsuwa waje d'aya, halin da yaga Abban Munaya ya dank'are masa zuciya. Cikin ma'aikatan wajen yay sallama daga waje, Nuren yabashi izinin shigowa, kayan marmarine yahad'o ya kawo musu bayan ya tsaftacesu, a saman center table d'in ya ajiye, sannan yakona yaciro musu ruwa a freight d'in dake falon da cups Na glass. Bayan fitarsa Galadima ya kalli Nuren d'in, “Brother wai miyasa ka kawoni nan ne?”. “cinikin kanka nayi”. ‘cewar Nuren yana harar Galadima’. “Wani k'asaitaccen murmushi Galadima ya saki, yakai hannu yana shafa sajensa zuwa gemu, cikin d'age kafad'a da la6e baki yace “baka kai girman saida kainaba yaro”. “uyim! Haka kace ko?”. ‘cewar Nuren yana kallon galadima’. “kaima kasan hakanne ai”. Mik'ewa Nuren yayi yashiga wani d'aki yana dariya, mintuna 4kacal saigashi tare da wani dattijo. Galadima da yake kishingid'e yad'ago ido yana kallon Nuren da dattijon, amma baice komaiba yacigaba da latsa wayarsa hankali kwance. Dattijo direban Alhaji balala ya zube k'asa yana kwasar gaisuwa ga Galadima. Galadima shi mutumne mai mutunta Wanda ya girmesa, dan haka Yakuma d'ago kai yana kallon dattijon, fuskarsa ba'a d'aureba ba'a sakeba, cikin muryarnan tasa ta isar masu mulki da k'asaita yace “no baba zauna da k'yau, kabar durk'usamin banaso”. Dattijo yace, “ai girmanka ne ranka ya dad'e”. Murmushi kawai Galadima yayi, ya ajiye wayar hannunsa yatashi zaune sosai, ruwa ya d'auka ya zuba a cup sannan ya d'ora k'afa d'aya kan d'aya yana kallon dattijo. “bawan ALLAH minene sunanka?”. Jikin dattijo Na rawa yace “Barau ranka ya dad'e”. “humyim baba barau, koka sanni?”. “sosaima ranka ya dad'e, wanene zaice bai sankaba a wannan nahiyar”. Galadima ya wani lumshe idanu yana cije lips nashi, ya bud'e idanun akan Mal barau da duk yake a tsure, sosai kwarjinin Galadima da cikar haibarsa suka rikita dukkan tunaninsa da kwarin guywarsa. Galadima ya katse masa tunani da fad'in, “Baba barau nasan akwai tambayoyi taf bakinka a gareni, saidai bazan baka amsar ko guda d'ayaba, zan baka dama da sharad'i, Na farko shine kanada damar fad'amin gaskiyar abinda kasani idan Na tambayeka, nikuma nabarka ka tafi salin alin, Na biyu inada sharad'in ka d'aukarmin alk'awarin komai zai fito abakinka ya zamto gaskiyar abinda Na tambayeka, idan kamin k'arya koka yaudareni kuma.... Humm”. ‘yak'are maganar da cije lips nashi batare da ya k'arasaba’. Hakan yasaka jinin Malam barau rawa, yana karkarwa yace, “insha ALLAHU ranka ya dad'e zaka sameni yanda duk kake buk'ata”. Nuren yace, “good daka fahimci hakan”. Galadima bai sake cewa komaiba yacigaba da latsa wayarsa. Nuren ya kalli Malam barau yace, “malam barau kasan wanene tsohon Sarki?”. “eh kwarai ranka ya dad'e Na sanshi, shine yake jinya a India yanzu haka aiko”. “shin minene alak'ar uban gidanka da tsohon Sarki?”. A rikice Malam barau yace “ranka ya dad'e miyasa zakamin wannan tambayar? Ku gafarceni, kuyi wata amma ba wannanan ba dan ALLAH”. Galadima ya d'ago idanu ya zubama Malam barau su, jiyay zuciyarsa tana Neman fara hasala, har zaiyi maganar sai kuma miya tuna yay shiru ya had'iyeta, maida kansa yayi yacigaba da latsa wayarsa. Nuren ya bud'e k'aramar drowa dake jikin center table d'in falon, saiga bindiga 'Yar k'arama ta bayyana, Malam barau ya waro idanu waje yana kallon yanda Nuren ke d'ura Bullets a cikin bindigar. Galadima duk yana kallon Nuren ta gefen ido amma baice masa uffanba, saida Nuren ya gama sannan ya tashi ya koma kujerar kusada Malam barau, cikin d'aure face yace, “nasan dai tsoron mutuwa ko rasa aiki zai hanaka bamu amsar tambayarmu, to tabbas in baka fad'anba zan fasa kwalwar kanka da wannan gun d'in, kuma ko k'arar fitar bullet d'inta baza'ajiba ballema asan an kasheka, akuma cikin falonnan zan binne gawarka wlhy!!”. Jikin Malam barau Na 6ari yarik'e wandonsa, dan har fitsari yafara fito masa kad'an, yace, “ranka ya dad'e mi kuke son sanine?”. Galadima dake latsa wayarsa hankali kwance, batareda ya d'agoba yace, 20 ga watan Yuli miya faru a masarautar gagara badau”. “ranka ya dad'e wlhy bansan komaiba, amma tabbas ogana yafito ransa a 6ace daga wajen meeting d'in dasukayi da Sarki shida abokansa. daga hakan bansan komaiba wlhy kaji Na rantse maka”. Idanu Galadima ya d'ago ya zubama Malam barau, yace, “malam Saminu kafadda!. koba shine ainahin sunanka ba? Na sanar da kai karkamin k'arya, dan tunkan nakawoka nan nasan komai daya shafeka, amma a tashin farko kamin k'aryar sunanka Malam barau, humm abin dariya, inason mutum mai gardama dason ku6tar da kai. Malam Saminu shiga tarkon Muhammad Sameer ba abune mai sauk'iba, ina aiki da kwakwalwa, kamar yanda gangar jiki take aiki da zuciya, karka yarda a maganarka ta gaba k'arya ta shigo, idan hakan ta kasance saina binneka da ranka, wannan tabbatacciyar maganar Muhammad Sameer Saifuddeen ce”. ‘ya k'are maganar da mik'ewa tsaye yana had'a yatsunsa biyu ya buga a saitin fuskar Malam Saminu, suka bada sautin d'as! d'ass!, sannan ya ra6a ta gefensa yafice’. Nuren ya girgiza kansa, “dattijo kayi kuskure kwarai da gaske, Galadima ya wuce dukkan tunaninka, tashi mu koma inda ka fito, a yanzu kam bazai ta6a saurarenka ba sai kuma wani karon”. Hawaye Malam Saminu yafarayi yana bama Nuren hak'uri, “yalla6ai dan girman ALLAH ka kirashi, wlhy zan fad'a yanzu, wlhy nagaji da zaman kurkukunnan, nasan hankalin iyalaina da mai gidana a tashe take, ka taimakeni”. K'ala Nuren baice masaba, ya dannashi a d'akin ya maida ya kulle sannan yabi bayan Galadima. ★):(★):(★):(★)(★):(★):(★):(★):(★ Tunda suka tafi babu Wanda yay maganar, saida suka shigo cikin gari sosai. Nuren yace, “dattijonnan nakula zaiyi taurin kai gaskiya”. Murmushi Galadima yayi yana kuma lafewa cikin seat, idonsa a lumshe batareda ya bud'eba yace, “mu wuce asibiti”. Amsawa da to kawai Nuren yayi. Sun isa asibiti suka iske duk 'yan gidanmu suna nan, saisu Munubiya da Dady yace su tafi gidajensu hakanan, tundama ba bari ake aga Abban ba basuga amfanin zaman nasuba, gashi mafi yawansu duk da tsohon ciki, sai kuma Munubiya da Fauziyya da Haleematu dake fama da laulayi. Haka ba dan sun soba kowacce takama hanyar gidanta, wadda mijinta kuma yace ta jirasa ta zauna jiransa. Suma su innarmu Yaa Anas ya kwashesu ya maida gida. Lokacin da su Galadima suka shigo asibitin mafi yawansu duk sun wuce, sai mazan kawaine a asibitin. Dan haka Galadima yasamu gaisawa da Munubiya dake jiran yaa marwan yazo d'aukarta. Munubiya ta tambayi 'Yar uwarta fa?, gaban Galadima yafad'i, danshi yama manta su Munaya suna hanya, guntun murmushi yayma Munubiya yace insha ALLAH suna hanya itama, maybe su iso cikin darene kokuma da asuba”. “ALLAH ya kawosu lafiya”. ‘cewar Munubiya tana sharar hawaye’. Tabama Galadima tausayi sosai, haka ya k'arasa wajen doctor domin kumajin ko ansamu wani cigaba a jikin abban.. Doctor yamasa bayanin duk an gyara karayar jikin Abba, hakama sauran ciwukan suna samun kulawa, kuma bugun zuciyarsa ta daidaita bakamar jiya zuwa safiyar yauba. Galadima ya jinjina kai, tareda sake jaddadama doctor gargad'in kulawa da Abba d'in sosai. Yad'an jima a asibitin sannan su sarkin mota sukazo d'aukarsa, Nuren kuma daga nan hotel d'in daya sauka yanufa. ya sauka hotel ne saboda basa buk'atar wani a masarautar su Galadima yasan da Nuren d'in. ___________________________ Wajen misalin 2:30 na dare su Munaya suka sauka, Sauban yayta wayge-wayge ko an zo d'aukarsu, amma baiga alamun wani mai alak'a da masarautaba, ya kalli Munaya yana dariyar tsokana, “Aunty gimbiya Honey d'inki ya manta damu, bai aiko d'aukarmu ba, kuma inatsoron mu shiga motar haya azo a kwamushemu, kinsan yanzun kasuwancin kidnapping shine keda tsada a 9ja”. Duk da Munaya tana tare da damuwa hakan bai hanata yin dariyaba, tace, “kai yaa Sauban bakada dama, ina zamu samu waya mu kirashi to?”. Kafin Sauban yabata amsa sukaji magana a bayansu. “to maganannu, saikuzo mu wuce, wannan surutun nakuma bayasa ayi kidnapping d'in naku ba”. Gaba d'ayansu juyowa sukai suna kallonsa, Galadima ne sanye cikin wando fari 3quarter da riga t-shirt pink mai gajeren hannu. harya kwanta suka fad'o masa a rai, babu shiri yazari mukullan mota yafito, bai tada kowaba a dogaransa saboda kasada irin tasa ya fito zuwa airport, isowarsa baifi da 17minutes ba jirginsu Munaya ya sauka, tunda suka fara fitowa daga jirgin idonsu a kansa, har tsayuwarsu da waige-waigen dasukeyi na son ganin Wanda yazo d'aukarsu yana kallonsu. shagala yay da kallon Munaya, wadda sai a yanzune yaga k'ibar da Samha ke fad'in tayi, ta murje tayi 6ul-6ul da ita, har wani haske yaga ta k'ara masa, saboda hasken daya haske ko'ina a cikin airport d'in. yadad'e tsaye a bayansu, duk gulmarsa da Sauban yayi akan kunnensa ne. Sauban ya k'araso da sauri ya rungume d'an uwansa, dukda jiyane kawai suka rabu saiyaji yayi kewarsa. Galadima yad'an daki bayansa yana fad'in “k'aton banza, ka girma bakasan ka girma ba”. d'agowa Sauban yayi daga jikin Galadima yana dariya, yayinda Munaya da Galadima suka had'a idanu, gira d'aya ya d'aga mata, itakuma tayi guntun murmushi tana kauda idonta gefe. (A ranta tace d'an duniya). Juyawa yayi batare da yak'ara magana ba, Munaya da Sauban sukabi bayansa, Sauban ya shiga baya, badan Munaya tasoba tashiga gaba kusada Galadima da zaiyi driving nasu, wannan ne karon farko da zataga tuk'insa a k'asarsa. Saida yatada motar suka fita daga airport d'in sannan a hankali kamar bataso tace, “yalla6ai mun sameku lafiya?”. Juyowa yayi kad'an ya kalleta ya maida kansa ga titi, saida yaja numfashi sannan yace, “kunzo lafiya my Friend?”. Kallonsa kawai tayi kad'an ta girgiza kai, a zuciyarta tace su Friend anji jiki, zanbika a hakan kodan samun yanda nakeso a kanka, danna cika alk'awarin danama mahaifiyarka insha ALLAH. jin batace komaiba yakuma fad'in “ko gajiyar tafiyarce?”. “kusan haka yalla6ai”. Yace, “to sannu yalla6iya”. Ba Munaya ba har Sauban saida yayi dariya da wannan suna, daganan motar ta d'auki shiru, har suka Isa masarautar. Muftahu dake binsu abaya ya sauke ajiyar zuciya, sannan shima ya shigo masarautar, tunda Galadima ya fito daga sashensa akan idonsane, Dan haka yay saurin bin bayansa da mota shima Dan yaga inda zaije. (Humm Muftahu😏). Sosai Munaya kejin barci da farinciki, yau gata tadawo k'asarta ta haihuwa, sun shiga sashen komai need tagansa, sai k'amshi dake tashi kamar kullum. d'akinta ta shige, Sauban da Galadima suka nufi nasa. Sauban ya zube a kujera yana kiran “wash!”. Galadima ya d'an hararesa, “amma idan yawonkane aibaka gajiya”. “yaya wlhy bazaka ganeba, nidai kawai bani wajen kwana na kwanta wlhy”. “Saidai ka kwana anan falo kuwa, kafin da safe a gyara sashenku ka koma can”. 6ata fuska Sauban yayi, “haba Yaya da gatana na kwana saman kujera, kadai katafi d'akin Aunty gimbiya ka kwana gaskiya kabani gadonka”. Galadima zaiyi magana Sauban yatashi da gudu ya shige bedroom d'insa ya saka key. Da sauri Galadima yace, “zan 6ata maka rai fa Sauban”. Ina, baima sauraresa ba, dafe kai Galadima yayi kawai, wlhy baisan lokacin da Sauban yafara rainashiba, kodan yaga tsawonsu kusan d'aya yanzu?. babu yanda ya iya dole yafita zuwa d'akin Munaya🤫.................✍🏼 Ho Sauban aikinka yay k'yau🤣, su Galadima dole a tafi😝, ba ruwana karya jini🤭⛹🏻‍♀ Readers kuma kuyi dariya a hankali fa🤫😝. Barkanku da juma'a🙋🏻. Musha weekend lafiya sisters😁🙋🏻⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀. *_ALLAH ka gafartama mahaifanmu😭🤚🏻✋🏻_* [7/3, 9:54 AM] Aysha Galadima: *_Typing📲_* *_Haske writer's asso...._*💡 *_♦RAINA KAMA......♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻 ~Book 2~ 👉🏻6⃣ ............Har ya fita ya dawo, laptop da wasu takardu ya d'auka a falonsa ya fita, zai zauna a falonta saikuma wata dabara ta fad'o masa, bedroom d'inta ya nufa yana wani ciccijewa (kaida zaka karoro, miye na fuska to yalla6ai?🤔😂). Munaya Na tsaye tana ninke hijjab d'in data rama sallolin dasuka risketa a hanya sai kawai shigowarsa tagani da sallama ciki-ciki. k'ok'arin warware hijjabin tafarayi tana masifa ita kad'ai a zuciya, haka kawai aita shigoma mutum d'aki babu izini, wannan wane irin rayuwane. Shikam Galadima kallo d'aya yamata ya d'auke kansa, Dan daga ita sai zani d'aurin k'irji. Laptop d'in hannunsa da takardu ya ajiye a bakin gadon, sannan shima ya zauna, batare da ya kuma kalllon Munaya ba yace, “kinajin yunwa ne?”. Ba yunwar takeji ba, amma dan Neman magana kawai tace “eh”. Kallonta ya sakeyi, bata yarda sun had'a idoba, yace “Saidai kisha fresh milk kuwa, dan bani da abinci”. Manyan idanunta ta waro masa waje, kamar wadda akace tasha wuta, cikin dafe k'irji tace “yalla6ai fresh milk?”. Da mamaki ya kalleta, danshi bai fahimci ma'anar razanar tataba, yace, “uhmmm”.... “Na yafe wlhy”. Tafad'a da saurinta. “To mine nawani birkicewa haka? fresh milk d'in wani abune dashi?”. “Humm”. Munaya tafad'a tana ta6e baki, tace “yalla6ai nikam idan kaga nasha fresh milk d'in data fito daga d'akinka saidai idan bana a hayyacina”. Da tsantsar mamakin furucinta yake kallonta, da yake basuda nisa saiya mik'a hannu ya rik'o nata, zatayi magana ya fizgota ta zauna kusadashi, kad'an ya rage ta hau masa laptop, amma yay saurin janyewa da d'ayan hannunsa. “wash hannuna”. Munaya tafad'a tana matse baki. Banza yamata, yakuma matsa hannun da mugunta. tasaki k'aramar k'ara tana fad'awa gefen kafad'arsa. Ya d'an kalleta ya janye yana ta6e baki “ban fahimci zancenki daga nesa ba, maimaitamin”.. Cikin tunzuro masa baki tace, “yoni babu abinda nake nufi fa, nidai bazan sha fresh milk d'in data fito daga d'akinka ba wlhy. haka kawai aje asakama mutum abinda zai halakashi”. ‘k'asa-k'asa ta k'arasa maganar, amma yajita sarai’. Shifa saima yanzu yagane inda zancenta ya nufa, wani miskilin murmushi yasaki yana danne dariyarsa datake shirin kufcewa, amma dukda haka saida taji sautin fitar murmushin nasa. Munaya dake satar kallonsa idonta harya cika da kwalla, a zuciyarta tace mugu d'an masa, dole fa kamin dariya. Saida yayi dariyarsa a zuciya ya gama ya kalleta, itakuma saiwani mar-mar takeyi da idanu wai zatayi kuka. Murmushi ya kumayi, sannan yace, “wannan bakin dakike tunzuromin ko, hummm.....”. ‘yak'are maganar da cije lips nashi’. Yunk'urawa tayi zata mik'e, tace, “yalla6ai ni wlhy barci nakeji fa”. Dawo da ita yayi ta fad'o jikinsa shima yana fad'in “nikuma gadinki zanyi ko? yalla6iya!”. Tace “wayyo innarmu kice ya fitarmin a d'aki please”. “ko waya zan baki ki kiratane”. ‘yay maganar cikin d'age gira d'aya’. Munaya tai saurin janye idanunta daga Kansa ga k'amshin turarensa ya gallabeta, barci takeji, amma takula mugunnan soyake ya hanata ma. Kamar zatayi kuka tace, “yalla6ai wai mikazo nemane please? Wlhy barci na keson yi?”. Shiru yamata, saida ya mula dan kansa sannan yace “jikina fa”. ‘yay maganar yana kallon k'ugunta’. Da sauri Munaya ta sauka daga jikinsa tana k'unk'uni da tura baki. Medical glasses d'insa ya d'auka ya saka, tareda cigaba da aikinsa a laptop, a zuciyarsa yana fad'in yarinyarnan akwai ruwan tsiwa, amma duk randa Na kama bakin tsiwarcan sai yamin bayani dalla-dalla kuwa. Ganin ya shareni ya cigaba da sabgarsa a System, nima sai ban kuma bi ta kansa ba Na d'auki kayan barcina nashiga bayi domin Na sanya. Sai dai zuciyata cike take da fargabar miya kawoshi d'akina?. haka na fito kamar wata munafuka ina lallak'ewa jikin bango. Duk yana kallona ta gefen idanu, amma yay kamar baima San dani a d'akinba. Sai zuwa can ya d'ago yana kallona, yana wasa da pen d'in hannunsa kan la66ansa, “idan bak'yajin barci zokimin wani d'an aiki nan”. Saida gabana ya fad'i, a raina nace aikin mi kuma?, a fili saina aro jarumta na yafama kaina, Dan nakula tsoron daya fara gani a idona ne yake neman fara rainani da samin fargaba (🤣ho munayan shagali). Takowa nayi inda yake, ina niyar zama bakin gadon sai ya nunamin tsakiyar gadon, shima laptop d'in ya tura sosai kan gadon ya haye tsakkiya yana gyara zamansa. kuma had'e fuska nayi ina wani dojewa na hau nima na zauna, cigaba yayi da danna laptop d'in, kusan mintuna 3 ya jehomin tambaya. “shin kinsan minene aikin Abba?”. Da mamaki na kallesa, nace “wai Abbana kake magana?”. “uhmm”. ‘yafad'a batare da ya d'agoba’. Shiru nayi alamar tunani, harya d'ago ya kalleni bance komaiba, maida kansa yayi ga laptop d'in yacigaba da aikinsa, zuwa can nace, “ma'aikacin gwamnati ne kawai tawani fanin kuma aikinsa yanada Nasaba da jarida”. Tunda nafara magana ya tsuramin idanu, bakina kawai yake kallo yana taune lips nashi, saida nakai aya sannan yace, “jarida?”. Nace, “eh, wani abune ya faru?”. Kansa ya girgizamin, “innalillahi” yashiga maimaitawa a zuciyarsa, baya fatan zarginsa yazama gaskiya, cikin dakiya yakuma cemin “kokin san abokansa? ina nufin cikin manyan mutane haka?”. “eh to, akwai senator halluru garba, sai kuma wani anacemasa Alhaji Mamman k'afur, last year yafito takarar shugaban k'asa......” Caraf ya kama hannuna, “kina nufin Alhaji Mamman k'afur abokin Abban kune?”. Ni tsoroma yabani, yanda yay maganar cikin rawar jiki, na jinjina masa kaina a hankali. Gani nai ya taune lips nashi da masifar k'arfi, ya kaima iska naushi. da sauri na matsa baya Dan karya nausheni, ganin kamar na tsorata sai yay murmushi, cikin k'asaitacciyar muryar nan tasa yace “my Friend! Yanzu ne zamu fara aiki tare da gaske ni da ke”. “kamar ya yalla6ai? wane irin aiki kuma?”. Murmushin takaici yayi, ya kalleni ido cikin ido, kasa jurewa nayi nai k'asa da nawa. shima lumshe nasa yayi yana fad'in “zaki gani”. daga haka ya janye laptop d'in gefe ya zame ya kwanta. Binsa nayi da kallo tamkar wata sokuwa, gaba d'aya ya kulle magudanar tunanina da wadda ke kaima kwakwalwata sakonni. Medical glasses d'in idonsa ya cire ya ajiye, sai kuma ya juyo gareni, hannunsa d'aya ya mik'amin yanamin alamar nazo gareshi. Idanu na d'an zaro, sai kuma na nok'e kafad'a alamar nak'i din. Wani murmushin da bako yaushe yakeyinsaba ya sakarmin, ya juyamin baya yay kwanciyarsa. bai sake juyowa gareniba har kusan 6minutes. nagaji da kallonsa da nazarin murmushinsa da tambayoyinsa na janye idanuna, waishi guy d'innan mike damunsa ne? gaba d'aya ya canjamin daga saukarmu zuwa yanzun, dubana nakai ga agogon d'akin. 3:27am, “ya salam” na fad'a a hankali, muna Neman kwana a zaune. can k'arshen gadon na koma na kwanta, zuciyata cike da tsoron ALLAH yasa bawani Abu ya shiryaminba, babu dad'ewa barci 6arawo ya saceni. Numfashina dake sauka a hankali yasaka Galadima gane nayi barci, juyowa yay yana kallona, yayinda zuciyarsa keta cud'a amsoshin dana basa yanzun, tabbas mahaifin yarinyarnan akwai abinda yasani, kwarai da gaske zaiyi amfani da ita wajen gano ko wanene mahaifinta?, minene alak'arsa da case d'ina?, sannan minene alak'ar Muftahu da ita?, Dan tabbas akwai manufar sako yarinyar acikin wannan tak'addamar, kuma Muftahu dashi aka shirya komai. yasaki wani murmushin mugunta tareda nuna kansa, a fili yace _MAK'IYAN MAHAIFINA SAINA ZAME MUKU_ *RAINA KAMA KAGA GAYYA* tabbas lokaci yayi dazakuga wannan *Gayyar*. Tofa masu karatu, ana zaton wuta a mak'era🤔, mikuna yasako Abban munaya a rikicin masarauta? Kodai ba masarautar kawai bace keda alhakin ciwon tsohon Sarki Saifudden Abubakar🤔?, shin tsakanin Galadima da Munaya & munubiya, innarsu Munaya. Wanene RAINA KAMA...... d'in🤗?. Kumuje zuwa kudai my Guy's😁, duk nisan jifa👆🏻, k'asa zai fad'o👇🏻🤗 ★___________________________★ Bayan shigewar su Galadima Muftahu ya fito daga mota shima yana murmushin dashi kad'aine yasan fassararsa, jiyay kawai handkerchief ya rufe masa fuska, yay saurin cirewa yana waige-waige dan dunba wanene ya jeho masa, wayam babu alamar mutum a wajen, bai gama dube-duben ba yay luuu zai fad'i, saigashi a hannun mutum, idanunsa sunriga sunyi nauyi, dishi-dishi yake kallon Wanda ya tareshi d'in, dama gashi ya rufe rabin fuskarsa ba'a gani, wasu samarine su biyu sukazo suka kama Muftahu tareda wancan suka danna a mota, tun yanajinsu sama-sama har idonsa da jinsa suka rufe baki d'aya. 🙆🏻tofa suwaye?. ★__________★_________★ Tun kusan around 8pm Nuren yake k'ofar wajen, a dukkan bayanan daya samu daga majiya mai k'arfi yarinyar Minister ta shigo gari yau, kuma zatazo shan ice-cream wajen, wayarsa ya d'auka yay wasu 'yan danne-danne, murmushi yayi ya maida wayar ya ajiye tareda dasama k'ofar wajen idanu, dolene kafin tashiga ciki zai saceta, dan bincikrnsa ya nuna masa cctv camera d'aya ce a cikin wajen kawai, a waje babu, dan haka bama ya buk'atar ta Shiga, murmushi yayi saboda ganin motar da driver d'inta yamasa kwatancen zasuzo aciki, saida driver n yaga motar Nuren sannan yazo kusada ita yay parking, bud'e murfin gefen mai zaman banza Nuren yayi, hakan kuma yay dai-dai da fitowar zankad'ed'iyar budurwa daga motar datai parking kusada ta Nuren d'in, murfin ne ya daki gefen hannunta kad'an. A fusace ta kalli motar Nuren, shikuma yay mata murmushi, wani haushine ya kamata, banda rainin wayo ya bigeta amma yamata murmushi saboda wulak'anci, yau saitaga wanene ubansa a garinnan?. da k'arfi tabuga saman motar tana lek'a kanta ciki, “kai wawa bakaga abinda kayi bane?”. Maimakon ya bata amsa saiya jefa mata handkerchief d'insa saman fuskarta, janyewa tayi da sauri zatayi magana kanta ya sara mata, da lalube ta dafa kujerar motar ta shiga ta zauna, sai faman lumshe idanu takeyi. murmushi Nuren yayi, ya taimaka mata ta ida shigowa Sannan ya rufe motar, komai akan idon driver n ta ya faru, bashida damar hanawa, dan Nuren yasashi a tsaka mai wuyane. Agaban idonsa Nuren yaja motarsa yabar wajen yana murmushin samun nasarar tafiyar plan d'insa yanda ya tsara. a wannan daren yanufi gidan Galadima dake can bayan gari inda aka ta6a kai Munaya. 😱humm yau 'yar kidnapping akeyi kawai😂🤪. ------------(((★)))-------------- Galadima yariga Munaya farkawa, dama bawani isashshen barci yayiba, tunani da damuwa suka taru suka hana idonsa rintsawa sai gabannin Asuba. Ana kiran sallar farko kuma yana farkawa, tashi yay zaune dafe da kansa, kusan mintuna biyu ya juya yana kallon munaya data juyo tana fuskantar inda yake yanzun, da gani kasan barcin bamai dad'i takeyiba, dan sai yamutse fuska takeyi a cikin barci. matsawa yayi kad'an ya d'ora yatsunsa biyu gefen fuskarta, sai yaji zafi jikinta, ya janye yana mamakin wai mike damun yarinyar nan kwana biyu haka? dolene yau yasata taga doctor idan sunje ganin Abba. gabansa yad'an fad'i daya tuna har yanzu itafa batasan komai ba, shi baima San ta yadda zai sanar mata abbanta yana cikin mawuyacin hali ba, ya dafe kansa yana ambatar sunayen ALLAH kozaiji sassauci a ransa. Da k'yar ya samu ya mik'e domin yin rakata ainul'fijir kafin akira assalatu. Bayan ya idar ya tadani, da k'yar na iya tashi dafe da kai, dan barcin bai isheniba, muryarsa da alamun shima rashin isashshen barcin yace, “time d'in salla yayi”. Idona dake bud'ewa da lumshewa Na kad'a masa alamar amsawa, yay saurin janye nasa saboda wata fad'uwar gaba da tsirgawar wani Abu dayaji lokaci guda tun daga Kansa zuwa yatsan k'afarsa, bai sake magana ba yafice. nikuma nakoma Na sake kwanciyata. 'Dakinsa ya shiga ya tada Sauban dansu tafi massalaci. Babu dad'ewa Sauban ya kammala alwala yafito ya iskeshi a falo yana jiransa, harara ya antayama Sauban, shikuma ya kauda kai gefe yana had'iye dariya (yo daga taimako saiya zama laifi?). Sarki yayi mamakin ganin Sauban, dan yaron bawani zuwa k'asar yakeba saida dalili mai k'arfi, bayan yagama k'ar6ar gaisuwa wajen jama'arsa Galadima da Sauban sukabishi zuwa sashensa. Kasa 6oye mamakinsa yayi, ya kamo hannun Sauban d'in dake d'ayan 6arinsa zaune kamar yanda Galadima yake, “yarona ne yau ak'asarsa ba biki ba ba bikin salla ba?”. Dariya Sauban yayi, yace “Abba nazo gaidakune kawai”. Sarki ya Murmusa yana kallon Galadima, “Galadima kodai akwai abinda ke faruwane kuke 6oyemin?”. Galadima ya d'ago kansa cikin damuwa yace “babu abinda muke 6oyewa ranka ya dad'e. Mahaifin Munaaya ne yay Accident shine suka taho da Sauban d'in”. “mu bamuda muhimmancin da zamu Sani kenan ko?”. “ALLAH ya huci zuciyarka ba haka nake nufiba, bayan barina wajenka jiya nima aka sanarmin, lokacin dana shigo kuma dare yayi”. Ajiyar zuciya mai martaba ya sauke, yace “ALLAH yabashi lafiya, zuwa anjima sai su waziri suje dubashi ai, tana ina ne ita d'iyar tawa?”. “tana nan cikin masarauta”. Jin jina kai kawai Sarki yay bai kuma cewa komaiba, sai zuwa can yacigaba dayima Sauban tanbaya akan jikin Abie, shikuma yana bashi amsa. Galadima dai Na jinsu bai saka bakiba. ************* Saida gari yafara haske ALLAH yabani ikon tashi, dan zazza6in kuma ya sauka, yanzu kuma haka yakemin, da dare yayi zan fara zazza6i, lokacin da gari zai waye saikiji ya sauka. Sai dai ciwon jiki. Saida nayi wanka da ruwa mai zafi sannan nayo alwala, sallar asubahi data kwacemin nayi, Na jawo handbag d'ina danazo da ita Na d'akko wayata, sim card d'ina Na 9ja Na d'akko shima Na saka akan wayar, massage suka turomin Na adadin awannin da suka bani sim card d'in zai d'auka kafin ya cigaba da aiki. ganin haka saina ajiye wayar natashi domin gyara d'akin, ina cikin kakka6e gado idona yakai bisa wayar Galadima. dad'ine ya kamani, koba komai nakira wani d'an gidanmu Na sanar dasu nazo 9ja. Wayar Na d'auka Na saka number Abbana, dan yanzu nafi kwad'aituwa dajin muryarsa fiye da kowa, kodan mafarkai marasa dad'i danakeyi a kansa, Mtn d'insa nafara kira amma a kashe, saina kira glo d'in, shima switch up, ban kawo komai a rainaba na maida kiran kan innarmu, bugu biyu aka d'aga, wani dad'ine ya kamani, cikeda d'oki nace “innarmu I miss you”. Aiyaan daya d'aga wayar yay dariya, aunty ba inna baceba. Nine, Nima Na iya waya yanzun”. Dukda naji dad'in jin muryar d'an uwana, hakan bai hana zuciyata shiga fargaba ba, nace “Aiyaan Kaine? ina innarmu d'in?”. “Tana wanka ne zamuje asibiti wajen Abba”. Da sauri Na dafe k'irji, nace “Asibiti kuma? miya sami Abban?”. “Lah Aunty baki saniba? Ai accident yayi fa, kuma innarmu nata kuka, hakama innaro dasu daddy”. “Aiyaan!!...” nafad'a da k'arfi, kafin nace wani Abu naji an rik'emin hannu ta bayana an zare wayar daga kunnena. Kuma rikicewa nayi, Na juyo da hanzari, cikin kuka naketa fad'in “abbana! Abba da gaske Aiyaan yake yi? Yalla6ai da gaske Abbana yayi accident?”. Wani tausayina yaji ya tsargashi, ya dafa kafad'una, cikin sigar lallashi yace “cool down mana my friend”. “to ka fad'amin da gaskene Abbana yayi accident d'in?”. Rasa mizaice min yayi, sai bin fusakata da idanu yakeyi, ya cije lips nashi yana fad'in “inhar kinason na kaiki ki gansa toki nutsu”. Share hawayena nayi da sauri nace, “to na nutsu muje”. Yaja hancina, a hankali ya furta, “good girl”. Sai ya juya kuma ya fita. Binsa nayi da kallo hawaye na zuba a kumatuna, kenan da gaske Aiyaan yakeyi Abba yayi Accident d'in, “hasbinallahu wa'ni'imal wakil”. Na dafe kaina tareda zama a bakin gadon nacigaba da raira kukana. Shikam yana fita ya dunk'ule hannunsa yana cije lips, yama akayi yabar wayarsa harta d'auka tayi kira dashi, ko kad'an baiso hakaba. Baiso tajiba kai tsaye. Saida naci kukana na gode ALLAH sannan natashi na hau shiryawa, atamfa na saka zani da riga, bawata kwalliya nayi ba, na shafa fauda kawai da lips gloss, turarema kad'an na shafa. ina cikin Neman mayafi ya shigo, kamshin turarensa yasani juyowa na kallesa, sanye yake cikin oxblood d'in shadda, hularsa takalmi agogo duk black, link d'in hannun rigarsa yake sakawa, sai alk'yabba pink da ratsin milk a hannunsa. d'auke kaina nayi naci gaba da neman gyalena a cikin kayan lefena. Baimin magana ba ya tako har inda nake, hannu yasaka a kafad'una ya d'agoni, fuskarsa babu walwala ko kad'an, idonsa akan fuskata, kusancin damukai da juna sosai yasaka numfashinsa ke sauka akan fuskar tawa, janye idona nayi na maida kan design d'in gaban rigarsa, yayinda shikuma ya warware alk'yabbar hannunsa mai k'yau ya sakamin, d'agowa nai muka k'ara had'a idanu, ya jinjina min kansa kawai. Jinai tamkar in fasa ihu, banason saka alk'yabba d'in nan nidai, dan nauyi sukemin, garama wannan batada nauyi gaskiya, dan tamkar riga After dress take, saidai suffar alk'yabba aka mata, kuma tanada kaurin dabaza'a ga jikin mutumba. Hannunsa yakuma d'orawa akan kafad'una ya d'ago hular alk'yabbar dake kwance a baya ya sakamin, ni kaina koba'a fad'aba nasan nayi k'yau, yanzunma baice uffanba ya juya ya fita yana nunamin agogon hannunsa alamar time yana tafiya. Handbag d'ita na d'auka da wayata nabi bayansa, dauriya kawai nakeyi na hana kuka tasirin zubowa. A falo na iskeshi shida Sauban dake zaune a kujera shima cikin manyan kaya, dayake ba sakawa yakeba sainaga ya canjamin, ya kalleni cikin halinsa na tsokana yana fad'in “kaga sarauniya gagara badau ta gobe, takawarki lafiya 6auna mai tafiyar k'asaita.......”. Harar da Galadima ya zuba masa ce ta sakashi gimtse bakinsa yana had'iye dariya. Nidai banma tankaba, dan yau zuciyata babu dad'i. Galadima ne yay gaba mukabi bayansa, tunda muka fito hadimansa suke zubewa gaishemu, Sauban kawai ke amsa musu, shikam Galadima saidai d'aga hannu, Niko ko kallonsuma banayi. Hakan yasa suka fahimci har yanzu akwai matsala kenan, dansu bama Susan munzo nida Sauban ba. Muna k'ok'arin shiga mota Harun ya iso wajen, gaidashi Sauban yayi, nima na gaidashi, ganin ni da Galadima kowa fuska a tamke sai abin yabashi mamaki, hannun Galadima ya kama suka koma gefe. Nikuma da Sauban muka shiga mota. “Sameer babu fad'a miya kawo gaba?”. Murmushi Galadima yayi, ya cije lips nashi kad'an yana kallon Harun, “bazaka ganeba Harun, na iske abinda ya dagula lissafinane kawai, naga kiranka jiya, amma ina cikin rud'ani a time d'in shiyyasa ban d'agaba”. “rud'ani? mike faruwa ne?”. “mahaifin munaya ne yay Accident, a time d'in ina hospital wajensa”. “ya salam, ya jikin nasa to?”. “Alhmdllh, zamuje canne bayan mun gaida jama'ar gidan”. “ok bara na k'arasa abinda zanyi kafin Ku fito saimuje”. Kai kawai Galadima ya jinjina masa. Bud'e masa gefena akayi ya shigo, yad'an kalleni, kamar zaiyi magana saikuma yayi shiru. Sashen mama Fulani muka fara Isa, amma sai aka sanar mana tasha maganin mura ta kwanta, daga nan muka nufi sashen matan Sarki, inda yafi ko ina k'awa da ado a gidan kenan. Mun sami tarba ta musamman ga Uwar gidansa, nidai matarnan tana k'aunata na lura, kuma tafi sakarma Galadima fiye da kowa a Matan sarki, tanada kirki sosai, haka taita jan Sauban a jikinta, nakula suma sunfi sakewa da ita. Sosai ta nuna damuwarta akan Accident d'in mahaifina da Galadima ya sanar mata, taita jinjina maganar tana lallashina da jerama Abba addu'ar tashi cikin k'oshin lafiya. Tasa aka kawo mana break fast wai saimun karya anan, Sauban ne kawai yaci, amma Galadima cewa yay ya k'oshi, nima nace bazan iya ciba. dan burina kawai naga mahaifina, gaisuwarma duk akan k'aya nake. Shima Sauban d'in bai wani ci abun kirkiba yace ya k'oshi, mun fito muka shiga sauran sassan, amma ba ko inaba. Sauban da harun sun tafi a mota d'aya, nikuma ni da Galadima. Sai motar dogaran Galadima guda biyu, sai kuma kuyangi hud'u da Uwargidan sarki gimbiya Zulfah tahad'oni dasu, wai kafin mu dawo nima a turamin bayina da zasu ke kula dani, ni dai da to kawai na amsa, Galadima kam baima ce uffanba. Babu mai magana a cikinmu daga ni harshi, sai saukar ajiyar zuciyata da share kwalla time to time danakeyi. ............................................ Innarmu na fitowa daga bayi Aiyaan ya sanar mata na kira, da mamaki tace masa kodai Munubiya ce?”. “wlhy Innarmu aunty Munaya ce, kuma batasan Abba bashida lafiya ba”. “ka sanar mata ne?”. tafad'a a rikice. “eh innarmu na sanar mata, kumafa naji tana kuka”. “innalillahi Aiyaan wayace ka sanar mata? da wace Number ta kira?”. Tayi maganar tamkar zata make Aiyaan. Runtse idanu yayi yana k'ank'ame jiki saboda tsoro. innarmu dukta rikice, tasan su Munaya da shiga Rud'ani akan Abu, yanzu haka tana cikin damuwar Munubiya itama, dan jikinta yakuma janga6ewa, ga laulayi ga wannan damuwar Abban. K'ok'arin kiran Number tashigayi danta kwantarmin da hankaki amma sai tak'i shiga. Har suka gama shirin asibiti wayar bata shigaba. Koda suna mota taita gwadawa. A asibitin suka had'u da mama Rabi'a suma sunje, ganin innarmu a cikin damuwa yasata k'ok'arin fara kwantarma 'Yar uwarta da hankali. Innarmu ta sanar mata kato6arar da Aiyaan yayi. “to Yaya ko su Munaya sunzo k'asarne?”. Anya kuwa Rabi'a, naga jiya mijinta na nan amma baiyi maganar zata zoba”. “ito da wannan dan wanann, amma ai bama fidda raiba”. “hakane”. cewar innarmu. Babu dad'ewa da zuwansu saiga gwaggon Haleematu da matan k'annen ta sunzo duba Abba, (dayake har yau bata dawoba ita). k'in gaisawa tayi da innarmu da mamansu yaa hameed, innarmu bata damuba, amma mamansu yaa hameed saida taja tsuka, babu dai Wanda ya tanka. Sukuma suka shiga suka ga Abban, dayake yau ana barin na jikinsa zuwa su duba shi. Koda suka fito harda kuka takeyi, matan k'aninta suka tafi amma ita saita zauna, kaf 'yan gidanmu babu Wanda yace mata danmi, kowama tasa ta isheshi aransa. ★★★★★ Tunda motocinmj suka shigo harabar asibitin sai kallo ya koma sama, 'yan gidanmu dakeda yak'in Galadima ne kowa tsumayen fitowarsa yakeyi, sauran jama'a kuma da 'yan dubiya son ganin wad'anda zasu fito sukeyi. Sai da aka bud'e mana sannan muka fito, suma su Harun duk sun fito. Su yaa Hameed suka taho garemu sunama Galadima sannu da zuwa, cikeda kulawa yake amsa musu. Kowannensu fuskarsa ta nuna farin cikin ganina, yayinda nikuma naketa faman zirar da hawaye. Cikin d'okin ganina Fauziyya tazo ta kama hannuna itada Safara'u, saina rungumesu na fashe da kuka, kukana ya karyar musu da zuciya suma suka fara, sauran 'yan uwanama duk suka taso gareni, dama duk sun zo, ni kad'aice wadda nake nesa. Saida baba k'arami yamana magana sannan suka sakeni, na matsa ina sharar kwalla na gaida iyayena, Munubiya ce kawai ban ganiba, ina share hawaye na tambayi tana ina?. Aunty khalisat tace “sunje ganin doctor itada yaa marwan, dan batajin dad'i itama”. Kaina kawai na jinjina, na k'arasa gabansu innarmu na durk'usa ina gaishesu, duk sun amsamin cikeda kulawa, da tambayata ya hanya?, nace “Alhmdllh”. Matan gidanmu kowacce kallona take da mamakin canjawata a cikin wata 1 kacal. Na katse musu tunani da tambayar d'akin da Abba yake. Aunty Ramlah ce taja hannuna muka shiga corridor d'in dazai sadamu da d'akin da Galadima yasa aka canjama Abba. A ciki na iske Galadima da Harun da Sauban, sai doctor da yaa Shafi'u yaa Hameed. Takun takalmanmu yasakasu juyowa suka kallemu, na zare hannuna daga na aunty ramlah ina toshe baki saboda kukan dake Neman kufcenin, taka wa nayi gaban gadon da Abba yake, na durk'ushe ina sakin kuka mai tsuma rai da zuciyar mai saurarona, tare da kife kaina jikin gadon. Kukana babu zuciyar Wanda bai karya ba, Galadima ya tako a hankali inda nake, hannayensa biyu ya saka ya kamoni na mik'e tsaye, fad'awa nayi saman k'irjinsa na kuma sakin wani sabon kukan. Bashida za6in daya wuce kar6ata, dan haka shima saiya saka hannayensa ya zagaye bayana dasu, ya d'ora ha6arsa saman kaina yana lumshe idanu da cije lips. kad'an-kad'an yake buga bayana alamar lallashi. d'ai-d'ai su yaa Hameed suka zare jikinsu suka fice daga d'akin, aka barmu mu kad'ai sai Aunty Ramlah da muka birgeta, itama ganin sun fita saita fice taja mana k'ofar. Munkai tsawon lokaci ahaka, saida na tsagaita da kukan sannan Galadima ya d'ago kaina daga jikinsa, hannunsa yasa yana gogemin hawayen fuskata, amma ya gaza cewa komai. sai girgiza min kai kawai yakeyi. Ajiyar zuciya kawai nake saukewa a jere, da hannu ya nunamin hanyar fita. Banyi musuba nabud'e k'ofar muka fito, ina gaba yana bina a baya. tafiya nake a hankali saboda juwar dake Neman fara hajijiya dani, burina kawai nakai inda 'yan gidanmu suke zaune akan kujeru nima na samu na zauna. Muna gab da k'arasawa wajen na dafe kaina, sai nayi baya luuuuuu. Da sauri Galadima dake bayanta ya tareta ta fad'o jikinsa, gaba d'aya 'yan gidanmu da mutanen wajen suka mik'e tsaye cikin ambaton sunan ALLAH. sosai Galadima ya tallafota jikinsa, yayinda wasu Nurses biyu suka iso da gudu domin kar6ar Munayar. Amma saiya hanasu yana daka musu tsawa da ambatar su kira Doctor. Basu ba kowama a wajen saida tsawarsa ta rikitashi....................✍🏼 *_Comments d'inku shike k'aramin k'arfin guywar rububutun nan wlhy, amma da tuni na ajiye saina samu lafiya🤦🏻‍♀, amma yanda kuke k'ok'arin Comments sai bana iya barinku banyiba😃, ina godiya kwarai da gaske, I love you all🥰🥰🥰🥰🥰🤝🏻👍🏻❤_* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_* [7/3, 9:54 AM] Aysha Galadima: *_Typing📲_* *_Haske writer's asso...._*💡 *_♦RAINA KAMA......♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻 ~Book 2~ 👉🏻7⃣ ................Gaba d'aya ya rikice ya rikita Nurses d'in da jama'ar wajen, cak ya d'auki Munaya, gadonma da aka kawo masa domin d'orata ko kallonsa bai yiba. Wani d'aki suka nuna masa ya shiga da ita. Da sassarfa doctor dazai duba munayar ya iso, dan dogaran Galadima tasoshi gaba sukaje sukayo. Kai tsaye Galadima yace baya buk'atar namiji mace yakeso ta duba masa matarsa. Hak'uri doctor d'in ya bashi, sannan yakira wata likita mace mai suna doctor Farida. Isowarta yasaka Galadima da yay bake-bake a k'ofar bata hanya ta shiga. Duk yanda taso yabata waje tayi aikinta yak'i, gashi duk yabi yagama rikitata da tsawarsa. Doctor d'in da Galadima ya hana ya duba Munaya ne ya matsa kusada su harun yana fad'in “dan ALLAH sir Ku lalla6a yalla6ai ya fito danta samu damar aikinta, wlhy dukya rikitata”. Murmushi Nuren da isowarsa kenan asibitin aka masa bayani shima yayi, suma su harun duk murmushi sukayi. Nuren ya kalli baba k'arami yana murmushi, “Abbanmu inharfa bakai kamasa magana ba bawai zai fito baneba”. Shikansa baba k'arami murmushin yakeyi, koba komai hankalinsu Yakuma kwanciya da zaman 'yarsu inda suke tunanin anfi k'arfinta. Bayan doctor yabi zuwa d'akin, Galadima dake zaune, kan Munaya na bisa cinyarsa sai murza tafin hannunta yakeyi wai kozata farfad'o, yayinda doctor Farida ke k'ok'arin lik'a mata oxygen ita kuma”. Shima baba k'arami da k'yar ya lalla6ashi ya fito. Tsawon lokaci doctor Farida tana ciki bata fitoba. Galadima dukya damu, danma ankawo masa kujera ya zauna, amma sai jan tsuka yakeyi time to time. Hankalin 'yan gidansu Munaya ma duk a tashe yake, jiran fitowar doctor Farida kawai akeyi dan aji mike damun munayar. Innarsu Munaya kam gefe ta koma tana sharar kwalla, itakam batasan yazata misalta wannan tsakaniba, miji da 'ya'ya duk babu lafiya, Munubiya ma fa sunacan ana k'ara mata ruwa. Fitowar doctor Farida yasaka kowa mik'ewa anason jin bayani, Galadima dai yana daga zaune ya zuba mata idanu shima. Doctor Farida tace su kwantar da hankalinsu ta farfad'o, amma tamata allurar barci, yanzu tanason ayo gwajin jinin Munayar data d'iba. Galadima ya lumshe ido yana ambatar “Alhmdllh” akan la66ansa. Sauban ne ya kar6a suka tafi shida Sarkin mota lab d'in. Dr Farida ta kalli Galadima tana murmushi, “ranka ya dad'e zaka iya Shiga ka ganta yanzun”. Nuren ya kalli Galadima ya jinjina masa kai alamar yaje. Saida yaja wasu seconds sannan yamik'e cikin takun nan nasa na k'asaita da izza, duk idon jama'ar wajen akansa yake, yana birge kowa. d'akin ya tura ya shiga, ya taka har gaban gadon da Munaya ke kwance, idanu ya tsura mata, tayi wani fayau da ita, ya jawo kujerar dake wajan ya zauna, har yanzu idonsa na kanta, cikin cije lips da lumshe idanu ya d'ora hannunsa bisa sumar kanta da d'ankwalinta ya zame ta fito, saikuma yasaka d'ayan hannunsa ya shafi kumatunta, a kan la66ansa ya furta “sorry my friend, ALLAH yana tare da masu hak'uri kinji”. Daga haka bai sake cewa komaiba, ya janye hannunsa daga kanta ya mik'e ya fito. A k'ofar d'akin ya iske Doctor Farida tsaye, kallonta yayi cikin maganarnar tasa mai kama da an masa tilas yace “zata iya kaiwa wane lokaci bata farkaba?”. “Ranka ya dad'e inaga daganan zuwa kamar awa d'aya”. Kansa ya jinjina mata, bai sake magana ba yanufi d'akin da Abba ke kwance. ya Tatar da doctor d'in dake kula da Abban a d'akin. Da sauri doctor yabashi kujera ya zauna, k'afa d'aya kan d'aya ya d'ora ya Ciro waya a aljihu yana danne-danne. batare da ya kalli doctor ba yace, “kunyi gyaran karayar?”. Doctor yace, “eh ranka ya dad'e duk an gyara, saidai na hak'ark'arinsa yaso kawo matsala, amma Alhmdllh komai ya dai-daita”. “humyim, maganar bayanan danace a tattara minfa?”. “shima komai ready ranka ya dad'e ”. “o right, insha ALLAH zuwa jibi nakeson mu tafi, amma wai har yanzu bai ta6a farfad'owa bane?”. “ai ba'a sume yakeba, allurar damuke masace kawai takesakasa yawan barci”. d'ago ido Galadima yayi yana kallon doctor d'in, yace “amma danme ake masa?”. “ itace ke taimaka masa wajen rage masa rad'ad'in ciwukan, dan maganar gaskiya yana cikin matsanancin ciwo”. Cije lips Galadima yayi kawai, yace “ALLAH ya bashi lafiya”. “amin ya rabbi”. ‘cewar doctor. Daga haka suka fito shida doctor d'in. Inda Harun yake Galadima ya nufa, “brother yau ba zakaje aikiba kenan?”. Kallon agogon hannunsa Harun yayi, sannan ya kalli Galadima, “ka rikitamu ne ranka ya dad'e shiyyasa ban kula time ya tafi hakaba”. Murmushi kawai Galadima yayi amma baice komaiba. Harun yay musu sallama ya fita da nufin zuwa anjima idan yatashi aiki zai dawo. Su yaa Hameed sukai masa godiya da fatan alkairi sannan yatafi. Daddy ya kalli su yaa Hameed d'in yace ai kuma da tafiyar kukayi, karku makara wajen aiki”. A ladabce suka amsa masa da to, suna shirin barin wajenne saiga motocin su waziri sun shigo, dole su yaa hameed suka dakata. Waziri ne da matawalle, sai Garkuwa da baraya, sai kuma wasu manya-manyan 'yan majisar Sarki. dogarai duksun kasa sun tsare, wasuma zato suke sarkinne yazo da kansa. Su daddy ne suka musu iso har d'akin da Abba yake kwance, sosoi suka nuna tausayawarsu gareshi, sunja doguwar addu'ar samun lafiya da fatan alkairi ga Abba. Sannan suka Isar da sak'on Sarki. Sun d'an jima a d'akin suka fito da nufin tafiya, a dai-dai time d'inne kuma doctor Farida ta iso gaban Galadima cikeda sassarfa. Bakinta a washe tamkar gonar auduga. Wani dogari Na k'ok'arin dakatar da ita Galadima ya d'aga masa hannu alamar ya barta tazo. Cikin girmamawa doctor Farida tace “wannan asibiti da dukkan jama'ar cikinsa suna taya masarautar gagara badau murnar samun k'aruwa daga jikin gimbiya Munaya, insha ALLAH nanda watanni 7 dawasu satittika zata zama uwa, ma'ana tana d'auke da cikin wata 1 da sati uku”. Atare dogarai suka d'auki kabbara, Galadima dake tsaye baki bud'e cikin tsantsar mamaki ya kafe doctor Farida da idanu, sai kawai yashiga zame agogon hannunsa mai masifar tsada da k'yau ya mik'ama doctor Farida. Sauban yazo ya rungumesa, hakama matawalle. 'Yan gidansu Munaya sai suka koma 'yan kallo kawai, amma bakin kowa yakasa rufuwa. Doctor Farida ta kalli Galadima cikin mamaki da al'ajabi, “ranka ya dad'e ni Na cancanci wannan agogon mai d'unbin tsada kuwa?”. Wani murmushin Daba a cika gani Galadima yayiba ya saki, ya gyara tsayuwarsa yana fad'in “idan duk abinda na mallaka a duniya kike buk'ata zan baki shi, saboda wannan shine albishir Na farko da aka ta6amin Na farinciki a rayuwata, kifad'i dukkan abinda kike buk'ata inhar baifi k'arfina ba kafin nabar asibitinnan za'a kawo miki shi”. Kanta ta shiga girgizawa, kafin ta d'aga agogon ga mutane su gani. Mamaki ya cika kashe matan gidansu Munaya hassada da al'ajabi ya cika zukatansu, tunma ba'a haifi cikinba Galadima yake wannan rawar kan inaga an haifoshi?, Kansu bai kuma kwanceba saida sukaji waziri da baraya Na sanarda tasu k'yautar ga doctor Farida, hakama matawalle da Nuren. Doctor Farida fa ta rikice, itakam yau taga farar rana, (🙄idan ta ALLAH ake niya kamata abama wad'annan k'yaututtuka ma😏). Nuren da matawalle suka hau rabon kud'i a asibitin, tamkar basu San ciwonsu ba. Waziri kam d'akin da Munaya take kwance aka musu rakkiya, sun mata addu'a kafin su fito, kowa bakinsa a washe, wasukam ta cikin Na ciki kawai😳🤭. Kafin kace mi labari yagama zagaye asibitin, gidan Sarki kam kafin su waziri su Isa labarin cikin Munaya yaje. hakama Sauban ya kira su Momma ya guntsa musu, Momma saida tayi sujudar shukur. Abie bakinsa yakasa rufuwa, kamar daga sama sukaji yace “ALLAH ya inganta”. Dukda a hankali yayi maganar hakan bai hanasu ganin motsawar la66ansa ba, Khaleel dake kusa dashi yace “Lah Abie yayi magana Momma!!”. ba momma ba hatta da jakadiya sakin kwanon hannunta tayi ta waigo tana kallon Abie. Aunty Mimi ta tura laptop d'in gabanta tafad'o, hakama Samha wuntsilowa tayi daga kujerar datake zaune tayo inda gadon Abie yake. Gaba d'aya suka rufu akan abie, kowa yanason sanin gaskiyar batun Khaleel, murmushi Abie yamusu yana jinjina kai alamar gaskiyane, sannan a hankali yakuma furta “da gaske Khaleel yake”. Ai yau babu kunya Momma ta rungume Abie a gabansu aunty Mimi ta fashe da kuka mai ban tausayi. Aunty Mimi ta had'a momma da Abie d'in ta rungume itama. Jikin Samha har 6ari yakeyi takira Number Galadima ta Nigeria. Ya rako su waziri da zasu tafi kiran Samha ya shigo, bai d'auka ba, itakuma bata gaji da kira ba. Saida su waziri suka wuce sannan yaciro wayar a aljihunsa cikeda haushin wanene mai nacinnan. yana dubawa yaga Samha Ce. Murmushi yayi kawai sannan ya kirata da kansa, bugu d'aya Samha ta d'aga, kuka kawai ta fashe masa da shi, zuciyar Galadima tashiga tsitstsinkewa. tsawa ya daka mata yana tambayar lafiya?. Share hawayenta tayi, murya Na rawa tace, “Uncle Sam wlhy Abie yayi magana, yanzun nan da Uncle Sauban ya kira yace aunty gimbiya nada ciki sai Abie yace ALLAH ya inganta”.. Galadima ya ciro wayar a kunnensa ya kuma kallon number, tunaninsa wasune kawai keson masa yawo da hankali, ganin dai da gaske number Samha d'in ce saiya maida a kunnen, cikin sanyi murya ya kira ainahin sunan Samha, “Zeenah! banason wasan banza kema kin sani”. “wlhy Uncle ba wasa nakeba, ga Momma ma kaji awajenta”. Kafin yace wani Abu yaji muryar Momma namasa sallama, yanayin muryarta yasakashi lumshe idanunsa. Momma tace, “Muh'd! Yau ranace dabazamu manta da itaba a tarihinmu, k'yautar abinda kud'i baya saya, ALLAH kuma yabama takawa damar magana, narasa yanda zan musalta farin cikina Muh'd”. Wasu hawayene suka gangaro a kumatun Galadima, ga murmushi yak'i barin fuskarsa, cikin nutsatstsiyar muryarsa yace “Momma ko yanzu Ubangiji ya d'auki raina yagama min komai, Momma mizanyi duniya tasan ina cikin tsantsar farincikin da tunda nazo duniya ban ta6a riska ba?”. Dariya momma tayi, tace “godiyar ALLAH ta wadatar da komai Muh'd, lallai yarona zai zama baba”. Galadima yayi dariya yana goge hawayen fuskarsa, “Momma bama Abie wayarnan”. Cikin tsokana tace, “nawa zaka biya? kasan mu yanzu komai Na kud'ine”. Sosai yasaka dariya, har jerarrun hak'oransa Na bayyana. Dogaransa duk sun saki baki suna kallonsa, duk da bajin maganar da yake sukeba, tunda suke da shi basu ta6a ganin yana dariya makamanciyar wannan ba, Sauban kan ai hotuna yaketa masa bai saniba. “shikenan Momma, inhar baki had'ani da Abie ba kema kuwa d'iyarki bazata dawo India ba ashe?”. “a'a miyay zafi? indai takawa ne gashi”. Nanma dariyar Galadima yayi, Abie da tun d'azu yaketa murmushi shima saboda a Hans free momma tasaka wayar duk sunaji, a hankali yace Daddyn Unborn!”. Galadima baiji mi Abie ya fad'a ba, amma tabbas yana jiyo alamun motsi, da sauri yace, “Momma video call please ”. Mota ya bud'e ya shiga, Sauban ma ya k'araso dan kuma taya d'an uwansa murnar k'aruwar daya samu. tunda aka bayyana maganar cikin Galadima bai samu Kansa ba, balle su ke6e. Motar yashigo shima, ganin video call Galadima ya had'a dasu Momma saiya matso kusada shi sosai yana d'aga musu hannu. Momma tace, “ho autana ina ka shige wai?”. “momma ina zaki ganni nazama Abban Unborn”. Dariya sosai suka sanya, Galadima ya rankwashi kansa. Wayar aka saka kusada Abie sosai, a hankali yace, “lallai wad'annan iyaye akwai zumud'i dai”. Basuji miya fad'aba. Amma sungane ta hanyar motsin la66ansa. cikin zaro ido Sauban yace “Abie!!”. Sai kawai ya rungume Galadima ya fashe da kukan farin ciki. Humm masu karatu, nabama kowa damar k'iyasta wannan farin cikin a zuciyarsa shima😁😉. ★*★★*★*★★*★*★★*★ A lokacin da Galadima suke can suna waya dasu Momma Munaya ta farka, doctor Farida ta cire mata k'arin ruwan danya k'are. Ta kalli doctor Farida tace “doctor Abbana fa? karki cemin dai Abbana ya mutu Dan ALLAH?”. Hannunta doctor Farida ta rik'o, fuskarta d'auke da murmushi tace, “gimbiyarmu Abbanki nanan da ransa, insha ALLAH kuma zai tashi, kedai kici gaba da masa addu'a kinji”. Kai Munaya ta jinjina mata, sannan tace, “to zanyi fitsari”. Doctor Farida ta amsa da to, da kanta ta taimakama Munaya tashiga bayi, fitowa tayi tabata waje, saida ta gama sannan ta kuma taimaka mata ta fito. “doctor 'yan gidanmu fa?”. Murmushi Dr Farida tayi, cikin tsokana tace, “Gimbiya Galadima yakamata ki fara tambaya ai”. Murmushi Kawai Munaya tayi, amma batace komaiba, Dr Farida tace “to bara Na musu magana”. Babu dad'ewa saiga 'yan gidanmu nata shigowa, yanda kowanne fuskarsa ke a washe sai suka bani mamaki, nakasa hak'uri nace, “Abba ne ya tashi? kuke farin ciki haka?”. “shima insha ALLAH zai tashi 'Yar albarka”. Cewar innaro tana dariya. Ni duk sun kuma d'auremin kai da addu'ar da sukeyi suna fad'in ALLAH ya inganta. Mamansu Fauziyya tace minakeso akawo min naci. Nace, “banajin yunwa mama, ni sonake ma Na kuma ganin Abba”.. “karki damu, Abba yana barci ne, kedai kisamu kici abinci babynmu yak'ara k'ato kafin ki haifo mana”. Ban fahimci maganar ta Fiddausi ba, Dan naga awajen akwai masu ciki da yawa, aunty Ramlah, aunty Khaleesat, aunty Hauwa'u, Siyama, Zarah, aunty Raihana duk cikinsu ya tsufa, haihuwa yau ko gobe. Na kalli innarmu dake tsaye batace komaiba, murmushi namata, itama saita mayarmin, nace, “wai har yanzu Munuhiya ba a cire mata ruwanba?”. Mama Rabi'a tabani amsa da cewar “an cire, barci takeyi”. Cikin marairaicewar murya nace “ALLAH sarki Sweetheart d'ina, ALLAH yabaki lafiya”. Duk suka amsa da amin. Doctor Farida tashigo tana sanar musu ga Galadima nan zai shigo. 'Yar rige-rigen fita iyayena suka farayi, kowa yana jin nauyin suruki ya shigo ya iskeshi, ni dariyama suka bani, nayi murmushi ina komawa Na kwanta. Saida suka fita kaf sannan nafara jiyo takun takalminsa. Idanu Na lumshe kamar mai barci. Tunda ya shigo idonsa Na kaina, yacigaba da takowa gaban gadon, duk tunaninsa barcin gaske nakeyi, maimakon ya zauna saiya dafa gadon ya rankwafo kaina, da sauri da sauri zuciyata tafara bugu saboda kusantoni da ya keyi, fuskarsa daf da tawa tamkar zai had'e bakinmu, mikuma ya tuna saiya janye ya maida saitin goshina ya manna min kisses guda biyu a goshi da saman hanci. Cikeda mamaki Na waro manyan idanuna, kallon ido cikin ido mukaima juna, ya d'aga min gira d'aya. Saurin kauda idanuna nayi gefe. Shikuma yaja kujera ya zauna dab da fuskata yana murmushi. Munja wasu seconds sannan yasaka hannunsa bisa kumatuna ya juyo da face d'ina inda yake, kin bud'e idona nayi Na kallesa, bai damuba yace “yalla6iya dama haka kike da saurin cafke Abu?”. Babu shiri Na waro idanuna kansa, nace “yalla6ai mina cafke?”. Idanunsa ya d'an jujjuya alamar tunani, saikuma ya kalleni, har yanzu hannunsa Na tallafe da fuskata, yace “uhuumm mima kika cafke? Na manta ma”. Ya k'are maganar da d'age kafad'a yana ta6e baki. d'an hararsa nayi ina tura baki, mutuminnan ya iya rainin wayo. Yanzunma murmushin yamin, saikuma ya d'ora hannunsa saman shafaffen cikina mai kama da babu ko kayan ciki balle kayi tunanin akwai mutum. Da sauri Na rik'e hannunsa ina fad'in “ yalla6ai lafiya kuwa?”. Cikin basarwa yace “itace ta kawo haka, bakimin murna ba”. Nace, “Murna kuma? tami?”. Cikin d'age gira d'aya yace “Muhammad Sameer Saifudden yazam pah-pah”. d'auremin kai maganarsa tayi, Na yunk'ura a hankali zan tashi, mik'ewa yayi ya taimakamin Na zauna yana fad'in “yi da kula karkima jama'ar gari 6arna, dan akwai sarkinsu anan”. Waige-waige Na farayi, nidai banga kowa ba bayan mu biyun dake zaune, saina d'auka da kansa yake, na d'an ta6e bakina kawai. Shima saiya ta6e bakin yana komawa ya zauna. kusan mintuna biyu duk mukai shiru. Zuwa can nace, “nikam dai na dawo normal, kace musu su sallameni kawai”. Batare daya d'agoba yace “nafi buk'atar hakan, mi kikeso Sameer yamiki k'yauta da shi?”. “k'yauta kuma? akanmi?”. “Abie ya fara magana”. Babu shiri na wuntsilo daga gadon ina fad'in da gaske?”. Da sauri Galadima ya ruk'oni, jikinsa har rawa yakeyi, jina nai kawai bisa cinyarsa. “yalla6ai!”. nafad'a cikin zaro idanu, sai kuma na hau waige-waigen kar wanifa ya ganmu. Daf yamatso da fuskarsa kusada tawa, numfashin junanmu na sauka bisa fuskokinmu, na marairaice fuska tamkar zanyi kuka, yanda yasaka idonsa cikin nawa tsigar jikina dukta mimmik'e, jikina har tsuma yakeyi, amma tsabar muguntarsa yak'i ya janye, yakuma hanani damar da zan janye nawa. A hankali tamkar mai rad'a, yace “ki kula, domin abin cikin kwan yafi kwan dad'i my friend ”. ‘ ya k'are maganar da d'age min gira sama’. Lumshe idanuna nayi kozan sami sassaucin daina ganin abinda ke yawo a idanun Galadima. hakan yabashi damar d'ora bakinsa akan nawa, shima ya lumshe nasa idanun. Babu shiri na bud'e nawa saboda tsorata, ni Munaya mike damun wannan bawa yau? duk yanda naso kwatar kaina hakan ya gagara, dole na sallama yayi iya yinsa sannan ya sakeni. Zumbur na mik'e daga jikinsa ina sharar kwallar takaici, shima saiya mik'e yana karkad'amin d'anyatsa, ya matso daf dani a hankali ya furta “k'yautar farko kenan”. juyawa yay yafita yana murmushi da gyara zaman hular kansa. Na bishi da kallo ina maimaita zancensa na k'arshe, “k'yautar farko? Kamar ya k'yautar farko? mi yake nufi to?”. ban kai ga samo amsarba doctor Farida ta shigo tana murmushi. “ginbiyarmu yalla6ai yace abaki sallama kuje gida ki huta gaba d'aya”. Saboda Banason tafiyar, sai nace doctor jikina bai gama sakiba, ki Ce masa sai dare zaku sallameni kawai”. 'Yar dariya tayi, ta nunamin Galadima dake bakin k'ofa tsaye ya hard'e hannaye a k'irji. Baki na tunzuro gaba saboda borin kunya. Shikuma ya janye idanunsa yana ta6e baki. Doctor Farida ta bamu sallama, na d'auki alk'yabbata na saka, tareda d'aukar handbag d'ita, sai wani ciccin Magani nakeyi, shi da nakeyi danshi yawani share tamkar bai gane da shi nakeyi ba. Jinai ya sak'alo hannunsa cikin nawa, na kalleshi da sauri, saiya kannemin ido d'aya. Ja nayi na tsaya, shima saiya tsaya, ga mutane duk sun zubo mana idanu, kuma har 'yan gidanmu. tamkar zan fasa ihu nace, “yalla6ai ni dai wlhy ka sakeni, kai bakajin kunyar su innarmu ma?”. Yace “kai ALLAH dai ya shiryeka Sameer, yalla6iya Sameer najin kunyar su Innarmu fa, sai dai kuma yana gudun amasa gangancin abin cikin kwan ne”. Kallonsa nayi, “ wai minene wannan abin cikin kwan daka ishi mutane da fad'a”. Ya d'an d'ora hannunsa saman bakinsa alamar mamaki, “yamzu nan bakisan abin cikin kwan ba friend? Lallai news ya wuce dake, ina tayaki jaje kam”. Kuma kullemin kai yayi a duhu. Ita dai doctor Farida dake bayanmu sai kuma birgeta muke da bata dariyar salon namu. Mutane kam dake kallonmu tunaninsu koda doctor Farida muke magana, Dan bazaka ta6a d'auka Galadima ya iya zaro magana hakaba. nikaina mamakin dama yana magana mai tsayi irin haka nakeyi, narasa miya d'abbak'a wannan farin cikin nasa na yau?, duk da bawai yanata dariya baneba, fuskarsa nanan yanda take babu walwala, sai dai yau akwai sakewa tattare dashi, kuma yakan yawaita murmushi bakamar ko yausheba. Nidai nace, “dan ALLAH yalla6ai kayi hak'uri, wlhy bazan iya zuwa gabansu baba k'arami ahakaba”. Baice komaiba ya saki hannuna, amma munci gaba da tafiya kafad'a da kafad'a dashi. Wata kuyanga cikin kuyangin da uwargidan Sarki ta had'omu tai saurin tasowa ta kar6i bag d'in hannuna, ban musaba na mik'a mata, mutane sai gaishini sukeyi, nidai kunyama ta isheni, Dan wasu sun girmemin. Mun Isa gaban 'yan gidanmu, kowa ya taso yana k'ara min sannu da jiki, nidai sai ce musu make na samu sauk'i. d'akin da Abba yake muka shiga, hawaye suka cikamin idanu, Galadima ya ruk'o min hannu, kallonsa nayi saiya girgiza min kai alamar kar nayi. Bance komaiba na janye idanuna, sannan na k'arasa gaban gadon nafara tofa masa addu'oi, shima Galadima ya matso ya tayani, daganan fitowa mukayi, Galadima yakuma gargad'ar police d'in akan su kula sosai, inhar wata matsala ta biyo baya to suyi kuka da Kansu. Cikin girmamawa suka amsa masa da insha ALLAH hakan bazata faruba ma. Ni dai ina wajen 'yan gidanmu, jinake kamar karna tafi wlhy, amma innaro tace kartaji karta gani, nabi mijina naje gida na huta, suma sauran 'yan uwana duk gida zasu tafi hakanan, tunda dai iya k'ok'ari galadima tsaye yake akan komai na abban, dukkan kulawa yasaka ana bashi gwargwadon iko. Nidai sai tunzura baki nake su Fiddausi namin dariya. Muna haka Galadima ya k'araso wajen, cikin girmamawa yace yakamata suma 'yan gidanmu suje gida hakanan su huta, insha ALLAH Abba zai samu kulawa tamkar suna nan. Godiya suka shiga yimasa, innaro nata kwararamasa addu'oin gamawa da rayuwa lafiya, da samun afuwa shima ga mahaifinsa, ta k'are maganar da f'adin “ALLAH ya kawo mana kishiyata ko angona duniya lafiya”. K'asaitaccen murmushi Galadima yayi, a kan la66ansa ya amsa da ammin Granny ”. Daga nan wajen Munubiya muka nufa, suma 'yan gidanmu suka shiga dansu k'ara ganin Abba su tafi. Munubiya na kwance tana barci har yanzu ana k'ara mata ruwa, rungumeta nayi ina hawaye, yayinda Galadima da yaa Marwan suke gaisawa cikin mutunta juna, inajinsu sunama juna Congrat, amma ban fahimci na mineneba. Nace “yaa marwan wai mike damun sweetheart ne haka ta rame?”. Dariya yaa marwan yayi, yace “babynku ne”. “lah yaa marwan kana nufin tanada cikine?”. Kansa ya jinjina min. Cikeda murna na kuma rungume munubiya ina fad'in “ashe na kusa zama mummy”. Galadima ya kauda kai gefe yana murmushi kawai, shina yaa marwan sai k'aramar dariya yakeyi. Da k'yar dai na hak'ura na baro asibitin nan badan nasoba, suma 'yan gidanmu duk sun wuce gida. ***************** A mota sai zun6ire-zun6iren baki nakeyi, saboda haushin banso rabuwa da 'yan uwana ba yanzu, Galadima ya wani shareni. shikam dukya gajine, bai cika wahalar zirga-zirga irin hakaba, gashi dama bawani isashshen barci yasamuba jiya. Batare dana kalleshi ba nace “wai ina yaa Sauban ne?”. Bai d'ago daga latsa wayar dayakeyiba ya bani amsa da “suna tare da Nuren”. Da sauri na kalleshi danjin ya ambaci sunan Wanda nake son Sanin wanene shi?, cikin kwantar da murya nace “yalla6ai wai wanene Nuren? ”. Tambayar tabashi mamaki, amma saiya share ya d'ago muka had'a ido, kowa ya janye cikin basarwa. bai bani amsarba har muka shiga cikin masarautar...................✍🏼 Kuyi manage da wannan sister's🤗. *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻 [7/3, 9:54 AM] Aysha Galadima: *_Typing📲_* *_Haske writer's asso...._*💡 *_♦RAINA KAMA......♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻 ~Book 2~ 👉🏻8⃣ .........Tunda aka bud'e mana muka fito hadimansa sukayo caa akan mu, kowanne k'ok'arin nuna farincikin sa yake ga Galadima. Casuke ALLAH dai ya infanta mana, ranki ya dad'e ALLAH ya saukeki lafiya. Cikin tsantsar farinciki yake amsa musu, murmushi yak'i barin fuskarsa. Nikam zuciyata Ce ta shiga tsitstsinkewa, idan har Na fahimci inda zancensu ya nufa cikine dani kokuma wani keda cikin? Galadima Na kalla, amma saiyamin wani miskilin murmushi yana kauda idonsa, alk'yabbar jikinace kawai taima mutane katanga da ganin zufar data gama jik'emin jiki. Tun a falon farko Na dakatar da kuyangin da damuke tare, handbag d'ita Na kar6a nace suje nagode. cikeda girmamawa suka amsamin suka fita suna min addu'ar k'ara samun lafiya. suna fita na juyo ga Galadima, amma tuni ya shige d'akinsa. handbag d'in Na dungurar saman kujera nabi bayansa, hankalina bazai ta6a kwanciya ba sainaji gaskiyar lamarinnan. Na iske babu kowa a falonsa, Dan haka nashiga bedroom d'insa, ranar farko kenan dazan fara shiga bedroom d'in. babu kowa nanma, sai motsin ruwa dana jiyo a bathroom. Waige-waige nafarayi ina k'arema d'akin kallo, komai ya birgeni a d'akin, sai k'amshin mayen turarensa da ya mannema d'akin. karaf idona ya sauka ga takarda kusada kayan daya cire, mik'ewa nayi Na d'akkota, Na dawo Na zauna. cikin nutsuwata nafara karantawa, nai mugun waro idanu ina fad'in “wlhy impossible, abindama bazai ta6a yuwuwaba kenan” sai kuma Na fashe da kuka. Dai-dai lokacin Galadima ya fito daga bathroom, sanye yake da rigar wanka fara, ahankali ya ringa takowa idonsa a kaina, sai dai fuskarsa a d'aure take tamkar bashine cikin walwala ba a asibiti. Bai k'araso inda nakeba ya tsaya a tsakkiyar d'akin ya cigaba da goge ruwan kansa zuwa fuska hankalinsa kwance. a harzuk'e nayo Kansa ina cigaba da kukana, naja birki a gabansa, da d'anyatsa Na nuna masa takardar, har yanzu kuma kukan nakeyi, nace “wannan cikin a jikin wa ake nufin yake?”. d'auke fuskarsa yayi daga kallona yana wani lumshe idanu, batare daya bani amsa ba ya taka zuwa wajen mirror, cikeda izza yace “sunanwa kika gani a jikin takardar?”. Da sauri Na ruk'o bathtub d'in jikinsa, cak ya tsaya, murmushin gefen baki yayi, saikuma ya kuma d'aure fuska sannan ya juyo yana fuskanta ta, inda Na rik'e ya kalla yana fad'in “kona kwance miki igiyar ne?”. Sakin rigar nai da sauri ina share kwalla, cike da tsiwa nace “aini ba 'Yar iska bace ba”. Shikuma cikin gatse yace, “amma kikayi ciki?”. Hannu na aza akaina nakuma fashewa da kuka, “wlhy koma mi za'ayi sai dai ayi bazan haifi wannan cikinba, aiba haka mukayi da kaiba, kawai daga auren Contract sai aganni da ciki? ka tabbatar saina zubar dashi yau d'innan, dan bazanje gidan miji da agola ba, ba kuma zan haifi d'ana Na bari gidan wani ba matar uba ta kashemin”. Da k'yar ya iya danne dariyar dake k'ok'arin kufce masa, yay saurin cafko hannuna saboda zaburar danayi xan fita. “k yi ahankali karkimin asarar abin cikin kwan fa”. Wani bak'in cikine ya turnuk'omin, Na harzuk'o masa da masifa amma saiya wani tsare gida, dolena Na had'iye maganar nacigaba da kukana. Shikuma ya watsa mini harara yana jan tagwayen tsaki, sannan yaja da baya yakoma bakin gadonsa ya zauna. Durk'ushewa nayi saman carpet d'in gaban gadon Na fashe da kuka mai tsuma rai ina rok'onsa. “dan girman ALLAH ka kaini a zubda cikinnan, kafa tuna da Girman alk'awari, a auren yarjejeniyarmu babu wannan, aikin had'in guywa ka nemeni muyi, kaifa ka tabbatarmin da zaka kasance mai cika alk'awari aranda Na kwana biyu a masarautarnan, miyasa yanzu zaka kasa cikawa? kacemin a matsayin kuskure abinda yafaru ranar ya faru, dukda zuciyata Na cike da bak'in cikin faruwar tasa haka Na hak'ura Na danne Na yarda dakai, ka taimakeni mu rabu cikin salama batareda d'ayanmu ya cutuba, karka k'ask'antar da rayuwata saboda kana ganina mace kuma talaka wadda take k'ark'ashin mulkinka, kamin adalci Dan girman ALLAH Muhammad Sameer”. Tunda munaya tafara magana Galadima ya tsaya daga k'ok'arin fara shafa man da yakeyi, idanunsa ya tsura mata, dukkan maganarta ta shigesa, dukda yana k'aunar cikin dake jikinta shima baiso gudan jininsa yazo ta wannan hanyar da babu soyayya tsakaninsa da mahaifiyar d'ansa ba, sai dai wayonsa ko dabararsa bazai ta6a canja k'addararsu ba shi da ita. da k'arfi ya cije lips nashi tamkar zai hudasu da hak'ori. Ya mik'e tsaye yana mai fidda huci mai zafi, takawa yay zuwa jikin window n d'akin, ya zuge labilan yana kallon waje, bayi keta kaikawonsu hankali kwance, dukda kasancewar rana ta take. ya maida labilan ya rufe Yakoma takowa tsakkiyar d'akin yana fad'in “tabbas ni Muhammad Sameer mai cika alk'awarine, kuma dukkan alk'awarin Dana d'auka miki ina k'ok'arin cikasu, sai dai nayi kuskure d'aya a cikin AUREN YARJEJENIYA, Na manta da babbar rahamar da ubangiji yake shinfid'awa ga dukkan wasu ma'aurata dazasu iya killace Kansu a matsugunni d'aya, Na manta da ko babu aure tsakanin mace da namiji inhar zasu kasance waje d'aya shaid'an yakan iya zama Na ukunsu ya sakasu aikata sa6o, balle mu da Muke ganin akwai igiyar aure a tsakaninmu, gaskiya kika fad'a, munyi yarjejeniyar aure domin gano mak'iyanmu bata zama Abu d'aya ba, amma kuma sai bamu d'auki matakan dazamu nisanta kawunanmu ba, daga ni har ke bamu Isa hana ubangiji ikonsa ba akanmu, tabbas ALLAH shidane bada gangan Na kusancekiba a wancan lokacin, sannan bansan ciki ya shiga jikinki ba, to mizaisa kizo ki titsiyeni kina min bore akan zubda shi. Bara kiji Na tabbatar miki yarinya, koda ace ta hanyar aikata zina Na Samar da wannan cikin inason abuna, kuma baza a zubarmin ba, ballantana sadaki Na biya d'unbin mutane suka shaida ke matata ce, mu uku kad'ai mukasan da wani Auren Contract. Dan haka kima nutsu idan zaki nutsu, kamar yanda kikace Duk abinda za'ayi saikin zubar da ciki ko? to Nima duk abinda zai faru saidai ya faru, babu ubanda ya Isa yasaka a zubar da cikinnan, sai dai idan Wanda yabani ne ya kar6a banida ikon hana wannan, idan kin gadama kici gaba da duk abinda kikeso har k'udirin zubda cikin, ni kuma Muhammad Sameer ina mai miki rantsuwa da ALLAH saina nuna miki ainahin color d'ina”. ‘ya k'are maganar da buga yatsunsa biyu suka bada sautin d'ass! d'ass!! A saitin fuskarta’. Fita munaya tayi da gudu daga bathroom d'in tana kuka, ahaka ta isa bedroom d'inta ta fad'a saman gado. Shi kuma tana fita yaja wani wawan tsaki ya fad'a kan gado yana dafe kansa dake sara masa. ga wata yunwa dake cinsa, shi saima yanzu ya tuna ko breakfast basuyiba suka fita, tsaki kawai yaja yana jawo wayarsa. number Nuren ya kira, bugu biyu ya d'aga yana tsokanarsa da fad'in “ho angon k'arni”. Galadima ya danne 6acin ransa, dan baya buk'atar kowa yasan wannan matsalar data kunne kai tsakaninsa da Munaya, muryarsa a sake yace “kun gama ne?”. “eh mun kammala, saidai kuma baka fad'i dawa-dawa za'ama visa ba cikin 'yan gidan nasu?”. Ya cije lips nashi yana gyara kwanciya, “tokai dawa yaka mata kake ganin zasu tafi?”. “eh, indai tanine gaskiya yakamata ace cikin k'annensa d'aya yaje, sai kuma mummynsu gimbiyarmu itama, tunda kaga itace first wife nashi”. “Okay hakan yayi, zuwa dare sai muje gidan muji yanda zasuyi, nasan kai dai bazaka shigo nanba, please kabama Sauban Abinci ya shigo mana dashi, dan ko breakfast My mata batayi ba”. “kai brother amma wannan sakacine ai, gashi ba ita kad'aiba?”. “wlhy Na mantane, saboda kaga ai yanayin da take tun barinmu gidan, inaga zanma inno magana a bamu mai abinci kawai”. “hakan zaifi kam, bara Na bashi ya taho yanzu kawai, amma zuwa anjima fa saika fito mun had'u”. “okay babu damuwa”. Yana yanke wayar kiran papi Na shigowa, fuskarsa d'auke da murmushi yay picking. cike da girmamawa yace “ran papinmu ya dad'e tare da k'yak'yk'yawan aminci”. “tunda kamin laifi fa ai dole ka faramin da dad'in baki”. Murmushi Galadima yayi har sarki Abdul'fatah na jiyo sautinsa, yace “a gafarceni ranka ya dad'e. ina fatan kuna cikin k'oshin lafiya kaida inno da dukkan ahalin masarautarka?”. “Alhmdllh Muhammadu. sai kuma wasu k'yawawan albishir suka riskemu a wannan rana. to ALLAH ya inganta, ya sauketa lafiya, shi kuma mahaifinka ALLAH yaci gaba da d'orar da lafiyarsa”. “Amin ya rabbi ranka ya dad'e ”. “Muhammad mikuma ya faru da sirikinka haka mara dad'in ji?”. “humm, ranka ya dad'e bansan miya sakoshi cikiba shi kuma?”. Murmushi mai sauti papi yayi, ya gyara zamansa akan kilisarsa, cikin nuna kulawa yace, “akwai abinda bamu saniba ne kawai, amma a fiddashi daga k'asar kafin mu fara wani yunk'uri”. Kamar Galadima na gabansa yashiga jinjina kansa, “to insha ALLAH zuwa gobe da daddare idan ALLAH ya kaimu zasu wuce". “hakan yayi, aci gaba da hak'uri dai kaji Muhammad, hak'uri jarine, jarabawa kuma tsanice ta zuwa wajen nasara, ALLAH yayi muku albarka”. “amin ranka ya dad'e, nagode sosai”. “yaushe zaku shigo?”. Murmushi Galadima yayi, hakan yana nufin kakansa nason ganinsa kenan, a ladabce yace “dasun tafi insha ALLAH ”. “ALLAH ya kawoku lafiya”. Tunda suka katse wayar saiyayta sauke ajiyar zuciya, koba komai ya sami nutsuwa akan wayar dasukai da papi. tashi yay ya k'arasa shafa man, sannan yasaka kayan da bazasu takurashi ba. Falonsa ya fito, abinda ake nunawa a tv ya d'auki hankalinsa sosai, ana cigiyar d'iyar Minister Ce, wai an nemeta an rasa tun a daren jiya. Akan la66ansa ya furta “Nuren!” Sai kuma yayi murmushi kawai ya kwanta saman doguwar kujera. A haka Sauban ya shigo ya sameshi da sallama, sai bayi buyu dake binsa a baya d'auke da ledoji. Galadima ya bud'e idanunsa yana kallonsu amma bai tashiba, bayan bayin sun ajiye suka zube sunama Galadima barka da hutawa, murmushi kawai ya musu ya d'aga musu hannu. Sauban yabasu izinin tafiya. Zama Sauban yayi a kujerar dake kallon Galadima, “kai yau ina cikin nishad'i wlhy yaa Sam...” Kallonsa Galadima yayi yana d'an murmushi, amma baice komaiba. Sauban yace “yaa Sam... Aunty gimbiya fa?”.. Galadima yace “barci takeyi”. “tofa Unborn babynmu yazo da sabon salo kenan”. Hararsa Galadima yayi, ya mik'e yana dariya ya shige bedroom. Galadima ya girgiza kai kawai yana tashi zaune. ledojin ya duba dan ganin mi suka sayo?. Abinda yasan zata iya ci ya d'auka ya fita. Saida ya d'anyi jimm a k'ofar d'akin sannan ya shiga da sallama, har yanzu tana a kwance tana kuka, lips d'insa ya d'an cija sannan ya ajiye abin hannunsa saman table d'in dake gaban gadon, idanu ya tsura ma bayanta nawasu 'yan seconds, ko alk'yabbar bata cireba, zama yayi a bakin gadon kusada ita, amma ya juya mata baya. Tun daga shigowarsa har zamansa tana jinsa, amma ko motsi batayiba, kusan mintuna 3 suna zaune a haka, ganin batada niyyar tashi ko kulashi ya sakashi juyawa yana kallonta, gyaran murya yayi sannan yace, “tashi kici abinci”. Shiru tayi ta shareshi, ko motsima bata yiba. Tsawa ya daka mata, babu shiri ta tashi zaune, jikinta sai rawa yakeyi, tunba yanzuba munaya akwai tsoron tsawa, bata barin saita kwana amma batason amata tsawa. Shi kansa yayi mamakin tsoratar tata, ya watsa mata harara yana kwafa, sai kuma yaja tsaki, alk'yabbar yacire mata, sai hawaye take zirarwa, bai kuma cemata uffanba ya bud'e abincin ya ajiye a gabanta, kafeta kawai yayi da idanu, hakan saiya tasirantar da tsoronsa a zuciyarta, dan haka tafara cin abincin, tanayi dai hawaye na zurara, cikin nata bamai tsurfa baneba, komai ci take hankali kwance, sai dai laulayi na ciwo. Dolenta ta saki jiki taci abincin, danya kafeta da idanu ga fuska cid'in-cid'in, duk jarumtarka dolene kaji shakkarsa. Kallo d'aga tamasa ta janye idonta, shi kuma ya harareta yana fad'in “kin k'oshi ne?”. Kanta ta jinjina masa tana matso kwalla. baice komaiba ya sauke sauran abincin k'asa, sannan yace “sauka kije kiyi wanka”. Baki ta bud'e zatayi magana ya dalla mata harara. sauka tayi tana k'unk'uni akan la66a. yana kallon motsin la66an nata, sai dai bayajin mi take fad'a. Yau kam Alhmdllh taji dad'in jikinta, ko k'arin ruwan da aka saka matane yasakata jin kwarin oho, ruwa mai d'an d'umi ta tara tayi wankan, tanayi tana hawaye, itafa ko mi zaiyi ba masifaba bazata bar cikinnan ba, babu yanda za'ayi ta reni ciki ta haifeshi sannan yazo daga baya ya saketa, bazata d'auki wannan rainin hankalinba, su maza a kullum d'aukar mace suke mai k'arancin tunani, kowane yayin rashin mutuncinsu suka kwaso saiya k'are akan mata, wlhy akan cikinnan tata d'aga masa hankali kenan harsai ya amince an zubar dashi sannan, kuma ana zubarwa zata k'ara gaba, mahaifinsa kam kobasa tare insha ALLAH zata cigaba da masa addu'oi ana aika masa. Jin shiru tak'i fitowa ya sakashi mik'ewa, bai wani kwankwasa ba ya bud'e k'ofar bathroom d'in kawai, danshi zatonsa ba wankan takeba ta tsaya kukane. A birkice munaya ta kalli k'ofar, ganin Galadima tsaye yana kallonta ta fasa k'ara, yay hanzarin ida shiga bayin ya rufe bakinta da tafin hannunsa dankar ta tara masa jama'a. Juyawa tayi ta ruk'unk'umesa, tare da saka hannayenta ta zagaye bayansa ta manne k'irjinta da nasa, ita duk bata son yaga jikinta ne😂😝. Shima fuskantar hakan da yayi ya sakashi sakin murmushi, saiya saka hannunsa biyu ya zagaye bayanta ya manneta sosai a jikin nasa. Shiru sukayi nawasu seconds, tana sauke ajiyar zuciya shima yana saukewa, saboda yanason ganin yanda zatayi saiya fara k'ok'arin janye jikinsa itama zai janye ta. K'ank'ameshi tayi ta fashe da kuka, jiyay tamkar ya kwashe da dariya, amma saiya daure, cikin dakiya yace, “malama sakeni mana? konaci bashinki ne wai?”. Cikin dasashshiyar muryarta datasha kuka tace, “to kabani zanina da hijjab na saka”. “to kin k'udunduneni ta ina zan iya baki wani zani? sakeni saina baki”. Kafad'a ta nok'e alamar tak'i. Murmushi Galadima yayi, ya shafa bayanta cikin murya k'asa-k'asa yace, “idan an hanani ganin can ai gashi ina kallon nan”. Da sauri tayi wata wulk'itawa ta koma bayansa ta 6uya. Kansa ya dafe yana fad'in “yau Sameer kaga ta kanka, ranar farin cikinka sai saka maka ciwon kai da zafin kai akeyi, wai ke yalla6iya mikike 6oyemin daban saniba ne?”. Baki ta murgud'a masa tana fari da idanu, dayake ba ganinta yakeba baisan hidimar datakeyi ba. K'ok'arin juyo da ita ya farayi amma tabi ta kanannad'e shi, rasa yanda zai mata yayi. yakula yarinyarnan 'Yar daruce kawai. zaninta ya jawo ya mik'a mata, saida ta tabbatar ta d'aura sannan ta sakeshi, yana juyowa ta juya masa baya ita kuma. Baice komaiba ya ta6e baki ya fice daga bathroom d'in. Harar bayansa tayi ta na fad'in “ALLAH ya isana”. Nace Humm.😏 Fita yay daga d'akin gaba d'aya, tunda dai yasamu taci abincin, harya kai k'ofarsa ya tuna batasha maganinta ba, dawowa yayi da baya. Ita kuma motsin fitarsa dataji yabata kwarin guywar fitowa. Shigowarsa tasata kwakumar hijjab ta saka, bakinsa ya ta6e ya wuce wajen handbag d'inta batare daya kalleta ba. Magungunan ya fido, ya zauna bakin gadon, “kizo kisha magani”. ya fad'a cikin k'asaitarsa. 6ata fuska tayi, tace “babu amfanin tattalin abinda za'a zubar ai”. Lips d'insa ya cije, sai kuma ya ajiye drugs d'in yana kallonta, mik'ewa yayi ya taka inda take, a bayanta ya tsaya, fisgota yayi ta fad'o saman k'irjinsa, saida ta rumtse ido dan zafin dataji, ya matso da fuskarsa daf da tata, a wani yanayin data kasa fassarawa yace “adadin nawa kike buk'atar na biyaki danki barsa?”. Rik'esa nayi da k'yau gudun karna fad'i, na janye idona dake cike da kwalla daga cikin nasa, “Bana buk'atar ko sisinka yalla6ai, cikinne kawai bana buk'ata, kuma bazan raineshi ba balle nakai ga haifeshi”. Wani murmushi mugunta yayi, sanan ya sakeni tamkar zai hankad'ani, mikuma ya tuna oho masa, saiya kuma damk'e hannuna, muryarsa a kausashe yace “wlhy idan kinga baki haifi cikin nanba to sai dai idan wanine a cikinmu numfashinsa yabar gangar jikinsa, sai kuma idan ubangiji ya kaddara Shiba mai Shak'ar iskar duniya bane, dan bani da hakk'in kowa, ubangiji kuma bazai barki ki shiga nawa ba”. yana gama fad'ar haka ya saki hannuna yafice daga d'akin baki d'aya. Yariga yasan zai fuskanci abindama yafi haka daga munaya, shiyyasa bai zafafama zuciyarsa akan wannan rikicin nata ba, shi babbanma burinsa yanzu Abbanta yabar k'asar nan, danya samu damar gudanar da aikinsa yanda ya kama ta. Da wannan tunanin ya dawo d'akinsa, ya iske Sauban kwance wai zaiyi barci, hararsa yayi yana fad'in “ kama tashi, time d'in zuhur yayi. Yana fita na raka bayansa da harara ina murgid'a baki, “oho dai, koma mizaka fad'a ka fad'a, nima ai bani tare da hak'k'in kowan, ALLAH kuma bazai baka damar danne nawaba, sokake nazama shashar mace ko? munyi auren contract batare da sanin iyayena ko naka ba, kazo kamin ciki na haifa maka ka sakeni na koma gidanmu, katashi da riba biyu kenan, nikuma babu ko d'aya sai bak'incikin danakema iyayena tanadi da kaina, Galadima ko a matanma ai _AKWAI BANBANCI?_ wlhy. gaskiyane Munaya, rik'e darajarki shine 'yancinki😄👍🏻. ******* Bayan sun fito massalaci sukejin labarin wai an rasa inda Muftahu yake, a safiyar yau aka samu motarsa a bud'e, sai kuma agogonsa da takalminsa d'aya a k'asa alamar da k'arfin tsiya aka saceshi. Hakan yasaka aka kama dogaran dake tsaron k'ofa ta uku, dan anga alamun tanan aka fita dashi. Dukda Galadima najin haushinsa saida hankalinsa ya tashi, dan haka suna shigowa ya d'au waya ya kira Nuren. Nuren na d'aga wayar Galadima yace, “Nuren Muftahu, kaine ko?”. “Muftahu kuma? nine naimi?”. “A daren jiya an rasa Wanda ya bar masarauta dashi”. “humm brother, dukda muna ganin Muftahu cikin masu mana zagon k'asa banta6a tunanin saina d'aukeshi zan gane hakaba, wlhy bani bane”. “ya salam”. ‘galadima ya fad'a cikin dafe kai da cije lips, wayar ya yanke ya Shiga safa da marwa, yarasa wazai hararo. Yana cikin wannan halin saiga harun shima a rikice, kowa yasan su ukunnan abokan junane, kuma akwai shak'uwa tsakaninsu, matawalle ne dama bai cika shiga cikinsu ba, saboda mama Fulani Na hanashi tun yana yaro, a cewarta shine d'an Sarki mai mulki, kuma shine mai jiran gado, darajarsa datasu Galadima ba dai-dai takeba, wannan hud'ubar ce tamasa tasiri sosai, amma yanason 'yan uwansa har zuciyarsa. “galadima shin kaji kuwa mike faruwa a masarautarnan?”. Cikin damuwa Galadima yace, “Harun su waye da wannan aikin?”. “kowa abinda yake tambaya kenan Sameer, Muftahu bashida wani abokin fad'a”. Hankalin Galadima kuma tashi yayi, shi duk damuwarsa karda a cutar da Muftahu ta dalilinsa, tunda ya kula duk wani makusancinsu shine abin harin mak'iyansa. shifa baima yarda ba Nuren bane da wannan aikin, dan yasan halinsa sarai, dolene kuwa yafita wajensa yanzunnan. Harun yace bara yaje, suna son akai report gidan radio da television. Jin jina kai Galadima kawai yayi, shima ya shige ciki danya shirya. Tun safe an sanarda jami'an tsaro 6atan Muftahu n, kuma suna a kan aikinsu. ★★★ Yunwar da yakeji tasashi bayan yayi shiri ya samu fresh milk yasha kawai, sannan yafito, d'akin Munaya ya lek'a, saiya isketa baje a gado tana shak'ar barci, baiyi yunk'urin tashinta ba yafito. Har dogaransa sun taso yace suyi zamansu su huta, zai fita shida Sauban, cikin damuwa sarkin mota yace, “kayi hak'uri ranka ya dad'e, koda nine kawai mu fita, Mai martaba ya sanar yau a fada kar'a sake barin wani d'an gidannan yafita wani waje shi kad'ai”. Kallonsa Galadima yayi, kamar zaiyi magana saikuma yafasa ya bud'e mortar da kansa ya shiga, batare da ya jira an bud'e masa ba. Da hannu sarkin mota yayma sauran dogaran nuni da su biyosu a baya idan sun tafi. A wani waje suka had'u da Nuren, Nuren ya fito daga motarsa yadawo inda Galadima yake, sai sarkin mota yafita yabasu waje kawai. Galadima yace “please idan kaine ka sakeshi”. Da mamaki Nuren yace, “wai Muftahu n dai? am telling you banida alak'a da d'aukarsa. yarinyar Minister ce kawai a hannuna”. “innalillahi, wlhy Nuren inajin tsoro, karsuje su cutar dashi”. “Sameer! nifa ina zargin kawai ya had'a baki da wasune suka kamashi dan yayi wasa da hankalinmu”. Idanu Galadima ya tsurama Nuren tamkar yana hango gaskiyar maganarsa, ya saki wani guntun murmushi, sannan ya gyara zamansa yana fad'in “well, koma minene dai zai fito ai”. Nuren yace “ni kaga dama kabar zancen wani Muftahu n banza can, way note mu wuce gidan sirikanka kozamu samu wasu evidence daga canma akan Accident d'innan”. Agogon hannunsa ya kalla, sannan ya kalli Nuren d'in alamar suje. Anan Nuren yabar motarsa suka tafi ata Galadima, saida suka fara tafiya Galadima ya lura da mototin dogaransa a bayansu. d'an murmushi yayi yana kallon Sarkin mota, yace “sarkin mota an karya min doka kenan?”. Sarkin mota daya fahimci Galadima yagane dogarai Na binsu sai yayi 'yar dariya, yace “ka gafarceni ranka ya dad'e, bazai yuwu mu barka ka fita kai kad'aiba ai, dan fitarka babu kowa tafi ta kowa had'ari a masarautarnan, mai martaba ma nasan saboda kaine ya saka dokar ai”. Galadima baice komaiba sai murmushi dayayi, Nuren ma murmushin yayi, sannan yace “amma kamar bayan motar dogaranka akwai wata bak'ar mota Na bin tasu?”. Galadima ya juya shima, tabbas anabin motar dogaran a baya, “sarkin mota su wucemu, karsu tsaya”. “To ranka ya dad'e”. Bayan sarkin mota ya sanar musu suka wuce su Galadima, motarma ta wuce, da kallo Nuren da Galadima suka bita, Nuren yay hanzarin d'aukar motar hoto a wayarsa. “humm da alama suna zaton kana d'aya daga cikin motocin canne”. Murmushi Galadima yayi, a k'asaitarsa yace, “kokuma suna son wasa da hankalinmu ba”. Da mamaki Nuren yace “kamar ya?”. Murmusawa Galadima ya kuma yi, ya kwantar da kansa jikin seat yana lumshe idanu, “Nuriddeen! Sameer ya wuce tunanin dukkan mai tunani, kai tsaye ba'a gane manufar zuciya, kwanji ko dama basu ke nuna k'arfin ikon mai ikoba, nazarin komai daki-daki da iya sarrafa duniya a yanda tazo shike nuna k'arfin gwarzan taka, mazantaka ba'a shaidata a fuskar namiji, duk lokacinda kai gamo da nama, kud'i, mata bisa hanya, karkayi rawarkan d'auka ko murnar ALLAH ne ya baka, zata iya yuwuwa tarko aka d'ana maka, shi k'yawu had'arine, 6oyeshi kuma nagartace, maiyi baya fad'an zaiyi, sai dai aga aikinsa a k'asa, tasowar iskar hadari bashi ke nufin ruwan zai zuba ba, watak'il sunan wannan iskar gyara kayanka. Dalili da dalilai basa ta6a saka zuciyar Wanda yake nema ta raunana, time d'in da zan nunama mak'iyan mahaifina d'an zaki ya girma yayi, sun durk'usar da shi a k'asa batareda tunaninsu yabasu ya haifi Raina kama ba, Su cigaba da raina aikin Muhammad Sameer daga k'arshe kuma saisuga gayya, tafiyar hawainiya bashike nufin gazawar kuzarinta bane, lokuta da dama hanzari kan katse igiyar cikar buri, a sannu kowa zai fahimci wanene *_RAINA KAMA....._*👎🏻 Ba Nuren ba hatta da sarkin mota maganganun Galadima ya shigeshi, tabbas mutane dayawa sunama Galadima kallon mutum mai yawan sakaci da rashin ho66asa, koshi yana d'aya daga ciki, amma wannan zantukan nasa sai suka sakasu a rud'ani, kenan akwai abinda sud'in basu saniba........... Dole tunaninsu ya katse saboda isowarsu gidansu Munaya. Fita sarkin mota yayi yanema musu iso, babu dad'ewa saiga baba k'arami ya fito, sarkin mota ya bud'ema Galadima, yayinda Nuren ya bud'e da kansa, zuciyarsa sai jujjuya hannunka mai sandar Galadima yakeyi. Dukda baba k'arami yayi mamakin zuwan Galadima haka ya danne, yaymusu k'ar6a ta girma, sannan suka shiga cikin gidan. Gidan tsitt tamkar babu mutane, saikace ba gidannan bane mai kama Dana 'yan dambe😂, (yo kowa Na tsoron a korashi gidansu🤣😝). A falon daddy aka musu masauki, dan danan aka cika musu gaba da kayayyaki, baba k'arami ya fita domin basu damar cin wani Abu. Babu abinda suka ta6a, dukda kuma Galadima ma yunwa yakeji, a haka daddy da baba k'arami suka dawo. Daddy yace “anya kuwa wannan d'an namu yana d'aukar gidannan matsayin nasu?”. Murmushi Galadima da Nuren sukayi, Galadima yace “sosaima daddy”. Baba k'arami yace “ta INA zamu amince da haka kuwa, bayan inada tabbacin ko ruwan gidannan Baka ta6a sha ba”. Kunya Ce ta kama Galadima, sai kuma yaga bai k'yautaba, ya rissinar da kai yana fad'in “amin afuwa zan gyara”. Mik'ewa baba k'arami da daddy suka kumayi, “to mun bada dama ta biyu”. cewar Dady yana dariya. Bayan fitarsu Nuren ya bud'e kulolin shima yana dariyar, danbun shinkafane daya samu nutsuwa ta musamman, sai k'amshi mai dad'i yakeyi, daga Galadima har nuren saida kwad'ayin cin abincin yazo musu. Kallon Galadima Nuren yayi yana d'aga gira, Galadima yay murmusa tareda fad'in “kadaiji kunya”. “kaima jinta zakayi yanzu, dan nasan ci zakayi”. Yau dai kam Galadima yaci abincin gidansu Munaya, kuma gashi girkin innarsu, babu kunya sukaita zuba Santi shida Nuren sunama juna dariya, Galadima harda su6utar baki yana fad'in “amma my mata muguwace, bata ta6amin irin wannan ba”.🙀 Mi Nuren zaiyi inba dariya ba🤣, su Galadima anji dad'i har kwalwar kai Baki ya bud'e😂😝. Saida suka mammala tsaf sannan su baba k'arami suka dawo, sunji dad'i dasuka iske sunci. Daga nan sukayi gaisuwa, su baba k'arami suka d'ora da godiyar d'awainiyar Abba da Galadima ya d'auke musu. Murmushi kawai Galadima yayi. Nuren ya gyara zama, a ladabce yamusu bayanin son fidda Abba da Galadima kesonyi, dan likitoci sunce ana buk'atar kulawa saboda karayar hak'ark'arinsa data k'ugu, “to yanzu haka dai angama setting d'in komai gameda tafiyarsa, har asibitin daza'a kaisa, visa d'insa da komai, sai dai anason tafiya da mutum biyu a cikinsu, mi kuka gani akan Wanda za'aje da shid'in?”. Daddy da baba k'arami suka kalli juna, summa rasa wane irin farin ciki zasu nuna dan Galadima yasan sunji dad'i? sunta jero masa k'yawawan addu'oi, kafin daddy yace “ai kawai sai atafi da jafaru da Ai'sha, dan bai kamata mutafi mu duka ba gida babu kowa, dukda akwai su Anas, gakuma su Hameed zasuke zagayowa, amma hakan yafi dai. Duk sun gamsu da hakan, dan haka suka buk'aci passport d'in baba k'arami da inna, ita inna babu, sai sunje an mata, amma baba k'arami an samu. Sun bari akan zuwa anjima za'azo akai inna tayo. Daga nan Galadima ya buk'aci number da aka kira aka sanar musu da accident d'in Abba. Daddy yace Ai'sha aka kira, saidai akawo wayar tata. Kiranta yay yace tabama cikin su Aryaan ya kawo wayarta. Babu dad'ewa saiga Aryaan d'in da ita, yanda yaron ya gaishesu saida abin ya birge Galadima, ya yarda yaran gidan akwai tarbiyya babu laifi kam. Galadima yace, “amma Dady ko numbers nawa Abba ke amfani dasu?”. baba k'arami ya bashi amsa da cewar “uku ne”. Nuren yace “kozamu samesu dukansu?”. Dukda baba k'arami da daddy sunshiga mamaki, dansu zukatansu basu kawo musu akwai wani Abu a k'asa ba, sun d'auka kawai Abba yayi Accident ne dai. Baba k'arami yabasu Numbers d'in duka. Bawani bincike Galadima yayi a wayar innarsu Munaya ba, wani Abu kawai ya saka (Wanda Nima ban saniba😱) yabama Dady wayar yana fad'in “zata bar wayar anan dan a can bazatayi aikiba, kuma gashi muna buk'atar wayar, dan haka daddy saika rik'e a hannunka tunda kai kana gida”. Dady ya amsa da to, duk su Galadima sun kuma sakasu a duhu. Sallama sukai musu suna fito domin tafiya. Harsun Shiga mota saiga Aiyaan da gud'u d'auke da wata Leda. Sarkin mota ya tareshi yana fad'in yaro miya farune?”. “Auntynmu za'a kaimawa inji innarmu”. Galadima yayma sarkin mota nuni da yabar Aiyaan d'in ya k'araso. Bud'e murfin Galadima yayi, Aiyaan ya k'arso, Galadima ya kamo hannun Aiyaan yana murmushi, “my friend ya akayi?”. 'Uncle innarmu ce tace akaima Auntynmu dan ALLAH”. murmushi Galadima yakumayi, sannan ya kar6i ledan yana fad'in “ita kad'ai banda ni?”. Aiyaan yad'an zaro ido waje, sai kuma yace “to bara naje Na fad'am innarmu kaima ta baka naka”. Da sauri Galadima ya kamo hannunsa dan yana neman tsillawa da gudune, “kaga dakata, idan naje saimu raba wannan da ita, yanzu dai ka fad'ama innarmu ta shiryaka gobe zan aiko a d'aukeka kazo ka zauna damu tunda kuna hutu ”. Cikin murna Aiyaan yace, “wajen auntymu?”. Galadima ya jinjina masa kai. “to amma kuma Aryaan fa?”. Cikin mamaki Galadima yace, “wanene Aryaan d'in?”. “lah baka San mu 2wins bane ba?”. “da gaske?”. “ALLAH kuwa”. “to shikenan, kacema innarmu ta shiryaku Ku duka biyun zakujema Aunty hutu”. Cikeda murna Aiyaan ya shek'a da gudu gida danya kai labari. Galadima yay murmushi yana rufe k'ofar motar, Nuren ma murmushi yakeyi, a fili yace, “yara sunyi wlhy”. Galadima ya kalleshi, cikin d'age gira sama yace, “kayi aure”. Sosai Nuren yay dariya. ****** A inda suka d'auki Nuren anan suka ajiyeshi, su kuma suka koma masarauta, sun iske tuni dogaran sun dawo abinsu. d'akinsa ya Shiga, ya iske Sauban nata barcinsa. Bai tadashiba, yadawo falo ya zauna. _____________________________ Da daddare Galadima Na falonsa zaune yana aiki a system akayi knocking d'in k'ofa, izinin shigowa ya bada, sarkin mota ya shigo hannunsa d'auke da leda. Galadima dake aikinsa bai d'agoba, a haka ya amsa gaisuwar sarkin mota. Sarkin mota yace “ranka ya dad'e kayi mantuwane a mota ”. d'agowa Galadima yayi ya kallesa, ganin ledar da Aiyaan ya kawo yatuna masa sak'on munaya, nuni yama sarkin mota daya ajiye. Sarkin mota ya ajiye yana masa saida safe. Nanma bai tankaba, kansa kawai ya jinjina masa. Bayan fitar sarkin mota ya mik'e d'auke da laptop d'insa da ledar, dama tunda ya shigo baima lek'a ta ba, dan Sauban yace yakai mata abinci, kuma tun d'azu suna tare suna hira. Hakan yasa yagane shine ta raina kenan. wannan haushin ya hanashi Neman inda take. A bakin gado ya isketa zaune tagama waya da Munubiya, k'in d'agowa tayi ta kallesa, tadai amsa masa sallama. Shima bai kula taba ya zauna bakin gadon d'an nesa da ita. Shiru kowa yayi suka share juna, haushi ya turnuk'e Galadima, lokaci yayi dazai daina d'agama yarinyar nan k'afa, yakamata su goga raini shi da ita. ta gefen ido ya saci kallonta, sai wani cika da batsewa takeyi, ya cije lips nashi. “k baki iya gaisuwa bane?”. Saida takuma tura bakin sannan tace “ina yini” tana mik'ewa da nufin bar masa d'akin, tana k'unk'uni Bai amsata, sai mik'ewa da yayi shima, matsawa tashiga yi baya yana binta, fuskarsa a matuk'ar d'aure, da jikin bango ta manne, shikuma ya mata runfa, hannunsa d'aya a dogare da bangon yayinda yasaka d'aya ya rik'o hannunta ya matsa da k'arfi, zatai magana ya jawota tafad'o jikinsa, ya manne bakinsa kan nata, duk yanda taso kwatar kanta hakan ya gagara, dan ya kama hannuwanta biyu ya murd'esu ta baya yanda ta kasa koda motsi. A haka ya wulk'itata takoma saman gadon, shima yabi bayanta. Ya d'ora hannunsa kan bakinta dan karta ishesa da tsiwa, idonsa ya saka cikin nata ya hanata kata6us, cikin tsare gida yace “dolene yau Na kora miki warning na musamman danki ringa banbance inda zakiyi tsiwa”. Bai bata damar dazata fad'i nata ba yashiga aikata yanda yakeso da ita🤥🙆🏻.................✍🏼 Kutttt Galadima auren Contract nefa😱😂, ba ruwana kaida masoyan Munaya aradu🤣⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀🤧. i miss you wujiga-wujiga my sweet fans😂😜😜😜🥳. *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*🙏🏻😭 [7/3, 9:54 AM] Aysha Galadima: *_Typing📲_* *_Haske writer's asso...._*💡 *_♦RAINA KAMA......♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻 ~Book 2~ 👉🏻9⃣ .................Salon nasa yasani bashi ragama, dan Galadima yazo min da sabon salo mai tafiya da gudun jini dana zuciya. Duk da kasancewata farin shiga, hakan bai hanani gane Galadima Na daban bane, kamar yanda kuka sanshi mutum mai izza da k'asaita, hakan bai canja ba ta wannan fanin, komansa a nurse da izzar k'asaita yake gudanar dashi. ban tashi farga nayi kuskure ba saida labari yafara nisan zango, anzo wajenda tsorosa yafara tasiri a gareni, Sai dai kuma nayi sakacin da Galadima yazama kurman dutsen dabaya ji baya gani. Sai lokacin hawaye suka fara ambaliya ga fuskata, hannayena na k'ok'arin d'agawa domin rok'o, sai dai ya hanani wannan damar gaba d'aya.......... 🤥🙆🏻kai babu ruwana, iya nan nagani nima🤫 aradu aunty Magajiya da aunty Ni'ima zasuci k'aniyata ne idan na k'arasa fad'a😱🤭⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀. Tabbas na gurzu, dan yau na banbance tsakanin aya da tsakkuwa, banbancin baya cikin hayyacinsa da yau d'inma kad'anne, dukda babu yanda za'ayi daren farko yayi dai-dai da kowacce rana ta bayansa. Duk ajiyar zuciyar danake saukewa yana jina, amma yay luf a gefena, hakan ne Yakuma tunzurani, a zalinceka akasa lallashinka saboda jin kai, wlhy kasaitar bawannan tayi masa yawa, duk randa yazama sarki kam fadawa sunga takansu, dan magana dai idan sarki na uku a fada toshi bazaiyi ko guda d'aya ba😏. Galadima daduk yake sauraren kukan nata da ajiyar zuciya ya juyo kad'an yana fuskantarta, hannu yasaka ya tallafo fuskarta ta matso dai-dai da tasa, jinai kawai ana huramin iska saman ido, tsaf na fahimmci iskar bakinsa yake huramin, amma saina dake nak'i bud'e idona. Muryarsa can k'asan mak'oshi ya furta “my friend are you okay?”. Banza na masa, nakuma k'i bud'e odon, lallai mutuminnan yacika d'an latsin rainin wayo number 1, yanzunan Galadima har yanada bakin yimin wannan banzar tambayar?, idona a rufe har yanzu na bud'e baki cikin salon tsiwa zan maka masa bak'ar magana, amma saiya d'ora yatsansa saman bakina yana fad'in “shiiii!🤫” da bakinsa, shirun kuwa nayi kamar an rufemin bakin Dan Nina Na tuna illar yin tsiwar.(😝😂) Ya matso dani jikinsa ya rungume, hannunsa na buga gadon bayana k'ad'an-k'ad'an, ya d'ora bakinsa saitin kunnena, “yanzu kin gane banbancin Sameer da Munaya right?, idan kuma har yanzu baki fahimta ba to bakinki ya cigaba d'amin tsiwa OK?, nikuma bazan gaji da punishment nashi ba sala-sala yalla6iya💋”. ‘ya k'are maganar da sumbatar cikin kunnena’. Babu shiri na k'ank'amesa dan har cikin kwalwar kaina naji sumbar nan. Kad'an ya buga bayana sannan ya janyeni daga jikinsa ya sauka daga saman gadon. “hasbinallahu wani'imal wakil” na iya maimaitawa kawai, na k'ank'ame pillows d'in gabana ina rintse idanu da cije lips (copy copy😝). Kusan mintuna 15 duk nazata yama fitane, sai kawai jinai an d'aukeni. a razane na bud'e idanuna, kallon ido cikin ido mukaima juna, da matuk'ar Sauri na maida nawa na lumshe. Wani muskilin murmushi Galadima yayi yana cije lips. Ba shiri na bud'e ido, saboda jina cikin ruwan zafi, yunk'urawa nayi zan mik'e cikin 6ata fuska ya maidani ya zaunar yana fad'in “za6i ya rage naki, zama kiyi da kanki, kokuma ni nayi miki..” Banma bari yakai k'arsheba na koma na zauna ina kare k'urjina. Kafad'a ya d'age sama yana ta6e baki da fad'in “hummm”. Fita yay daga bathroom d'in ya rufe mata K'ofar. Na kai tsawon lokaci a bayin ina Gasa jikina, dan nasan idanma banyiba kaina nama mugunta, saida naji ko ina ya saki sannan nayi wankan tsarki ina hawaye, bansan yanda zan fassara wannan muguntar ta Galadima ba kuma, wannan karon kuma tsautsayin zaice kokuwa ba yin Kansa bane?. Haka dai na kammala na d'aura towel d'ina, a zuciyata ina addu'ar ALLAH dai yasa ya fita, dan towel d'in guntune, bai gama rufe cinyoyina bama baki d'aya. Da sand'a na fito, yauma inajin zafi kad'an-kad'an, amma ba kamar na ranar ba. ganin baya d'akin saina ida rufe k'ofar na tako cikin d'akin sosai. Ina neman kaya a wardrobe ina share hawaye, indai rashin tsiwar dayake fad'ace na daina masa, dan bazan zauna ya illatani a banza ba, wannan k'addararren cikinma daya hanamin gangar jiki hutawa da ciwuka ya isheni, basai na cigaba da 6alloma kaina wata muguntar tasa ba. wata 'yar riga mai d'an nauyi-nauyi na samo, na cirota dan sanyi nakeji, juyowar da zanyi saina gansa zaune bakin gado yana danna laptop, hannunsa d'aya rik'e da glass cup yana shan fresh milk hankali kwance. Saida nad'anja baya, nakuma bud'e rigar ina kare jikina. Duk abinda takeyi yana kallonta ta gefen ido, amma yawani share kamar baima San da itaba. Da bin bango da sand'a na koma bayin, ta gaba kuma ina karewa da rigar. Saida ta shige ya d'ago kai yana kallon k'ofar bayin, saikuma ya girgiza kai yana murmushin gefen baki. cigaba yayi da aikinsa a nutse. Barci nakeji, ga zazza6i yafara rufeni, hakan yasa ina gama saka rigar na fito, naci serious kawai sannan na fito. d'ago idanu yayi muka had'a ido, da sauri nad'an rankwafa inajan rigar barcin k'asa wai danta rufemin cinya zuwa kwauri. Baki ya ta6e yana wani janye ido cikeda basarwa. Irin shi baiga abin kallo d'in nanba. Ni kuma na dalla masa Harara ina k'ok'arin hayewa gadon. “ji mana”. ‘yafad'a cikin izza’. Banza na masa zan haye gadon. Yace “iyim, bakije daddarawa ba kenan yarinya, saina sake kaiki yanzunnan....”. Kafin ya rufe baki nama iso gabansa na tsaya. d'agowa yayi yana kallona yana kur6ar fresh milk nashi, ya d'agamin gira d'aya. Baki na turo masa ina share hawaye. Ya kamo hannuna ya zaunar kusa da shi, “nikam yalla6iya karki haifomin abin cikin kwan da halin kuka, bana son ragwan taka, 'yata ko macece jaruma za'ayi, irin wadda labarinta zai zaga lungu da sak'o na duniya”. Harara na balla masa, yay saurin rik'e cup d'in hannunsa dayake zuba frash milk a ciki, “eh me, malama karkisa hantar cikina fitowa, irin wannan harara haka”. Kad'an yarage banyi dariya ba, da gaskiyar Momma, halin Galadima d'aya da Sauban, tsantsar harmutsine da sanya damuwa a rai ya lullu6e halinsa na barkwanci, hakan kuma yanada nasaba da rashin samun mai jansa a jiki yana d'auke masa kewa da rage masa rad'ad'in damuwarsa. Momma hankalinta nakan jiyyar Abie, Aunty mimi kuma rainon Sauban, mom kuma tayi aure lokacin dayake buk'atar makusanci, s....... Firgigit nayi saboda hancina da yaja, na kalleshi ina tura baki. “maida wuk'ar yalla6iya, abin bana fusata bane, wace duniyar kika tafi hakane da nisa inata magana?”. Marairaice fuska nayi ina shirin fara kuka, “please ka barni na kwanta barci nakeji”. Kofin hannunsa ya mik'amin, na waro idanu ina girgiza masa hannu alamar a'a”. Shima saiya waro nasa idanun yana fad'in “why?”. “kawai ni bazan sha bane, aje a zubamin wani abu”. “hakane kuma”. ‘ya fad'am yana kamoni ya jawoni jikinsa’. Saman cinyarsa na zauna, da hanzari nafara k'ok'arin mik'ewa. shima saiya kama hannayena ya maidasu baya yanda bazan iya kata6us ba, madarar ya d'auka ya guntsa da yawa a bakinsa. Waro idanu nayi ganin ya nufo bakina gadan-gadan, duk yanda naso kauda fuskata ya gagara, na datse hakwarana da sauri, shi kuma saya toshemin hanci, hakan yasa ni bud'e baki dole, dan ina buk'atar shak'ar numfashi. Tas ya juyemin fresh milk d'in abakina, sannan ya kuma rufe hancina saida na shanyeta sannan ya janye bakin, ni dashi duk muka hau sauke numfashi, kuka na sanya masa, amma hakan bai hanashi kuma guntsar madarba ya kuma juyemin a baki na, haka yayta min, ya kuma k'ara rabin kofi kuma, saida yaga ta kwalin ta k'are sannan ya sakarmin hannu na tashi zaune. Bansan kawai na fara kaima k'urjinsa k'ananun dukaba, ina fad'in wlhy sai ALLAH ya sakamin, kai bama zan yarda ba fa, saboda k'azanta kaita had'a yawunka da fresh milk kana d'uramin, ni bazan yardaba”. Shagala kawai yayi yana kallona, yakasa kare kanshi balle yunk'urin hanani, saida nayi mai isata sannan na fad'a k'irjin nasa ina raira kuka. Lumshe idanunsa yayi yasaka hannayemsa ya zagayeni sosai yana kuma sakani jikinsa sosai. Nima sainayi luf Ina shak'ar k'amshinsa da yariga ya mannema fatarsa. Munja wasu times a haka, ni ina kuka shi kuma idonsa a lumshe yana shafa kaina da saurarena. Jiyay kawai jikinta ya saki, alamar barci ya d'auketa, sai ajiyar zuciya da take ta saukewa, bud'e idonsa yayi, sannan yakai bakinsa a hankali ya sumbaci sumar kanta dake tare da danshin ruwa har yanzu. zafin zazza6inta dake ratsa 6argon jikinsa ya sakashi fidda huci yana kuma sumbatar kanta. Dr Farida ta sanar masa babu abinda zai hanata wannan zazza6in, koda tasha magani ya sauka saiya dawo, sai idan cikin yayi kwarine maybe ta daina ma gaba d'aya, amma mai juna biyu ba'a rabata da k'ananun ciwo makamantan haka. jiyay ya kuma k'aunar Momma d'insa a ransa, a hankali ya furta I love you my Momma”. Tashi yay d'auke da Munaya a hannu, ya kwantar da ita sannan yaja bargo ya lullu6a mata. tare da sunkuya wa ya sumbaci goshinta ya shafa cikinta da hannunsa sannan ya mik'e ya koma inda yake. Ya cigaba da aikin dayake a laptop Wanda ban fahimci komaiba a ciki, tsawon lokacin yana aikin, saida ya fara hamma sannan ya kashe. bayi ya shiga ya d'auro alwala, ya gabatar da nafila kafin yay shafa'i da wutiri yaja doguwar addu'a da kirari wa Ubangijin talikai, harda hawayensa sannan ya mik'e. Ya kuma daidaita hasken fitilar d'akin sannan ya hau gadon shima ya kwanta, yay musu addu'a ya shafe cikin munaya (😂Galadima saboda tsaro ba tsoroba ko🥺). a zatona zai rungumeta, sai naga ya gyara kwanciyarsa kawai a gefenta yaja bargo shima. Galadima asuba ta gari, (ni dai rungume nawa mijin zanyi aradu🤫🙈⛹🏻‍♀). Ga bannin asubahi zazza6in munaya ya sauka, hakanne ya sakata samun dad'in barci sosai, ta kuma kanainaye Galadima, wanda shi da kansa ya mirgino har inda take cikin barci ya rungumeta, dukda zafin zazza6inta nata ratsa nashi jikin yakasa barinta. ahaka kiran sallar farko ya riski kunnuwansu. Kusan a tare suka farka, ganinsu manne da juna yasaka kowa barin jikin d'an uwansa da sauri, munaya dai kunya ta sakata juya baya, amma boss ko a kwalar rigarsa, saima tashi da yayi yana wani ciccin Magani ya shiga toilet. Alwala ya yo, baiyi mata magana ba ya fice abinsa. Munaya ta raka bayansa da harara tana fad'in Girman kai dai rawanin tsiya wlhy. tashi tayi itama ta shiga bayin, amma sa6anin shi ita harda wankan gasa jiki (lallai kinji basawa Munaya🤭, wannan gasa jiki dabaya k'arewa haka🤥😂). Fitowa tayi tanata kumbura fuska, ni dai na lalla6a na shige bayinta danna dandalo arzik'i😝 lol (koya kukace fans🤷🏻‍♀😂?). **************************** Ban sake jin d'uriyarsa ba sai around 9:30am. Tashina a barci kenan na rarrafa zuwa bayi da k'yar nayo wanka, dan banajin dad'in jikina gaba d'aya, danan ya saki sai nan ya kama ciwo. Motsin mutum naji a bayana dan haka na waiga, Galadima ne cikin Farin wando da t-shirt itam fara tas, ya d'aure k'ungunsa da Navy blue d'in belt, sannan ya kawo jacket navy blue itama ya saka, babu takalma a k'afarsa, sai dai k'afar fes tamkar ba'a takata a k'asa, sai agogon azurfa mai k'yau d'aure a tsintsiyar hannunsa. hummm dan k'yau kam dai yayishi, sai dai ni bawai ya birgeni bane😏 (ho Munaya banda zuk'i ta malli dai🤥🤣😝🙆🏻). Janye idona nayi na maida kan gyaran gashina da nakeyi. Shima baice uffanba ya wuce wajen frigate, fresh milk ya d'akko yatako gaban mirror inda nake zaune. a saman mirror ya ajiye kwalin madarar ya jingina bayansa shima, idonsa a kan gashina danake gyarawa. ya d'au madarar ya zuba a cup d'in daya d'akko tare da mik'omin. “ni ba ita zan shaba”. na fad'a ba tare da na kalleshi ba. “mikenan?”. shima yafad'a cikeda k'asaita. Yanzunma ban kalleshi ba nace “tea”. Kofin ya dire saman mirror yana tattare hannun rigarsa, “salon ki k'onamin idon abin cikin kwan kenan, to za6i ya rage naki, sha da arzik'i ko kuma d'ura”. Babu shiri na d'auki kofin na kwankwad'e, dama iyayine inajin yunwar. Kofin na mik'a masa ina 6ata fuska tamkar zan fasa ihu. Ya d'agamin gira yana fad'in “taimakon kai my friend”. Gefe nayi da fuskata ina fad'in “kai duk salon mugunta ka sani ai”. “martabar gudan jinina nake karewa”. yay maganar yana k'ok'arin ficewa. Baki na na ta6e ina harar bayansa, su gudan jini anji jiki kuwa. Ganin zai fice nai saurin cewa “nifa inason zuwa kitso, kuma zan koma school”.. Tsayawa yay cak daga yunk'urin fitar da yakeyi, Batare daya juyoba yace “babu wannan tsarin a masarautar gagara badau”. Yana gama fad'a ya ida ficewarsa. Tamkar zan fasa kuka nayi jifa da cumb d'in hannu na ina fad'in “ina ruwana dawani tsarinku ni, makaranta ta nakeson komawa ehe”. Yana jiyota amma ko'a jikinsa yaci gaba da k'ok'arin fitarsa hankali kwance. ★★★★★★★★★ Tunda Aryaan ya shigo da gudu inna ta tareshi tana fad'in “kai lafiya? minene na gudu?”. “innarmu wlhy Uncle ne yace ki shirya mana kayanmu ni da Aiyaan zai aiko gobe a kaimu wajen Auntynmu”. Inna tayi d'an murmushi kawai, dan ita bata d'auki maganarma serious ba. Su dai su Aiyaan sunata murnarsu, sun tafi d'aki sun hau had'a kaya. Babu dad'ewa da yin haka saiga daddy ya shigo da sallama, inna ta amsa masa tana gyara zama, shima zama yay kujerar dake kusada k'ofa, ganin haka inna ta fahimci da magana yazo, dan haka ta maida dukkan hankalinta Kansa. Bayani yamata dalla-dalla akan zancen da su Galadima sukazo dashi, ya d'ora da fad'in “saiki shirya dan zamuje ai miki passport”. Inna tace, “amma dadynsu nake ganin ai da kud'in kukaje kamar zaifi”. Murmushi Dady yayi, yace “Ai'sha nasan miyasa kikeso zamewa, to ai kaf cikin matan yayan kece ya cancanta kije koda ace bawai Galadima ne ya biyaba, maganar ciwo Muke bawai jin dad'i ko gutsiri tsomar wasu ba, ki shirya dan zai turo wanda zamuje immigration office d'in”. daga haka ya tashi ya fice. Shiru kawai inna tayi, itadai inda ta itace da antafi da ko innaro, dan tasan wannan tafiyar dukda ta ciwoce sai ta janyo 6acin rai a gidan. Aiko tamkar inna tasani, dan ana fad'ama innaro tace “bata amince ba, ita ta haifi auwalu kuma da ita za'aje tayi jiyyar yaronta, bazata bama kowacce mace acikinsu wannan ragamarba. Shiru baba k'arami da daddy sukayi, taci masifarta ta gama tayi shiru. Baba k'arami yace, “amma dai inna kinsan jinyar Yaya sai da matarsa a kusa, kekuma k'arfinki ya k'are ya za'a d'ora miki d'awainiyar da matansa ne keda hakki a kai?”.. “yo d'awainiya ba tare da kai za'a tafiba? Kai basai kamasa ba. ni dai fa ban amince Ai'sha tajeba, dan wlhy bazan ta6a son Ai'sha ba komi zata zama, tunda dai ta silar jikokinane balle amin ilimi. k'ilama itace ta jefeshi dan taga ta kama k'asa 'yarta Na auren d'an Sarki, t........”. “innaaaa! haba mana, dan ALLAH karma ki bari maganar nan ta fita, waishin minene laifin Ai'sha a gareki? duk cikin matanmu banga wadda take girmamaki da d'aukarki matsayin uwaba irinta, inna ya kamata wannan k'iyayyar ta koma soyayya hakanan, a baya kince dan basuda asali, kin dawo kince juya ce bata haihuwa, gashi kuma yanzu har ALLAH zai fidda jikoki daga tsatsonta, to miye kuma matsalar?”. “toko zaka shak'eni Na fad'a makane Hameesu?”. “a'a inna, ALLAH yabaki hak'uri”. “kaidai ka Sani, ni yanzu bara Na tashi Na shirya Ku kaini inama kace, imagesa nema ko uwarmi oho”. Daga Dady har baba k'arami babu Wanda ya tanka mata, tana shigewa baba k'arami ya mik'e yana cema dady “yaya ka jireta, bara naje mutafi da maman 'yan biyun, kota fito kace naje shiryawa ne”. Kai Dady ya kad'a masa yana murmushi, baba k'arami ya fita da hanzari. Bayan wasu mintuna saiga innaro an fito ana warware gyale za'a yafa, “yauwa jafaru muje Na shirya”. Habiba dake kitchen tana girki duk diramar da ake tana saurare ta tuntsure da dariya, lallai tsohuwarnan akwai daru, mama Na hanya ai, itace maganinki (gwaggo Safiyya mamarsu). Kallonta Dady yay yana murmushi, yace “to inna mu jira jafar d'in yaje shiryawa”. “ato shikenan bara kafin ya dawo nad'anci abinci, k! Habiba zubomin idan abincin nan ya tsotse, gara Na fita cikina da d'an nauyi”. Habiba ta had'iye dariyarta sannan tace “innaro bai tsotseba, amma nanda kamar dai minti 5”. “babu damuwa ai, nasan jafaru ma bai dawoba harnaci, kinsan shi da dak'undar shiri, ya tsufa amma kullum kallon kansa yake sa'ar Abdul-hameedu”. Dariya Dady ya had'iye da k'yar, yasa handkerchief yana toshe baki dan karta fito. ★★★★★★★★ Tsaf na kammala shiryawa sannan Na kimtsa d'akin, ni dukfa a nufina nayi shirin asibitine. Fitowa nayi dan naga ko yana falone, wayam babu kowa, sai sallama da nakeji a bakin k'ofar, amasawa nayi na bada izinin shigowa saboda naji muryar matane. Su 10 ciff suka shigo, k'asa suka zube suna gaisheni, Na amsa musu da 'yar sakewa, “lafiya dai?”. “lafiya lau ranki ya dad'e, mune zamu kasance hadimanki, masu miki dukkan hidima. Nifa wlhy banason wasu bayi, amma dolene Na barsu tunda wad'ancanma Galadima ne yace su tafi, yanzu kuma baya wajen, ni kuma banida ikon korarsu tinda bansan kan abinba. Amsa musu nayi da “to” sannan nawuce Na zauna a kujera. Tasowa sukai suka biyoni, a tsanake suka dinga fad'amin sunansu da aiyukan da zasuyi. Wad'anda naga bazan iya yarda suyiba Na canja musu aiki. Sallamarsu nayi, Ina k'ok'arin tashi Na shige ciki saiga Sauban ya shigo, duk zubewa sukayi suna kwasar gaisuwa a gareshi, ya amsa musu yana wani yatsine face, sai kuma ya basu izinin tafiya, fita sukayi harabar sashenmu. Na kalleshi ina murmushi, “ashe kaima dai sarautar Na jininka yaa Sauban? Wanda bai saniba saiya d'auka duk bazaka iya wani Abu daya shafi sarautaba”. Dariya yayi yana zama, “aunty gimbiyar mu kenan, wannan ai sai mijinki”. Nima murmushi nayi kawai. Ya mik'omin kayan hannunsa yana fad'in “ga break fast d'inki”.. “wayyo yaa Sauban, nikam dai nagaji da ciye-ciyennan ma, zuwa zanyi Na fara abinci da kaina”. “wlhy dakin taimakemu Aunty gimbiya, mijinki shiya saba da cin abincin waje shiyyasa bai damu ba, ya kamata kafin Na wuce gobe naci girkinki”. “kamarya gobe? Kana nufin zaka koma kenan?”. “tab da gudu kuwa, aini bazan iya zaman k'asarnanba Na tsawon lokaci, tarema zamu wuce da Abba ai, harma da innarmu, yaa Sam bai sanar dakeba kenan?”. Baki bud'e Na girgiza masa kai alamar a'a. Sauban yay murmushi, “kinsan halin Galadiman namu ai, soyake yamiki surprise maybe, yanzu hakane yaje cuku-cukun visa d'insu ne. waito miyasa bazamu koma tare da kubane?”. Murmushin yak'e nayi, nace, “maybe akwai ayyukan dabai gamaba shiyyasa”. “inaga hakanne kam, ni bara naje, yace Na iskeshi birnin gayu, ga mahfuz can Na jirana”. “ok sai kun dawo” Na iya cewa, danni daga 'yan matan masarautar har samari ba kowa Na saniba, tunda time d'in daya kamata nad'an San mutane sai muka tafi India. ni bama nason Na saba da kowa, ni da ba zama ya kawoni ba. Maganar fita da Abba da Galadima yakeyi sai yayta cin zuciyata, kimar Galadima da darajarsa saita cika zuciyata, inason mahaifana, kuma dukkan Wanda zai nuna musu kulawa bazan manta da shiba, harda 'Yar kwallata Na share, Na tashi Na koma bedroom ba tare da nayi break fast d'inba ma. ***************************** Innaro dai tun ana jiran dawowar baba k'arami harta fara gyangyad'i, habiba data kammala abincin ta d'ebo ta kawo mata, nuni Dady yay mata akan ta koma. Habiba ta koma da baya ba tare da ta k'araso falonba. Tun tana gyangyad'i harta 6ingire a kujerar barci mai nauyi ya d'auketa (ho innaronmu ta mutunci🤸🏻‍♀😜). Baba k'arami da innarsu munaya kam tuni sunyi ficewarsu, dayake Abu Na kud'i dandanan aka gama cuku-cukun komai, Nuren ne tsaye, saida komai ya daidaita suka samu visa d'insu a hannu sannan suka fito. Har gida ya maidosu ya koma suna jera masa godiya da addu'a shi da Galadima. Innaro daga gyangyad'in jiran abinci ya tsotse aka zarce da barci mai nauyi, shima Dady lalla6awa yay ya fito dan asibiti zaije. Tafiyarsa babu dad'ewa saiga gwaggo Safiyya ta iso da yaranta biyu. Hayaniyar su Dahiru ita ta tada innaro, ta mik'e zumbur tana fad'in “yauwa Jafaru kadawo mu tafi ko? Habiba bar abincin kawai idan muka dawo naci. Mi Dahiru da Naja'atu zasu ba dariya ba, suka shiga shek'ama innaro dariyar shak'iyanci. Wai kota kwanta da yunwa ne. Zaginsu ta hau yi ta d'auki filon kujera tana dukansu. Sai da gwaggo Safiyya ta musu magana sannan suka nutsu, “inna ina zakuje da Jafaru ne?”. Gyara zama innaro tayi tashiga bama gwaggo Safiyya labari. Murmushi kawai gwaggo Safiyya tayi, danta gane wayo suka mata suka gudu kawai, itama sai tace “to inna ki cigaba da jiransu, k'ila dan sunga kina barcine suka jira ki tashi sannan Ku tafi. Da wannan gwaggo Safiyya ta rufe bakin innaro ta zauna jiran su dady. Aiki🤣🤣😝. ********** Galadima daya fita kai tsaye asibiti ya nufa, su yaa hameed kawai ya iske can, dan dady ya hana matan gidan zuwa sai anjima, doctors Na complain akan suna cika wajen da yawa. Cikin mutunta juna Galadima ya gaisa dasu yaa sabi'u sannan yashiga yaga daddy. Yau kam Alhmdllh dan ba barci yakeba, kumbirin fuskarsa kuma yad'an sa6e kad'an, saidai baya iya magana sai dai yayta bin mutane da idanu. Dukda bazai iya amsawa ba haka Galadima ya risinna ya gaidashi, tare da masa fatan samun lafiya sannan ya fita office d'in doctor. Bayan sun gaisa doctor ya bama Galadima file d'in bayanan Abba dasuka tattara. Kar6a Galadima yayi ya duba, dukda bawai ya fahimci bayanan bane, ( kusan dai rubutun doctors sai su). Suka d'an tattauna akan cigaban da aka samu sannan Galadima ya fito. Ya iske daddy ya iso, suka gaisa sannan yamasa dukkan bayanan da doctor yamasa shima. Dady ma yaji dad'in cigaban da aka samu. Galadima yay musu sallama ya fito. Guntun tsaki yaja saboda yanda jama'a suka wani zuba masa idanu tamkar sunga magiji, da sauri wani dogari ya bud'e masa motar ya shiga, sannan suma suka shiga. Daga asibiti Galadima yace su wuce birnin gayu plaza. Cike da girmamawa sarkin mita ya amsa da to. Maida kansa yayi jikin seat ya kwanta tareda lumshe idanu ya fad'a duniyar tunani................✍🏼 Barkanku da juma'a💋💋💋🤝🏻. Musha weekend lafiya sisters⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀😄. *_ALLAH ka gafartama iyayen mu_*🙏🏻😭 [7/3, 9:54 AM] Aysha Galadima: *_Typing📲_* *_Haske writer's asso...._*💡 *_♦RAINA KAMA......♦_* _{Kaga gayya}_ *_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻 _________________________ _Duk marubucin daya kafa alk'alaminsa bisa takarda tabbas yagama tanadar yanda labarinsa zai kasance ne, amma sai wasu wabubuwan mamaki kaga sun gaza k'arewa a social Media, ban saniba ko samunmu available ne yakesa a kullum kuke mana kallon marasa aikinyi?, ni dai nasan time d'in dana shirya labarin RAINA KAMA ban zauna tebirin shawara da kowaba a online, inkuwa hakane tayaya wasu har suke tunanin nafara sauka akan layin labarin?, to magana d'aya zanyi a wannan ga6ar, ban gina labarin Raina kama akan kwanciyar aure bane, dan haka masu maganar munaya bata da aiki saima Galadima rashin kunya saisu jira saina kai k'arshen labarin kafin su k'alubalanceni, abin dariya, (wai aikina kenan daga nasa munaya ta murgud'a baki sai ta harari Galadima da masa k'unk'uni) tunda aikina kenan babu lallai wajen 6ata lokaci karantawa, haka Na tsara labarina tun farko kuma haka zanyi, duk wanda yaga bai masaba zai fara iya rubuta nashi shima kawai. wannan abun da kukema writer's yana 6ata mana rai, bai kamata ku dinga k'alubalantar writer's ba, bayan su suke da masaniyar yanda suka shirya labaransu, idanma zakuyi saiku ringa tanadar lokaci har zuwa bayan mun kammala, hakan zaifi tasiri fiyeda katsalandan a tsakkiyar labaran mu, akoda yaushe kuzama masu kula kafin Ku k'alubalanci mutum🤷🏻‍♀._ *Ba akan kaina kawai nayi wannan bayaninba, harda sauran writers da yawa da akema makamancin hakan koma fiye da nawa.🙅🏻* _____________________________ ~Book 2~ 👉🏻1⃣0⃣➖1⃣1⃣ ...................Koda motocin suka tsaya sarkin mota ya bud'e masa k'ofa yakai tsawon lokaci baiko motsaba, saboda tsantsar tunani da zuciyarsa ta lula, aduk sanda zuciya take cikin matsanancin matsi gangar jiki ma gazawar karfin ikon jini dana 6argo sukan mata k'aranci, shi kansa yasan yanada buk'atar mataimaki a kan wannan lamarin, amma k'arancin rik'on amana Na d'an Adam ne yake yawan gargad'arsa da taka masa birki, ba kowane zai fahimci ma'anar nok'ewar tasaba, sai mutum daya tsinci kansa a makamancin halin da yake ciki......... “Ranka ya dad'e mun iso”. Sarkin mota yasake fad'a cikin taraddadi da taka tsantsan. A hankali Galadima ya bud'e idanunsa da suka koma launin jaa saboda damuwa a kan sarkin mota, batareda yace uffanba ya ziro k'afarsa k'asa yana cije lips da had'iye wani kududun damuwa a mak'oshi. Tunda ya fito ma'aikatan wajen suketa masa sannu da zuwa, dan tunda ya shigo k'asar sai yanzu ne zai shiga cikin plaza d'in. Hannu kawai yake iya d'aga musu, amma bakinsa yay masa nauyi, kallo d'aya kuma zaka masa ka nazarci damuwa da buk'atar hutun dake tartare da kuzarinsa. A cikin plaza d'in ma bata sauyaba, d'aga hannu agaresu shine yazama linzamin amsa gaisuwar dasuke masa. Da hannu yayma d'aya daga dogaransa nuni da amso masa key. Da sauri dogarin ya amsa yana mai nufar sashen da zai kaishi office d'in Saleem mai kula da CCTV camera's. Sai dai kafinma yakai ga k'arasawar suka had'u da saleem, Wanda tun shigowar motocin Galadima ya gansa. Keys d'in ya damk'ama dogarin, sannan ya k'araso domin mik'a gaisuwa ga ogansa na wajen aiki kuma magajin garinsa. Shima d'in dai hannu Galadima ya d'aga masa, hakan kuma ya saka Saleem fahimtar akwai damuwa kenan. Koda aka bud'e ya shiga saiyayma dogaransa nuni da suje kawai, sannan ya maida idanunsa ya lumshe tareda kwanciya jikin kujerar yana lilawa a hankali. Shi kansa baisan tsawon lokacin daya d'auka a hakanba, amma tabbas yasan yashiga kudin nazari mai zurfin gaske. Knocking d'in k'ofar da akayi yasakashi bud'ar baki da k'yar ya bada izin a shigo. Nuren daya shigo ya maida k'ofar ya kulle, kafin ya ida takowa cikin office d'in, idonsa nakan d'an uwannasa. Zama yay a d'aya daga kujerun dake fuskantar Galadima, “brother what happen?”. “Northing”. Galadima ya fad'a batare da ya bud'e idonsa ba. Shiru kawai Nuren yayi shima, ya d'akko laptop a briefcase d'in daya shigo da ita, kunnawa yay, kusan mintuna biyu ya d'ago ya kalli Galadima, sai kuma ya maida kansa ga laptop d'in. “Sameer nasan kaga cigiyar da akeyi takowacce kafar yad'a labarai ta k'asarnan akan d'iyar minister, sannan jami'an tsaro tsaye suke akan binciken inda take. yakamata musan abinyi kafin lokaci ya k'ure mana”. Guntun murmushi Galadima yayi, batareda ya bud'e idanunsa ba yace “Nuren indai har babu wata waya datake aiki inda kakai yarinyarnan, kuma ka cire sim card d'in phone nata a lokacin daka d'auketa, to babu wata hanya dawani jami'in tsaro zai ganota, dama hanya d'ayace da kuskure zai basu damar bibiyarta, na d'aya lokacin daka d'auketa yazam wayarta na aiki, tabbas zasubi ta wannan hanyar su gano har iya inda ka kashe wayar, hanya ta biyu itace ka kashe wayarta baka cire sim card d'in ta ba daga phone nata, koda wayar a kashe take zasu bibiyeta ta hanyar 📡 su ganota” ya tashi zaune sosai yana bud'e idanunsa akan Nuren, “wannan hanyoyin biyu kawai ke garesu saikuma idan da camera tare da ita, idan duk babu wannan basuda wata hanya, ka kwantar da hankalinka my brother, komaina da tsarinsa right?”. Murmushi Nuren yayi, kafin ya salute d'in Galadima yana fad'in “I thrust to you my dear broth”. Shima galadima salute d'in Nuren d'in yayi yana murmushi. Komawa yay ya sake kwanciya jikin kujerar, “yanzu inaga time d'in turama minister Massage yayi?”. Cikin zaro idanu Nuren yace “baka kallon hakan a matsayin ganganci kuwa?”. Baki Galadima yad'an ta6e yana crossing k'afarsa, cikeda izzarsa yace “sai idan nabama wani damar hakan ai”. Nuren baice komaiba, dan yagama sanin hatsabibancin Galadima wajen iya sarrafa Computer, dan haka ya bar wannan zancen ya d'akko wani. “yauwa to maganar Malam Saminu fa? Kasan yana hannunmu fa har yanzu?”. “wannan barsa saiya kuma magantuwa, dan da alama yasan wani Abu, saidai akwai abinda ya sakashi za6ar 6oyewa. ni yanzu damuwar 6atan Muftahu yafi damuna, nasaka camera's jikin mutane 10 danake iya zargi a masarauta amma banga alamun da hannun koda mutum d'aya ba, hakan ya tabbatar min da gaske Muftahu na bibiyar lamarina, sai dai bansan dalilinsa ba, ko kuma waye sakashi?”. Nuren ya jinjina kansa, “brother aini da Harun dama mun dad'e da zargin Muftahu, Kaine kawai kake masa kallon mutumin kirki daman”. Lips kawai Galadima ya cije, amma baice uffanba, Nuren yaci gaba da 'yan danne dannensa a laptop d'in, zuwa wasu mintuna batareda ya d'agoba yace, “maganar Sirikinka fa?”. Shiru Galadima ya masa, saida ya mula dan kansa sannan ya murmusa tareda maida idonsa ya lumshe, “a daren jiya nagama da wannan matsalar, sim card d'insa 3, akwai Contact 300 da 38, mtn yanada mutum 172, ya fara saka credit a layin shekaru 15 kenan, ranar 3/6/2005, glo 107, ya fara amfani dashi shekaru 8 kenan, wad'annan sune Sim card d'insa da yake mu'amulla da kowa a ciki, kuma anfi saninsa da su, akwai 6oyayyen layinsa Na mtn shima, yafara aiki dashi shekaru 13 kenan, kuma mutane 59 ne kawai acikinsa, sannan ba kowane yasan layinba, dan dukkan family nashi basu San da zamansa ba, ita kanta mahaifiyar su Munaya batasan anyi saving number a phone nata ba, suma da suka kirata basusan da number a wayarta ba, dan baita6a kiranta da shiba, akwai matakan tsaro dake tattare da Layin, hakanne ya tabbatar min da akwai abinda yake 6oyewa a Sim card d'in, dan sai time to time yake amfani da shi, kiran matarsa da sukayi da layin wannan shine kuskuren farko da suka tafka da Sameer ya samu hanyar musu takun sauro. zan fara aiki akan layin na shigesu ta hanyar da basu zataba”. Jinjina kai kawai Nuren yakeyi dan mamaki, Galadima da banne, kamar yanda basirarsa take daban, ya sauke ajiyar zuciya yana kama hannun Galadima da idonsa ke a lumshe har yanzun, cikin karsashi yace “lallai kai RAINA KAMA ne Sameer”. Murmushi kawai Galadima yayi, amma baice uffanba. Knocking akayi, Nuren ya kalli k'ofar yana bada izinin a shigo, Sauban ya shigo da sallama, su duka idonsu a kansa, Nuren yace “lafiya kuwa?”. Zama Sauban yayi yana sauke Numfashi da k'yar, cikin magana d'ai-d'ai da alamar a birkice yake yace, “wlhy Yaya binmu aka ringayi da wata bak'ar Jeep, da k'yar mukasha wlhy, ni dai yau zanbar k'asarnan gaskiya”. Sauban ya fad'a tamkar zaiyi kuka’. Gani kawai sukai Galadima yana dariya, saida yayi mai isarsa sannan ya tsagaita. Nuren da Sauban suka tsaya kawai suna kallonsa. Tashi yayi tsaye yana takawa cikin izzar k'asaita, ya dafa bango yana lek'en waje ta window d'in office d'in, yakai wasu adadin lokuta a wajen, sai kuma ya juyo yana kallon Nuren d'in da Sauban da suma suka zuba masa idanu. “my dear brother! daka tsaya sun kamaka ai, tabbas da wannan shine kuskuren da zasuyi Wanda bazasu ta6a mantawa da waye Muhammad Sameer Saifudden ba a tarihin rayuwarsu. Waya gaya maka kana yawo cikin 9ja ne batareda idon Sameer ba a kanka?”. Sauban ya sauke ajiyar zuciya yana share gumin daya jik'a fuskarsa, “wlhy yaa Sam daka fad'amin da bazan tsorata ba”. Daga Galadima har Nuren dariya suka kwashe da shi, Nuren ya dafa kafad'ar Sauban yana fad'in “matsoracin banza”. “uhm-uhm yaa Nuren bazaka ganeba wlhy, tsoro halak ne fa”.. Galadima dai baice komaiba ya koma ya zauna yana murmushi. ★)))*(((★)))*(((★)))*(((★)))*(((★ Ganin har anyi sallar Magriba babu baba k'arami balle Dady ya saka Innaro d'aukar gyale ta fito, lokacin gwaggo Safiyya tana salla, shiyyasa batasan innaro ta fitaba, habiba da Naja'atu dake tsakar gida suna tattare kaya saboda hadari na farkon damina dayake nuna alamar zai zubda ruwa. suka kalli juna, Naja'atu tace “yaya habiba tsohuwarnan fa bata da dama wlhy”. Dariya habiba tayi, “ai kad'anma kika gani Naja'atu, yanzu dai zataje ta tadama baiwar ALLAH hankali”. “to ALLAH ya k'yauta”. ‘cewar Naja'atu tana rik'e ha6a’. Lokacin da Innaro ta shigo gidan d'akin Innarsu Munaya ta nufa kai tsaye, sai dai ta iskeshi rufe, kwala kiran sunanta ta shigayi cikin masifa, “Ai'sha!! Ai'sha!! Nasan kina jina, wlhy ki fito kafin yau d'innan igiyar aurenki ta tsinke”. Mamansu yaa Hameed da gwaggon Haleematu ne suka fito, mamansu yaa hameed tace “aiko tafita fa inna, dan gab da magribar nan naga Fadeel ya shigo sun fita, bansan mike faruwa ba dai”. “yaza'ayi kusan mike faruwa tunda anyi k'ulle-k'ullen munafunci, lallai jafaru, wai yau da kaine za'a muzantani hannun mak'iyana, to nikuma naga ta yanda Ai'sha zataje wata k'asa jiyyar Auwalu da raina”........ haka taita zuba banbamin masifa matan gida na saurarenta, daga daddy har baba k'arami suna gidan amma sukak'i fitowa. Jarabar Innaro ta saka kowa na gidan fahimtar mi ake ciki, nanfa hassada da bak'in ciki suka kume zukatansu, dukda kuwa sunsan tafiyar bata dad'i baceba, maman fauziyyace kawai hakan yamata dad'i, koba komai inna ta huta da cin zarafin Innaro koyayane. Sai da Gwaggo Safiyya ta shigo tama Innaro magana sannan ta tafi gida, su matan gidanma sai yanzu suka San da zuwa gwaggo Safiyya d'in. Amma sunso ace innarsu munaya na gida Innaro tayi wannan rashin mutuncin. Hummm😕. **************************** Bayan fitowar su Galadima daga birnin gayu, sun wuce gidane, Nuren kuma yakoma hotel d'in daya sauka. Galadima kawai ne ya shiga sashensu, amma Sauban 6angaren mai martaba ya nufa neman yarima Mahfuz. Munaya na zaune a falon farko tareda sabbin kuyanginta guda uku, (dan bata amince su shiga falonta ba, saita gama tantance su sannan) ba wani hira sukeyiba, d'ayace a cikinsu ke sak'a shine abin ya birge Munaya take kallo, tana kwance cikin doguwar kujera ne, yayinda su kuma su ke zaune a k'asan lallausan carpet d'in falon. Dogarai biyune suka fara shigowa hannunsu d'auke da ledoji, sai kuma mai gayya mai aiki Galadima. Da sauri bayin suka mik'e tsaye, saida ya ida shigowa sannan suka d'urk'ushe a k'asa suna kwasar gaisuwa. A la66ansa ya amsa yana d'aga musu hannu, yayinda idanunsa ke kan munaya da itama ke satar kallonsa Duk d'insu kowa janyewa yayi, yayinda bayin da dogaran suka fice bayan sunkai ledojin falon Galadima. Baice da ita uffanba yafara takawa zai shige, tamkar mai tsoron fad'a tace, “sannu da zuwa”. Ysayawa yayi cak, sannan ya juyo da kansa tamkar mai ciwon wuya ya kalleta, bata yarda sun kuma had'a idoba takuma fad'in “nagode sosai”. “for what?”. ‘ya fad'a cikin isa’. Shiru munaya tayi, ta kasa cewa komai. Shima bai sake cewa komai ba ya taka ya shige abinsa. Harara munaya ta raka bayansa da shi, sai kuma ta sauke numfashi tana tashi itama, bedroom d'inta ta koma, a saman sofa ta zauna tana dafe kai, sosai take buk'atar zuwa sake duba mahaifinta, amma ta kula Galadima bashida niyyar cemata taje, kai itako wannan wane irin abune haka? shi dama gidan Sarautar haka yake bakada 'yancin kanka?, komai saida k'a'ida. tun d'azu kuma take kiran number inna bata d'agaba, tadai kira baba k'arami da daddy sun gaisa ta tambayi jikin Abba, shine ma har suke kuma sanar mata k'ok'arin da galadiman keyi. tabbas hakan da yayi yasata jin farin ciki, koba komai tasan shi adaline, ko anan gaba ragamar shugabanci ta riskesa zaiyima na k'asa da shi adalci. Galadima daya shiga tun a falo yafara k'ok'arin cire navy blue d'in jacket d'insa, ya wullata saman kujera, sassauta belt d'in yayi shima amma bai cireba, ya zauna cikin tsantsar nuna gajiya yana furzo iskar bakinsa, remote ya d'auka ya kunna tv, tamkar ya saita lokaci saiga hoton d'iyar minister mai amsa sunan Farhat ana nunawa, an saka 2.5 millions ga dukkan wanda ya kawota koya bada bayanan sirri akan wanda yasan wani Abu akan 6atanta. Wani mugun tsaki Galadima yaja a zuciyarsa yana fad'in wawaye, saiku k'ara yakai 100millions ba 2 ba, idan ubanta ya shirya kawo kansa gareni nima a shirye nake nabashi shashashar 'yarsa mai zubin ta6arya, ya kashe TV d'in kawai ya mik'e ya shige ciki. Ko ina fes da shi, yasan baida Matsala da Sauban a 6angaren tsafta dama. kayan jikinsa ya ida cirewa ya shiga wanka. Bayan ya fito samu yay yad'an kwanta, dan ya samu Hutu kona 2hours ne, dan yanzu akayi sallar zuhur. aiko kwanciyarsa babu dad'ewa barci yay gaba dashi. Munaya ta jawo wayarta da nufin kuma kiran inna, amma sai taga Ashe credit d'inta yama k'are, kanta ta dafe dan haushi, zuwa can tamik'e domin bin shawarar zuciyarta. turare ta kuma fesama jikinta ta d'auki gyale ta yafa. Ta d'an dad'e a k'ofar d'akin tana tunanin idan kuma ta shiga hasashenta bai zama gaskiyaba ya kenan?, wata zuciya tace kije abinki k'ilama wanka yake. Da sand'a na ida shiga tamkar wata 6arauniya, sai kuma na tuna ai yanada CCTV camera, nutsuwa nayi na daidaita kaina, na koma normal saboda tsaro. Ganin babu abinda naje nema d'in a falo saina zarce bedroom ina wani ciccijewa. Mamaki ya kamani ganinsa kwance a kan gado yana shak'ar barci hankali kwance, hakan yamin dad'i kam. Saida nabi ko'ina na bedroom d'in da kallo, ganin babu alamar akwai camera a nan saina ida shiga, wayoyinsa biyu na ajiye gefen filon dayake kwance, rabin hannun damarsa ma nakan d'aya ya d'ora cikin barci halan?. Dole saina hau saman gadon, dan haka na tsaya tunanin yanda zanyi, banida wata mafita dan haka nahau a hankali, kai kace wata hawainiya ce. Cikin rintse ido da cije la66a nakai hannu zan d'auki wayar d'aya. Caraf aka rik'emin hannu, babu Shiri na bud'e idona zuciyata nawani tsitstsinkewa. Fisgoni yayi na fad'o jikinsa, zafin danaji ya sakani sakin k'aramar k'ara. Ya matseni a jikinsa batare da ya kula miya aikata ba. nikam jikina sai rawa yakeyi, tsorona karya d'auka ko cutar da shi zanyi ma........ maganarsa cikin yanayin barci ta Sani kallonsa. Kad'an ya bud'e idonsa dake jajir, alamar da gaske barci yakeyi, muryarsa a sark'e irinta barci yace, “sata kika koma?”. Baki na tunzuro ina marmar da idanu da suka cika da kwalla, nace “ALLAH ya kiyaye, arafa zanyi”. Kuma matseni yayi har saida na rik'e hannunsa,, yace “wannan ba aro bane sata ce yalla6iya, dan haka dolene ki kar6i punishment”. Jin ya ambaci punishment saina kuma rikicewa, nahau k'yarma ina rantse-rantae da matso kwallan idona. Bai wani saurareni ba ya hau sumbatar wuyana, tureshi nafarayi amma saina gaza, dan haka na koma mintsini, shima a banza man kare😩. Dukna d'auka wasa yakeyi kawai farfaganda Ce danna tsorata, amma saina tsinci ya fara sakin layi, iya yina da rok'o, yakushi, mintsini, ban samu ku6uta ba, saima salonsa yafara tasiri a kaina, nima nai luf harda k'ok'arin maida murtani. saida naji zai kama wata tashar nai azamar tsaidashi ta hanyar fad'in “please yalla6ai camera”. Maganinki ai baby😝, su Galadima akwai bak'in wayo dai🤥😂, idan ta gaskiya za'abi ni banga abin punishment anan ba🤣, dama yadawo 'Yar matsalarsa dai tsautsayi ya kawo mai karanbani dason banza ta fad'a tarko😜🥳😆. **********★******** Koda inna ta dawo saita had'ama su Aryaan kayansu, da nufin su koma wajen mamansu yaa hameed harta dawo. Amma suka tibire akan bazasu jeba, su Uncle yace zaizo ya kaisu wajen Auntynsu. Tun inna na lallashinsu harta kai ga mammakesu suka fara kuka, daga nan sukai barcin dole. Bata fasa had'a kayanba, tagama tsaf ta d'auki akwatin zuwa d'akin mamansu yaa hameed. Su Bintu kawai ta iske a falo suna kallo, Aminu ne yace “innar 'yan 2 ina zaki da daddare?”. Murmushi inna tamasa tana fad'in “kayansu Aryaan ne Aminu........” Bata gama rufe bakiba mamansu yaa hameed ta fito. ganin innarsu munubiya da kaya saita had'e fuska. Inna bata damuba tace “ga kayansu Aiyaan, saisu dawo nan da zama kafin na dawo”. “to”. Kawai mamansu yaa hameed tace tana kauda kai gefe. Ran inna ya sosu, amma sai batace komai ba ta ajiye ta fice jiki a sanyaye. Da murnar Haneeff ya tashi zai d'au jakar yakai d'akinsu, amma sai Maman ta watsa masa harara. babu shiri ya koma ya zauna. Jakkar dai sai anan ta kwana, bata d'auka ba, bata bar 'ya'yanta sun d'auka ba saboda bak'incikin inna zataje jiyyar Abba ba itaba. ALLAH ya k'yauta😡. **************************** Dakatawa yay daga abinda yakeyi, ya bud'e idanu a hankali akan fuskata, murya k'asa-k'asa ya furta “camera?”. Kaina na d'aga masa batareda na bud'e idoba. Bai kuma cewa komai ba ya koma ya kwanta yana furzar da huci mai zafi daga bakinsa, sai kuma ya cije lips yana gyara kwanciya da sake rungumeni kawai. Idona na bud'e a tsorace, azatona zai cigaba ne, sainaga ba haka bane. A cikin kunnene ya furta “barci please”. Kallonsa nayi ta gefen ido sai naga idonsa a rufe, nima banida za6in daya wuce na rufe nawan, dan haka na lumshe kawai. Ni sai barcin ya d'aukeni, amma shi ya k'auracema idonsa, mamakin furicina ya dami zuciyarsa, dama yadad'e yana zargin akwai camera a d'akin nan nasa, sai dai bawai ya tabbatar bane, kuma bai ta6a yunk'urin dubawa ba. da wad'annan tunanin ya cinye lokacin barcinsa har aka kwala kiran sallar la'asar. Bud'e idanunsa yayi akan fuskata, yad'an tsuramin ido nawasu time's, sai yaga barcin yamin k'yau, kauda idonsa yayi cikeda basarwa, saikuma ya janyeni daga jikinsa yana yunk'urin tashi, hakanne ya sakani farkawar nima, na tashi da hanzarina ina gyara rigata, sai kuma na sauka na fice batareda nako waiwayoshi ba. Bina yay da kallo harna fice sannan ya janye yana ta6e baki. Ban kuma jin labarin Galadima ba har dare yayi, nafito wanka ina shirin barci ya shigo, yau dai babu laptop d'in kaddara, dagashi sai phone guda d'aya ma, yana sanye da kayan barci kalar gwaiduwar kwai masu duhu. Zama yay a kujerar dake cikin d'akin, yayinda ni kuma na k'arasa saka hijjab d'in dana jawo, babu walwala ko alamar wasa kwata-kwata a face nashi, dan haka nima saina kama kaina. cikin k'asaitarsa yace “muyi magana mana”. Kallonsa na d'anyi, saikuma na amsa da “ina jinka”. d'ago ido yay muka kalli juna, da ido yay min nuni da bakin gadon. Ban musaba nazo na zauna, amma sai nayi k'asa da kaina ina wasa da zoben hannuna. Maida kallonsa yayi ga zoben danake jujjuyawa, kusan mintuna 4 harna d'auka ya ma fasa maganar, na d'ago na kalleshi. Ya kauda kai gefe yana fad'in, “waya fad'a miki da CCTV camera a d'akina?”. Nima ban kalleshi ba na bashi amsa a tak'aice, “bakai ka saka kayarka ba danni?”. Da mamaki ya kalleni, sai kuma ya kausasa muryarsa, “Munaayaa seriously nake miki magana!”. nad'an razana, amma saina dake, nace “kana nufin bakasan da itaba?”. “idan nasan da ita mizai sani aikata wani Abu na sirrina a d'akin”. da mamaki na kalleshi domin tabbatarwa, tsantsar gaskiya na hanga a idonsa, dan haka na danna yatsun hannuna da k'arfi suka bada sautin “k'asss!, k'asan zuciyata na tunanin minene sirrin nasa?”. Idonsa a kaina ko k'yaftawa bayayi, nima na d'ago mukaima juna kallon ido cikin ido, dukda tsorata danai da hango masifa cikinsu ban janyeba, nafara fad'in “tabbas naga camera a falonka, tana nan saitin hotonku kaidasu momma, inda flower d'in nan take, hakanne yasani zargin kai ka saka kayarka saboda tsaro”. “hummm”. kawai yafad'a yana janye idanunsa, sai kuma ya taso ya dawo inda nake zaune, ganinai kawai ya rungumoni jikinsa, na waro idanu dan mamaki, shikuma ya lumshe nasa tareda sumbatar goshina a hankali, shigar sumbarce tasakani lumshe nawa idanun nima tareda k'ank'ameshi. Cikin kunnena ya furta “i'm proud of you my friend”. Da sauri na waro idanu ina kallonsa, saiya d'agamin gira d'aya yana wani miskilin murmushi, sannan ya tadani zaune shima ya tashi ya fita. Baki da idanu da hanci duk na saki ina binsa da kallo, a k'asan raina ina tambayar mike damun guy d'innan ne wai?. Banida mai bani amsa, dan haka na mik'e na cire hijjab d'in nai kwanciyata. d'akinsa ya koma ya d'akko wani Abu kamar k'aramar ball🎱 ya ajiye saman table d'in gaban gadon, sannan ya manna wani dogon Abu a jikin 'Yar ball d'in, ya d'akko laptop d'insa ya kunna. shiru na kusan mintuna uku ya k'urama abinnan ido, zuwa can yafara wata k'aramar k'ara d'i! d'i! d'i!, sai kuma k'aramar danja ajikin abinda ya manna d'in shima tana kawo haske jaa da d'aukewa. Murmushin takaici kawai yayi, a zuciyarsa yanama ALLAH godiya dabai ta6a kusantar Munaya a d'akin nanba. dan tabbas ga CCTV camera ya gani a d'akin, an sakatane can ta saman wardrobe, yanda ko alama hankalinsa bazai kaiba, baiyi yunk'urin cirewa ba, ya d'auki kayan aikinsa ya koma parlour, dan yaga itakuma tanan a ina take?. yanama shigowa tun'a k'ofar tsakanin bedroom da falon ya gani, baima k'arasaba ya koma ciki, kashe laptop d'in yayi ya d'auke k'aramar ball d'in ya 6oye. Duk wannan hidimar da Galadima keyi Sauban na kwance bisa gadonsa yayi d'ai-d'ai yana kwasar barci. Gyara masa bargo yayi saboda tasowar hadarin farkon damina da iska tafara kad'awa sanyi ya busa. daga nan ya kashe masa fitila ya fita zuwa d'akin Munaya. Ita harma tayi barci, tana k'ank'ame da fillo saboda sanyin hadarin dake busawa, gadon ya hau tareda warware bargon ya lullu6a musu. dai-dai iska ta taso mai azabar k'arfi, a rikice Munaya ta juyo ta k'ank'amesa saboda tsorata. Rik'eta yay sosai yana fad'in “uchh! Karki karyani”. Babu shiri munaya ta bud'e idonta, tana k'ank'ame da shi tace, “wai miyasa bazaka ke kwana naka d'akinba ne?”. “k miyasa time d'in da kikaje India kika gajemin d'akina?”. Shiru tamasa bata amsaba, amma yanajin alamar murgud'a bakinta akan k'irjinsa. “punishment ya tabbata agareki yalla6iya”. Da sauri nace “wlhy a'a, inba hakaba zaka koma saman sofa ne, ai kaima haka kamin a d'akinka”. “uyim Madan tsiwa, to ai nima dankar ki murk'ushemin abin cikin kwan cikin barci yasani kwantawa anan?”. Zan bashi amsa aka kwad'a wata tsawa data sakamu ruk'unk'ume juna babu shiri, sai kuma ruwa ya 6alle. Da wannan damar Galadima yay amfani wajen canja salon kwanciyar tamu, tun ina nuna banaso har salonsa ya sakani sakin layi, (😆anya munaya wannan cikin naki bashine tarkon da Galadima ya d'ana miki ba?😜). Da asuba tashi nayi inata zum6ure-zum6ure, baice dani uffanba yashiga toilet ya tsarkake jikinsa. Bayan yafito nima na shiga. Baki ya ta6e yana wani d'age gira d'aya tamkar ina kallonsa ya fice. Saida nasha kukana sannan nayi wankan tsarki, narasa mike sakani biyema Galadima? insha ALLAH zan d'auki mataki (🤣idan babu abin cikin kwan ba😂, nasan inhar yana nan babansa zaita samun bonus😜). Bayan na idar da sallar ban koma barciba, saina gyara d'akin nayi wanka, shirin fitarma na sake yi yau, dan baba k'arami yacemin k'arfe goma na safe zuwa 11 zasu tafi. Kammalatawa kenan ya shigo, ko kad'an banji alamar shigowarsa ba, saida na gama fesa turare ina k'ok'arin ajiyewa na hango kamar mutum tsaye a bayana. Da sauri nayi azamar juyowa, dayake yana gab dani kad'an ya rage na fad'a masa a jiki, na dai samu nad'anyi baya na jingina da mirror ina tura baki. Ko motsi baiyiba shikam, bai kuma janye idonsa daga kallona da yakeba. Haushi ya kamani, nima nabi jikin nawa da kallo kozanga abin da yake kallon, ganin babu wani Abu daya faru na d'ago na kuma kallonsa, “wai yalla6ai mi kake kallone haka?”. d'an yatsansa d'aya yasaka yad'an shafi girarsa yana gyara tsayuwa, “abin cikin kwan mana”. ‘ya fad'a cikin basarwa’. “ta gefensa na ra6a zan wuce ina fad'in “ai lokaci kad'an ya rage maka ka bar ganin nasa”. Da sauri ya rik'o hannuna, na juyo muka kalli juna, mayun idanunsa ya saka cikin nawa, “kina zaton idan nabar ganinsa kema za'a cigaba da ganinki?”. Guntun murmushi nayi ina janye idona daga cikin nasa, nace “kana zaton kasheni zakayi nima?”. “cire maganar ma zato”. Kallonsa na kuma yi, cikin yanayin da shi kansa bai ta6a zaton ina dashiba nace “saika fara shiri”. Shima a dake yace “dama a shirye nake kullum”. Na murmusa ina k'ok'arin cire hannuna daga cikin nasa, amma ya hanani damar hakan, kallonsa na kuma yi nace “ko har lokacin yayi ne?”. Fisgoni yayi na koma da baya, ya mannani jikin mirror d'in tare da maida hannuna baya ya rik'e, ya matseni da jikinsa, fuskarsa gab da tawa tamkar zai had'a bakinmu, yayinda idonsa ke cikin nawa, wani miskilin murmushin gefen baki yayi, yasaka yatsansa yana zagaya janbakin dake kan la66ana a hankali, cikin muryarnan tasa mai kama da an masa dole ya fara magana cikin karsashi “ko Ubangiji yakanyi hukuncine ga bawan daya bijirema umarninsa, koda ace zubarda wannan cikin kikayi dolene saikin kuma d'aukar wani, zubar da shi na dai-dai da haihuwar yara goma anan gidan kafin na aikaki inda shima ya tafi” ya matsa la66ana da k'arfi, wani zafi ya ratsani saiga hawaye a kumatuna, murmushi yayi, yasaki la66an ya dangwali hawayen a d'an yatsansa, nunamin yay yana fad'in “lallai momcyn abin cikin kwan kin cancanta 100%, amma bayan abin cikin kwanfa akwai k'annensa, please bar kuka my dear friend”. ‘ya k'are maganar da sumbatar la66ana sannan ya sakeni yaja baya. Koda ya sakeni sainayi murmushi kawai, sannan na juya ina fuskantar mirror, foda na d'auka na gyara fuskata, na sake saka jambaki kad'an kamar yanda na saka d'azun. Tsayawa yay cikeda mamakin abin da nayi na ko inkula yana kallona, mi wannan yarinyar take shiryawa ne haka?..... Kafin ya samu amsa Na juyo gareshi, fuskata d'auke da murmushi na ra6a zan wuce sa, bina kawai yay da kallo, naje gaban wardrobe na bud'e, alk'yabba na d'akko na sanya, sannan na d'auki handbag ina kallonsa har yanzu fuskata d'auke da murmushi. Gira ya d'agamin shima yana wani k'asaitaccen murmushi, ya juya ya fita batareda yakuma magana ba. Yana fita na sauke ajiyar zuciya ina dafe k'irji, wlhy ni kad'ai nasan dukan da zuciyata takeyi, kad'an yarage ya ranfo a tsorace nake, kalamansa ne suka shiga dawomin cikin zuciyata, mi wannan yake nufine wai..........? “Shin bazaki bane?”. Muryarsa ta daki dodon kunnena, da sauri na gyara yanayina na d'ago muka had'a ido, Ashe yana bakin k'ofar bai tafiba. Bance komai ba na biyo bayansa. A falon farko na iske kuyangina suna gaidashi, hannu kawai ya d'aga musu ya fice abinsa. Tsayawa nayi muka gaisa, d'aya a cikinsu ta yunk'urin k'ar6ar handbag d'ina. Na iske harya shiga mota, nima aka bud'emin na shiga, handbag d'ina ta mik'omin tana fad'in “ranki ya dad'e ana buk'atar rakkiyarmu ne?”. Murmushi namata, na juya na kalli Galadima danjin mizaice, kansa ya girgiza alamar a'a. Juyawa nima nayi na girgiza mata kai, tamana addu'a tana rufe k'ofar. Tunda muka tafi babu wanda yace uffan, yanata latsa wayarsa. Airport muka nufa kai tsaye. Bayan motocin sun tsaya sarkin mota na yunk'urin fita yace “2 minutes ”. Sarikin mota yace “to ranka ya dad'e”. Ni ban fahimci mi suke nufiba, naga dai sarkin mota ya fita mukuma ba'a bud'e mana ba, sai kawai nakai hannu zan bud'e. Hannuna ya rik'o, na juyo ina kallonsa, har Yanzu idonsa nakan waya,, ajiye wayar yayi ya juyo yana fuskantata, ina yunk'urin tambayar lafiya naji la66ana cikin bakinsa. Ya salam, na fad'a a zuciyata, saida ya shanye janbakin la66ana tas sannan ya sakeni. yanda kukasan gunki haka na koma masa, ya buga yatsunsa biyu saitin fuskata suna bada k'arar d'as d'as yace “gargad'i, first and last dazanganshi abakinki yayin fita”. Harya fita ban iya motsawa ba, saida aka bud'e murfin 6angaren danake sannan na iya sauke numfashi, na kasa fahimtar damuwar guy d'innan kwata-kwata. fita nayi nima, yana tsaye yana jiran fitowata. a tare muka jera muna tafiya, yayinda dogaransa ke take mana baya. ya wani miskile fuska tamkar bashine yagama ta6argaza ba a mota yanzun. Mutane sai kallonmu suke, masu gulma nayi masu nunamu nayi, ni dai duk sainaji wani iri, shima tsaki yayi danya tsani kallo. A mamaki na duk sai naga 'yan gidanmu ma a wajen, gaggaisawa muka shigayi, muka rik'e hannun juna nida munubiya muka k'arasa inda innarmu take, gaisheta nayi, nace “su Aiyaan fa?”. “suna gida zasu zauna da mamanku mana”. “kai innarmu, ya zaki barsu wajen muguwarnan, bama gara Maman fauziyya ba komu suzo wajenmu”. Murmushi kawai innarmu tayi, tace, “ashe bazaki canjaba Munaya?”. 6ata fuska nayi, ina fad'in “kai inna, duk canjawarnan danayi”. Murmushi sukayi itada Munubiya. akuma dai-dai time d'in Ambulance ta shigo airport d'in, sai mota biyu a bayanta sai motar police guda d'aya. Gaba d'ayanmu hankalinmu saiya koma can, Galadima ya k'arasa wajen Ambulance d'in, yayinda sauran motocin biyu Sauban da Nuren baba k'arami Dady ya Shafi'u da yaa Naseer yaa hameed suka fito. Zuwansu baifi da mintuna 15 ba aka fara kiran sunan wad'anda zasu tashi a jirgin. Sai kuma ma'aikatan wajen mutum uku suka iso wajen Ambulance d'in aka fara k'ok'arin fidda Abba. Hankalin jama'a da yawa ya tashi a airport d'in nan saboda tausayin Abba, mukam kuka ma wasunmu sukeyi ai, muna kallo aka gungura gadon da aka d'oroshi har zuwa ga jirgin. Suma su innarmu suka shiga itada baba k'arami da Sauban. Rungume juna mukayi nida munubiya muma muna kuka. Galadima bai fito cikin jirginba saida yaga komai ya dai-daita. yana fitowa babu dad'ewa jirgin ya d'aga zuwa sararin samaniya, yayinda mukuma muke binsu da addu'oin fatan alkairi da samun sauk'i.................✍🏼 🤥kutt harda na gobe nayi🙄⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_* [7/3, 9:54 AM] Aysha Galadima: *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻1⃣2⃣ ...............Maman Fauziyya tamatso ta kama hannunmu ni da Munubiya tana lallashinmu, da fad'a mana mu bisa da addu'a, insha ALLAHU da k'afarsa zai dawo. Ganin mun fara shirin tafiya na taka inda Galadima yake tsaye da Nuren suna magana, tun d'anzun ina lura dashi ya kafeni da idanu, yanzunma suna maganar amma idonsa na kaina na k'araso garesu. Nuren daketa fara'a yace, “gimbiyarmu barka da hantsi”. Murmushi nayi sannan na gaisheshi, ya amsa yana tambayata yaya jikina?. Nace “Alhmdllh na warke ai”. “to ALLAH ya k'ara afuwa gimbiya”. ‘yafad'a yana matsawa gefe domin bamu waje. Galadima dake kallona hannunsa duk biyu cikin wandon sky blue d'in shaddarsa da tsawon rigar iyakarsa rabin cinyarsa, yace, “Lafiya?”. Dakewa nima nayi, cike da jan ajina nace “k'alau. Dan ALLAH zanbi Munubiya please yalla6ai”. Janye idanunsa yayi daga kaina yana fad'in “awane farashi?”. “kamarya farashi? ciniki mukeyi?”. Hannunsa d'aya ya fiddo daga aljihu ya shafa sajensa zuwa gemu, cikin kafeni da idanu yace “kusan haka, kinsan rayuwar bani gishiri in baka manda akeyi yanzun”. Cikin son tura masa haushi nace “Ai ni bana gane Hausa cikin hausa”. “really? lallai kin fad'o kuwa, kuma saiki ce ke bahaushiyace?”. Baki na tunzura masa saboda haushin rainin wayon da yake min, gasu Munubiya kuma shirin tafiya sukeyi. “Kinsan wannan bakin kika bari na kamashi a airport d'innan....., hummm”. Idanuna na waro, “mi kake tunanin zakayi kenan?”. “kuma turowa saina nuna miki”. ‘yafad'a yana matsowa’.. Baya na matsa da sauri zuciyata na harbawa, anya kan Galadima d'aya kuwa?. Kwafa yayi yana kallon agogon hannunsa yana k'ok'arin zaro waya daga aljihun gaban rigar datake ring. Nikuma na hararesa a zuciyata ina fad'in mara kunya ai nasan zaka iya. A fili kuma nace “please yalla6ai nidai badan halina ba”. Bai bani amsaba, sai sallamar danaji yayi wayarsa akan kunne. Jinai kawai yace, “Harun kana inane?”. Bansan wace amsa ya bashiba, naji yana fad'in “ok idan ka tashi saimu had'u”. daga haka ya yanke wayar sannan ya kalleni. “uhm mikike cewa?” Haushi tamkar zai karni nace “please mana autan Momma”. Murmushi yayi yana cije lips, “wlhy yarinyarnan kin gama rainani, ninema Autan?”. “lah nama manta ashe kaifa na tsakkiyar momma ne, karma Yaa Sauban ya jini”. “kinsan ALLAH na damk'eki a airport d'innan saikin fad'amin dawa kike”. Dariya nayi ina d'aga masa yatsu biyu, “karka damu yalla6ai zanyo maka tsarabar sweet and biscuit yeah”. Da sauri yay yunk'urin damk'o hannuna ganin zan gudu. yana rik'owa mukaji ance “hallo”. A bayanmu. Batareda ya saki hannuna ba duk muka waiga ni da shi. Matashiyar budurwa fara k'al, kuma k'yak'yk'yawa masha ALLAH. Dan danan ya tsuke fuska, tamkar ba shine yagama murmushiba yanzun. Nima bansan murmushi ya gushema tawa fuskarba, baiyi magana ba, sai nice nace “lafiya kuwa?”. yanda nayi maganar cikin rainin hankali yasaka yarinyar rik'e ha6a tana ta6e baki tana fad'in “ke kuma fa?”. Kamar zanyi magana saikuma Na shareta kawai, galadima Na kalla fuskata a cunkushe alamar fushi, d'ayan hannunsa ya d'agamin yana ta6e fuska alamar shifa babu ruwansa. Na tura baki tareda juyawa zan bar wajen. Hannuna dake cikin nasa ya kuma damk'ewa da k'yau, hakan yasani dawowa baya tamkar zan fad'a jikinsa, amma nayi jarumtar tirjewa kodan jama'ar gidanmu. Dama ajikin wasu motoci muke, sai kawai ya fisgi hannuna muka shige tsakkiyarsu ya mannani jikin mota shikuma yamin rumfa. ban ankaraba naji bawan ALLAHnnan ya ha.......🤥. Jikina kawai rawa yakamayi saboda tsoro, wlhy ban ta6a tunanin da gaske yake zai iya hukunta bakin nawa a airport d'inba. Ita kanta budurwarnan idanu ta zaro waje cikin wangale baki. Nuren dashi kad'ai yake saitin dazai iya ganinmu saikuma wasu tsirarun mutane dake nesa damu, wad'anda ba lallaine ma su fahimci abinda akeba, kaucewa kawai yay daga wajen yana tuntsura dariya. 'Yan gidanmu sunga lokacin da Galadima yaja hannuna muka shige tsakkiyar motocin, amma basa hangomu. tsabar gulma irinta mamansu Yaa Hameed da Momy da Maman Safara'u sai suna shiga k'ok'arin son ganin mi mukeyi a wajen?😱 su duk tunaninsu wata maganar banza nama budurwarnan yake shukamin rashin mutunci Dan duk agaban idonsu tazo wajen har rik'omin hannu da yayi, dukda basa jin mi Muke fad'a Dan muna nesa dasune. Yaa Sabi'u dabasu lura da abinda ke faruwa ba suka Shiga musu maganar INA zasuje? suzo su ajiyesu gida sufa wajen aiki zasuje. Ina basu saurareshiba saida sukazo saitin dazasu iya ganinmu. A tare suka zaro idanu, Baki da hanci, duk sun shiga mamakin ganin Galadima Na kissing d'ina, ai babu shirin suka koma baya zukatansu Na tukuk'i da jifanmu da kalmar 'yan iska fitsararru. (🤣Yo wayace kuje gani? kazantar dabaka ganiba sunanta tsafta😏😜). Yana Sakina kunya tasakani fad'awa k'irjinsa Na 6oye fuskata, hannayensa yasaka ya zagaye bayana yana dallama yarinyarnan wata muguwar harara data saka hanjin cikinta kad'awa, babu shirin tabar wajen tana mak'yark'yata da tunanin Galadima ko dai kurmane da gaske. Driver d'inta dake kallon komai tun d'azun ya tuntsure da dariya yana fad'in ALLAH ya k'ara, bana fad'a miki Shiba Na wasan yara bane ba, banda jaraba kinbi kin nanik'ema bawan ALLAH daga had'uwa a jirgi, kinbi kin addabi rayuwata saina nemo miki number sa, aini nama godema ALLAH da kuma sake had'uwa ya kuma nuna miki ainahin halinsa, saida Na fad'a miki baima dad'e dayin aureba, ke gadararriya kikace aurensa bai damekiba........ Yanda ta daka masa tsawa yasakashi firgita ya russuna yana Neman afuwarta. Cikeda masifa tace “tada mota mukoma gida”. “Amma ma'am kin manta jirginku yakusa tashi?”. A tsorace yayi maganar. Harara ta Dalla masa tace “Ubanka ne ya viyamin kud'in jirgin”. Wasu yawu masu rad'ad'i driver ya had'iye yana girgiza mata kai, ya bud'e motar ta Shiga sannan ya rufe shima ya zagaya mazauninsa suka koma Inda suka fito😜. Nasan dai kun fahimci yarinyarnan Ce da suka zauna waje d'aya a jirgi itada Galadima randa zaizo😆🥳. Ganin tabar wajen Galadima yay murmushi sannan yafara k'ok'arin d'agoni daga k'irjinsa, ban yarda mun had'a idoba na bar wajen. “Saikin dawo” ya fad'a a hankali. Kasa daurewa nayi saida Na waigo Dan tabbatar da shine yay maganar kokuwa dai wanine?. Ido muka had'a ya janye nasa cikeda basarwa yana la6e baki. Nima harara Na watsa masa ina barin wajen. Tunda Na taho Maman safara'u da mamansu Yaa hameed da Momy suka zubamin ido. Nikuma fahimtar kallon k'urillar da sukemin saina canja salon tafiya da kuma had'e fuska na nufi zuwa wajen gungun yaran gidanmu masu aure dasuke hira. Suma duk kallona sukayi, namusu murmushi ina fad'in “lallai munada cin ragunan suna kwannan nan ashe”. Dariya duk sukayi, Fiddausi tace “yariman namu shikuma da kwad'ayin naman suna yazo?”. Harara Na zuba mata ina kai mata bugu ta waske itama tana dariya, yayinda su Munubiya ke tayata. Mun gaggaisa tareda tambayar lafiyar juna, muka d'an ta6a hira kad'an da alk'awarin duk zanje mu gaisa, suma sukace zasuzo tunda ba yanzu zan koma ba. daga nan mukai shirin tafiya, Siyama da Zarah anata mana iyayi su masu motar hawa, (dayake kowacce a motarta tazo). Ni dai ni da Munubiya Yaa Marwan ya d'aukemu muka tafi. ____________________________ Tunda nabar wajen Nuren yazo ya tasa Galadima da tsiya, wai dama haka yake ashe?, rashin kunyar tasa har agaban surukai?. Banza Galadima yamasa yay shigewarsa mota yabarsa yana iskancinsa. Anan suka tafi suka barsa dayake da mota yazo shima. Galadima na barin airport gidanmu ya nufa shima. A lokacin 'yan gidanmu suma sun Isa gida, sunata k'ananun magana akan abinda Galadima da munaya sukayi, dan saida suka bama sauran labari, nanfa suka kacame da zancen harda k'arin k'arya akai wai ba kiss kawai sukaiba ('yan gidansu munaya annamimatu🙆🏻😂). Itadai Maman Fauziyya batace k'alaba, saima dariya da zancen ke bata, Dady kuma bai dawo gidanba, daga nan wajen aiki ya wuce, yaran gidan ma kowa gidanta ta koma basu biyo nanba. Innaro da gwaggo Safiyya kam gida suka shige ana saukesu, dan haka basuji komaiba. Galadima bai shiga gidan ba, saiya nemi iso gidan Innaro, Habiba ta fito tamasa jagora. Innaro na falo tana cika da batsewa gwaggo Safiyya na lalla6ata akan ta kwantar da hankalinta. Koda Galadima ya shigo innaro sai antaya masa harara takeyi, yana kula da ita ta gefen ido, ya murmusa yana zama saman kujera, cikeda tsokana yace “Sweet Granny Yaya dai?”. Harara innaro ta zuba masa sosai, tana fad'in mikuma kazo min nan?”. Galadima ya murmusa yana maida hankalinsa ga gwaggo Safiyya, gaisheta yayi ta amsa masa cike da kulawa, sannan ta d'ora da godiya da kwarara masa addu'ar fatan alkairi. Yaji dad'i sosai, ya amsa cikin fara'a, sannan yace, “Granny ina furar tsufa?”. “ai bazaka shata ba ”. Nanma murmushin Galadima yayi yana mamakin wannan rikitacciyar tsohuwa. Yace “tunda bazan shaba Ashe kema kuwa bak'yaje India ba”. Zabura innaro tayi, ta maida hankalinta ga Galadima tana fad'in “da gaske kake ko shak'iyancine?”. Mi su Naja'atu zasuyi inba dariya ba, Galadima ma handkerchief ya saka ya rufe bakinsa kawai. Gwaggo Safiyya kanta saida ta dara. Galadima ya gyara zamansa yana fad'in “karki damu Granny ninmu, insha ALLAH tare dake zamu tafi idan zamu koma”. Dad'i ya kama innaro ta shiga sakama Galadima albarka. Shidai murmushi kawai yakeyi. saida yaga sun nutsu sannan yace yazo tafiya dasu Aiyaan ne, babu musu innaro ta mik'e da kanta zuwa gidan danta kawo masa su. Bayan fitarta gwaggo Safiyya tabama Galadima hak'uri akan darun innaro. “karki damu gwaggo, ai dama kowa yasan idan sunkai irin wannan age d'in saida lalla6awa, ALLAH dai yaja mana ransu”. Amin gwaggo Safiyya tafad'a cikin jin dad'i. Tunda 'yan gidansu Munaya sukaji wai Galadima ne da kansa yazo tafiya dasu Aryaan sai zukatansu suka kuma tunzura, kowa tana ganin hakan salon munafurcine, Maman Fauziyya ta kawoma innaro su, dama suna d'akinta, dan mamansu yaa hameed suna dawowa ta d'auki jakkarsu Aiyaan ta kaimata, wai sai dai su zauna wajenta ita d'akinta babu fili. Maman Fauziyya batace komai ba ta kar6i su Aiyaan tana jinjina bak'in hali irinnan jama'ar gidan. Amma kuma yanzu sai gasu sune dajin haushi. Ita dai innaro ko'a kanta ta jawo hannunsu Zainab ta d'akko jakkar kayansu suka taho. Koda sukazo ma sai Galadima yace abar kayan nasu su kad'ai yake buk'ata. ya ajiyema Gwaggo Safiyya da innaro alkairi ya fito rik'e da hannun su Aiyaan daketa murna. Innaro har wajen mota ta rakosu, bata komaba saida taga tafiyarsu. tana komawa gida tahau had'a kayan tafiya, wai gara ta had'a ta huta, duk randa Galadima yazo sai tafiya kawai. Ita dai gwaggo Safiyya dariya kawai tayi, dan maganar Galadima gaskiyace, lamarin innaro yana buk'atar uziri, ta tsufa sosai, kawai dai ALLAH yabata lafiyane, dan da wuya kaga innaro na kukan wani waje namata ciwo irin na tsufa. (masifarta kam dai kunsan ance abinda kayi a k'uruciya shi kake maimaitawa lokacin tsufa, ALLAH ka azurtamu da k'yak'yk'yawar k'uruciya to🤦🏻‍♀). ★★★★)(★)(★★★★ A k'ofar sabon matsakaicin gidan motocin biyu suka tsaya, cikin wad'anda suke a motar baya d'aya ya fito ya bud'e motar farko, hamshak'iyar macece mai ji da mulki da kud'i ta fito, kallo d'aya zaka mata ka tabbatar tagama samun duniya, cikin tsantsar tink'aho da homa take zuk'ar iska tareda taku d'ai-d'ai irin na manyan mata. Cikin sauri aka bud'e mata k'ofar gidan ta shiga guard d'inta na take mata baya. A tsakkiyar tsakar gidan taja tunga, sai hura hanci takeyi tana harare-harare. d'aya a cikin guards nata yace, “ ma'am nan shine d'akin da yake”. Batace uffanba taci gaba da takawa d'ai-dai har zuwa k'ofar d'akin, hannu ta d'aga musu alamar su dakata. Dukkansu baya sukaja domin cika umarninta. Zaune yake a kujera an d'ad'd'aureshi, kallo d'aya zaka masa ka tabbatar a galabaice yake. Shigowarta baisa ya d'aga kai ba balle ya motsa, yasan dai bazai wuce k'artan dasuka kawosa wajen baneba. sai dai jin k'amshin turaren mace yabashi mamaki, hakanne ya sakashi d'ago idanu domin tabbatar da yaren hancinsa. Bakinsa na rawa yace, “Wacece ke?”. Bata bashi amsaba, saima kujera data ja irin wadda yake kai ta dinning ta zauna, k'afa d'aya ta d'ora akan d'aya tana wani cika da batsewa. “yaro baka isa sanin ni wacece ba, Sai dai cigaba da 6atamin aiki zai sakaka sanina”. Murmushi Muftahu yayi, ya d'ago idanunsa yana mata kallon rainin wayo, “Saninki dama aikin banzane a gareni, aikin ki kuma da kike ik'irarin ina 6atawa duk da ban sanshi ba, kisa a ranki yanzu ne na fara 6atawa, saiki shirya nunamin ke d'in wacece?”. “hahaha, yaro baisan wutaba saiya taka”. “Humm, wuta bata san yaroba saisu k'ulla”. “karan farauta yaushe uban gidan naka yafara koya maka irin izzarsa haka?”. “Kinsan zama da mad'aukin kanwa aishi ke kawo farin kai”. “lallai zan had'a da kanwar da mad'aukin nata duk na koyar dasu darasi. Shi kansa Sameer d'in baikai darajar karen gidana ba balle kai yaronsa”. Murmushi Muftahu yayi, “ Uhmm sai yanzu na fahimta, sai dai zan tunatar dake abinda kika manta, Wanda kikeyi danshi baima San da zamanki ba, kinga ashe ihu kikeyi bayan hari..........”. “hhhhhhhh! Abin dariya, inbai fahimta ba ai zai fahimta lokacinda sak'on sunana da gawarka suka isa a gareshi, yanda ban haifi magajin masarautar gagara badauba, zeenah bata isa haihuwar magajinta ba wlhy”. Idanu Muftahu ya tsura mata, sai yanzu yafara hango kamannin d'aya daga matan tsohon Sarki Abie da suka bar masarauta bayan shekaru biyu da fara jinyarsa, bashida wayau a time d'in, Dan dagasu har Galadima bazasu wuce 7-7 year's ba, saida suntaso sunji labarin bijirewar matan a lokacin da za'a tafi da Abie India, dama shekaru biyun da suka zauna basu ta6a saka hannu a jiyarsa ba, sai Momma keta fama........... Marin da aka zuba masane ya sakashi dawowa daga dogon tunanin daya tafi.... “tunanin mi kakeyi Karen farauta?”. Jajayen idanunsa ya zuba mata, sai kuma ya kwashe da dariya, saida yayi mai isarsa sannan ya dakata tareda tsuke fuska, “ina tunano mummunan fuskarkine, in banda abinki miye na kishi da abinda kika bari da kanki? nasan dai Momma ba itace ta hanaki haihuwa ba ai, inason kisan ni ban isa kare Galadima ba dama, amma kulum cikin kariyar Wanda ya haliccesa yake, a tunaninki 6ata sunansa da kikayine ke nufin bazai mulki masarauta mai d'unbin tarihi da girmaba? kinyi kuskure babba wlhy, Dan kinsaka kanki a ramin damisa. duk ranarda Galadima ya gane kece kika saka amasa 6atanci a jarida wlhy saikinyi nadamar rayuwarki.......... Bayan Hannu tasaka ta bugi bakinsa, gefe yay da kansa yana murmushi, ga jini na zuba a gefen bakin, dayake hannunsa a d'ure suke. Tace, “kafin ni nayi nadamar kai ne da shi zakuyi, Dan yanda kake a tarkona shima yanacan a cikinsa, wawa kawai, kai aboki mai gaskiya ko? zan shayar dakai mamaki, domin saikaga gawar Sameer a gabanka kwance kafin kaima kabishi baya”. Dawo da kallonsa yayi gareta yana murmushi, “miyasa kika tsorata tunban k'arasaba, Galadima maruci ne, kuma kainuwane, gashi dakalin majina, kina hawansa zamewa zakiyi wlhy, ina tausaya miki yayinda tunaninsa ya waiwayo kanki, Dan yanzu aikin manyanki ne a gabansa ba nakiba, d'ana masa tarkonki kuwa tamakar kin tado damisane daga barci, hakan kuma fitinace babba a gareki da shi kansa Karen farautar taki Harun, tirrr da zuciyarki, ni kaina danasan ma kece bazan 6ata lokacina wajen bibiyar ki ta hanyar Harun ba, amma banyi bak'in cikiba, ko babu komai na ribantu da abubuwa masu yawa, domin ta silar hakan na had'a auren sunna, gashi harda ribar ciki, magajin Galadima Sameer kenan....... A fusace ta d'aga kofin glass zata kwala masa. Yace, “relax relax mana giwar mata, ai bangama fad'aba OK?” ba kince zaki kawomin gawar Galadima ba sannan, to miye kuma na fusata haka da wuri?, ni ina kuma tabbatar miki indai Galadima ne zaizo, daga lokacinda yasan ina nan tabbas zai zo, banza karyar farautar wasu, na tabbata k'arya kikeyi ba aikin kanki kikeba kema, sakaki akayi, lallai ke farashinki ya fad'i k'asa, matar sarki mai fad'a aji irin Sarki Saifudden Ce ta k'are ahaka? Abin kaico abin jaje, tirrr”. Dariya ta kwashe da shi tana tafa hannaye, saikuma ta matsa gabda Muftahu tana magana cikin kunnensa “lallai bayan Sameer akwai magajin sa a gagara badau ashe?”. “oh sai yanzu kika fahimta ashe?”. “karen Sameer zaka mutu kaida uban gidan ka, saina saka wannan zuciyar tasa ta buga wannan shine k'udirina”. “hhhhhhh abin dariya, kudirin wasu dai, danke naki bamai muhimmanci baneba, tunda kuka kasa saka zuciyar Sameer bugawa a lokacin da k'uruciya da rashin sanin kansa ke damunsa, miyasa kuke tunanin zata buga a lokacin da yagama tanadar makaman yak'insa, ranar shiga filin daga kawai yake jira, nagaji da tattaunawa dake please”. “kaima kace wani Abu yaro, Dan haka mu zuba, kwana uku kawai zakaga gawar Sameer a gabanka!!!!!”. Bata jira yabata amsaba ta fice daga d'akin, tareda jan k'ofa da k'arfi. Idanunsa kawai ya rintse. Baya tsoron makircinta, amma yana tsoron na Harun, dan Galadima ya rigada ya yarda da Harun 100%, bazai ta6a kawo zai cutar da Shiba. Waige-waige yashiga yi, yasan babu wani abunda Galadima zai iya bibiya tare dashi. Da sauri ya girgiza hannunsa saboda tunowa da agogo, jin agogon tare dashi ya sakashi lumshe ido yana ambatar Alhamllh. Matsala d'ayace baya ganin agogon, saboda hannunsa yana a baya ne. Amma dukda haka zai gwada idan za'a dace. ___________________________ Yau na kasance cikin farin ciki, saboda gani tsakkiyar 'yan uwana, dukda ma zazza6ine mai zafi ke nuk'urk'usata, amma kewarsu ta hanani gajiyawa, mun bud'e babin fira a tsakkiyar falon mama Rabi'a, duk abinda akayi bana nan shine ake labarta min, yayinda Nima nake basu labarin India da nuna musu hotuna. Haka mu kai wannan yini cikin farin ciki da annashuwar kasancewa da junanmu, musamman ma ni da 'Yar uwar tagwaicina da k'addarar aure ta tilasta mana nisantar juna, ji muke tamkar mun shekara ba'a tareba. Kowannenmu k'ok'arin ganin farin cikin d'an uwansa yakeyi. _____________ Tunda Galadima yabaro gida dasu Aryaan saiya wuce wajen wani hutawa dasu, ya yawata dasu sunata farinciki, yayinda shi kuma yake biyema shirmensu dan d'auke musu kewar mahaifiyarsu, yana son yara, shiyyasa ko yaushe Khaleel d'in aunty Mimi zakigansa manne dashi, sa'annin Khaleel dasu Aiyaan kuwa zai iya zuwa d'aya. Cikin lokacin k'ank'ani suka saki jikinsu dashi. Daga nan plaza ya nufa, haka kawai zuciyarsa keta tsikara masa zancen 6atan Muftahu, dukda k'ok'arin wofantar da lamarin da lamarin da ya keyi. Waya ya d'auka ya shige danne-danne, alamu sun nuna masa wayar Muftahu na cikin masarauta, kenan bai d'auki wayarba, yad'an murmusa kawai yana cije lips, yayinda idonsa ke kansu Aiyaan da Saleem yazo d'auka suje wajensa danya huta. Bye suka masa, shima ya d'aga musu hannu yana murmushi. Suna ficewa ya sauke ajiyar zuciya tare da mik'ewa tsaye. zagayen office d'in ya farayi hannunsa goye a baya, a wannan karon bazai ta6a k'yale Muftahu ba, dolene yayi wani Abu akansa, dama yana d'aga masa k'afane domin son ganin gudun ruwansa kawai, yanzu kuma lokacin yayi dazai San mi yake k'ullawa...........✍🏼 *_Duk Wanda yaga ban amsa massage nashiba yamin afuwa, cakwakiyar network tasani clearing charts d'ina batareda na dubaba, tun around 3:47pm nayi posting amma yak'i tahowa._* Dan haka ina gayyata kowa gobe a court, zamu shiga shari'a ni da network ne🙄. Wad'anda suka ga basa ganin posting d'ina gaba d'aya a satinnan duk aikin network ne🙄. *_ALLAH ya gafartama iyayenmhiyayenmu😭🙏🏻_* [7/3, 9:54 AM] Aysha Galadima: *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻1⃣3⃣ ...............Muna tsaka da hira saiga Aunty salamah tazo, daga ni har Munubiya da Ayusher rungumeta mukayi. Cikin tsokana ta ture Munubiya da Ayusher tana fad'in “ku matsamin, kullum Ku ina ganinku, kewar gambo nakeyi”. Gwalo na shiga yi musu, mama Rabi'a da Feena namana dariya. Bayan mun zauna Aunty Salamah ta shiga yaba canjawar danayi tanamin shak'iyanci, nanfa su Munubiya ma suka samu abinyi, sosai suka tasoni gaba sai mama Rabi'a ke kareni. Can muna tsaka da hira takamo hannuna tana fad'in “zo nabaki wani sirri nan autana”. Mik'ewa mukayi inamasu Ayusher gwalo, yayinda suma suka tubure basu yardaba sai an bada sirrin dasu. da k'yar muka samu muka shige d'aki muka kulle. A bakin gado muka zauna Aunty slamah ta sauke ajiyar zuciya tana kamo hannuna cikin nata, serious nima na zama na maida hankalina gareta. Tace, “Munaya! Aiki yatafi yanda ya kamata, saidaifa labarin ya canja daga yanda kike zato, Muftahu ba munafuki baneba”. A matuk'ar razane naja baya ina ture hannunta daga cikin nawa, “Aunty kinsan mi kike fad'a kuwa? Anya yaranki Muftahu suka kama?”. Hannuna ta kamo tana murmushi, kinga zauna, shiyyasa na saka aka d'auki komai dan kema ki gani da idonki”. Zaman nayi kuwa, ita kuma tayi 'yan latse-latsenta a iPad d'inta ta mik'omin. kar6a nayi cikeda fargaba, da kaina nayi playing d'in video n, tun daga fitowar Aunty salmah daga mota har shiganta cikin gidan zuwa shigarta d'akin, tsayarwa nayi na kalli Aunty ina dariya, “kai Auntynmu kinfa iya Acting wlhy, wanifa saiya d'auka da gaske irin mugayen hamshak'an matan nanne”. Dariya Aunty Salamah tayi, “wlhy koni dai nayi mamakin dakewata, bakiga sai wani hura hanci nakeba, sukuma su Ameer saikace guards d'in irin manyan mutanan nan”. Dariya mukayi, sannan nakuma playing na cigaba da kallo. Shigar Aunty Salamah d'akin da tattaunawarsu da Muftahu. gaba d'aya jikina yayi sanyi, zuciyata sai wani tsitstsinkewa takeyi, idona cike da kwalla nace, “anya gaskiya Muftahu yake fad'a Aunty Salamah?, wlhy da gaske fa shine ya saka mana desire tablets, inhar bada wata manufaba miyasa yay haka?, kumafa ni banta6a ganin wani alamar rashin gaskiya ba ajikin Harun”. Murmushi Aunty Salamah ta yi, ta dafa kafad'ata tana fad'in, “Munaya mugu bashida kama, Ai Muftahu baisan nid'in ba matar sarkin bace ta gaske, mizaisa ya za6i 6oyemin? yanda yanuna akan k'yamar matar sarkin tabbas akwai mai mugun hali a cikin su da gaske, kinga ai kince bakiga fuskar wanda kika kama yana wayarnanba a bayan window d'inki randa kuka iso”. “Eh hakane, ban ganiba, maganganun kawai naji”. “to kin gani, kifa tuna kuma firar da kika ta6aji Galadima nayi a asibiti shida aunty Mimi. wad'annan alamomin sun nuna akwai wata a cikin matan Sarki dakeda hannu a ciki, maganar Harun kuma idanu zamu saka masa tamkar yanda mukaima Muftahu, dan ayanzu idan mun saki Muftahu zakiga sun cigaba da takun sak'ar datafi ta da zafi, dan nariga da nasaka rud'ani a zuciyar Muftahu cewar zamu kashe galadima, tabbas ta wannan hanyar Harun zaizo hannunmu. Maganar Galadima kuma har yanzu karki fara kwantar masa da kai, dan kwantar da kanki zai d'arsa masa rashin aiminci a kanki, ke dai kinsan halin mijinki ai yanzu, kinkuma fi kowa sanin yanda yakamata ki cigaba da tafiya da shi”. Insha ALLAH Aunty zan cigaba da k'ok'ari nakuma gode da gudunmawarki akanmu, sai dai akwai matsala, dan na lura agogon hannun Muftahu kamar akwai wani sirri a cikinsa, dolene a daren yau a fitar da Muftahu daga gidanan, zanma sarkin mota bayanin yanda zai taimakeku a maidashi masarauta kamar yanda yaymana aikin d'akkoshi, shima Galadima zansa ido akansa saboda tsuntsune shi nai azabar wayo”. “Hakan yayi Munaya, ALLAH ya cigaba da bamu nasara, insha ALLAH zamu gano komai, ALLAH dai yabama Abba lafiya, yasa mu fahimci komai cikin sauk'i, akan Galadima kuma kici gaba da k'ok'arin da kikeyi Fiyeda da, dan dolene saimun samu had'in kansa kafin musan komai, ALLAH ya ku6tar damu baki d'aya, dan kina dai ganin yanda suka maida Abba”. Hawayen da suka ziraromin a kumatu na share, cikin Murmushin k'arfin hali nace, “insha ALLAH Aunty Salamah, domin raina da farin cikina fansane akan mahaifina, kuma zuwa yanzu Auren Contract bai damuna, sai dai bazan 6oye mikiba aunty Salamah wannan cikin shine damuwata a yanzu, inaji ina gain zan haifishi na barsa inda yafi k'arfina, bansan wace rayuwa zaiyiba a wannan gidan da kowa zuciyarsa takeda k'arancin imani, Aunty Salamah gidan sarauta tsantsar matsalace kawai, bazaki fahimci hakaba saikin tsinci kanki a ciki, Aunty dan ALLAH ki amince na zuba da cikinnan”. “munaya waishin miyasa bakida hankaline? to idan baki saniba wannan cikin shine zai zamemiki tsanin mallakar cimma nasara, kuma ta hanyarsane kawai zamu samu had'inkan Galadima domin fidda Abba daga wannan matsalan da Ku kanku ahalinsa, kina tsammanin koda Abba mutuwa yay masu farautar rayuwarsa zasu barku Ku6utane? Dolene saisun samu abinda suke nema koda ace dukkan gidanku zai k'are, bak'ya tunanin aurenku yana cikin abinda yakuma hasala zukatansu, a zatonsu Abbanki yasamu damar had'a kan mijinkine, ya ina jinjinama fik'irarki ke da munubiya kuma zaki 6ata shirin, karma ki bari 'Yar uwarki taji maganar zubda cikinnan, wlhy zaku samu Matsala ne babu ruwana”. Munaya ta share hawayenta, “shikenan Aunty Salamah nabar maganar insha ALLAH. Amma a yaran nan masu mana aiki bak'ya tsoron wani yaci amanarmu?”. “komai zai iya faruwa, domin amana tayi k'aranci a rayuwa, tunda yau gashi Harun yafito cikin masu cin dunduniyar Galadima, amma ki kwantar da hankalinki, su duka ukunnan da kike gani amintattunane, kuma Saleem ya saka mana idanu sosai a kansu”. “to Alhmdllh aunty, ALLAH kamana jagora”. “amin dai, saikima Munubiya dukkan bayanin da mukayi, ki bata itama ta gani, zuwa gobe zan aiko Bilkisu ta kar6a min, kuma ki fad'a mata yakamata ta koma gidan ta, dan gaskiya aiki bazai cigaba da yuwuwaba tana gidannan, saboda kinga ba ita kad'ai baceba, yanzu haka randa zaku zo da zamu kama Muftahu wlhy nasha wahala wajen nemanta naji kokin iso? dan ta tabbatar min inhar kin iso k'asarnan saitaji a jikinta, amma naita kiranta batayi picking ba, ashe wai wayar na hannun Feena”. murmushi nayi nace, “sorry sweet auntynmu, insha ALLAH zata koma gobe”. “shikenan, bara na wuce to”. “to Aunty ngd sosai, ALLAH ya bada ladan zuminci, ammafa gaskiya kinci zalin muftahu da yawa”. Dariya tayi sosai, “kibari kawai, nima wlhy ina marinsa tausayinsa Na ratsani, insha ALLAH zan nemi yafiyarsa zuwa nan gaba, ALLAH yasa ya yafemin dai”. “hhhh zai yafe miki aunty ai duk cikin aikine”. Mun rakota har tsakar gida, su Munubiya na tsokanarmu wai nad'an sammusu sirrin suma. Daga ni har aunty Salamah dariya mukayi kawai. Bayan dawowarmu na turama Munubiya massage akan taje tagani itama. Sai da taja wasu times sannan tamik'e tana fad'in bara tad'an watsa ruwa. duk muka amsa da to saita fito. ************************** Su Abba sun isa lafiya, anzo da motar Ambulance d'in asibiti aka d'auki Abba, yayinda Sauban da baba k'arami da inna khumar yazo d'aukarsu su kuma. Inna da baba k'arami sai baza ido suke suna kallon gari. Gida suka wuce kai tsaye, yayinda aka wuce da Abba hospital shikuma. Sun iske jakadiya a gidan, dandanan aka shirya musu abinci, itadai inna sai jinjina k'yawun wannan gida take, yanzu anan gidan jininta ta rayu?. shi kansa baba k'arami ya yaba, Yakuma k'ara tabbatar da manyan k'asarmu Na hutawarsu. ************************** Babu yanda Muftahu baiyiba dan ya sarrafa agogon hannunsa amma hakan ya gagara, Dan bak'aramin d'auri ya shaba. Kusan gab da magriba Wanda ke kawo masa abinci ya shigo, ajiye kular abincin yayi sannan ya matsa kusada muftahu zai kwanceshi, cikin murya k'asa-k'asa kamar mai rad'a yace “yalla6ai inhar zaka biyani wlhy zan ku6tar dakai”. Kallonsa Muftahu yayi sosai nawasu mintuna, “ka tabbatar?”. “wlhy Oga da gaske nakeyi, Dan wannan matar da kake gani bata wasa bace, duk abinda ta fad'a zata iya aikatashi wlhy”. Murmushi Muftahu yayi, yace, “nawa kake buk'atar Na baka?”. “tab aini Oga dubu 100 ma ta wadatar”. Muftahu yakuma Murmusawa, “zan baka 200”. Da sauri yaron yaja baya cikin razana, “oga dubu 200 fa? Yo ai sai a d'auka nafara yankan kaine”. Sosai abin yabama Muftahu dariya, Dan haka ya dara, yo dubu 200 a wajensa ai bata wuce ta siyen agogo ko takalma ba, amma shine shi yake ganin 200k a matsayin wasu kud'in da har za'a iya d'auka yayi yankan kai. Kallonsa yayi yana murmushi, “karka damu to, amaimakon nabaka kud'in a hannu a zargeka mizai hana Na bud'e maka wata Sana'a da zakabar wannan aikin da kakeyi yanzu”. “to ai Oga karkaje kasa a kamani wataran, nikuma inhar zan samu Sana'a to zan nutsu”. “haba abokina, ya zakamin rana nikuma Na maka dare, karka damu kaidai ka aminta dani kawai”. “to Na amince, yau sai k'arfe 11 zan kawo maka abincin dare, a time d'in sauran sun fita club, insha ALLAH nikuma zan dawo baya nace Na manta da abincinka, daga nan saina ku6tar dakai, sukuma na sanar dasu Na dawo ban gankaba”. “shikenan babu damuwa, idan zaka dawo kazo da account number, dana koma zan maka transfer insha ALLAH”. “to Oga Na gode sosai”. Ya fad'a cike da d'oki. Murmushi kawai Muftahu yayi. “yauwa Oga bara Na kwanceka kaci abincin to”. Girgiza kai Muftahu yayi, yace, “a'a ka barsa kawai, banajin ci, in kanaso d'auka kaci kawai”.. “amma Oga ai.......”. Kai Muftahu ya girgiza masa alamar karyace komai. Shiru yaron yayi ya d'auki kular ya fice kawai, Muftahu kuma ya bishi da kallo. ************************** Har akayi isha'i Galadima yana birnin gayu, saida aka kira sallar magriba ne yafita zuwa massalacin dake plaza d'in yay salla tare da ma'aikatan wajen masu salla, daga nan ya gaggaisa da makwaftan wajen dakan zo masallacin yin salla suma, bai fitoba saida akayi sallar isha'i. daga nan yacema saleem yaje dasu Aryaan su za6i dukkan abinda sukeso ya mik'a mass ATM d'insa, shikuma ya kuma shiga office ya kulle kansa ya d'ora tunaninsa daga inda ya tsaya. Ya dad'e yana zagaye office d'in, yayinda zuciyarsa ke k'ulawa da kwancewa, agogon hannunsa ya kalla, ganin time yayi nisa yasashi furzar da huci, kayansa ya tattaro ya fito, dogaransa duk suka mik'e, suna gaisheshi, amsawa ya shigayi tamkar baya so. d'aya aciki yace, “zamu tafine ranka ya dad'e?”. Kansa ya jinjina masa alamar eh, sannan yace “ama saleem magana”. Da sauri suka amsa da to. Ficewa yayi, sauran dogaran sukabi bayansa. Mota aka bud'e masa ya shiga, za'a rufe murfin ya hana, idonsa akan k'ofar plaza d'in harsu Aiyaan suka fito tare da saleem, dogarai biyu d'auke da manyan ledoji. Suna hangoshi suka k'arasa da gudu, murmushi yayi ya d'aukesu d'ai-d'ai da kansa ya saka a motar, sannan aka rufe musu k'ofar. Sudai dogaransa sai mamakin yanda yake sakema su Aryaan sukeyi. Har sun fara tafiya ya fad'ama sarkin mota suje zasu taho da Munaya. A ladabce sarkin mota ya amsa da to. ***************** Muna tsaka da hirarmu aka kira wayata, sharewa nayi tamkar bazan amsaba, Munubiya ta harareni, ramawa nayi nima sannan Na d'aga. Ciki-ciki nayi sallama, ya amsa daga can, mamaki ya kamani danjin muryar Galadima, katseni yayi da fad'in “ki fito”. Bai jira cewata ba ya yanke wayar. Kamar zanyi kuka haka naji, Yaa Marwan ya fito daga d'aki yana saka rigarsa, kallona yayi yana fad'in “k ba jiranki akeba ne?”. Sai da Na kumbura baki sannan Na mik'e. shikuma ya fice. Da taimakon feena Na had'a komaina, har abubuwan da mama Rabi'a ta bani, sannan suka rakoni. Mun iske Yaa marwan tsaye jikin motan ya dafa k'ofar suna magana da Galadima dake ciki bai fitoba. Dogari d'aya ya zagaya ya bud'emin, ido muka had'a da Galadima Na janye da sauri, shima janyewa yay ya maida hankalinsa ga Yaa marwan dake masa magana. Mamaki ya kamani ganin su Aiyaan, suma cikeda d'oki suka fad'amin a jiki suna dariya da fad'in “Auntynmu!”. Juyowa Galadima yay yana kallonmu, shima Yaa marwan yay dariya kawai, sannan ya rufe mana murfin yanama Galadima sai da safe. Su Aryaan sun kacame da bani labari, yayinda nikuma naketa musu dariya da biye musu, mamaki ya kama Galadima, bai ta6a tunanin ina magana hakaba, ya lafe jikin seat yana kallonmu cikeda birgewa. Nikam nama manta ko gaisheshi banyiba, saida yay gyaran murya sannan Na d'ago Na kallesa, murmushi namasa ina fad'in “yalla6ai barka da dare”. Shima wani miskilin murmushi ya min yana d'agamin hannu batareda yayi magana ba. Aiyaan yay saurin fad'a “auntynmu bafa yalla6ai sunansa ba, sunansa Uncle”. Kamar zan harari yaron sai kuma nad'an murmusa ina kallon Galadima dake kallonmu shima. janye idona nayi daga gareshi Na cema Aryaan to naji zanke fad'a. Har muka kai gida basu barmu mun hutaba, sai surutu suke da bani labarin abinda yafaru a gida bana nan, danaji zasu kauce hanya kuma sainai saurin waskewa. ★★*★*★★*★*★★ Sarkin mota yana ajiye su munaya ya duba gefen seat d'in data zauna, takarda ya gani ya d'auka, dan sanda zasu shige tamasa wata inkiya da hannu. Dubawa yay yaga mita rubuta. Sallama yayma sauran 'yan uwansa sallama akan zai shiga gida. Daga nan ba gidan ya shigaba, saiyay dabarar da yabar masarautar gaba d'aya. Sun had'u da Saleem a inda suka shirya, saleem Ya bama sarkin mota handkerchief d'in da zasu shak'ama Muftahu. Sarkin mota ma yaje ya bama Ameer ne, daga nan ya dawo k'ofar fada amma k'aramar k'ofa tacan baya inda keda k'arancin tsaro. Agaban idonsa su Ameer suka sauke Muftahu a mashin yana cikin yanayin barci saboda abinda suka shak'a masa, saida ya tabbatar sunbar wajen sannan shima ya koma ciki. Yau dai kam ni kad'ai Na kwanta a d'akina, Galadima ko lek'e bai lek'oba, yana can tare da su Aiyaan a d'akinsa. Nima kawai saina kira Momma mukasha hirarmu, tana bani labarin yanda jikin Abie yaketa k'yau a tsakaninnan, dukda kar yanzu maganar bata fita amma yakanyi bamai tsawoba, naji dad'i sosai, na masa addau'a mai tsawo tareda fatan alkairi, daga nan muka cigaba da tattaunawa akan maganar Abbana, da zancen su innarmu dasuka k'i yarda su zauna a gidan, innarmu ta dage bazata zaunaba tunda muma anan muke, saida Momma ta saka baki da mata bayanin da zata gamsu sannan ta amince zata zauna. Nasha dariya, dan dama nasan za'ayi hakan, innarmu kawai kunya da kawaici. Daga nan har muka dawo kan ta Muftahu, dayake tasan komai a kai, da taimakonta nima nake samun k'arfin gwuywa. Itama tasha mamakin jin Harun a lamarin, ta dad'e tana jinjina maganar nan. ta bama Samha muka d'ora da hira, saida naga time yaja ga zazza6in fama ya rufeni, sallama mukayi nai addu'a Na kwanta. Masu iya magana since sabo tirken wawa, saina kasa barcin, naji kawai ina kewar Galadima. Shima kansa yanacan sai juye-juye yakeyi, yakasa barci, bayan sun gama hirarsu dasu Aryaan yay musu shirin barci da kansa suka kwanta, aiki yad'an ta6a yana Neman dabaru akan binciko Muftahu, baiwani dad'eba ya kwanta shima, amma saiya kasa barci, juye-juye yaytayi agadon, ganindai da gaske ya kasa barcinne saiya mik'e yana jan guntun tsaki, kwanciya ya gyarama su Aryaan ya lullu6esu da bargo sannan ya fito da nufin wai zai duba munaya 🤣😜. Jin shigowarsa yasani k'ara lafewa tamkar nayi barci, ya kunna fitilar d'akin yana kallona, yaja wani dogon lokaci sannan ya kashe ya tako zuwa gadon, “nasan idonki biyu ai, dama kin tashi kinbar wani kumshe-kumshe”. Shiru nayi nakumak'i motsawa. Kwanciya yayi a gefena, yaja bargon shima ya lullu6a, tareda juyamin baya, yace “miya hanaki barcine?”. “farkawa nayi”. Na fad'a batareda ba kalleshi ba. Murmushi yayi yana fad'inn “ Hummm”. Daga nan duk mukayi shiru nawani lokaci, kamar an matse bakina nace “yalla6ai na tambayeka please? ”. Yace, “Uhmm”. Juyowa nayi ina fuskantar bayansa, a nutse nace, “wai dan ALLAH ina sauran matan Abie yanzu?”. Da sauri naga ya juyo gareni, ni harma tsoro ya kamani nai baya da sauri, nazata makeni zaiyi, amma sainaji ba hakaba, yace “Munaya mi kika sani a kaina ne?”. “yalla6ai kamarya mina sani a kanka? daga tambaya?”. Yace, “Humm yana matsowa gareni, zan matsa ya rik'o hannuna................✍🏼 Kuyi manage da wannan please🤦🏻‍♀ *_ALLAH ya gafartama mahaifanmu😭🙏🏻_* [7/3, 9:59 AM] Aysha Galadima: *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻1⃣4⃣ ................Yanda ya rik'e hannun yasani fad'in “please yalla6ai akwai zafi fa”. Sassauta rik'on yayi, ya sauke ajiyar zuciya, muryarshi a sanyaye yace, “Miyasa kikeson 6oyemin abinda kika Sani? shin bak'ya tausayinane? kullum cikin aiki kwakwalwa ta take, aikin Neman kud'in da zan taimaki kaina da ahalina, aiki akan mak'iyana, ya kike tunani a kaina? yanzu haka ji nake tamkar kwalwar kaina zata tarwatse saboda damuwa da abubuwan da suka sakata matuk'ar nauyi, ta6a kiji yanda zuciyata takoma bugawa a slowly”. ya kamo hannuna ya d'ora a k'irjinsa, saitin zuciyarsa. da gaskiyarsa kad'an-kad'an zuciyarsa ke aiki, ba kamar kowanne bugun zuciya dake tafiya normal ba. Sai naji tausayinsa ya kamani, cikin sanyin murya nima nace, “yalla6ai kayi hak'uri da abinda zan fad'a maka, inhar ka kawoni gidanka ne domin muyi aiki tare a matsayin Friend bai kamata ace ka gaza yarda daniba akan sirrinka. kasan minene yake saka kwalwarka da zuciyarka wannan nauyin kuwa?”. Kansa ya girgiza mini. Na gyara kwanciyata ina kallon p.o.p, “Matsalarka d'ayace baka yarda da kowa ba sai kanka, mu cire Momma da papi, dansu aiyukansu sunkai amusu uzuri, Momma hankalinta akan jiyya yake, dan haka kana k'ara mata damuwa, papi kuma babbane shawara da dabarun manya kawai kake buk'ata daga garesa. Sai kuma Muftahu da Harun nakula suma kakan d'an saki jiki dasu akan wasu abubuwan, to amma fa.........”. Saitayi shiru bata k'arasaba. Ya matso jikinta sosai, tare da d'ora hannunsa saman cikinta, murya k'asa-k'asa yace, “Harun da Muftahu amma fa mi? Please ki k'arasa mana”. Kad'an Na juyo nad'an kallesa, Na d'ora hannuna nima akan nasa daya d'ora akan cikina. Janye fuskata nayi Na koma kallon p.o.p d'in. “kayi hak'uri da abinda nake fad'a, badan ina zarginsu bane zan fad'a d'in, dama zancene Harun da Muftahu kuma kamar bai kamata 100% susan komaiba, dan za'a iya sayensu ko tursasasu suci dunduniyarka. domin koba komai har yanzu bakada tabbas d'in cewar babu hannun wasu a cikin masarautar nan. amma kayi hak'uri idan na shiga hurumin daba nawaba”. Shiru yay baice komaiba tsawon lokaci, har nayi zaton nayi laifi ko yayi barci, a sanyaye nakuma fad'in “please & please kamin afuwa yalla6ai”. “is okay”. ‘kawai ya fad'a yana kuma sakani a jikinsa, tareda d'ora ha6arsa saman kaina. Babu Wanda yasake magana a tsakaninmu, kowa yay shiru yana k'ullawa da kwancewa, har dai barci yafara fisgata. “Kina ganin su Aiyaan bazasuyi kuka ba idan suka farka sukaga su kad'aine?”. Naji maganarsa cikin kunnena. “a'a” na fad'a ina girgiza masa kai, “ko'a gida sukad'ai suke kwana dama”. “okay”. Saikuma muka kuma yin shiru, har barci yakuma fara d'aukata yakuma fad'in “kozaki sha Magani ne?”. ‘yay maganar yana ta6a gefen wuyana’. Kaina Na girgiza masa batareda nace uffanba. shima bai sake cewa komaiba.. Yanda numfashina ke sauka a hankali sai ya fahimci nayi barci, shiko gaba d'aya yakasa nasa barcin, tunanin wani Abu daya ta6a faruwa a baya ya fad'o masa, dukda shi ba yayi imani da hakan baneba. 👇🏻 *_Wata ranar juma'a a India, sai suka tashi da matsananciyar damuwar motsawar ciwon Abie, a time d'in ma sun zata rai zaiyi halinsa, hankalin Galadima ya tashi har ciwonsa shima yakai ga motsawa, amma yak'i yarda doctors su dubashi, yace abarsa kawai gara ya mutu ya huta, hankalinsu momma ya tashi, amma Galadima yak'i sauraren kowa, daga k'arshema saiya sulale daga asibitin ya fice abinsa, haka yayta tafiya rik'e da k'irjinsa saboda azabar ciwon da zuciyarsa ke masa, mutane sai kallonsa sukeyi, shiko baimasan sunayiba, yayi tafiya mai nisan gaske batareda yasaniba. k'arfinsa da kuzarinsa sukai gazawar da bazai iya cigaba da tafiyanba, shine yazube a wajen ya fad'i._* *_bai tashi farkawa ba sai awani d'aki mai kama dana bunu, ya yunk'ura zai mik'e amma saiya kasa, wani tsoho ba indiye, a cikin indiyawan ma irin masu k'yawunnan sosai, ya dafa kafad'arsa, cikin harshensu yace ma Galadima “koma ka kwanta d'an saurayi, bakada lafiyane”. Galadima yace “kayi hak'uri baba gida zanje nasamu sauk'i, zamana annan bak'aramin tashin hankali bane ga ahalina”. tsohon yay murmushinsu Na manya, yace “zakaje gida d'ana, ni da kainama zan kaika, amma lallai kai acikin al'amuranka akwai abubuwan ban mamaki da al'ajabi, gakuma tsantsar rud'ani, saidai komai yanada lokacinsa, kuma lokaci zai tabbatar maka hakan, albishir d'aya zanmaka, nanda wasu shekaru dabasu Gaza 7 ba mai taimakonka zatazo, kwarai zatazo gareka, ba lallaine ka fahimci abinda nake fad'aba ko yarda dani, Dan Na lura kaid'in musulmine, kuma bad'an wannan k'asarba, amma wannan mai taimakon naka itace zata zama fitilar haska maka hanya kakai ga cinmma burinka, domin taurarinta da naka sunada matuk'ar k'arfi, harma suna gogayya da juna, zaku zama sh........”. Saikuma yayi shiru yana murmushi, ya shafa kan Galadima yana fad'in “tarin Albarka sucigaba da baibaye rayuwarka data zuri'arka”._* *_daga wannan maganar sai barci mai nauyi ya kwashe Galadima, koda ya farka saiya gansa a asibiti tareda su Momma, yata tambayarsu INA tsohon yake sukace su basu San wani tsohoba, wasu samarine su biyu suka kawoshi asibitin, wai sungansa yafad'i a gefen hanya, zancen tsohon yata damun Galadima a time d'in har yayta bincike kozai gansa amma ko alamun mai kamarsa bai ta6a ganiba, daga hakama saiya cire abin a ransa yacigaba da harkokinsa._* Ajiyar zuciya ya sauke, tareda kuma rungume Munaya, a kan la66ansa ya furta “ALLAH kaine mafi sani”. daga haka yay shiru tareda lumshe idanunsa, barcine yayta fusgarsa harya samu nasarar sacesa. Can gabannin asuba yay wani mafarkin daya sakashi farkawa a firgice, har itama Munaya ta farka tana tambayarsa lafiya?. Kansa ya dafe, da hannu yaymin nuni na bashi ruwa. Sauka nayi daga gadon dan zazzza6inna ya fara hucewa nima, freight na bud'e na d'akko masa ruwa, na had'o da Kofi, zama nayi kusa dashi a gefen gadon na tsiyaya ruwan a Kofi na mik'a masa. kar6a yayi ya shanye, ya mik'o min kofin, zan kar6a ya girgiza min kai tare da min nuni da in k'ara masa. Kuma tsiyaya masa nayi, yakai rabi ya d'aga min hannu alamar ya Isa, bayan yakuma shanyewa ya mik'a min kofin yana fad'in “Thanks”. Kar6ar kofin nayi, ba tareda na tashiba nace “Yalla6ai lafiya kuwa”.. “Mafarki”. ‘yafad'a yana komawa ya kwanta’. Idanu kawai Na zuba masa, kusan 4minutes ya juyo da kansa ya kalleni, “kizo ki kwanta mana”. K'aramar ajiyar zuciya kawai Na sauke Na mik'e, Na d'ora ruwan da Kofi a dirowan gefen gadon na koma inda nake na kwanta. Ganin ya sauya hannun da yay mafarkin kuma yana addu'a sai ban sake cewa komaiba, na kwanta shiru ina sak'e-sak'e a raina mafarkin mi yayi to? da har yasakashi firgita irin haka?. banida mai bani amsa dan haka nayi shiru. Saiya zamto da asuba na rigashi tashi, harma saida nayi alwala sannan na tadashi, da k'yar ya iya tashi yana dafe kai, binsa nayi da kallo kawai harya shige toilet. Lokacin daya fito na fara salla, dan haka saiya fice kawai. A mamakinsa saiya iske Aiyaan da Aryaan sun tashi suna alwala, hakan ya Burgesa sosai. Sai kawai ya kama hannunsu suka tafi massalaci. Bayan an idar da salla bai yarda sun had'u da Sarki ba, ya gudo. Sai dai abinda bai saniba shi Sarki ya gansa, dan yau ya makara salla shima. Wajen Around 9am nagama gyaran d'aki nayi wanka, saina d'an fito falon domin duba dubawa, natarar sabbin kuyangina suma komai sun gyarashi k'al, harma da mana break fast, banyi yunk'urin bud'ewa ba ma balle tunanin son ci, dukda kuwa natashi da yunwa, to amma Momma ta gargad'eni sosai akan cin abinci wani a masarautar, dan haka na fito daga kitchen d'in kawai. Tunkan na shigo nake jiyo maganarsu Aryaan, zaune na iske Galadima su Aiyaan na kusa dashi suna bashi labari, anmusu wanka tsaf, sunsha sabbin kaya iri d'aya. Har yanzu Galadima bayada walwala, na zauna ina gaisheshi, batareda yabar latsa wayarba ya amsa min, su Aiyaan suka dawo kusa dani suna gaisheni, kumatunsu naja ina murmushi, “oh my guys kunsha k'yau, waya muku wanka haka?”.. Atare suka amsa min da fad'in “Uncle ne, kuma ya saka mana tirare yanda kuke mana”. Murmushi nayi, na saci kallon Galadima da yay biris damu kamar baya d'akin, alhalin sanda na shigo na iske suna hira shidasu 'yan 2. Sallamar da wata baiwa keta kwad'awa na amsa, sannan na mik'e na fita dannaji minene? A k'ofar falona na isketa, nace, “miya farune?”. Duk'ewa tayi ta gaisheni, sannan ta mik'omin ledojin hannunta tana sanarmin Sarkin motane yace “na kawo wannan ranki ya dad'e”. Kar6a nayi, na koma ciki. Ajiye ledojin nayi a gabansa, “gashi wai inji sarkin mota”. Idanunsa ya d'ago ya kalleni, yace, “breakfast d'inku ne”. Tashi yay ya fita yana fad'in na shirya zaije ya dawo mu shiga cikin gida gaida mutane. Na amsa masa da to. ___________________ Tun a daren jiya wasu bayi sukaga Muftahu, dan haka suka shiga ihu, dandanan sauran bayin dake kusa da wajan suka firfito, manyan bayin cikinsu ne suka kai maganar cikin gida, shine akasakasu d'aukar Muftahu su shiga dashi. Lamarin yabama kowa mamaki, babu wani mummunan rauni a jikinsa, inbanda d'an jini dake gefen bakinsa, saidai sun sami kwanciyar hankali ganin yana numfashi. Maganar dawowar Muftahu bata baje masarautar ba sai washe gari. Bayan Galadima ya fito daga sashensa zaije fada yaji anata k'ananun magana akan dawowar Muftahu, saidai kuma miskilancinsa bai barsa ya tambayi kowaba ya nufi Fada. Ya isa mai martaba baikai ga isowa ba, dan haka suka gaisa da 'yan majilissar Sarki dake fadar, sannan ya nemi mazauninsa dake gefen Sarki Na dama ya zauna. Zamansa baifi da mintuna 10 ba Mai martaba ya iso, gaba d'aya suka mik'e tsaye, dogaran Sarki sunata kirari da fad'in gyara kintsi da k'yau, duksun baza riguna ba'a gani mai martaba, basu bar kowa ya gansa ba har saida ya zauna a kujerarsa. Baya suka mammatsa mai martaba ya bayyana, atare su Galadima suka rissinar dakai alamun girmamawa, sannan kowa yafito tsakkiyar fada ya mik'a gaisuwarsa ga Sarki, yayinda fadawa ke faman amsawa, tsakanin Sarki dasu kuwa shine d'aga hannu. Mai martaba yayi mamakin ganin Galadima yau azaman fada, bawai baya zaman bane, sai dai yakan dad'e bai zaunaba, an masa uzurine kasancewar ansan ba zaune yake dindin dinba, kuma idan yazo akwai harkokinsa Na kasuwanci da yakeyi, sai dai dolene yakan shigo yayi gaisuwa. Bayan fada ta nutsu aka fara fadanci. K'a idane fadar gagara badau takanyi fadancine a sati sau hud'u kawai, litinin ba'a zaman fada, domin ranace da ake tunawa da abinda ya faru ga tsohon Sarki mahaifin Galadima, talata, laraba, alhamis, asabar, sune ranakun da ake fadanci, ranar juma'a ma ba'ayi saboda muhimmancin ranar ga al'ummar musulmi. A wad'annan ranakun akanyi zamanne daga 10am zuwa 12:30pm, da an tafi sallar zuhur ba'a dawowa, idan kaga anwuce wannan time d'in a fada to tabbas akwai abinda ya farune. A wannan zaman fadancine maganar dawowar Muftahu ta fito, sun tattauna akai harda shirin kuma d'aukar matakai Na tsaro a masarautar. Bayan anyi sallar zuhur ne Sarki ya shige gida, sauran fadawa ma kowa ya kama gabansa, Galadima bai shiga gidaba saiya nufi sashen su Muftahu domin dubashi. Bayan an masa iso ya shiga, ya iske mahaifiyar Muftahu da 'yan uwansa zagaye dashi, har yanzu kuma yana cikin yanayin barci. Ya jajanta musu, Yakuma kwantarma da mamansu Muftahu hankali, kusan mintunsa talatin ya fito ya koma sashensa. Ya iske su Aiyaan kawai a falon Munaya suna kallo, suka taso da gudunsu suka rungumesa, fuskarsa cikeda fara'a ya tarbesu, ya tambayesu ina Auntynsu?. A tare suka bashi amsa, “Uncle tana d'aki ta kwanta kuma tace karmu tadata, inba hakaba jiki magayi”. Murmushi yayi yaja kumatunsu, “kuce zatayi zana kenan idan aka tada ita?”. Nanma atare suka amsa da “eh Uncle, kasanfa Aunty Munaya tacika fad'a, gidanmu tsoron masifarta akeyi, amma ita Aunty Munubiya babu ruwanta”. Galadima yace, “da gaske?”. “ALLAH kuwa Uncle, idanfa mukayi rashinji ita ke zanemu ba innarmu ba, kuma dukanta da zafi, gashi taita hararmu da katun-k'atun idanunta nan”. Sosai abin yabama galadima dariya, dan haka ya dara sosai abinsa yana fad'in, “kubari tajiku to, idan ta zaneku babu ruwana nidai, kunga bara naje naga kota tashi, karfa Ku shigo, dan zata iya zaneku”. Sukace “ai bazamu shigoba Uncle”. Yace, “good boys”. Da sallama ya shigo, amma saiya isketa baje a gado tana shak'ar barcinta, yad'an murmusa kafin ya k'arasa ya zauna a bakin gadon saitin fuskarta, yatsunsa biyu yasaka a gefen wuyanta dan yasan da wahala wannan barcin ya kasance na lafiya, aikam jikinta ringim yake da zazza6i, tausayinta ya kamashi, lallai uwa dabance acikin al'umma, Ashe haka sukeshan wala, tundaga d'aukar cikinma zuwa rainonsa, akoma rainon yaro, daganan tarbiyarsa, lallai masu raina mata ko kallonsu masu k'arancin tunani sune masu k'arancin tunanin ai, ya d'an lumshe idanunsa yana cije lips, ganin ta dunk'ule a waje d'aya saiya ja bargo ya lullu6a mata, harya mik'e ya koma ya zauna, risinowa yay kanta a hankali ya mannama goshinta kiss, sannan yamik'e ya fice. Koda ya dawo saiya wuce d'akinsa, yabar su Aiyaan suna kallonsu. Kayan jikinsa ya cire ya kwanta shima, dan yana buk'atar hutawa kona 2hours ne, kwanciyarsa kuwa babu dad'ewa barci ya saceshi. Kiran sallar la'asarne ya tashesu kusan lokaci d'aya, Galadima yatashi da k'yar, a mamakinsa sai yaga Aiyaan da Aryaan kwance a gefensa suma suna barci, murmushi kawai yayi yasako, saida ya watsa ruwa sannan yay shirin tafiya massalaci cikin k'ananun kaya. Harzai fita saiya dawo yashiga wajen Munaya. tana tsaye gaban wardrobe tana neman kaya, da alama wanka tayi, dan daga ita sai towel. Banji sallamarsa ba, saboda shi idan zaiyi magana bayason bud'e baki, ganin batajishiba saiyayi gyaran murya, a tsorace na waigoshi, ganin shine nai saurin saka kayan dana d'akko ina kare k'irjinna da tura baki, bakinsa ya d'an ta6e, sai kuma ya shiga takowa inda nake, duk takun da yayi sai gabanna ya fad'i, na waiga kozan samu nabar wajen ko abinda zan suturta jikinta sosai, amma sainaga babu a kusa, kuma ina jikin wardrobe d'inne sosai ai. ban gama yanke shawara ba ya k'araso daf da ni, kuma matsawa nayi na matse jikinna sosai a drowa d'in, shikuma yawani had'e gabas da yamma, wannan ne yakuma sakamin tsoronsa a raina, na zata kowata tsiyarce ta kawoshi. Hannu yasaka ya d'ago da ha6arta muka kalli juna, ya tsareni da idanu yanda nakasa janye nawa cikin nashin, munkai kusan 2minutes a haka, kafin yakumamatsoni sosai, ya kai fuskarsa gab da tawa tamkar zai had'e bakinmu, dan haka saina lumshe idanu, murmushi yayi ya hura mata iska akan idanun, ta rumtse idon sosai, ya d'an ja baya yana ta6e baki, kafin yasaka hannu ya cire nata dataketa faman kare k'irji da kayanta, still ya kuma matsawar saitin kunnenta yana fad'in “wane darene jemage bai ganiba yalla6iya”. ‘ya k'are maganar da shafa kirjina ya fice abinsa. Kad'an yarage namasa ihu wlhy, aiko yana fita na durk'ushe a wajen ina sauke numfashi, sometimes nakan rasa yazan fassara Galadima da ayyukansa. Da k'yar Na iya tashi nayi sallar nakoma kan gado Na kwanta. Galadima kam daya fita dariya ce taita cinsa, ya kula Munaya akwai tsoro, kuma haryanzu a tsorace take dashi, cikinnan ne kawai kanci galaba akanta yake samunta cikin sauk'i, ya girgiza kansa kawai yana murmushi. Bayan ya dawo massalaci d'akin nata ya dawo, dan yanason suje su gaida jama'ar gidan, maybe gobe suje masarautar papi ma. A kwance ya iskeni, nak'i kallonsa, jingina yay da mirror yana fad'in “yaya jikin naki?”. Ban kalleshinba nace, “da sauk'i”. “ALLAH ya k'ara sauki, idan zaki iya tashi ki shirya muje cikin gida, kafin waccan tsohuwar tafarama mutane surutu”. “to” nafad'a ina mik'ewa, Na sakko a gadon, harna nufi wardrobe zan d'auki alk'yabba saina tsaya, batareda Na kalleshi ba nace, “toka fita Na shirya”. Hard'e hannayensa yayi a k'irji yana fad'in “ashe bazaki shirya d'inba, dan bazanje ko inaba”. “karkaje d'in, ai akwai bayi” nayi maganar a zuciyata. Kayan Na d'auka na shiga toilet, shikuma ya ta6e baki. Babu dad'ewa na fito tsaf, nayi k'yau, nazo ta gefensa na d'auki turare nasaka kad'an sannan na kallesa nace, “na shirya”. Baice komaiba ya nunamin hanya, gaba nayi yana bina a baya muka fice. Kasancewar tazarar dake d'an tsakaninmu da sassan nasu muka shiga mota, dan banajin dad'in jikinna, bama zan iya tafiyarba. 6angaren Abba hayatudden muka fara zuwa, daga nan sai sashen matan mai martaba, soyayyar da uwargidansa ke nunamin yasani k'ara k'aunarta, sai addu'a take zabgamin akan ALLAH ya saukeni lafiya. Galadima kad'ai ke amsawa, amma ni saidai a zuciya kawai. daga nan muka d'an shishshiga wasu sassa, 6angaren mama fulani shine k'arshen zuwanmu. Kunsan dai mutuniyar taku akan mulki, tana kishingid'e kuyanginta nata bauta, mai matsa kafa daban mai firfita daban, ga masu bata labarai, tufa takeci cikeda k'asaita da izza. Amintacciyar baiwarta data mana iso tana gaba muna biye, mama Fulani ta d'agama kuyanginta hannu alamar subata waje. Rige-rigen ficewa suka, yayinda mukuma muka k'arasa gareta, idonta a kammu ko k'yaftawa batayi, nidai tsarin ALLAH na nema daga sharrinta, ina dalili wannan kallon k'urilla haka?. Galadima yace, “barka da yammaci”. nima saurin fad'a nayi. A yatsine ta amsa mana, ta d'ora da fad'in “Saraki kayi wuyar gani?”. Galadima ya murmusa yana kallona, “Ranki ya dad'e kinsan mai amarya ai yafi dubu wahalar gani dama”. “Humm” kawai tace batareda ta amsaba. Sai zuwa can tace “nafa manta, ina tayaku murnar samun k'aruwa”. “mun gode ranki ya dad'e, amma taki murnar itace tazo a latti, gashi kuma idonkine yafara hango abin cikin kwan tun a india”. Mama Fulani ta tsatstsare Galadima da idanu, shikuma yay salute nata yana murmushi. Jitai kamar zata makesa dan haushi. Ya lura da haushin da taji, dan haka ya kama hannuna muka mik'e tsaye yana fad'in, “bara mukoma inda muka fito ranki ya dad'e, a huta lafiya”. Bai jira amsartaba mukayi fitowarmu. Da kallo kawai ta bimu, takasa koda motsawa, tarasa miyyasa yau Galadima da matarsa suka mata wani mugun kwarjini? batada mai bata amsar tambayar tata... Yini guda yau Galadima a gida yayishi, baije ko inaba, sai da daddare Nuren yazo sukayi magana, daga nan yace ya nema mana tickets d'in zuwa masarautarsu. Washe gari muka tashi da shirin tafiya masarautar su papi, mukad'ai muka tafi, babu kuyangi babu dogarai, dagani sai shi dasu Aiyaan, sai Nuren..................✍🏼 *_ALLAH ka gafartama mahaifanmu_*😭🙏🏻 [7/3, 9:59 AM] Aysha Galadima: *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS. ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻1⃣5⃣ ...................Abin yabani mamaki ganin yanda akazo tarbarmu, yo saikace wani Sarki, hakan yakuma tabbatarmin da Galadima d'an gatane a wannan masarautar. A masarautar ma gungun mutane muka iske wai masu tarbarmu, ni dukma sai kunya ta kamani wlhy, musamman da Mom ta rungumeni tana fad'in “ga maman twins d'inmu ga Maman twins d'inmu”. Galadima dai murmushi yayi, Nuren kam dariya ya kemin. Lallai naga tsantsar soyayya a wannan masarauta, sai nan nan ake dani kamar wata sarauniya, duk wani Motsina Inno tace minakeso? hakama mom. Aiyaan da Aryaan kam ai suna tare da Galadima, duk inda yasaka k'afa suna biye. Nikam dai a kwana biyun da mukayi babu abinda zance da wad'annan bayin ALLAH sai godiya, naga karamci naga hallaci sosai, hakama k'annena. Sosai Galadima yasamu tattaunawa da papi a tsakaninnan, sunyi maganganu masu muhimmancin gaske. Musamman akan ciwon Abie da cikin jikin Munaya, harma da Abbanta. sosai kuma Galadima yakuma samun haske akan lamuran. Kwannamu biyu muka dawo cikeda kewarsu, tare da tarin alkairi ga wad'annan mutane masu tsayawa a rai. Mun dawo da kwana 1 yaran gidanmu na ma'auri suka kawomin ziyara. Aunty khaleesa, aunty Hauwa'u, aunty Ramlah, aunty Raheenat, matansu ya hameed, Fiddausi, Siyama, Zarah, Safara'u, Fauziyya, Haleematu,Munubiya, Ayusher, Feena. Wayyo dad'i wlhy saika d'auka biki akeyi, rasa inda zansaka kaina nayi saboda dad'i, shi kansa Galadima ya fahimci ina tare da tsantsar farinciki, nima dagewa nayi namusu hidima iya hidima, dan hardani aka shiga kitchen. Sukam duksun rikice da mamaki, dama haka gidan sarautar yake, dan saidama Galadima yaje da kansa ya shigo dasu. Su Aiyaan anata murna anga 'yan gida. Ranar dai anan suka yini zir, dazasu tafi Galadima yay muzu alkairi mai yawa tareda godiya ta musamman. Sunji dad'i sosai kuma sunyi farinciki, sunata masa godiya nima ina tayasu. Da zasu tafi jinai tamkar na rik'esu, aiko harda 'yan kwallana, sauk'inama kawai su Aryaan tare dani. Kowaccensu tatafi da labarin data gumtsawa uwarta a bayan fage, dansu Zarah dai sun Shiga taitayinsu, sun gane ruwa ba sa'an kwando bane, nanfa hassada da bak'inciki tamkar ta babbake zukatansu, mamansu Yaa hameed hardama Abba ALLAH ya Isa tana sharar kwalla, wai yasan da gidan sarautar amma ya yarda Zarah ta auri d'an sanata, ga aunty khaleesa nanma kullum cikin matsala da miji, dan kishiyarta akwai kissa. *_ALLAH yarabamu da ciwon hassada fans_*😏 Sati d'aya da zuwansu muka koma India, saboda Company suna Neman Galadima da gaggawa. harda innaro iya bala'i muka tafi🤣. A jirgi taita kudundune fuska a gyale wai batason ganin tashin jirgi, duk tsare gidan Galadima saida yayi dariya, Aryaan da Aryaan kam sukaita tsokanarta. Yau babu masifarnan dan bata kulasuba, saima Galadima ne ya hanasu. nikam banza na musu dan tawama ta isheni nikam. Jikina sai ciwo yakeyi, ga cikina na mun ciwo shima kad'an-kad'an. Khumar da Sauban da Samha sukazo d'aukarmu, muka rungume juna da samha muna farinciki. Daga nan muka wuce gida, yaukam munashan k'auyancin innaro, ni harma tabani haushi, komai tagani saita tambaya, Kodai su Aiyaan basa abinda takeyi. Mun iske jakadiyane kawai sai bayi, Su Momma da innarmu suna asibiti, Mudai sama muka haye ni da shi, 'yan biyu kuwa suna wajen Samha ta kasa ta tsare, innaro kuma aka barta da jakadiya. Ko ina tsaf yasha gyara tamkar mai d'akin na nan, Muna shiga kwanciya nayi bisa kujera, naja bargon saman gadon na lullu6e, kallona yayi da mamaki “k lafiyarki kuwa?”. “zazza6i”. kawai nace masa na k'udundune har kaina. Zama kawai yayi ya zubamin idanu cike da tausayi, ganin zaman bazai masaba yatashi ya shiga toilet, saida ya gama dukkan uzirinsa sannan nima ya had'amin ruwan wanka, tadani yayi, na tashi da k'yar tamkar zan masa kuka. Yace, “tashi kije kiyi wanka kozakiji dad'i”. Baki na tura masa gaba. “idan bazaki iyaba tashi muje na miki”. ‘yay maganar cike da basarwa’. Harara na zuba masa sannan na mik'e na nufi bayin. shikuma ya ta6e baki yana wani mikilin Murmushi. Abincima sai nan ya saka aka kawomin, dan nakasa sauka. Innaro sai catake wai nacika langyare, dan naga yana shagwa6anine shiyyasa nake ta6ara, ai badaga kaina aka fara cikiba. Galadima dai murmushi kawai yayi danshi lamarin innaro abin dariya ya d'aukesa, tana buk'atar uzuri. Bayan nasamu naci abinci daya bani nasha magani, harzan kwanta a sofa yace na koma saman gadon, kamar zanyi magana saina fasa, na tashi kawai na koma. Yana kammala duk abinda ya dace yafice asibiti domin duba Abie da Abba. Yaji dad'in yanda yaga canji sosai a jikin nasu su duka, dan raunuka da yawa sun warke a jikin Abba, da bakinshi ma ya amsa masa gaisuwa yana masa godiya, inna da baba k'arami sunata saka masa albarka. maganar da abie ya fara kuwa rungumesa yayi yana kuka Abie nayi, hakama su Momma, a hankali Abie yace “ina d'iyata Muh'd”. Murmushi Galadima yayi, yace, “zuwa anjima zaka ganta Abie, yanzu na barta tana barci zazza6i ya rufeta”. Momma da Aunty Mimi sukace “ALLAH dai ya sauketa lafiya to”. Babu kunya Galadima ya amsa da amin. Aunty Mimi dake kusan dashi ta doki gefen hannunsa, “kai mara kunya, shine zaka amsa”. Hannu ya saka ya rufe bakinsa yana fad'in “ni jikan Abdul'fatah da Abubakar”. Dak'uwa Momma tamasa tana kai masa duka, ya matsa da sauri yana dariya. Abie ma murmushi yakeyi, lallai yau yakuma ganin canji tare da d'ansa sanyin idaniyarsa, sukam yaushe rabon da suga irin wannan nutsuwar tare dashi haka, lallai dolene su godema ALLAH da shigowar Munaya cikin rayuwarsa, basu da wani abinda zasu iya biyanta har abadan, saidai suyita mata fatan alkairi da k'yautata rayuwarta. Saida na tashi sannan muka tafi asibitin muma, wajen su momma muka fara zuwa, Momma da aunty Mimi sukazo suka rungumeni tamkar zasu had'iyeni dan dad'i, nikam duk kunyarsu ta gallabeni, sai 6oye fuska nakeyi, koda zan gaida Abie ban yarda na kalleshiba. Sauban da Samha sai dariya sukemin. Duk bak'in halin innaro saida tayi kuka ganin halinda Abie yake ciki, taita kwarara masa addu'a kuwa. Su momma sunji dad'i, kuma sunata girmamata. Samha sai dama-dama takeyi dasu Aiyaan, motsi kad'an tace, “ALLAH yasa Aunty gimbiya muma ta Haifa mana irinku”. Su Momma sunata amsa mata da amin. Nidai kaina na k'asa saboda kunya, ina lura da Galadima kuwa duk sanda tafad'a saiya murmusa kuma bakinsa ya motsa alamar yana amsawa da amin. Sosai naji dad'in ganin jikin Abbanmu shima, dan har magana mukayi, jikinsa yayi k'yau sosai, karayunne ma kawai suka rage nakula, amma k'ananun ciwukan duksun warke, to wajene dayake samun kulawa ta musamman. Munaya harda rungume inna, itako ta tureta tana hararta, su Aiyaan kam duk sun d'are bisa cinyarta suna d'okin ganinta da kewarta. Itama tayi kewarsu over, tsakanin uwa da d'a kenan (iyaye mata ga naku fa🥰🥰🥰❤👍🏻). Haka muka dawo gida ina farinciki, koba komai nasamu nutsuwa mai yawa a yau d'innan, aiko ban yarda mun kwantaba saida nayi nafilfili domin mik'a godiya ta ga ubangijin sammai sannan na kwanta. Galadima kuwa muna shigowa d'akin sirrinsa ya shiga yanata aiki. ___________________________ Hankalin Minister ya kai k'ololuwar tashi shida families nasa akan 6atan 'yarsa, farhat, duk wata hanya daya kamata subi sunbita amma babu koda labarin Wanda ya ganta, tun lamarin nabasu mamaki harya koma basu tsoro, ga wani text massage da akama minister d'in d'in kwana 10 daya wuce. _Idan kana buk'atar 'yarka kana iya mik'a wuya._ Wannan massage ya tsaya masa a rai, har police sun kar6a amma sun gaza gane komai gameda massage d'in ko wannada ya turo shi. Mahaifiyar Farhat harda kwanciya asibiti, dan ita kad'aice mace a gidan, dan haka suke masifar son yarinyar da mata gata, dudu shekarunta 16 ne kawai, tana wata private boarding school ne a abuja. a binciken da Galadima yakeyine ya gano hakan, kuma yayta bibiyar yarinyar har saida yasamu nasarar saka Nuren ya kwamuso masa ita. ___________________________ Tunda muka dawo India bani da lafiya, kullum innaro cikin min gorin ni ragguwace take, bana wani kulata dan tawa ta isheni, koma uwarmi zata fad'a ta shekara fad'i, bazan yarda mu Raba hali a gidan surukai naba, nakan bar lamarinta a wasan jika da kaka agabansu, amma ni nasan badan hakan takeyimin ba, ita kanta innarmu bata kulata ko kad'an, idan tanayi shiru take mata ma. Kulawa kam bazanyi butulciba ina samu wajen Galadima dasu Momma, musamman ma jakadiya da Aunty Mimi. Saukina ma cikin bamai tsurfa baneba, komai inaci hankali kwance, kuma ban ta6a amaiba ko wani zubda yawu, saidai zazza6i da ciwon jiki. Yaudai dole Akash yazo har gida ya sakamin k'arin ruwa, kozan sami sasaauci. Yini guda yau a gida Galadima yayisa, duk wani motsina akan idonsane. ************************** *_5 months ago_*🙆🏻🙄😆 A kwana atashi babu wahala wajen ubangiji, rayuwa ta shud'a, kwanaki nata sauri, a wanni da mintuna kam ai ba'a cewa komai, abubuwa masu yawan gaske sun faru a watanni biyar d'innan, ciki harda warkewar Abbanmu sarai, tamkarma baiyiba, saidai k'afarsa da yakan d'an tizgid'a saboda matsala data samu, shima saika k'uramasa I done zaka fahimci hakan. Innaro dai dasu Aiyaan tuni suka koma saboda makaranta, sai dai duk Hutu Galadima yakansa azo dasu Aiyaan d'in, hakama Munubiya da yaa marwan sunzo sun mana sati biyu sukaga jikin Abba da Abie. A wattani biyar d'inna Galadima yaje Nigeria kusan sau hud'u, dukda bai ta6a fad'amin wani abuba ina samun bayanai ga Saleem da sarkin Mota. har yanzu kuma Farhan d'iyar minister tana hannunsa, hakama Malam Saminu driver Alhaji Balala. Yaran gidanmu masu cikkuna duksun haihu, su Siyama an zama iyaye, naji haushin rashin halartar taron suna ko d'aya, dan dana fad'ama Galadima inason zuwa banza yamin, naci kukana kuwa na hak'ura, sai turomin abubuwan da akayi sukaitayi ina gani. Cikina ya fito kwarai da gaske, dan yanzu yana cikin wattani 7 da wasi kwanaki, yamin d'as yakuma sakani k'iba, duk kamannina sun canja, kumatuna sunyi manya, dukdai wanda ya ganni zaisan na canja, hakama Munubiya, idan ta turomin hotonta nata dariya kenan. Tsakanina da Galadima kuwa har yanzu muna a yanda kowa ya sammu, canji d'aya zance ansamu shine nuna yawan tausayinsa akan cikin jikina, dan dukkan wani motsina cikin nuna damuwarsa yake. Idan yana wajen aiki kam yakan kirani sau uku sau hud'u dan yaji lafiyata kawai. A 6angaren iyayensa da danginsa kam banida abin fad'a sai godiyar ALLAH, dan tamkar a kainane aka fara ciki haka suke nunamin kulawa. Hakan nama Innarmu da Abba dad'i, hankalinsu na kuma kwanciya sosai akan aurenmu. baba k'arami yakanyi wata d'aya ya tafi Dady kuma yazo, haka suka dingayi har ALLAH yabama Abba lafiya. Jikin Abie ma said dai muyitama ALLAH godiya, dan bayan magana an kuma samun cigaba 6angaren motsa hannunsa, yanzu kuma maganarsa takan d'an fito yanda akeji, saidai duk wannan cigaban da ake samu babu Wanda yasan dashi, har mai martaba k'aninsa, kaf masarautar gagara badau da dukkan wani makusanci bai San komaiba a kai, dan papi yahana fidda maganar, ko zuwa akai dubashi yakan komane tamkar yanda ya saba kamar da, daga mama Fulani har mai martaba sunzo kusan sau uku dubashi, hakama Muftahu da Harun, 'ya'yan Sarki ma dama suna k'ok'arinzuwa lokaci-lokaci suma. Hakama Hayatuddin Autan mama Fulani. amma babu Wanda aka bama damar sanin wani sirri akan jikin Abie d'in. dagamu sai mu kawai muka Sani. Dukda fama danake da kaina haka na dage muka cigaba da addu'oin nan, zuwan innarmu ma yakuma sakamu ho66asa saboda taimakon da take bamu, sannan muka raba addu'oin ga wasu musulmai malamai dake nan suma suka cigaba da tayamu, aka cigaba da bama Abie yanasha da wanka, doctors d'in sunyi surutunsu harsun gaji sun barmu, dan munk'i fasa masa amfani dasu, tunda muna ganin haske a lamarin sosai. A wata ranar talatar da su Abba suke shirin tafiya k'arshen satinne ina zaune a falo ni kad'ai, dan Galadima ya fita aiki tun safe, zafine ya isheni na dawo falon na k'ure AC, dan Galadima ya saka ma na bedroom d'in key saboda k'urewa da nakeyi, gashi inata fama da mura, shi kansa abin cikina ance tana Neman shafarsa. nikam bana iya hak'uri da Abu mai sanyi konasha ko AC. Sosai na baje ina kwasar dad'ina, sai faman lumshe idanu nake a cikin kujera, gama wayarmu kenan da Munubiya itama tana bani labarin halin son Abu mai sanyin datake a ciki, kullum Yaa marwan fad'a shida mama Rabi'a amma bata d'aga k'afa, data faki ido saita sha, Ayusher da dole ta dawo gidan tayata wasu abubuwan saita gani ta sanarma Yaa marwan, shikuma yay ta jarabar masifa, amma hakan bazai hana gobe tagani ta shaba........ Jinai kawai iskar dake ratsani ta daina shigata, na bud'e ido sai naga Galadima tsaye jikin k'arfen bene daya shigo ta falon ya hard'e hannayensa a k'irji ya zubamin ido ransa a 6ace, hannunsa rik'e da remote d'in ACn. Tsorone ya kama ni, na tashi zaune ina wani marmar da idanu, da hura kumatu danaketa yi, takowa yayi inda nake, idonsa tamkar zai fad'o dan hararata “k kin rainani ko? bazan hanaki Abu sau d'aya ki daina ba, ki duba muran dake damunki tun cikinnan nada wata 3, shin ke bazaki tausayama kanki baneba?”. Shiru nayi bance masa Uffanba, sai faman kumbura baki dai nake yi. “kinsan ALLAH idan baki maida wannan bakinba na kamashi saiyayi jini”. Da Sauri na maida bakina, dan ban manta muguntar da yaminba kwana biyu daya wuce, ba k'aramin morata yakeba yanzu, saboda ALLAH yabani ciki mai sakani yawan buk'ata, sai komai ya lafa nayita masa kuka, shikam ya shareni saboda shegen miskilanci da k'asaita, idan na ishesa yace zai makeni, aibashi yace na kawo kaina ba, dan haka nabar cika masa kunne da ihu, anjima ma nazo yi zaiyi tunda ba fyad'e yaminba ninake kawo kaina. Sometimes nakanji haushin furucinnan nasa, nakuma yi alk'awarin nisantarsa, amma bana iyawa, kona d'auki alwashin saina karya, da yazo yara6u jikina nake mik'a wuya, mugun tunda ya gano lagona saiya dunga bina ta wannan hanyar, duk sanda yaji buk'atata yasan yanda zaiyi ya ra6u da jikina harta kai ga wani abinda nikuma zan mik'a wuya batareda na saniba, saidaga baya nake gane kuskurena. Ganin namasa banza nak'i tankawa saiya shige bedroom yana tsaki, komawa nayi na kwanta ina share hawaye. ga zafi ya fara addabata. Kusan mintuna 19 sannan ya fito, ya canja kayansa zuwa k'ananu, da Alama wanka ma yayi, k'in kallon inda yake nayi harya samu kujera ya zauna, remote ya d'auka ya kunna TV. Haka mukaita zama tamkar wasu kurame, kusan 30minutes, kiran da Nuren yamasane yasakashi d'agawa, bansan miyake fad'a masaba naga dai ya mik'e ya shiga d'akin sirrinsa. Na dad'e ina kallon k'ofar, zuwa can nima na yanke shawarar binsa kawai. Doguwar rigace yellow a jikina, batada hannu, sannan bata kaimin k'asa ba, kad'an ta wuce guywata👗, banason kaya masu nauyi saboda jin zafi, sai silifas d'in k'afata jaa mai taushi. cikinan ya kaimin ko ina, jinake kamar na jawo haihuwar na juyeshi na huta. Ciki-ciki nayi sallama, bai jiniba, hankalinsa nakan Computers d'in d'akin dayake k'ok'arin dai-daitawa, duksun kawo wuta, har k'aton glass d'in dake jikin bango guda na d'akin, ban ta6a d'aukar shima Computer baceba sai yau, dukna d'auka saboda ado aka sakashi a wajen. Sallamar na k'ara yi, ya juyo yana kallona, idonsa na cikin medical glasses mai haske, dan har kwayoyin idanunsa ina hangowa. Kamar zai shareni saikuma ya amsa mini, juyawa yayi yacigaba da abinda yakeyi, mikuma yagani saiya juyo, ya jawo kujera ya gyaramin, yay min alamar da ido na zauna. Babu musu na zauna, ya d'auki remote ya rage gudun AC d'in d'akin, sannan ya juya ga abinda yakeyi. Yanda yake sarrafa Computers d'in saiya tafi da imanina, kai guy d'innan yasan Computer over. Bansan lokacinda bakina ya su6uce nace, “yalla6ai ALLAH ya baka”. Juyowa yayi yana kallona da mamakin furucina, ya saka pen d'in hannunsa a baki yana wasa da shi, kafin ya shiga takowa gareni, k'asa nayi da idanuna nabar kallonsa, yaja kujera ya zauna kusa dani, idonsa a kan cikina, ban Ankara ba naji hannun nasa a saman cikin, idanu Na d'ago Na kallesa, ya d'agamin gira d'aya yana fad'in “ALLAH ya bani k'yautar magaji?”. Murmusawa nayi ina girgiza masa kai, “niba haka nake nufiba fa”. “mikike nufi to?”. ‘yay maganar yana janye hannunsa daga cikin nawa’. Fuska nad'an ya mutse, cikin salon yanga nace, “ina nufin ALLAH yabaka nasibin sarrafa Computer's ”. Yanda nayi maganar cikin salo saiya sakashi murmusawa yana ta6e baki, “toni miye namin yanga yalla6iya? saikace kina tare da masoyinki?”. Haushi ya kamani Na dalla masa harara. Bai kulaniba ya mik'e yana fad'in, “masu cikifa saida uzuri”. Harna yunk'ura zan mik'e yace, “oh haushi kikaji? to sorry zauna kiga wani abu”. Komawa nayi Na zauna INA k'unk'uni. Hotunane da yawa ya nunomin daga cikin Computer, ya danna hoton farko ya fito sosai. Batareda ya kalleni ba yace, “wannan sunansa *Kabiru Ibrahim*, nasanshi shekaru kusan 9 da suka shige a dalilin neman bayanan sirrina tacikin Computer, nabashi dama yashiga sosai saboda a time d'in yaci k'arfina, inada yak'inin wanine yabashi wani yanki sirri daga abinda nake da shi, ganin ya zuk'i bayanai 90 a cikin 100, saina tura masa goman gaba d'aya, saida ya zamana 99 duk sun shige ga Computers d'insa sannan Na nuna masa banbancina da shi, Na lalata abinda yake da shi da Wanda ya samu agareni, tundaga wannan ranar kuma nafara bibiyar rayuwarsa. Abin mamaki saina gano yanada Ubangida, shine wannan, *Timothy yoha*, dukkan abinda ya aikata agareni Umarnin uban gidansane Timothy, Na maida akalar tunanina ga Timo, saina iske shima aiki yakema wani, ba kowa bane face tsohon shugaban k'asarmu *Labaran Ahmad kachia*. shine wannan, nasan kuma k'ila kisansa dukda dai lokacin dayayi shugabanci bana tunanin an haifeki ma gaskiya, ta silar *Former p... Labaran Ahmad Kachia* nasamu wani kundin bayanai akan tsantsar abotar dake tsakaninsu su a k'alla 15, babu maijin sirrinsu saboda Kansu a matuk'ar had'e yake, ALLAH yayima 4 daga cikinsu rasuwa shekarun baya kad'an, saisu 11 suka rage”. Ya kumayin wasu 'yan danne-danne nidai duk ina kallonsa da mamaki, hotunan mutane 15 suka bayyana, sai dai an lik'e fuskar mutum 4 alamun wad'anda suka mutu kenan. Gaban frigate d'in d'akin yaje ya had'a Coffee a mug, sannan ya tako zuwa gareni ya mik'amin, kaina Na girgiza masa alamar a'a, ya d'aga kafad'a sannan ya juya zuwaga Computers d'insa. “wannan mutane hud'un sune jiga-jigan wannan abota, d'aya ya rasu a cikinsu saura uku, *Josaya Bamma* shine mataimakin *Alhaji Lawan tanderu*, bayan mutuwar tanderu shugabancin wannan abota ya dawo hannunsa, dukkan wani shigi da fici na man fetur dake faruwa a Nigeria josaya Bamma yasanta, dan sune masu yinsa, yanda ake fita da mai a k'asar da yanda suka mallaki rijiyoyin mai ba bisa k'a ida ba, gwamnati kuma batada damar magana domin sune masu fad'a aji, sune tsoffin shugabanni da suka San dukkan sirrin k'asar, sai *Bana baba gana*, dukkan wasu magunguna dake shiga Nigeria saida saka hannunsu, akwai wad'anda batareda k'a idaba suke kaita shi da *Alhaji balala* da *William Solomon*, domin manyan likitocine masana sosai, *Hajia A'i Barnawa*, babbar d'iya ga tsohon soja *Garba mai dala sokoto*, tashiga wannan group d'in sanadin k'awarta *Victoria*, dukkan wani cin zarafi mata ko cin dunduniya suke saka ido, kullum suna ik'irarin sune masu Kare hak'in mata a zahiri, amma a bad'ini ba aikin da sukeba kenan, suna aikin gyara aljihunansu ne. wannan shine *Mansur Habibu Abu*, wannan kuma *Abdul-Naseer Nafi'u*, da *Miracle Asun*, wad'annan dukkansu manyan 'yan kasuwa ne, amma a bayyane, amma a 6oye su sukasan tsiyatakun dasuke shiryawa a k'ark'ashin k'asa *Sagir sulaiman Sulaiman* minister mai mulki a yanzu, sai wannan da wannan duk sun mutu banida matsala a yanzu tsakanina dasu, Munaya inason sanin alak'arsu da Mahaifina, wad'annan mutanen, domin sune mahaifina yay zama dasu ana gobe wannan ciwon zai sameshi, a daren ranar kuma Abie yashiga wajen mama Fulani domin gaisheta, jakadiya data masa rakkiya ta tabbatarmin da lallai yafito ransa a 6ace daga wajenta. Sannan a wannan ranar matarsa ta uku ce ta kawana a turakarsa, alhalin kuma kwannan matarsa ta biyuce, amma saboda kud'in data bama jakadiya da dad'in bakinta saita kaita turakar Abie a wannan daren, takuma sanarma matarsa ta biyu cewa takawa bashida lafiya yana fama da mura. kwana biyu kuma kafin faruwar dukkan wad'annan abubuwan Abie yayi zama Na musamman da Hakimansa saboda kama Wazirinsa da yayi Dacin amanar Masarauta wajen d'aukar sirrin cikinta ya bama wasu bak'in turawa da ba'asan dalilinsu na yin hakanba, a bincikena d'aya a cikin turawan ya Mutu, amma d'ayan yana nan da ransa. Abie ya kwanta jiyya da sati biyu aka kashe babban malaminsa, limamin masallacin sarki maikuma bama Abie shawara akan addini. dukkan wad'annan dana ambata miki sunayensu a kwai hotunansu anan d'akin, akwai abokin mahaifinki da kika fad'amin, shine Alhaji Mamman k'afur Wannan babban yaron Alhaji Lawan tanderu ne, dan wannan group sunema suka tsaya masa ya fito takarar shugaban k'asa, babbar matarsa k'anwar matar tanderu ce, wadda a gidan tanderun ta taso tun tana k'arama. Senetor halluru garba abokin Alhaji Mamman k'afur Ne sosai, akwai wani 6oyayyen sirrin dake tsakaninsu kuma, sai dai ban saniba ko Abbanki yasan wani Abu a ciki. Idan nace zan cigaba damiki bayanin sirrikan dake cikin d'akinnan kanki bazai iya d'auka ba Munaya, amma nabaki damar kimin kowace tambaya ni kuma zan baki amsarta batareda shamakiba”. Ajiyar zuciya Na sauke, Dan tabbasa kaina bazai iya d'aukar wannan bayanan nashiba inhar suka wuce zurfin haka, Na yink'ura zan mik'e, saiya matso ya taimaka min da kansa, zaman silifas d'ina Na gyara a k'afata, sannan Na taka ga wasu hotuna, hotona na nuna masa dana muftahu, yad'an murmusa yana ta6e baki, kafin ya ajiye cofin hannunsa ya hard'e hannayensa a k'irji, “Ba manufar wannan hoton ke d'inba, dan haka manta da wannan kawai, sai nan gaba watak'il zaki iya sanin wani abu”. Zanyi magana ya girgizamin kansa, alamar karnace komai. Idona na janye daga garesa kawai, na maida kan hoton Muftahu tareda nunashi da yatsa. Takowa yay har inda nake, ya kama hoton yana kallo tamkar yau ya fara saninsa, “Muftahu d'an uwa nane, kuma abokina, sai dai bakomai ne nake sakin jiki da Shiba, domin lokacin muna yara mutumne shi mai yawan k'arya, hakanne yasaka ko yaushe muke fad'a, babu abinda na tsana ga hallayar d'an Adam irin k'arya dacin amana, wannan halayyar tasa saita gaza barin zuciyata har girmanmu, kullum kallonsa nake bai canjaba, wannan yasakani fin yarda da harun fiye dashi, saikuma yake gwadamin wasu halaye na rashin gaskiya a lokuta da dama, ban k'ara tsinkewa da lamarinsa ba sai a time d'in da abinnan yafaru tsakanina da ke a birnin gayu, Muftahu shine Wanda yakawomin shawarar mizai hana na aureki ko ta wannan hanyar zansan wani Abu, da farko na d'ana masa tarkone, na yarda da auranki na shekara d'aya, yanda yacigaba da rawar jiki sai lamarinsa yacigaba da tsoratani, randa ya saka mana pill's a fresh milk daga ranar na yarda 100% shi maicin dunduniya tane, kuma akwai wani 6oyayyan al'amarin da yake son cimma buri, wannan yasakani kauda idanu a kansa, nabashi dukkan dama, dukda kullum Harun kan nusar dani illar hakan, amma na share komai tamkar bana gani, sai dai wannan zuwan danayi maganar da kika ta6amin a wani dare ya sakani cikin dogon nazari, daga time d'in kuma na saka idanuna akan Muftahu da Harun, zuwannan da nayi na k'arshe Nigeria, naga wani abin mamaki da ban al'ajabi. akwai wani d'aurin Aure da mai martaba yace mu wakilcesa ni da Hakeem (Wambai) amma sai Harun da Muftahu sukace zasumin rakiya, ba rakkiyarce ta sani Ankara a kansuba, yanayinsu ya nusar dani kowanne akwai manufarsa, ban kulaba mukaje muka halacci d'aurin auren, anatashi Hakeem yace shi zai wuce, Dan yanada wajen zuwa, banbi ta kansaba Dan bana d'aukar raini, karramawar da aka shirya yima mai martaba sai ta juye kaina, aka karramamu sosai, ni bammaci abincinba, sai Harun da Muftahu ne sukaci, suna tsaka da cin abincin sai aka kira Harun, bai d'aga wayar a gabanmu ba ya tashi ya fice, ko alama ban kawo komai a rainaba, muka cigaba da hira ni da Muftahu, abinda na lura da shi rabin hankalin Muftahu akan Harun yake, dan yanayinshi ya nuna, zuwa can sai shima ya mik'e ya fice, yacemin yana zuwa, fitarsa babu dad'ewa d'ayar wayar Harun tayi ring, ni mutumne dabai damu da shiga abinda babu ruwansa ba, amma a ranar saina tsinci kaina da duba wayar, bansan Number d'inba, amma nasan fuskar wadda take jikin hoton da Number ta bayyana, ba kowa bace face d'aya daga cikin matan Abie na”. “Matan Abie kuma?”. “kwarai kuwa, wannan shine abinda na gani, Wanda ya zaunamin a rai, koda Harun ya dawo yaga wayarsa kusa dani sainaga kamar baiji dad'iba, na bashi ina fad'in hajia ta kiraka, kinga kuwa yanda yanemi zubewa? humm saida Muftahu ya taimaka masa, dana tambayesa se cewa yayi wai tunkan mu taho dama kansa na ciwo, nasan ba haka baneba amma na sharesa. tunda muka taho na lura ana kallon kallo tsakanina Muftahu da Harun, kuma duk sanda hakan tafaru, Muftahu kanyi wani murmushi mai tattare da ma'anoni masu yawa, Wanda har yanzu nakasa fasarasu”. Huci na fidda daga bakina, na koma Inda na taso na kuma zama, shima saiya tako zuwa inda nake, ya durk'usa a gabana tare da d'ora hannayensa bisa Gwiwoyina, idanu na d'ago a hankali na sakasu cikin nashi, k'ok'arin janyewa na farayi, saboda wasu abubuwa danake hangowa cikin idanunsa. Amma saiya hanani wannan damar, yay wani sassanyan murmushi yana fad'in.............🤫✍🏼 Barkanmu da dawowa sister's😄🤝🏻🥰🥰🥰. *_ALLAH k'a gafartama iyayenmu😭🙏🏻_* [7/3, 10:02 AM] Aysha Galadima: *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻1⃣6⃣ .................“Kin shirya taimakon Mijinkine Munaya?”. A salon da yay maganar saida tsigar jikina ta tashi, nad'an lumshe idanu sannan na bud'e a kansa, muryata na rawa nace, “ni bansan komaiba. kuma ina ganin a wajen Abie yakamata ka k'ara samun haske ai, tunda yanzu yana magana”. Murmushin takaici yayi, sannan ya kamo hannuna cikin nashi, “Kinsan miyasa nabaki dukkan wannan labarin daba kowanne mahaluki ya sansu baki d'aya ba?”. Kaina na girgiza masa a sanyaye. Ya murmusa, tareda d'ora hannunsa saman cikina, hannun nasa na kalla, shima idonsa na a wajen, yace, “saboda kece wadda zata zama uwar d'ana ko 'yata, ina fatan koda nabar duniya ban cimma burina ba kibama duk abinda kika haifa labarinnan domin ya ida cimma manufata, wannan wasiyyace ga abinda zaki haifamin, dan inaji a jikina komi zaki haifamin insha ALLAH ba zai zama ragoba, sannan kuma tabbas kin cancanta, domin kece mutum ta farko dana ta6a yarda bazataci amanata ba bayan Mahaifiyata da kakannina da yayata da k'anina. daga k'arshe ina rok'onki girman ALLAH ki sanarmin da abinda kika Sani game dani, dan tabbas nasan kinsan wani Abu, nasha auna fik'irarki a ma'auni kuma ina samunta dai-dai, dan haka batun 6oyemin ma kibarsa zuwa yanzu, kinga Abba jibine zasu koma, to lallai rayukansu tana cikin had'ari kuma komai zai iya faruwa, saboda a yanzu mak'iyansa sunyi shirin dayafi na farko ma, a zatonsu Abbanki yasanar dani komai ne. ni kuma ban ta6a wannan maganar dashiba, sannan Abie da kike magana likitoci sunyi gargad'in kar'a tuna masa da abinda ya wuce yanzun, saboda gudun dawo da hannun agogo baya, kuma kodama na tambayesa zai iya dakatar dani yace ya yafe, ni kuma nariga nataso da BURIN 'DAUKAR FANSA, a cikin zuciyata da kwanjina, Ni nasan Yaya nayi jiyana, yau d'ina ma a wahale take kasantuwa, dan haka nakeson gyara gobena da goben 'ya'yana da dukkan ahalina, inason sanin dalilinsu nama mahaifina hakan, inba hakaba bazan ta6a samun kwanciyar hankaliba”. Nad'an muskuta domin gyara zamana, ina fad'in “shikenan, amma kabani lokacin please”. “Nabaki”. yafad'a yana mik'ewa tsaye. Binsa kawai nayi da kallo, saiya kuma bani tausayi, dukda kasantuwar rayuwarsa cikin Rud'ani, hakan bai habashi zama kamilin mutum mai tarin Nutsuwa ba, gashi da sauk'in kai, saidai idan baka fahimceshi baneba, kamar yanda na kasa fahimtarsa a farko, saika masa kallon mai girman kai. A gaba d'aya yinin wannan ranar cikin nazarin maganganun galadima na yisu, tabbas abotar Alhaji Mamman kurfe da Senator Halluru da Abbana abin dubawace, na shiga tunano wasu abubuwa danaita karo dasu a d'akin Abbana ni da Munubiya, a wani time d'in da Innarmu ta sakamu masa wani gyaran d'aki, Wanda shine sanadin shigowarmu wannan cakwakiyar kuma, na dafe kaina saboda saramin d'in da yakeyi, motsin da d'an cikina yayine ya sakani dafe cikin ina lumshe idanu, gaba d'aya kaina yana Neman kullewa, har a washe garin ranar haka naita fama da tunani, danma yana hanani, amma danaga ya matsa zan d'ora daga inda na tsaya, yanzu ma dazai fita aiki saida yamin gargad'i, yace na sauka k'asa wajensu innarmu nayi hira, to kawai nace masa, amma yana fita ban fasaba, ganin lokaci na k'ara k'urewa saina d'auki waya na shiga rubuta massage mai tsawo dazan turama Munubiya. Duk abinda takeyi a idon Galadima ne, tun d'azun yana lura da dukkan motsita ta camera d'in daya ajiye a d'akin wadda koda wasa Munaya batasan da zamanta ba, ya murmusa tareda godema ALLAH, dan yasamu damar kamata a hannu, ta wannan hanyarce kawai zaiyi amfani da ita wajen samun abinda yake buk'ata ga Abbanta, dan Abba yak'i bashi kowacce k'ofa dazai san wani abinda ya sakashi shiga wannan halin, alhalin yaga tarin damuwoyi a idanunsa, masu kuma matuk'ar muhimmanci a aikinsa. Wayarsa tai 'Yar k'ara alamar Munaya na sarrafa wayarta, saurin saita abinda ya saka mata a wayarta bata saniba yayi, harta gama typing ta tura sak'on akan idonsa, shiga yayi ya duba, saiyaga Munubiya ta turama sak'on, yay hanzarin bud'ewa. (Galadima ya had'a wani tarko a wayar Munaya batareda ta saniba, dukkan wani Abu dazai shiga wayarta ko fita saiya gansa a wayarsa, ta wannan hanyarne yaga na yanzu, saimu bishi muga abinda Munayar ta rubuta to). _“ ‘Yar uwata, tabbas Allurafa na shirin to no galma, anzo ga6ar da lallai yakamata mu sanarma Galadima komai akan abinda muka Sani, danna fahimci lallai zatonmu yazama gaskiya, wannan sunedai ahalinnan da mukaga bayanai a Kansu, dukda nakula Abbanmu nasan basarwa, saidai bansan manufarsa tayin hakanba, bayan wannan itace damarsa ta k'arshe dazai yadda kwallon mangwaro ya huta da k'uda, sweetheart minene shawararki? dan burina dana haife cikinnan auren contract ya k'are a tsakaninmu, domin babu alak'a kuma kenan, kinga nima na samu 'yancin kaina, nayin auren din din din kamar kowacce mace”._ Babu shiri Galadima ya mik'e tsaye, jikinsa har wani tsuma yakeyi, lallai anzo ga6ar Ashe, hasashensa yazama gaskiya kenan kokuma zai zama, tomi wad'annan yaran suka sani? kenan Munaya Nada dalilinta na yarda da auren su na Contract? Mi Muftahu ya Sani gameda Munaya dahar ya d'anata a gareshi a matsayin tarko?, bayan shi yana nan yana ik'irarin yima Muftahu tarko da auren Munayar. Lallai kan yakula itama Munaya da 'Yar uwarta da Muftahu suna Neman zame masa RAINA KAMA. Baifi mintuna 15 ba da tura sak'on da Munaya tayi, saiga Munubiya ta kirata, duk Galadima yana kallo daga camera d'insa da kuma saitin wayarsa, dukda kuwa yana office ne, Munaya bata d'aga kiranba, saida ya katse sannan ita ta kirata, munubiya na d'agawa Munaya race, “Sweetheart kinga sak'ona kuwa?”. “Na gansa sweetheart, amma fa ni duk kin rikitani, kinga wata alamace data tabbatar miki ahalin Galadima ne?”. “Munu, tabbas alamomi da yawa sun nunamin hakan, sannanfa shima yasan Alhaji Mamman k'afur fa, kuma kinga ai a takardarnan munga sunan Alhaji Mamman k'fur d'in, gashi abokin Abbanmu sosai, nifa yau wlhy abubuwa masu yawa ya fad'amin game da sirrinsa, dukda kasancewarsa mutum mara yarda, duk dai da inaji a raina kamar ya fad'amin wani yankin sirrinsane danya bigi cikina be, amma ni wlhy tausayi guy d'innan yake bani da gaske”. Munubiya tayi murmushi daga can, cikin tsokana tace, “to ALLAH yabar k'auna dai, sweetheart”. “ban ganeba, k'aunar mi zai bari?”. “keda Galadima mana, ai soyayya kan fara da tausayine”. “Mtsoow dan ALLAH muyi magana mai amfani Munu, yanzu ya kika gani, danya rok'eni ALLAH akan nafad'a masa mina Sani, nikuma ina tsoron koba akansa d'in baneba Abbanmu yake cikin damuwar, karmuzo kuma muyi aikin Baban giwa”. Ajiyar zuciya Munubiya ta sauke, ta gyara kwanciyarta tana fad'in Munaya kodai mu sanar da innarmu ne kozata bamu shawara?”. “kai amma bakida hankali yasin, sokike innarmu taci k'aniyarmu Ashe, zatace miyasa tun a farkon lamarin bamu sanar mataba, k'ilama tayi fushi, Dan nima wlhy ayanzu ina ganin munyi wauta fa”. “to komadai miye munrigada mun aikata. Yanzu mafita zamu nema, mizai hana ki rok'eshi inhar bashi bane kokin fad'a Dan girman ALLAH karya tada zancen kawai, yakuma rik'e mana sirrinmu, idan kuma zai taimakemune akan Wanda kema Abbanmu barazana da mutuwa ai kingani munsamu madafa muma, kinga dai yanda sukaso cin galaba wajen kashesa, wlhy Munaya jinake kamar kar Abbanmu su dawo k'asarnan”. “Ni kaina tsoron dawowar tasa nakeji, musamman da jiya Yakuma maimaitamin, shiyyasa kawai na Yanke shawarar mu fad'a masa, idanma ba shi bane saiya taimakemu wajen gano wanene”. “to shikenan, sai naji yanda kukayi kenan, Yaya unborn d'inmu?”. “gashi nan ya isheni da motse-motse wlhy, na k'agara ma ya fito na huta, kema Yaya namu da lafiyarki?”. Cikin tsokana Munubiya tayi dariya, “aikoya fito nanda wata shekarar Munafata wani ya Shiga sweetheart”. “wlhy na kula bakida man kai Munubiya, sai anjima”. Munaya tafad'a tana yanke wayar. Galadima daga can yay wani k'asaitaccen murmushi yana shafa Kansa da cije lips, ya koma jikin kujera ya lafe yanamai lumshe idanu. 👭 🤣Galadima Kodai-kodai🤫 ************ Muna gama waya da Munubiya na sakko k'asa, babu kowa gidan dagani sai su innarmu sai jakadiya, a falon k'asa na iskesu suna hira. Jakadiya tace, “ranki ya dad'e kin fito?”. Murmushi namata, ina fad'in “na fito jakadiya, ya k'ok'ari?”. Tai 'yar dariya tana cewa “kuke fama da k'ok'ari ai, ALLAH dai ya raba lafiya”. Bance komaiba na zauna ina gaida Innarmu ta amsa tana tambayata ya jikin. “da sauk'i” na fad'a kaina a k'asa, nace, “innarmu Abba fa? ko barci yakeyi?”. “A'a sun fita ai shida Sauban tunda safe, zasuga likitansa daga nan sud'an zaga gari”. “Oh ALLAH ya dawo dasu lafiya to, zaisha yawo kam indai fita da Yaa Sauban ne”. Dariya jakadiya tayi, tace, “ai mai sunan manya sai a hankaki, shibama ya gajiya”. Inna tace, “a baya gajiya kam, ni ai birgeni yakeyi, babu ruwansa, sai tsokana da barkwanci”. “Ai tamkar gadone abin nasu, dan mai martaba lokacin yanada lafiya, dukda kasancewarsa shugaba hakan baya hanashi barkwanci da mutane lokaci-lokaci, to hakama magajin gari yake, daga bayane shi sai nasa halayyar suka canja, yazama shiru-shiru, amma shi mai sunan manya saibai canjaba kuma”. Ina jinsu nidai bance komaiba, sai murmushi danake tayasu dashi kawai. Mun dad'e a falon har su Abba suka dawo, masaukinsu ya wuce, Sauban kuma ya zauna muka cigaba da hira, tashi innarmu tayi tabi bayan Abba. Sauban ya mik'e yana cewa zaije ya watsa ruwa, itama sai jakadiya tashiga domin nunawa kuku abinda zai dafa, ganin haka natashi na nufi masaukin su innarmu. Nakama handle d'in k'ofar zan murd'a tareda yunk'urin sallana sainaji muryar innarmu kamar tana kuka, “Haba Abbansu dan ALLAH ka sanarmin damuwarka, Yaya kana cikin matsala amma ka gaza fad'ama kowa?, tunda tafiyarnan tamu ta gabato ina lura dakai baka ko barcin kirki, sannan inajinka kana sambatu cikin mafarki jiya da asuba akan kozasu kasheka bazaka bayarba, shin wai minene? kuma su waye?, nidai tun bayan haihuwar su Munubiya na fuskanci kana cikin wata damuwa, amma kullum cikin k'ok'arin 6oyewa kake, bansan minene kake 6oyewarba, haba Auwal, a tunanina yanzu munzama irin d'ayan da bazaka 6oyemin matsalaba kowacce irice, a nawa tunanin munkai bigiren raba farinciki ko sa6aninsa, ko kasan ranar da muka fita da dasu Samha naga lokacin da wani bak'in mutum yazo kuka ke6e gefe, kana kuma magana tsakaninka dashi cikin fushi”...... A rikice naji Abba ya katseta da fad'in Ai'sha kenan ido kike sakamin ban saniba?, dan kawai kin ganni da mutum saiki fassara da wani Abu, Toni banma sanshiba, dan kawai ya ganni bak'in fatane shine yake tambayata, amma daga hakan babu komai, tunba yanzuba kikemin tambayar mike faruwa ina baki amsa babu komai, miyasa bazaki yarda babu komai d'inba, ni nama matso da tafiyar tamu baya, dan doctor yakuma tabbatarmin da babu wata sauran matsala, ki sanarma Munaya ta sanar da mijinta gobe zamu koma kawai”. “gobe kuma Abbansu?”.. A fusace yace “eh!”. Ni kaina saida na razana da tsawarsa naja baya daga jikin k'ofar, da sauri nabar wajen jin alamun za'a bud'e k'ofar, tabbas akwai abinda Abbanmu ke 6oyewa da gaske, to wanene bak'in fatar da innarmu tagani tare da Abba ranar? a ranar tare dasu muka fita, saidai sun rigamu tafiya, saboda ni da Galadima mun biya asibiti wajen awo, saida akamin sannan mukabi bayansu, kenan kafin muje abin ya faru? dan tabbas na tarar Abba baya cikin walwalarsa, harna tanbayesa ko jikinsa ne? Amma yacemin a'a kansane kawai ked'an ciwo. Bansan na iso bedroom d'inmu ba saboda zirfi danayi a tunani, ko hawan benen ma bansan nayoba, juyowa nayi da sauri saboda jin an kama hannuna. ganin Galadima saina rajaza zanyi baya, da sauri ya rik'oni da k'yau yana fad'in “Nutsu mana”. Da k'yar na tattaro nitsuwa ta, shikuma ya zaunar dani gefensa, hawayrne suka shiga ziraromin a kumatu, Abbana yana cikin matsala, amma wani dalili ya hanashi fad'a, takai har inda yake jiyya ana bibiyar rayuwarsa kenan?. Ido Galadima shidai ya zubamin, bai hanani kukanba baikuma tambayeni dalilin yinsa ba, kusan 5minutes sannan ya kwanto da kaina jikinsa, jina a k'irjinsa saina fashe da sabon kuka, nanma k'ala bai ceminba, yadai cigaba da bubbuga bayana alamar lallashi, saida nayi mai isata nayi shiru sannan ya d'agomin kaina, dukkan kumatuna ya rik'e cikin tafin hannunsa, Kafin yay k'ok'arin saka idanunsa cikin nawa, cikin k'asaitacciyar muryarnan tasa mai kama da anmasa dole yace, “Haba yalla6iya, sokike ki haifamin abin cikin kwan mai saurin kuka irinkine wai shin?”. Bansan Sanda murmushi ya su6ucema fuskata ba, na lumshe idanuna saboda bana da jimirin jure kallon da yakemin, shima murmusawa yayi, sannan yakai fuskarsa dab da tawa yana huramin iskar bakinsa a saman ido. Ban iya hanashiba kusan mintuna 2 sannan ya daina, bud'e idona nayi nad'an kallesa, ya d'agamin gira yana fad'in, “ya dai?”. Cikin tunzuro baki nace, “babu komai”. “To miye abin jin haushi daga tambaya”. ‘yay maganar yana sakin kumatuna’. Binsa nayi da kallo, ganin zai fara k'ok'arin cire kaya, na mik'e zan fice, dan yanzu na lura lamarinsa kullum k'ara girmama yakeyi, baya shakkar cire kaya a gabana ko sakawa, sai dai ni na fita na bashi waje. Hannuna ya rik'o, na waro ido waje cikin mamaki. “ina zaki?”. ya fad'a cikin tsare gida. “ba wanka zakayi ba?, idan kagama zan dawo ai”. “toni dodone?”. “A'a na fad'a ina ta6e baki”. “to koma ki zauna ki kalli sadakinki”. Idanu na waro masa waje da hangame baki. Yiyai kamar bai ganniba ya basar. bai sakeniba yakuma cigaba da cire kayansa da hannu d'aya. Ni daifa k'in kallonsa nayi, dan wlhy kunya nakeji sosai, dukda 'yar shak'uwa ta shiga tsakaninmu hakan bai sa mun saki jiki da junaba, garama shi idan rashin kunyarsa ta motsa yakanyi abinda ya gadama yana basarwa a dole kar'a kawo masa raini. Yakan bani dariya sometimes, amma nima saina Basar saboda Jan aji. Iska kawai naji a cikin kunnena, da sauri na waigoshi, ganin sa dagashi sai boxer sai na juya fuskata. Bayana ya koma ya zagayo da hanayensa duka akan cikina, yayinda kansa ke a kafad'ata, muryarsa can k'asan mak'oshi yace, “miya sakaki kuka?”. Salon da yay maganar ya sakani lumshe idanu saboda tsigar jikina data tashi. Nace “kabari ka gama zan fad'a maka”. “miyasa ba yanzu ba?”. “ka saka riga to”. Murmushi yayi yana shafa cikina, “my friend sarkin tsiwa sarkin kuma Kunya, akwaiki da abubuwan bi........” Saikuma yay shiru yak'i k'arasawa, hannuna na saka na rik'e hannunsa da ke yawo saman cikina, nace, “ka k'arasa mana, akwaini da mi?”. “Humm” kawai ya fad'a yana sakina, yaja bathrobe d'insa dake jikin hangar ya sanya, saida naga ya fara k'ok'arin d'aure igiyar sannan na d'ago na kalleshi. “To mikuma kike kallo?”. Ya fad'a cikin tsare gida. Baki na ta6e ina fad'in, “miye abin kallon to?”. Ya d'an fiddo ido sannan ya matsoni, “zona nuna miki”. Nasan ko guduwa nayi saiya kamoni dan haka na duk'e ina fad'in “wash ALLAH cikina”. Tsayawa yay cak, saikuma ya tako da hanzari yana tambayar lafiya?. cikin marairaice face nace “Motsi yakeyi ALLAH”. rankwashina yayi aka yana cewa “ke d'inan ko”. Dafe wajen nayi, bai kulani ba ya shige bathroom, na harari bayansa ina masa gwalo, nasan inda banyi hakaba bakina ne zaisha wahala. Ina zaune ya fito, na d'auke kaina tamkar ban ganshiba, shima hakan yayi, ya wuce wajen frigate ya d'akko ruwa da Kofi, kujerar dake wajen karatunsa ya jawo ya zauna yana fuskantata, batareda yayi yunk'urin cire bathrobe d'in jikinsa ba, yanzun kam babu wasa a fuskarsa, ban damuba dan nasan halin kayana yanzu, yanzu zakiga yasaki jiki yana magana kamar ba shiba, anjima kad'an saiya koma Asalin Galadimansa dana fara gani a Hospital, Mara dariya mara later r😏. K'afarsa d'aya ya d'ora kan d'aya yana shan ruwa, yasha kusan rabi sannan ya cire, batareda ya ajiye kofinba ya maido dukkan hankalinsa kaina, “A kwana biyunnan kokin lura Abba yana cikin damuwa?”. d'ago idanuna nai na kallesa, a sanyaye nace, “abinda naji innarmu na masa Complain kenan yanzu, amma saiya nuna fusata”. “shine kika shigo kina kuka?”. Na jinjina masa kai batareda nace komaiba. Shima bai sake cewa komanba ya kauda idonsa daga kaina yana kur6ar ruwansa. kusan 2minutes sannan yakuma kallona, “Munaayaa mukawo k'arshen 6oye-6oye mana”. Kallonsa nima nayi, nace, “kamar ya?”. “humm” yafad'a yana cije lips, mik'ewa yayi tsaye ya ajiye cup d'in hannunsa a gabana, sannan ya shiga zagaye d'akin hannunsa goye a baya, nikam dai binsa kawai nakeyi da kallo kamar na samu television, maganarsa ta katsemin tunanina. “Munaaya! Mikuka ta6a gani a d'akin Abba ke da 'Yar uwarki?”. Zumbur na mik'e dan mamaki, “yalla6ai a ina kasan wannan?”. batareda ya kalleni ba yace “Munaya Sameer ya wuce dukkan tunaninki, dan haka fad'amin?”. Ajiyar zuciya na sauke, wadda ta tilasta masa juyowa ya kalleni, nace, “yalla6ai ba fad'a maka bane matsalar, kuskuren muhallin fad'arne da kuma makomata”. “bakida dukkan Matsala da wad'annan, idan bai danganceni ba zan d'auki matakin taimakon sirikina, makoma kuwa inada yak'inin kare martabar matata uwar d'ana ta kowanne hali”. Furicinsa yaban mamaki, dan haka nace, “matar Contract ko?”. “Well Duk yanda kika fassara dai-daine, abinda na Sani kawai wannan maganar batada nasaba da waccan, dan haka kibar kowanne a muhallinsa sai lokacin yinsa yayi”. “humm” kawai na fad'a na koma na zauna inda na tashi. Idonsa a kaina ko k'yaftawa bayayi. Na nisa sannan nafara fad'in, _“Na tabbata tunkan ka k'ulla alak'a dani saida kasan koni wacece, dan babban mutum irinka bazaiyi Abu babu wani tanadiba, banida matsala wajen maimaita maka sunana ko tarihin ahalin dana fito, kamar yanda kasani mu 'yan biyune hakan yasaka ba'a banbancemu ni da 'yar uwata, sai dai hallaya takan banbantamu ga Wanda ya sanmu, Munubiya mutumce mai hak'uri da yawan kawaici, a wajen gadon hali tabbas ta biyo mahaifiyarmu ne, sa6anin ni Munaya mai zafi da yawan tsokana, a lamarina babu ragi ko d'aga k'afa, inhar kaga nayi dogon zama da mutum babu sa6ani to ka tabbata ya tanaji matakan iya zama danine, basai amfad'a ba nima kaina nasan halayena na kamanceceniya dana Mahaifina da kuma kakata innaro, a wata litinin d'in da bazan ta6a mantawa ba sai mahaifinmu yayi wani bak'o, matsalar da aka samu shine yazo bai iske Abba a gidaba, a wannan ranar innarmuce da aiki, dan haka hak'in tarbar wannan bak'o saiya rataya a wuyanta, maimakon tayi da kanta saita saka cikinmu ni da Munubiya wani yayi”._.......................✍🏼 Mu had'u a page na gaba🤫 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu🙏🏻😭_* [7/3, 3:55 PM] Aysha Galadima: *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉1⃣7⃣ _..................“Da haushi na d'auki ruwan da innarmu ta bani na fita, saboda muna tsaka da kallon wani film daneke masifar sone, Munubiya dan kartaje kaiwa saita hau barcin k'arya. Tunda na shigo shegen mutumin nan ya tsura min idanu yana lasar baki, kai kace tsohon mayene yaga nama, a zafafe na dire tiren agabansa ko k'ararsa zatasa ya dawo hayyacinsa, amma wawannan yayi nisa, na buga tsaki a zuciyata zan fice, caraf ya kamo hannuna, ban dubi girmansa ba na dage na watsa masa mari, hakan kuma yayi dai-dai da shigowar Abbanmu falon. Amma d'an iskan ganin Abbanmu da marin danai masa baisashi sakin hannunaba, saida Abba ya daka masa tsawa da fad'in “SD! wane irin iskancine wannan? a cikin gidana ka kama hannun 'yata?!”. Abba na rufe baki ina kuma bashi mari na biyu, tunda naga alamar shi bunsurune. a wannan karon ya saki hannun nawa, saboda janyeni da Abba yazo yayi, Abba ya nunamin k'ofar fita, koda na fita saina la6e a corridor d'in shiga falon bak'in._ _A zafafe Abbanmu naji yana fad'in “SD ubanwa yabaka damar shigomin gida ne?”. sautin tafin bak'on na jiyo dan haka nai saurin lek'awa ta kafar labule, gani nai yana zagaye Abba yana dariya da tafi, cikin shak'iyanci yake cewa “Alhaji Auwal, Alhaji Auwal! dama kanada k'yawawan 'yammata haka? Woow nice babie, idan na samu wannan ai ko rana bazata sake ganina ba, wlhy nasan zan kwashi rom........., mari Abba ya zuba masa a kumatu, yana nunashi da yatsa, a matuk'ar fusace yace, “wlhy idan ka kuma furtawa saina datse kazamin harshenka a falonnan, wawa kawai”. SD ya shafa kumatunsa sannan ya sumbaci hannun yana hurama Abba, “Kafa birgeni Alhaji Auwal, kai jarumi, 'yarkama jaruma, kai inason irin haka mutumina uhhhhhhm mutccch”. ya k'are maganar da kuma kissing hannunsa. Banza Abba yamasa ya d'auke kai daga kallonsa yana fad'in “miya kawoka gidana?”._ _Alhaji Auwal kenan, kaima kasan dakaga SD kasan zancen, a wannan karon da albishir d'in k'arin farashi akan tayin baya nazo maka, sannan kuma damace a gareka ta k'arshe hakan, mun yanke shawarar baka naira milyan 500”. Abba yaja tsaki yana hararsa, “ka koma ka sanar ma iyayen gidan naka ina kan bakana, sannan Ku farka daga barcin da kukeyi, dan bazan ta6a badawa ba, kamar yanda ban ba da jiya ba, bazan bayar yauba, sannan gobe ma bazaku samuba, wannan kuma yazama first and last dazaka shigomin gida, inba haka ba ina mai tabbatar maka zaka aikata kuskuren da bayan bayanka ma saisunyi takaicin jin yanda zaka k'are”. “kwantar da hankalinka sarkin jarumai, tabbas zan tafi, bakuma zan sake dawowa ba balle nayi nadama Oga, ammafa bazan 6oye makaba, kana bani mamaki, kak'i bama Wanda akace ka bamawa, sannan kak'i saida mana mu masu buk'ata, shikuma wannan Abu ba tuwoba balle muyi tunanin zakacine, waikai mike damun kankane haka? ka zauna kanata rik'ema Wanda yarigada ya mutum amana, shikuma Wanda kakema tanadin bashida maraba da gawa, koda yake ashefa ga Galadiman Ku nan, koshi kakema tanadi?”. “wannan ba matsalarka bace”. Abba yafad'a cikin karsashi. “kumafa gaskiyarka wannan ba matsalata baceba, amma tabbas inada yak'inin kai zata zama taka matsalar maybe ma harda santaleliyar budurwar 'yarka, lallai labarin k'yak'yk'yawa da ahalinta zai Shiga duniya kwanannan, nabarka lafiya, ka huta”._ Da sauri nabar wajen gudun karya fito ya ganni, nakoma cikin gida ina juya wad'annan zantuka na abbamu da bak'onsa, masu tsananin wahalar fassara, mi bak'on yake nema a wajen Abba dahar yake ik'irarin sun basa zunzurutun kud'i naira na gugar naira, d'ai-d'ai har miliyan d'ari biyar? Amma dukda yawansu Abba bai firgitaba balle mik'a wuya?, sannan wanene Galadima kuma? Miyake nufi da labarina zai shiga duniya? Na shiga uku ALLAH karka bama bawannan damar cutar da rayuwata ko ahalina gaba d'aya. Munubiya data lura da halin danake cikin ta sakani gaba da tambayar, tun ina k'ok'arin 6oye mata Dan kar hankalinta itama ya tashi, harna fito fili na sanar da ita gaskiyar abinda naji da kuma gani, harma Wanda na aikata. Hankalin Munubiya ya tashi sosai itama, nanfa muka Shiga kullawa da kwancewa Munason gani gaskiyar lamarin, amma mun kasa kama bak'in zaren, fita kuwa mun koma yintane a d'arare saboda tsoron furucin mutuminnan. a wata ranar talata da Abba zai dawo daga tafiya sai innarmu ta sakamu gyaran d'akinsa saboda kanta namata ciwo. muna tsaka da aikin sai muka tsinci wani file da yasha k'yak'yk'yawar adana a awani akwati dake cikin wardrobe d'in Abba, to dama da biyu muke aikin, harda bincike akan Neman hasken maganganun da mukaji ranar, jikinmu har rawa yake muka bud'e wannan file, a shafin farko mukaci karo da wani Abun daya kuma rikita tunaninmu”. 👇🏻 *_Tabbataciyar wasiyya ga ahalina, koda ace na kwanta dama kafin cimma burina ko mik'a wannan sak'on amana ga Wanda ya cancanta, to na shaida muku da cika umarnina na ida nufina a garesu 'ya'yana ko 'yan uwana, inason Ku isar da wannan amana da aka bani ga ahalin wannan masarauta............”._* “iya nan rubutun ya tsaya, muka bud'e shafin na biyu kozamuga sunan masaurar da Abba ke magana da k'arashen zancensa, amma sai sunayen mutane muka gani a k'alla sunkai goma. Wucewa mukayi shafi na uku, a dai-dai wannan lokacin Abbanmu ya shigo d'akin batare da mun Ankara ba, wata hargitsatstsiyar tsawa mai tsinka hanji ciki da zukata ya daka mana yana fad'in “ku harkunkai girman da zakumin bincike a d'aki a matsayina na mahaifinku? mi kuka sani akan wannan takardar dahar kuke binciken abinda ke cikinta? Yaushe kuka koma la6e?”. haka Abba ya rikice gaba d'aya muma ya rikita mu, ya dinga zabga masifar dahar tajawo hankalin jama'ar gidanmu, indai tak'aice maka bayani har innarmu saida fushin Abba ya shafa ranar, hakanne yasani fahimtar Abba ya gane naji komai a ranar. munshiga damuwa a time d'in matuk'a, dukda hak'urin da muka bashi yak'i saurarenmu, ya d'au tsawon lokaci yana fushi damu kafin ya daina. bayan komai ya daidaitane kuma wani yammaci mun fito daga school saiga motocika a jere suna tsula uban gudu a titi, wucewarsu tamkar iska yasakani fad'ar bak'ar magana ga manyan k'asarnan har 'yan uwana na tayani. Sai kuma mukaji sunanka a bakin wani saurayi da 'yammata biyu. Wannan ganinaka ne yasakani dawoma Munubiya da abinda ya wuce, saboda sunan Galadima da mukaji saurayinnan ya ambata, sai muka dinga tunanin kokaine Wanda muka ta6aji a furucin bak'on Abba?. ga kuma sunan masarauta da muka gani a rubutunsa, dukda bamuji sunan ainahin masarautarba kuma, balle mu tabbatar da kaid'inne.. Ganinmu dakai na biyu kuma saika bani haushi, dan ganinka mutum mai yawan izza, sainaga bebekin Abba daya saka kansa had'ari akan Wanda shi baima damu da damuwar kowaba sai tasa gakuma tarin girman kai Dana hango tartare dakai”. (Kafayi hak'uri, gaskiyata nake fad'a, guntun murmushi kawai Galadima yamata baice uffanba) taci gaba da fad'in “Wannan ne dalilin yimaka tsak'i a asibiti, idan har baka mantaba, har dogarinka d'aya yataho da zummar d'aukar mataki amma ka dakatar dashi da fad'in ya barni”. Galadima ya murmusa alamar bai mantaba. Nace, “ka tuna kenan?”. “Na tuna kwarai da gaske, dan bancika manta abuba saidai idan na d'aukeshi mara muhimmanci, amma a time d'in ai banga face nakiba, shiyyasa banida tabbacin kece, saidai na muku kallo d'aya a lab da muka iskeku keda sisters d'inki, ni nama zata Ku 'yan uku ne ai”. “Umyim, amma a time d'in babuma Wanda zai d'auka Kasan da zamanmu a lab d'in, dan gaisuwar da ake maka ma, kamak'i amsawa sai d'aga hannu, hakanne ya tunzurani na fito daga lab d'in, dasu munu sukace kainema kabada jinin da za'a sakama feena ban yardaba”. Baki Galadima ya d'an ta6e yana shafa kwantaccen sajensa, ya d'agamin gira d'aya yana fad'in “bazaki fahimta bane yalla6iya. yanzu labarin da kika bani ya farune duk a wace shekara?”. Na d'an ya mutsa fuska ina fad'in bamai nisa bace, dan ko 2years cikakku baza'a k'ulla ba, Muna Exam d'in NECO nema, dan har results d'inmu suka fito aka fara biyan JAM Abbanmu ya biyama sauran 'yan uwanmu amma banda ni da Munubiya, sai baba k'aramine ya biya namu, so munfara karatu dai babu dad'ewa muka shirya da Abbanmu saboda magana da dad d'insu Ayusher yamasa Yakuma sake bashi hak'uri. tundaga nan komai yazama Normal. Amma kaikanka yakamata kayi mamakin yanda a kwanaki kad'an na amince da tayin auren Contract d'in da kukaimin, dukda ba waccan binciken namu kawaine keda alak'a da amintar tawaba, akwai wani dalili daya shafi ahalina”. Mik'ewa Galadima yayi yana salute d'ina, yace, “kin cancanci yabo my friend, dukda tabbas a farkon aurenmu kema kina cikin zargina akan turoki akai gareni tun farko, amma yanda kike halayyarki da d'abi'unki sai kika kauda hankalina, a tunani na dukkan mutum dazai kwantarmin dakai yaringa nuna tsorona to tabbas wannan mutumin sunamsa *MAGE MAI KWANCIYAR 'DAUKAR RAI* a wajena, amma kece mutum ta farko kuma mace data iya mayarmin murtanin magana kai tsaye, batare da shakka ba, sai dai inason Sanin minene alak'arku da Muftahu to?”. “muftahu kuma? babu wata alak'a bayan wadda kasani, dan tare Na fara ganinku ai”. Takowa yay zuwa inda yake zaune a da, ya koma saman kujerar ya zauna, “kin tabbatar babu alak'a ta kowane fanni?”. “miyasa kake kokwanto? inhar zaka kasa gaskatani a nan bai kamata ka aminta da zancena Na farkoba kenan?”. Ya murmusa yana fad'in “kozaki gaji Abba ne?”. Nace, “akan me?”. “jaridanci mana, naga kin shahara wajen iya bincike”. Mik'ewa nayi saboda k'afata tafara yaamm alamar jinina yana buk'atar motsawa, nafara d'an takawa. hannaye kawai ya hard'e a k'irji yana bina da kallo, saida nad'an zagaya d'akin kafin nabashi amsa da fad'in “yalla6ai kasan wani Abu kuwa?”. Kansa ya girgizamin kawai. Nace, “humm nifa nan daka gani, kwakwalwata tana aiki fiyeda yanda kake aiki da agogo”. “really?”. “baka buk'atar jayayya”. Ya d'aga kafad'a yana ta6e baki, “hakane kuma”. Sharesa nayi na zauna a bakin gadon danna d'an mik'e, a haka najawo filo na kwanta k'afafuna a k'asa. Tasowa yayi ya dawo ya zauna saman k'aramin table d'in gaban sofa, jinai kawai ya kama k'afata ya d'ora saman cinyarsa yana matsamin a hankali. Da mamaki na d'ago kai na kallesa. Ido d'aya ya kannemin yana d'an ta6e gefen bakinsa, ya maida kallonsa ga k'afar. Sabon salo, na fad'a a raina. a fili kuma nace, “yalla6ai kaine......” Bai bari na k'arasa ba yay saurin fad'in, “ba dole na taimaki lafiyar abin cikin kwan ba”. Harara na dalla masa ina janye k'afata, ya kalleni da mamaki, “ya haka? ko haushi kikajine?”. “miye zai Sani jin haushin? saika bari idan yafito duniya ka matsa tashi k'afar”. “oh ni Sameer naga ta kaina”. “zama kaga ta k'afa bata kaiba, Sunan nakama bazaka iya fad'arshi da r ba”. “oh nan kuma kika dawo?”. Matsawa nayi baya saman gadon sosai batareda na bashi amsaba. shima saiya taso ya hawo gadon, hakan yasani yunk'urawa zan sauka na bar masa, fan nasan hawan nasa bazai haifar da d'a mai ido ba, yasa hannu ya rik'eni, “yalla6iya ai saikin maimaita mikika fad'a dalla-dalla”. “lah wasafa nake maka, kaga rigar wankace a jikinka kaje ka cire kar mura ta kama ka”. “Ai kinga dai-dai kenan”. Yay maganar yana k'ok'arin kwance igiyar rigar. Hannunsa nayi azamar rik'ewa ina marairaice face alamar yaji tausayina. Baki ya ta6e yana ture hannuna, na kuma k'ank'ame nasa nak'i bari. Murmusawa yayi, ya kwanto gefena tareda sakani jikinsa ya rungume. “Nace please wankama zanyifa, zafi nakeji”. Maidani yayi ya kwantar, cikin kunnena yace, “kedai fad'i gaskiya, ko kina son a.......”. Rufe bakinsa nayi da tafin hannuna ina kukan shagwa6a, ya shiga k'ok'arin cirewa amma nak'i bari, shi dariyama na bashi, irin wannan hak'ilo haka. duk yanda yaso na barsa k'i nayi, saida barci yafara fisgata hannun ya zame. Kansa ya girgiza kawai yana murmushi, a fili ya furta “mai bakin tsiwa”. Ya k'are maganar da sumbatar goshinta yana gyaramata kwanciya a jikinsa. Ya tsira mata idanu yana kallon yanda take fidda numfashi a hankali, a zahiri idonsa a kanta, amma zuciyarsa maganganunta taketa cud'awa, shi baima ta6a ganin mace yarinya k'arama mara tsoro da shiga rikita-rikita irinta ba, bata gudunma shiga had'ari? ya sauke ajiyar zuciya yana tashi zaune, k'afafunta yashiga mammatsa mata a hankali, aikam harda gyara kwanciya su madam munaya, yad'an murmusa, yasan ko'a d'azun tanaso fa, amma iyayi yasata hanashi ya mata. Ya d'auki tsawon lokaci yana mammatsa mata jikinma gaba d'aya, yayinda zuciyarsa kuma ke tattance bayananta dalla-dalla, daga k'arshe sauka yay daga gadon ya fice zuwa d'akin sirrinsa, duk abinda tafad'a yasamu sabon file ya bud'e masa, baya wasa da evidence komai k'ank'artarsa, balle ma nata ya wuce Na wasa, ya dad'e yana rubuce-rubucensa kafin ya koma kan Computers, sunan SD kawai ta ambata masa, dan haka yafara searching gameda SD d'in kawai, babu abinda ya fahimta akan hakan, dama baiyi tunanin fahimtarba, waya ya d'auka ya kira Nuren, bayan sun gaisa yace, “Nureddin acikin yaransu Tanderu kasan SD?”. “SD! SD! kai anya kuwa? amma dai ina zuwa bani mintuna 30”. “ok saina jika”. Galadima Na yanke wayar ya nemo number d'in Abba da bakowa ya sani d'innanba yafara aiki a kansa, dukkan Contact d'in ciki suka bayyana, d'aya bayan d'aya ya dinga binsu yana nazarin adadin kiran da aka ta6ayi, sau nawa aka kira Abba sau nawa ya kira shima? Mafi yawa ma kiransu yafi yawa, yad'an murmusa yana wasa da tsinken hannunsa a kan la66a da nazarin yanda zai 6ullo musu, dan duk hanyar daya kamata yayi bincike an d'auki mataki a kanta, tsawon lokaci bai fahimci komaiba, sai zuwacan wata dabara tafad'o masa, nutsuwa yay yana sarrafa Computer's d'in cikin tsantsar kwarewa da gwaninta, ya kafa musu tarko ne a wayar innarsu Munaya, dan ya tabbata watan watarana zasu iya kira ko sak'o, amma abinma haushin saiya iske wayar inna a kashe, ya dafe kansa, saifa da yacema dady aringa barin wayar a kunne. Babu shiri ya d'auki waya ya kira daddy, bayan sun gaisa yaymasa maganar kunna wayar innar. cikin mamaki Dady yace, “ai a kunne take koda yaushe, Change ma baya k'arewa nake kuma sakata, idankuma zan zo nan nakan sanarma Jafar shima ya kula, amma ina zuwa dai”. Galadima ya amsa da to, amma k'asan zuciyarsa tana mamaki. babu dad'ewa Abba ya sake kiransa, “Ashe Change ne ya k'are babu dad'ewarnan ban lura ba, amma gashinan Na sakata”. “to Dady, Na gode sosai”. Sunayin sallama da Dady Kiran Nuren Na shigowa, d'agawa yayi, Nuren yace, “inagafa brother hanya d'ayace dazata saka musan shi wanene SD d'in, dan abinda Na lura dashi baya amfani da hakan ta kowanne fanin yanar gizo, maybe da full name yake amfani. yanzu zan sayi ticket insha ALLAH zanje domin bincika a wajen Malam Saminu, nasan ya magantu yanzu, zai amsa mana dukkan tambayarmu”. “ok hakan yayi, idan ka fahimci bai saniba karka takurashi, ka binciki yarinyarnan itama, koma ka fara bincikarta dan ita bama wayo ta cikaba sosai, k'ila kafi samu cikin sauk'i a wajenta, abinda yasa Malam saminu baison fad'ar komai, babbar 'yarsa cikin 'ya'yan Alhaji balala wani ya mata ciki, kuma sun dai-daita akan idan ta haihu za'ama yaran aure, wannanne yasakashi tsoron fad'ar komai, dan karya lalata waccan alak'ar, dan tabbas yasan yana fad'a auren bazai yuwuba, to nima banason shiga hak'in kowanne ahali akan aikina, shiyyasa nabashi dama kaga bankuma waiwayarsa ba, yanzu haka yarinyar ta haihu kwana hud'u kenan, amma shi yaron ya kawota nan Dubai ta haihu ne, a nufinsu bayan haihuwar da sati d'aya zasu dawo Nigeria a d'aura musu aure sannan su dawo Dubai d'in, dan Alhaji balala baya son abinda zai 6ata record d'insa, kuma mamar yaronce ta Dage sai anyi auren dan ita mutuniyar kirkice, dan haka mu bama Malam Saminu wannan damar”. Ajiyar zuciya Nuren ya sauke, cikin mamaki yace, “duk ya akayi kasan wannan brother? ”. galadima ya murmusa, yana fadin “Nuren kenan, to bara nayi copy d'in my mata, kwakwalwata tana aiki fiyeda yanda kake aiki da agogo, nasha fad'a maka bada kwanji kawai ake yak'i ba, sai anhad'a da dabarun tunani dana nazari, so kad'an nafad'a maka daga abinda ya shafi Malam Saminu, kaidai saina jika kawai, a time d'in da zakuyi maganar ka tabbatar ka had'a Communication dani ok?”. “babu damuwa aljanin munaya”. Dariya sosai Galadima ya shiga tuntsurawa da iskancin Nuren, wato shima ya maida Aljani yau, wlhy yaronnan yagama rainashi, wai Aljanin Munaya, d'an iska zan kamaka ai. Kashe komai yayi ya fito daga d'akin, bai koma cikiba saiya sakko k'asa, ya iske Sauban kad'ai a falo, shima shigowarsa kenan daga asibiti yake. Galadima ya zauna yana fad'in “jirgi sarkin tashi daga ina?”. Dariya sauban yayi, yace, “kai Yaya, nine kuma jirgin?”. “Kamafi jirgi ai. Wane shiri kakeyi gameda zuwa bautar k'asarka Nigeria”. Sauban ya 6ata fuska kamar zai fasa ihu “yaya yanzu fa ca za'ayi saina koma 9ja har zaman 1year?”. Hararsa Galadima yayi, “to zakayi anan k'asar ne?”. “Ni Yaya ALLAH da anayi da nayi, a manta da bautar k'asar kawai mana, nayi joining masters d'ina”. K'aramin tsaki Galadima yayi, yay crossing k'afarsa yanama Sauban wani kallon bammasan amsar dazan bakaba, saida ya d'auki wasu mintuna sannan yace, “rashin yin ai bazai zama matsalar kowaba sai taka, bakuma zaka gane hakanba sai nan gaba idan ALLAH ya kaika inda bakayi zatoba, idan kace bazakayiba it's better, nidai ai nayi nawa ko. tashi kabani waje”. Ganin ransa ya 6aci Sauban ya marairaice fuska zaiyi magana, amma sai Galadima ya d'aga masa hannu, sannan yamasa nuni da k'ofa alamar ya fice masa. Fita Sauban yayi yabarsa, shifa tsakani da ALLAH zaman masarautar ne baya son yi shi kad'ai. Galadima ya girgiza kai kawai yana fad'in “ALLAH ya shiryeka, gata kasamu tunda katashi kaga komai basai ka nema ba”. Jakadiya data fito ta rissina tana fad'in “Ashe ka shigo magajin gari, barka da dawowa”. Murmushi Galadima yayi, yanason matarnan saboda halaccin datake wa rayuwarsu, “yauwa jakadiya, ya gidan?”. “lafiya lau Ranka ya dad'e, a shirya abinci ko?”. Agogon dake tsintsiyar hannunsa ya kalla, sai kuma ya maida ga jakadiya, “bar abincinan jakadiya, akwai Inda zanje”. “to ALLAH ya dawo dakai lafiya”. Hannu ya d'aga mata kawai sannan ya tashi ya fice. mashin ya hau yafita. Abba dake can gefe a harabar gidan tsakanin wasu flowers yana hutawa ya sauke ajiyar zuciya, tundaga fitowar Galadima har hawansa mashin da fitarsa akan idonsane, rufe idanunsa yayi yacigaba da tunaninsa da tun d'azun yake zaune a wajen yanayi. Asibiti Galadima ya nufa, yay kici6us da Aunty Mimi Na shirin tahowa gida ta huta, ta kalleshi da mamaki, “my k'ani dawowa kayi?”. Gefen girarsa yad'an shafa da d'an yatsa d'aya, “eh , ina zakije k?”. “gida zanje nad'anyi wasu abubuwa”. “ok sai kin dawo”. yafad'a yana ida shigewa, ita kuma ta fice. Momma Na zaune tana waya da papi, ya zauna d'aya a kujerun yana kallonta cikeda sha'awa, uba da 'Yar sun birgeshi, juyawa yay ya kalli gadon Abie, barci yakeyi, har Momma ta gama wayar ison Galadima Na kan Abiensa ko k'yaftawa bayayi, shi kad'ai yasan mi zuciyarsa take sak'awa. “Muh'd daga ina haka?”. Maganar Momma ta katse masa tunani. Janye idonsa yayi daga kan abie ya maido ga Momma, “Daga gida Momma, har yanzu barcin Abie yakeyi?”. “eh tunda ka Fita bai farkaba, mike faruwa naganka cikin damuwa?”. Huci ya furzo daga bakinsa, zaiyi magana sai kuma yayi shiru. “Nifa tsiyata dakai kenan Muh'd, Yaya Abu nacin ran mutum bazai iya fad'ama kowa a taimakeshi da shawara ko addu'a ba, kaga yanda jijiyar kanka ta tashi kuwa? Haba Muh'd Sameer d'ina, kaifa yanzu ubane, girmanka ya k'aru, aringa rage damuwarnan da miskilanci mana, ni ALLAH ma yasa ba haka kakema d'iyar tawaba?”. “kai Momma”. ya fad'a amarairaice cikin 'Yar shagwa6a. Murmushi tayi tace “to fad'amin mike faruwa?”. Yay d'an tsaki, “Ni ai Momma bammasan ta ina zan fara baneba”. “kafara ta sama kawai”. Momma ta fad'a tana dariya. Shima dariyar yayi kad'an sannan ya gyara zama, kuma maida muryarsa k'asa-k'asa yayi yana maganar ahankali, tsaf ya zayyanema Momma yanda sukayi da Munaya, ya d'ora da fad'in “Amma kinsan wani Abu kuwa Momma?”. “a'a saina fad'a dear”. “uhm gani nake kamar bakomai ta fad'a minba, ta 6oye wasu abubuwan dai kamar, saidai bansan dalilinta ba. Momma ta jinjina kai tana murmushi, “To Muh'd mizai hana kacigaba da binta a hankali, nasan zata fad'ama sauranma, ni aganina kamar tana ganin kaima ka kasa yarda da itane shiyyasa tafad'i wasu tak'i fad'in wani, idan har ka yaba da hankalin matarka yakamata ka fara sakin jiki da ita wajen Neman shawararta da sakata cikin wasu al'amura naka Na tabbata itama zata fara fad'a maka nata”. “gaskiya kika fad'a Momma, dan naga fa'idar hakan kwarai da gaske, zan kula insha ALLAH. ya addu'oin Abie akwai saura?”. “saura kad'an, gashi bakuyi wasuba”. “mai k'arfin yince tazama sai a hankali, daga barci sai barci take yini”. “ALLAH Sarki d'iyata, ai tanama k'ok'ari, dama idan ciki ya fara tsufa hakane, ALLAH dai ya sauketa lafiya”. “To amin Momma”. Sun cigaba da 'yan hirarrakinsu har zuwa lokacin da Abie ya farka..................✍🏻 *_inata gaisheku da yawa da yawa, comments naku Na sakani nishad'i over🥰🥰🥰🥰🥰😍😍😍😘😘😘_*. I love you wijiga-wijiga sister's🥰🥰🥰🥰 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🤚🏻✋🏻 [7/4, 2:30 PM] Aysha Galadima: *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻1⃣8⃣➖1⃣9⃣ .................Na dad'e ina barci kafin Na tashi, nayi mamakin ganina ni kad'ai, bansan time d'in da Galadima ya ficeba, sakkowa nayi daga gadon Na nufi Na watsa ruwa. Ina tsaka da shafa mai Samha ta shigo, saida tayi sallama nabata izinin shigowa sannan, ledar hannunta Na kalla ina fad'in “mikika samo mana 'Yar Uncle?”. Cikin dariya ta zauna kan sofa tana cewa “kayan dad'i ne Aunty gimbiyarmu, alfarma nazo nema wajenki keda Uncle”. Hankalina gaba d'aya Na maido kanta, “Alfarmar mi kuma?”. “Aunty gimbiya please ki lalla6a Uncle ya barki muje birthday d'in k'awata Dhibya, ALLAH yarinyarnan tana sonki sosai, kullum hirarki”. Nad'an zaro ido “kai Samha yaza ai naje wani birthday da wannan cikin? kuma kema kinsan bazai bariba tunda Na 'yammatane”. “kai aunty, cikin saikace Wanda yayi wani k'ato, kumafa a cikin gida za'ayi wlhy, iyamu goma ne kawai”. “to naji, ALLAH yasa ya bari, mikika kawo mana a ledar?”. “yes my sweet aunty, wannan wani sari ne yamin k'yau a wani shagon da muke zuwa siyan kaya, shine nayi alk'awarin siya miki, Uncle Sauban ya cikamin na siya, yanzu Na kar6o please ki gwada muga”. Dariya nayi, nace, “inye kaga 'Yar Uncle Anfara jink'an iyaye, to amma ni ina na iya saka sari?”. “kowama koya yayi nidai ki saka muga dan ALLAH”. “to shike nan bara na gwada, ALLAH ya saka da alkairi, ina alfahari da d'iyata”. Samha ta fita tana dariya, nikuma na warware kayan, masha ALLAH sarin ya had'u gaskiya, farine anmasa kwalliya da pink and silver kad'an-kad'an. Na saka rigar, sai dariya ta kamani, saikace wata bafulatana🤭🤣. Warware zanin nayi, tofa anan akeyinta, dan ban iya nad'awaba, na tsaya gaban mirror inata gwadawa amma na kasa, dariya ta kamani, yau naga takaina, Samha ta had'ani da aiki. Tunda ta fara k'ok'arin d'aura zanin sarin yana tsaye a k'ofa, ya hard'e hannayensa ak'irji kawai yana kallonta, kamar zaiyi dariya saboda yanda taketa murd'e-murd'en d'aurawa. A hankali ya taka zuwa inda take, jinai kawai andafa min kafad'u ta baya, na d'ago a tsorace muka had'a ido ta cikin mirror, fuskarsa babu walwala, ya d'agamin gira d'aya, maida idona k'asa nayi, yayinda shikuma ya juyo dani ina fuskantarsa. Gwiwarsa d'aya ya saka a k'asa ya dogare d'aya, nidai kallonsa nake mizaiyi?. Batareda ya kalleni ko min magana ba ya zare zanin dake tattare a hannuna, nikam kamar wata sokuwa saina sakar masa. Yiyay kamar zai warware zanin, nayi saurin rik'ewa, ya d'ago fararen idanunsa yanamin alamar na saki, ban iya musa masaba na sakar masa. Shima sai bai yaye dukaba ya dai-daitashi, ammakina sainaga yana nad'amin, babbar magana Galadima da nad'a sari. Dazai saka wanda a ke sokewa a gefen kugu sai yayi dawani salon daya sakani zabira saboda sak'onsa yajemin har kwalwar kai, ya d'ago ya kalleni yana wani miskilin murmushi da d'agamin gira. Sai kawai na lumshe ido dan naji kunya wlhy. Ya mik'e tsaye yana daidaitamin na kafad'ar shima, nidai harya gama ban bud'e idoba. baiyi magana ba ya warware reborn d'in kaina, da sauri na bud'e idon, yanda yawani tsareni da idanu sai nakasa jurewa na maida na rufe. Cumb ya d'auka yahau gyaran kai, to nikma naga abinda yafi k'arfina yau d'innan, wai dama guy d'innan ya iya abin mata ne?. Bai barni ba saida ya gama yanda yakeso dani, ya zubamin ido kawai batareda yace komai ba. nikuma nakasa bud'e idona na kallesa, ahankali yafara busamin iskar bakinsa saman idona, dole nafara marmar da idanu, dainawa yayi, na bud'e idon ahankali a kansa, kuma matsoni yayi muka Zuba juna ido ko k'yaftawa bamayi, gashin dake neman shigarmin ido ya saka d'an yatsa ya matsar, na maida idanun na lumshe ina sauke k'aramar ajiyar zuciya. Shima nannauyan numfashi ya sauke kafin yaja da baya, wardrobe d'insa ya nufa, jin yabar wajen saina bud'e idona, duk jikina ya saki, kallo d'aya namasa na d'auke kaina na juya ga mirror Dan naga yanda ya maidani, murmushi nayi ina saka hannu na gyara gashina, nima na yarda da gaske nayi kyau. Nakuma d'ago ido da nufin sake kallon kaina sainaganshi a bayana, sark'a ya ziro a ya sakamin tareda gyara zamanta ta zauna sosai a k'irjina, ya janye gashina ta baya yana sak'ala sark'ar, nidai nawa idone, ya gama ya cire d'an kunen dake kunnena ya sakamin na sark'ar, sannan ya mannani da jikinsa yana zagayo hannunsa duk biyu saman matashin cikina, hannuna ya kama yana sakamin bangles, cikin k'asaitacciyar muryarnan tasa yake magana cikin kunnena, “haka dama sari kema Afirikawa k'yau?”. Murmushi nayi, na d'ago idona muna kallon juna ta cikin mirror, haryanzu hannayena na cikin nasa yana saka bangles d'in da guda d'ai-d'ai. Ya lumshe idanu yana shanshanar wuyana, jikina yafara rawa, babu shiri na saka hannuna d'aya daya gama saka bangles d'in na shafo gefen kumatunsa, cikin rawar murya nace “please kabari yalla6ai”. Batareda ya dainaba cikin sark'ewar harshe yace “mizaisa na daina? yalla6iya”. Yanda yake min akan dokin wiya da yanda hannunsa d'aya ke canja salo a jikina sainayi k'ok'arin juyowa garesa, ko hakan zaisa yabari d'in. Ashe dama ma na sake bashi, gaba d'aya yawani rikice kamar ba Galadiman Dana saniba. Hannunsa ya sak'alo kuguna yana kuma matsoni jikinsa sosai, yasaka d'ayan hannun ya tallafo kaina tareda d'ora la66ansa akan nawa. Kasa jurewa nayi, na mik'a masa wuya kawai, harda bada gunmawa nima........ Tofa munga idi, daga gyaran sari🙆🏽😹. Samha tataho da karsashinta dantaga ko Munaya ta saka, daga nan ta nuna mata yanda zata nad'a zanin sarin, tunda tasan bata iyaba, ko kad'an babu Wanda yaga shigowar Galadima, Dan babu kowa a falon, jakadiya ta tafi asibiti itada Sauban da innarsu munaya, aunty Mimi kuma barci takeyi, Dady kam yanacan baya inda ya maida lambun tunaninsa, itako Samha tana bama Munaya sari takoma d'aki danta bata lokaci ta shirya a tsanake. Sallama d'aya kawai tayi ta turo k'ofar tana kwala kiran “Aunty gimbiyarmu kin saka?”. Galadima dayake Neman fara zirmawa yay hanzarin sakin Munaya, da sauri naja baya nima, dan kamar a sama mukaji muryar Samha. Itama Samha baya ta koma da sauri gabanta na fad'uwa, Dan ganin Wanda batayi zatoba a d'akin. ALLAH ma yaso bataga komaiba, lokacin datake sako k'afarta a d'akin Galadima ya janye bakinsa yana k'ok'arin matsawane baya. Wata uwar harara mai kad'a hanji da hanta ya zubama Samha, hakanne yasakata yin baya da sauri ta koma. Nikam kasama d'aga ido nayi balle na kalleshi dagashi har Samhar, saima wani yaam nakejin jikina tamkar zan fad'i. Lura da hakan da yayine yasakashi azamar rik'o hannuna, na shige jikinsa ina sauke tagwayen ajiyar zuciya, dagani harshi idanu kowa ya lumshe, tsawon lokaci muna a haka munkasa sakin juna, ahankali na shiga k'ok'arin janye jikina, bai hananiba yabani damar barin jikinsa, ra6awa nayi ta gefensa na wuce, na koma saman sofa na zauna ina dafe kai, juyowa yayi yana kallona, kafin yatako shima zuwa bakin gado ya kwanta, k'afafunsa na k'asa duka, yayinda yay filo da hannayensa yana lumshe idanu. Duk munyi shiru d'akin tamkar babu wata halitta mai numfashi a cikinsa, kowannenmu shiyasan mi yake sak'ama zuciyarsa. K'arar wayarsace ta sakamu d'an firgita mu duka, duk sai muka zubama wayar ido tamkar wani ojuju. harta tsinke bai d'aukaba, saida aka sake kira sannan ya cirota daga aljihun wandonsa yay picking. Muryarsa vary low yace, “Nuren Yaya dai?”. Mamaki da al'ajabi ya cika Nuren, yakuma Ciro wayar daga kunnensa ya duba Dan tabbatar da Galadima ne kuwa?, lallai shine, maida wayar yayi a kunne yana fad'in “brother lafiyarka kuwa?”. Taune lips nashi yayi, ya yanke wayar, dan indai ahaka zasuyi wayarnan bazai fahimci komaiba, ajiye wayar yayi yatashi ya shige bathroom. Da kallo k'asa-k'asa kawai na iya binsa, amma nakasa ko kwakwkwaran numfashi. Daga can kuwa Nuren kwashewa yayi da dariya saboda tuno wani Abu, (to su Nuren dai dama bariki sune manyanta🤣), dariya yakeyi iya iyawa yana dukan kansa, daya fara tsagaitawa saiya kuma saka wata, saida yayi ta ishesa sannan ya daina, ya rik'e ha6a yana fad'in “oh ni su brother ansan takan tsiya, ina ganinsa lab-lab Ashe d'anba sauk'ine, toma uwar miye na d'agamin wayar tunda yasan yafara sauka a network🤣, yakuma saka dariya saikace wani sabon kamu.😬 Galadima kam ruwa ya sakarma kansa kawai, ya dafe bango da hannu biyu ruwan na kwarara saman kansa, sai faman taune lips yakeyi shi kad'ai, yayi da zuciyarsa ke sak'awa da kwancewa, saida ya ji k'arfi-k'arfi sannan ya kashe shower d'in yaja bathrobe d'in ya saka yana faman sauke 6oyayyar ajiyar zuciya. Inda yabarta anan ya fito ya isketa, kallo d'aya yamata ya d'aukekai, bakin gadon ya zauna yana goge kansa da k'aramin towel, yajawo wayar da d'ayan hannun ya danna kiran Nuren. Bugu d'aya Nuren d'in ya d'aga, da k'yar yasamu ya danne dariyarsa, “brother wai miya farune naji muryarka haka? nifa ka tadamin hankali”. “Ba komai, shin kajene?”. Nuren ya toshe bakinsa gudun kar dariya ta kufce masa, Sameer d'an rainin wayone ALLAH, wai babu komai, to naji babu komai aje a haka. “wai kana jina kuwa?”. Galadima yafad'a. “Oh sorry brother network nayin wasa, gani a gidan, amma bankai ga shiga inda takebane”. “ok tom kaje, amma kabar wayar a kunne, inason naji komai”. Nuren yace “to”. Da sallama ya shiga d'akin, sai wani ciccin magani yake. Farhat dake zaune bakin gadon d'akin ta zabga tagumi ta d'ago kai tana kallonsa, yayin da wasu hawaye ke shirin zubo mata. Kujera guda d'aya dake d'akin ya jawo ya zauna. Farhat ta share hawayen kumatunta, murya a sanyaye tace, “yayana dan ALLAH kayi hak'uri, wlhy ina missing d'in families d'ina da karatuna, dan ALLAH idan kasheni zakayi ka kasheni kawai na hutama rayuwa ma ni gaba d'aya”. Murmushi Nuren yayi, idonsa a kanta yace, “bazan kashekiba Farhat, dan bakimin komaiba, kamar yanda na sanarmiki mahaifinkine yaja miki, ki kwantar da hankalinki, insha ALLAH zaki koma gidanku kwana kusa, yanzuma dukba wannanba, wata tambaya nazo yimiki, ALLAH yasa zaki bani had'in kai?”. Kanta ta jinjina masa tana kuma share sauran hawayen, “insha ALLAH inhar nasani zan fad'a maka”. “good girl ”. ‘cewar Nuren yana gyara zama’. “Farhat nasan kinsan duk yaran Abbanki ko?, ina nufin masu masa hidima a office ko a gida?”. “Eh nasan mafi yawansu, dan ina zuwa wajensa a Office, kuma wasu acikinsu sukanzo gidanma”. “Masha ALLAH, kokin san SD?”. “SD!?”. “eh shi”. “gaskiya a yaran Abbana dana sani babu wani mai suna SD”. “okay, amma ko wani mai Something sunan dazai iya kasancewa full name bazaki iya hasasowa ba?”. Shiru tayi ta lula duniyar nazari, shidai Nuren ya zauna mata idanu yana kuma jinjina ma ubangiji akan yin k'yak'yk'yawar hallita, dan Farhat black beauty ce masha ALLAH. A jiyar zuciya ta sauke, “yaya inaga kamar dai akwai wani Sagir dauda dana Sani, amma bansan aikin da yake a k'ark'ashin Abbanmu ba, sai kuma ya Shareffudden k'anin Aunty Umma, sai Steven Daniel”. “shi Steven d'in wanene shi a gidanku, itama Aunty Umman haka?”. “Driver d'insu Mom ne, shike kaisu anguwa, ita kuma Aunty Umma matar Abbanmu ce ai, itace amaryarsa”. “Uhyim”. Nuren yafad'a yana jinjina kai. “Dan ALLAH yayana in tambayeka mana?”. “ina saurarenki”. “laifin mi Abbana yamuku hakane?”. murmushi Nuren yayi, “karki damu nangaba kad'an komai zai wuce, kuma bashi yay laifinba, wanine yayi na kusa dashi”. “to ALLAH yasa Ku kamashi, amma dan ALLAH karkuma Abbana komai”. “insha ALLAH babie”. Murmushi Farhat tayi, Nuren kuma ya mik'e tsaye idonsa a kanta. “babu dai wata Matsala ko?”. Cikin shagwa6ar data saba tace, “please ko TV ka samin, banajin dad'in zaman hakanan”. “Am sorry to say dear, har kibar gidannan dokace, babu television, babu phones, amma way not nakawo miki irin Hausa novels d'innan danaga mata na karantawa?”. Idonta ya cika da kwalla, “ayya yayana wlhy ban iya karatun hausaba sosai, yana bani wahala”. Ido yad'an zaro waje, yace, “saboda mi? Keba bahaushiya bacene?”. “bahausa mana”. ‘tafad'a cikin turo bani irinnan ta6ararru’. Baki ya ta6e yana kama hanyar fita, “zaki cigaba da kad'aicinki ashe kuwa”. Ganin zai fice da sauri tace, “please ka siyo zan fara koya to”. “it's better”. ‘yafad'a yana ficewarsa’. Saman gadon ta fad'a ta fashe da kuma mai ban tausayi. Duk abinda ke faruwa Galadima najin komai ta waya, Munaya ma na zauna a sofa har yanzu tana satar kallonsa, amma batajin miyake saurare da ya nutsu haka. Cire wayar yafara k'ok'arin yi ya jiyo muryar Nuren na fad'in “hello brother kana jina?”. Galadima yace, “eh”. “okay duk kaji aimi ta fad'a ko?”. “duk najiku, saika samin ido akan duk d'unsu, a bincikomin komai daya shafesu”. “indai wannanne insha ALLAH angama, amma ni a ganina banda wannan Shareffuden d'in datace, domin babu wani kamanni a cikin nashi sunan, ballema tace k'anin step mom natane”. “Humm Nuredeen kenan, shifa mak'iyi ba'a rainashi, mutane da yawa sukan d'auki cinnaka ba komaiba, amma idan yacijesu sukan ji cizon har a ransu, dan haka karka ta6a d'aukar mage mafi sauk'i akan kare, itama idan taga nama citakeyi”. “wannan gaskiyane brother, ALLAH yabamu sa'a”. “amin ya rabbi, naji kuna maganar buks da ita, kaje ka samo mata dukkan Wanda take buk'ata, har English novels d'in, sannan ak'ara tanadar mata dukkan abinci mai k'yau datake so”. “insha ALLAH angon Munaya”. Girgiza kai kawai Galadima yayi ya yanke wayar. Kallon Munaya yayi suka had'a ido, saita janye cikeda basarwa. Shima tashi yayi ya koma gaban mirror, duk uzirinsa yayi ya gama sannan yamatsa ga wardrobe ya ciro kayan dayake buk'ata. Ganin haka Munaya tazame ta kwanta cikin kujerar yandama bazata gansaba. Baki kawai ya ta6e yacigaba da saka kayansa. Bayan yagama yamatsa kusada ita, “tashi ki canja kaya ki rakani wani waje”. Fuska Munaya tad'an yatsina, kamar zatace wani Abu saikuma ta yunk'ura zata tashi kawai, hannunta ya kama ya taimaka mata ta tashi zaune. fita yayi abinsa. Hakan yasata fahimtar zai jirata a falo kenan. Bata 6ata lokaciba ta canja kayanta da atanfa skt da riga, takawo after dress ta saka sannan ta nad'a Vail d'in rigar, d'as ta fito itada cikinta, kamar ka saceta ka gudu abinka. Tunda ta fito ya zuba mata idanu, ko k'yaftawa bayayi, saida yaga tana gabda k'arasowa garesa ya basar yana mik'ewa. Gaba yayi tabisa abaya, yandama yake taka steps d'in benen dolene ya birgeka, duk takunsa nakan idonta, yayinda itama take binsa daki-daki a hankali. Babu kowa a falon, dan haka suka fice basu nemi kowanba. A mota yana tuk'i da sauraren karatu itakuma tana latsa waya suna charts a families group d'insu. Sai murmushi take zubawa, duk abinda take yana kallonta ta gefen ido. Sun isa wani k'aton shagon saida kayan babies, duk abinda kake buk'ata zaka sameshi indai na yarane daga 1year zuwa 15. Itadai mamaki ya ishi Munaya, miye nawani kawota nan? yabari a haihun mana ma. Tarba ta musamman aka musu, hakan ya tabbatar ma Munaya yasan mai shagon kenan, dan yanda aketa girmamasu sai abin ke bata mamaki. gashi indiyanci sukeyi bata fahimtar maganganunsu. Itadai tana zaune hankalinta ya rabu gida biyu, wajensu Galadima da kuma wasu mata biyu da yaransu uku dabazasu wuce 7-7years ba, yaran k'yawawa masha ALLAH, ga wayo. Galadima ya juyo zai mata magana saiya lura da inda ta zubama idanu, shima shagala yay a kallon yaran, iyayensu na za6ar kaya amma su suna tibirewa sai Wanda sukeso za'a d'auka. Munaya sai zuba murmushi takeyi, dan suntafi da imaninta, shima murmusawa yayi yana lasar lips, kafin ya d'auke kansa ya maida ga Wanda suke maganar. Zuwa can gardama ta hark'ume tsakanin yaran akan wani game da iyayen ke dubawa maybe zasu saya musu ne. Kuma games d'in suna kusada Munaya ne, d'aya a cikin yaran ya d'akko yazo wajen Munaya yana tambayarta wai “Aunty wannan yafi dad'i aidai ko?”. Munaya bata fahimceshiba, dan yayi maganane da yaren dabata ji, dan haka saitayi murmushi ta tambayesa yanajin English?. Yaron ya d'aga mata kai alamar eh. Ta kuma murmusawa, duk abinda ke faruwa a idon Galadima ne. Da turanci munaya tace, “yarona kai kata6a irin wannan game d'inne?”. Murmushi yamata shima, yace “aunty akwai dad'i ma sosai, ranar saida na cinye kharan a gidansu ma”. “da gaske?”. munaya tafad'a tana dafa kafad'arsa. Kansa ya d'aga mata, cike da d'oki yace, “Aunty na koya miki?”. Munaya ta d'aga masa kai. Game d'in ya d'ora a cinyarta, ya danna wasu Number, sai kuma ya zubasu cikin d'aya, duk suka shige. Cikin mamaki munaya tace “mikenan to?”. Shima dariyarsu ta yara yayi, yace “Aunty ai wayo na miki, Abu guda d'ayane, amma sainayi ammafani da numbers daban-daban, kuma kowanne a cikinsu aiki d'aya yayi na canja da wani, kekuma zakiga kamar na had'a daban-dabanne, kuma kowanne da aikinsa, amma aiki d'aya ne na had'aka kuma akan Abu guda d'aya kacal”. Sosai abun ya birge munaya, tayi dariya har hak'oranta na bayyana, jawo yaron tayi a jikinta ta rungume. Iyayensa dake tsaye suna kallonsu tun d'azun duk sukayi dariya suma, sannan suka matsa kusada munaya suna bata hannu alamar gaisuwa. itama ta mik'a musu suka gaisa, d'aya tace sunanta Radha, d'ayar kuma tace Anjali, munaya ta fad'a musu nata suna itama, sannan takamo hannun saran yaran tana tambayarsu suma, d'aya yace vanish, d'ayan kuma Anjun, duk kumatunsu ta sumbata tana sakama rayuwarsu albarka. Wadda tace sunanta Radha tace “kiyi hak'uri da surutun Vishnu shi baya gajiyane ko kad'an”. Munaya tace babu komai. Daganan sukai gaba, munaya tana binsu da kallo tana murmushi, yaran sai waigenta suke suna d'aga mata hannu. Sunje wajen biyan kud'i akace subar kud'insu inji mai shagon, da mamaki suka tambayi wanene? Mikuma yasa ya barmusu. Mai kar6ar kud'i ya murmusawa yana fad'in mijin matarcan da kuka gaisane mai shagon ai. Munaya batasan mike faruwaba taga sun dawo, godiya suka shiga yimata, ta tambayesu akan me?. Suka bata amsa da cewar mijinta bai kar6i kud'in kayansu ba. Murmushi tayi, k'asan ranta tana mamakin dama shagon na Galadima ne?. Sun katse mata tunani da tambayar kozasu samu number ta, babu musu tabasu sukayi sallama suka tafi. Maida kallonta tayi ga Galadima dake zaune yanata latse-latsen laptop tamkar baisan mike faruwaba, da alama yana duba kayane ko wani Abu, dan time to time Wanda yake gefensa yakan nuna masa wani yanki na kayan dake shagon, shikuma ya waiga ya kalla, idan bai hango sosaiba saiya kalla ta cikin Computer d'in dake tareda cctv cameras d'in shagon. Munaya tace kai mutuminnan akwai son kud'in tsiya, kai komai kana saidawa, wata zuciya tace idan bai nemi kud'iba dame zai kula da mahaifinsa?. “hakane kuma”. ta fad'a a fili tana sauke ajiyar zuciya. Kusan mintuna 15 saitaga ya taso ya nufota. Zama yay kujerar kusa da ita yana fad'in “sorry friend na barki ke kad'ai. kin gaji mu tafi ko?”. Munaya tad'an yamutsa fuska tace “ba sosaiba”. Ya d'an murmusa, “ok tunda baki gajiba kozaki d'an mana taimako ni da abin cikin kwan?”. Hararsa tad'anyi, itafa haushin wannan abin cikin kwan dayake fad'a takeji. Hannu yasa ya dafe bakinsa yana fad'in “maida wuk'ar”. A tare suka dinga zagayawa cikin shagon, dayake babbane sosai, kayan yarane kuma zalla a wajen, komai bibbiyu take d'auka, baice komaiba, dan yasan dai bai wuce tana had'awa da cikin 'Yar uwarta Munubiya bane. Sund'an d'iba kaya babu laifi, yabada ATM d'insa aka d'auka harda na wad'ancan matan, yaran shagonne suka kai musu har cikin mota. Yanzuma haka suka taho tamkar kurame. Kowa da abinda yake sak'awa.... Danja data tsayar damune yasakashi juyowa yad'an kalleni, ganin hankalina nakan wasu yara 'yan makaranta dake mota yace, “dama haka kike da son yara?”. Juyowa nayi Na kalleshi, amma saiya d'auke kai tamkar bashine yay maganarba ma. Nima maida kaina nayi ga yaran, a kuma time d'inne muka sami damar barin wajen. Saida muka fara tafiya nabashi amsa da “yalla6ai kenan, waye zaice baison yaro, a duniya babu abinda yafi k'uruciya dad'i”. Kad'an ya juyo yad'an kalleni yana fad'in “really?”. Nima kallon nasa nayi ina fad'in “na tabbata amsarnan kowama zai baka idan ka tambayesa”. Bai kalleniba yanzun kam, hankalinsa naga tuk'insa, yace, “ALLAH ya kawoka duniya lafiya abin cikin kwan”. “shiru namasa bance uffanba”. Har muka isa gida kuma babu Wanda ya sake magana a cikinmu. Saida yay parking motar a harabar gidan sannan ya juyo gareni, ina niyyar bud'ewa Na fita ya ruk'o hannuna. kallonsa nayi da mamaki, yawani ci magani irin babu raininnan, kamar zanyi magana saikuma nayi shiru muka zubama juna ido, kowannenmu zuciyarsa Na bugawa da sauri-sauri. Cikin k'asaitarnan tasa yace, “Addu'a nayi amma jan aji yahanaki amsamin da amin”. Ni dariyama ya bani wai jan aji, hakanne yasakani murmusawa kad'an ina k'ok'arin janye idona daga cikin nasa, amma saiya hanani hakan, nace, “na amsa ai, bakaji bane kawai”. “aiba kurma kika auraba”. Uhm wannan aure ana tak'ama dashi, Na fad'a a raina, a fili kuma nace, “a zuciya Na amsa”. “k'arya haramun, banji wannan sak'onba a tawa zuciyar”. Da mamaki Na waro idanu waje ina fad'in “ban fahimceka ba”. Lips d'insa yad'an ciza da hak'ora yana matsoda fuskarsa dab da tawa, gashi ya sark'eni da idanu nakasa matsawa, d'an yatsansa ya d'ora saitin zuciyata, muryarsa k'asa-k'asa tamkar mai rad'a yace, “zuciyoyi aminan juna sukan kar6i sak'on juna alokacinda d'aya ya aikashi ga d'aya, karki jahilci kanki har yanzu akwai sauran dama”..... Yana gama fad'a ya saki hannuna, tareda bud'e motar ya fice. Galala nabisa da kallo tamkar wata sokuwa, nakasa motsi nakasa fassara zantukansa da ma'anarsu. Tsawon mintunan dahar bayin gidan sungama kwashe kayan da mukazo dasu ban fitoba, bud'ewa naji anyi, hannunsa kawai ya mik'omin alamar nakama Na fito. tamkar sokuwa haka Na d'ora hannun cikin nasa, ya kamoni ahankali Na fito, maimakon ya sakeni saiya jawoni Na shige jikinsa, ya d'ora kansa a dokin wuyana, cikin kunnena yace “wasu bayanan basa buk'atar fassara, ayanda sukazo ahaka ake barinsu, karki zurfafa tunani, dan yana kawo ciwon kai da hana Hutu”. Ya d'ago kaina tareda janye jikinsa yana d'agamin gira da salute d'ina, ya juya zuwa cikin gida. Binsa kawai nakeyi a baya tamkar kazar da kwai ya fashema a ciki. A falo muka iske duka ahalin gidan, har Momma dazata kwana yau a gida, Abba ne kawai babu, muduka sun birgemu, Dan hira suke ta nishad'i da girmama juna. Dagani harshi gaishesu mukayi, Sauban da Samha dasuka k'arasa da kayanda da bayi suka shigo dasu suka sakko daga samanmu suna mana sannu da zuwa. Ni kad'ai Na amsa, Galadima hannu kawai ya d'aga musu. Momma tace, “kuje ku huta mana”. mik'ewa mukayi duk a kunyace, ina gaba a yanzu yana baya, suduka da kallon sha'awa suka bimu, dad'i da farinciki Na ratsa zukatansu, innarmu harda kwalla suka cika idonta, Wanda ita kad'ai tasan fasaarar kayanta. ★★★★★★★ Da daddare Galadima Na zaune akan sofa ya d'aura k'afafunsa saman teble yana latsa laptop, yayinda Munaya ke zaune a tsakkiyar gado tana karatun wani English novel na Galadima, buk d'in love story ne dan haka taketa faman zabga murmushi, lokaci-lokaci yakan d'ago ido ya kalleta, saboda idan tayi murmushi yakan jiyo sautinsa. Maida kansa yayi, yacigaba da aikinsa dayakeyi akan numbers d'in layin Abba na sirri, kwatsam sai maganar yaron d'azu na shago mai suna Vishnu ta fad'o masa a rai. *_Aunty ai wayo na miki, Abu guda d'aya ne, amma sainayi amfani da numbers daban-daban, kuma kowanne a cikinsu aiki d'aya yayi na canja da wani, kekuma zakiga kamar na had'a daban-dabanne, kuma kowanne da aikinsa, amma aiki d'aya ne na had'aka kuma akan Abu guda d'aya kacal._* Saida yakuma maimaita maganar kusan sau uku a ransa, kafin ya kalli Munaya da dukkan hankalinta ke kan Novel, “Friend!”. Ya kirata a nutse. Da “na'am” Na amsa ina kallonsa, saikuma Na janye saboda wandon jikinsa baiko rufe masa cinyaba, sai k'aramar riga mara hannu. Yace, “mikika fahimta ga zancen abokinki na shago?”. “abokina? waye abokina?”. Tasowa yayi dagashi har laptop d'in da coffee d'insa ya hawo gadon, nima saina tashi zaune sosai. Ya zauna ta gefe tareda ajiye mug d'in hannunsa a drowa d'in gefen gadon, laptop d'in kuma a saman gadon d'ayan gefensa. hannu ya mik'amin alamar nazo. Ban musa masaba Na matso, ya kamoni ya sakani a jikinsa, dan tsakkiyar k'afafunsa ya sakani, saina zame Na kwanta na d'ora kaina a cinyarsa, (dama wajen lak'ewa nake nema🤪). Ya kar6i buk d'in hannuna ya ajiye gefe, ya d'ora hannunsa a saman cikina. Kuma maimaita masa tambayar nayi. Ya shafa sajensa yana cije lips, “miyasa wataran kike da basarwa”.. “ni d'in?”. ‘nafad'a ina nuna kaina da kallonsa’. Bai bani amsaba yace “ina nufin yaron d'azun”. “Oh sorry”. nafad'a ina gyara kwanciyat. Nace, “wai Vishnu? ”. Kansa ya d'aga min “to amma wace maganace tasa? tazama abin nazari yalla6ai?”. “game”. “game! game!” nashiga fad'a ina k'ok'arin tunanowa. “okay, wai yanda yafad'i yaci game d'in?”. “Uhhm”. ya fad'a a tak'aice.. Nikuma saina murmusa, “to dukda dai bansan ma'anar d'aukar maganar da muhimmanciba amma anawa tunanin yana nufin _abinnan mabanbantane, amma saiyayi amfani dasu cikin Abu d'aya, kuma sukai masa aiki iri d'aya, sannan duk shi kad'ai ya sarrafasu akan Abu d'aya bawai yayi tarayyar da wasu mutane da yawa bane ko aikinsa had'aka,_ wannan itace fahimta ta ga zancen nasa”. Lumshe ido Galadima yayi, ya duk'o a hankali ya mannamin Sumba mai k'au a goshi. Sannan ya d'akko novel d'in ya damk'amin a hannu, yajawo laptop d'insa yacigaba da aikinsa. Kallon mamaki kawai na zuba masa, kokad'an ban fahimci muhallin maganar tasaba da son fashin bak'i. Batareda ya kalleni ba, idonsa akan system d'insa yace, “kallonfa?”. Janye idona nayi ina ta6e baki. Shima saiya ta6e nasa alamar yaganni kenan. karatuna nacigaba shima yacigaba da aikinsa yana shan coffee time to time. Yayi aiki mai tsawo kafin yasaki wani murmushi da ajiyar zuciya, ya kalli munaya da barci ya kwashe, fuskarta ya shafa yana kuma sakin wani murmushin, “tabbas gaskiya Vishnu ya fad'a, mutum d'ayane ke amfani da Numbers daban-daban wajen kiran Abba munaya, duk wadda yagama da ita bazai sakeba, tagama aikinta, a wannan karon lallai kunyi aiki da basira, wadda harta birkita tunanin Sameer, kuna kiran Abba da mabanbanta Numbers wad'anda kunrigada kun gama shirya matakan da kowacce number bazata sake aikiba, shima kansa ya d'auka mutane daban-dabanne ke kiransa. O ALLAH wannan shine bada k'afa, to ai inkunsan wata bakusan wataba kuma, Muhammad Sameer ruwane, idan bakasha yanzuba zakasha anjima, idan kak'i kuma k'ishirwa ta kasheka. Inhar tarkon dazan d'ana zai d'annu dai-dai, tabbas zan cafke kurayen daji mai duhuwa a wannan karon”. ‘Ya k'are maganar da jan hancin munaya yana kuma sumbatar goshinta’. Kwanciya ya gyara mata sosai, ya ja bargo ya lullu6a mata sannan yaje bayi ya d'auro alwala, kamar yanda ya saba ya raya wannan dare da nafilfili da godiyar ALLAH, kafin yazo ya kwanta gefen munaya zuciyarsa na cike da annashuwa da farinciki, kaikace komai yayi done ne. Addu'a ya musu sannan yasakata jikinsa barci ya Lula dashi shima. Nima mai d'aukar rahoto bara nad'an rintsa my sweet sisters😉🤩......................✍🏻 Duk Wanda yaga ban amsa massage nashiba yamin afuwa, nayi up date WhatsApp d'inane🥰🥰🥰🤝🏻 *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻1⃣8⃣➖1⃣9⃣ .................Na dad'e ina barci kafin Na tashi, nayi mamakin ganina ni kad'ai, bansan time d'in da Galadima ya ficeba, sakkowa nayi daga gadon Na nufi Na watsa ruwa. Ina tsaka da shafa mai Samha ta shigo, saida tayi sallama nabata izinin shigowa sannan, ledar hannunta Na kalla ina fad'in “mikika samo mana 'Yar Uncle?”. Cikin dariya ta zauna kan sofa tana cewa “kayan dad'i ne Aunty gimbiyarmu, alfarma nazo nema wajenki keda Uncle”. Hankalina gaba d'aya Na maido kanta, “Alfarmar mi kuma?”. “Aunty gimbiya please ki lalla6a Uncle ya barki muje birthday d'in k'awata Dhibya, ALLAH yarinyarnan tana sonki sosai, kullum hirarki”. Nad'an zaro ido “kai Samha yaza ai naje wani birthday da wannan cikin? kuma kema kinsan bazai bariba tunda Na 'yammatane”. “kai aunty, cikin saikace Wanda yayi wani k'ato, kumafa a cikin gida za'ayi wlhy, iyamu goma ne kawai”. “to naji, ALLAH yasa ya bari, mikika kawo mana a ledar?”. “yes my sweet aunty, wannan wani sari ne yamin k'yau a wani shagon da muke zuwa siyan kaya, shine nayi alk'awarin siya miki, Uncle Sauban ya cikamin na siya, yanzu Na kar6o please ki gwada muga”. Dariya nayi, nace, “inye kaga 'Yar Uncle Anfara jink'an iyaye, to amma ni ina na iya saka sari?”. “kowama koya yayi nidai ki saka muga dan ALLAH”. “to shike nan bara na gwada, ALLAH ya saka da alkairi, ina alfahari da d'iyata”. Samha ta fita tana dariya, nikuma na warware kayan, masha ALLAH sarin ya had'u gaskiya, farine anmasa kwalliya da pink and silver kad'an-kad'an. Na saka rigar, sai dariya ta kamani, saikace wata bafulatana🤭🤣. Warware zanin nayi, tofa anan akeyinta, dan ban iya nad'awaba, na tsaya gaban mirror inata gwadawa amma na kasa, dariya ta kamani, yau naga takaina, Samha ta had'ani da aiki. Tunda ta fara k'ok'arin d'aura zanin sarin yana tsaye a k'ofa, ya hard'e hannayensa ak'irji kawai yana kallonta, kamar zaiyi dariya saboda yanda taketa murd'e-murd'en d'aurawa. A hankali ya taka zuwa inda take, jinai kawai andafa min kafad'u ta baya, na d'ago a tsorace muka had'a ido ta cikin mirror, fuskarsa babu walwala, ya d'agamin gira d'aya, maida idona k'asa nayi, yayinda shikuma ya juyo dani ina fuskantarsa. Gwiwarsa d'aya ya saka a k'asa ya dogare d'aya, nidai kallonsa nake mizaiyi?. Batareda ya kalleni ko min magana ba ya zare zanin dake tattare a hannuna, nikam kamar wata sokuwa saina sakar masa. Yiyay kamar zai warware zanin, nayi saurin rik'ewa, ya d'ago fararen idanunsa yanamin alamar na saki, ban iya musa masaba na sakar masa. Shima sai bai yaye dukaba ya dai-daitashi, ammakina sainaga yana nad'amin, babbar magana Galadima da nad'a sari. Dazai saka wanda a ke sokewa a gefen kugu sai yayi dawani salon daya sakani zabira saboda sak'onsa yajemin har kwalwar kai, ya d'ago ya kalleni yana wani miskilin murmushi da d'agamin gira. Sai kawai na lumshe ido dan naji kunya wlhy. Ya mik'e tsaye yana daidaitamin na kafad'ar shima, nidai harya gama ban bud'e idoba. baiyi magana ba ya warware reborn d'in kaina, da sauri na bud'e idon, yanda yawani tsareni da idanu sai nakasa jurewa na maida na rufe. Cumb ya d'auka yahau gyaran kai, to nikma naga abinda yafi k'arfina yau d'innan, wai dama guy d'innan ya iya abin mata ne?. Bai barni ba saida ya gama yanda yakeso dani, ya zubamin ido kawai batareda yace komai ba. nikuma nakasa bud'e idona na kallesa, ahankali yafara busamin iskar bakinsa saman idona, dole nafara marmar da idanu, dainawa yayi, na bud'e idon ahankali a kansa, kuma matsoni yayi muka Zuba juna ido ko k'yaftawa bamayi, gashin dake neman shigarmin ido ya saka d'an yatsa ya matsar, na maida idanun na lumshe ina sauke k'aramar ajiyar zuciya. Shima nannauyan numfashi ya sauke kafin yaja da baya, wardrobe d'insa ya nufa, jin yabar wajen saina bud'e idona, duk jikina ya saki, kallo d'aya namasa na d'auke kaina na juya ga mirror Dan naga yanda ya maidani, murmushi nayi ina saka hannu na gyara gashina, nima na yarda da gaske nayi kyau. Nakuma d'ago ido da nufin sake kallon kaina sainaganshi a bayana, sark'a ya ziro a ya sakamin tareda gyara zamanta ta zauna sosai a k'irjina, ya janye gashina ta baya yana sak'ala sark'ar, nidai nawa idone, ya gama ya cire d'an kunen dake kunnena ya sakamin na sark'ar, sannan ya mannani da jikinsa yana zagayo hannunsa duk biyu saman matashin cikina, hannuna ya kama yana sakamin bangles, cikin k'asaitacciyar muryarnan tasa yake magana cikin kunnena, “haka dama sari kema Afirikawa k'yau?”. Murmushi nayi, na d'ago idona muna kallon juna ta cikin mirror, haryanzu hannayena na cikin nasa yana saka bangles d'in da guda d'ai-d'ai. Ya lumshe idanu yana shanshanar wuyana, jikina yafara rawa, babu shiri na saka hannuna d'aya daya gama saka bangles d'in na shafo gefen kumatunsa, cikin rawar murya nace “please kabari yalla6ai”. Batareda ya dainaba cikin sark'ewar harshe yace “mizaisa na daina? yalla6iya”. Yanda yake min akan dokin wiya da yanda hannunsa d'aya ke canja salo a jikina sainayi k'ok'arin juyowa garesa, ko hakan zaisa yabari d'in. Ashe dama ma na sake bashi, gaba d'aya yawani rikice kamar ba Galadiman Dana saniba. Hannunsa ya sak'alo kuguna yana kuma matsoni jikinsa sosai, yasaka d'ayan hannun ya tallafo kaina tareda d'ora la66ansa akan nawa. Kasa jurewa nayi, na mik'a masa wuya kawai, harda bada gunmawa nima........ Tofa munga idi, daga gyaran sari🙆🏽😹. Samha tataho da karsashinta dantaga ko Munaya ta saka, daga nan ta nuna mata yanda zata nad'a zanin sarin, tunda tasan bata iyaba, ko kad'an babu Wanda yaga shigowar Galadima, Dan babu kowa a falon, jakadiya ta tafi asibiti itada Sauban da innarsu munaya, aunty Mimi kuma barci takeyi, Dady kam yanacan baya inda ya maida lambun tunaninsa, itako Samha tana bama Munaya sari takoma d'aki danta bata lokaci ta shirya a tsanake. Sallama d'aya kawai tayi ta turo k'ofar tana kwala kiran “Aunty gimbiyarmu kin saka?”. Galadima dayake Neman fara zirmawa yay hanzarin sakin Munaya, da sauri naja baya nima, dan kamar a sama mukaji muryar Samha. Itama Samha baya ta koma da sauri gabanta na fad'uwa, Dan ganin Wanda batayi zatoba a d'akin. ALLAH ma yaso bataga komaiba, lokacin datake sako k'afarta a d'akin Galadima ya janye bakinsa yana k'ok'arin matsawane baya. Wata uwar harara mai kad'a hanji da hanta ya zubama Samha, hakanne yasakata yin baya da sauri ta koma. Nikam kasama d'aga ido nayi balle na kalleshi dagashi har Samhar, saima wani yaam nakejin jikina tamkar zan fad'i. Lura da hakan da yayine yasakashi azamar rik'o hannuna, na shige jikinsa ina sauke tagwayen ajiyar zuciya, dagani harshi idanu kowa ya lumshe, tsawon lokaci muna a haka munkasa sakin juna, ahankali na shiga k'ok'arin janye jikina, bai hananiba yabani damar barin jikinsa, ra6awa nayi ta gefensa na wuce, na koma saman sofa na zauna ina dafe kai, juyowa yayi yana kallona, kafin yatako shima zuwa bakin gado ya kwanta, k'afafunsa na k'asa duka, yayinda yay filo da hannayensa yana lumshe idanu. Duk munyi shiru d'akin tamkar babu wata halitta mai numfashi a cikinsa, kowannenmu shiyasan mi yake sak'ama zuciyarsa. K'arar wayarsace ta sakamu d'an firgita mu duka, duk sai muka zubama wayar ido tamkar wani ojuju. harta tsinke bai d'aukaba, saida aka sake kira sannan ya cirota daga aljihun wandonsa yay picking. Muryarsa vary low yace, “Nuren Yaya dai?”. Mamaki da al'ajabi ya cika Nuren, yakuma Ciro wayar daga kunnensa ya duba Dan tabbatar da Galadima ne kuwa?, lallai shine, maida wayar yayi a kunne yana fad'in “brother lafiyarka kuwa?”. Taune lips nashi yayi, ya yanke wayar, dan indai ahaka zasuyi wayarnan bazai fahimci komaiba, ajiye wayar yayi yatashi ya shige bathroom. Da kallo k'asa-k'asa kawai na iya binsa, amma nakasa ko kwakwkwaran numfashi. Daga can kuwa Nuren kwashewa yayi da dariya saboda tuno wani Abu, (to su Nuren dai dama bariki sune manyanta🤣), dariya yakeyi iya iyawa yana dukan kansa, daya fara tsagaitawa saiya kuma saka wata, saida yayi ta ishesa sannan ya daina, ya rik'e ha6a yana fad'in “oh ni su brother ansan takan tsiya, ina ganinsa lab-lab Ashe d'anba sauk'ine, toma uwar miye na d'agamin wayar tunda yasan yafara sauka a network🤣, yakuma saka dariya saikace wani sabon kamu.😬 Galadima kam ruwa ya sakarma kansa kawai, ya dafe bango da hannu biyu ruwan na kwarara saman kansa, sai faman taune lips yakeyi shi kad'ai, yayi da zuciyarsa ke sak'awa da kwancewa, saida ya ji k'arfi-k'arfi sannan ya kashe shower d'in yaja bathrobe d'in ya saka yana faman sauke 6oyayyar ajiyar zuciya. Inda yabarta anan ya fito ya isketa, kallo d'aya yamata ya d'aukekai, bakin gadon ya zauna yana goge kansa da k'aramin towel, yajawo wayar da d'ayan hannun ya danna kiran Nuren. Bugu d'aya Nuren d'in ya d'aga, da k'yar yasamu ya danne dariyarsa, “brother wai miya farune naji muryarka haka? nifa ka tadamin hankali”. “Ba komai, shin kajene?”. Nuren ya toshe bakinsa gudun kar dariya ta kufce masa, Sameer d'an rainin wayone ALLAH, wai babu komai, to naji babu komai aje a haka. “wai kana jina kuwa?”. Galadima yafad'a. “Oh sorry brother network nayin wasa, gani a gidan, amma bankai ga shiga inda takebane”. “ok tom kaje, amma kabar wayar a kunne, inason naji komai”. Nuren yace “to”. Da sallama ya shiga d'akin, sai wani ciccin magani yake. Farhat dake zaune bakin gadon d'akin ta zabga tagumi ta d'ago kai tana kallonsa, yayin da wasu hawaye ke shirin zubo mata. Kujera guda d'aya dake d'akin ya jawo ya zauna. Farhat ta share hawayen kumatunta, murya a sanyaye tace, “yayana dan ALLAH kayi hak'uri, wlhy ina missing d'in families d'ina da karatuna, dan ALLAH idan kasheni zakayi ka kasheni kawai na hutama rayuwa ma ni gaba d'aya”. Murmushi Nuren yayi, idonsa a kanta yace, “bazan kashekiba Farhat, dan bakimin komaiba, kamar yanda na sanarmiki mahaifinkine yaja miki, ki kwantar da hankalinki, insha ALLAH zaki koma gidanku kwana kusa, yanzuma dukba wannanba, wata tambaya nazo yimiki, ALLAH yasa zaki bani had'in kai?”. Kanta ta jinjina masa tana kuma share sauran hawayen, “insha ALLAH inhar nasani zan fad'a maka”. “good girl ”. ‘cewar Nuren yana gyara zama’. “Farhat nasan kinsan duk yaran Abbanki ko?, ina nufin masu masa hidima a office ko a gida?”. “Eh nasan mafi yawansu, dan ina zuwa wajensa a Office, kuma wasu acikinsu sukanzo gidanma”. “Masha ALLAH, kokin san SD?”. “SD!?”. “eh shi”. “gaskiya a yaran Abbana dana sani babu wani mai suna SD”. “okay, amma ko wani mai Something sunan dazai iya kasancewa full name bazaki iya hasasowa ba?”. Shiru tayi ta lula duniyar nazari, shidai Nuren ya zauna mata idanu yana kuma jinjina ma ubangiji akan yin k'yak'yk'yawar hallita, dan Farhat black beauty ce masha ALLAH. A jiyar zuciya ta sauke, “yaya inaga kamar dai akwai wani Sagir dauda dana Sani, amma bansan aikin da yake a k'ark'ashin Abbanmu ba, sai kuma ya Shareffudden k'anin Aunty Umma, sai Steven Daniel”. “shi Steven d'in wanene shi a gidanku, itama Aunty Umman haka?”. “Driver d'insu Mom ne, shike kaisu anguwa, ita kuma Aunty Umma matar Abbanmu ce ai, itace amaryarsa”. “Uhyim”. Nuren yafad'a yana jinjina kai. “Dan ALLAH yayana in tambayeka mana?”. “ina saurarenki”. “laifin mi Abbana yamuku hakane?”. murmushi Nuren yayi, “karki damu nangaba kad'an komai zai wuce, kuma bashi yay laifinba, wanine yayi na kusa dashi”. “to ALLAH yasa Ku kamashi, amma dan ALLAH karkuma Abbana komai”. “insha ALLAH babie”. Murmushi Farhat tayi, Nuren kuma ya mik'e tsaye idonsa a kanta. “babu dai wata Matsala ko?”. Cikin shagwa6ar data saba tace, “please ko TV ka samin, banajin dad'in zaman hakanan”. “Am sorry to say dear, har kibar gidannan dokace, babu television, babu phones, amma way not nakawo miki irin Hausa novels d'innan danaga mata na karantawa?”. Idonta ya cika da kwalla, “ayya yayana wlhy ban iya karatun hausaba sosai, yana bani wahala”. Ido yad'an zaro waje, yace, “saboda mi? Keba bahaushiya bacene?”. “bahausa mana”. ‘tafad'a cikin turo bani irinnan ta6ararru’. Baki ya ta6e yana kama hanyar fita, “zaki cigaba da kad'aicinki ashe kuwa”. Ganin zai fice da sauri tace, “please ka siyo zan fara koya to”. “it's better”. ‘yafad'a yana ficewarsa’. Saman gadon ta fad'a ta fashe da kuma mai ban tausayi. Duk abinda ke faruwa Galadima najin komai ta waya, Munaya ma na zauna a sofa har yanzu tana satar kallonsa, amma batajin miyake saurare da ya nutsu haka. Cire wayar yafara k'ok'arin yi ya jiyo muryar Nuren na fad'in “hello brother kana jina?”. Galadima yace, “eh”. “okay duk kaji aimi ta fad'a ko?”. “duk najiku, saika samin ido akan duk d'unsu, a bincikomin komai daya shafesu”. “indai wannanne insha ALLAH angama, amma ni a ganina banda wannan Shareffuden d'in datace, domin babu wani kamanni a cikin nashi sunan, ballema tace k'anin step mom natane”. “Humm Nuredeen kenan, shifa mak'iyi ba'a rainashi, mutane da yawa sukan d'auki cinnaka ba komaiba, amma idan yacijesu sukan ji cizon har a ransu, dan haka karka ta6a d'aukar mage mafi sauk'i akan kare, itama idan taga nama citakeyi”. “wannan gaskiyane brother, ALLAH yabamu sa'a”. “amin ya rabbi, naji kuna maganar buks da ita, kaje ka samo mata dukkan Wanda take buk'ata, har English novels d'in, sannan ak'ara tanadar mata dukkan abinci mai k'yau datake so”. “insha ALLAH angon Munaya”. Girgiza kai kawai Galadima yayi ya yanke wayar. Kallon Munaya yayi suka had'a ido, saita janye cikeda basarwa. Shima tashi yayi ya koma gaban mirror, duk uzirinsa yayi ya gama sannan yamatsa ga wardrobe ya ciro kayan dayake buk'ata. Ganin haka Munaya tazame ta kwanta cikin kujerar yandama bazata gansaba. Baki kawai ya ta6e yacigaba da saka kayansa. Bayan yagama yamatsa kusada ita, “tashi ki canja kaya ki rakani wani waje”. Fuska Munaya tad'an yatsina, kamar zatace wani Abu saikuma ta yunk'ura zata tashi kawai, hannunta ya kama ya taimaka mata ta tashi zaune. fita yayi abinsa. Hakan yasata fahimtar zai jirata a falo kenan. Bata 6ata lokaciba ta canja kayanta da atanfa skt da riga, takawo after dress ta saka sannan ta nad'a Vail d'in rigar, d'as ta fito itada cikinta, kamar ka saceta ka gudu abinka. Tunda ta fito ya zuba mata idanu, ko k'yaftawa bayayi, saida yaga tana gabda k'arasowa garesa ya basar yana mik'ewa. Gaba yayi tabisa abaya, yandama yake taka steps d'in benen dolene ya birgeka, duk takunsa nakan idonta, yayinda itama take binsa daki-daki a hankali. Babu kowa a falon, dan haka suka fice basu nemi kowanba. A mota yana tuk'i da sauraren karatu itakuma tana latsa waya suna charts a families group d'insu. Sai murmushi take zubawa, duk abinda take yana kallonta ta gefen ido. Sun isa wani k'aton shagon saida kayan babies, duk abinda kake buk'ata zaka sameshi indai na yarane daga 1year zuwa 15. Itadai mamaki ya ishi Munaya, miye nawani kawota nan? yabari a haihun mana ma. Tarba ta musamman aka musu, hakan ya tabbatar ma Munaya yasan mai shagon kenan, dan yanda aketa girmamasu sai abin ke bata mamaki. gashi indiyanci sukeyi bata fahimtar maganganunsu. Itadai tana zaune hankalinta ya rabu gida biyu, wajensu Galadima da kuma wasu mata biyu da yaransu uku dabazasu wuce 7-7years ba, yaran k'yawawa masha ALLAH, ga wayo. Galadima ya juyo zai mata magana saiya lura da inda ta zubama idanu, shima shagala yay a kallon yaran, iyayensu na za6ar kaya amma su suna tibirewa sai Wanda sukeso za'a d'auka. Munaya sai zuba murmushi takeyi, dan suntafi da imaninta, shima murmusawa yayi yana lasar lips, kafin ya d'auke kansa ya maida ga Wanda suke maganar. Zuwa can gardama ta hark'ume tsakanin yaran akan wani game da iyayen ke dubawa maybe zasu saya musu ne. Kuma games d'in suna kusada Munaya ne, d'aya a cikin yaran ya d'akko yazo wajen Munaya yana tambayarta wai “Aunty wannan yafi dad'i aidai ko?”. Munaya bata fahimceshiba, dan yayi maganane da yaren dabata ji, dan haka saitayi murmushi ta tambayesa yanajin English?. Yaron ya d'aga mata kai alamar eh. Ta kuma murmusawa, duk abinda ke faruwa a idon Galadima ne. Da turanci munaya tace, “yarona kai kata6a irin wannan game d'inne?”. Murmushi yamata shima, yace “aunty akwai dad'i ma sosai, ranar saida na cinye kharan a gidansu ma”. “da gaske?”. munaya tafad'a tana dafa kafad'arsa. Kansa ya d'aga mata, cike da d'oki yace, “Aunty na koya miki?”. Munaya ta d'aga masa kai. Game d'in ya d'ora a cinyarta, ya danna wasu Number, sai kuma ya zubasu cikin d'aya, duk suka shige. Cikin mamaki munaya tace “mikenan to?”. Shima dariyarsu ta yara yayi, yace “Aunty ai wayo na miki, Abu guda d'ayane, amma sainayi ammafani da numbers daban-daban, kuma kowanne a cikinsu aiki d'aya yayi na canja da wani, kekuma zakiga kamar na had'a daban-dabanne, kuma kowanne da aikinsa, amma aiki d'aya ne na had'aka kuma akan Abu guda d'aya kacal”. Sosai abun ya birge munaya, tayi dariya har hak'oranta na bayyana, jawo yaron tayi a jikinta ta rungume. Iyayensa dake tsaye suna kallonsu tun d'azun duk sukayi dariya suma, sannan suka matsa kusada munaya suna bata hannu alamar gaisuwa. itama ta mik'a musu suka gaisa, d'aya tace sunanta Radha, d'ayar kuma tace Anjali, munaya ta fad'a musu nata suna itama, sannan takamo hannun saran yaran tana tambayarsu suma, d'aya yace vanish, d'ayan kuma Anjun, duk kumatunsu ta sumbata tana sakama rayuwarsu albarka. Wadda tace sunanta Radha tace “kiyi hak'uri da surutun Vishnu shi baya gajiyane ko kad'an”. Munaya tace babu komai. Daganan sukai gaba, munaya tana binsu da kallo tana murmushi, yaran sai waigenta suke suna d'aga mata hannu. Sunje wajen biyan kud'i akace subar kud'insu inji mai shagon, da mamaki suka tambayi wanene? Mikuma yasa ya barmusu. Mai kar6ar kud'i ya murmusawa yana fad'in mijin matarcan da kuka gaisane mai shagon ai. Munaya batasan mike faruwaba taga sun dawo, godiya suka shiga yimata, ta tambayesu akan me?. Suka bata amsa da cewar mijinta bai kar6i kud'in kayansu ba. Murmushi tayi, k'asan ranta tana mamakin dama shagon na Galadima ne?. Sun katse mata tunani da tambayar kozasu samu number ta, babu musu tabasu sukayi sallama suka tafi. Maida kallonta tayi ga Galadima dake zaune yanata latse-latsen laptop tamkar baisan mike faruwaba, da alama yana duba kayane ko wani Abu, dan time to time Wanda yake gefensa yakan nuna masa wani yanki na kayan dake shagon, shikuma ya waiga ya kalla, idan bai hango sosaiba saiya kalla ta cikin Computer d'in dake tareda cctv cameras d'in shagon. Munaya tace kai mutuminnan akwai son kud'in tsiya, kai komai kana saidawa, wata zuciya tace idan bai nemi kud'iba dame zai kula da mahaifinsa?. “hakane kuma”. ta fad'a a fili tana sauke ajiyar zuciya. Kusan mintuna 15 saitaga ya taso ya nufota. Zama yay kujerar kusa da ita yana fad'in “sorry friend na barki ke kad'ai. kin gaji mu tafi ko?”. Munaya tad'an yamutsa fuska tace “ba sosaiba”. Ya d'an murmusa, “ok tunda baki gajiba kozaki d'an mana taimako ni da abin cikin kwan?”. Hararsa tad'anyi, itafa haushin wannan abin cikin kwan dayake fad'a takeji. Hannu yasa ya dafe bakinsa yana fad'in “maida wuk'ar”. A tare suka dinga zagayawa cikin shagon, dayake babbane sosai, kayan yarane kuma zalla a wajen, komai bibbiyu take d'auka, baice komaiba, dan yasan dai bai wuce tana had'awa da cikin 'Yar uwarta Munubiya bane. Sund'an d'iba kaya babu laifi, yabada ATM d'insa aka d'auka harda na wad'ancan matan, yaran shagonne suka kai musu har cikin mota. Yanzuma haka suka taho tamkar kurame. Kowa da abinda yake sak'awa.... Danja data tsayar damune yasakashi juyowa yad'an kalleni, ganin hankalina nakan wasu yara 'yan makaranta dake mota yace, “dama haka kike da son yara?”. Juyowa nayi Na kalleshi, amma saiya d'auke kai tamkar bashine yay maganarba ma. Nima maida kaina nayi ga yaran, a kuma time d'inne muka sami damar barin wajen. Saida muka fara tafiya nabashi amsa da “yalla6ai kenan, waye zaice baison yaro, a duniya babu abinda yafi k'uruciya dad'i”. Kad'an ya juyo yad'an kalleni yana fad'in “really?”. Nima kallon nasa nayi ina fad'in “na tabbata amsarnan kowama zai baka idan ka tambayesa”. Bai kalleniba yanzun kam, hankalinsa naga tuk'insa, yace, “ALLAH ya kawoka duniya lafiya abin cikin kwan”. “shiru namasa bance uffanba”. Har muka isa gida kuma babu Wanda ya sake magana a cikinmu. Saida yay parking motar a harabar gidan sannan ya juyo gareni, ina niyyar bud'ewa Na fita ya ruk'o hannuna. kallonsa nayi da mamaki, yawani ci magani irin babu raininnan, kamar zanyi magana saikuma nayi shiru muka zubama juna ido, kowannenmu zuciyarsa Na bugawa da sauri-sauri. Cikin k'asaitarnan tasa yace, “Addu'a nayi amma jan aji yahanaki amsamin da amin”. Ni dariyama ya bani wai jan aji, hakanne yasakani murmusawa kad'an ina k'ok'arin janye idona daga cikin nasa, amma saiya hanani hakan, nace, “na amsa ai, bakaji bane kawai”. “aiba kurma kika auraba”. Uhm wannan aure ana tak'ama dashi, Na fad'a a raina, a fili kuma nace, “a zuciya Na amsa”. “k'arya haramun, banji wannan sak'onba a tawa zuciyar”. Da mamaki Na waro idanu waje ina fad'in “ban fahimceka ba”. Lips d'insa yad'an ciza da hak'ora yana matsoda fuskarsa dab da tawa, gashi ya sark'eni da idanu nakasa matsawa, d'an yatsansa ya d'ora saitin zuciyata, muryarsa k'asa-k'asa tamkar mai rad'a yace, “zuciyoyi aminan juna sukan kar6i sak'on juna alokacinda d'aya ya aikashi ga d'aya, karki jahilci kanki har yanzu akwai sauran dama”..... Yana gama fad'a ya saki hannuna, tareda bud'e motar ya fice. Galala nabisa da kallo tamkar wata sokuwa, nakasa motsi nakasa fassara zantukansa da ma'anarsu. Tsawon mintunan dahar bayin gidan sungama kwashe kayan da mukazo dasu ban fitoba, bud'ewa naji anyi, hannunsa kawai ya mik'omin alamar nakama Na fito. tamkar sokuwa haka Na d'ora hannun cikin nasa, ya kamoni ahankali Na fito, maimakon ya sakeni saiya jawoni Na shige jikinsa, ya d'ora kansa a dokin wuyana, cikin kunnena yace “wasu bayanan basa buk'atar fassara, ayanda sukazo ahaka ake barinsu, karki zurfafa tunani, dan yana kawo ciwon kai da hana Hutu”. Ya d'ago kaina tareda janye jikinsa yana d'agamin gira da salute d'ina, ya juya zuwa cikin gida. Binsa kawai nakeyi a baya tamkar kazar da kwai ya fashema a ciki. A falo muka iske duka ahalin gidan, har Momma dazata kwana yau a gida, Abba ne kawai babu, muduka sun birgemu, Dan hira suke ta nishad'i da girmama juna. Dagani harshi gaishesu mukayi, Sauban da Samha dasuka k'arasa da kayanda da bayi suka shigo dasu suka sakko daga samanmu suna mana sannu da zuwa. Ni kad'ai Na amsa, Galadima hannu kawai ya d'aga musu. Momma tace, “kuje ku huta mana”. mik'ewa mukayi duk a kunyace, ina gaba a yanzu yana baya, suduka da kallon sha'awa suka bimu, dad'i da farinciki Na ratsa zukatansu, innarmu harda kwalla suka cika idonta, Wanda ita kad'ai tasan fasaarar kayanta. ★★★★★★★ Da daddare Galadima Na zaune akan sofa ya d'aura k'afafunsa saman teble yana latsa laptop, yayinda Munaya ke zaune a tsakkiyar gado tana karatun wani English novel na Galadima, buk d'in love story ne dan haka taketa faman zabga murmushi, lokaci-lokaci yakan d'ago ido ya kalleta, saboda idan tayi murmushi yakan jiyo sautinsa. Maida kansa yayi, yacigaba da aikinsa dayakeyi akan numbers d'in layin Abba na sirri, kwatsam sai maganar yaron d'azu na shago mai suna Vishnu ta fad'o masa a rai. *_Aunty ai wayo na miki, Abu guda d'aya ne, amma sainayi amfani da numbers daban-daban, kuma kowanne a cikinsu aiki d'aya yayi na canja da wani, kekuma zakiga kamar na had'a daban-dabanne, kuma kowanne da aikinsa, amma aiki d'aya ne na had'aka kuma akan Abu guda d'aya kacal._* Saida yakuma maimaita maganar kusan sau uku a ransa, kafin ya kalli Munaya da dukkan hankalinta ke kan Novel, “Friend!”. Ya kirata a nutse. Da “na'am” Na amsa ina kallonsa, saikuma Na janye saboda wandon jikinsa baiko rufe masa cinyaba, sai k'aramar riga mara hannu. Yace, “mikika fahimta ga zancen abokinki na shago?”. “abokina? waye abokina?”. Tasowa yayi dagashi har laptop d'in da coffee d'insa ya hawo gadon, nima saina tashi zaune sosai. Ya zauna ta gefe tareda ajiye mug d'in hannunsa a drowa d'in gefen gadon, laptop d'in kuma a saman gadon d'ayan gefensa. hannu ya mik'amin alamar nazo. Ban musa masaba Na matso, ya kamoni ya sakani a jikinsa, dan tsakkiyar k'afafunsa ya sakani, saina zame Na kwanta na d'ora kaina a cinyarsa, (dama wajen lak'ewa nake nema🤪). Ya kar6i buk d'in hannuna ya ajiye gefe, ya d'ora hannunsa a saman cikina. Kuma maimaita masa tambayar nayi. Ya shafa sajensa yana cije lips, “miyasa wataran kike da basarwa”.. “ni d'in?”. ‘nafad'a ina nuna kaina da kallonsa’. Bai bani amsaba yace “ina nufin yaron d'azun”. “Oh sorry”. nafad'a ina gyara kwanciyat. Nace, “wai Vishnu? ”. Kansa ya d'aga min “to amma wace maganace tasa? tazama abin nazari yalla6ai?”. “game”. “game! game!” nashiga fad'a ina k'ok'arin tunanowa. “okay, wai yanda yafad'i yaci game d'in?”. “Uhhm”. ya fad'a a tak'aice.. Nikuma saina murmusa, “to dukda dai bansan ma'anar d'aukar maganar da muhimmanciba amma anawa tunanin yana nufin _abinnan mabanbantane, amma saiyayi amfani dasu cikin Abu d'aya, kuma sukai masa aiki iri d'aya, sannan duk shi kad'ai ya sarrafasu akan Abu d'aya bawai yayi tarayyar da wasu mutane da yawa bane ko aikinsa had'aka,_ wannan itace fahimta ta ga zancen nasa”. Lumshe ido Galadima yayi, ya duk'o a hankali ya mannamin Sumba mai k'au a goshi. Sannan ya d'akko novel d'in ya damk'amin a hannu, yajawo laptop d'insa yacigaba da aikinsa. Kallon mamaki kawai na zuba masa, kokad'an ban fahimci muhallin maganar tasaba da son fashin bak'i. Batareda ya kalleni ba, idonsa akan system d'insa yace, “kallonfa?”. Janye idona nayi ina ta6e baki. Shima saiya ta6e nasa alamar yaganni kenan. karatuna nacigaba shima yacigaba da aikinsa yana shan coffee time to time. Yayi aiki mai tsawo kafin yasaki wani murmushi da ajiyar zuciya, ya kalli munaya da barci ya kwashe, fuskarta ya shafa yana kuma sakin wani murmushin, “tabbas gaskiya Vishnu ya fad'a, mutum d'ayane ke amfani da Numbers daban-daban wajen kiran Abba munaya, duk wadda yagama da ita bazai sakeba, tagama aikinta, a wannan karon lallai kunyi aiki da basira, wadda harta birkita tunanin Sameer, kuna kiran Abba da mabanbanta Numbers wad'anda kunrigada kun gama shirya matakan da kowacce number bazata sake aikiba, shima kansa ya d'auka mutane daban-dabanne ke kiransa. O ALLAH wannan shine bada k'afa, to ai inkunsan wata bakusan wataba kuma, Muhammad Sameer ruwane, idan bakasha yanzuba zakasha anjima, idan kak'i kuma k'ishirwa ta kasheka. Inhar tarkon dazan d'ana zai d'annu dai-dai, tabbas zan cafke kurayen daji mai duhuwa a wannan karon”. ‘Ya k'are maganar da jan hancin munaya yana kuma sumbatar goshinta’. Kwanciya ya gyara mata sosai, ya ja bargo ya lullu6a mata sannan yaje bayi ya d'auro alwala, kamar yanda ya saba ya raya wannan dare da nafilfili da godiyar ALLAH, kafin yazo ya kwanta gefen munaya zuciyarsa na cike da annashuwa da farinciki, kaikace komai yayi done ne. Addu'a ya musu sannan yasakata jikinsa barci ya Lula dashi shima. Nima mai d'aukar rahoto bara nad'an rintsa my sweet sisters😉🤩......................✍🏻 Duk Wanda yaga ban amsa massage nashiba yamin afuwa, nayi up date WhatsApp d'inane🥰🥰🥰🤝🏻 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu👏🏻😭_* *_ALLAH ya gafartama iyayenmu👏🏻😭_* [7/8, 1:47 PM] Aysha Galadima: *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ___________________________ _jinjinar gaisuwa a gareku da fatan alkairi, Bilyn Abdull ta gaisheku, gaisuwa irin ta musamman d'innan my lovely sister's🥰🥰🥰🥰🥰🤝🏻_ *_Aysha Manshart (Ummu zunnur😍), Hafsa abdulaziz, mmn fukaihat, Hannah A Ali, marnona, Mmn Al'ameen, Sumee waziri, Ummu walid, Yar tulluwa, Khadija Aliyu Sa'id, Umm Abdul, Umm Yusuf, Mrs Ahmad, zubby abdullahi, Hajara Ismail shatu, Ummu barakat, maryam haruna, Ummu sulaym, Ummu Ahmad, Haizarana halliru._* I love you mazga-mazga😂🤸🏻‍♀ ____________________________ ~Book 2~ 👉🏻2⃣0⃣➖2⃣1⃣ ................Tafiyar su Abba dai ta kankama, dan Abba ya matsa ainun, dole Galadima ya musu dukkan shirin daya kamata, zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu jirginsu zai d'aga. Da yake yau Saturday ce babu aiki, amma hakan bai hana zama gidan shiru ba, su Sauban da innarmu sun fitane, nikad'aice a gidan sai jakadiya, nima barci nake suka gudu suka barni a gidan. Yunwar dana farka da ita ta tilastamin sakkowa k'asa neman abinci, dan a 'yan kwanakinnan nazama wata acici, danaci abinci danaji sabuwar yunwa, narasa wannan dalili. Bannemi kukun gidanba ma ko cikin bayi, nahau dafa abinda zaimin saurin dahuwa, kafin ya dahunma saida na d'umama madara nad'ansha sannan 'yar nutsuwa tazomin. ina sauke abincin kuwa Na juyoshi a plate na koma sama. tun a hanya naji k'amshin turarensa, ban kawo yashigo gidan bane nidai na ida hawa. ban tsaya faloba na shige bedroom. Galadima dake zaune a sofa yana kwance igiyar takalminsa ya d'ago ido yana kallona da amsamin sallamar danayi. Sandunan wasan Golf d'insa daya shigo dasu ya zube a carpet d'in gaban gadon na janye gefe na zauna, dan nafijin dad'in xaman k'asan yanzu. Shidai bai fasa kallona ba baikuma bar cire takalman ba, dan abincin dayaga ta zubo yakema kallon mamaki, kafinfa yafita harda kukanta ta farka wai yunwa takeji, haka dole yafita yasaka kuku dafa mata abinci, baibar gidanba saida taci takoma barci, da fitarsa kuwa baifi 3hours ba, amma jita yanzu dawani abincin. Ya janye takalaman daya gama cirewa a gefe ya zubamin ido kawai, dukda abincin nada zafi haka nakecinsa da sauri-sauri. Janye plate d'in yayi daga gabana, fuskarsa babu walwala yace, “waike mike damunki hakane?”. Idona harya fara tara kwalla cikin marairaicewa nace, “dan ALLAH kabani, wlhy yunwa nakeji bata wasaba”. Rasa ma mizaicemin yayi, ya zubamin ido kawai yana kallona. a mamakinsa saiyaga ma ina hawaye, abincin ya tura min yana fad'in “wannan cin naki yayi yawa, gama muje wajen Akash ya dubaki”. Uffan bance masaba, shima bai sake tankawa ba yanufi bathroom, yaja wasu mintuna saigashi ya fito d'aure da towel, kallo d'aya namasa na janye idona, wannan abun nasa yafara damuna, yanzu baijin kunyar yafitomin a duk yanda yaso, ko yana mantawa bashi kad'ai bane a d'akin oho. Shima dai kallonta kawai yakeyi, dan nacinye abincin plate d'in tas, a ransa yace shiyyasa taketa zama k'atuwa, irin wannan ci haka. Oho bansan yanayiba, nidai mik'ewa nayi nashige bathroom abuna, nasamu nai wanka da ruwa mai sanyi dan naji dad'i. lokacin dana fito yagama shiryawa cikin ainahin kayan malam bahaushe, blue d'in shaddace akaima d'inkin wando da 'yar shara, saidai tasha aikin sarauta d'an asali da d'aukar hankali, ya kawo bak'ar hularsa ya d'ora, itama dai irin ta mutanen dace *dara* (irin wadda su ibro suke sawa), saidai wannan batakai waccan tsawoba, dai-dai take kamar sauran huluna. harga ALLAH kwalliyar tasa tamin k'yau, dan yafito a cikakken bahaushensa, turare yake fesawa amma nakasa d'auke idona daga kansa. Duk kallon k'urillar datake masa yana kallonta ta gefen ido, wani miskilin murmushi yayi Na gefen baki, ya juyo muka had'a ido, saurin janyewa nayi cike da basarwa. Shikuma ya ta6e baki yana takowa inda nake. tuni zuciyata harta fara tsitstsinkewa, dan ayanzu babu abinda nake gudu kuma irin yace zai ra6u jikina koya nunan buk'atar wani abu, shima inaga fahimtar hakanne yasa a kwanakinnan bai cika takurani kamar abaya danake kawo kaina ba. Ganin yanda ta tsorata sai abin yabashi mamaki, waskewa yay yafasa zuwa gareta, ganin ya canja hanya Na sauke ajiyar zuciya wadda har fitar sautinta saida yaji. Kansa kawai ya girgiza ya zauna a bakin gado yana fad'in “kishirya mana”. Bance komaiba nawuce Na d'auki Arabian gown da zan saka, dan yanzu sune kawai kayan dakemin dad'in sakawa, bathroom nakoma Na saka, Na fito Na iskeshi yana waya da Akash dake fad'a masa inda zamu iskeshi. wucewa nayi nad'an gyara fuskata, inason shafa mai a k'afa amma ina tunanin yanda zan sunkuya. Lura da yay da hakan yasashi mik'ewa, wajen takalmanmu yanufa ya d'aukamin masu taushi cikin wad'anda ya siyamin saboda naji sauk'in tafiya. Kafad'una ya kama ya zaunar dani ga stool d'in mirror, sannan ya d'auki man ya duk'a k'asa a gabana yakamo k'afata yana shafamin, nidai kallonsa kawai nakeyi, harya gama yasakamin takalman ya d'auran igiyar yana fad'in “yakamata ma mufara fita kina motsa jiki, dan k'afarnan kamar tana d'anyi fushi a kwanakin nan”. Nace, “ai bata ciwo”. Baice komaiba yamik'e yana kama hannuna ya mik'ar dani. A falo muka iske jakadiya tana kallo, tamin sannu sannan ta gaida Galadima. yafad'a mata zamu fita, tabimu da addu'ar dawowa lafiya. Tafiyar tamu takasance shiru kamar yanda muka saba inhar ta had'amu mu biyu, maimakon muje asibiti sai gamu awani gida mai k'yau da tsari, kafin nasamu damar tambayarsa saiga Akash yafito yana zabga murmushi, rungume juna sukayi da Galadima, kafin ya d'ago yanamin sannu da zuwa. Fuskata da murmushi Na amsa masa tareda gaishesa. A tsararren falon gidan muka yada zango, komai ya birgrni dan an tsarashi yanda ya kamata. dandanan Akash ya tara mana kaya a gaba, sannan ya zauna muka sake sabuwar gaisuwa. Suka d'ora da barkwancinsu irin Na abokan da suka shak'u. A firar tasune nakejin Auren Akash d'in ya matso, dan zasuyi baiko next week da wadda zai aura, Na tayashi murna da fatan kaiwa da rai. ya amsamin bakinsa har kunne. Bayanin yawan cin abincina Galadima yamasa, Akash yay dariya, “to inbanda abinka Sameer ai dole taci abinci fiyeda da, karka manta yanzu ba ita kad'ai bace, kuma saitaci abin cikinta zai samu shima, kunk'i yarda ayi scanning muga adadin 'ya'yan namu ko jinsun su”. galadima ya murmusa kawai, karka damu, miye Na zazzari, kwana nawane insha ALLAH zaizo ko zatazo duniya, yanzu dai tunda ba Matsala bane cin abincin ai Alhamdllh”. “no babu wata Matsala, abindama yasa zakuga yanzu takanyi saurin jin yunwa cikinta ya tsufa, shima yak'ara girma abin cikin nata, dan zama ta dingajin idan bataciba ana motsi da harbe-harbe a cikin, idan da zaka kalli cikin a time d'in datakejin yunwar sosai har yanda yake wuntsilniya saika gani kaima, Madam ko hakan baya faruwa?”. Nace, “yana faruwa sosai, amma da zaran naci abincin sai a nutsu”. Akash yay dariya, “Alamun yana cikin k'oshin lafiya kenan, abincinne kawai buk'atarsa”. Galadima ya juyo muka kalli juna, gira ya d'agamin nikuma nayi murmushi ina kauda idona gefe. Daga nan wata hirar suka koma, wadda nake zargin akan Abba nane, dan naji Akash Na fad'in doctor Johnson yabama Abba glasses d'in amatsayin medical glasses, kuma ya gargad'esa karyayi wasa dashi saboda jijiyar idonsa nason samun Matsala, to sunason glasses d'in yazama riga kafine, dayake da turanci suke magana sai yazam inaji nima. Murmushi Galadima yayi yana jinjina kai. A raina nace mikuma Galadima ya shiryama Abban?. banida mai bani amsa, dan haka nayi gum. Muna niyyar tashi Akash yace bamu isaba, bazamu tafi bamuci komai a gidansa ba, kodan munga bashida matane. Badan munsoba mukad'anci abinda zamu iya, sannan yayo mana rakiya har wajen mota. Saida munaya tashiga mota sannan Galadima ke fad'ama Akash yayi mantuwa. Akash yace “tami?”. Babu kunya Galadima yad'an ciza lips yana tambayar Akash wai miyasa yanzu take gudunsa?. Akash yabashi amsa da maybe salon cikine, danshi babu yanda baya zuwa ma mace, wani yasata sha'awa wani kuma akasin hakan, amma idan na haihu zan iya komawa normal. Galadima ya basa hannu sukai musabaha sannan ya shigo mota yana masa godiya. Tunda muka fara tafiya saina kasa jurewa, na jeho masa tambaya muryata a sanyaye. Kad'an ya juyo ya kalleni ya maida kansa ga tuk'i, saida yaja wasu mintuna kafin yasaki ajiyar zuciya tareda cizar lips nashi, batareda Yakuma kallonna ba yace, “Friend! Wani karatun baya buk'atar fashin bak'i, akan karantashine a barsa a yanda yazo”. Murmushi nayi ina maida hankalina gareshi, nace “yalla6ai koda shi wannan karatun zai iya fita a jarabawa?”. “Humm” yafad'a yana rage gudun motar, yanzunma bai kalleniba, yad'an zakud'a jikin sitiyarin sosai, “sometimes akanyi burin cin jarabawane domin canjin aji ko gama makaranta ko shiga, saidai awannan karon ni nawa jarabawar da banbance-banbance tazo, dan bana buk'atar cin jarabawar kai tsaye, har sai harsashina ya isa ga zukatan malaman”. “to amma yalla6ai karka manta Hasashefa ba shi bane yak'ini”. “wannan gaskiyane yalla6iya. Saidai yak'ini kuma baya amsa sunan tabbaci, daga lokacinda kika shiga fili wasa kika saka aranki bazakiyi nasara ba, to da kamar wahala kiyi nasarar, duk abinda zanyi nakan rok'i ubangiji nasara Kafin yinsa, sannan na cika zuciyata da kwad'aituwar samun wannan abin, lokuta da dama mutane kan Gaza tsarkake zuciya kafin su cikata da buruka, shiyyasa kikaga duk gudun jirgi a samaniya wataran gaggawa nasakashi tarwatsa a filinda ba muhallin saukarsaba, kiringa zama mai yak'ini saikiga kin tabbata a jerin masu samu”. Murmushi nayi har hak'orana na bayya, nace, “dakai kanarine danace kafi dukkan halittar kanari iya raira zance, dakuwa mawak'ine saina saka a jerin masu zak'ak'an murya, inkuwa a Marubuci kazo to tabbas kai Kanada yawan fik'ira, domin hikayarka zata yawaita saye zukatan mabiyanka ne”. Gefen hanya ya gangara, ya kashe motarma baki d'aya ya maido hankalisa gareni. “Munaaya!” yakirani cikin wani yanayi kuma murya ahankali. nima saina amsa masa a sanyaye. Hannuna ya kamo cikin nasa yana mirza yatsun a hankali, yaci gaba da fad'in “A shekarun baya ni mutumne mai ra'ayin Kansa, ma'ana murd'ad'd'e mai wahalar sha'ani, sannan mai zama a bisa tsarinsa, kece mutum ta farko dana fara doguwar magana da ita koda bana so, nakanyi mamaki a duk lokacin da kika taya nazamo mai sallama miki, anya kuwa bakizo da wani Siddabaru ba?”. Idanu nad'an fiddo waje, nace “siddabaru kuma yalla6ai? to ai awajena ni har gobe kana akan wad'annan ra'ayoyin naka, dan banga canjin dakake hasashen kasamu ba, amma miyasa kace hakan?”. Numfashi ya sauke ahankali, kafin ya ciji gefen lips nashi yana Sosa girarsa d'aya da d'an yatsa “wannan sak'on zuciyane, kibata dama, zata tabbatar miki da cewar wannan Muhammad Sameer d'in yasha banban dana shekarun baya”. “sak'on zuciya kuma?”. nafad'a cikin hasashe, dan nikam Yakuma dilmiyar dani. Mortar ya tada yana fad'in “well basai kin zurfafa ba, dan haryanzu akwai sauran dama”. Baki na d'an ta6e ina gyara zama, “har walau zancen “dama! dama! dai again?, bana son saka baki a hurumin daba nawaba, amma abinda nasani dama dai duk damace, sannan mai ita yakan tanadar mata dukkan muhalin daya tadace da ita, damarmu ce mu damata takowane hanya mukaso”. Idanunsa ya lumshe yana sakin wani k'asaitaccen murmushi daba koyaushe yake irinsaba. Jin Sautin murmushin ya sakani juyawa na kallesa, ya d'agamin gira yana maida hankalinsa ga tuk'insa. Babu Wanda yasake yin magana har muka Isa gida. har yanzu babu Wanda ya dawo, dan haka muka haye sama kai tsaye. dama na k'agara na cire rigar jikina saboda azababbiyar zufar danakeji, danma ya tausaya min yad'an saka AC a mota, ban iya zama ba saida na watsa ruwa, nifa abubuwan sunmin yawa, nice jin zafi nice ci kamar gara, harda alwala nayo, Dan magriba tayi. Ina fitowa shima yashiga yayo alwala. Koda yafito saiya wuce masallaci. Ina jiyo hayaniyar su Samha dasuka dawo amma nakasa sauka, ina kwance abina, hawa da saukarnan bak'aramin wahal dani yakeba yanzu, ahaka Galadima yadawo ya iskeni, sallamarsa kawai na amsa, amma ban iya d'agowa na kalleshiba. Saida ya sauya kayan jikinsa zuwa marasa nauyi kafin yazo ya zauna kan sofa yana fad'in “lafiya dai?”. d'ago ido nai namasa d'an murmushi, nace, “babu komai, gajiya ce kawai”. Shima murmushin yamin, cikin lumshe ido yace, “Sorry friend, saura k'iris insha ALLAH”. “Humm” kawai nafad'a batare da nace masa komaiba. Daga nan muka d'anyi shiru, kusan mintuna 3 yanata latse-latsen wayarsa, batareda ya kalleni ba yace, “Abba kuwa yana saka zobe?”. Kallonsa nayi, amma hakan baisa ya kalleniba, a d'arare nace, “eh yana sakawa amma miyasa kamin wannan tambayar?”. Wayar ya ajiye yana sauke ajiyar zuciya, ya saka d'an yatsansa yana bubbuga la66ansa ahankali, yayinda idonsa yake a kaina tamkar mai nazari, “kina ganin idan kika bashi zai saka?”. Yunk'urawa nai na tashi zaune sosai, “dan sakawa zai saka, amma kana ganin bazai zargi wani abuba kuwa?”. “miyasa kikace haka?”. Shiru nad'anyi, dan ganin ina neman zirma kaina, saina d'an murmusa kawai cikin basarwa, nace, “waynot abashi ba kai tsayeba”.. Murmushin gefen baki yayi, yace, “y'ar tsuntsuwata wai mikike tunanine? da har kiketa kwana-kwana haka?”. Baki na tunzuro gaba, ina fad'in “nidai ba tsuntsuwa bace ba”. Dariyace ta kufce masa babu shiri, yasaka hannu yana rufe bakinsa. Haushi ya kamani na d'auki filon dana kwanta na jefa masa. da sauri ya cafe yana cigaba da dariyarsa, hakan yasa najawo na kujerar ina cigaba da kai masa duka yana karewa da wancan. daga k'arshe sakkowa yay yahad'a nida filon ya rik'e yana fad'in “sorry sorry na bari, ba 'yar tsuntsuwa ba giwar mata”. Hararsa nayi nafara kukan shagwa6a kuma. dariya Yakuma sakawa yana fad'in “toni bansan mikikeso nace mikiba kuma?”. “ni banaso duka”. “to shikenan nabari, yanzu dai yaza'ayi Ring yaje yatsan Abbanmu to?”. ‘yay maganar yana d'ora kaina jikin kafad'arsa’. “saika fad'amin sirrin sannan zan fad'a nima”. Ya murmusa yana jan hancina, “kin cika wayo yarinyarnan wlhy”. K'aramar dariya nayi nace, “ai awajenka na koya”. Murmushi kawai yay baice komaiba, ya jawo wata 'yar k'aramar bag mai k'yau fara ya mik'omin. Kar6a nayi ina tashi zaune sosai na bud'e jakkar ina fiddo kayan ciki, agogone mai masifar k'yau da tsari, na azurfa 'yar asali mai tsada, sai wani d'an akwati da ring mai k'yau na azurfa shima, an masa ado da farin stone mai garai-garai tamkar diamond, na jujjuya zoben kafin na d'ago mu kalli juna ni da Galadima, ido d'aya ya kashemin😉. Janye idanuna nayi nakuma maidawa ga zoben ina k'ok'arin sakashi a yatsana, saidai yamin yawa sosai, na cire ina fad'in “amma gaskiya zobenan ya had'u sosai yalla6ai”. “duk haduwarsa bai kaikiba ai”. ‘yay maganar acikin kunnena’. Kallonsa nayi, amma saiya basar tamkar bashi yay maganar ba. Lips na cije na d'an hararesa. Shikuma ya ta6e baki. Na maida kayan duk a cikin bag d'in dad'an hanzari ina rik'e cikina dayay wata wuntsulawa. “lafiya?”. ya fad'a yana rik'o hannuna. 'Dagowa nayi na kallesa da k'yar, da hannu na nuna masa cikina dake juyamin, jinake kamar numfashine zai bar jikina. Babu shiri ya dire wayar hannunsa ya rik'oni jikinsa da k'yau. Sosai na fara murk'ususu ina kuka da k'ank'amesa, dukya rikice, yama rasa mi zaiyi?. Ana cikin haka saiga sallamar Aunty Mimi dataga shirun yayi yawa sun dawo ban sakkoba, saitai tunanin kobana jin dad'ine, sallama tayi Galadima ya amsa murya a rikice, hakanne yasakata shigowa batareda jiran isoba. Da hanzarinta ta k'araso tana tambayar miya faru?. nidai kuka kawai nake ina kuma k'ank'ame Galadima. Shine yasamu damar mata bayani sama-sama, yak'are maganar da fad'in “Aunty mutafi asibiti please, maybe haihuwa Ce?”. Da sauri tace, “badai haihuwaba Sameer, cikin dake wata takwas, kaga ina zuwa”. Ta fita a hanzarce. Babu dad'ewa sai gata tadawo da innarmu da jakadiya, dak'yar innarmu ta amince ta hawo, danma taga tsantsar rikicewar da aunty Mimi tayine. har yanzu dai kukan nake ina jikin Galadima dashima dukya koma kalar tausayi kamar zaiyi kukan. Ganinsu a haka yasaka innarsu munaya k'ok'arin komawa da baya, dan saitaji kunya ta kamata, dukda tasan suma bada son ransuba ne. ita kanta jakadiya taji kunya. ganin innarsu munaya zata gudu Aunty Mimi tayi azamar rik'o hannunta. “please inna karki duba ta kunya, halen datake cikine abin dubawa, kowa yasan dai ba haihuwa baceba tunda da saura”. Ajiyar zuciya inna ta sauke, batare da ta motsa daga inda takeba takuma musu kallo d'aya ta d'auke kanta, tace, “inaga juyine ai, zai lafa insha ALLAH”. ‘tana gama fad'a ta fice abinta’. Jakadiya da aunty Mimi suka kalli juna, murmushi jakadiya tayi, tace, “gaskiya ta fad'a, juyine, amma nadad'e banga uwa mai kawaiciba irinta a wannan zamanin”. Murmushin itama aunty Mimi tayi, ta maida kalonta kansu, yafara lafawa sosai, dan haka munaya tafara tsagaitawa da kukan. Galadima yakuma k'ank'ameni a jikinsa sosai yana shafa kaina, nikam sai ajiyar zuciya nake saukewa tareda shashshekar kuka, ya manna min kisses a kaina idonsa a lumshe, danshi yama manta dasu Aunty Mimi a d'akin. Jakadiya ma dai lalla6awa tai ta gudu, dan taga magajin gari yau sai a hankali. Aunty Mimi ta tako inda suke ta zauna a sofa tana fad'in “sannu Munaya”. Bud'e ido Galadima yayi, harsun kad'a zuwa launin jaa, yad'an furzar da iska yana lek'a fuskarta, barci ya d'auketa. ido ya d'ago yana kallon aunty Mimi dake kallonsu cike da sha'awa, tamasa murmushin kwantar da hankali, ajiyar zuciya ya sauke yana cije lips da jinjina mata kai. Tace, “tayi barcine?”. Nanma kansa ya jinjina mata, yana gyarama Munaya kwanciya a k'irjinsa yanda zataji dad'i, yace, “Aunty Mimi amma yakamata muje asibiti aga miye matsalar?”. “karka damu my k'ani, juyine kawai, insha ALLAH babu wata damuwa. bara inje nima saida safe, idan kuma kaga dawata matsala saika kirani muje asibitin tunkan dare ya kumayi”. Bayan fitar aunty Mimi kuma k'ank'ameta yayi yanamai jin tausayinta na ratsashi, ya sumbaci goshinta, kafin ya d'auketa dukda nauyin datayi ya maidata saman gadon, yanzunma a jikinsa ya sakata, yaja bargo ya lullu6esu tareda musu addu'ar kwanciya. Cikin barci ta farka da wata matsananciyar yunwa, k'irjin Galadima na shiga girgizawa ina kuka. Galadima ya farka a firgice yana rik'e hannunna, ya yunk'ura da k'yar ya tashi zaune, “miya faru?”. ‘yafad'a cikin muryar barci’. “yunwa yalla6ai, abinci xanci, kafad'a masa magana yabar halbina”. Dukda tabashi tausayi saida ya murmusa, sauka yay yafita, k'asa ya sauka zuwa kitchen, yau saiga Galadima a kitchen🤣, rasa mizaimayi yayi, ganin yana 6ata lokacine kawai dan ba iya uwar komai yayiba saiya fice, dole yaje ya tado kukunsu. Mai aiki da aikinsa dannan saigashi ya had'a mata Abu mai sauk'i, Galadima ya kar6a da kansa Yakoma saman. Isketa yayi zaune tsakkiyar gado tana kuma rurus, saita k'ara bashi tausayi, ya haye gadon da abincin, da kansa yabata yana lallashi. saida tayi nak sannan ya sauka da tiren yana sauke tagwayen ajiyar zuciya. Nikam hankalinna kwance nazame na kwanta, barci ya sake kwasheni. Mamaki yasakashi tasata gaba yana kallo, saikace wata mai aljanu, lallai duk namijin daya kasa tausayawa matarsa lokacin da ciki yake jikinta yacika mara tausayi number d'aya, babu abinda miji zai iya biyan matarsa dashi akan rainon cikinsa datayi da tarbiyyar 'ya'yansa, amma a wannan time d'in wani namijinma rashin tausayinsa ke tashi akan matar, ALLAH ya ganar dasu to. Amin galadima🙁😔. ********************** Washe gari A safiyar yau su Abba suka tashi da shirin komawa Nigeria, gaba d'aya saina tashi duk babu dad'i, jinake kamar karsu tafi, dana tuna yaune zasu barmu sai hawaye ya zubomin, inama zai amince nidai nabisu mu tafi tare?. Agogo da zoben jiya na d'auka nafita masaukin su Abba, dan Galadima ya fita tunda sasaafe, bansan ina yajeba. Saida nayi sallama aka bani izinin Shiga sannan na shiga, Abba na zaune a bakin gado agogo rik'e a hannunsa suna magana da innarmu dake tsaye ita kuma tana zuba sauran kayansu a k'aramin akwati. Abba yay murmushi yana fad'in “sannu munaya kinji”. Murmushi nayi a kunyace, na dafa gadon zan durk'usa k'asa na gaidasu amma saiya dakatar dani ta hanyar rik'e hannuna, “kinga zauna, inake ina durk'uso yanzu”. da taimakon Abba na zauna a kujerar dake kusada gadon, sai faman jeran sannu yakeyi, nikuma ina amsawa cikeda jin kunya. gaishesu nayi, suka tambayeni yaya jikin? na amsa da “Alhmdllh”. Jakar hannuna na mik'ama Abba, ya amsa yana fad'in “minene kuma?”. “Abba ka bud'e to”. ‘nayi maganar a shagwa6e’. Dariya yayi yana k'ok'arin bud'ewa, “yanzu dai fitinarki k'aruwa ma tayi Munaya”. Innarmu dake ta6e baki tace, “ai bamaka san fitinarta ta zarce tadaba sai jiya, juyi kawai ta zauna tana rusama mutane kuka a gidannan, yo ke aibama asan abin fad'in dazaki bariba ranar haihuwar?”.. “babu abin fad'in dazata bari insha ALLAHU”. cewar Abba yana juya agogon fuskarsa d'auke da murmushi. Nima sai ban kula zancen Innarmu ba nace, “Abba yayi k'yau?”. “sosai kuwa Munaya”. “Abba kawo na saka maka to”. “to amma kekuwa ina kika samu kud'in sayen wannan agogon da zoben mai tsada haka?”. Murmushin nayi, nace, “Abba awani shago mukaje sayen kaya tun kwanaki dashi, daga nace agogon yamin k'yau shinefa yace na d'auka to”. “Amma munaya yayi tsada da yawa, karna sakejin irin haka, dan takurawace ai, idan kuma bashida k'arfin siyen abunfa? Karki sake kinji ko?”. “inasha ALLAHU Abba bazan sakeba, amma dan ALLAH karkace bazaka kar6i wannanba, dan shima bazaiji dad'iba”. Murmushin Abba yayi, yashiga sanya albarka a garemu da abinda ke cikina, hardama addu'ar d'orewar lafiya ga Abie shima. cikeda d'oki naita amsawa da amin, da kaina na saka masa agogon da zoben. Daga nan muka d'an ta6a hira. Dan akwai sauran time sosai na tafiyarsu. Mun dad'e muna hira, dan ko break fast yau tare dasu na sakeyi, dama tun asuba ni yanzu nakeyin nawa🤭, sanda kowa zai k'ara sainayi na biyu.😂 Galadima ma daya dawo ya kimtsa nan yazo ya samemu, yanda suke sakin jiki da juna shida Abba abin na bani mamaki, Galadima yakuma yima Abba bayani sosai akan yanda zaicigaba da tattalin lafiyarsa da kulawa da dukkan dokokin da sukai masa, daga nan muka cigaba dad'an ta6a hira, itadai Innarmu duk adabaibaye take, danma taga yau zasu wuce da bazata zaunaba. Wajen 12pm mukabar gidan zuwa asibiti, a asibitine akayi dogon zama, dan godiya ta musammance tashiga tsakanin surukan guda biyu, Abba kuma yay alk'awarin kuma tsayawa wajen dagewa da addu'oi na musaman ga jikin Abie da alk'awarin kawo wasu taimakon na tsarin jiki, dan sunga fa'idar addu'a sosai. Kowa jiyake tamkar karsu tafi, saboda shak'uwace ta musamman tashiga tsakanin wad'annan families guda biyu, zaman mutunta juna ya gudana sosai a tsakani. Kuka na shiga rairawa lokacin danaga tafiyarfa da gaske yinta za'ayi, sai alokacin muka san ashe wai harda Sauban, zai rakasu saudiyya suyi umrah ta kwana 10, daga nan saisu wuce shikuma yadawo. na kama hannun Abba na rik'e gam nak'i saki zai hau jirgi, su Sauban suka tasani da dariya kuwa, oho ban kulasu ba, Galadima ya girgiza kaiwai yana murmushi, yarinyarnan ta6ararta tayi yawa, yafad'a yana takowa inda muke da Abba yana lallashina. A Kallonsa Abba yayi sukayi murmushi, Abba ya zame hannunsa a hankali yajuya zuwa ga jirgi, yunk'urin binsa nayi Galadima yay azamar rik'o min hannu batareda yayi magana ba, juyowa nayi na fad'a k'irjinsa ina kuma sakin sabon kuka. Hannu biyu ya saka ya rungumoni yana guntun murmushi. Innarmu dake hangenmu ta cikin jirgi ta share hawayenta itama tana murmushi, banda aure waya isa ya rabaka da 'ya'yanka. Abba daya zauna kusada ita ya saka hannunta cikin nasa yana murzawa, juyowa tayi ta kallesa, yamata murmushi yana share mata hawayen da har yanzu sun kasa tsayawa, jikin kafad'arsa ta d'ora kanta kawai. Sauban dake kallonsu yay murmushi, lallai Aunty gimbiya 'yar gatace a gidansu. Saida naji alamun jirgi zai tashi sannan na d'ago kaina, inaji ina gani jirgin yafara shawagi a samaniya harya shilla da iyayena. A motama haka naita sharar hawaye, dayake dagani sai shi da Samha a motar, cankuma Aunty Mimi da Khaleel da jakadiya. Samha tana ta bani hak'uri, amma tamkar tana zuganine, saida Galadima ya harareta yana mata alamar tamasa shiru sannan tayi shiru, shikam ko sau d'aya baicemin uffanba.. Asibiti muka koma, tunda muka shigo Momma ta taso ta rungumeni a jikinta tana lallashi. Galadima ya jingina da bango ya hard'e hannayensa yana kallonmu, a haka sauran suka shigo suka iskemu, Abie ma kallonmu yakeyi cike da tausayina. Saida nasamu na tsagaita da kukan sannan nacema Momma zanci abinci. Galadima yaje kusada Abie ya zauna yana k'aramar dariya, “dama kice yunwa kikeji kika zauna kinama mutane ta6ara?”. Hararsa Momma tayi tana masa dak'uwa, hakama Abie, aunty Mimi kam saida ta rankwasheshi akai. Gurin ya dafe yana fad'in “a'a yazaku tararmin ne kuma?, gaskiyafa na fad'a ko Samha?”. Samha tace, “Uncle nima dai ina bayan aunty gimbiya”. Idanu ya kwalalo alamar tak'aremin. Muka had'a ido na hararaesa. Lips d'insa ya ciza yanamin alamar zan kamakine da ido. Na ta6e bakina nikuma. Dolenesa yatashi yanemomin abinda zanci. ★★★★★★★★★★ Tunda su Abba suka tafi lafiya tamin k'aranci, bana iya tsinanama kaina komai sai kwanciya, dukna fita hayyacina na canja kamanni, ga cikifa sai kuma bud'ewa yake yana k'ara girma. Kai kace ba halitta d'aya bane a cikinsa. Galadima dole ya d'auki hutu a office, idan abinda yazama dolene saiyaje Office kam yakanyi shine ta yanar gizo. Gakuma nasarar jikin Abie daketa k'ara k'yau, dan wasu sassan jikinsa suna nuna alamun fara aiki kamar yanda doctors d'insa suka sanar mana. A kwana na 8 da tafiyarsu Innarmu ranar a asibiti na kwana, saboda jiki dai yak'i dad'i, ga masifaffen cin abinci abin babu arzik'i. ★★★★★★★ Su Abba sun gudanar da ibadar Umrah cikin kwanciyar hankali da nutsuwa, ga Sauban dake nuna musu komai yanda bazasu wahala ba. Suna cika kwanaki goma yasakasu a jirgi suka nufi k'asar haihuwa Nigeria kenan, sun rabu cikeda kewar juna suna saka masa albarka. Sun isa Nigeria batareda sanin kowa namuba sai Yaa marwan da Galadima yakira ya sanarma yaje ya d'aukesu a airport. Isowarsu gidanmu tazama a bazata, hakan yasaka gidan rikicewa da murna, dukda kishin daya cika matan gidan ganin innarsu munaya takoma wata d'anya shakaf saboda Hutu da canji wajen zama data samu, dandanan 'yan anguwa suka shiga shigowa taya murna dama Abba jajen ALLAH ya kiyaye gaba. Innaro babu kunya taketa haba-haba da d'anta, kota innarsu munaya batayi, dan haushinta takeji taje ta zauna a India itako an maidota gida. (Babu mai iyama Innaro dai sai ALLAH🤦🏻‍♀🤣). Su Ayusher da sukazo suka zage suka gyarama inna d'akinta, komai ya koma need, tamkar ba shineba ya had'a uban datti na tashin hankali. Tafiyarsu Abba Nigeria da kwana 5 Sauban ma ya dawo India, ya iske ina asibiti, dan gado suka bani dole, babu ranar sallama ma, k'ila saina haihu. Saidai randa mukayi waya da Munubiya nake fad'a mata tace ai gidama yakamata na dawo na haihu, itama batada lafiyar sosai. Da to na amsa mata kawai, amma ina tunanin yanda Galadima da ahalinsa zasu amince da zuwana haihuwa Nigeria, kuma tunda 'Yar uwata ta ambata dolene hakan za'ayi, kona so koban soba kuwa. ___________________________ *_Two months ogo_*😬🤭 Watanni biyu kenan da tafiyarsu Abba, tunda sukatafi kuma babu wani Abu mara k'yau kona Sosa zuciya dayay gamo dashi, harma ya koma wajen aikinsa hankali kwance. Jama'ar gidansu Munaya kuwa sunyi haushin da nuna hassadar ga inna harsun gaji sun bari, dan sudai san ba kulasu zatayiba, ita yanzu babbar damuwarta ma 'ya'yanta su sauka lafiya, dansu Safara'u duksun haihu sukam, kuma dab da dab sukaita kancamo 'ya'yan, ayanzu haka sunan d'an Fauziyyane kawai yarage gobe idan ALLAH ya kaimu, dan itace k'arshen haihuwa.. Su fiddausi duk suna gida sunzo wanka, iyayensu kowa ta zuba k'arya a hidimar sunan 'yarta, yanzu maman Fauziyya da innarsu munaya kawai aka zubama ido aga yanda zasuyi nasu. Inna dai bata d'ad'ara kanta da k'asaba, iya abinda ALLAH ya hore mata iya shine tai k'udiri yi a hidamar sunansu Munubiya idan sun haihu. Fatantama su sauka lafiyar, dan gasu suna neman share watanni na goma haihuwa babu amo babu labari. Mama Rabi'a cema kawai keta k'ok'arin ta na ganin sun tanadi dukkan abin fita kunya, sai Aunty Salamah dake taimaka musu, wadda a yanzu tazama 'Yar uwa agaresu makusanciya, dan komai nasu tana tsaye a akai tsakaninta ga ALLAH. WASHE GARI akasha sunan d'an Fauziyya. Wanda mijinta da mamarta suka bada mamaki, masu shirin asha kunya sai aka barsu su dajin kunyar da shak'ar bak'inciki irinna masu hassada. Itama tamkar su Haleematu gida ta taho wankan jego. ************************** A wata ranar talata datai dai-dai da cikar cikunanmu wata goma da sati biyu natashi da matsanancin ciwo, Wanda ya rikita Galadima da ahalinsa, nan take doctors sukace haihuwace, aka fara shirin kar6arta amma ina, gadai haihuwar gadan-gadan da gaske amma kuma nagagara haihuwar har washe garin laraba. Nayi masifar galabaita, Galadima yace sumin cs idan bazan iya haihuwa da kaina ba. Amma sukace zan iya haihuwa. Ranar laraba da daddare Galadima da Momma na kusadani suna ta tofamin addu'a saboda zufar danakeyi, nace su kiramin munubiya, babu musu Galadima ya kira Yaa marwan. Shima dakaji muryarsa zakasan a rikice yake, hakan yasaka Galadima tambayarsa ko lafiya?. Yaa Marwan yace, “dadai sauki ranka ya dad'e, tun daren jiya Munubiya ke nak'uda amma haihuwa shiru, sai sunan Munaya kawai taketa kira”. Mik'ewa Galadima yayi tsaye, yace, “muma ai halin da ake ciki kenan, yanzuma itace tace akira mata ita, please kakai mata wayar”. “ok”. Yaa marwan ya amsa yana nufar d'akinda Munubiya take...............✍🏻 Barkanmu da dawowa.🤩✋🏻 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 [7/9, 2:53 PM] Aysha Galadima: *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* _________________________ *_HASKE WRITERS...._* _gaisuwarku ta musammance, alkairin ALLAH ya baibayeku aminan kwarai abokan tafiya👍🏻😽._ I love you manya-manya fa🥰🥰🥰🥰🤩🤸🏻‍♀ ________________________ ~book 2~👉🏻2⃣2⃣ ................Cikin kuka Munubiya tace, “y'ar uwata ki taho gida please”. Munaya dake saurarenta ta share nata hawayen itama, “insha ALLAH zan taho, ki kwantar da hankalinki, daga yau zuwa gobe ko yaushe zaki iya ganina sweetheart”. Daga haka munaya ta mik'ama Galadima wayar tana cigaba da share hawaye. Hankalinsa atashe yace, “miyasa zakimata alk'awarin zuwa? bayan kinsan ga halin da kike a ciki”. “kayi hak'uri yalla6ai, gara ka barni Na tafi shine mafi a'ala, tun farko y'ar uwata bata 6oyeminba ta sanarmin naje gida Na haihu, idanma baka kainiba to wahala kawai zanta sha anan d'in tunda hakan take buk'ata”. Galadima jiyay tamkar ya make Munaya, ya haukace mata da masifa kaikace zai cinyeta d'anya, “wannan ai canfin banzane da wofi, ALLAH shine kawai maiyi ai bawani alk'awarinku ba, shin Ku bazaku tausayama kanku baneba? yaufa kwannanki biyu kina wahalarnan, wane irin taurinkai ne wannan.......?”. Dakatar dashi Momma tayi ta hanyar d'aga masa hannu, ta dafa k'afad'ar munaya dake kuka tana fad'in “y'ata dama kinmata alk'awarin zakije Nigeria ki haihu ne?”. “Momma ba alk'awari namataba, amma kusan 2months kenan tacemin gida zanzo Na haihu ko? nikuma bance mata komaiba”. Murmushi Momma tayi, ta kalli Galadima dake tsaye yanata kumbura dan haushi. “Muh'd anemi ticket d'in Nigeria yanzunnan”. Da sauri yace “Momma amma......” Hannu ta d'aga masa alamar bata buk'atar jin komai. ya had'iye wani k'ullutu daya tsaya masa a mak'oshi, shifa ba tafiyar tata bace matsalarsa, shima akwai tashi manufar da dalili, amma bashida ikon yin jayayya da Momma, waya ya zaro a aljihu. Ya lalubo wata number yay kira, ficewa yay daga d'akin. Momma tacigaba da lallashin Munaya daketa hawaye, ga zufa Na cigaba da jik'eta dukda AC dake aiki a d'akin. Kusan mintuna talatin Galadima yashigo shida doctor, dannan aka shirya Munaya, nurses biyu suka kaita mota. Wannan karon harda Momma rakkiya Airport, tanata jerama Munaya addu'oi har suka isa. Haka sukai wannan tafiya babu shiri, Galadima kayan tun safenema a jikinsa bai ko koma gida ya canjaba, hakama aunty Mimi. A jirgi yana rungume da ita tanata murk'ususu idan abin ya motsa, wai danma waje Na musamman aka basu dankarta takura. idan nak'udar ta lafa sai barci mai dad'i ya kwasheta, da abin yamotsa kuma tata kuka kenan tana k'ank'amesa, dukta jimasa ciwo da farce, shikam tausayinta dukya cika zuciyarsa. Yaa marwan ma cikin haushi yakira inna ya gaya mata abinda Munubiya tayi, inna taita fad'a tamkar zata ari baki, itada ta haifi su munaya ita tasan halin kowa acikinsu, tabbas a fili Munaya tafi Munubiya fad'a, amma a bad'ini Munubiya tanada ak'idar tsiya da tsatstsauran ra'ayi, lokuta da dama idan takafe akan Abu bata tankwaruwa, kuma dolene Munaya ta amince ayi kokuwa tasha wahala, dan idan Munubiya ta murd'e abin bazai ta6a ya yuwuba saidai idan Ubangiji ya juna mata ikonsa, to amma bata ta6a zaton shirmen nasu zai iya ta6a har lafiyarsu irin hakaba. Dole inna tashirya zuwa asibitin da kanta, taita zubama Munubiya dake fama da kanta fad'a, su mama Rabi'a da Maman Fauziyya sunata bata hak'uri, tunda dai anrigada an aikata, saidai kuma a kiyaye nagaba. Su Munaya sun iso Nigeria lokacin tsakkiyar ranane anan, dan irin 1pm d'innan ne, dayake yakira su sarkin mota ya sanar dasu time d'in dazasu iya isowa, tun wajen 11am ma suna airport d'in.. Tunda Galadima yafara sakkowa daga matakalar jirgin rungume da Munaya akan idonsune, hakanne yasaka sarkin mota matso da motar bisa alfarmar ma'aikatan wajen, suna gama sakkowa k'afarta ta rik'e, dole ya d'auketa daga ita har nauyin cikin ya k'arasa da ita motar, mutane duk tausayinta yakamasu. Tunfa a mota labari yafara canjawa, dan Munaya tafita hayyacinta sosai, Galadima sai tsawa yakema sarkin mota, ALLAH daine kawai ya kaisu asibitin lafiya, aiko suna shiga dogarai suka shiga da gudu cikin asibitin kiran doctors. Tunima Galadima ya kuma sunkutarta yayi ciki, a hanya yagamu da nurses da gadon d'aukar marasa lafiya, bai d'orataba, yawucesu abinsa, doctor Farida ta nuna masa d'akin da aka canjama Munubiya. Gadon da aka tanada dan Munaya ya d'orata, Munubiya tashiga mik'o mata hannu tana kuka, itama a wahalce tamik'a mata nata, dan gadon kusa da kusa aka sakasu.... A tare suka dinga Neman yafiyar junansu suna kuka, sai tausayinsu ya kamasu Galadima. Da k'yar doctor Farida tasamu Galadima ya fita suyi aikinsu, dama haka tasha dagama da Yaa marwan shima, saida ma Abbansu yamasa magana, Dan shima yana asibitin. Munubiya da Munaya Haka suke rik'e hannun juna kowa nashan azabar nak'uda, (wannan k'auna dabance gaskiya, nak'uda ba abun wasaba amma suna son jin junansu a kusa, wato koma mutuwace tazo musu a tare?😽). Haihuwar Munubiya ce tafara gadan-gadan, Dan haka Munaya ta k'ank'ame hannun y'ar uwarta tana kuka da kiran sunanta a galabaice, itama sai labarin yafara canjawa, Nurse da doctor Farida and doctor Zainab dake Kansu duk suka maida hankali ga Munubiya, cikin rahamar ubangiji saiga jinjiri yayi sallama duniya da kuka. tamkar jira itama Munaya ta kar6a, a time d'in Munubiya tayi shid'ewar wucin gadi, amma hannunta na cikin na Munaya datake shan azaba itama. Ba'a d'auki tsawon lokaciba itama tata mace tafito, saikuma sabuwar nak'uda ta tashi a tare suduka, yanzu Munubiya mace Munaya kuma namiji, na Munaya na fad'owa wani yakuma biyo baya😳. Turk'ashi, ALLAH sarkin rahama da tausayi, maiyin yanda yaso kuma ga Wanda yaso, Munubiya ALLAH yabata k'autar tagwaye mace da namiji, yayinda Munaya keda uku, maza biyu mace d'aya. Su doctor Farida duk sun kacame da murna da k'ok'arin gyara yaran, kaikace su akama haihuwar. Dandanan aka shiga goge yara da zaitun, amma cikin hattarar kar a had'esu agaza ganewa.. Su Munaya ma dai kulawa ta musamman aka basu, amma Munubiya ta suma, kuma bata farfad'oba, hakanne ya tada hankalin su doctor Farida suka rufu akanta suna bata dukkan wani taimako, sama-sama Munaya ma kejin 'Yar uwarta tashid'a, hakanne yasata kuma k'ank'ame hannunta hawaye na zurara mata, itama bawani k'arfine da itaba, Dan ko idanu dak'yar take iya d'agawa, dishi-dishima take ganin komai. Lamarin yana san zama babba, Dan saida wani babban doctor ya shigo dole, ganin shigi da ficinsu doctor Farida yayi yawa yafara ankarar dasu Galadima. Nanfa suka fara turkesu da tambayar ko lafiya?, sukuma suna basu amsa da babu komai, kowa dai bai yardaba, dukda suna jiyo kukan jariran. An d'auki wasu adadin mintuna kafin numfashin Munubiya ya dawo, ajiyar zuciyar da Munaya tasaki duk saida yasaka su doctor Farida kallon ta da tausayi, dukda tana cikin wani hali itama, amma hankalinta nakan 'Yar uwarta. Sun kimtsasu tsaf, daganan aka musu allurar barci dansu sami Hutu, yara dai kam Alhmdllh, duk da sun lura d'aya daga cikin na Munaya bai cika kuzariba, kamar sauran mace da namijin sun fishi lafiya, amma basuda tabbas tunda basu bincikaba. Nurse d'aya tafito ta kar6i kayan haihuwar takoma, duk an saka musu, dukda basu zama iri d'aya ba tunda sunzo babu tabbacin miza'a haifa, musamman ma su Galadima, gara su Yaa Marwan sunsan ita Munubiya dama biyune. Tunda su doctor Farida suka fito Galadima dake ta kaikawo shida Yaa marwan da Muftahu suka maido hankalinsu Kansu, Galadima bai iya matsawa ba, saisu aunty mimine suka k'arasa ga su doctor Faridan. Kowa yana k'ok'arin tambayar abinda ke faruwa. Doctor Farida tayi murmushi, tace, “to ai bakine bazai iya fad'a ba ma, inaga kawai angunan k'arnin su shiga daga ciki, idan sun fito kwaji komai”. Yaa marwan da Galadima suka kalli juna, kowa yana fargabar abinda zai tarar d'in. Aunty Mimi ce takama hannayensu tana fad'in “kuje mana, mi kuke tsorone wai?”. Kowa tamkar an doke masa gwiwa haka suka nufi d'akin, Yaa marwan ne gaba Galadima a baya.. Duk sukayi sororo a k'ofar d'akin suna bin gadajen matan nasu da jariran kusa dasu da kallo. Badan kowa yasan kayan jikin matarsa ba dabasu iya banbancewa ba (kunsanfa mu 9ja 'yan gargajiyane🤭, kod'an canja kayannan na asibiti bamayi🤣). Galadima da Yaa marwan suka kuma kallon juna, kowa ya kasa cewa uffan, doctor Farida dake bayansu tamkar ta kwashe da dariya, tadai daure ta danne. Ra6asu tayi ta shigo ciki sosai, ta tsaya tsakkiyar gadajen tana kallon hannun Munaya da Munubiya dake had'e da juna har yanzu, sunyi-sunyi su saki amma sunk'i, sai suka saka musu lokar asibiti a tsakkiyar aka d'ira hannayen Dan kar suyi sanyi.. Juyowa tayi ta kallesu da murmushi a fuskarta, tace, “wannan itace Munubiya ga babies d'inta nan 2 mace da namiji, wannan kuma Munaya ga nata 3 maza biyu mace d'aya. Ina muku fatan alkairi gaba d'aya, ALLAH ya rayasu akan sunna”. tana gama fad'a ta juya ta fita tabarsu. Binta sukayi da kallo harta fice, sannan suka maido ga iyalan nasu, saikuma kowa ya k'arasa da hanzari ga matarsa. Yaa marwan yasaki murmushi yana d'aukar macen, sanan ya d'auki namijin shima, dukya rungume. Galadima kam durk'usawa yay gaban gadon yasa gwiywoyinsa a k'asa ko k'yank'yami bayayi, dukda angyara wajen tsaf tamkarma ba'a haihunba. Hannunsa d'aya ya d'ora agoshin Munaya da duk yaga ta masifar rame masa yau, d'ayan kuma yafara tsafa kumatun yaran d'ai-d'ai, hawaye masu d'umi Wanda shikad'ai yasan ma'anarsu suka fara sauka a kumatunsa. Cikin lumshe ido ya matsa ya sumbaci goshin Munaya da hancinta, sannan ya dawo kan babies nashi yana sumbatarsu. Yaa marwan ma yanacan ya duk'ufa kan matarsa yana mata kalamai masu dad'i acikin kunne k'asa-k'asa, kai kace idonta biyu tana jinsane😹. Galadima ya share hawayen fuskarsa, cikin murmushi yace, *“UBANGIJINA ka gamamin komai, yau nine da k'yautar abin cikin kwan d'ai-d'ai har 3 a lokaci d'aya, badan k'arfina kabaniba, bakuma Dan nafi sauran bayinka ka baniba, suma y'ay'a jarabawace ga iyaye, ya Mahaliccinmu kabamu ikon bama yarannan tarbiyar da zasu zama cikin alfaharin MANZON ka da addininmu mu da mahaifansu mata, ka rayasu bisa turbar addinin islama, ALLAH yasa suzama masu tausayi da jink'ai gana k'asa dasu damu kanmu, su zama masu girmamawa da mutunta na sama dasu a duk inda suka shiga, ya RABBI ka rinjayar da zukatansu ga bautarka domin rabauta a duniya da lahira, ka nisantar da zukatansu da gangangar jikinsu ga sa6onka komin k'ank'antarsa dagasu har 'yan uwansu gasunan guda biyu da k'annensu masu zuwa da dukkan y'ay'an Al'ummar musulmi. I love you so more and more my Darling children's, ina muku barka da isowa duniya gidan gwagwarmaya, ALLAH yabaku damar cinye jarabawar da ubangiji ya k'addaro a cikin tsawon rayuwar da zakuyi a dunia kafin Ku koma garesa”.* Yaa marwan ya amsa da amin shima fuskarsa d'auke da murmushi. Tashi Galadima yayi yaje gareshi suka rungume juna. Galadima yace, “d'an uwana ina tayaka murna”. Yaa marwan ma yace, “ranka ya dad'e nima ina tayaka murna”. Sakin juna sukayi suna dariya, saikuma suka kuma cafke hannun juna cikin musabaha da nuna tsantsar farincikin dake baibaye da zukatansu a yau d'innan. Aunty Mimi kasa hak'uri tayi ta danno kai d'akin babu ko sallama. To shigowarta cefa ta fallasa komai, kowa yasan d'unbin alkairin daya sauka a wannan families guda uku a yau. Dan danan labari yafara karad'e asibiti da gidajen su Galadima Dana su Munaya. Masarautar gagara badau, masarautar su papi, su Momma duk labari ya Isar musu harda hotunan babies gaba d'aya, kafin kacemi labari yafara zagaye social media, *FANS NA RAINA KAMA FA* babu ala, dama duk sungama shirinsu, (danma ansamu sa6ani masu tafiya india🤣, Wanda basu kai ga tafiya ba ALLAH ya taimakesu saiku tattala kud'in jiyginku babu ruwana😹😂🤸🏻‍♀). Bakin Galadima da Yaa marwan da dukkan ahalin wad'annan dangi kam yakasa rufuwa, hardamu ma masoyansu. Yauma dai su doctor Farida da jama'ar asibiti sunsha k'yaututtuka, Dan Muftahu ya baza abin mamaki, ( lokacin da su sarkin mota zasu fitone yagansu kamar a rikice, shikuma zai fita daga masarautar shine ya tambayesu, sarkin mota ya fad'a masa, bai bisuba saiya wuce asibiti, shine yasaka aka canjama Munubiya d'aki, aka tanadi gadon Munaya kuma). dukda Galadima yayi mamakin ganinsa hakan bai sakashi tambayarsa ba ko katse masa hanzari, ko'a fuskama bai nuna mamakiba. *************** Mama Fulani Na kishin gid'e bisa kilisarta kuyanginta Na bautar da suka saba, Wambai na gefenta yana nuna mata pictures na gidaje dayake son za6ar d'aya daza'a gina masa shima acikin masarautar, don mama Fulani tamatsa suyi aure, shi matawalle yamace bazai zauna da matarsa a k'asarba. Amma mama Fulani tace dolene saiya zauna. Wata baiwace ta shigo jikinta sai 6ari yake, ta zube a gabansu tana huttai, Wambai ya daka mata tsawa. Firgita tay tayi baya zata fad'i, Mama Fulani ta d'aga masa hannu alamun ya barta. “haba Granny kina ganinfa yanda ta shigoma mutane a haukace, saikace wasu sa'ointane a wajen?”. Uffan mama Fulani batace masaba, sai wani k'asaitaccen murmushi datayi tana kallon amintacciyar baiwarta, alamu tamata da ido na ta tambayi mi dattijuwar tazo dashi?.domin itace dama mai kawo ma mama Fulani duk wata gulma takowane 6angare a masarautar, Dan ita babu sashen dabata da 'yan lek'en asiri, kuma wannan dattijuwar baiwa itace shugabarsu, komai suka tattaro ita zasu fad'awa ita kuma takawo ga mama Fulani. “mike faruwa tulluwa?”. Amintacciyar baiwar mama Fulani ta fad'a tana kallon dattijuwa tulluwa dahar yanzu jikinta baibar 6ariba. “Ranki ya dad'e ki gafarceni da abinda nazo fad'a, banida za6in daya wuce hakan, domin da kiji a bakin wasu gara kifara ji abakina danki tabbatar nasan aikina”. Mama Fulani ta hura hanci, yayinda izzarta ta k'aru, sosai ta tashi zaune idonta akan tulluwa. Batareda tace uffanba tulluwa tacigaba da magana, Dan tasan ma'anar kallon ta cigaba da magana kenan. “ranki ya dad'e yanzunnan labarin haihuwar matar Galadima ta iso wannan masarauta, ba haihuwar baceba abin girgiza abinda ta haifanne, idan kinbani izini sai na fad'a uwar gijiyata”. Wani kakkauran yayu mama Fulani ta had'iye, Wambai daya cika yay fam da haushin wannan shegiyar baiwar ya Dalla mata harara, “dalla malama kifad'a kinwani zauna cancana magana kamar wata zuma”. “ALLAH ya huci zuciyarka ranka ya dad'e, maganarce tanada nauyi. dama labari ya iso ta haifi yara uku ne maza biyu mace d'aya....” Wambai yay masifar razana harda mik'ewa, mama Fulani kam ko motsi batayiba, sai wani k'ayataccen murmushi na k'asaitattun mata masu izza da mulki tayi, ta d'ago ido ta kalli Wambai cikin harara tace “kai kuma miye na mik'ewar?”. Tunawa yay akwai kuyangi saiya saki murmushi basarwa, yace “mamaki mana Granny, 'ya'ya uku fa a 1 time, dolene na taya d'an uwana murna ai”. bai jira cewarta ba yafice da hanzari. Lumshe idanu mama Fulani tayi bayan Wambai ya 6acema ganinta, ta kalli amintacciyar baiwarta fuska d'auke da murmushi nan tace araba k'yaututtuka, takuma sallami kowa. K'yaututtukan da mama Fulani tasaka a rabama bayin gidan yasaka zancen haihuwar munaya yakuma karad'e lungu da sak'o na masarautar, masu murna nayi masu kuka nayi, dan kowa dai yasan magadan masarautar gagara badau sun iso, tunda kowa yasan Galadima ne magaji mai jiran gado, _(karku manta haryanzu sarkin yanzu sarautarsa ta ruk'on kwaryace, Dan mahaifin Galadima tsohon Sarki bawai mutuwa yayiba, sannan ba murabus yayi da kansa yace yabarma Sarki na yanzu sarautarba, so sarautar ruk'on k'warya yakeyi, kuma ko a yanzu tsohon Sarki yasamu lafiya dolene ya sauka yabashi kujerarsa, mai guri yazo kenan, mai tabarma dolensa ya nad'e🤷🏻‍♀)_. ************** A 6angaren gidansu Munaya ma bata canja zaniba, Dan hassada k'ararace tafito a fuskokinsu da matuk'ar razanuwa, kenan arana d'aya Innarsu munaya ta wayi gari da jikoki 5 kenan? miyasa a komai sai Ai'sha ta fisu ne? bayan kuma sun fita gata sun fita dukiya, sukeda dangi da tarin 'ya'ya a gari, suke da ilimin zamani, k'asarsu ce ba karoro sukazoba?. Innaro kam dai tadage sai zuba gud'a take da taka rawa, gud'artace ma ta ankarar da jama'ar anguwar mi ake ciki, dandanan aka cika mata gida ana tayata murna. Babu kunya tasaka Shu'aibu ya kaita asibitin, bayan kwanakin munubiya biyu akan gwiwa kuma tasani amma bata ta6a nuna sha'awar zuwa dubata asibitin ba ma.😏 *************** Tunda kuyanginta suka fice tamik'e zaram itama, safa da marwa tafarayi na tsantsar tashin hankali a makeken falonta daya gama jin kayan alatu tamkar bana tsohuwa ba, zufa dukta jik'eta sharkaf, sai kuma maimaita fad'in “y'a'ya uku? Y'ay'a uku fa? wannan 'yar yarinyar ta haifa y'ay'a uku?, kai banma yardaba gaskiya, kodai k'aryane basuji d'ai-daibane?. jikinta na rawa ta jawo wayarta tayi Kiran Momma. Momma dake cikin tsantsar farinciki saboda isowar labarin haihuwar jikokinta sabbi fil a Leda har uku, ta d'aga kiran mama Fulani. A mutunce ta gaisheta kamar yanda ta saba koyaushe. Mama Fulani bata amsaba, sai tambaya data jehoma Momma, “Zeenah ashe matar d'anki ta haihu? Amma aka kasa sanarmin sai dai naji a jita-jita?”. Murmushi momma tayi, tace, “ranki ya dad'e a gafarceni, amma Nima yanzunnanma nakeji, dan suna isowa Nigeria tafara nak'uda tun a mota”. Cikeda mamaki mama Fulani tace, “yo a ina ta haihun?”. “anan Nigeria ne ai mama”. “Ai nazata anan India ne shiyyasa na kira, to ALLAH ya raya, bara nasa a bincikan asibitin”. bata jira cewar Momma ba ta yanke wayar, murmushi kawai Momma tayi tana girgiza kai, ta k'agara Abie ya tashi a barci ta guntsa masa wannan daddad'an labari. Saman kujera mama Fulani ta jefa wayarta tana cije la66anta da sakin wata k'aramar k'ara hawaye na zubo mata, ita kuma tata ta k'are, Matawalle ya dace da haihuwar wad'annan 'ya'yan ba Galadima ba, dolene tanemo mafita da gaggawa kafin lokaci ya k'ure mata. 🤣🤣🥴 ★★★★★★★★★★ Kiran Momma daya shigo a wayar Muftahu ya saka shi mik'ama Galadima, dama shiya kirata ya Sanar mata haihuwar, ganin haka ta kirashi danya had'ata da Galadima, tunda taga suna tare. Hakkanne yasaka Galadima fitowa harabar asibitin yana amsa mata, cikeda tsantsar farin ciki suka shiga taya juna murna, ya tambayi ina Abie, ta Sanar masa yana barcine. Momma tace, “an sallamekune?”. “a'a Momma, har yanzu suduka barcima suke, gashi magriba ma ta gabato anan, banama zaton sallamarnan yau, maybe sai zuwa safiya”. Ajiyar zuciya momma ta sauke, tace, “to Muh'd yau fa barci bai gankaba, dolene idonka yazama abud'e tundaga kan doctors, Nurse's, da makusantanka, hankalin duk wani idon mak'iyinka yanzu akan wad'annan bayin ALLAH guda uku yake, sunsan shine kawai tarko mafi tsauri dazasu maka a yanzu, su zaituna suna hanya itada kuyangi 5 amintatu da zasu zauna daku, itama Zaitun (mom) bazata komaba sai anyi suna, anayin suna kuma Munaya zata koma gidansu tayi wanka irin na al'ada da kowa ya Sani, tunda kasan dokar masarautar taku kenan. Wannan kawai shine mafita”. Ajiyar zuciya Galadima ya sauke, muryarsa cike da damuwa yace, “insha ALLAH Momma duk za'ayi hakan, amma zama gidan nasu bak'ya ganinsa kamar had'ari? tunda za'a iya tsutar dasu a can, dan babu wani tsaro”. Murmushi Momma tayi har Galadima najin sautinsa, tace, “nasan abinda nakeyi ai Muh'd, bazance aturasu canba nasan zasu cutu, kaidai kawai kayi hakan, sauran bayani saika dawo zakaji komai, su zaitun nasan suna gab da isowa insha ALLAH. Papi ma yace yakira wayarka bata shigoba daga kai har Haneefa”. “tab, yoni Momma ai banmazo da waya ko d'aya ba wlhy, duk nan na mantasu a mota, kima saka khumar ya kawo miki, saidai zuwa Safiya nasamu k'arama na r'ik'e”. “to shikenan, dama haka nafad'a masa nima maybe kabar wayoyin anan, idan ta farka dai a kirani naji muryar d'iyata nima, konaji sanyi”. Murmushi Galadima yayi yace “insha ALLAH Momma”. Koda wayar ta yanke saiyayta juya maganganun momma a ransa yana musu fashin bak'i d'ai-d'ai. Haka ya koma zuwa cikin asibitin, dan anfara addabarsa da kallo, shi saiya rasama mi suke kallon? Shidai bayasha banban da sauran halitta bane, bakuma za'a kallesa ace ba bak'in fata bane, bakuma wasu kayan ado na musamman ya sakaba, hasalima k'yank'yamin kayan jikinsa yakeyi, dan sun kwana suna Neman yini a jikinsa, (tunda ba time d'inmu d'aya da India ba) yaja guntun tsaki yana k'arasawa ciki ya mik'ama Muftahu wayarsa. *********** Sai bayan isha'i su mom suka iso, dan basu sami jirgi da wuri ba, a lokacin jama'ar gidansu Munaya suna asibitin, masu kukan zuci nayi masu murna da gaskiya nayi, hakama a wasu daga masarauta suna nan, wasu lek'en asiri kawai aka turosu, wasu ko na taya farincikine da tabbatarwa. Yau dai yan gidansu Munaya suna kallon abin mamaki, da gaske dai inna Ai'sha tamusu fintinkau irinna jirgi, saidai hange daga nesa da harara cikin duhu. Mom bakinta yak'i rufuwa, harda rungume Galadima, Nuren kuwa hardasu taka rawa🤣, Muftahu na masa lik'i. Mutane abin ya birgesu, Galadima yay murmushi yana d'an dukan kafad'ar Nuren da Muftahu kawai. Su Munubiya basu farkaba har sannan, doctors sunce babu wata Matsala, a barsu su huta sosai yanda zasu tashi da kwarinsu zuwa Safiya. Dole dai Galadima yasa aka zuba police a asibitinan ranar, sauran kuma anbarma UBANGINJIN TALIKAI dake kallon motsin kowa. Masu tafiya duk suka tafi, aka bar masu kwana kawai. Galadima da ya dage anan zai kwana shima, da k'yar dai mom ta lalla6ashi ya tafi gida kodan yasamu yad'an huta, kallo d'aya zaka masa ka gane a matuk'ar gajiye yake, jijiyoyin Kansa sunyi rad'a-rad'a, ga yunwa waddama ya manta da ita da alama. Wannan dare dai ya kwana rayashi da bautar ALLAH ne da godiya mai yawan gaske. Innarsu Munaya ma dai kuka sosai tasha na dad'i, itama haka ta raya wannan dare, hakama Abba, shima yamik'a godiyarsa ga ALLAH dan lokacin dayake buri da tanadi ya cika, koba komai zai sauke nauyin dake rataye a wuyansa insha ALLAH. Washe gari...............🤩✍🏻 *_media ko bala'i, kayi turanci a novel ace ka cika iyayi da son asan ka iya turanci🤦🏻‍♀, muda muke koyo muyi ace bamusan abinda mukeba🤦🏻‍♀, kai jama'a babu mai iyama 'yan social media sai ALLAH, ko uwarka ka yanka kagasa tasha mai kwallan tana d'iga, da wani yagama ci zaice bataji gishiri ba🙄, ALLAH ya shiryar damu muda bakunanmu dai.🙏🏼._* _Ayshan sadiq sak'onki ya iso gareni, nakuma gode kwarai da gaske, saidai ina mai baki hak'uri da sauran fans d'ina, a gaskiya weekend d'inan ina muhimman abubuwane a cikinsa, bazan iya alk'awarin typing ba, sannan ni kaina idanuna 👁👁da Brain 🧠 d'ina suna buk'atar hutu, inada aure, akwai wasu hak'k'oki a kaina bana typing kawai ba, kunga yadace suma na basu lokacina, dan Ku gamsu nake zaman yin typing mai tsawo, insha ALLAH idan mukai hak'uri kamar yaune raina kama zaizo k'arshe abarma yayinsa Ku manta dashi saikuma wasu dazasu 6ullo daga sauran writers namu, dan haka muringa hak'uri da abinda ALLAH ya k'addara namu a lokacin da ya tsara, kar muyi gaggawa domin aikin shaid'ance, nima Ku duba nawa buk'atun amatsayina na mutum kuma mace mai rataye da igiyar auren. Ina godiya kwarai da gaske da k'aunar da kuke nunama wannan buk, bammasan yanda zan nuna muku farincikina ba kusan inajin dad'in Comments naku nima, amma ina sonku irin sosai d'inan a raina, kumuje zuwa guys, duk Nisan jifa k'asa zai fad'o👎🏻_ I love you mazga-mazga all.😘😘🥰🥰😍😍😍🤝🏻. Ayshan sadiq, ina miki fatan alkairi a duk Inda kike😘😘😘😅🤝🏻. *_ALLAH ka gafarma iyayenmu_*🙏🏼😭 [7/11, 1:10 PM] Aysha Galadima: [7/9, 11:05 AM] ❤y'ar K'asa❤: *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻2⃣3⃣ ...............Koda Muftahu ya sauke Galadima saiya sake shiri Yakoma asibitin, tunda ya shigo idon Nuren a kansa, sai mamaki ya kamasa, shin miya maido Muftahu asibitin? bayan kuma tare suka tafi da Galadima. Bai masa maganaba dan karma yasan ya gansa, saiya saka ido a dukkan wani motsin Muftahu d'in, shidai Muftahu baisan yanayiba, dan baima je d'akinda su Munaya sukeba, sai zagaye-zagaye dayaketa famanyi har ALLAH ya wayi gari lafiya. Wannan lamarifa ya zaune a zuciyar Nuren yanata kaikawo, anya kuwa ba suna zargine akan abinda ba haka yakeba?, dukda jami'an tsaro dake wajen Muftahu Nada damar aiwatar dadukkan abinda yay k'uduri tunda kowa namasa kallon makusancin Galadima, amma har ALLAH ya wayi gari baimayi wani yunk'uri na shiga d'akinba balle alamun rashin gaskiya, saima aikinsa dayay kama dana mai k'ok'arin bama wani abu kariya, “ya ALLAH ka warware wannan lamari cikin sauk'i kodan wannan bawa naka yasamu nutsuwa shima”. Nuren ya fad'a a fili yana d'aga hannayensa sama alamar rok'o. Muftahu dake kallonsa yay murmushi yana amsawa da amin a la66ansa, daga nan yafice abinsa ya koma masarauta, saboda anata kiraye-kirayen sallar asubahi **************** Misalin 7:30am Munaya ta farka, kamar a kunnen Munubiya itama saita farka, su mom dake d'akin suka shiga musu sannu, cikin tsantsar farin cikin farkawar tasu, dandanan aka kira doctor. Alhmdllh babu wata matsala a tattare dasu, aka kikkimtsasu dagasu har yaran daketa barci irinna jinjirai, daga Munu... Har munaya dai kallon y'ay'a biyar sukeyi, amma tunaninsu ko cikin y'ay'an y'an uwansune. Doctor Farida data lura da hakan tayi murmushi kawai. umarni tabama Nurses d'in abama kowa nata, kallon kallo akeyi tsakanin Munaya da Munubiya, amma kowa bakinsa yagaza furta komi, saisu kalli juna sukuma kalli jariran gabansu. Doctor Farida dai dataga basuda niyyar d'aukar yaran tace “y'an biyu wannan itace k'yautar da ALLAH ya baku, Munubiya 2, Munaya 3. Duk waro ido sukayi, Dan Na Munaya ne yabasu mamaki, tunda dukansu sunsan Na Munubiya dama. Munubiya ta sakko daga gadonta batareda ta d'auki ko d'a d'aya anata ba, gadon Munaya ta nufo, ta durk'usa k'asa tana rungumo yaran, ga hawaye ga dariya tanayi, saikace sokuwa. Munaya ma dai batabi takan nata d'inba, saita nufi Na Munubiya ta d'auka duk ta sakasu a jikinta, k'aunarsu Na ratsa dukkan 6argonta kamar yanda take k'aunar mahaifiyarsu. Galadima da Yaa marwan dake tsaye a bakin k'ofa suka kalli juna suna murmushi, kowanne yana mamaki a ransa, anacewa y'an biyu akwai shak'uwa, sukam suna mamakin ta wad'annan Matan nasu, soyayyar dake tsakaninsu tanada ban mamaki da birgewa. Galadima ya k'arasa ga Munaya da har yanzu take a tsaye idonta arufe y'an biyun Munubiya na jikinta, had'ata yay itada yaran ya rungume. A firgice tabud'e ido, saitaji k'amshin turarensa, tayi baya kad'an yay saurin ruk'ota. Idonsa ya saka cikin nata yana wani murmushin dabata ta6a ganiba daga garesa. Ahankali ya furta haba “Maman y'an biyar a hankali mana”. K'aramar harara ta sakar masa, ya saka k'aramar dariyar da tadawo da Yaa marwan daga duniyar daya tafi😳, danshifa mutunmin naku har yana Neman sakin layi🤭🥳. Mom dake bayansu tayi gyaran murya, kowa saiyaja baya daga jikin matarsa🤣, suna wani susar k'eya. Munubiya da Munaya sai suka koma kusa da juna, Munaya ta kama hannun Munubiya a cikin nata. ita mom dariyama suka bata, Dan haka tad'an dara tana fad'in “An sallamemu to yanzu ya za'ayi?”. Munubiya da Munaya suka kalli juna, da alama dai basa buk'atar rabuwa, sudai su Galadima kallonsu suke kawai. Ganinfa zasuyi daru sai mom tai murmushi, da ido taima Galadima da Yaa marwan magana akan su fita. Babu musu suka fice, itakuma takama hannun Munaya da Munubiya ta zaunar a bakin gado. Magana take musu k'asa-k'asa wadda (banajin🙄). Sai naga duk sunyi murmushi suna 6oye fuska. Itama murmushin tayi tana saka musu albarka. Dan murmushin nasu ya tabbatar mata dasun amince. Daga nanfa shiri aka fara, kowacce aka had'a mata kayanta da y'ay'anta. Gayyar gidansu Munubiya su mama Rabi'a suka kwashi nasu, nasu Galadima ma haka. Manne da hannun juna suka fito, mutane sai kallonau sukeyi abin sha'awa da birgewa. Harda masu musu hotuna daga gefe.. Su doctor Farida ma saida suka matso akayi musu hoto danya zama acikin tarihin wannan asibiti. Saida Munubiya ta saka munaya a mota sannan takona tashiga wajen mijinta itama, kowanne Na share hawaye, ba'a San ransu za'a rabasuba. Saikace wad'anda za'a raba gaba d'aya🤣, kai ALLAH yabamu 'yan biyu😂⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀. ★★★★★★★★★★★★ Tarba ta musamman su Munaya suka samu a masarauta, harma abin yaso basu mamaki, hakan dai baisa Mom tayi sake da yaran ba, duk wani motsi dai idonta Na Kansu, an musu rakkiya har sashensu dayasha gyara, yayinda Galadima keta kar6ar barka ga ahalin wannan masarauta, tun daga hadimai zuwa y'an uwansa na jini, maza da mata yaro da babba. Za'ayi walimar cin abinda data sannu da zuwa ga y'an uku a masarautar k'arfe 8pm, wannan yasa ba'a jimaba aka barsu suka shige Dan Munaya tasamu ta huta. Mamaki ya kama Munaya ganin an cika mata gado da tarkacen Teddy's, wannan abun haushi da yawa yake, kuzo Ku kama jera d'iyan aljanu agado kawai. Sudai su mom suka jasu gefe aka kwantar da yaran, itama zama tayi abakin gadon tana dafe kai. Aunty Mimi tace, “lafiya dai k'anwa?”. “wlhy kaina ke ciwo aunty mimi”. Sannu suka shiga yimata, mom tace, “bara laraba tazo ayi wanka kisamu kici abinci saiki sha magani”.. Munaya ta amsa da “to” tana d'an kwanciya a bakin gadon. ********* Laraba amintacciyar baiwar inno tama Munaya cikakken wanka da babu algus acikinsa, itako sai raki takeyi da zille-zille. a haka dai aka gama wannan wanka, lokacin da suka fito sun iske yaranma Mom tamusu da kanta, ana tsaka da shafesu da mai itada Aunty Mimi. Munaya dake d'aure da zani ta rufo babban towel a jikinta ta zauna a bakin gadon tana jingina da fuskar gadon, k'asa-k'asa take kallon yaran da mamakin anya kuwa itace wai ta haifesu? koda yake ba'a jayayya da ikon ALLAH ai, tanajin k'aunar yaranta a har cikin jininta, hakama Na y'ar uwarta, amma data tuna zasu rabu kwana kusa sai hawaye suka cika mata ido. A dai-dai wannan time d'inne Galadima yay sallama, hannunsa d'auke da Leda fara. Aunty mimi da mom dake sakama yaran kayan sanyi suka d'ago duk suka kallesa suna amsa masa sallamar. Idonsa akan Munaya datai masa kallo d'aya ta d'auke ido, murmushi yayi kawai ya zauna a bakin gadon yanama su mom sannu. Cikin tsokana mom tace, “aikin kud'i nikam nakeyi, musamman akan kishiya sa haushi, bar saurin godemin”, tai maganar tana dungure d'an hancin macen dake hannunta. Murmushi kawai Galadima yayi, sai Aunty Mimi CE ke bama mom amsa da “habawa Mom, dukfa kishinki keda Momma kwayi Ku gama, itafa wannan sarauniyar saita za6a ta darje ehe”. Mom tai dariya tana mik'ama Galadima ita, “yo da wannan nanannen hancinne zata za6a ta darje d'in? maji magani dai ai”. Galadima ya lumshe ido yana manna yarinyar da k'irjinsa, k'aunarta Na rsatsashi, ya sumbaci goshinta sannan ya bud'e idonsa, kwantar da ita yayi akan cinyarsa ya bud'e ledar yana fiddo dabino mai k'yau da tsafta, a bakinsa ya saka ya tauna, kafin ya d'ora bakin nasa akan na yarinyar ya zuba mata, da farko yamutse fuska ta shigayi, taji bak'on abu a bakinta, saikuma a hankali tafara motsa d'an bakin, galadima dai yana kallonta da murmushi, dadai taji zak'i saita mamule abinta. Mom tace, “oh su madan kamila kenan, anji zak'i”. Dariya duk sukayi, ya d'auketa yamata kiran sallar hud'uba a kunnenta sanan ya ajiyeta a gefe yana fad'in “ALLAH ya rayaki akan sunnah da tafarkin gaskiya”. Su mom suka amsa masa da amin. Kallon Munaya daketa shafa manta kamarma batasan dasu a d'akinba yayi, yanda taketa wani basarwa shi mamaki tabashi, baiyi zaton hakanba gaskiya, cayake zata nuna tsantsar farincikinta akan yaran?. janye idanunsa yayi ya kar6i d'ayan yaron. Shima haka ya tauna dabino ya bashi, sannan yamasa hud'uba da addu'a ya kwantar dashi. Kar6ar d'ayan ma yayi, Wanda bai cika kuzariba, yad'an masa kallon wasu mintuna yana tatta6a jikin yaron, sai kuma ya kalli mom da Aunty Mimi da suma kallonsa sukeyi. Mom tace “Yaya dai Sameer?”.. K'aramar ajiyar zuciya yayi yana shafa sumar yaron, “mom yaronnan kamar baida kuzarin sauran 'yan uwansa”. “nima na lura da gakan Sameer, amma maybe yanayinsa kenan, kasan kowa da yanayin da ALLAH yake yinsa ai”. “hakane”. ya fad'a cikin sauke ajiyar zuciya, sannan ya d'auki dabino shima yamasa tamkar sauran y'an uwansa, yaron yadad'e bai shanye dabinon ba, daga Bayama saiya fara kuka mara sauti. Rungumesa Galadima yayi yana hura masa k'aramar iska a kunne da d'an jijigashi, sai kuwa yayi shiru, shima hud'uba yamasa, ya kwantar dashi kusada y'an uwansa amma sai yaron yakuma Sanya kuka, gashi muryarsa bata fita da k'yau. d'aukarsa ya kumayi yana murmushi da fad'in “oh little Sameer what happen?”. Mom tace, “shagwa6a ce mana”. Dariya Aunty Mimi tayi, yayinda Galadima da Munaya suka murmusa, Dan duk abinda ke faruwa tana allonsu ta gefen ido, amma ta basar kamar bata d'akin. Fita Aunty Mimi da Mom sukayi suka barmusu d'akin. tuni 6angaren ya rikice da k'amshin girki, dan cikin kuyangin da su mom sukazo dasune suke tsara girki wa maijego dasu kansu. Tashi Galadima yayi d'auke da yaron a jikinsa ya nufi inda Munaya take zaune, tun d'azun tagama shafa man amma tak'i tashi ta saka kaya. Zama yay kusada ita sosai jikinsa har yana gogar nata. Da sauri ta yunk'ura zata mik'e, ya saka hannu d'aya ya ruk'ota yana maidata. Kallonsa tayi fuska a cunkushe kamar zata fasa kuka, idanunsa ya saka acikin nata yanda bazata iya janyewa ba, aiko duk k'ok'arinta nason ta janye d'in ta kasa, sai cika sukayi da kwalla, dan yana ganin k'yallin ruwan hawayen. Yad'an murmusa yana lumshe ido da bud'ewa a kanta. muryarsa cikeda k'asaita da sanyi yace, “kekuma salon taki murnar kenan?”. Had'iye kukan dake Neman kufce mata Wanda itama batasan dalilinsa ba tayi, tayi murmushin takaici tana janye idanunta daga cikin nasa, muryarta a sark'e cikin sanyin rauni tace, “Ina tayaka murnar sosai yalla6ai”. Lips nashi yad'an cije, ya lalla6a ya ajiye yaron da barci ya d'auka gefen y'an uwansa, Munaya duk tana kallonsa. Kuma matsawa yay jikinta sosai ya jawota jikinsa, batayi yunk'urin hanashiba, kamar yanda bata hana hawayenta zubaba. Ya saka tattausan hannunsa yana share mata hawayen, “Friend dukda bansan miya sakaki kukaba ina mai baki hak'uri, wannan ranar bana buk'atar damuwar kowa sai farinciki, musamman ma daga gareki, ina rok'onki alfarmar fansar wannan damuwar taki da farinciki akan kowanne farashi, komai tsadarsa kuwa”. ya k'are maganar da sumbatar sumar kanta. Murmushi tayi, ta d'ago daga jikinsa idonta akan yaran dake jere reras abin sha'awa. Shima d'in su yake kallo. “bana cikin kowacce damuwa da kake tunani yalla6ai, kawai dai...” sai tayi shiru. Kallonsa ya maido gareta, yace, “kawai dai mi yalla6iya?”. ‘ya k'are maganar cike da tsokana’. Ta murmusa tana mik'ewa tsaye, wardrobe ta nufa ta fiddo sabbin kayanta cikin na lefe, bata kuma kallonsa ba ta wuce bathroom domin saka kayan. Binta yay da kallo harta shige, yasaki miskilin murmushi yana kwantawa kusada yaran, a fili ya furta “yarinya nasan matsalarki”. yay maganar yana sumbatar kuncin na kusa da shi, sauran kuma ya shafa Kansu. A haka Munaya ta fito ta iskeshi, ya ta6a wannan ya ta6a wancan, kallo d'aya tamasu ta d'auke kanta. Sallamar da akayi a bakin k'ofar ya saka Munaya amsawa da bada izinin shigowa. Laraba tashigo d'auke da tire babba. Da sauri Munaya ta nufeta ta kar6a, Dan dattijuwace sosai, sannu ta mata tana fad'in “iya aida wanine ya kawo”. 'Yar dariya laraba tayi, tace, “dole na kula da amanar uwar gijiyata ai ranki ya dad'e”. Munaya da Galadima suka kalli juna suna murmushi, Dan sunsan inno take nufi. Laraba ta juya zata Fifa saboda ganin Galadima na nan. Kiranta yay ta juyo, yace, “zokiyi aikinki kar Inno taga ta rame tace baki rik'e amanaba, nima yarana abincinsu suke buk'ata”. Hararsa Munaya tayi, yay Biris kamar bai gantaba, saima d'an yatsansa daya saka cikin hannun yaron, shiko ya rik'e gam tamkar yasan minene. Laraba tace Munaya ta zauna ga abinci taci.. Yamutsa fuska Munaya tayi, kamar zatayi kuka tace, “wlhy iya bakina banajin d'and'anon koda yawuna ma”. “hakane ai saidai hak'uri ranki ya dad'e, dama wasu idan sun haihu sukanyi k'am baki, amma a hankali zai canja”. Badan munaya tasoba ta zauna, laraba tabata kunu mai k'yau da aka dama don ita, sai k'amshin kayan yaji yakeyi, sai farfesu. Kallon abincin kawai Munaya keyi, amma ko kad'an batajin sha'awar ci, ta tuna kwanakin baya da idan taga abinci jikinta har rawa yakeyi wajen son ci, hikimar ubangiji daban ce, ta d'ago ido suka kalli juna itada Galadima dake kallonta tun d'azu, a zuciyarsa yana tuna kwanaki uku rak dasuka shige, yanda ta maida abinci, murmushi yamata ta d'auke idonta ta maida ga abincin. A haka Mom ta shigo ta iskesu, zama tayi tana fad'in “yanaga bakici komaiba?”. Idon Munaya cike da kwalla tace, “ALLAH mom banajin d'and'ano”. Zama mom tai kusada ita, tace laraba taje itama ta karya. Kunun ta d'auka ta tsiyaya a Kofi ta d'iba mata farfesun, “kar6a maza runtse ido ki shanye kunun nan d'iyata”. Kunyar Mom ta sakata k'ar6a tana had'iye kwallarta, tafara sha badan tanajin dad'inba, sai dan tsatstsareta da ido da Galadima yayi shida Mom. ahaka dai tasamu tasha yafi rabi, dama yunwar takeji, dad'in bakinne kawai bataji, shima farfesun tad'anci, dandanan tafara zufa. tace, “Mom dan ALLAH bara na kunna AC”. “a ina?”. ‘galadima ya fad'a yana tashi zaune da sauri’. Ita mom ma dariya ya bata, yawani had'e fuska yana harar Munaya, “malama babu wani AC da zaki sakama mutane anan, kina ganin yara duk da mura sukazo duniya saboda rashin jin maganarki.....” Mom ta katseshi da fad'in “ai bama zai yuwuba, itada ke jego ko fankace a d'akinnan ai saidai kallo kuma, yanzu ruwan sha ma sai mai zafi”. Galadima ya sakko daga gadon yana fad'in “hakan ai shine dai-dai wlhy, remote d'in AC d'in ya d'auka a lokan gefen gadon ya masa yanda bazata iya control d'insa bama gaba d'aya, sannan yafice abinsa yana murmushin mugunta. Mom ta girgiza kai kawai, a ranta tana mamaki canjawar Sameer...... Maganarsa ce ta katse mata tunani, harya fita ya dawo baya, “mom ga maganinta nan tasha, kuma yaranan yunwa sukeji”. ‘yak'are maganar cikin marairaicewa’. Dakuwa mom tamasa, “Sameer kaci kidanku, wai yaushe kama fetsare hakane ban saniba?”. Fita yayi yana dariya, ta kirashi da sauri. Kuma dawowa yayi, tace, “kasandai Doctor tace a nemi madara, naga kuma bama kada niyyar hakan”. Gaba d'aya fara'ar fuskarsa ta d'auke, yad'an shafi girarsa da d'anyatsa d'aya yana fad'in “Mom wai wace madara ga abincinsu?, ALLAH dai ai shiya haliccesu, kuma shine zai wadatasu da abincin nasu, amma kawai sai a kama wani danna musu wata madara? dan ALLAH mu ajiye zancen madarar nan ma gefe mom”. Numfashi mom ta sauke, tasan murd'ad'd'en halin Galadima da dagewa akan ra'ayinsa, cikin kwantar da murya tace, “na yarda da maganarka, amma ita za'a tausaya mawa, shayar da yara uku bafa abune mai sauk'iba Sameer, wasuma d'ayane idan suna da fargabar shayarwa kaga duksun k'are sun lalace, koda dai sau d'ayane sai a ringa basu madarar a rana, tunda ALLAH dai baya hanaka yanda zakayi bane”. Tashi Munaya tayi tana hawaye, taje ta hau gadon kawai tayi kwanciyarta, ta kula Galadima yacika son kansa, tanaga saita tuna masa da matsayin auren nasu da alfarmar yarda ta haifa masa y'ay'an dayake neman nuna mata mulki a kansu, aidai abin shayarwar a jikinta yake, sai kuma yanda taso tayi da kayanta, dolene ta takama wannan homar tasa birki. Daga Mom har Galadima da kallo suka bita, yaja guntun tsaki yana juyawa zai fita. Mom tace, “zaka siyo d'in?”. A k'ufule yace, “zan duba”. Yay ficewarsa. shifa ya lura yarinyarnan ma batason yarannan, shin bak'in ciki take ALLAH yamasa k'yautar abinda kud'i baya sayane ko me? ALLAH zaiyi maganinta kuwa. 🤣🤣ho Galadima, uwa ta ta6a k'in d'antane🤦🏻‍♀. ★★★★★★★★★★★★ Mama Fulani dai yau tagaza gane kanta, duk yanda taso danne zuciyarta tayi murnar koda ganin idone ta kasa, shiyyasa ko zuwa wajen tarbarsu batayiba. Takuma hana dukkanin bayinta da kuyangi shiga inda take. Abinda bata saniba idon Galadima fes yake akan dukkan Wanda ya tayashi murna da samun k'yautar ALLAH, wad'anda bama su fitoba sun shiga black lists, kuma d'aya bayan d'aya saiya kartama kowa rashin m acikinsu. ★★★★★★★★★ Innaro kuwa dai saita hau tsiya dataji labarin su Munaya kowa mijinta ya d'auketa zuwa gidanta, tahau zazzaga masifa anmata ba daidaiba, babu Wanda ya kulata, dan masu zugatan suma hassada ta ishesu, basuda kuzarin taya 6era 6ari😂.. Haka tagama jarabarta takoma gida tana huci, Abba yasha dariya, danshi lamarin mahaifiyar tasu yanzu kallon rikicin tsufa kawai yake masa, inba rikicin tsufaba miye abin tada jijiyar wuya anan? Sunada damar hana yaran komawa gidajen mazajen sune?. Shikam baba k'arami ma lokacin da take jarabar zuwa yay ya ra6a ta gefenta ya fice daga gidan. Ai lamarin innaro sai ita🤣🤦🏻‍♀. ****************** A 6angaren Munubiya ma Alhmdllh, dukkan wata kulawa mama rabi'a tana tsaye akan 'yarta da jikokinta, sai zuba mata gata akeyi da k'yak'yk'yawar kulawa mai ban sha'awa. Suruka ta gari dadi alkur'an💃🏻💃🏻😘😘. ★★★★★★★★★★★★ Mom dai da k'yar suka lalla6a Munaya itada Aunty Mimi ta amince ta shayar da yaran, suna sha tana kukan zafi kuma😹, sunsan zataji zafi tunda Na farkone, ga yaran a buk'ace suke dama, amma kukan datake yawuce Na zafi kad'ai, (basusan harda haushi Galadima bane😂🤭). Mom data fahimci hakan saita fara lallashin da nuna mata muhimmanci hak'uri, su maza komai zasu iyayi akan y'ay'ansu, musamman ma shi da yake tsaka da d'okinsu yanzu, karma tabari irin wad'annam abubuwan su dameta, shima yafad'ane kawai amma zai sayo madaran”. Itadai Munaya kai kawai take d'agawa amma batace uffanba, dan tagama Sanin Galadima da halinsa Na kafiyar tsiya da dagiya akan ra'ayinsa. Bayan duk sunsha sun k'oshi Aunty Mimi tace ta kwanta ta huta kafin time d'in walimar yayi. ALLAH ya taimaketa maganin yasata barci kuwa, yaran Na gefenta suma suna nasu barcin, kowa cikinsa ya cika kenan😘. Ajiyar zuciya Aunty Mimi ta sauke tana murmushi, tace, “Mom d'an nan naki bazai canja ba dai ashe? lamarin Sameer saishi wlhy, koda bayaso susha madarar saiya fad'a da harshe mai dad'i ba fad'aba”. “Humm, kibari kawai, nifa harna fara murnar ya canja, Ashe yana nan yanda nasan kayana, yarinyar tanada hak'uri kuma wlhy, dan zama da mai halin Sameer saika daure, muma iyayen idan mun k'ureshi ba iya mana kawaici yakeba”. Aunty Mimi tayi dariya, “papi ne mai tankwarashi kobai soba ai, idan yak'i bari abasu madaran dashi kawai za'a had'ashi, komin wadatar nono shayar da yara uku ba sauk'i ne dashiba, balle ita farin Shiga ma”.. Mom tace, “hakanma shine kawai mafita ai”. *************************** *_8:15pm_* Liyafar cin abinci tafara gudana a babban d'akin taro Na masarautar gagara badau, Munaya da y'an uku duk sunsha k'yau, hakama uban gayya Baban y'an uku Galadima, duk d'insu sunci kwalliyane cikin ainahin kayan sarauta, yaranma an nad'esu cikin k'ananun alk'yabbu. (Gado kenan🥰) Kwai da kwarkwata Na gidan nan zaka sameshi a wajen, saidai marasa lafiya da wad'anda basa nan, mai martaba ma yana wajen, dan shine da Kansa ya shirya liyafar domin taya d'ansa murnar k'aruwa da kar6ar bak'uncin jarirai, yaran duk suna kusa dashi cikin d'an gadon da aka ajiyesu a ciki. Kowa anan yake zuwa ya lek'asu, yamusu addu'a. Yara sunsha addu'oi da k'yaututtuka ga iyaye da kakanni, abin zakkyau da birgewa. Ita kanta Munaya tasha nata k'yautar. ( k'yauta da bajinta kan saka zama isashe a gidan sarauta, wannan babbar al'adace tamasu mulki a masarautun k'asar hausa, shiyyasa suke ado da ita akowanne motsinsu🤩👍🏻). Tsakanin Munaya da Galadima babu uhum babu um-um, sai y'ar wullama juna harara (🤣nifa dariya suke ban), banga abin jin haushin junaba, duk da Na lura ita dama Munaya akwai haushi kaine ka jamin shan wahala😂, kaikuma Galadima k'asaita da jinkai ya sa kakasa fahimta balle kayi lallashi da kwantar dakai aji da y'an jariranka🤣. To maji dai maga yanda za'a kwashe😹. Sai 11 dai-dai taro ya tashi lafiya kowa ya kama gabansa. Shirin kwanciya Munaya tayi, suma yaran aka musu, saiga Galadima ya shigo cikin tasa shirin kwanciyar shima, mom tace, “yauwa Sameer ya za'ayi kwanciyar kenan? A falo zaka kwanta saboda tsaro ko?”. Murmushi Galadima yayi yana shafa kansa, yace, “kai Mom wai saboda tsaro”. “ALLAH kuwa Sameer, lamarinne yanada ban tsoro ai, dukda nasan ga dogarainan suma suna aikinsu, gakuma mu kammu, amma dole saida namiji a kusa, da canai shima Nuren ya dawo nan Ku had'u”. “mom kincika tsoro gaskiya, karki damu, ko ina Na sashennan akwai CCTV camera, kuma koyaya aka ta6a k'ofa ko windows akwai securitys a jiki zanji insha ALLAH”. “To shikenan Alhmdllh, ALLAH yak'ara tsaremu da tsarewarsa”. Galadima ya amsa da “amin” yana matsawa jikin gadon wajen yaran. Munaya dake saurarensu a ranta tace to ALLAH ya k'yauta, a gidanka kana zama saida tsaro inaga kafita?, amma jibarsu a awajen walimarnan kaikace kowa zuciyarsa fes take babu wani k'udiri, lamarin sarauta sai ALLAH, kaita buri tamkar ALLAH yamaka alk'awarin dawwama a cikin duniyar ne, bazaka mutuba bazaka tsufa ba, ALLAH ka iya mana da iyawarka, da ace inada dama saina cirema yaranan burin sarauta a ransu, amma ya zanyi, tarigada ta zama jininsu sai dai addu'a kawai....... Saukar numfashin dataji a gefen wuyanta ya sakata saurin dawowa daga tunanin data tafi, ta waigo da sauri sai taga Galadima. Fuska ta had'e shima yaci serious yana gyara zama. Waige-waige ta fara saitaga babu kowa a d'akin, ashe Mom ta fita. Baki ya ta6e ya nuna mata k'ofar bayi da d'an yatsa alamar mom tana ciki kenan. Cikin zaro ido ta kalli yanda yazo yawani shige mata, saitaja baya, ai da kunya dai mom ta fito ta gansu a haka wlhy. Yanda tayi d'in sai yaso bashi dariya, amma saiya had'iye, ya ciji lips nashi yana kallon yaransa, “tunanin mikikeyi ne? kinsan dai doctor tace jininki har yanzu bai gama sauka ba gaba d'aya, so ki kula, shi tunani baya kawo mafita sai matsala”. ya k'are maganar yana mik'ewa tsaye, itadai kallonsa kawai takeyi, bata ankaraba taji saukar tagwayen kisses a goshinta da kan bakinta. Idanu ta ware waje baki bud'e, ko kallonta bai sakeyiba ya fice abinsa yana murmushi. Mom data fito daga bayin ta girgiza kai kawai, don ganinda Galadima yamatane ya sakashi ficewa. Kallon Munaya tayi tace, “to rufe bakin kema”. Kunya ta kama Munaya taja bargo tarufe har fuskarta tana fad'in ka kasheni wlhy yalla6ai. A falonsa ya iske Nuren haryayi shirin barci shima, yana zaune yana shan tea da laptop a gabansa yana aiki, Galadima ya zauna yana sauke numfashi.............✍🏻 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏼_* [7/11, 1:32 PM] Aysha Galadima: *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻2⃣4⃣ .............Kallonsa Nuren yayi da y'ar dariya, “angon jego ai dole kake sauke numfashi, irin wannan aiki dakayi haka? Y'ay'a uku fa a lokaci d'aya, a fuska dai kamar bazaka iya komaib.....” Nuren bai samu k'arasawa ba saboda filon kujera d'aya daki bakinsa, wanda Galadima ya jefa masa. Dafe baki Nuren yayi yana kallonsa cikin 6ata fuska. Galadima ya cije lips yana fad'in “cigaba mana parrot ”. Nuren ya cire hannun yana kwafa da jinjina kai, alamar zan kamaka ne. Galadima ya ta6e baki yana hararsa, “yaro aini yanzu na daina halin yara, sai dai kayi da wani kuma”. Dariya Nuren ya kwashe da shi, “o manya o manya, ai yakamata ma mai martaba yay murabus yabaka kujera kawai, kainefa Wanda kafara kafa tarihi a masarautar nan, Sarki Salisu barde shi yak'in filin daga yaje ya samo sunan gagara badau, kaikuwa yak'in kashe arna kaje kasamo sarakunan gagara badau”. Girgiza kai kawai Galadima yayi yana fad'in “kai dai d'an iskane wlhy, yakamata papi sumaka aure kodan y'ay'an mutane su samu lafiya ma”. “ni wlhy dama zakaje kace amin auren daka taimakeni”. Nuren ya fad'a cikin ta6e baki da d'aga kafad'a. Murmushi Galadima yayi yana gyara zama, “ALLAH ya shiryeka to, mike tafiya akan al'amura?”. Zama Nuren ya gyara yana komawa serious, “wlhy d'an uwa abubuwannan sun cika tsauri da yawa, a duka mutanen nan uku da yarinyarnan ta fad'a da gaske fa babu SD, amma ga pictures d'in wajen mutum 30 ka nunama Mumcyn Triple's ko zata ganeshi a cikinsu. dukansu yaransu tanderu ne, Sannan nifa inaga lokaci yayi da zaka binciki Muftahu face to face, dan lamarinsa yafara birkitan tunani gaskiya”. “kafad'i gaskiya Nuren, nima kuma ina tunanin hakan shine mafita, dan ni kaina lamarin nasa yafara kaini ga dogon nazari”. “To ALLAH yasa muji alkairi”. “amin dai”. Galadima yafad'a yana mik'ewa, “nifa na shige zan kwanta, ka kwana lafiya”. “ok ALLAH ya tashemu lafiya gwauro”. Galadima yay dariya, batareda ya juyoba yace, “duk lalacewar goma dai tafi biyar albarka tuzuru”. Nuren ya kwashe da dariya, yana fad'in, “oho dai, muma mun kusa zama gomar”. ★★★★★★★★★★★★ Zumid'i ya hana Momma komai, ta k'agara Abie yafarka yasha kanu, hakama su Samha su dawo school suji babban labari. Ana cikin haka saiga Sauban tamkar an jehoshi, babu kunya ya rungume Momma yana fad'in “wayyo dad'i Momma y'ay'a uku fa wlhy, kuma dai-dai da ranar haihuwar Yaa Sam, dan yau birthday d'insa wlhy, ciwon aunty gimbiya ya mantar dashi”. Itama rungumeshi tayi cikeda farin ciki, “hakane wlhy my love, yau ina cikin farinci mai tarin yawa, tarihi ya maimaita kansa da wani sabon salo mai banmamaki”. “Wlhy nima haka Momma, kallafa pictures d'in babies d'inmu”. Dukda tagani itama bata katse masa hanzariba ta kar6a wayarsa tana kuma kallo, harda na Munubiya. Momma tace, “kai yau innarsu yazataji, jikoki 5 a lokaci d'aya, baiwar ALLAH, dama mahak'urci mawadacine, tayi kukan shekaru masu yawa ga lokacin dariya kuma yayi”. “wlhy kuwa momma, nakira Yaa Sam batajeba”. “Ai yama manta wayoyinsa a nan, kasan sun tafi hankalinsa ba kwance ba, nima da wayar Muftahu mukayi wayar”. “wayyo Momma dan ALLAH kicema Yaa Sam mutafi gobe, wlhy kamar nayi tsuntsuwa na ganni a 9ja nakeji”. Dariya Momma tayi, tarasa inda zata saka kanta dan dad'i. Motsin da Abie ya farane yasakasu maida hankali garesa, idonsa ya bud'e ahankali a kansu. ganinsu tsaye kansa sunata murmushi saiya ma Momma alama da ido wai miya faru?. Da sauri Sauban ya rungumesa yana fad'in “Albishirinka Abie d'inmu, matar Yaa Sam y'ay'a uku ta haifa”. Ba k'aramin shock bane ya kama Abie, ya kalli momma alamar da gaske?. Kanta ta jinjina masa tana murmushi. Wasu hawayen dad'ine suka gangaro a kumatunsa, fuskarsa d'auke da k'ayataccen murmushi, A hankali yaketa jero Alhmdllh. Yace, “Mafarkina na shekaru da yawa yazama gaskiya Zeenah, tabbas ubangiji shine masanin gaibu, ya ALLAH na gode maka, godiya marar yankewa balle gajiyawa”. A hankali yake maganar Amma su Momma naji saboda sun matsar da kunuwansu. Dad'i duk yakuma lullu6esu, Abie yakuma fad'in “Zeenah wannan yarinya ta zama alkairi ga Ahalinmu, ALLAH ya albarkaci rayuwarta da abinda ta Haifa daku ma gaba d'aya”. Sauban da Momma suka amsa da amin. Yace a kira masa Galadima. A time d'in sunta neman Number Mom amma bata wuceba saboda Network, hakama ta Nuren da Muftahu, daga k'arshe dai sun hak'ura ne sai wani lokacin a sake gwadawa. Yau dai kam har doctor's d'in Abie sun shaida yana cikin farinciki, dan jikinsa ma ya nuna haka, k'arfin muryarsa ya k'aru, hakama bugun zuciyarsa dawasu yankunan halittun jiki dake bama d'an adam garkuwa, sun tabbatar a kowanne lokaci ALLAH zai iya gwada ikonsa ga wannan bawa, bayan tsawon shekaru daya d'auka a kwance sai an juyashi. Wannan albishir ya k'ara yalwata farin cikin wannan ahali, saima dasu Samha suka iso, duk sun rikice da ihun murna, yau d'in ta dabance a ransu. Isowarsu ce ta tunama Galadima da ranar haihuwarsa dai-dai da haihuwar yaransa, kuma dai-dai da haihuwar su Munaya ma😳😜. Wannan abin al'ajab da yawa yake, ita kanta munaya sai lokacin ta tuna, wayar Ayusher ta kar6a ta kira Munubiya tana mata tuni da ranar haihuwarsu. dad'i ya kama Munubiya ma, dan itama ta shafa'a, sai murna kan murna ta k'aru🤸🏻‍♀. ************************** Uban gayya dai Galadima da k'yar barci 6arawo yake sace sa a kowace rana, daya rimtse ido 'y'ay'an sa kawai yake hangowa, badan kar aga rashin hak'urinsa ba shikam da dasu zai ringa kwana. O baban zumud'i😘😘😽. A 6angaren yalla6iya ma hakane takan kasance, da taga laraba tayi barci dash Ayusher da Samha, (dayake itace take kwana dasu) saita tashi ta dinga d'aukarsu d'ai-d'ai tana runguma da musu addu'oi, jitake kamar ta had'iye kayanta ta huta kawai, takan dad'e tana Abu d'aya kafin barci yaci k'arfinta take kwantawa. Tosu yalla6iya anaso ana kaiwa kasuwa😂😜. ************************* Fad'a muku yanda abubuwa suka cigaba da kasance ga y'an barka ai 6ata lokacine ma, dangin Munaya ma sun taka rawar gani, Ayusher ma dai ta dawo nan zata zauna har ayi suna, hakama madam Innaro Galadima da kansa yaje ya kwasota🤣😜, aiko baki har kunne. Gaskiya fans sannunku da k'ok'ari, irin wannan tururwa haka, lallai kunma Galadima halacci shida yalla6iya, ALLAH ya saka muku da alkairi dai my sweetness🥰🥰🥰😘😘😘😘❤🤝🏻. Dole Galadima ya nemi waya da sim card ya lalubo su Abie da Momma d'insa da jakadiya dabasu samu zuwaba, suna shan hira a kullum shida su Abie ta video call, ga jarirai aita jera musu sunata shan kallo abin birgewa, Abie jiyake kamar yay tsuntsuwa ya gansa a 9ja, tsakanin nan yana cike da kewar k'asarsa ta haihuwa, yana fatan yakuma takata ko sau d'ayane kafin yabar duniya. “Insha ALLAH zaka taka da yawa Abie😭”. Mu tafi ran suna kawai😨⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀. Abubuwa da yawa sun faru a kwanakin bakwai d'innan, sai dai Alhmdllh bamasu tayar da hankali bane, dan jinjirai suna cikin k'oshin lafiya da kariyar ubangiji. Samha dai konan dacan bata matsawa, duk wani motsinta nakan yaranan, tazama bodyguard d'insu itada Ayusher da hajiya innaro, dan itamafa ta kafa ta tsare🤣. Mama Fulani dai ta danne zuciyarta tazo har sashen Galadima taga babies, harma suka samu k'yauta mai tsoka daga gareta. Ana gobe suna masarautar gagara badaufa tayi dank'am da jama'a, dan bikin suna na ban mamaki Sarki ya shirya, abin ba'a cewa komai. Inno ma dai wannan karon ba'a barta a baya ba, tazo masarautar su sunan tatta6a kunnenta, kuma 6angaren mama Fulani ta sauka😳😜. Koba komai zata kafa zata tsare, takuma raka ta jira🤸🏻‍♀😂 mana ga Mama Fulani. Harun da baya k'asar yayi tafiya a fannin aikinsa yau ya diro a Daren suna cikin masarautar, dama tun yana can labari yagama Isar masa Galadima ya samu y'an uku, Muftahu da kansa ya kirashi ya Sanar masa haihuwar, Yakuma tura masa hoton babies😽🤥 ***************** Wajen 8pm Galadima suka dawo daga masallaci sallar isha'i, shikad'ai ya shige falonsa, dan yana son magana da Munaya, gaba d'aya yinin yau tun safe daya Shiga bai samu komawa wajensu ba saboda hidimomi sun masa yawa. Ayusher ya kira, dan itama Munaya batazo da waya ba, lokacin da su Sauban zasu taho kuma basusan inda ta saka layinta Na Nigeria ba, sai sukaga babu amfanin d'akko wayarma. d'agawa Ayusher tayi, Galadima yace ta bama Munaya. Murya k'asa-k'asa tace bata da lafiya. Tashi yay daga kwanciyar da yayi, yace, “ciwon cikin ne dai?”. “eh shine wlhy Yaa Galadima ”. Dukda kunyar shiga mutanen yake dole ya mik'e ya fita, sashen nasu kam Alhmdllh da yawan jama'a babu laifi, ga yawan bayi da suka k'aru saboda inno da tawagarta, dukda ba'anan ta sauka ba. Tunda ya fito suketa gaisuwa da jama'a, wad'anda ma basu sanshiba yau sun gansa, musamman wasu a y'an uwan Munaya. cirko-cirko ya iskesu tsaye, Munaya Na kwance a gado ta cure waje d'aya da alama tanajin ciwon sosai, Aunty Mimi nata faman jijjiga yaron d'aya dake kuka. Duk kallonsa sukayi, cikin damuwa yace, “ciwon cikinne?”. Da eh suka amsa masa, ya taka zuwa gaban gadon ya zauna kusada ita, har zai ta6ata Mom tamasa nuni da a'a ya barta. dakatawa yayi shima ya zuba mata ido cikin tausayawa, gaba d'aya fita hayyacinta take idan cikinnan yana ciwo, kuma saida ta kwana biyu da haihuwa sanann yafara. ya tsira mata idanu ganin yanda take zufa, dukda garin akwai sanyin ruwan da akayi da yammaci. Yakai tsawon mintuna 30 a zaune kafin ya lafa mata, ahankali tafara gyara kwanciyarta tana mik'ewa sosai, da Galadima suka fara had'a ido, yace, “sannu”. Kanta ta d'aga masa cikin murmushin k'arfin hali, suma duk sukai mata sannu sauran. Nanma ta amsa cikin d'aga kai. Maganin da laraba ta tace a Kofi ta mik'o mata, Na gargajiyane, kar6a tayi ta shanye tana yamushe fuska, ta mik'a mata kofin sannan ta zauna sosai. Tausayinta ya kama Galadima, iyaye mata nashan wahala akan y'ay'a, ALLAH ne kawai zai biyasu. Ganin ta dawo dai-dai duk sai suka fita suka basu waje, bayan Aunty Mimi ta d'ora masa babyn a cinyarsa. Sannu ya kuma mata yana gyarama yaron kwanciya, murya a hankali tace, “ya daina ai, amma wlhy ciwon cikinnan yamafi haihuwar zafi”. ‘ta k'are maganar idonta cike da kwalla’. Tausayi ta kuma bashi, ya matso kusada ita sosai yana ruk'o hannunta, yace, “insha ALLAH Akash zai zo miki da Magani zuwa gobe, zai daina gaba d'aya ”. Kanta kawai ta d'aga masa amma batace komaiba. Kukan da macen tayi yasakasu kallonta su duka, nuni yamata ta d'auketa. Batayi musuba ta d'auketa ta saka a acinya, kamar jira suma sauran suka farka harna hannunsa, kai Munaya ta dafe tana fad'in “ni jikar fharuk ku shikenan da d'aya ya tashi kowa saiya tashi”. Murmushi yayi, “to basu birgeki ba ma, sunyo gadonku ne keda Munubiya, Ku ba haka kukayiba?”.. “a'a mukam ba irin wannan mukayiba yalla6ai”. “humm, ai inna ta sanarmin komai yarinya”. Da mamaki Munaya ta waro masa ido, ya d'aga mata gira yana kashe ido d'aya. 'Dauke idonta tayi cikeda basarwa. Shima saiya mik'e tsaye d'auke da yaron d'aya, ya kalli agogon dake a hannunsa sannan ya kalleta “inason ganinki”. daga haka ya sunkuya ya d'auki macen ya juya zai fita. “wai ina?”. ta fad'a da saurin dan karya fice. Juyowa yayi ya d'an kalleta, kamar bazaiyi magana ba sai kuma yace, “sashena”. bai jira cewarta ba yay ficewarsa. Kanta ta dafe tana sauke ajiyar zuciya, shi bama ya ganin gida cike da mutane, fitinar yalla6ai yawane da ita wlhy. batayi yunk'urin binsa ba, saima zaman shayar da Wanda ya bari tayi, harsu Samha suka dawo ganin ya fita. Shikam yanacan kwance a gado ya d'ora yaran saman cikinsa yana shafa bayansu, yayinda zuciyarsa ta tafi wata nahiyar tunani, ganin lokaci yaja bata zoba ya kalli a gogon hannunsa, shidai bazai kuma kiranta akan tazo ba, idan ta gadama kartazo. Mom data lura babu sauran yaran ta tambaya, cikin kunya Munaya tace, “suna wajensa”. Banbancin babba da yaro saurin fahimta, mom ta fahimci d'an nata yana buk'atar ke6ewa da matarsa, shiyyasa ya d'auki abinda dole tabishi inda yake ta kar6o.. Tace, “to aiko jeki ki kar6osu, dan shirin barci zan musu nima Na kwanta, gobe ba zama za'a samuba hidimomi zasuyi yawa”. Kamar Munaya tai ihu haka taji, to a aiki Ayusher da Samha su kar6osu mana, ai ba dole sai itaba, amma babu yan da ta iya, dan bazata iya sa6a umarnin Mom ba dai. Dogon hijjab ta d'auka ta zumbula, Mom kamar tayi dariya, a ranta tace, Munaya shi namiji ai ba'a hanashi yanda yaso, balle naku na yanzu da suke a fetsare ma. Harzata fice mom tace, “shima zoki d'aukesa”.. Ta kalli mom d'in tana fad'in “mom aikuma zasuyi yawa wajen d'akkowa”. “eh d'auka, basai ya tayaki ku d'akko ba”. Babu yanda Munaya ta iya dole shima ta dawo ta d'aukeshi, sai wani k'yallo idanu yakeyi Lamar yasan mi akeyi. Babu kowa a afalon, harma television an kashe, babu yanda ta iya dole ta nufi bedroom d'in, saida tayi sallama yabata izinin shiga sannan ta shiga. Harta zauna idonsa a kanta itada babyn hannunta, saiyaga ta k'ara masa k'yau ma da girma. Yace, “kin gama jan ajin? ai saki bari sai randa nazo tad'i ki jamin bawai yanzu ba”. Munaya ta ciza lips d'inta kawai batare da ta tanka masaba, Yaran ya kwantar gaba d'aya, sannan yatashi zaune yana fad'in “taso”. “intaso kuma, ba magana kace zamuyi ba? please ka fad'a a haka”. ta fad'a kamar zatayi kuka, (Dan hirar innaro da laraba ta tuna da sukace jiya wata yarinya sati biyu da haihuwa ta yarda da mijin saiga ciki ya fito yaro Na wata uku, ciki wata biyu da sati biyu🤣, itama fa yanzu kaffa-kaffa zatakeyi da Galadima, inma baka badaba sai'a saka maka k'arfi🤭😂). Tsaf Galadima ya fahimceta, dan haka yay wani miskilin murmushi yana fad'in “oh kina min bak'in cikin sake ajiye abin cikin kwan ne?”. Sosai Munaya ta waro idanu, a firgice tace, “ban ganeba?”. “Zaki gane lokacin da kika zo hannuna”. Ta yunk'ura da sauri ta mik'e, ita tama manta da yaro ajikinta, ALLAH dai ya kiyaye tai saurin tarboshi, Galadima ma dirgowa yay daga gadon, saidai kawai ta gansa kusada ita. Rungume yaron tayi tana sauke ajiyar zuciya, gashi mai kamar mara lafiyarne. Shima Galadima had'ata yay itada yaron ya rungume, ganin haka saita mik'a masa shi ita ta janye jikinta. hannunta ya rik'o ya maidota, daga k'arshema janta yay zuwa gado, ya zaunar da ita shima ya zauna, fuskarsa babu walwala yace “Munaya badai haka kikemin ganganci da yaraba?”. A tsorace ta girgiza masa kai idonta Na cika da kwalla, “wlhy yalla6ai a'a, yanzu ma Na shafa'ane”. Taune lips d'insa yay tayi yana kallonta, haushima ya hanashi samo amsar bata, jima yake kamar ya maketa, anya zaibar yarinyarnan zuwa wani wankan banza can, taje tamasa wasarere da yara?. Yanda ya koma duk saitaji babu dad'i, shi yaronma bafa kuka yakeba, yad'an dai firgita ne kawai yay kamar zai shid'e. Saida ya gama cikarsa da batsewa sannan yay kwafa, ita shima abin yabata mamaki, shikenan yanzu y'ay'ansa kawai ya Sani, mutum bazai ta6a iya kuskure ba a Kansu saiya hauma mutane bala'i, shin ya fita sonsune itada tasha wahalar d'aukar ciki da haihuwa?. Kwantar da yaron yay yanata wani had'e fuska, itama tasha kunu ta shareshi. K'aton akwatin dake gefensu ya matso dashi, kayane Na jinjirai masu k'yau da birgewa, Wanda kallo d'aya zaka musu Kasan Na musamman ne, kala-kala ne amma kowanne set uku ne, abinda ya banbanta su wannan Na macene wannan Na mazanne. kowanne da takalma abindai masha ALLAH. tsaf Munaya ta gama gani, ta kallesa tana fad'in “Sunyi k'yau”. Yana basarwan nan tasa yace, “wanda zakuyi amfani dashi gobe ne, idan akwai abinda bai yiba saiki fad'a da safe a nemoshi, ga naki nan kema”. ‘yay maganar yana nuna mata d'ayan akwatin’. Jawowa tayi ta bud'e, duk an d'inka kayan, kayane masu tsadar gaske Na mace y'ar gata, bama tasan ta rungumeshi ba Dan dad'i, sai jero masa godiya da addu'oin fatan alkairi takeyi. Shima tuni ya manta da fushin ya rungume kayarsa yana murmushi. cikin kunnenta yace, “kinfi k'arfin komai a wajena friend dan kin gamawa Muhammad Sameer komai”. Munaya ta murmusa tana d'an dukan k'irjinsa, tace, “kana shamin k'amshin ne nagama maka komai?”. Hannunta ya rik'e yana murmushi, yamatso da fuskarsa gab da tata, murya k'asa-k'asa yace, “ke d'ince Zuma ce...... ” Harar data dalla masa ta sakashi fasa k'arasawa ya wani basar yana kashe mata ido d'aya, “dad'ina dake akwai mazurai, gaki babu k'arfi ga tsoron tsiya”. Munaya tayi dariya, “aka gaya maka banida k'arfi? kabari nakuma samun lafiya sai a gwada kwanji”. Wata dariyar mugunta Galadima yayi yace really?”. “yes” ta fad'a cikeda karsashinta. Ya mik'a mata d'an yatsansa alamar su k'ula. Babu musu tabada nata itama suka k'ula. Murmushi yaytayi saboda muguntar dayasan yana shiryawa, wadda ita Munaya bata fahimci komaiba a ciki saboda wauta.🤣 *_Washe gari_* Ta kasance safiyar suna, inda aka rad'a sunan yara bayan sallar Asubahi, *_Abdurrahman, Abdurraheem, and Amaturrahman_* masha ALLAH Babies ALLAH ya raya Ku akan sunnah da tafarkin addinin Islam. Yara sunsha Addu'oin fatan alkairi sosai, tun kuma a safiyar shagalin suna ya fara, dan kowa yana cikin walwala da farinciki, mai jego munaya ansha k'yau itada babies har an gaji, kamar ka sacesu ka gudu, hotuna dai suna shansu kala-kala a yau d'inan, Su Momma ma da basa kusa anata sambad'a musu, dan duk wani motsin da za'ayi Sauban da Samha basa gajiya da tura musu, sai sukaji tamkarma suna nan suma, saboda kallon komai suke tamkar live, farin ciki da walwala sun yalwatu a zuciyar Abie, bakinsa yakasa rufuwa dan tsabar nishad'i daya tsinci Kansa yau aciki. Hummm babbar magana, kayan barka dai sun iso, fans yaufa nasha kallo, kaga Inda akeyi don ALLAH, ta bakin Munaya tace INA zasu da wad'annan kaya haka, lamarin tamkar fariyya, gashi kowanne sashe sai kawo nasu sukeyi, gidan sarauta manya, babu Wanda zaiso aga kasawarsa, ballema wannan kana k'inyi za'a CE bak'inciki kakeyi, shiyasa mama Fulani aka ware aka zuba kayan barka Na gani Na fad'a, daga gidansu Munaya ma su inna sun taka rawar gani dai-dai k'arfinsu, daga ita har Munubiya komai iri d'aya aka musu, kayan babies ne kawai Na munaya yafi Na munu saboda su su uku ne ita kuma Nata biyu. Nanfa y'an gidan suka Shiga k'us-k'us d'in gulmar Ina inna ta samu kud'in yin wannan hidima haka? dansu basuyi zaton hakanba, musamman da abin yazo da yawa ma, itadai inna ma ko kallo basu isheta ba, hidimar gabanta da farincikin datake cikine a gabanta, bakinta yakasa rufuwa saboda farinciki da godiyar ALLAH mai sassauya al'amura a yanda yaso a kuma lokacin da yaso, idan ALLAH ya jarabceka karkayi bak'in ciki, hak'urinka zai iya zama sauyin alkairi a gareka, inama iyayensu Nada rai suga wannan k'yak'yk'yawar rana, ta share hawayenta tana murmushin farin ciki, sannan ta kira y'ar uwarta a waya suka cigaba da tattaunawa. ***** K'arfe uku da rabi kuma za'a gudanar da gagarumar walima da aka kama babban hall Na musamman. A wannan rana yara dai har fada aka kaisu sukayo gaisuwa da hotuna da mai martaba da gayyar y'an uwa da abokan arzik'i, su Harun dai sune gaba-gaba, uban gayya kuwa Muhammad Sameer Saifudden Galadima Baban y'an uku😂 ai ba'a cewa komai, koma ganinsa ba'ayi saboda tsabar shiga hidima, wannan suna ko bikidai iyaka kenan. Nasan kuma fans duk kunyi shirin wannan walimar baje dad'i😋😋. Nifa buhu Na tanada walle😆, saura kuce Bily tacika zari da son banza kuma🙄, har y'an anguwarmu saina kar6oma gifts d'insu😜😂🤸🏻‍♀. **************** Alhmdllh yaran Mununbiya ma an rad'a musu suna bayan sallar Asubahi, Namijin *_Aminudeen macen Ameenatu_* ALLAH ya raya wad'annan yara masu albarka😘😘🥰. Yau daikam farin cikin da Abba da innarsu suke ciki 6ata lokacine ma, kai da dukkan masoyansu irinmu, masu bak'inciki kam Ku k'ara himma, hassada ga mai rabo takice😏🤷🏻‍♀. Kowa nabashi dama ya k'iyastama zuciyarsa yanda bidirin suna yake guna, dan Alk'alamin Bily yau yayi k'ank'anta wajen wallafowa, sai mugama Na wannan satin bikin sunan bai k'areba😁.................✍🏻 Kuyi manage da wannan yau inada uzuri🤦🏻‍♀. ☺my Guy's a kafta kawai danjin yanda bikin suna zai gudana gobe idan ALLAH ya kaimu, kowa dai ya k'ure adaka dan karfa a kawo mana raini😕, kunsan dai halin mama Fulani, tana iya hanawa abarmu shiga😩🥺. *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻2⃣5⃣ ................Aunty Salamah da kanta tazo yima Munaya kwalliyar zuwa wajen walima, saida tafara biyawa tama Munubiya sannan ta wuto nan, ta iske su duk a damuwar kukan da Abdurrahman ketayi, sai faman jijjigarsa akeyi amma yaro yak'i yin shiru, an basa nono yak'i kar6a, innro ta kar6esa ta hura masa kunne, ya kuma k'yak'yacewa da sabon kuka yana dunk'ulewa waje d'aya, tace “inaga kunnensa ke ciwo yaronnan”. Munaya Na gefe zaune ta zuba tagumi kawai tana kallonsu, ita kad'ai tasan suyar da ranta ke mata, gashi Galadima baisan wainar da ake toyawa ba, yanacan tareda su Akash da suka iso yanzu. Innaro ta dungureta, d'ago idanu tayi ta kalleta, ta mik'a mata Abdurrahman daketa sauke ajiyar zuciya, “d'iga masa ruwan nono kad'an acikin kunnen insha ALLAH idan aka dace zai daina”. Kar6arsa tayi, ta d'ora kan cinyarta, dukma ta rikice ta rasa yanda zatayi, saboda sai mimmik'ewa yakeyi azaba na cinsa, ga Amaturrahman itada Abdurraheem suma sun d'akko nasu kukan, laraba ta rik'e matashi ta samu ta d'iga masa, ruwan nonon Na shiga yakuma mimmik'ewa yana kwalla ihun sabon kuka. Saiga hawaye a na zuba a idon Munaya, tasaka hannu ta toshe kunen ta kozataji sassaucin jin kukan nasu dake d'aga hankalinta. Tausayinta saiya kama laraba, tasan indai wannan ne yanzu ma aka fara, yaro d'aya ma ya kake k'arewa balle yara uku. Cikin amincin ubangiji kuma duk sai sukayi shiru, innaro da laraba sunata faman jijjiga, itama Aunty salamah ta kar6i Na hannun munaya, tun suna ajiyar zuciya har barci ya kwashesu. Munaya ta shige bayi tana share ragowar hawayenta. Baki innaro ta ta6e tana fad'in “lallai aiki yasamu mata, yo indai kukane yanzu ma kika fara”. Daga Aunty salamah har laraba dai babu Wanda ya tanka. Munaya kuwa data jiyota daga bayi tace “aniyarki ta biki, mai mugun fata kawai”. Wanka tayo ta fito, Aunty salama kawai ta tarar a d'akin sai bayi biyu dake morping, suka durk'ushe k'asa suna gaida Munaya. Hannu ta d'aga musu kawai dan batasonyin magana, har yanzu raunin tausayin Abdurrahman baibarta ba. ta kallesu duk suna kwance kan gado barci ya d'aukesu, yayinda Aunty Salamah ke zaune kan sofa tana warema yaran kayan da za'a saka musu. Ta d'ago ido tana kallon Munaya, “haba auta kuka kikayi da gaske? Please kidaina musu kuka, ba'ason uwa Na zubarma d'a hawaye dukda wannan Na tausayine kinji”. Munaya ta had'iye abinda yamata tsaye a mak'oshi tana gyad'ama Aunty salamah kai. Saida Aunty salamah ta gama ware kayane sannan ta taso suka fara kwalliyar, anutse sukeyin komai, dan da sauran time, hakama Munubiya a nutse aka mata tata, anama Munaya tana kallon hotunan Munubiya, taji dad'in yanda y'ar uwarta tasha k'yau, dukda ma batakai ga saka kayaba. ★★★★★★★★★★★ Muftahu nata kai kawo a tsakar d'akinsa, tunanin tawace hanya zai fargar da Galadima kawai yakeyi, dan dolene saida hannunsa zaiyi wannan aikin, saboda had'arinsa, gudun kar reshe ya juye da mujiya, sannan aikin yana buk'atar takune da sirri. Fitowa yay yanufi can cikin k'aton lambun masarautar indasu Galadima suke tareda mafi yawan y'ammata da samarin masarautar. Wasu sunata hirarsu in group, wasuko hirar tasu ta masoya ce, Muftahu ya k'araso inda su Galadima suke, sun baza babbar darduma anata hira, Bama zaka ta6a Sanin suna lambun ba saboda sunacan ciki nesa da sauran yaran. Galadima na zaune a gefe cikin kujera, ya d'ora k'afafunsa a wata kujerar, sanye yake da farar shadda d'inkin boda, fuskarnan babu walwala ko kad'an, gaba d'ayan hankalinsa yanaga system d'in daya d'ora bisa cinya yana latsawa. Muftahu ya mimmik'a musu hannu sukayi musaba cikin fara'a. Amma tsakaninsa da Harun ba hakan baneba, kowa murmushi mai cikeda ma'anoni yay ma d'an uwansa, kafin su saki hannun juna. Muftahu ya matso kusada galadima shima ya bashi hannu sukayi musabaha, k'aramar takardar dake mak'ale a hannunsa ya sakarma galadima a hannu. Kallonsa galadima yayi, sai yay masa murmushi yana signal da ido alamar ya duba. Galadima bai ce komaiba ya cigaba da abinda yake ya basar da takardar. Muftahu kuma ya koma cikin su Harun aka d'ora hira, tamkar babu abinda ke damunsa. Galadima baibi takan takardar da Muftahu ya basaba har tsawon wasu adadin mintuna, sannan ya bud'e ya duba. _Ranka ya dad'e ina buk'atar muyi magana kafin a zauna wajen walima, magana mai muhimmanci please._ Iya abinda ke jikin takardar kenan. Galadima ya d'an ja eyeglasses d'insa k'asan ido ya kalli Muftahu, cije lips nashi yayi yana janye idonsa. Ya sauke k'afafunsa yana d'ora laptop d'in saman kujerar, ya d'auki ruwan gabansa yana sha da maida hankali garesu. jin hirar tasu ta y'ammata ce sai ya zuba musu ido kawai bai saka bakiba, dan shi dama ba'a wannan hirar dashi tun can da, suma duk sunsan haka, shiyyasa ko suna shirmensu basa sakoshi. Ganin zasu saka masa cinwon kai saboda hayaniyarsu Na Neman yin yawa saiya mik'e d'auke da Laptop d'insa. Duk kallonsa sukayi, Zayyan yace, “ina zuwa daddyn Triple's?”. K'aramin tsaki yaja, da k'yar ya bud'e baki yace, “zaku samin ciwon kaine, zanje nad'an huta kafin time yayi”. ya k'are maganar da kallon agogon hannunsa. Matawalle yay murmushi yana salute nashi, shima murmushin ya masa yana kaimasa rankwashi, ya kauce gefe yana murmushi, (dayake shima bai cika hayaniya ba). Wuce warsa yay cikin takun nan nasa Na izza da k'asaita, da sauri wasu yaran masarautar dasuka had'a tasu dabar agefe biyu aciki suka taso suka k'ar6i laptop d'in hannunsa saboda girmamawa, ya mik'a musu yana murmushi, yana gaba suna binsa a baya, sai zuba masa surutu suke akan shagalin daza'a sha yau, shidai murmushi kawai yake musu babu magana, basu damuba, dan kowa yasan halin galadima a masarautar nan, haihuwar nan ma wasu da yawa zasu iya cewa sunga hak'oransa a waje. duk inda suka gitta ana kwasar gaisuwa, bayi kam zubewa suke domin girmamawa a garesa. Har sashensa suka masa rakkiya, sarkin mota ya kar6a laptop d'in ya k'arasa masa da ita zuwa ciki.. Baibi ta ainahin k'ofar da zata kaishi babban falonsu ba, saiyabi wata k'aramar k'ofa da kai tsaye nasa sashen zai shige basai mata y'an suna sun gansa ba. A falo ya iske Sauban kwance yana barci, da alama yagama yawonsa ne gajiya ta makesa, da kallo Galadima ya bisa, amma dan ya tabbatar da lafiyarsa saiya d'ora yatsunsa biyu a wuyan Sauban d'in, babu zafi, ya maida goshinsa saiyaji zafi sosai, Galadima ya girgiza kai, yasan dama ba lafiyace zata saka Sauban barci a irin wannan lokacin ba ana wannan hidimar. Bai tasheshi ba ya shige cikin bedroom, zama yay a bakin gadon yana cire bottom d'in rigar guda uku, ya huro isaka daga bakinsa yana zamewa ya kwanta batareda ya cire rigarba, zuciyarsa tana ta jujjuya mi Muftahu yake nufi ne? wace magana zasu tattauna?. waya ya jawo da nufin kiransa, sai kuma ya fasa, jefar da wayar yayi yamik'e yana ida cire kayan gaba d'aya. ya shige wanka. ya ja adadin wasu mintuna masu tsayi kafin ya fito sanye da bathrobe fara sol, sai k'aramin towel a hannunsa yana goge fuskarsa zuwa wuyansa. Yana tsaye gaban mirror zai fara shafa mai ya jiyo ana knocking d'in k'ofar falonsa, Computer d'in daya ajiye wadda yake kallon kowane 6angare na sashen daga cctvs cameras d'in daya zagaye ko ina, tun zuwan dayayi Na k'arshe ya saka akayi masa wannan aikin, sannan ya d'auki mataki akan waccan cctv d'in da Munaya tamasa hannunka mai sanda da ita. Sarkin k'ofa ya gani, sai kuma Muftahu daga can waje alamar yana jiran iso ne. Guntun tsaki Galadima yayi, ya fito zuwa falo, Sauban dake barci ko motsi baiyiba balle yasan ana knocking d'in. yana daga tsaye yabama sarkin k'ofa izinin shigowa. Cikin girmamawa yace, “ranka yadad'e yalla6ai Muftahu ne ke Neman iso”. Da hannu Galadima ya masa nuni da ya shigo. Sarkin k'ofa ya amsa da to sannan ya fice. Komawa Galadima yay ciki yacigaba da shafa mansa, saida ya gama tsaf sannan ya zira jallabiya Brown ya fito. A falo ya iske Muftahu zaune yana control d'in television da remote. Galadima ya zauna a kujera mai zaman mutum d'aya, sai wani d'aure fuska yake. Muftahu bai wani damuba, dan yariga ya saba da wannan ai. Kallonsa Galadima yayi cikin lumshe ido yana fad'in “Mike faruwane?”. Ajiye remote d'in Muftahu yayi, ya kalli Sauban dake barci. d'an ta6e baki Galadima yayi, yace, “karka damu, kayi maganarka kai tsaye kawai”. Cikin jinjina kai Muftahu yace, “Ok, babu abinda ke faruwa saidai shirin faruwar kam, Ranka ya dad'e bamuda isashen lokacin wata magana mai tsawo yanzu, saidai ga wannan takardar ka duba, so yanzu wannan ne akan ga6a, shine yakamata mu d'au mataki akansa, daga baya komi kenan namaka alk'awarin warware makashi, fatana dai ka fahimci wannan d'in saboda had'arinsa”. Kar6ar takardar Galadima yayi, ya d'auki medical glasses d'insa daya ajiye a teble glass d'in dake gefen haggunsa ya saka, duba takardar yay a tsanake, cikin wani yanayi dake nuna tsantsar tashin hanki yace, “Muftahu wannan maganar gaskiya ce kokuwa? karkamin wasa da hankali a wannan karon dan bazan d'aga maka k'afa ba a wannan ga6ar alwashi nane”. Murmushi Muftahu yayi, ya sauke ajiyar zuciya yana fad'in “Nabaka wannan damar, inhar kayi gamo da sa6anin hakan karka barni da numfashi ranka ya dad'e”. Wani shegen Murmushi Galadima yayi, yamik'e d'auke da takardar ya koma bedroom batare da kuma kallon Muftahu ba. Tausayin Galadima ya kama Muftahu, mik'ewa yay shima ya fice. Jefar da takardar Galadima yayi akan gado yana taune lips nashi tamkar zai huhhudashi, wata irin suya zuciyarsa ke masa, lallai dolene ya jinjinama Munaya, dan ta taka rawa wajen shagaltar dashi wanene shi? minene burinsa?, ganin tunani bazai masaba yatashi jikinsa Na rawa yafara wasu had'e-had'en abubuwa, waya ya d'auka ya kira Ayusher, ta d'aga cikin hanzari tana mik'ama Munaya dake shayar da Amaturrahman data tashi daga barci tana kuka. Kallonta tayi da mamaki tace, “wace Ayusher?.......”. Galadima ya katseta da fad'in “ki kawomin kayanda su Abdurraheem zasu saka”. iyakar maganar da yay kenan ya yanke wayar yana cigaba da latse-latse, zuwa can kuma ya ajiye ya mik'e yana cire jallabiyar jikinsa. Baki sake Munaya tabi wayar da kallo, mike damun galadima haka? Muryarshi irin wadda tasan asalin galadima ce, hakan na nufin akwai matsala kenan? to mine zaiyi da kayan da yara zasu saka?. batada mai bata wad'an nan amsoshin dan haka ta mike tana ajiye Amaturrahman d'in, aiko ta fashe da kuka an cireta bata k'oshiba, tsaki Munaya tayi tana fad'in “ai saikiyi tayi, ku matsala ubanku matsala mutum yarasa wazai kama. Ayusher da Aunty Salamah suka kalli juna suna gumtse dariya. Gyale taja ta lullu6a, dama tasaka doguwar rigar matirial kafin dai time ya k'arasa. ganin zata wuce yarinya na kuka Auntu Salamah tace, “dawo ki d'auketa mana, idan kinje can saiki bata nonon”. Tamkar Munaya zata saka kuka haka ta dawo ta kwashi Amaturrahman ta fice tana k'unk'uni. A falo ta iske Sauban Na barci, wucewa tayi cikin bedroom d'in kanta tsaye, amma saida tayi sallama ya bata izinin shiga. Tun da ta shigo taga yanayin da yake sai gabanta ya dad'i, tamkar kazar da kwai ya fashema a ciki ta mik'a masa ledar data zubo kayan sannan ta zauna a kunyace saboda yanayin da yake babu kaya. Ba tare da ya kalleta ba ya hau Fiddo kayan, ya zubesu saman gado yana d'aukar hotonsu a waya, yay latse-latse nawasu mintuna kafin yasaka wayar a kunne. “Saleem ka dubamin kalar kayannan, koda basu kaisu tsadaba, yanzunan kataho ka kawominsu”. Bataji mi Saleem yafad'a daga canba. Muryarta a raunane tace, “yalla6ai mike faruwa wai?”. Jajayen idanunsa ya d'ago ya kalleta, k'ala baice mataba ya mik'e ya d'akko wani k'aramin box ya dawo ya zauna, ita duk saima kunya takuma kamata, saboda dagashi sai boxer, amma taga ko a kwalar rigarsa bai damuba, hidimar gabansa kawai yakeyi. Kwantar da Amaturrahman tayi kusa dashi ta tashi zuwa wardrobe d'insa, k'aramar t-shirt ta d'akko, tazo ta mik'a masa. Ya d'ago ido yana zuba mata harara, dukda ta tsorata saita daure tace, “please mana yalla6ai”. tayi maganar muryarta a raunane. Saida yayi k'aramin tsaki kafin ya amsa ya saka, wani abu da batasan minene ba taga yana mak'alawa jikin kayan yaran, saida yagama tsaf sannan ya maidasu a ledar, kallon Amaturrahman dake k'yalla y'an idanu zata fara k'aramin kuka yayi, ya shafa kumatunta batare da ya d'auketa ba. Laptop d'in sa ya jawo ya saka eye glasses d'insa, ya kalli Munaya yamata alama da ido akan tazo. Babu musu ta taso zuwa kusa dashi ta zauna. Laptop d'in ya d'ora mata akan cinya yace, “wanene SD a cikin su?”. Nutsuwa Munaya tayi tana kallon hotunan, cikin waro ido tace, “kai ga Fu'ad ai”. Da mamaki Galadima yace, “Fu'ad!?”. “eh wlhy yalla6ai, Wanda ya kaimu birnin gayu plaza ranar da abunnan ya faru”. Kar6a laptop d'in Galadima yayi yakuma kallon hoton da k'yau yana taunar lips, kuma mik'a mata yayi batare da yace komaiba. itama batace dashiba tacigaba da bin hotunan da kallo sannu a hankali. Harta kai k'arshensu babu SD. ta kalleshi cikin damuwa, “yalla6ai babushi fa anan gaskiya”. Kansa ya jinjina mata yana kar6ar laptop d'in, cigaba yay da danne danne, itadai Munaya tana kallonsa. Kuma d'agowa yay ya kalli Munaya, “duba annan kuma fa”. Kallon hotunan ta shigayi, canko saiga hoton SD, tace, “Alhmdllh gashi anan”. Kallon hoton Galadima yayi, da mamaki yace, “kinsan wanene wannan kuwa?”. “Ah! yalla6ai SD ne mana”. “Munaya kin tabbata wannan ne kika gani a wajen Abba?”. “Wlhy shine yalla6ai, bazan ta6a manta fuskarsa ba ai komai dad'ewa. balle acikin abinda bai rufa 2years ba, amma kasanshi ne?”. Bai iya cemata komaiba, sai zuciyarsa dake wani irin bugawa da sauri-sauri kamar zata fad'o, mamaki ya hanashi motsin kirkirma, Alhaji Shehu Darma shine SD kenan, babban Amini kuma d'an uwa ga Mahaifin su Samha, innalillahi, ya abubuwa keneman koma masa rikid'ar hawainiya haka?, wannan fa Fu'ad d'in d'ane ga yayar Uwargidan Sarki mahaifiyarsu Matawalle, cikin cije lips ya buga hannunsa akan gadon yana fad'in “Kai!!!! miyasa hakane? miyasa duk Wanda Na yarda dashi shike fara bayyana a maicin dunduniyata?!! miyasa rayuwa tazomin da irin wannan rikicin ne?, oh God!!”. ‘ya k'are maganar cikin matsanancin k'araji, tareda runtse hannayensa waje d'aya. Tsoro ya kama Munaya, ganin yanda duk ya rikice kamanninsa suka canja, idonsa yayi matuk'a jajur, jijiyoyinsa da gashin jikinsa duk sun mimmmik'e, ga Amaturrahman data tsorata lokacin daya buga gadon, d'aukarta tayi tahau jijjigawa. Sauban ma a firgice ya tashi, ya hau waige-waige, ganin babu kowa a falon saiya nufo hanyar bedroom d'in Galadima, tabbas muryarsa yaji a yanayin da ba'aso. harzai murd'a k'ofar saiya fasa saboda jin kamar muryar Munaya tana magana. Tunda tasamu Amaturrahman tayi shiru sai ta d'auki towel d'insa ta goyata, ta matsa kusadashi a tsorace, hannunta ta d'ora akan nasa daya dafe mirror, ko motsi baiyiba balle ya kalleta. Murya a d'arare kuma a sanyaye tace, “please yalla6ai, fushi baisa a samu sauk'i saidai ya k'ara zafi, kaine kasha gayamin wani karatun baya buk'atar fassara ko dogon nazari, akan barsane kawai a yanda yazo, dukda bansan tushen matsalarba zan iya bada gudunmawa wajen kama bakin zarenta, kayi hak'uri ka kwantar da hankalinka, ita fahimta fuskace, ba fushinka ko tsantsar damuwa ne abin buk'atarba yanzu, d'ana tarkon dazai fara kamo maka hannun mak'iya shine jarumta, ka danne kuma ka daure, ni dama Dan banida ikon hana walimar nanne kawai, amma inaji a jikina akwai lauje cikin nad'i, saidai wad'anda suka nad'a d'inne bamuda ilimin saninsu sai ALLAH yaso Samar damu, amma ai duniya makarantace, idan su a can suka yini kaikuma saika nuna musu kwana kayi, lokuta da dama fushinka ke lalata maka aiki, dan inhar kana cikin fushi dukkan aikinka tafiyar hawainiya yake, wannan lagon naka suka samu suke wasa da hankalinka, koda ace wani ya salwanta cikin yarannan karka d'aga hankalinka, ALLAH n daya baka yafika sanin hikimar k'addara hakan, duk lokacinda kaga Matsaloli sun raunana, buk'atu kan kuma kan yalwata ne, kasa a ranka wannan wata damace tazo gareka, ai duk lokacin da aka rasa kwallo a cikin wasa, ba wasan ake dainawa ba, wata kwallon ake jehowa a cikin fili”. Duk maganar da takeyi ko motsawa baiyiba, baikuma juyo ya kalleta ba, saidai alamu sun nuna yana saurarenta, ta janye hannunta ta juya zata fita tana hawaye. Cak ta tsaya saboda rik'o hannunta da yayi, kusan minti 1 suna a haka, ta waigo ta kallesa, har yanzu yana a yanda yake, kallon hannunsa daya ruk'o nata tayi. Bai kalletan ba kuma bai saki hannunba yace, “Lallai ina shaidama dukkan Wanda ya maida rayuwata data ahalina magijin kallonsa, zan tsiyayar masa da idanun, sannan zan kacaccala rayuwarsa Na binnesa da ransa”. ya mik'e tsaye sosai tareda juyowa ya jawo hannunta ta fad'o jikinsa, saurin dafe Amaturrahman dake bayanta tayi da d'ayan hannun. Ya saka idonsa dasuka firgitata cikin nata, fuskarsa dab da tata yace, “kedai kibama yaranki kariya kawai, dan sune fitilar zuciyar mijinki”.. sakin hannunta yay ya zagayeta yabar wajen. Tamkar sokuwa haka ta bisa da kallo, yayinda zuciyarta keta kuma maimaita maganar tasa, _yaranta, kuma mijinta?_ mi yake nufi to?, amsar itace bata saniba. Jitai kawai ya saka mata ledar kayansu Abdurraheem a cikin hannu, baice k'alaba yabar wajen zuwa gaban wardrobe d'insa yafara fiddo had'add'iyar Shadda gizna ash colour, sai maik'o take da d'aukar idonu. Ganin ya shareta yana cigaba da hidimarsa itama saita juya ta fice. Tunda Sauban yaji motsin kama handle d'in k'ofar yabar wajen da sauri. Fitarta babu dad'ewa Saleem ya kawo kayanda Galadima ya umarcesa. __________________________ Munaya Na komawa Aunty Salamah tahau shiryata, dukda taga a yanayin data dawo bata tambayeta daliliba, saida tagama gyara mata fuska tana gyara mata gashi Munaya tafara fad'a mata iya abinda taga ya dace kawai Aunty Salamahr ta iya Sani, sauran kuma sirrinta ne ita da mijinta. Murmushi Aunty Salamah tayi, tace, “dukda banida tabbacin faruwar wani Abu dagani har Munubiya dama mun shirya hanyoyin d'aukar matakai saboda tsaro, kowa baisan dalilin Munubiya na dagewa akan ki dawo gida ki haihuba, amma ita tasan dalilinta, ba son zuciya ya sakata yin hakanba, Ubangiji Na kallon kowa kuma zaiyi maganin komai, tun a shekaran jiya Saleem yazo mungama tsara komai dama, kuma ya tabbatar min Muftahu yasan komai dan yaga alamar shima tsaye yake da k'afafunsa, inaga yau dai shine yabama Galadima satar amsa, kuma hakan da yayi shine dai-dai, saboda duk abinda zai faru a yau d'innan shi Galadima zai fara zargi”. Munaya tace, “hakane Aunty Salamah, shiyyasa wlhy Muftahu yafara bani tausayi, ALLAH ya kawo ranarda zai wankesa ayi walk'iya aga kowa dai”. Amin ya rabbi gimbiyar Galadima Sameer, ku kwantar da hankalinku, komai kam ya taho gangarar zuwa k'arshe, dan alamomi suna nuna haka”. “nima inajin haka a jikina Aunty Salamah”. Da wannan hirar aka gama gyaran kan tahau shiri cikin less d'inta Ash colour irin kamar kayan da Galadima zai saka kenan. Hummm masha ALLAH, maganar k'yawun da Munaya tayima 6ata lokacine, amma tayi k'yau. Yaranma tsaf aka gama shiryasu, abin kamar ka sacesu ka gudu, sunyi fes. Kowa yagama hada-hadar shiri, ana fitowa daga sallar La'asar za'a fara kwasar mutane zuwa hall d'in da aka tanada. *_4:00pm_* Dukkan mai ruwa da tsaki akan wannan taro ya hallara a gaban motocin da za'a kwashi jama'a, ana fitowa daga salla kuwa aka fara tafiya. Munaya dai tana d'aki bata fitoba, hakama Galadima saida ya dawo salla sannan yafara shiri ma shi. Saida kusan kowa ya tafi sannan iyayen gayya suka fito. Munaya ce tafara fitowa, kuyangi Uku Na d'auke da yaran a bayanta, yayinda wasu kuma ke take mata baya, a babban falon sashensu suka tsaya jiran fitowar Galadima. Tunkan ya fito daddad'an k'amshinsa ya fara isowa, saikuma sautin takun takalminsa wanda tarihi yaso maimaita kansa ga munaya, dan takun nasa Na daidaituwa ne da bugun zuciyarta. Yana gaba Sauban na binsa a baya, Tunda ya fito Kuyangin duk sukai k'asa da Kansu, yayinda ya k'araso sai suka zube k'asa suna kwasar gaisuwa, hannu kawai ya d'aga musu, idonsa akan Munaya wadda itama ta risinar da idonta tana masa kallon k'asan ido. Ba k'arya yayi matuk'ar k'yau, komai nasa Ash colour ne, kuma kayan sarauta y'an asali, harda rawanin daya kuma fiddi ainahinsa Na jinin sarauta, rawanin ya sakaya sajensa hancinsa zuwa bakinsa kawai ake iya gani, idanunsa na cikin eyeglasses dabaka isa kaga kwayarsu ba, dan ya toshe su 6am. Juyawa yay ya kalli Sauban dake gefensa, Sauban ya fiddo Alk'yabbar dake cikin bag d'in hannunsa ya mik'a masa, kar6a galadima yayi yana mik'ama Sauban had'ad'd'iyar sandar hannunsa da zaka iya d'auka ta gold ce, ya warware alkyabbar ya matsa gaban Munaya dake tsaye har yanzu, yayinda kuyanginta ke a dur kushe har yanzu suma. Matsawa yay jikinta tamkar zai rungumeta, k'amshin turarensa ya cika hancinta ta lumshe idanu, ya sako alk'yabbar ta bayanta, Sauban na gefe yanata zuba murmushi da d'aukarsu hoto. Tamkar sokuwa haka Munaya ta tsaya har Galadima ya gama saka mata alk'yabbar a jiki, ya juya Sauban yakuma bashi turaren dake cikin jakkar, feshi ya shiga yimata da turaren, zuciyarta sai kaikawo take yi na d'umbin mamaki da al'ajabin wannan salo, Bayan ya gama ya maidawa Sauban turaren yanama Munaya nuni da suje da hannu. Haka suka fito a jere Kuyangi na take musu baya, yayinda Sauban yake gefe yanata zuba musu hotuna a Camera. Motar da Sarki ya bada ita aka bud'e musu suka shiga, Sauban ya kar6i yaran d'ai-d'ai ya mik'a musu, sannan ya shiga gaba kusada sarkin mota da Amaturrahman shima. Motar ta d'auki shiru tamkar babu wani mahaluki mai numfashi, Galadima ya zubama Abdurahman dake hannunsa ido kawai yana kallo, yayinda ya sak'ala hannunsa d'aya cikin Na Munaya yana murzayatsuna a hankali. Itama dai tayi shiru sassan jikinta Na kar6ar sak'on ninsa. A haka suka Isa har cikin harabar hotel d'in, Wanda ya cika dank'am da motoci, duk Wanda yagani yasan yau taron Na manyane, kodan tsaro Na musamman da wajen ya samu tundaga farkon Layin da hotel d'in yake. Sauban da Sarkin mota suka fito, ba'a bud'e su Munaya ba, kalonta Galadima yayi fuskarnan dai babu walwala har yanzu, batareda yayi maganar ba ya kamo kwalliyar zaren gaban alk'yabbarta ya matso da fuskarta kusa da tashi, ta bud'e baki zatai magana ya d'ora nashi. Saida ya shanye jambakin lips d'inta tas sannan ya saketa yana zuba mata harara. Idonta harsun tara kwalla, cikin lumshe idanu da k'asaitacciyar muryarnan tasa mai had'e da izza yace, “Sau d'aya nake gargad'i, karki bari nasake miki na uku akan fita da lipstick a baki”. ya k'are maganar da kad'a mata yatsansa. Wani yawu Munaya ta had'iye kawai tana jinjina masa kai, wannan ikon ikoko yana bata mamaki, shiyyasa fa tace Aunty salamah ta saka mata janbakin kad'an, gashi yamata k'yau amma tsabar mugunta ya shanye, lips d'insa sai zafi yakeyi, ta harari Abdurraheem dake cinyarta, saikace shine yayi laifin🤭😂. Bud'e musu akayi suka fita, Samha da Ayusher suka kar6i yaran. Munaya taji matuk'ar dad'i da ganin ashe harda y'ar uwarta a walimar, itama sunsha k'yau cikin Brown d'in kaya itada yaa Marwan, tana cikin less irinna Munaya, kalarce kawai ta banbanta, shikuma Yaa Marwan harda babar riga, maganar k'yawun dasukaima 6ata lokacine, suma Yaa Fadeel da Feena suna d'auke da yaransu. Sun shiga cikin hall d'in da tawagar rakkiyar Kuyangi da dogarai, masha ALLAH Munaya tafad'a dan ganin d'unbin jama'a da aka Tara a wannan k'aton hall, manyan mutane da iyalansu sun halarci wannan waje, hakama ahalinsu Munaya kwai da kwarkwata sunzo, harda y'an anguwarsu, duk yawan mutanen nan bai hana a saka mata kan tsaro masu tauriba a wajen. Kowa saida su Galadima suka birgesa, abin akwai tsantsar birgewa da sha'a a cikinsa, A cikin fans harda masu k'yasa Galadima🙆🏽. barama namuku gulma, can Na hango muku tawan Miss xoxo fa idonta kamar zai fad'o, hakama zee bawa da Aysha dansabo da kdeey🤥, dukda harar da Maman Khady da takwara billy galadanci ke musu sunk'i rusunar da idanu, lamari ya girmama Slimzy harda k'ok'arin mik'ewa fa wai zata iya barin sadeeq d'inta, da sauri saffiya Huguma ta maidata mazaunin tana hararta, Ummi Ai'sha tace, “kai dan ALLAH Ku nutsu kar'ace 'yan Haske muncika ruwan ido”, Faxy Fation da party zarah da Feedohm sukace ai Galadima d'inne fa yaji gishiri da magi, Hafsat Rano ta toshe baki tana dariya, hajja kam yitai kamar bata wajen, sai loda nama take a baki, Ayusher da khaleesat dake kallonta sukace wai hajja bazaki rage filiba a cikinki?, Mamu gee tace, “kukuma ga sa ido” “kema k'ya fad'a dai” cewar zee yabour, Asmy b Aliyu datun d'an tai shiru itada Ummu Basheer suka yamutsa fuska suna fad'in “please kuja aji mana 'yan haske, kunafa ganin yanda aka karrama mu fiye da kowa, karku jafa a maidamu kujerar baya wlhy”. Ni bilyn Abdull da lamarinsu ya girmeni nace, “kubarsu kudai kawai, sosuke susa a hanamu ganin sarakuna, kokuma mama Fulani ta rainamu, kuna dai ganin innaro ma kanta yanda taja aji ta kwamushe a gefe tana mazurai. Miss xoxo dake gefena tayi k'asa da murya tana dai-daita kanta, tace, “gaskiya kika fad'a tawan, nidai kinsan dama dai Galadima ya dad'e a k'ok'on raina, ko sau d'ayane kisan yanda kikayi aka mana hoto tare”. Nace, “karki damu tawan, Salfe ma zakuyi, amma fa ki kula, dan Munaya babu sauk'i”. “gulmar mi kukeyi?” cewar Ayusher tana jeho mana handkerchief d'in hannunta. zamanmu muka gyara nuna wani basarwa🥺, kunsan fa muma mun fara koya a wajen Galadima😜. Lallai, fans sannunkufa, lallai kunma munubiya da Munaya kara, ko Galadima nasan kun gama birgesa aradu, irin wannan anko da kukasha, ko a UK albarka y'ay'an baba buhari😝. ____________________ Isowar Sarki Jalaluddeen da Sarki Abdul-fatah da tawagar wasu amintattun sarakunan abokan Abie ya saka kowa ya mik'e cikin girmamawa, saida suka zauna sannan kowa ya koma ya zauna, an fara bud'e taro da addu'oi ga jarirai da kuma kakansu sannan aka fara gudanar da abinda ya Tara jama'a cikin nutsuwa. Kusan dai lamari Na manya, mudai Fans d'in raina kama sai zuba salfe muke, karkaje kabada labari ace k'arya ka zula bakajeba😆, shiyyasa muka kafa hujja koya kukace my sweet fans🤷🏻‍♀😂?. Masu 6oyayyen shiri a zuciyaa fa sunata k'iyasata yanda abubuwan da suka shirya zasu gudana, saidai kuma idan sunsan wata basusan wataba, dan eyeglasses d'in idon Galadima Google ne😏, (wato camera ne) tundaga Inda yake yanayo zooming d'in wad'anda suka k'arshen hall d'in ma, duk Wanda zuciyarsa ta saka masa alamar tambaya akansa yana tantancesu ne d'aya bayan d'aya. Nidai Galadima ka kula banda fans d'in raina kama😨🙆🏽. Anyi nisa da taro harma Anfara zubama cikin maik'o da mask'i, ga mai zak'i da sanyi muna korawa, Galadima ya kalli agogon azurfa dake hannunsa sannan ya d'ago ya kalli Muftahu suka had'a ido, lips ya ciza, Muftahu daya fahimci yaren ya gyad'a masa kai, ya kuma kallon Saleem da Nuren da Aunty mimi Mom and Sauban Samha Ayusher, kowannensu Kansa ya gyad'a alamar fahimta.................✍🏻 Turk'ashi, tofa masu karatu, shin mike shirin faruwane haka? Wannan amsa tana page 26 da zaizo ranar Monday insha ALLAH. musha weekend lafiya sisters and brothers.🙋🏻🙋🏻🙋🏻 Barkanku da juma'at😁🤝🏻 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 [7/15, 2:13 PM] Aysha Galadima: *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ___________________ _Writer's namu ina mik'o gaisuwa da babbar murya_.🙋🏻 *_(takwara) Bily s Fari, (mamana) Maryam IG, (mamana) Ummu hanan, Hauwa'u A Usman (jidda😘) Rufaida Umor, Qurratul ayn, Ai'sha Alto, Leemat, gwoggo😜 Asykhaleel, miss Xakss, Jameela Janaf, (takwara) Ummie Garkuwa, Khadeeja Candy, Billy Sarki, Sister Naja'atu, Reefat yahya, Sad-Naf, Maryam wasagu, Maman Shaheed, classic Feedo, Mzzdady._* 🙆🏽 _Yawane da kufa. Alkairin ALLAH ya kai gareku aduk inda kuke, bilyn Abdull na nayinku wujiga-wujiga🥰😘😘👍🏻_ ___________________ ~Book 2~ 👉🏻2⃣6⃣ ...................MC yafara shelanta cewa wannan bikin sunafa an had'ashi da bikin birthdays ne, domin ranar haihuwar yaran tai dai-dai da ranar haihuwar iyayensu, dan haka suka had'e wannan biki a yau guri d'aya, dan a waccan ranar murnar haihuwar bata basu damar yanka cake ba😂. Dariya aka sanya, saboda a yanayin barkwanci mc yayi maganar, Galadima kam ai kod'an murmushin ma baiyiba, garama Yaa marwan ya murmusa. Galadima ya kalli munaya, cikin maganar nan tasa mai kamada an masa tilas yace, “Kina da sa'a”. “Sa'a kuma?”. ‘Munaya ta fad'a cikin yanayin mamaki’. Harya bud'e baki zaiyi magana sai kuma ya basar. ganin haka itama Munaya saita sharesa, dan takula yau y'an mulkin ne a kansa. Saida ya gama shan k'amshinsa sannan yace, “wannan ne karon farko da Sameer yata6a bikin birthday”. Baki munaya ta d'an ta6e, tana fad'in “Humm, kodai y'ay'anka suna da sa'a?, domin dai a dalilin haihuwarsu ne kayi”. “ko kina jealous ne?”. ‘yay maganar cikeda basarwa’. tura baki tai gaba. Idonsa akan yaransa yace “idan kika bari na kama wannan bakin a wajennan humm.” ya cije lips d'insa. Sanin k'aramin aikinsane ya akaita abinda ya fad'a d'in ya sata saurin gyara bakinta , tad'an saci kallonsa, ya wani Fiske tamkar ba shine yay maganar ba ma. ita dai tana mamakin kasaita da izza irinna bawan ALLAH n nan, jinin mulki yana da matuk'ar k'arfi a jikinsa. tunaninta ya katse lokacin da hankalinta ya koma kan abinda ke faruwa a hall d'in Khaleel da Aiyaan, Aryaan ne suka turo cake mai k'yau da tsari, Wanda yasha kwalliyar White and Golden, an saka sunan Galadima da shekarunsa 31years a sama, a jikinsa kuma daga can k'asa ansa Muhammad Sameer (Dadyn Triples), an d'ora candlestick🕯guda uku, Sai hotonsa da yay k'yau sosai cikin shigar sarauta. Galadima ya kalli Sauban da Samha, yasan dai wannan aikinsu ne, k'in kallonsa sukayi sukam ballema suyi gamo da tsarabar harara😅. Ita Munaya ma sai yanzu taga Su Aiyaan, batayi zaton anzo da suba, tunda bataga yaran gidansu k'anana ba a waje, sai manya maza da matan Na ma'auri. MC ya taso k'eyar su Khaleel har inda su Galadima suke zaune, kowanne aka d'ora masa yaro d'aya, suma mik'ewa sukayi bisa umarnin MC d'in, a tare suke takawa ita da shi, sai k'yastu ake zuba musu, masuyi a waya da masu cameras, sai gidajen TVs d'in da aka gayyata suna nuna live. Sun Isa gaban cake d'in hannunsa rik'e da sandarsa, kaikace sarkine da kansa (gaskiyar Munaya Galadima akwai k'asaita, Kodai sarkin da Kansa ya shafa masa lafiya🤭). Bayan anmasa wak'ar happy birthday yayma munaya nuni waita hura candles d'in. Cikin k'asa da murya tace, “yalla6ai bafa haka akeyiba, ka hura abinka da kanka”. Hannunta ya kama ya matsa yanda zataji zafi, yace, “zakiyi?”. Ai baima kai k'arshen maganarba ta risina ta hure wutar, hall d'in ya d'auki tafi. cake d'inma dan rigima wai saidai su yanka tare. “haba yalla6ai, saikace Na wani aure?”. Cikin ta6e Baku yace, “wama ya sani kona auren ne”. Shiru tayi bata tanka ba, dan itadai fatanta a rabu lafiya, hannunta ta d'ora kan nasa dake rik'e da wuk'ar suka yanka taren. nanma dai tafin akayi. Ya lakata a d'an yatsa ya duk'o gasu Aiyaan ya daddan gwalama yaransa a hanci da kumatu, sannan ya juyo ga Munaya da haushi ya kamata, ai ita yakamata ma yafara sawa ba yaranba. Itama akan hanci ya shafa mata yana fad'in “yalla6iya haushi kikajine?”. Kafin tabashi amsa yakuma lakata ya shafama Aryaan Khaleel da Aiyaan suma. Dole munaya ta had'iye maganarta. Amma ta kudiri saita rama. Itama itada Munubiya k'aton cake nasu aka kawo kalar pink and White , Munu da Yaa marwan suka taso a tare. Munaya da Munubiya suka rungume juna suna maijin dad'in tunawa da ranar haihuwar su, shekaru 20 cif da kwana 7. Sun yanka cake atare suka sakama juna abaki kad'an-kad'an, sannan kowacce cikin son tsokana ta lakatama y'ar uwarta a fuska suka rungume juna suna dariya da k'ananun hawaye, suncika shekaru 20 ranarda yaransu sukazo duniya suma. Abin ya birge mutane, Munubiya ta matsa ga mijinta ta saka masa a baki kad'an, cikin murmushi yace, “happy birthday my heartbeat ”. Tace, “Thanks you my luv” k'arasawa tayi ta sakama yaran munaya dasu Aryaan a kumatu, sannan ta sakama nata yaran. Munaya danta rama abinda Galadima yamata, takai cake bakinsa kamar zata bashi, saida ya bud'e baki saita juya ta shafama yaran Munubiya a kumatu, sannan nata. Yanda Galadima yay shock akan abinda Munaya tamasa sai mutane suka sanya dariya suna tafa mata, mai martaba da papi ma dai saida suka Murmusa. Munaya ta dawo ta dangwalama Galadima akan hanci tana masa gwalo. Shi kansa baisan k'asaitaccen murmushin ya kufce masaba, ya saka handkerchief ya goge yana dawowa mazauninsu ya zauna. Daga nan aka fara gudanar da wasa, Comedian's sukazo sukad'an saka mutane dariya, saikuma mawak'a da suka bada nasu salon. Tun da Galadima ya fara yawaita kallon agogon hannunsa su Muftahu duk suka sake shiri, dan lokaci yana gab kenan. Galadima yay k'asa da murya batareda ya kalli Munaya ba, yace “ki shirya, shirinsu na farko d'aukewar wutar hotel d'in nan gaba d'aya, na gaba kuma shine banida tabbas. Yara dai ALLAH yana tare dasu, gakuma su Aryaan suma”.. Cikeda mamaki Munaya ta kallesa, sannan ta kalli yaran dake gabansu a wani d'an gado mai k'yau. Jikinta har rawa yake tace, “yalla6ai mi su Aryaan zasu iya? Please k.....”. Hannu ya d'aga mata alamar karfa ta ishesa yace, “wani ilimin aduhuwar daji kawai ake laluboshi, kinsan kuwa dolene a gamu da had'arurruka Aciki”. batada za6i sainyin shiru, ta kalli su Khaleel daketa wasa da abinci a teble da suke zaune hankalinsu kwance. Hawayene ya cika mata idanu, yama za'ayi wad'an can sakarkarun yaran ace suna masu bama yaranta kariya? Yaushe suka gama sanin ciwon Kansu ma balle na waninsu? gaskiya wannan gangancine kawai, tasa handkerchief ta share hawayen da ke k'ok'arin zubo mata. Duk abinda take Galadima yana kallonta. duk tausayinta saiya kamashi, ya tuna da wahalar datasha, amma bashida za6in daya wuce hakan, kuma itace tabashi k'arfin gwiwa ai, yasaka aransa ko salwanta yaransa sukayi zaiyi tawakkali insha ALLAH. Duk Wanda yake cikin shirinsu Galadima ya gama shirinsa, haka suma mak'iya masu buri a shirye suke. Gaba d'aya saura mintuna 25 atashi, saboda gabatowar sallar magrib, a kuma time d'inne Sarki Abdul-fatah da Sarki jalalludden dadai duk wani babba Wanda sukazo tare suka mik'e domin tafiya, ganin haka Galadima yama Yaa marwan sigina da ido akan ya fita da Ameen and Ameena suma, yabi tawagar su papi, dan baya buk'atar a cuta musu.. Jikin Yaa marwan a sanyaye ya d'auki yaran ya fita cikin dabara, yana kallon y'an uku, shidai dan kawai Galadima ya dagene, amma bai kamata a saka yarannan a matsayin tarko ba. Munaya ma dai ta danne zuciyarta tayi shiru, tanason bama Galadima kwarin gwiwa. Su papi na fita y'an rawar k'oroso suka fara wasa, mintuna goma da aka basu ya k'are, sai wani mawak'i ya fara nashi, nanfa y'an mata da samari aka samu nayi, dama ganin su mai martaba ne ya sakasu nok'ewa, ana tsaka da cashewa hall d'in yay d'iff, wuta ta d'auke agaba d'aya hotel d'in, mutane aka fara hayaniya kowa na k'ok'arin damk'e dukiyarsa a hannu da k'ok'arin kunna fitulun waya. Gaba d'aya jikin Munaya yahau 6ari, ta fashe da kuka tana laluben gadon da yaran suke, ruk'ota Galadima yay yasaka a jikinsa, muryarsa na rawa yace, “please ki nutsu”. “bazan iyaba yalla6ai, karsu......”. Yay saurin rufe mata baki, da tattausan tafin hannunsa..... A dai-dai wannan lokacinne kuma wutar hotel d'in tadawo. Hall d'in ya kuma kaurewa da hayaniya, zaram Munaya da Munubiya suka nufi gadon da yaran suke ciki, wayam babu komai. Munaya tayi luuu zata fad'i, saurin ruk'ota Munubiya tayi, Galadima yataso daga inda yake shima zuwa garesu. hall d'in yagama rikicewa da tsantsar hayaniyar rashin ganin yaran, sai kallon kallo akeyi. Securitys d'in da aka baza sun rikice da wannan tashin hankali, dan sune mutane na farko da za'a fara tuhuma. Rufe hotel d'in akayi aka hana kowa shiga balle fita, Galadima ya shafama Munaya ruwa ta kawo numfashi, fashewa tayi da sabon kuka ta fad'a jikinsa, hannu biyu ya saka ya rungume ta shima yana had'iye kwallar bak'in cikin dake Neman zuboma idonsa. Tausayinsu ya kama mutane da yawa, innaro harda kukanta, hakama inno, abinda yabani mamaki shine tsantsar damuwar da mama Fulani ta nuna, dan itacema tabama Galadima ruwa ya shafama Munaya ta farfad'o. Da farko Munaya ta d'auka ko Galadima wasa yake mata yasan inda yaran suke, amma ganin damuwar da yake ciki saita kuma rikicewa, dandanan numfashinta yafara gagarar k'irjinta, ta mik'e a kid'ime, dan taji a jikinta kuka sukeyi, nononta sai tsitstsirawa suke, wani jirine yafara hajijiya da ita da zuciyarta ta k'iyasta mata zafa su iya kashe mata yara, luuuu tayi baya Galadima ya ruk'ota. sume musu ta kumayi. Hankalin Galadima kuma tashi yayi, dole ya d'auki Munaya aka sakata a mota suka bar hotel d'in. Sauran mutane kam kowacce mota zata fita sai an binciketa. Yayinda Securitys d'in suka bazu ko ina na hotel d'in ana bincikawa. Gida aka wuce da munaya, har suka isa tana jikin Galadima, yanata murza tafin hannunta kozata farfad'o, har d'ora bakinsa yayi akan nata ya jawo iskar numfashinta amma a banza, hakanne yakuma tada hankalinsa. Kai tsaye d'akinsa ya wuce da ita, ya shimfid'eta a kan gadon ya cire mata alk'yabbar jikinta, Akash suka k'araso da hanzari shima, taimakon gaggawa yafara bata shida doctor jalal, cikin amincin ubangiji saigashi takawo numfashi, bama su bari tadawo dai-dai ba suka mata allurar barci. Suna fita Galadima ya cire rawani da alk'yabbar jikinsa shima, ya sassauta bottom d'in wuyan rigarsa. Safa da marwa ya shigayi a tsakar d'akin yana Mirza agogon hannunsa Wanda daka gani kasan ba normal agogo bane,. Wayarsa datai k'ara yay saurin d'auka, d'agawa yayi yasaka a kunne, “Muftahu ya ake ciki?”. Cikin hakki Muftahu yace, “komai yana tafiya yanda ya kamata ranka ya dad'e, har yanzu gamu muna bin bayansu, amma munkai inda yakamata ka fara Controlling namu, yanzu mun.......” Da sauri Galadima ya katseshi ta hanyar fad'in “karka damu ina kallon Ku, saidai kilometer's d'in dake tsakaninku dasu fa yakai 1½, Saleem da Sauban sunfi kusa dasu, dan haka ku k'ara azama. daga lokacin da suka farga da abinda nasaka jikin Amaturrahman tabbas zasu cireshi, kuma zamu rasasune gaba d'aya”. “Ok babu damuwa, ranka ya dad'e”. Yanke wayar sukayi, Galadima ya bud'e wani k'aramin akwati ya fiddo kayan aiki wanda a ready dama yagama had'a komai, bajesu yayi akan gadon kusada Munaya, ya zauna yafara Control cikin matuk'ar kwarewa. Saleem ya kira aunty Salamah wadda itama take tare dasu Ameer yaran da suka sace Muftahu, d'agawa tayi jikinta na rawa, “Saleem kuna inane?”. “Aunty Salamah gamunan bayansu kad'an, amma mund'an basu k'afa saboda na kula sunfara fuskantar muna bin su, yanzu dai haka mun ajiye motarmu mun samu mashin”. “Hakan yayi, insha ALLAH indai ta Anguwar da muke tsammanin zasu shigane kamar yanda kaji Harun d'in yay magana to tabbas mu dai mun iso, saidai suzo su iskemu, ka kira yalla6ai ka sanar masa yakamata ya fito yanzu”. “no Aunty Salamah, bazai yuwu boss yabaro masarauta ba yanzu, saiya tabbatar mun Isa, saboda dukma inda suka shiga yana bibiyarsu, dan bazai saka yaransa a matsayin tarko ba babu tsaro k.......” Tai saurin k'atseshi ta hanyar fad'in “yauwa ina zargin kamar gasunan a wata bak'ar mota sun wicemu fa”. “Alhmdllh, su Ameer Susan yanda zasuyi su bisu bara na kira boss”. “ok”. Kawai Aunty Salamah ta fad'a ta yanke wayar. Kiran Galadima Saleem yayi, bugu biyu ya d'auka, “Saleem mike faru yanzu?”. “Ranka ya dad'e gamu dai biye dasu, amma Aunty Salamah tacemin gasu tagansu”. “wacece Salamah? ”. Gaban Saleem ya fad'i, dan ya manta Galadima baisan Salamah ba, “Am sorry sir, idan komai ya dai-daita zan maka bayani”. “Saleem!!!”. Galadima ya kirayeshi a tsawace. Saida Saleem ya janye wayar akunnensa, muryarsa na rawa yace “ka yarda dani sir, wlhy itama ta kwarai ce”. Ajiyar zuciya Galadima yayi, muryarshi cikin tsantsar damuwar yace, “wannan anguwar da kuke tanada hanyoyi da yawa, dan haka Ku fara amfani da live GPS navigation maps naku, yanzu zanyi settings komai yanda zaku ringa ganinsu duk layin da zasu shiga insha ALLAH, waye yake driving d'in a cikinku?”. “nine sir”. “ok bama Sauban wayar”. Saleem ya mik'ama Sauban wayar, Galadima na fad'a masa yanda zaiyi, shikuma yana Controlling maps App d'in dake cikin System d'in cikin kwarewa, (dan shima Galadima bai barsa hakaba, dukda bashida ra'ayin karantar wannan fannin saida ya tsaya tsayin daka ya koyan saboda irin wannan ranar). Saida Galadima ya tabbatar komai ya dai-daita, sannan ya kira su Nuren ma, suma suka dai-daita komai nasu, cikin sauk'i duk suka koma ganin inda yaran suke, saboda Galadima ya saka Abu jikin Amaturrahman, dukda bawai hotonsu ko video suke kalloba kai tsaye. Duk da haka Galadima ke fad'a musu su shiga layin haggu, ko dama, kosu canja hanya dadai sauransu. Duk Wanda yake a wannan masarauta yau hankalinsa a matuk'ar tashe yake, saifa kallon kallo da hasashen juna ake a zuciya, kowa yana zargin Wanda ya raina. Hankalin Abie a matuk'ar tashe ya nemi ganin Galadima, koda sarkin k'ofa yazo yana knocking Galadima bai amsaba, kuma yana kallonsa ta CCTV. d'an aike ya koma ya sanar Galadima ya kulle kansa a d'aki yak'i bud'e k'ofa. Papi inno ya kira, yace maza taje sashen Galadima taga mike faruwa. Ko kuyangi inno batajira sun mata rakkiyaba, hasalima babu Wanda yaga fitowarta a sashen mama Fulani, dan kowa a rikice yake da wannam bak'on lamari na satar yara. Galadima daya ga sarkin k'ofa yabar wajen ya mik'e shima daga gaban kayayyakin da yake aikin, shaddar jikinsa ya cire yasaka bak'in wando da t-shirt, ya kawo bak'ar jacket mai k'yalli kamar rigar sanyi ya ajiye gefe, a bakin gadon ya zauna yana d'aura takalminsa yana cigaba damasu Sauban da Nuren bayanin hanya, a dai-dai lokacinne Inno ta iso sashen nasa, da hanzari Sarkin k'ofa ya bud'e mata k'ofar, bata jira wani isoba ko masa sallama ta turo k'ofar falonsa ta shigo, babu kowa a falon, komai ma a kashe yake. Bedroom d'insa ta nufa, nandai saida tayi knocking kam, saidai kafin yay yunk'urin tasowa ya bud'e mata ta turo k'ofar ta shigo, mik'ewa yay yana kallonta da d'aukar jacket d'insa zai saka. Ajiyar zuciya inno ta sauke, saboda ganinsa normal. “Ranki ya dad'e da kanki? lafiya dai ko?”. “Inafa lafiya Muhammad? takawa ya aiko a kiraka ance ka kulle kanka, gashi baka sanar mana halinda yarinyar nan take cikiba”. Galadima yace, ba kulle kaina nayiba, bansan kuma d'an aiken daga papi yakeba” ya juya yana kallon Munaya da cigaba da fad'in, “itama ta farfad'o, amma sun mata allurar barci”. ‘ya k'are maganar da daidaita zaman kwalar rigar jacket d'insa’. Ajiyar zuciya inno ta kuma saukewa, tace, “to Alhmdllh. ina kuma zaka naga kana shiri?”. Wani murmushin takaici yayi zuciyarsa dake gudun daya wuce kima da suya ya dafe, Inno dai ta zuba masa ido, takowa yay inda take ya kama hannunta ya rankwafo (dan yafita tsaho) ya d'ora bisa kansa, cikin murya mai nuna tsananin karsashi da alwashi yace, “kisamin albarka inno, zanje farautane”. Da sauri ta janye hannunta daga kansa tana matsawa baya, “Muhammad mikake nufine? kana ganin tashin hankalin da muke ciki shine zaka k'irk'iro mana wani kuma? kana tunanin wad'annan mutanen zasu barkane? dama kai suke fako, shiyyasa sukayi tarko da bayin ALLAHn dabasu ji ba basu gani ba, su takawa cikin k'ok'arin d'aukar mataki suke, yanzu haka naga IG da kansa gashican ya iso bisa umarnin kiransu”. Galadima dake tattara abinda zai amfani dashi yana zubawa a aljihu, yace, “inno Muhammad Sameer d'inku ba ragon namiji bane da zai zauna jiran Police d'in da suka gaza gano wad'anda suka durk'usar masa da mahaifi tsawon shekaru a yanzu kuma nayi tunanin zasu iya dawomin da gudan jinina har uku, ba sune sukamin tarko ba nine namusu tarko, idan tsoron na mutu kuke, Ku cire inno, ko babusu mutuwa tabbataccen abune rubutacce a kundina, kimin addu'a saina saina dawo”.. Biyosa inno tayi har babban falo tana Kiransa amma yak'i dakatawa, saima d'aga mata hannu da yakeyi, yana gab da zai fita ya juyo yana fad'in “karki d'aga murya da yawa ranki ya dad'e, dan kunnen magauta a bud'e yake”. Yana fitowa Sarkin mota ya taso, dan suna zaune jigum-jigum a rumfar bunun dake sashen na Galadima, duk gaisuwar da suke masa babu ta wacce ya amsa, yau kam ko d'aga hannun basu samuba ma. Basu damuba dan dolene kowa yamasa uziri. Da kansa ya bud'e mota ya shiga mazaunin driver, Sarkin mota daya k'araso yace, “ranka ya dad'e ka gafarceni gani”. Da hannu yamasa nuni da gefen mai zaman banza batareda yace uffan ba. Sarkin mota bashida za6in daya wuce zagayowa ya shiga. A 360 Galadima ya ja motar, kamarma ya manta yana cikin masarautane, saida suka fito gaba d'aya sannan ya bud'e baki da k'yar yace, “ka dinga kallon bayanmu, dan nasan dole za'a samu masu binmu”. Da “to” sarkin mota ya amsa cike da girmamawa. Sarkin mota yace, “tabbas ranka ya dad'e ana binmu”. Cije lips Galadima yayi, ya canja hanya, cikin salon iya taku suka 6acema su Harun dake bin su tundaga masarauta. Hankalin Harun ya tashi kwarai da gaske, dan bai shirya fito na fito da Galadima ba yanzu, saiya cimma burinsa, daga nan komai ta fanjama fanjam, iya zagaye-zagayensu baiga ko motar datai kama data Galadima ba. Shima yana 6ace musu ya dawo kan titi sosai, Maps d'in GPS ne yazama jagoran Nuna masa hanya, da taimakon Sarkin mota kuma dayasan gari. Danshi Galadima ba tuk'i yakeba idan yazo 9ja, saidai idan ta kama tilas babu yanda zaiyi kamar irin haka. Sunyi tafiya mai tsawo, yayinda yake Communication dasu Nuren dasu Saleem. A haka ya iso inda suke, duk fitowa sukayi daga motocin, shima Galadima ya fito, idonsa akan agogon hannunsa, yad'an kallesu sannan ya koma kan waya yana fad'in, “maps d'in ya nuna suna a wajennan, kunga kenan tsakanin gidajennan guda hud'une dake kallon juna?”. “kwarai da gaske suna nan”. cewar Muftahu yana furzar da iska. Galadima yace, “Sauban da Saleem zaku cigaba da Control namu”. ‘yay maganar yana ciro agogon hannunsa ya mik'a musu, “ga wannan kuci gaba da using dashi”. Suka amsa da “to” suna kar6a. ya mak'ala abinda zai taimaka masa yaji magana, suma su Nuren duk yabasu suka saka. Har zasu bar wajen ya dakatar dasu ta hanyar d'aga musu hannu, takawa yay gaban k'ofar gidan farko ya haska gaban gate d'in da fitilar wayarsa, babu abinda yake nema, ya matsa na biyu ma haka, komawa yay d'ayan 6angaren, yana haskawa saiga sawun tayar mota data shiga gidan, duk'awa yay ya d'iba k'asar wajen ya shinshina, ya d'ago ido ya kalli gidan yana jizar lips, saiya zubar da k'asar daya d'iba ya mik'e, da hannu yayma Nuren da Muftahu nuni nan ne. Tahowa sukai garesa, Aunty Salamah datun d'azun suna daga cikin mota suna kallonsu suma suka fito ita da su Ameer. A tare suka rissina suna gaida Galadima ya amsa yana bin su da kallon mamaki. Da yake su Saleem sun sanar dasu Muftahu su Aunty Salamah d'in sai Nuren ya kuma yima Galadima bayani. Aunty Salamah tace, “ka gafarcemu ranka ya dad'e, nasan zakayi mamkin mun shigo abinda ba'a gayyacemu ba, insha ALLAH zakaji dalilin shigowar tamu nan gaba. game da shiga gidan nan mungama komai, maza 5 ne da mata biyu, wad'anda shigarsu ta tabbatar min suna cikin hadiman masarauta su matan kenan”. Kai kawai Galadima ya iya jinjina masa. daga nan yaymata nuni da zasu iya farawa. Da taimakon su Ameer suka shiga gidan. ★★*★★★*★★★*★★ Fitar Galadima da kusan awanni hud'u, around 2am Munaya ta farka a firgice, Inno dake zaune akan Sofa, mom da Aunty Mimi kuma a gefen gadon suka kalleta, tashi Mom tayi da sauri ta nufeta tana rik'eta, itama Aunty Mimi ta taso. Kuka munaya ta sanya tana fad'in “Mom sun mutu ko? Nasan dama kashesu zasuyi, Aunty Mimi dan ALLAH miye laifinsu su? kwanansu 7 fa kacal yau a duniya, mi suka sani game da abinda ake tuhumarsu? An durk'usar musu da kakansu, an hana mahaifinsu nutsuwar zuciya data rayuwa, shin wannan tabon bai Isa a barsu su taso da shiba a rayuwarsu? Har sai an had'a da salwantar dasu kenan?”. ta fashe da kuka maiban tausayi. Tasowa inno tayi ta zauna a bakin gadon itama, kamo hannun Munaya tayi ta kwantar da ita a jikinta tana shafa kanta, yayinda itama kwallar kebin nata kumatun. Aunty Mimi da mom ma duk hawayen sukeyi, kalaman Munaya sun ta6a zukatansu. Lallashinta da magana mai dad'i suka shiga fad'a mata, sai sauke ajiyar zuciya takeyi, ga jikinta yayi ringim da zazza6i saboda nononta sun mata hak'e-hak'e, rabonsu da shansa tunda rana, tausayinsu ya kuma kamata, tasan yunwa da k'ishi ma kawai sun Isa su k'arar da numfashinsu, hawaye masu d'umi suka kuma gangaro mata a kumatu suna sauka jikin inno dake shafa kanta. Shayi Aunty Mimi ta had'o mata, amma fir tace ta k'oshi, da k'yar inno ta samu ta lalla6ata tasha Quarter d'in kofin. Mom tace, “wannan nono kid'an matsesu kozasu rage miki nauyi, dan shine yakawo wannan zazza6in”. Bata musaba aka kawo k'aramin bowl ta matse aciki, Aunty Mimi ta zubar a bayi”.. Tanason tambayar ina Galadima tanajin kunya, sukuma babu Wanda ya sanar mata komai, kodan gudun k'ara tada hankalinta. Magani suka bata tasha takoma ta kwanta, yayinda sukuma suka mik'e duk suka d'aura Alwala suna mik'ama Ubangiji kukansu, danshi masanin sirrin 6oyene, yana kallon komai, kuma shine zai kawo iyakar komai d'in. ★★★★★★★ Duk wannan abun dake faruwa su Momma babu Wanda ya sanar musu, saidai sukaji a jikinsu tamkar akwai matsala, sunta kiran numbers amma daga wadda zasu samu a kashe sai wadda network zai hanata shiga. Sai suka d'aura ko shagalin sunan ne yakawo hakan. ******************* Tunda Munubiya suka koma gidan kuka takeyi, ko kad'an tak'i sauraren yaran da keta tsula kuka suma, balle tabasu nono. Ba itaba hatta su Ayusher dasu feena kukan sukeyi, hakama Samha harda shid'ewa, dan itama su tabi bata koma masarauta ba, Yaa marwan da mama Rabi'a ne kawai ke k'ok'arin danne nasu suna lallashinsu. Yayinda dare yay nisa duk sai suka d'aura alwala suka zo suna mik'ama Ubangijin talikai kukansu da k'ok'on barar bama wad'annan k'anan alhaki kariya da fatan ku6ta. A 6angaren gidan su Munaya kam duk hassadarsu yau dai sun tausayama gudan jininsu da yaranta, sundawo gidane kowa yana sharar kwalla da addu'ar ku6tar yaran. Ita innarsu Munaya ma ai ba'a magana, ALLAH kad'aine yasan halin datake ciki, ta shige d'aki ta rufe kanta tana jera nafilfili, dan wannance kawai gudunmawar dazata iya bayarwa a garesu akan wannan lamari mai sark'ak'iya da yawa. Abban su munaya ma yau harda hawayensa, dukda bashi da tabbas akan hasashensa yasan komai zasu iya, saboda SD yanada kusanci da wannan masarautar sosai, duk abinda ke hannunsa da bayanan daya ajiye ya shiga tattarasu waje d'aya...............✍🏻 😿Duk nisan jifa dai k'asa zai fad'o, kwana 99 na 6arawo, 1 kuma tak namai kaya.👎🏻 Fans insha ALLAH dai abuwa sun fara warwarar zare, sai mubi su Galadima muga yanda zasu dawo mana da triplets d'inmu gida😭, yau Munaya tabani tausayi daga ita har Galadima, dan shima dai dannewa kawai yake saboda jarumta, ALLAH ya rabamu da sharrin mak'iyi komai k'an k'antarsa, Harun da sauran munafukai MAZA BISA KANKU🏇🏻🏇🏻🏇🏻🏇🏻🏇🏻. Barkanmu da dawowa my sweet fans🤕😡. Yau bana cikin yanayin dariya😡 *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭👏🏻 [7/16, 5:34 PM] Aysha Galadima: *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻2⃣7⃣ ................Tunda suka d'akko yaran suketa kuka, musamman Abdurraheem dahar shid'ewa yakeyi, ALLAH dai yabasu sa'a ne saida suka fito suka fara kukan, neman haukatasu ma sukaso yi tun amotar, jisukai tamkar su rufesu da duka, saidai babu damar hakan, dan basuga abin duka jikin wad'annan kwad'unan yaranba. Da farko sunga kamar ana binsu, sai daga bisani ne sukaga ba haka baneba, har dai suka iso gidan y'an uku basu barsu sun shak'i iska ba. Suna shiga suka danna musu wasu allurai, cikin mintuna k'alilan jikinsu dukya saki sukayi luf. ganin lokaci yaja har kusan 10pm babu alamar wani motsi hankalinsu ya kwanta, dan sunsan dai tabbas sun tsira, wayar wadda ta sakasu aikin suka kira, amma tak'i yin picking. Cikin matan d'aya tace, “kusan dai bazata d'aga ba, saboda nasan masarauta a haukace take yanzu, saidai mubari zuwa safiya”. Tsaki d'aya yaja, “kai nifa gaskiya a tsorace nake, gara ta d'auka asan mafita, bana buk'atar gawar yarannan takwana a hannunmu, kunsanfa babansu mayene wlhy, tsaf zai bibiyemu”. “kai dalla ai yanzu bashida wannan damar, caza'ayi a fad'ama police, sukuma aikinsu zai farane zuwa safiya, kafin sannan munma gama binne gawar yaran mun kama gabanmu”..... “eh kumafa hakane”. Suna tsaka da wannan hirarne su Galadima suke shigowa, gidan k'aton gaskene dan haka suka kasa fahimtar INA zasu dosa, Galadima Yakuma danne abin kunnensa da d'anyatsa d'aya cikin murya k'asa-k'asa yake fad'in “Sauban kufara muje”. “yauwa Yaya zaku shiga hannunku Na haggu, duk sunajin maganar dan haka sukabi hannun haggu, yayinda su Ameer ke binsu a baya suma. Galadima dake gaba ya bud'e k'ofar a hankali duk suka shiga, daga can Saleem yace, “duk Ku rarrabu sir, dan abin ya nuna yaran suna ainahin tsakkiyar gidanne”. Batare da sunyi magana ba duk suka rarrabu. 'Daya acikin 6arayin yace, “kai nifa kamar motsi nakeji gaskiya”. “to sannu mai kunnen maciji”. cewar d'aya aciki. Cikin matan d'aya tayi dariya tana fad'in “nakula kaidai bibo matsoracine halan?”. Hannu ya d'aga zai kwad'eta, a harzuk'e yana fad'in “k wlhy kacaccalaki zanyi, bar ganin kinfito daga masarauta, kubadan ma an had'amu aiki dakuba kun Isa saninmu ne? jimin y'ar iskar mara kunya”. Hak'uri y'an uwansa suka bashi, ya mik'e yana jan tsaki ya fito danya duba. Galadima dake la6e cikin labule yay saurin fitowa, abinka da dogon mutum dan danan yasamu damar shak'osa ya shaka masa abin hannunsa, tun yana k'ok'arin kare kansa har jikinsa ya saki ya kwantar dashi a k'asa. Jinjina Muftahu dake kusa dashi yamasa, sannan suka cigaba da shiga. 'Dayar baiwar tana kitchen tare da wani suna iskancinsu Nuren yasamu damar sad'ad'awa, (kunsan dai shahararren kidnapper ne🤭😂) yauma tsiyar ya aikata wajen jefa ma namijin handkerchief a fuska, macen tai yunk'urin zuba ihu yasa k'afa ya tad'ota ta fad'in, sannan ya danne bakinta da ya shak'a mata itama. K'arar fad'uwarta taso fargar da sauran, dan haka duk suka mik'e suna fara lek'e-lek'e, aikam Muftahu yasamu ya tad'e d'aya ya fad'i, Ameer dake bayansa shima ya shak'a masa, harda mangareshi yana fad'in “kwallon shege taka ta k'are, inakai ina satar sarakunanmu insha ALLAH”. dariya taso kufcema Muftahu amma ya danne bakinsa da hannu yana girgiza kai saboda tsiyar Ameer. Fad'uwar wani da suka juyo ya sakasu kuma saurin waigawa wajen, Galadima ne ya sakeshi ya fad'i, “shegen k'arfin jinine dashi dak'yar abin yay masa tasiri”. Galadima ya fad'a yana halbinsa da k'afa. Gaban d'ayar baiwar dake la6e jikin labule ya fad'in, dan tabbas wannan muryar Galadima ce, kowa yasan bai iya R ba, zuface tashiga keto mata jikinta na 6ari, ta to she bakinta saboda kuka daya kufce mata, saigata tana tsilala fitsari saboda ganin Galadima yanufo ta wajen, shikenan itakuma tata tak'e, wannan zakin gagara badau d'in binneta kawai zaiyi da ranta. Waige-waige Galadima ya fara saboda jin numfashin mutum dayakeyi kad'an-kad'an ta wajen, har yayi gaba ya dawo baya yana yaye labulen wajen. shi da farkoma ya zata aljanace saboda yanda ta zazzaro masa ido. fincikota yayi ya Watso tsakar d'akin, mamaki ya kamashi ganinta da kayan manyan kuyangin gidansu. “tashi tsaye”. ya fad'a cikin matuk'ar d'aure fuska, kad'an yarage kashi ya kufcemata. “ina suke!!!”. Yafad'a cikin matuk'ar tsawa daya firgita hatta su Sauban dake saurarensu a waya. Wannan tsawar tasa ce ta saka d'ayan fitowa a tsorace da gun a hannu, Aunty Salamah dake bayansa bai saniba ta hankad'ashi yay gaba zai fad'in, Nuren ya ida tad'eshi da k'afa. Gun d'in data fad'i ta silalo gaban Galadima ya taketa da k'afa yana huci da taunar lips. Handkerchief d'in hannunsa yasaka ya d'auki bindigar, ya saita namijin da ita. Mazari jikinsa ya fara yana d'aga hannu sama, “dan ALLAH ranka ya dad'e karka kasheni, wlhy bansan komaiba, oganmu ne yasan komai da wannan baiwar”. Kunamar bindigar Galadima ya d'ana, nanfa su Muftahu duk suka rud'e, Nuren yace, “Brother please karkayi harbi, nasan zasu fad'a mana, dan ALLAH kayi hak'uri”. Gaba d'aya jijiyoyin kan Galadima sun mimmik'e, sai fidda huci yakeyi a wahalce. Muftahu ma yashiga rok'onsa, Su Saleem dake sauraren komai dagacan duk suka rud'e, Sauban yace “yaa Sam ALLAH ya huci zuciyarka, amma idan ka aikata haka a wajenwa Zamu samu hasken sauran abubuwan?, dan ALLAH kayi hak'uri badan mun isa mu saka ka ba, saidan halin da mahaifinmu ya tsinci Kansa tsawon shekaru, gakuma dama tazo mana ta Sanin sirrin 6oye, muyi amfani da ita ta sauk'ak'ak'iyar hanya....” Sakin gun d'in Galadima yayi ak'asa yana dafe k'irji, wani mugun bugawa zuciyarsa keyi, da baya-baya yanemi zubewa a k'asa, cikin hanzari Nuren da Muftahu suka taresa, da taimakonsu ya zauna akan kujera. Yana nuna baiwar da d'ayan hannusa. Aunty Salamah data fahimci mi yake nufi tace, “ina yaranne?”. Jikin baiwar Na 6ari ta nuna k'ofar wani d'aki, shiga Aunty salamah tayi itada Ameer suka d'akkosu. Saidai duk a firgice suke, dan yaran babu alamun rai tare dasu, zufa ta shiga ketoma Aunty Salamah, haka ta fito rungume da Abdurraheem da Amaturrahman, shikuma Ameer ya d'akko Abdurrahman yana fad'in “Aunty kamarfa yarannan sun mutu”. Wannan kalma caraf a kunnen Galadima. Wata muguwar zabura yayi yamik'e tsaye, sai ya kuma dafe k'irjinsa da sauri hajijiya tafara katantanwa dashi, basu fargaba sai jinsa sukayi kawai a k'asa. Gaba d'aya suka kuma rikicewa, sukayi kansa. Muftahu yace, “bamuda isashen lokaci, asuba ma ta gabato, dolene mubar gidannan dan ko yaushe zamu iya gamo da abinda bamu shirya masaba”. Duk sunyi na'am da wannan maganar tashi, nan fa suka fara kwasar wad'anda suka sumar suna kaiwa mota, sannan suka tasa k'eyar d'ayar baiwar da wancan, suma. Yayinda Nuren yad'an bincika gidan, ganin babu wani abunda zasu k'aru dashi yazo suka kama Galadima daya Suma suka fita dashi. Hankalin Sauban ya tashi matuk'ar tuk'ewa, ya fito yana nufarsu da ta6a jikin d'an uwansa, “Yaa Nuren miya farune? miya faru da Yaa Sam?”. “Sauban bamu hanya, ba lokacin wannan baneba yanzu”. Sole Sauban ya matsa baya hawaye Na kwarara a idonsa, suka shinfid'ar da Galadima a bayan mota, sai lokacin Sauban yaga yaran a hannun Aunty salamah da Ameer, da hanzari suma ya nufesu, Aunty salamah ta bashi Abdurraheem, jujjuya yaron yayi yaji kamar baya numfashi, “innalillahi....” yashiga maimaitawa zufa Na keto masa, dolene Yaa Sam ya suma, hawaye yafarayi yana rungume yaron a jikinsa, Tausayin dukkan ahalinsa da suka kwallafa rai ga yaran ya kamashi, musamman ma iyayensu, ya ALLAH nasan bazaka jarabcemu da abinda bazamu iyaba, ALLAH kabamu juriya”. Muftahu yace, “su shiga mota, duk shiga sukayi, Nuren dasu Ameer suka wuce da wad'ancan sauran wani waje daban, Muftahu kuma ya kira police d'in da suka shirya komai dasu, a hanya suka had'u, sai sukai joining d'insu tamkar tare sukayi aikin, suka kira manyansu suna sanar musu gashifa sun kama wani matashi da baiwar masarauta da yaran.... Wannan labari yama su d.p.o dad'i ya kira IG shima ya sanar masa, yaji dad'i shima, koba komai mai martaba zai yaba k'ok'arin dasukayi, akace yanzu suna inane?. Amsawa sukai da gasu a masarauta, dan harda Galadima sukayi aikin, yana kuma cikin wani yanayi shida yaran yanzu haka. Basuda za6in daya wuce suce musu to suma gasunan zuwa masarautar. Tun'a mota su Muftahu sun gargad'i baiwar nan da d'ayan mutumin akan suce su biyune suka sacesu, inhar sukace basu kad'ai bane wlhy saiya kashesu, sannan su tanaji fad'ar wani abun ba ainahin gaskiya ba, (dan Galadima baya buk'atar police su shiga cikin aikinsa yanzu, yafison saiya kama kowa sannan, dan inhar police suka shiga aikin mutane da yawa zasuyi escape ne) shiyyasa Muftahu yayma wad'ancan gargad'in tunma kan su k'arasa cikin masarauta. Da yawa wasu basu rintsaba a masarauta gagara badau yau. Munaya dai dole aka sake d'irka mata allurar barci mai k'arfi, dan kusan kuma haukace musu tayi gabannin asuba, dalilin wani barci daya figeta tayi mafarki mai matuk'ar tada hankali. Su inno Na zaune har yanzu suna kai kukansu ga ALLAH Muftahu da Sauban suka shigo d'auke da Galadima da suka kamo tamkar gawa, sai Saleem da police biyu dake falo d'auke da yaran sukuma. Zaram duk suka mik'e suna tambayar lafiya? Miya sami Galadiman?. Basu sami wata amsaba, saida suka kwantar dashi a gadon sannan Sauban ya share hawayen fuskarsa yana fad'in “suma yayi inno”. Aunty Mimi da mom sukayi kan Galadima suna kuka, inno tace, “kun samo yaranne?”. “eh gasu can a falo tareda police, saidaifa duk sun mutu, shiyyasa ma Yaa Sam ya suma”. yak'are maganar yana kuka. Hawaye suka zuboma inno, waya ta d'auka ta kira papi, Wanda shima dai a zaune suka kwana dagashi har Sarki jalaludden. A time d'in dama har ankai musu bayanin shigowar su Muftahu d'in. Yau dai kam tilas Manyan Sarakuna biyu suka nufo sashen Galadima da Kansu, abinda waninsu bai ta6a yiba kenan. Maganar ganin yara yafara baje Masarautar tun'a daren, dan kowa kunenensa a bud'e yake, da masu fatan a gansun da masu fatan kar'a gansun. Lokacinda papi da mai Martaban suka iso Inno Na rungume da yaran duka tana hawaye, sukuma su Aunty Mimi suna bedroom wajen Galadima. Kusan a tare Akash da Dr jalal suka iso dasu papi. Mai Martaban da papi suka kar6i yaran daga hannun inno, Suna zama bisa kujerun. Akash wajen Galadima ya nufa, dukda ba shine likitansa Na zuciya ba zai iya bashi taimakon gaggawa, shikuma Dr jalal ya fara kar6ar Abdurraheem dake hannun inno, yan d'ube-dube, yayi Na tsawon lokaci kafin ya ajiyeshi ya kar6i Na hannun mai Martaban, shima yagama duk abinda ya dace ya kar6i Amaturrahman a hannun papi, ajiyar zuciya ya sauke yana fad'in “Alhmdllh duk basu mutuba, allurar barci mai k'arfi sosai suka musu, shiyyasa numfashinsu yay nisa sosai, danta musu k'arfi da yawa, amma idan kuka saka kunne nawasu mintuna saitin jikin zuciyoyinsu zakuji suna motsawa kad'an-kad'an, sai dai ta wannan tafi yin k'asa sosai gaskiya”. Ya nuna Abdurraheem dake hannun inno. Su mai Martaban suka sauke ajiyar zuciya suna hamdala ga ubangiji. A cikima Akash nata iya bakin k'ok'arinsa ganin Galadima ya farfad'o, Ahaka su mai Martaban suka k'araso cikin d'akin d'auke da yaran a hannun, Munaya Na gefen Galadima an lullu6a mata bargo batasan wainar da ake toyawa ba, dan barcin nata shine mafita fiye da zama ido biyu. A gadon suma yaran duk aka shimfid'esu, Dr jalal yad'an musu dabarun likitoci sauran kuma aka barma ubangiji ikonsa Na jiran farkawarsu. Hankali kuma duk saiya koma ga Galadima da aketa fama. Har aka kirayi sallar Asubahi babu amo babu labari akan farfad'owar tasa. daga k'arshe dai Akash saida ya kira likitan Galadima na zuciya. Shiya dunga fad'ama Akash d'in yanda yadace yayi, lokacin shiga salla ya saka su mai Martaban fita masallaci dole, sukabar Akash da Dr jalal dake taimaka masa suna aikinsu, saisu Aunty Mimi da suka kasa matsawa ko nan da can, Sauban ma da k'yar su papi suka lalla6asa yabisu salla. Har gari ya waye sashen Galadima ya cika da manyan masarautar irinsu mama Fulani matan Sarki da sauransu Galadima babu wani bayani, zuwa yanzu ma wasu sun fara tunanin kodai yama mutu ana 6oyewane kawai. Wajen 8:00am Dr Yaseen Ali Modibbo babban likitan zuciya da akeji dashi ya iso, bisa kiran da Dr jalal ya masa yafad'a masa, dan abubuwan da sukaima Galadima bai farfad'oba Akash yakuma sanarma likitansa, shine yace tofa gaskiya Kodai asamo ainahin likitan zuciya ko kuma su taho dashi kafin cikar awanni 12, idan ba haka ba komai zai iya faruwa. A k'iyasin da sukayi cikin awanni 12 bazasu Isa india ba, tunda duk tsiya sai an samu jirgi mai tafiya, sannan ma kafin komai ya biyo baya. Hakkane yasaka Dr jalal kiran Dr Yaseen Ali Modibbo d'in, cikin amincin ALLAH kuma ya amsa zaizo d'in, saikuwa gashi ya iso. Canjama Galadima d'aki akayi, dukkan kayan aikin da Dr Yaseen yazo dasu aka shigo dasu, rufe d'akin sukayi suka duk'ufa su uku kansa suna taimakon Dr Yaseen d'in. Sun jigata kwarai da gaske kafin zuciyar Galadima tafara bugawa k'asa-k'asa, sai numfashinsa yafara fisga yana k'ok'arin fita. Duk ajiyar zuciya suka sauke. Suka cigaba da aikinsu, ana sakama Galadima wani abu a k'irji kamar dutsin guga, saiya girgiza sannan a cire, akuma maidawa. Basu barsa ba saida yasaki wata ajiyar zuciya mai matuk'ar sauti, harsu mai Martaban dake falo saida suka jiyosa kuwa. Wannan ne yasaka zukatan doctors d'in uku sanyaya, Dr Yaseen da Dr jalal suka had'a baki wajen fad'in “Alhamdulillah!”. Numfashin Galadima ya dawo dai-dai, amma sun masa allurar barci danya samu nutsuwa. Yaranma an kawosu ne Dr Yaseen ya kuma bincikawa, shima dai yace suna da ransu, amma Abdurraheem yanada ciwon zuciya shima, shiyyasa yafi sauran y'an uwansa jigata, ALLAH nema dai yay rabon yanada sauran numgashi, amma allurar tamasa k'arfin da zata iya dakatar da bugun zuciyarsa. Suma dai sun kuma samun taimako, musamman ma dai Abdurraheem da tausayinsa ya kama mutane da yawa a wajen. *_2:00pm_* Zuwa wannan lokacin Munubiya da mama Rabi'a da Ayusher Feena duk sunzo masarautar, Hakama baba k'arami da daddy, dan an sanar musu samo yaran da halin da galadima yake ciki. Amma saboda kara irinta Abba da innarsu Munaya sai suka bar su Baba k'arami da maman Fauziyya da mamansu yaa Hameed, maman Safara'u suka taho, sai innaro da gwaggo Safiyya. Ba'a barin wani bak'on fuska shigowa masarautar a yau, amma su sai mai Martaban yasa aka shigo dasu, basu samu ganin ko d'aya a cikin su Munaya ba, saidai Munubiya da aka shigar d'akin galadima inda Munaya ke kwance, Sauran kuma sun shiga ayarin y'an zaman jigum-jigum da jiran tsammani. Har zuwa wannan lokacin Galadima da Munaya babu Wanda ya farka, Amaturrahman da Abdurrahman dai sun farfad'o, sai dai suna kuka ko fita bayayi. Wanka laraba ta musu aka gasa musu jikinsu sosai, yau dai dole aka nemo madarar da Galadima bayason susha d'in, ita aka dama aka basu sukasha, aiko sun shata sosai dan yunwa sukeji, bayin ALLAH, rabonsu da abinci tun jiya da rana kusan I war haka d'in. Tausayinsu ya kama Munubiya dake basu madarar, tana yi tana sharar hawaye, da da farko nono inno tace ta basu, sai papi yace, “a'a kar ayi wannan gangancin, dan ba'asan abinda ALLAH zaiyiba wataran, ko akwai k'addarar aure a tsakanin yaransu, kar azo ayi Dana sani a watarar da baza'a iya maido wannan ranarba balle a gogo 6arnar da akayi”. Kowa ya gamsu da wannan magana, dan haka Muftahu yafita suka nemo madara shi da Saleem. Shine aka basu. Baiwar da aka kami da mutumin kuma suna hannun police, kuma kowa yaji cewar tana cikin bayin gidan wad'an da aka aminta dasuma sosai, saidai ba'asan ta wane sashe bace. Wannan Abu ya tsurar da zukatan Sauran bayin, dan dolene ya shafesu. Hankalin Uwargidan Sarki Sarauniya Zulfah (mahaifiyar su matawalle) a tashe yake, amma dayake ta iya takunta bazaka ta6a fahimtar haka ba, saima nuna tsantsar damuwarta akan lamarin da tayi fiye da sauran matan Sarki. dama kuma tafi nuna kulawarta ga Galadima kowa yasan wannan, shiyyasa babu Wanda yakawo wani Abu game da ita, saima wasu daban ake zargin. Munaya da Galadima sun farfad'o ne kusan time d'aya, amma Galadima ya riga Munaya, dama allurar awanni 4 kacal aka masa, da Sunan ALLAH a bakinsa ya farka, sannan yafara kiran yaransa d'aya bayan d'aya yana fad'in karsu tafi su barsa.. Rik'eshi Dr Yaseen yayi yana fad'in “ka kwantar da hankalinka ranka ya dad'e, dan zuciyarka tana cikin yanayin jiran k'iris ne, inamaka albishir da cewar yaranka suna raye, yanzu nan zakagansu insha ALLAH”.. Galadima ya sauke nannauyar ajiyar zuciya yana kallon Dr Yaseen, ya lumshe idonsa a hankali sannan ya bud'e, hanunsa ya d'ora akan saitin zuciyarsa saboda wajen yamasa matuk'ar nauyi. Ana haka Dr jalal ya shigo d'auke da yaran biyu, dan Abdurraheem shi yanan a d'akin kusa dashi bai farfad'o ba. Tunda Galadima yaga yaran sa suna a raye saiya kuma rungumesu a k'irjinsa da Dr jalal ya d'ora masa, wasu hawaye masu zafi suka gangara gefen kunnensa. Dr Yaseen yaji dad'in kukan da Galadima d'in yakeyi, dan zai rage masa rad'ad'in da yakeji da nauyin zuciyar, hakan ya nuna aikinsu zaiyi k'yau insha ALLAH. Galadima ya dad'e rungume da yaran, saidaga baya ya farga babu guda d'aya. A hankali ya bud'e baki yana fad'in, “ina d'ayan?”. Murmushi Dr Yaseen yayi, yace, “gashi a gefenka yana barci shima”. Juyawa Galadima yay ya kallesa, ganin d'an cikin yaron Na motsi alamar fitar numfaahi sai dad'i ya kuma ratsashi, ya lumshe idonsa yana yun k'urawa zai tashi zaune, taimaka masa. Dr Yaseen yayi, yatashi rik'e da yaransa, kwantar dasu yayi sannan ya matsa ga Abdurraheem hannunsa dafe da k'irjinsa har yanzu, rankwafawa yay kan yaron ya sumbaci goshinsa da kumatunsa, sannan ya shafa kansa la66ansa suna motsawa alamun yana masa addu'ar fatan samun lafiya a garesa shima. A 6angaren Munaya Itama tana farkawa da kuka ta farka, tana kiran yaranta, itadai afad'a mata idan sun mutu kawai saita hak'ura. Rungumeta Munubaya tayi tana lallashi da mata albishir d'in dawowar yaran garesu, hakan yasaka Munaya d'agowa da sauri tana kallon Munubiya, “Sweetheart da gaske kikeyi?”. “da gaske nakeyi Sweetheart, yanzu haka suna tare da mahaifinsu”. Dad'i ya ratsa Munaya, ta kuma k'ank'ame Munubiya suka rungume juna suna kuka da dariya lokaci d'aya. Hakan kuma saiya sanya su inno kukan tausayinsu da sha'awar wannan k'aunar juna nasu. Saboda su mai Martaban sun shiga wajen Galadima sai akace ita Munaya tayi wanka kozataji k'arfi kafin su fito. Bata musaba ta amince, ruwa mai zafi laraba ta had'a mata, tashiga wankan. Tanayi tana kukan farin ciki. bata cuci kantaba tayi wanka sosai ta gasa jikinta. Kafin ta fito an gyara d'akin tsaf, sai k'amshin daddad'an turaren d'aki yakeyi, babu kowa duk sun fice. Su mai Martaban suna tare da Galadima, sunyi farin cikin tashinsa, hakama yaran. sunkuma yima Abdurraheem addu'ar tashi shima. Sun d'an jima a d'akin, dan har saida aka shigo dasu Dady da baba k'arami, Yaa marwan, Yaa Hameed suma suka gaidashi da masa jajen ALLAH ya kiyaye gaba sannan suka fita gaba d'aya. Daga nan manyan irinsu mama Fulani, inno matana Sarki da sauran su duk suka shigo suma, harda su innaro da akaita kuka. Galadima dai Kansa kawai yake iya d'agawa, idonsa a lumshe. Baya buk'atar kallon kowa a cikinsu. Su inno duk tausayinsa ya kamasu. Innaro aka share hawaye tace, “barka da arzik'i kaji, ALLAH ya kiyaye gaba, ya shiga tsakanin nagari da mugu, ya tona asirin duk makirin dake cikin wannan satar yara”. Duk da amin suka amsa. Galadima ma yace amin akan la66ansa. sai tunani yake ina Munaya take?, dan hankalinsa yafara tashi da rashin gilmawarta, musamman daya tuna a halin daya tafi itama ya barta. Yadai kasa daurewa ya bud'e baki da k'yar yace, “Mom ina Munaya wai?”. Saida mom ta matso da kunnenta sannan tajishi, tasan yana lafiya ma ya aka k'are da k'asaitar magana balle yanzun. Murmushi tayi, tace, “tana d'aki, itama sai yanzu ta farka, dan dole aka sake mata allurar barci bayan tafiyarka, waccan bata dad'eba ta saketa”. Tausayin Munaya ya kuma kamashi, ya jinjina kai yana yunk'urawa zaune sosai. Cikin yamutse fuska yace, “Mom nima yakamata nayi wanka Na rama sallolin dake kaina”. Mom tace, “to bara a kira su Muftahu su kamaka ”. Kansa ya girgiza mata da mata alamar, zai iya da kansa. Mom tace, “Alhmdllh”. Rigarsa ya jawo yasaka, dan da dagashi sai best. d'aukar Abdurrahman da Amaturrahman yayi ya fito, yabar mom tana gadin Abduraheem dabai farko ba. babu kowa a falonsa Dan duk sun fice. Da k'afa ya turo k'ofar, Munaya Na zaune a bakin gadon rik'e da mansa zata shafa amma dukta kasa, burinta taga halinda Galadima da yaranta suke ciki kawaine damuwarta, gashi har yanzu babu Wanda yazo yakirata akan su papi sun fita. bud'e k'ofar ya sakani d'ago ido. Zummbur na mik'e tsaye ganin Galadima rungume da yaran, ai yau nama manta dawata kunyar towel na d'aura, hawaye suka shiga zarya tsakanin idona da kumatu, Galadima ya tako a hankali zuwa gareni idonsa a kaina. Da sauri namatso garesa nima, nahad'ashi shi da yaran na rungume ina sakin kuka mai k'aramin sauti. Shiru yay kawai ya zubama gashinta ido yana tausaya mata daga ita har yaran, ansakasu a yak'in dabasu San mafariba, ya godema ALLAH da yarannan sunada sauran numfashi a duniya. Da baisan yanda zaiyi da munaya ba. Ganin kukan nata zaiyi yawa ya bud'e baki da k'yar yace, “ya isa mana”. d'ago idanu nayi na kallesa, cikin muryarta data dishe saboda kuka nace, “Nagode yalla6ai, dasun mutu nima mutuwa zanyi”. Murmushin gefen baki yayi, cikin d'age gira d'aya yace, “dama ana sonmu haka?”. Sai yanzu kunya ta kamani, nai k'asa dakai ina kallon k'afafunmu. Bai sake cewa komaiba ya ra6a ta gefena yaje ya shimfid'e yaran akan gado. bathroom ya nufa yana cire rigar jikinsa, nidai Na k'arasa gadon Na rungume yaran ina sumbatarsu, wani dad'i da tsantsar farin ciki Na ratsani, Na d'aukesu Na fara shayar dasu ko zasu rage nauyin da sukamin, aikam kamar jira sukeyi suka kama sha. Hannun rigar namijin Na d'aga saboda tanan muke gane shaidarsu, ganin Abdurrahman ne saina fara tunanin ina Abdurraheem shikuma?, hankalina yaso tashi amma saina daure ina jiran Galadima ya fito naji daga garesa. Galadima dake kallonta bata saniba ya d'an cije lips, ya tabbatar yanzu tana son yaransa, amma baisan miyasa take ignoring d'insu ba idan yana waje? Kokuwa tsabar jan ajinne oho?. Har Lokacin daya fito wankan tana shayar dasu, ta shafa kan wannan ta shafa Na wannan, sosai suka birgeshi itada yaran, jin kamar motsi yasakani kallon wajen, da sauri na janye yaran daga bakin nono naja towel d'in na rufe abinna ina turo baki gaba. Baki ya ta6e yashiga takowa inda muke, ya rankwafo kaina ruwan fuskarsa yana d'iso min a jikina, a kasalance yace, “wane darene jemage bai ganiba malama, tunkan su sha ni........”. Da sauri na saka hannu na toshe masa baki. Zama yayi yana janye hannunna, cikin waro idanu yace, “to mikike tunanin zan fad'a? lallai kinfi k'arfina, niba can Na dosaba to”. Sosai naji kunya, na sauke yaran a kan gadon na sakko, zuciyata cikeda mamakin sa, ya d'aure fuska yana basarwa yayta sakin magana kuma kamar bashi yayiba. Ficewata nayi bayan na d'auki bathrobe d'insa na d'ora akan towel d'in jikinna. Wani kallo ya bita dashi yana ta6e baki, kafin ya maida ga yaransa daketa kalle-kalle, ya shafa kumatunsu sannan ya mik'e zuciyarsa na tunanin su Momma, addu'arsa d'aya kar wani ya sanar musu. Kasa fitar nayi saboda jin kamar da mutane a falon da zanbi ya sadani da 6angarena. Badan nasoba tilas Na dawo baya. Galadima dake gaban mirror yana shafa mai yana kallonta ta ciki, amma sai yayi biris tamkar bai gantan ba. Komawa nayi na zauna a bakin gado ina tunanin mafitar yanda zan samu kaya, da jin haushin sharenin da yayi. Ana haka mukaji knocking, saida ya kalli Computer d'in yaga Mom Ce d'auke da Abduraheem sannan ya mik'e yana amsawa.. Zuwa yay ya bud'e mata, bata shigoba ta mik'a masa yaron da har anmasa wanka Ashe, ta mik'a masa kaya a leda tace na Munaya ne. Galadima yace, “mom ya tashine?”. “ya tashi, tunma fitowarka babu dad'ewa, harma an masa wanka”. Sumbatar kumatun yaron yay yanama mom sannu Idonsa akan yaron yana kuma sumbatar goshinsa cikin lumshe idanu ya k'araso inda nake dana zuba musu idanu cikeda sha'awa. Kusa dani ya zauna ya d'ora minshi akan cinya. nima rungume kayana nayi na sumbaci goshinsa, inason bashi abinci amma inajin kunyar Galadima, gashi ya zubamin ido yak'i tashi. Lura da hakan dayay ya sakashi yin miskilin murmushi ya mik'e yabar wajen. d'an hararan bayansa nayi ina fad'in mugunta dai babu k'yau a kan la66ana..................✍🏻 “Hummm fans nasan kwace wai ina Harun ne?🤔, kumuje zuwa dai danjin ina ya shige haka? Ita kuma sarauniya Zulfah (uwar gidan Sarki mike matsalarta)?.😨😏 *_Ya Rabbi ka gafarta ma iyayenmu_*😭👏🏻 [7/17, 6:21 PM] Aysha Galadima: *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻2⃣8⃣ ............A yanda Na kula har yanzu bayajin dad'in jikinsa, dan komai a d'an wahalce yakeyinsa, koda ya fiddo kayan daga wardrobe saiya dawo bakin gadon ya zauna ya dafe Kansa, kallonsa nayi cikin damuwa nima, Na cire Abdurraheem Na kwantar, sannan Na mik'e zuwa garesa, durk'usawa nayi Na d'ora hannayena akan gwiwarsa, “yalla6ai lafiya?”. Shiru yamin kusan minti 1, harna fidda ran samun amsa ma na yunk'ura na mik'e da nufin barin masa d'akinma duka. Hannuna ya rik'o, na juyo na kallesa, har yanzu yana yanda yake baiko d'ago motsa ba. Na cije lips ina had'iye kukan dakeson zubomin, rayuwar nan tasa bana sonta wlhy, ni y'ar dangi Ce, nariga natashi gidan yawa, dukda gidanmu bahagon gidane mukanyi hira koyayane, amma shifa magana ma idan bai ra'ayiba wahala take masa, Abu na damunsa a rai amma bazai iya fiddashi yaji sauk'iba, Momma ta had'ani da aiki, a watannin baya kad'an kamar yafara canjawa, amma gashi yakuma birkicewa yanzu, tayaya Momma take tunanin zan iya canja Galadima? murd'ad'd'en mutumne shi mai wahalar sha'ani, ga tsantsar mulki da k'asaita da suka zama jinin jikinsa, s......... Tunanina ya katse lokacin danaji an jawoni, nai firgigit saboda fad'awa danayi jikinsa, shikuma yay baya ya fad'a kan gadon, kad'an ya rage mu danne Amaturrahman, yad'an kauce kad'an yana sauke ajiyar zuciya. Uffan bai ceminba ya maida idonsa ya lumshe. Mamakin wannan lamari ya kamani, hannu yasaka ya kwantar da kaina a k'irjinsa yana d'an buga bayana da d'ayan hannun, zanyi magana ya d'ora yatsunsa hannunsa uku na tsakkiya akan bakin alamar nayi shiru. banida za6in daya wuce yin shirun, nabisa yanda yakeso. Yanayin da zuciyarsa ke bugawa sai yabani tsoro, na saka hannuna na danne wajen sannan na d'ora kaina bisa hannun, ajiyar zuciya yayi yana cizar lips.. Tsawon mintuna 3 muna a haka, har knocking d'in k'ofa akayi amma baiko motsaba bai barni na motsaba, na yunk'ura zan tashi ya maidani. Munkai mintuna 7 sannan ya zameni ya kwantar ya mik'e zaune, batareda ya kalleni ba ya sauka daga gadon, bathroom ya Shiga, babu dad'ewa ya fito, nidai kallonsa kawai nake da mamaki, Dan fuskarnan amatuk'ar d'aure take tamkar baisan minene dariyaba a rayuwarsa, ya shinfid'a abin salla, domin rama sallolin da suka riskesa yana barci. 6oyayyar ajiyar zuciya na sauke, na tashi zaune idona akan yaran, duk sun koma barci, na tsurama Abdurraheem ido, saboda fitar numfashinsa ta banbanta dana y'an uwansa, tunani nai ko yanayin nasa barcin kenan shikuma, saboda wahalar da suka sha, d'aukar ledar kayan da mom ta kawo nayi, na fiddasu na saka, ban jira ya idarba na fice abina. Nayi mamakin da yanzu babu kowa, harsu Munubiya sun tafi, haushi ya kamani kamar zanyi kuka, aidai sa jira na fito mu gaisa ko? hawayen da suka zubomin a kumatu na share, namafi jin haushin Munubiya wlhy. Sallamar da akeyi na amsa da k'yar, sannan na bada izinin shigowa, cikin bayina ne guda biyu, zubewa k'asa sukayi suna gaisheni. Cikin girmamawa d'aya tace, “dama ance mu gani idan kin fitone”. Nace, “Hummm”. Fahinmatar iya amsar dazan iya basu kenan ya sakasu mik'ewa suka fita, zamewa nai na kwanta cikin kujerar ina cigaba da zirar da hawaye. Kusan mintuna 5 saiga Samha ta shigo, ta durk'usa gaban kujera tana sharemin hawayena, d'ago ido nayi na kalleta, namata murmushin k'arfin hali ina tashi zaune. Muryarta da alamun tasha kuka itama tace, “Aunty Uncle Sam na kiranki”. Kai na jinjina mata kawai, na tashi gaba d'aya na d'auki mayafi muka tafi tare. Koda mukaje k'ofar falon bata Shigaba, nikad'ai na Shiga ita kuma ta juya ta fice daga sashen gaba d'aya. A falo na iskeshi cikin doguwar kujera a kwance, ya kifa yaron d'aya a k'irjinsa Wanda nake k'yautata zaton Abdurraheem ne, wayace manne a kunnensa, amma a hankali yake magana koni danake tsaye cikin falon banaji, na kalli abincin da aka jere a tsakar falon ina zama a kujera. Bai dad'eba ya kammala wayar, idonsa dake jajir har yanzu ya d'ago yad'an kalleni, jijiyar kansa dukta tashi rud'u-rud'u. saida yad'an lumshe idanu kafin ya motsa la66ansa ahankali yace, “kici abinci inji inno”. Dukda maganar taban haushi haka na danne, wato inji inno ma ba injishi ba ko?. Sakkowa nayi k'asan lallausan carpet d'in, d'aya bayan d'aya na bubbud'e kulolin da kwanikan, a rai na ina tunanin ina zamu kai wanna abincin haka?. Tashi nayi zuwa ga show glass d'in dake falon, wadda aka jera mugs and glass cups, mug d'aya na d'akko, naje wajen wanke hannu dake a wajen dinning, Wanda babu tebirin cin abincin ba'a sakaba, bansan dalinsa nak'in sakawarba, wanko mug d'in nayi na had'o kayan tea a ciki dake a wajen show glass d'in suma, na zubo ruwan zafi daga dispenser na dawo, yana kwance yanda na barsa, yanzuma garda su lumshe idanu yanata shafa kan yaron zuwa bayansa. Na kallesa a d'arare Dan yaune karan farko dazan aikata hakan, komi yake buk'ata yakan yi da kansa, ko ruwa wannan inhar bana manta ba bai ta6a cewa na d'auka masaba, sometimes ma sai idan yasaka Samha ko Sauban su masa Abu saini na tashi nayi idan naga rashin dacewar hakan, amma dai dakansa yace Munaya yimin kaza, gaskiya bai ta6aba. muryata na rawa nace, “bismillah”. Shiru kamar bazai bud'e idonsa ba saikuma ya bud'e d'aya yad'an kalleni ya kauda kansa. cikin k'asaitar nan tasa yace, “miyasa?”. “miyasa kuma?”. ‘nakuma maimaita maganar ina k'ok'arin janye hannuna’. Carab ya rik'e hannun nawa, ni tsoroma ya bani, na kalli hannunsa da nawan ga mug cikeda ruwan zafi yanata turiri, kuma zafin yana ta6amin gwiwar yatsuna, idonsa a lumshe har yanzu, idona harya fara tara kwalla, nayi alk'awarin koda hannun zai toye gaba d'aya bazan tanka masaba, ai yasan abinda yake dai-dai da akasin haka. Saida mukayi 1minute a haka kafin ya maido face d'insa inda nake yana kallona, ya d'age gira d'aya yana fad'in “da zafi ne?”. Humm lallai Galadima akwai rainin wayo, na fad'a a zuciyata, janye idona nayi daga kansa na maida kan Abdurraheem dahar yanzu yake kwance a bisa cikinsa. Ya yamutse fuska yana sakin hannun, cikin basarwa yace, “inason jarumta”. Had'iye kukan dake k'ok'arin tahomin nayi, na ajiye Mug d'in na cigaba da zuba masa farfesu a k'aramin bowl batareda nayi koda tariba. Tashi yay zaune yana jije lips, yayinda hannunsa ke rik'e da yaron, d'ayan kuma ya dafe saitin zuciyarsa, a wahalce yake fisgo numfashi kafin ya fesoshi, tun kuma d'azu na lura da hakan, kalmar zafi daya fad'amin na shiga fassarawa, har na fahimci da manufa ya fad'a, hakanne ya Sani murmusawa batareda na d'agoba ina zuba masa farfesun nace, “tabbas duk zafi sunansa zafi, amma akan samu banbance-banbance wajen banbancesu, wani zafin a gangar jiki muke jinsa, wani ko tawani sashen jikin ake samunsa, wani zuciya, wani rayuwarma gaba d'aya Ce ke tsintar kan a zafi, saidai babu zafi mafi rad'ad'i daya kai na Mutuwa, idan da zamuyi nazari zamu fahimci rayuwa tana a tsare ne mataki-mataki, sannan iri d'ayace ga kowanne launin halitta na mutum ko aljan ko dabba, Dan mukan tainci kanmune akusan mizani d'aya, dukda ubangiji ya banbantamu ta halitta da ayyuka da tunani ko nace kaifin basira, ko'a jinsi launi biyune, akwai namiji akwai mace, dukkan rayuwa takan farane da mafari yalla6ai” na d'ago ina sake mik'a masa mug d'in tea d'in again, a mamakina a yanzu saiya kar6a, na lashi lips d'ina na k'asa ina gyara zama sosai da maida hankalina wajen juya kunun dana zuba a cup da tsokali, cikin nisawa nacigaba da fad'in, “mafarin rayuwa shine dasuwar bawa a cikin mahaifiya, mukanyi wannan rayuwarne a cikin halin su wanene mu? daga nan sai matakin haihuwa, shigowa duniya a bisa bigiren wane ahali muka kasance, dukkan ahalin daka Sani sunada matsalarsu, saidai tawasu tafi tawasu zafi, daga ranka ka iso filin gwagwarmaya wato duniya, shikenan littafinka dayazama rubutacce tun a cikin mahaifiya saiya fara aiki, mala'iku masu kula da fitar numfashi su dasa alk'alaminsu, masu kula da abinci suma haka, masu kula da ruwa ma haka, masu kula da magana ma haka, masu kula da kallo ma haka, masu kula da ji ma haka, masu kula da duk wani motsinka ma haka, tafiya, zama, kwanciya dadai sauransu, kowa ana haihuwarsa tsaftatatccene, iyaye suke fara juya akalar rayuwa, walau mai k'yau ko sa6aninta, (kaga kenan akwai hisabi tsakanin iyaye da y'ay'a ma kenan?) daga nan rayuwa zata cigaba da yad'o kamar d'an duma, tun ana maka, harka koma koya, harka fara iyawa da kanka, harma ka kware ka koyama wani, (wanne ka iya? ko ka koya? yarage ruwanka) duk Wanda kaga an masa a farko to tabbas za'a k'ara masa a k'arshe, kodai silar tsufa, ko ciwo, kokuma iftila'in rayuwa, kokuma na k'arshe shine hidimar gawarka, a dukkanin dunk'ulalliyar rayuwar da kowanne bawa yakanyi zakaga cike take da k'alubale masu zuwa da zafi kala-kala, yalla6ai kasan mike taushe wannan rad'ad'in zafin kuwa?”. nayi maganar ina d'ago ido na kallesa. A mamakina sainaga ya girgiza min kansa. na murmusa ina janye idona daga kansa na maida ga kofin tea d'in ina masa alamar yasha mana. Yamutse fuska yay irin kalar tausayinnan. Nima sainayi kwal-kwal da ido kamar zanyi kuka, na had'e hannayena waje d'aya alamar rok'o🙏🏼.. Lips d'insa yad'an ciza kafin yafara shan tea d'in. Nayi salute nashi ina masa jinjina👍🏻. Basarwa yayi, nima saina kad'a ido ina tunzura baki gaba, sannan nacigaba da fad'in, “Abinda ke taushe wannan rad'ad'in zafin shine *_HAK'URI_*. hak'uri muhimmun sinadarine dake jagorantar garkuwar jiki ta kowacce launin halittar jiki na d'an Adam, walau a fili take ko a 6oye take, saidai babban makarinsa da taskar adanashi shine *_ZUCIYA!_* a duk lokacinda k'arfin zuciya ya raunana to zaka samu madarar hak'uri ta salwanta, idan zafi yanata yawa babu wannan hak'urin bugu d'aya take duk wani ma'adani na cikinta saiya tarwatse, saikaga an rasa ayyukan jiki dana ruhi, shikenan wane yazama labari. daga lokacin da rad'ad'in fitar rai ya kusanci bawa dukkan mala'ikunan da suka kasance tare dakai a randa kazo duniya saisu fara janyewa daga gareka, wani bawan kafin ranar mutuwarsa zakaga ya daina cin abinci, hakan na nufin mala'ikan dake kula da abinci ka yagama aikinsa, domin ya zagaye duniya kaf duk yawan abincin dake cikin ta babu rabonka koda kwayan gero ne, ka gama cinyewa, wani kafin ranar Mutuwa ya daina shan ruwa, aikin mala'ikan dake kula da ruwa shanka yagama k'arewa kenan, duk yawan koramu da tafkuna na duniya bakada sauran rabo na ruwa, ka shanye naka, wani kafin Mutuwa ya daina magana, mala'ikan dake kula da furucinka yagama aikinsa, babu sauran wata kalma data rage harshenka ya furta, wani kafin Mutuwa ya daina ji, mala'ikan dake kula da jinsa ya gama aikinsa, babu wata kalma data rage kunnensa zaiji, wani kafin Mutuwa ya daina gani, mala'ikan dake kula da ganinsa ya gama aikinsa, kwayar idonsa bazata sake kallon wani abuba, wani kafin Mutuwa ya daina tafiya, mala'ikan dake kula da tafiyarsa ya gama aikinsa, haka-haka wad'annan mala'ikun zasuyita ja baya suma barinka, har yarage sai mai kula da fitar numfashi kawai, daga ranar da UBANGIJI yace yana buk'atar ganinka shikenan takuma k'are, sai rundinar mala'iku su had'u su takewa kwamandan mala'ikan d'aukar rai baya, idan kai mutumin kirkine fararen mala'ikune, idan na banzane mala'iku masu azaba zasu take masa baya, sauran al'amari kuma sai Wanda ya haliccemu yasan ya zata kasance😭. zakasha mamaki idanfa nace maka duk wannan zafin k'aramin zafine acikin kashi-kashin na abinda ya shafi haluttu, shi wannan zafin ana kiransa zafin na za6in kai, kokuma zafi na a haka tsarin yazo, ma'ana kaine ka had'ama kanka wannan zafin, kokuma wanine ya had'a makashi. Abu na biyu shine zafi na rad'ad'in Mutuwa, dolene kowa saiya d'an d'anashi, walau kafiri ko Musulmi, saidai akwai banbance-banbance na awanne tsari ka koma ga ALLAH, ba wannan zafinne kawai ke jiran d'an Adam ba, akwai zafin na *_BARZAHU_* shi ake kira kwanciyar kabari, mika tanada, mi zaka tarar shine abin tambayar, wannan kam ALLAH ne mafi sanin wad'anda zasu d'and'ana wannan zafin (ALLAH ka datar damu😭)”. Akan la66a Galadima ya amsa da amin, Munaya ta share hawayenta, ta cigaba da fad'in sai zafi mai gaba d'aya, shine na makoma, *_WUTA KO ALJANNA_*, yalla6ai wad'annan jimullar zafin ga d'an Adam tilas ne, na cikin rayuwa shine zafin da zaka iya controlling nashi ta hanyar hak'uri, to Ashe bai kamata ka tasirantar da wannan zafin ya cigaba da k'onaka ba, musamman idan zakayi dubi dawasu ni'imomin da ALLAH yamaka a cikin wannan zafin, ka kasance mai yawan hak'uri saikaga kanka cikin masu yawan riba, wlhy ta wannan hanyarne kawai zaka zama mai *_NASARA_* akan mak'iya ni..........”. Maganata ta katse saboda knocking d'in k'ofar da akayi, kallon juna mukayi ni da shi, yay wani luuu da idanunsa ya lumshesu, hakanne ya sakani bada izinin shigowa kawai batare da na jira amsa daga garesa ba. Sarkin k'ofane ya shigo, ya zube yana gaishe mu, nice kawai na amsa, boss kam hannu kawai ya iya d'aga masa, yay mana ya jiki again, nanma nice nakuma amsa shi, cikeda girmamawa yace, “ranki ya dad'e yalla6ai harun ne ke buk'atar iso”. Saida gabana ya fad'i, na had'iye wani yawu mai kauri ina kallon galadima dayay biris damu yanata shafa kan d'ansa, bud'e idonsa jajaye yayi akan Sarkin k'ofa, ya jinjina masa kai alamar ya shigo dashi. Kallonsa nayi tamkar zanyi magana saikuma nai shiru, a raina ina mamakin wannan munafukin dami yazo kuma?..... ban kai k'arshen zancen zucin ba Harun yay sallama, nid'ince dai na amsa cikin danne zuciya da fushina. Ya zauna fuskarsa d'auke da murmushi. Nima saina saki tawa ina fad'in, “barka da hantsi ranka ya dad'e”. “Barka dai gimbiyarmu, ya jikin ki dana yalla6ai?”. Na kalli Galadima dayay shiru kansan jingine da kujera ido a rufe, “da sauk'i”, na fad'a ina mik'ewa na koma saman kujera, dan bazan ta6a barin falonba sainaji uwarmi ya kawosa. Ya amsa da “masha ALLAH, ALLAH ya kiyaye gaba ya k'ara lafiya”. “humm” na fad'a ina amsawa da “Amin dai”. Hankalinsa ya maida ga Galadima, “Sameer ya jikin?”. Bud'e idonsa yayi shima, ya ajiye mug d'in hannunsa a teble d'in dake gefen damarsa, batare da yace uffanba ya sauke ajiyar zuciya yana taunar lips. Banga alamar damuwar rashin amsawar tasaba a fuskar Harun, dan yariga ya saba da halinsa. Saidai idonsa k'uri akan Abdurraheem dake cinyar Galadima d'in yana barci, mik'ewa yay yana fad'in, “my son zo mu gaisa ko?”. Ganin haka nima nayi azamar mik'ewa nakai ga Galadima kafin shi ya isa, na d'auke Abdurraheem d'in ina fad'in “ai barcima yake ranka ya dad'e”. Ba Harun ba hatta da Galadima saida yaymin kallon mamaki, nakoyi cid'in-cid'in da fuska yandama bazaice nabama Harun d'inba. Baki ya bud'e kamar zaice wani Abu saikuma yay shiru yana kauda kansa daga kallona, nima saina ta6e baki ina barin falon da harar Harun ta gefen ido. Gaban Harun ya fad'i, mi yarinyarnan take nufi?...... Kafin ya lalubo amsar ya tsinkayi maganar galadima yana cewa, “sorry Harun, kasan har yanzu a tsorace take, duk wani motsinsu akan idontane”. Murmushin basarwa harun yayi, yace, “ai dolene hakan ranka ya dad'e, abinne akwai tsoratarwa, wlhy jiya tashin hankalinnan ne yasaka azababben ciwon kai rufeni, shiyyasa ko ganina ba'ayiba, yanzu police d'in ina suka samosu?”. “humm” Galadima ya fad'a cikin tsananin taune lips da k'unar zuciya, ya bud'e baki a hankali zaiyi magana nida ke bayansu basu saniba nai saurin tareshi da fad'in “a hannun wasu munafukaine ranka ya dad'e, ai koni daza'a bani baiwar nan da aka kama da yaran wlhy saina tsoma kanta cikin drum d'in ruwa harsaita daina Numfashi zan barta, kafin sannan kuma nagamajin labarin Wanda ya sakata, amma shi my boss ai a station suka zauna har aka kawo yaran, badasu akaje farautarba”. Tsuramin ido Galadima yayi cikin tsagwaron mamaki, miyasa to zanzo na kasa na tsare dukkan wani motsin Harun d'in? ya kula satar yaran tana Neman ta6a tunaninta takasa banbance Wanda zata zarga, ai Harun yawuce ya 6oye masa wani sirri na sashen rayuwarsa, tun da babu abinda bai saniba na baya, saidai abinda ba'a rasaba kam, danne ransa yayi ya nuna hakane, yabari har Harun d'in ya tafi sannan yaji dalilinta. Ina kallon Sassanyar ajiyar zuciya da Harun ya sauke a 6oye, sannan yace, “ai police d'in sun cancanci Babar k'yauta, shiyyasama na shirya musu ita, sunyi aiki irinnan jaruman masu tsaro”. “hakane wlhy ranka ya dad'e ”. Na fad'a cikin murmushi. Dukfa yanda Harun yaso bugar cikin Galadima yaji yanda abun yake, na kafa na tsare, dayayi tambaya nike bashi amsa, saiya d'auka kodan Galadima bashida lafiyarne shiyyasa bai iya amsawa, tun da tunda ya shigo baice k'ala ba, kuma yasan yanayin ciwonsa, a baya ma shikan bashi taimako, baidai tsinci komai ba yay mana sallama ya fita, da k'udirin anjima ma zai dawo ne. A sace na raka bayansa da harara, sannan na kalli Galadima na basar, dukda kallon tuhuma dayake jifana dashi kuwa. Wani farfesun na sake zuba masa na mik'a masa. Batare da ya kar6aba cikin k'ank'ance idon bala'i yace, “mikikayi haka? kinsan waye Harun a wajena?”. Kaina na girgiza masa. Yaja tagwayen tsaki yana hararata, “halan satar yaranki yafara shafar tunaninki ne? kina tunanin akwai abinda Harun zai iya gazaji daga sirrina?”. Na d'an ta6e baki ina jawo teble d'in gabansa, na d'ora bowl d'in dana zuba farfesun, baki ya bud'e kamar zaiyi magana saikuma yay shiru. nima bance uffanba na ajiye masa sannan na koma k'asa Na zauna na zuba sabon kunu nahau sha. Kwafa yayi, yace, kinma maidani d'an iska ko?”. “Hummm” na fad'a kawai, naimasa kallo d'aya “yalla6ai wani karatun akan barsane a yanda yazo, sai idan lokacin fasaarashi yayi amasa fashin bak'i, nasan darajar alak'ata dakai batakai koda rabin tsakaninka da Harun ba, domin ni alak'ar wucin gadice ta had'amu, k'iris ma ya rage ta k'are, saidai inason nabama y'ay'ana kamar yanda ka fad'a kariya koda sau d'ayane a rayuwarsu kafin na barsu, dan haka maida wuk'arka a kube, lokacin zareta baiyiba, sometimes kalmar Mahangi da mai hange takanyi kamanceceniya, dan bakowa ke iya rarrabata wajen fasaara ba, amma kalmomine duka masu harshen damo, wani k'alubalen saida tunanin mai zurfi, wata k'oramar ruwan mutanen dake zagaye da ita sukanyi imani bazata balle harta cisu ba, saboda sun yarda sud'in masuntane da kullum suke rayuwa cikin wannan k'oramar, abin mamaki saikaga wataran an wayi gari da mutanen da muhalansu duk wannan ruwan ya had'iyesu, abinda basu ganeba bakowacce irin alak'a bace ake kulla amana da ita, wani farin idan yashiga cikin fari banbance k'arkonsa saidai ALLAH”. Tashi nayi nai shigewata bedroom d'insa. A fusace shima ya mik'e zai bini, kad'an yarage ya zubda farfesun dana ajiye masa, ALLAH dai ya kiyaye ya shallakesa ya wuce. Hucin mutum kawai naji a bayana, hakan yasani waigowa da sauri, hannu ya dunk'ule zai kaimin naushi, nai azamar fad'awa saman gadon ina zaro ido waje, a lallai Abu ya girmama, nikuma miye nawa da zai sauke fushinsa a kaina? nai maganar a zuciyata. Janye hannunsa yayi yana ciza lips d'in sa da k'arfi, idonsa dukya kuma rinewa, ya dunk'ule hannun ya daki d'ayan dashi, muryarsa har rawa take yace, “Miyasa zaki kuma hargitsan tunani ne? Minene laifin Harun shikuma? kuna nufin duk Wanda na yarda dashi shine mak'iyina? Kai impossible wlhy, Munaya wakikema aiki a kaina? ya rankwafo kaina, kaikace cinyeni d'anya zaiyi, saikace zaki yaga bandar nama, da k'arfi yace, “bazaki sanarmin ba saina k'arar da numfashinki ne waishin Ubanwa ke fad'a miki wad'annan maganganun da kike d'aureni dasu a ko yaushe?!!!”. Ya k'are maganar cikin tsananin tsawa da k'araji. Ba k'aramin firgita nayiba, badan karnayi k'arya ba danace har wutar bala'i Nagano a idonsa tana ci, wannan bawa akwai zuciyar tsiya, idan zai zama jami'in tsaro da k'asarmu ta amfanu da yawa......... Da k'arfi ya girgizani, saboda ganin saboda rainin wayo tunanima na tafi.......... A firgice nace “yi hak'uri zauna zan fad'a maka”. na fad'i hakanne dan kawai ina ganin itace mafitar dazan nema ya fasa had'iyeni. a mamakina kuwa saiya tashin ya zauna yana dafe k'irji hawaye nabin kumatunsa. Tsantsar tausayinsa ce ta kamani, na tashi na d'akko ruwa na dawo kusa dashi na zauna, addu'oi na shiga tofawa a ruwan, yana zaune dafe da kansa, da alama kuka ma yakeyi, dan ajiyar zuciyar da yakeyi ta yawaita. Saida na gama na dafa ka fad'arsa, tamkar bazai d'agoba saikuma ya kalleni, ruwan addu'ar na basa, babu musu ya kar6a ya shanye, duk da baima san mita bashiba, idanma poison ne dai gara ma yasha ya mutu ya huta. Mintunansa biyu zuwa uku dasha yafara sauke ajiyar zuciya mai k'arfin gaske, saiya zame kuma ya kwanta, kafin kacemi barci ya saceshi a haka. nima ajiyar zuciyar nayi ina girgiza kai da share hawayen dake silalomin, ina rok'on ALLAH ya kawoma wannan bawan nasa sauk'i da rangwame cikin gaggawa da warwarewar al'amura. Dagashi har yaran tausayi suke bani, nayi zurfi a tunani wayarsa tayi ring, kamar zan share saikuma Na tuna maybe Momma ce, tashi nayi zuwa inda wayar take, aikam dai itace, nayi picking jiki a sanyaye, dan tunanina kota gamajin komai, amma sainaji sa6anin haka, da y'ar raharta ma tace, “Muh'd duk hidimar sunance haka?”. “Uhm Momma bashi bane nice”. “a'a d'iyata kece?”. “eh Momma, kuna lafiya? ya jikin Abie?”. “Alhmdllh d'iyata, ya k'arfin jikinki kema? ina yaran?”. Gabana ya fad'i, Na had'iye wani yawu da k'yar, cikin in ina nace, “lafiyar kowa k'alau Momma, shima y... yana barcine”. Dagacan Momma ta murmusa tana gyara zama a harabar asibitin, dan batason Abie yaji wayar da zatayi, tace, “humm d'iyata kema 6oyemin zakiyi kenan? yanzu koda mutuwa yaran sukayi dashi kansa kowama saiya shiga fargabar gayamin?”. Na had'iye yawu dak'yar, “kiyi hak'uri Momma, ki gafarcemu”. “Bakumin laifin komaiba ni, hakan da Muh'd yay shine dai-dai, dan lokaci yayi dazai daina zama jiran sak'on mak'iya ko zuwansu, shine yakamata ya fita farautarsu domin kawo k'arshen komai, na yarda dake 100% Munaya, nakumayi imani insha ALLAH kece zaki sauyamin yaro daga k'uncin dayake ciki zuwa farin ciki, tamkar yanda Na fad'a miki tun farko karki ta6ama Muh'd sanya ko nuna tsoronsa, lokacin dazaki kwantar masa dakai kizama kowacce irin mace a agidan mijinta har yanzu baiyiba, kada ciwonsa yasakaki fargabar fad'a masa gaskiya, rayuwa da mutuwa duk Na ALLAH ne, ko ayanzu Muh'd yabar duniya bazanyi bak'in cikiba, domin ya nuna musu shi jarumine, kuma ya haifi wad'anda zasu iya zama magadansa su sauya komai koda ba'aso, nanda kwanaki biyu komai ya gama lafawa ki tabbatar kin masa maganar tafiya wanka gida, wannan shine target d'inmu Na k'arshe akan rayuwar zaman aure na dindin, kowacce irin birkicewa zai miki akan bazaki jeba, kema ki birkice masa, dan nasan abinda yafaru zaisashi dagewa akan yaran bazasuyi nesa dashiba, idan kuma har aka cigaba da tafiya a haka, kowane irin dana Sani zai iya biyo baya”. Momma ta share hawaye dake kwarara a idanunta, taci gaba da fad'in “ALLAH yayi miki albarka Munaya, dake da abinda kika haifa, yanda kikamin biyya wajen k'autata kar6ar Abu mai wahala (duk da bani na haifekiba) kema ALLAH yasa y'ay'anki sumiki biyyaya fiye da wannan, ALLAH yasaka hannu adukkan lamarinki keda mijinki da sauran y'an uwansa, nusar dashi abinda duk baki gamsu dashiba shine zai rage ma zuciyarsa baraza, dan tarawar yagani a lokaci d'aya shine mafi had'ari Munaya, zuciyarsa zata iya bugawa a lokacin, kiyi hak'uri nasan bak'yajin dad'in zama da Muh'd ko kad'an, domin ni kaina mahaifiyarsa wataran gaza gane kansa nakeyi, amma inaji a jikina akwai sauyi maiban mamaki dazai zo ya rusa komai, ki sameshi fiyema da yanda kikeso, ALLAH yayi muku albarka, idan ya tashi ki kirani naji ya jikin nasa”. Bata jira nayi magana ba ta yanke wayar, da alama kukane yaci k'arfinta. nima saina fashe da kukan ina kallon Galadima, insha ALLAH zan cikama baiwar ALLAHr nan burinta, koda ace mun rabu dashine, dan maganar gaskiya bazan iya rayuwa da mutum murd'ad'd'e mara yarda irin Galadima ba, labarinsa kawai kukeji, amma halinsa saika zuna dashi, Mara hak'uri zai iya gundurarsa ne cikin awanni biyu kawai, dan zaka dinga kallonsa a matsayin mai wulak'anci ko dizgi, girmankai da sauransu. Na sauke ajiyar zuciyarsa ina maida kallona ga Abdurrahman dake motsin tashi, nasan dukansu saisun tashi inhar d'aya ya tashi, saina lalla6a na kwanta kusa dashi na saka masa nono a baki. ******************** Har akayi la'asar Galadima bai farkaba, Nuren yazo shida Sauban, da Saleem har sau biyu suka iske yana barci, hakama Mom da inno da mama Fulani. Gashi su inno 4:30pm zasu wuce ma, laraba tazo tama yaran wanka, dan tuni sun farka, Nima nakumayi sannan naci abinci, kaina ciwo yakemin sosai, dan haka Sauban yafita ya samomin Magani nasha na kwanta, munyi sallama dasu Mom, zasu dawone kawai idan Galadima ya farka kafin su tafi. yaran kam duk d'insu suna can an kaima papi su tun d'azun. Nidai barci yay awon gaba dani, daga nankuma bansan wainar da aka cigaba da toyawa ba a gidan. ******************* Bayan la'asar kad'an Galadima ya farka, ganin shi kad'aine a d'akin ya tashi zaune bakinsa d'auke da addu'ar tashi barci, jin k'irjinsa yayi sakayau yasaki babu nauyin kamar d'azun, saidai abinda ba'a rasaba, yatashi zuwa bathroom yay wanka da alwala. Sallan zuhur da la'asar ya rama, tareda addu'ar neman sauk'i akan wannan lamari da samun k'arfin zuciya, dolene saiyayi yak'i da dukkan abinda zai zama makamin barazana a agaresa inhar da gaske aikin zaiyi, falo ya fito bayan ya kimtsa, zamansa da mintuna baifi 2 ba saigasu inno. Basu jira isoba suka shigo, a zatonsu yana bedroom yana barci, sunsan Munaya kuma tana d'akinta tana barci tunda daga can suke. ganinsa a zaune ya saka fuskar kowannensu fad'ad'a da murmushi. Shidai kallonsu kawai yake d'ai-d'ai. Inno ta mangari kansa tana fad'in “ja'iri baka sanmu bane halan?”. Hannunta ya rik'e yana kallonta, cikin maganarnan tasa ta k'asaita yace, “Inno wai ina zakuje ne?”. “inda muka fito mana”. Inno tafad'a tana zama kujerar kusa dashi. “saikace wad'anda ake kora?”. “A'a wazai koremu nida gidanmu, komawar dai ne yafi cancanta, dan takawa ma yace a gaisheka basai ya shigoba, zakuyi waya, idan ka murmure kaje yana nemanka”. “To shikenan ALLAH ya tsare hanya, mun gode sosai da sosai”. “Amin” inno tafad'a tana shafa kansa ta ciga da kwararo masa addu'oi shida matarsa da yaransu, falon kowa tana amsawa da amin, itama mom tayi nata. Yace, “mom hada ke wai?”. “eh mana Sameer, zaman mi zanyi to? tunda ALLAH ya iyakance komai cikin sauk'i, nanda y'an kwanaki kuma basai na zagayo naga masu jego ba da jikin naka, a dai dunga kulawa sosai, gasu laraba nan da bayi 2 anbar muku, dukdai wata kulawa insha ALLAH zasu taimaka wajen badata akan yaran, dan yakamata dukkan bayi da kuyangin sashen nan naka ka sallamesu kawai”. Kansa ya jinjina mata alamar amsawa. A gurguje sukad'an kuma tattaunawa da kwantar masa da hankali suka fito, dukda yaso musu rakkiya suka dakatar dashi. Abincin da mom ta zuba masa takumace yamata alk'awarin zaici ya dage yaci sosai, sannan Sauban daya dawo rakkiyarsu d'auke da y'an uku shida bayinnan biyu yabashi magani yasha, kar6ar Amaturrahman yayi, Sauban kuma na zaune dasu Abdurraheem yana musu wasa wai dole sai sunyi dariya, (nace, “aiki jaa kenan, inba dariyar k'udaba ta jarirai idan suna barci keyi aiko ka dad'e baka ganiba Uncle triplets😂). Galadima ma madai yatsansa d'aya ya saka cikin hannun Amaturrahman yana wasa dashi, dukda idonsa a lumshe yake ya jingina kansa da kujera, maganganun Munaya na d'azun kawai yake nazari dalla-dalla. Ana cikin haka Samha tayi Knocking, Sauban yace ta shigo, saida ta gaida Galadima damasa ya jiki. Ya amsa mata batareda ya kalleta ba, tareda tambayarta Khaleel fa?. Tace, “yana 6angaren Ummu hasheem”. Baice komaiba, itama ta k'araso ta d'auki Ammaurrahman data rik'e yatsansa gam tak'i saki.. d'agowa Galadima yay yana kallon yarinyar, Samha dai dariya takeyi, har Sauban shima ya farga da abinda ke faruwa ya shiga tayata. Galadima ya zare yatsansa yana murmuahin gefen baki da lakatar hancin Amaturrahman. Har Magriba suna nan sun shashance akan yaran, yayinda Galadima ke zaune yanata cud'awa da tantancewa, lokaci-lokaci yakan kallesu dagasu har yaran. Tunda ya tambayesu Munaya sukace tasha Magani tana barci bai sake tambaya ba. ******** Ban tashiba saida suka fara kuka, a time d'in har magrib tama wuce, nagama shayar dasu na lek'a Galadima, na iske doctor jalal tareda Dr Yaseen da Akash Wanda yake shirin komawa gobe, sai Muftahu da Nuren. Muka gaisa dasu suka kuma tambayata jikinsa? na Amsa musu da Alhmdllh. fitowa nayi na barsu, da aka kawo mana abinci ma can nace akai musu, Sauban yazo ya kwashi yaran bisa Umarnin Galadima, doctors zasu kuma duba lafiyarsu. ★★★★★★ Tunda Harun ya fita saiya kira wata Number lokacin daya k'arasa d'akinsa, dukkan abinda ya faru ya labarta mata, daga can tace k'aryane bahaka akaiba, ita an sanar mata lallai da Galadima aka kar6o yaran, babu wasu police, amma itafa kamar tafara saka alamar tambaya akan wannan ficikar matar tasa. Harun yace, “haba dai, wannan y'ar yarinyar mizata iya, akwai dai abinda bamu saniba, yanzu dai kibari zamuyi maganar daga baya, zand'an bincika yarannan danni na lurama kamar ba wad'anda muka saka bane sukayi aikinnan?”. “sunefa gaskiya, abinda dai na lura dashi sun had'a aikin da wasune, shiyyasa suke 6oye mana Kansu, tunda kaga mudai baiwarnan bamu muka sakata ba, amma shi namijin yana cikinsu, nasan sunyi luff ne sai k'ura ta natsa su fito”. “ok shikenan to, zandai sake bincikawa, dan Sameer yanada wayo, shiyyasa naso bugar cikinsa akan batun, amma wannan shegen k'asaitar tasa ta rainin hankali ya hanashi tankamin, sai matarce ke bani amsa”.. “karka damu zamu sauke masa shine ai”...............✍🏻 🤣abin dariya, ku a naku zaton yaranku sun 6oye Kansu be?, to suna hannun Galadima, lafiya kawai muke jira ya samu ya yagalgalasu kuma ya cafkoku munafukai🙄😏. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu._*😭🙏🏼 [7/18, 2:19 PM] Aysha Galadima: *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻2⃣9⃣ ..............Harmun kwanta zuciyata ta kasa samun nutsuwa, inason naje naga halin da yake ciki, Dan koda su Nuren suka wuce ban komaba, sakkowa nai daga kan gadon, laraba dake a tsakar d'akin kan katifa tace, “ranki ya dad'e lafiya kuwa?”. Banason ta kalli abun da wata manufa, dan haka nad'an murmusa, “uhmm iya inason duba Abbansu ne, ban saniba koyasha maganinsa kafin ya kwanta”. “eh lallai hakan yanada k'yau, badan ma jego ba ai bai kamata ya kwana shi d'ayaba”. “aiba shi kad'ai baneba iya, Sauban ne zai tare dashi ”. A to hakan yayi. Bance komaiba Na kar6i gyale wajen Samha Na saka na fita. Masarautar tayi tsit, da alama kowa yasamu nutsuwa a sashensa, ban tsaya knocking ba na shige kawai, a falo na iske Sauban zaune yana kallon ball, cikin tsokanar da ya iya yace, aunty gimbiya kin kasa barcine?”. Nayi murmushi, “yaa Sauban matarka taga ta kanta wlhy”. Dariya yayi kawai, nikuma na wuce abina. Saida nayi sallama kusan uku banji an amsaba, saina shige kawai. Zaune na iskeshi a bakin gado ya jingina da fuskar gado, hannunsa d'auke da Qur'an yana karatu a hankali, idonsa cikin medical glasses, gakuma system a gefe itama a kunne. naji dad'in yanda na sameshi, Addu'a da karatun Qur'an babban jigone dake wanke zuciya da damuwar d'an Adam (duk lokacin da ranki ya 6aci d'auki Qur'an ki karanta koki saurara, wlhy zakuji sassauci mai yawa). Har zan juya na fita sai naji yay gyaran murya, juyowa nayi na kallesa, har yanzu dai karatunsa ya keyi. na dawo na zauna a bakin gadon ta d'ayan gefen, shikuma ya cigaba da karatunsa, kusan mintuna 6 kafin ya rufe Qur'an d'in ya ajiye, ya cire medical glasses d'insa shima ya ajiye yana kallona, ko kad'an fuskarnan babu walwala, nuni yamin da inzo. Ban musaba na tashi nadawo 6angaren inda yake, zama nai d'an nesa dashi kad'an. Ya lashe le6ensa da cizarsa kad'an yana hard'e hannayensa a k'irji. Muryata can k'asan mak'oshi nace, “yaya jikin?”. Kansa kawai ya jinjina min cikin lumshe ido, sannan ya motsa baki kamar zaiyi magana saikuma yay shiru, saida yaja wasu seconds sannan yace, “Munaya!?”. “Na'am”. Na amsa ina kallonsa da janye idon lokaci d'aya saboda ya tsareni da nasa. Huci yad'an furzar, ya cire hannayensa daga k'irji yana gyara zama, “Nayi nazaci sosai akan maganganun ki na d'azun, nakuma fassarasu aji-aji, na fahimcesu a yanda tawa fahimtar take, so a wannan karon rok'o nake miki na k'arshe akan ki fad'amin abinda kika sani, ni d'an Adam ne, ban isa cewa komai na sanshi a rayuwaba ko na iyashi, sai abinda Ubangiji yaso in sani kawai, Munaya ada ba haka rayuwata takeba, mutumne ni mai yawan raha dason nishad'i, amma daga lokacinda nafara sanin kaina da matsalar mahaifina sai komaina ya canja, nazama mutum mai yawan rashinson magana, nafison kullum na kasance ni kad'ai a kuma ke6antaccen waje” yay murmushin takaici sannan ya cigaba da fad'in “Bawai hakan Na birgeni baneba ko a San raina, saboda Ina shiga k'uncine, amma banida za6in daya wuce hakan. nasha wahalhalu Na rayuwa kala-kala kafin na tsaya da k'afafuna, zuciyata ta bushe namance daga wane tsatso na fito, domin idan kinganni a lokacin da nake karatu da koyan sana'oi bazaki ta6a kawo ni jinin sarauta baneba, ko d'an wani, nayi gwagwarmaya sosai irin wadda d'a Mara gata yakeyi, badan mahaifiyata bata sona bane ta tsaya tsayin daka wajen ganin na horu kona nemi na kaina, hikimarta itace nazama jarumi mai yawan juriya, nakuma kwato mana y'ancinmu a lokacinda ya dace, duk wannan fad'i tashin da kikaga inayi wlhy badan nayi mulki baneba kamar yanda su suke tunani, Burina kawai nasan miyasa aka durk'usarmin da mahaifi? Tabbas ni jinin sarautane gaba da baya, kuma yana yawo a cikin jinina, amma rashin kwanciyar hankalin dake cikin sarauta baya birgeni, kallon kitse kawai akema rogo, ayau inason Kituna kema kin haifi yaranda sun rigada sun shigo cikin wannan harmutsi, tunda tazama jininsu, ki fad'amin kodan mu gyaramusu gobensu su rayu cikin salama koda bama numfashine, nasan hakanan bazakima Harun abinda kikai masa d'azunba saboda son zuciya kawai, please miyasa kika hanashi d'aukar Abdurraheem ne? Miyasa kikak'i barina na fad'a masa gaskiyar abinda ya faru?”. Shiru nayi nakasa cewa komai, sai faman had'iye abinda ya tsayamin a mak'oshi nakeyi, Dan bansan yanda zai kalli abunba koya fahimceshi, babu Abu mafi saka rud'u irin cin amanar makusanci, gashi dai a Ransa shifa ba k'aunarka yakeba, amma kulum yafi kowa kusanci da kai, da Nuna girmama alak'ar tsakaninku. (ALLAH ka Shiga tsakaninmu da duk wani Wanda yake tare damu a matsayin fuka biyu, Dan yanzu abinda yafi komai yawaita kenan a rayuwar d'an adam☹😭). Cikin katsemun tunani Yace, “please my friend say Something mana”. Kaina na jinjina masa, cikin nutsuwa nafara masa bayani, Dan yau nayi alk'awarin sanar masa komai, koda zai samu wani haske akan lamarin, shima yasamu nutsuwa a rayuwarsa. “Tabbas kamar yanda kake zargi aiki nakema wani, saidai fahimtar wanene d'in shine mai wahala, na fad'a maka tun farko a dalilin bak'on Abbanmu naji wani yankin matsalasa da bai ta6a sanarma waniba a ahalinsa, a lokacin da wancan abin yafaru Abba yak'i fad'ama kowa dalilin fishinsa a kanmu, dakuma abinda muka masa, hakanne yasaka innarmu zuwa tasamu baba mai kanwa abokin kakanmu na k'ut da k'ut ta sanar masa fushin da mahaifinmu keyi damu, ankuma bashi hak'uri yak'i sauraren kowa, gashi ba dad'in zama takejiba cikin matan gidanmu, wannan Abu daya faru sai sukejin dad'i damata arashi da habaici, harma damu kanmu. baba mai kanwa yace taje zai masa magana, bayannan bamusan misuka tattaunaba. Sai da bayan komai ya lafa harma mun fara karatu sai sanata halluru ya buk'aci abbanmu yabama y'ay'ansa biyu auren yara cikin yaransa, sunzo gidanmu har suka nuna mune za6insu, a lokacin tabbas naji a raina Sa'eed yamin sosai a rai.....” Galadima ya tsuk'e fuska yana taune lips dajan k'aramin tsaki. 'Dagowa nayi nad'an kallesa, amma saiya basar tamkar bashine yayiba, nima sharewa nayi na cigaba, “bamusan miya faruba sukace Zarah da siyama sukeso, wannan Abu ya 6atama Abbanmu rai, dan aganinsa anyi wani abune domin k'untatama mahaifiyarmu, hakkane yasashi zuwa ya sanarma Baba mai kanwa, dama duk dai wani Abu dazai taso gidanmu shine ake sanarmawa, yayi sasanci koya tsawatar, koda kuwa innro ce. bayan Abbanmu yaje da kwana d'aya, sai innarmu ta aikemu wajensa muka kaimasa goro da y'ar sayayyar da takan masa lokaci-lokaci, saboda yamusu hallaci a rayuwa a yanda take bamu labari, shiyyasa a kullum take d'aukarsa uba”. Mun iske baba mai kanwa a d'akinsa na zaure kamar ko yaushe, muka gaidashi cikin girmamawa da tsokanarsa a matsayinsa na kaka, shima ya tsokanemu tareda sakamana albarka kamar yanda ya saba, saiya murmusa tareda gyaran murya, hakanne yasaka muka nutsu dan fahimtar magana mai muhimmanci zaiyi, ya nisa cikin dattako na tsufa ya fara fad'in___”. _“yarana kuyi hak'uri da damuwar da kuka tsinci kanku a ciki, wadda tunkafin Ku mahaifiyarku a ciki take, amma nasan watan watarana kuda ita duksai kunci ribar wannan hak'urin, karkuyi bak'inciki akan hanaku wannan auren da akayi na y'ay'an halluru, dama can sud'in ba mazajenku baneba, hasalima aurensu ba alkairi baneba”._. “A razane duk muka kallesa baki bud'e”. Yayi murmushinsu na manya, _“abin ya baku mamaki ko? Humm ba abin mamaki baneba, yau zan fad'a muku wani sirrin dabaku saniba, domin ina hango wani tarin alkairi tattare da rayuwarku, inakuma ji ajikina kune wad'anda zaku fidda mahaifinku daga wata sark'ak'iya daya Shiga a dalilin taimako tun kafin a haifeku. Alhaji halluru da wata manufa ya nema ma y'ay'ansa auren d'iyan mahaifinku, amma Shifa na fuskanci bai fahimci hakanba, sabo da ya aminta da amintar dake tsakaninsu ta tsawon shekaru. Alhaji halluru yanason shiga jikin mahaifinku ne sosai danya kar6ama iyayen gidansa wani sirri dake hannun Auwalu, ina k'yautata zaton shine kukaji wani Abu a ciki, shi kansa Auwalu baisan minene a ciki ba, domin kuwa bashi akai amana ya Isar dashi ga Wanda yadace, kuma baita6a yunk'urin ya duba ba ya barsa a yanda aka bashi. Kuyi hak'uri akwai wasu k'alubale dake tunkaro rayuwarku, kuma yanada tsananin sark'ak'iya, saidai insha ALLAH zan baku dikkan gudunmawa inhar ALLAH yabani tsawon ran kaiwa wannan lokacin, Ku dage da yawan sadaka kudai da mik'a lamuranku ga ALLAH mai kowa da da sirrin komai, ALLAH kuma ya cigaba da tsareku.”_ “duk cikin tsantsar damuwa muka amsa masa da amin, haka muka baro gidan jikinmu duk a sanyaye, dan har innarmu tata bincikarmu a lokacin, sai muka fake da ciwon mara. sati biyu da faruwar wannan lamari sai Munubiya tafara min k'orafin yawaita mafarkin wani bawan ALLAH, kullum takan gansa ne a cikin dokar daji zagaye da wasu irin halittu masu ban tsoro suna kaimasa hari zasu halakashi, yakanyi k'ok'arin kare kansa amma saiya gaza, idan yanemi taimakonta kuma bata zuwa, saboda tsoro suke bata. Duk sanda tafad'amin wannan mafarki sainace bata addu'a ne, shaid'anune kawai. haka taita jera wannan mafarki kullum dare, kuma da gari ya waye bazata fasa fad'aminba, tundai abin na damunmu har muka watsar muka cigaba da harkokinmu. Ranar kuma sai nima nayi mafarkin makamancin na Munubiya, saidai nikuma na shige ina taya wannan mutumin kare kansa ga wad'annan halittun kamar yanda ya buk'ata, na jigata sosai dan harnatashi jikina duk yayi week, nima ban 6oyema Munubiya komaiba na sanar mata, abin yabata mamaki, kuma tundaga sannan nima na cigaba da mafarkin, kullum kuma ina taimakon wannan mutumin dako fuskarsa ban ta6a ganiba, itako Munubiya takan cemin saidai ta tsaya kallonsa daga nesa yana bata tausayi, kuma yana shan nuna mata tazo ta taimakesa, amma saitak'i ta nok'e kafad'a. nikam a nawa mafarkin duk lokacin da ya nuna na taimakesa nakanje nashiga muyita fama da wad'annan halittu, ita Munubiya tana ganin fuskarsa, amma da zaran ta tashi, saita manta, niko ban ta6a ganin fuskarsa ba ko sau d'aya. Muna cikin halin wannan mafarki ne aka shiga bikin salla, tabbas randa muka had'u dakai a asibiti sainaita jin haushinka akan dalilin da ni kaina nasan bai isa daliliba, (dan kawai ina maka kallon mai girman kai bai kamata naji haushinka ba, tunda bawai hud'ace ta had'amuba, banikuma da tabbacin akanka abbanmu ke a had'ari), saidai had'uwarmu ta filin idi tasha banban data asibiti, dan a filin idi tsoro-tsoro mai gauraye da mamakinka ne suka zaunemin a zuciya, bayan kabani wayarka kabar wajen inata mamaki da juyata da tambayar kaina kaid'in wanene? Sai wata murya ta bani amsa da cewar *Galadima!* saidai koda na waigo banga kowaba sai alamar gittawar mutum mai jajayen kaya, na dad'e soaai wannan al'amiri bai bar rainaba, a haka muka shiga shagalin bikin y'an gidanmu, harda kuma su siyama, anan ne muka had'u da Fu'ad, harga ALLAH bansan wanene Fu'ad ba, bankuma San daga wace tawagar ango ya fitoba, amma amamakin kaina lokaci d'aya na aminta dashi, dukda kasancewata mutum mai masifar tsarta, cikin kwana d'aya kacal na saki jiki dashi, dukda ban amsa masa Cewar na kar6i soyayyarsa ba, daga ni harsu Ayusher bansan miya shiga kanmu ba muka yarda ya kaimu birnin gayu plaza ba, dukda kowannenmu ransa akwai fargaba, musamman ni danakeji kamar akwai wani gagarumin Abu dake tunkaro rayuwata. hardai muka shiga muka fito abinda ya faru ya faru a tsorace nake. fitowar wannan jarida a washegari yasaka dukkan wani ahalinmu a rud'ani, Wanda bansan yazan musalta makashi ka fahimtaba, lokaci d'aya da akazo bincikar wacece a cikinmu na amsa, dan jinai bazan iya bari Munubiya ta amsa laifinba, saboda tanada hak'uri, amma tanada tsauri Wanda nikad'ai da mahaifiyarmu muka San wannan tsaurin nata, dan sometimes takanyi mugunta amma tayi tamkar ba ita baceba, kai tsayema sai'a zargeni ita ba'ayi tunanin zata iyaba....” Galadima ya katseta da fad'in, “kina nufin bakece kika kusa fad'iwaba a plaza?”. Nad'an murmusa ina gyaran mayafina dake zamowa saboda kayan sunada santsi, “tabbas bani baceba yalla6ai, Munubiya ce, tausayi. Y'ar uwata yasani kar6ar laifin. Bayan wannan Abu ya faru nanma kowa yata fushi damu musamman Abbanmu, haryace saina nemo miji cikin 2weeks kacal, wannan ya d'agamin hankali, dan nikam kaf samarina babu Wanda yamin, amma sainaga kamar zan iya auren Fu'ad, wannan dalilin yasani kiransa bisa shawarar su feena, amma saiya toshe sukkan hanyar dazamu iya yin magana. bansan yazan misalta maka halin dana tsinci kaina a tsakaninba, naji natsani Fu'ad matuk'a, a wannan time d'inma na cigaba da wancan mafarkin, amma yazomin dawani sabon salo, sannan ita kuma Munubiya ta daina, mafarkin ya canjane zuwa salon da mutumin kanyi yunk'urin ta6ani, amma nakan hanashi damar hakan ta hanyar ja baya da masa gargad'i, shikuma saiya ringa rok'ona da cemin karna masa haka, ni fitilarsa ce. Har sannan kuma still bana ganin fuskarsa, abubuwa da yawa sun had'u sun dagulemin, dukna fige na fice hayyacina. A lokacin da baba mai kanwa yaje dubani asibiti bayan maganar aurenmu da haidar ta rushe saiyake magana cikin murmushi, k'asa-k'asa kuma ta yanda wani bazai jimu ba”. _“Ki kwantar da hankalinki Hussaina, har yanzu dai mijinki bai kai ga zuwaba, kuma bayan wannan ko 10 zasu k'ara zuwa saisun barki, dan akwai k'alubale a gabanki kafin kisamu nutsatstsiyar rayuwa._” “Da mamaki na kallesa, amma saiyak'i bani damar neman k'arin bayanin komai a wajemsa. Bayan na warke nadawo gida kuka saka aka saceni kaida Muftahu, na koma gida mangariba ta rufa a ranar, ashe wai baba mai kanwa yaga sanda na shiga gida a firgice, sai'a washe gari ya aiko a kirani, innarmu da Munubiya sunyi mamakin kiran, dan cayay Hussaina taje, (shi dama baya kiranmu Munubiya da Munaya, sai Hassana da Hussaina). Haka na saka hijjab naje, a yau baiyi wasan daya sabayi da niba, kai tsaye yafara maganarsa”. _“Hussaina jiya daga ina kika dawo a firgice?”._ “A tsorace na kallesa, dan lallai tsohonnan yafara bani tsoro, dama tun muna yara mukanji ana cewa tsoronsa akeji, saidai bamusan manufar tsoronba, murmushi yayi yana gyara zama da cigaba da gyaran wasu takarsu Dana tarar yanayi, yace___”. _“karkiji tsoro, nimai taimakonki ne gwargwadon abinda ALLAH yabani ikon sani, dan haka ki fad'amin gaskiya_”. “dak'yar na iya had'iye yawu, sannan na fad'a masa abinda yafaru tsakanina daku. Murmuahi yay mai matuk'ar sauti, wanda ya bayyana fararen hak'oransa da basu wuce goma sha ba da suka rage, wad'anda a kullum zaka sameshi da ashuwaki yana d'abbak'a sunna, yace___”. _“Hussaina ni bazance ki amince ko karki aminceba, saidai nabaki dama kije ki duk'ufa rok'on ALLAH, a cikin kwana ki biyu rak ALLAH zai nuna miki mafita da abinda zai zama alkairi a gareki, sannan karki sanarma Hasaanar ki, danna kula bazata amince ba tacikin sauk'i, tashi kije”._ “A wannan ranarma haka baba mai kanwa ya sakani cikin rud'ani, nazo dukna hana kaina nutsuwa da kwanciyar hankali, saidai nabi shawararsa ta mik'a kukana ga Ubangijin al'arshi, dan shine gatana kuma fitilata, a kwana na biyu kuwa saiga dalilin dayasani amincewa da buk'atarka ya faru, na amince maka badan hankali na ya kwantaba. tunda kuma lokacin baba mai kanwa bai kuma min maganar data shafi auren ba, harma na d'auka duk mafarki nayi, har maganar da mukayi d'in dakai. Saida ana gobe d'aurin aurenmu da safe na fita yin wani Abu na gamu da baba mai kanwa, shine yace na biyoshi gida. Mun Isa gida a d'akin zaurensa, yabani wasu abubuwa dabansan mineneba na sha, sannan yabani turare kashi biyu, yace ni 1 Munubiya 1, yace____” _“Hussaina kimin wata alfarma mana?”._ “A sanyaye nace kabani Umarni akwai baba. Yay murmushi da fad'in___”. _“ALLAH ya yimiki Albarka Hussaina, ina tausayinki ta wani fannin, ta wani fannin kuma murna nake tayaki, duk abinda nake hasashe a kanki nasan zaki iya, dan kinfi y'ar uwarki wayo, ni dake zamu had'a kaine wajen fidda mahaifinku a sark'ak'iya, su a gangancinsu sun tozarta kune domin tunzura mahaifinku da karyar masa da zuciya, amma basusan Ubangiji mai hikima baneba, yafisu sanin akan abinda su bai basu damar saniba, kiyi hak'uri inata miki magana a cirkud'e, zaki fahimci komai anan gaba kema, alfarmar da zakimin shine dukkan abinda kikaci karo dashi a rayuwar aurenki ki sanar min shi, insha ALLAH Zan miki fashin bak'i gwargwadon abinda na fahimtar nikuma, maganar zaman aurenku da yanda kuka ginashi kuma ya rage naku bayan warwarewar komai, wannan ba hurumina baneba, tashi kije, daga nan dai zamu dinga tayaku da du'ai”._ “Dukda banida tabbacin mijin dazan aura wannan magana tashi tamin nauyi da wahalar fasaara, da y'an gidanku suka kai lefena kuma saina kuma tsintar kaina a rud'ani da firgici, ban kuma fita daga wannan firgicinba har aka kawoni wannan masarautar. Saka pills da Muftahu yayi mana shine k'alubale na farko dana fara cin karo dashi Wanda nake k'yautata zaton baba mai kanwa ya hangomin, hakanne kuma ya sakani tada hankali nace nafasa auren, dan a zatona kun had'a bakine da Muftahu, amma sai maganar tafiya India ta datse dukkan hanzarina, ko kad'an banyi yunk'urin sanarma baba mai kanwa wannan batunba, dan aganina baya cikin abinda shima zaiso Sani. Idan baka mantaba a lokacin da ka kaini sallama gida da kuma gidansu Munubiya ka barni a can?”. Kansa ya jinjina mata idonsa a lumahe ya jingina da gado, kai kace ba saurarenna yakeba barci yakeyi. Ajiyar zuciya na sauke, na cigaba da fad'in “Aunty Salamah tazo gidan ta sameni ai, saboda Munubiya ta sanar mata zaka tafi dani, wannan itace damar farko dana samu na rok'onta yimin bincike akan Muftahu da Saleem yaronka na plaza, (abinda yasa Saleem yashiga Layin zargina saboda randa abinnan ya faru bayan fitowarmu shikuma naga ya fito daga tsakanin wasu motoci a firgice, dayake a time d'in bamusan mizai faruba ban kawo komai a rainaba sai washe gari, danayi bincike a kansa saina gane yaronkane na shago kuma amintacce) daga ita har Munubiya a lokacin basusan dalilina nason amin bincikenba, saidaga baya Munubiya ta fiskanci komai, dayake tanada kaifin basira, amma batasan tsakanina da baba mai kanwa ba. mun tafi India nabar Aunty salamah da wannan aikin”. Knocking k'ofa da akayine ya saka Munaya yin shiru bata cigaba ba, na kalli Galadima da har yanzu idonsa a lumshe, batareda ya bud'eba yabada izinin shigowa, yasan dai bazai wuce Sauban ba. Samha ce ta shigo, ta risina tana gaidashi, sannan tace, “Aunty Amaturrahman ta tashi itada Abduraheem”. Yunk'urawa nayi zan mik'e galadima ya katseni ta hanyar fad'in “jeki kawosu”. Na kallesa da mamaki, yayinda Samha ta fice abinta, “amma yalla6ai darefa yayi, mubari mu k'arasa zuwa gobe mana?”. “uhm-uhm”. Kawai ya fad'a. Shiru nayi nakasa cewa uffan, har Samha da Sauban suka shigo d'auke da yaran duka uku, kar6ar Abdurraheem nayi, dan yaron tausayi yake bani saboda rashin kuzarinsa (karku manta har Yanzu Munaya batasan yaron yanada irin ciwon mahaifinsa ba), su kuma Sauran ya kar6esu. Sauban da Samha suka fice sudai suna tunanin wannan zaman nasu, komi suke tattaunawa oho. Bayan fitarsu a cikin gyale na fara shayar da yaron, Galadima dai baice dani uffanba, sai kallon yaransa kawai yakeyi, na cigaba da fad'in “Abu na biyu dana fara cin karo dashi shine ganin Abie a halin daya tsinci kansa, wannan lamari ya d'aga hankali na, amma a lokacin banida wayar kiran baba mai kanwa na sanar masa, ina tsoron na saka a wayarka kuma ka gano wataran, sai kuma tarihin masarautar nan da Momma ta bani.......” Cikeda mamaki Galadima ya kalleta, dak'yar ya bud'e baki cikin yamutse fuska yace, “Momma!?”. Nace, “eh lallai Momma da kanta, dukkan rayuwar dakasha ta gwagwarmaya ta sanar min, tundaga yarinta zuwa girmanka, ta sanarmin hakanne danna lura da abinda ban saniba a masarautar, kar wani yayi amfani dani wajen cutar dakai. Bayan nan babu dad'ewa kabani waya, daga nan nasamu damar sanarma baba mai kanwa sirrinan guda biyu, ciwon Abie da tarinku. shine yabani dukkan addu'oin da maganin daza'a nema arink'ama Abie, kuma Alhmdllh munakan ganin haske. daga nan kuma na cigaba da samun haske game da dukkan Motsin Muftahu, amma kuma babu wani abinda bai daceba ko cin amana tattare dashi, damukaga mun shiga kokwanto saimuka saka Sarkin Mota da Saleem suka sace manashi a randa kaje d'akkomu a airport ni da Sauban lokacin da Abba yay accident ”. “ya salam! Kina nufin kece?”. Murmushi na masa, nace, “kwarai nice, hakan shine kawai mafita agareka damu kanmu, dan satar nashi ya zame mana haske, aunty salamah taje masa a amatsayin d'aya daga cikin matan Abie, ta hakanne kuma muka ji sunan Harun a bakinsa. daga nan muka sakama Harun ayar tambaya, su Ameer suka cigaba da bibiyar Harun d'in, kayi hak'uri ka gafarceni da abinda zan fad'a yalla6ai”. ‘nai maganar ina kwantar da Abdurraheem na d'auki Amaturrahman dake cinyarsa, itama na fara shayar da ita. “ki fad'i komi ke bakinki, na shirya kar6arsa da makamin HAK'URI”. Murmushi nayi cikin nisawa, “yalla6ai akwai sirrin dabaka saniba Wanda ya banbanta Muftahu da Harun, Muftahu shine masoyinka na gaskiya, Harun kuwa akwai manufar ra6arka tattare dashi, yasan kuma komai game da satar yarannan, akwai dalililai masu yawan gaske dazan iya kare kaina dasu, amma nabaka dama kayi wannan binciken da kanka. Sannan k'arin bayanin dazan maka shine, mak'iyane zagaye dakai, sannan kowanne akwai manufar sa a kanka, abinda yasa suka taru maka da yawa akwai k'iyayyar mahaifanka data dawo kanka a yanzu, wasu saboda tsoron ta6argazar dasuka aikatane basason kayi mulki ka yak'esu, wasu y'ay'ansu sukemawa, wasu iyayensu ne, wasu kuwa kansune, dukkuma akan inhar kahau mulki zaka iya canja komai da hukunta kowane ya sakasu wannan k'iyayyar a gareka, a yanzu dai kanada Avedance guda hud'u zuwa biyar a hannu, na farko sune wad'anda ka kama da yaran nan, yakamata kasan wanene ya saka su kafin kasan dalilin sasun, na biyu Harun, yakamata kasan miyasa yake tad'eka bayan ka yarda dashi Yakuma San airrinka, na Uku shine Saleem, dolene a wannan karon kasan wanene ya sakashi aikin tsaida CCTV cameras a waccan ranar, na hud'u shine SD minene had'insa da mahaifina, na biyar shine Fu'ad wanene ya sakashi kaimu birnin gayu a waccan ranar, sai Malam saminu driver Alhaji balala dan akwai abinda ya Sani tabbas, hakama farhat ku sake bata tsaro sosai, dan mahaifinta zai kawo kansa gareka cikin sauk'i saboda k'aunar dasuke mata, Sauran kuma zuwa nan gaba zan baka haske a kansu, wad'annan dai ka gaggauta sanin abinda suka Sani a cikin kwanaki biyunnan kacal, dan mak'iya bazasu zauna kallonka ba suma, sunacan suna had'a kayan yak'i. zanje na kwanta, saboda yakamata zuwa gobe mu fara shirye-shiryen komawa gida bisa al'adar haihuwar Fari, yau Munubiya tana can ma ita”. Ido kawai ya tsura min yakasa koda motsi, na d'auki Amaturrahman Na Goya, sannan Abdurrahman da Abdurraheem kuma a hannu nayi ficewata. Sauran bayani na k'ok'arin mahaifiyarsa Momma kuwa bazan fad'a masa yanzuba, sai komai ya lafa, saboda suna tattarene da sirrikan dasuka shafeni wad'anda bazan ta6a yarda ya sansuba................✍🏻 *Kudai k'ara hak'uri dani, nasan a zak'e kuke da sonjin Galadima ya fara caskale, komai a sannu-sannu ne, dama ba tufk'ar keda wahala ba warwarar, babu abinda yakai k'arshen Novel da saka ciwonkai irin k'arshe, musamman ma mai sark'ak'iya, idan kuka cigaba da hak'urin bina kamar yaune komai zai k'are, shiyyasa nakebi daki-daki yanda kuma zaku gamsu cikin sauk'i.* _lallai Comments naku nasakani nishad'i, musamman addu'oin Ku gareni ni da mahaifina😭, harma nakan Gaza sanin yanda zan nuna muku jin dad'ina, amma ina kallon kowa wlhy, saidai idan bana cikin group d'in kuwa, ALLAH yabar zuminci, ina yinku irin Trillion's d'innan, I love you all wujiga-wujiga wlhy🥰🥰🥰🥰😍😍😍😍😘😘😘😚😅🤝🏻🤝🏻👍🏻🤸🏻‍♀_. *_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏼 [7/19, 4:48 PM] Aysha Galadima: *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻3⃣0⃣ ................Galadima daskarewa yay a zaune, gaba d'aya magudanar jininsa tana neman Gaza aiki, saboda jininsa a daskare yake, dai-dai da bugun zuciyarsa salon datake bugunta da banne a yanzu, lallai masu kiran mata masu k'arancin *TUNANI* a zahiri sune masu k'arancin tunanin, lallai mata suna suka Tara, akwai mata akwai mata maza, juye-juye yay tayi a gadon ya kasa ta6ukama kansa komai, barci ya k'auracema idonsa, d'aya bayan d'aya Brain nasa ke markad'a maganganun Munaya dalla-dalla, wani murmushi yasaki yayinda yakai hannunsa yana shafo kwantaccen sajensa zuwa gemu, dukkanin bincikensa akan dai-dai yake, saidai rashin tsoron Munaya da kaifin basirarta ya matuk'ar k'ayatar dashi, ya tashi zaune yana jawo laptop ya kunna, saiga su Munaya sun bayyana a itada yara da Samha a kan gado, saidai yanda ya lura ba barci takeba itama, Dan tana d'an girgiza k'afarta daga kwancen. tsayin wasu mintuna ya kashe tareda mik'ewa ya d'auro alwala, abin salla ya shimfid'a ya fara gabatar da nafila kamar yanda ya saba inhar yanada lafiya. ******************** Yau likitocin Abie dasu Momma suna cikin farin ciki, saboda k'afarsa ta dama sun wayi gari tana motsawa, bayan gwaje-gwaje suna tabbatar da canjin da aka kuma samu a dukkan halittun ga66ansa, yau daga shi har Momma harda kuka, tako rungumeshi cikin tsantsar farin ciki da godiyar ALLAH, jakadiya sai fita tayi jiki na rawa..... Galadima na tsaka da salla kira ya shigo wayarsa, koda ya idar saiya share, har yana masifa a ransa wane ke kiransa a wannan time d'in bayan yasan shi mai iyaline (🤣 kaga mai iyali😜👍🏻). Ganin dai baza'a barsa yaji da abinda ya damesa ba saiya d'auka a masife da nufin kashewa, kad'an ya rage ya aikata hakan sai yaga Ashe Momma ce, mugun zaro idanu yayi, jikinsa na rawa yay picking video call d'in, Momma ce ta bayyana tana sharar kwalla, har taune harshe yake wajen fad'in “Momma mike faruwa ne?”. Ganin ya rikice saita hau dariya da share kwalla tana masa bayani, ta matsa kusada Abie ta had'asu, yaukam dai Galadima harda k'ananun hawaye yayi Dan dad'i, gashi yau yaji muryar Abie d'insa tafito sosai ba laifi. Sunja lokaci suna waya, har kud'in wayar Momma ya k'are sannam suka hak'ura, baibi kiranba yacigaba da mik'a godiyarsa ga ALLAH. ranar dai zumbur akan abin sallah yayisa, sallar asubahi ma a d'aki yayi sannan ya samu ya kwanta, barci mai nauyi kuwa ya kwashesa. Da shirye-shirye Munaya ta tashi, dukkan abinda zasu buk'ata tagama tanadar musu itada yara, Samha dai tayi tagumi tamkar zatayi kuka. Bayan anma yara wanka Munaya ma tayi sai ta zauna yin break fast, suna d'an hira jefi-jefi da laraba dake ma y'an uku shiri cikin wasu kayan sanyi masu laushi. A kullum Munaya kan tsarkake sunan Ubangiji idan ta kalli yaranta, takanyi mamakin anya kuwa daga jikinta suka fito? idan ta tuna a yanda mahaifinsu ya Samar dasu takanyi murmushi da cizar lips (copy copy😜😂). Duk abinda takeyi laraba na lura da ita, Munaya na birgeta sosai, Dan idan tana wani abun takanyi tunani kodai Munaya jinin sarautace? Dan salonta da takunta tana kamada na mashahuran y'ay'an sarakuna masu aji da Jan aji, cikin hikima irin tasu ta manya tace, “Ranki ya dad'e ko Baban y'an uku yatashi? Naga bakije dubashiba, gashi tun d'azun naga ankawo Karin kumallo, kuma since shima sunkai NASA amma baya falo. Munaya tad'an Sosa k'eya tana murmushi, tace, “eh iya, ban saniba koya tashi, amma bara na lek'a na ganni”. “yauwa ko kefa ranki ya dad'e”. d'aukar k'aramin mayafi tai ta fita, sanye take cikin sket da riga na wani yadi mai kama da boyal Orange color, an masa kwalliyar surfani kad'an da stones da milk . Sai mayafinta siriri ya kasance milk shima, tayi k'yau sosai gashi tasha d'aurin zarah buhari😜. Tunda ta fito daga bedroom d'inta idon Galadima a kanta, fitowarsa kenan daga wanka sanye da bathrobe da k'aramin towel a hannu yana tsane ruwan kansa zuwa fuska da wuya, daina tsane ruwan yayi yatsaya kallonta ta cikin Computer d'in, harta shigo falonsa, tad'anyi kalle-kalle da lakatar center table d'in falon da d'an yatsa, da alama tana duba ko da dattine, idonsa yad'an lumshe yana lasar lips, yabar gaban Computer d'in zuwa ga mirror, zamansa babu dad'ewa tayi knocking k'ofar tare da sallama, kamar bayaso ya amsa mata, ko kad'an bata wani jisaba, Dan haka ta harari k'ofar sannan ta bud'e ta shigo. Ko motsi baiyiba daga inda yake, saima cigaba da shafa mansa dayayi, itama batareda ta kallesa ba ta wuce zuwa ga bed d'insa tana fad'in “yalla6ai barka da asuba”. Yanda tayi wani masifar basar dashi saiya d'an waigo ya kalleta, sa6anin da da yake kallonta ta cikin mirror. Zanin gadon ta cire hankalinta kwance, ta wuce ga wardrobe nashi ta d'akko wani tazo tana k'ok'arin shinfid'awa. Mik'ewa yay ya tako gareta. Jinsa akwai nayi a kaina, amma ban lura da sanda yabaro gaban mirror d'inba, k'amshin sabulun dayay wanka dashi da man days shafa duksun addabi hancina, na d'ago gaba d'aya na ina gyara mayafina domin ya rufemin k'irji da k'yau, saboda kayan babu laifi sun kamani, wajen yakuma cika sakamakon shayarwa. Dab dani yake a she, koda na mik'e sainayi kamar zan fad'a masa a jiki, nadai samu nad'an jaa baya ina tunzura baki, taku d'aya yayi yakuma matsoni, na matsa nima, shima ya matso, hardai muka kai k'arshen bango, kad'an ya rage na yandda Prime dake saman drowan gefen gadon, Wanda hoton Y'an uku ne yasa akayi ya ajiyeshi a wajen, na kalla ina gyara masa zama cikin d'an rankwafawa kad'an, hakkane yabama gyalen damar kuma zamewa, batareda na luraba na tsaya sosai, nad'an 6ata fusaka ina fad'in “yalla6ai lafiya kuwa?”. Luuu yay da idanu saikuma ya bud'e a kaina yana cizar lips, ganin ya tsurama waje d'aya ido a jikina saina kalli wajen, baki na bud'e nakama gyalen zan rufe k'irjina da sauri ina tura baki. Caraf ya rik'e hannun, zan saka d'ayanma shima ya rik'esa, sosai na had'e fuska idona na tara kwalla, kuma matsoni yayi sosai, ya rankwafo da kansa saitin k'irjina, rufe idona nayi ina k'ank'amesu sosai saboda tsoron mizaiyine haka?......... Bankai k'arshen tunanina ba naji saukar iska a wajen, a hankali na bud'e idona, sainaga Ashe gyalen yake hurawa da iskar bakinsa danya bud'e sosai, kunya ta kamani, dan rabin k'irjin duk abid'e yake, wuyan rigar ya cika girma. Wata muguwar girgiza nayi, had'eda shock a lokaci d'aya, saboda saukar nutsatstsiyar Sumbata danaji a wajen, babu shiri na maida idona na lumshe ina sauke ajiyar zuciya cikin shashsheka da nima bansan nayiba. Hakan ba k'aramin yamutsa jinin Galadima yayiba, ya d'ago yana matsoni jikinsa sosai da maida hannuna duka baya ya rik'e da hannu d'aya, na manne da jikinsa sosai. K'asa nayi da kaina saboda wata matsananciyar kunya data ratsani da mamakinsa, murmushi ya saki, Wanda tundaga zuciyarsa ya taho, Dan naji alamar hakan ta k'irjinsa, ya wani kuma maida muryarsa very slowly cikeda k'asaita yace, “yalla6iya dama kinada lafiya haka?”. Bansan na d'ago kai da idoba na kallesa, baki bud'e nace, “kamarya? Dama nace maka banida lafiya ne? ni kabarni nayi aikina inada abunyi”. ta k'are maganar da kauda kai gefe tana tura baki. Gira d'aya ya d'age sama, cikin ta6e baki yasa yatsu biyu ya maido fuskata Inda take, yace, “kin tabbatar kinada lafiya?”. Yay maganar yana d'aura yatsansa kan la66ana da zagayasu a hankali. Yanzunma tilas na lumshe ido, jikina harya fara tauma, zuciyata kam sai fat-fat take tamkar zata faso k'irji ta fito. Gangaro da yatsansa yafarayi daga saman bakina zuwa wuyana har yazo k'irijina. Bansan nafara kamo addu'a inayiba azuciyata, gashi na kasa bud'e idanu, muryata na rawa nace, “please yalla6ai k...ka...kabari”.. Uffan bai ceba, idonsa akan fuskarta yana murmushi da taunar lips, kuma bai bar abinda yakeba har saida ya dire saitin da zuciyata take, yace “ita wannan miyasata fargaba?”. Bud'e ido nayi a hankali dan naga miyake nufi? Na kallesa, ya nunamin k'irjina da ido, a d'arare na kalla inda yatsan nasa yake, na had'iye wani yawu dak'yar ina fad'in “babu komaifa, kaga yara zasu iya kuka ina nan fa”. “Uhmyim” yafad'a yana d'auke yatsansa daga saman k'irjina yana maidawa kan k'uguna, ya tura hannunsa cikin rigata cikeda wani salo, hannuna nafara yunk'urin kwacewa, saiya tsaya kawai yana kallona, saida nayi harna jigata kafin yayi wani munafikin murmushi, ya matso da k'uguna da k'arfi ya had'e da jikinsa, saida naji zafi na yamutsa fuska da cewa “Uhchhh! Yalla6ai ciwo”. “Da gaske?”. ‘yay maganar cikin matso da fuskarsa dab da tawa tamkar zai had'e bakinmu, idonsa cikin nawa yace, “kinsan mizan baki?”. Kaina Na girgiza masa kamar wata sokuwa. Hannunsa Yakuma turawa cikin rigata har zuwa gadon bayana, a hankali yace, “k'yauta”. “K'yauta kuma? Tami to?”. K'ala baice daniba ya juyani ta hanyar murza k'uguna ya maidani saitin gadon yana lankwasani a hankali, yayinda shikuma yake biyoni idonsa kan lips d'ina danake motsawa amma maganar ta gaza fita. Muna gab da kaiwa gadon ya saki hannayena ya tallafe bayana da hannunsa, d'ayan kuma yana rik'e da k'uguna har yanzun, ahaka muka fad'a saman gadon, saidai bai sakemin nauyinsaba sosai, koda ya fad'o jikina banji zafi mai tsananiba, yay min runfa da faffad'an k'irjinsa yana matso da face nashi daf da tawa. cikin wata iriyar murya mai sanyi da k'asaita yace, “bud'e ido ki gani”. Ban musaba na bud'esu, sai cikin mayun nasa da har yau launinsu yakeda sirkin jaa, duk yanda naso fiddawa na kasa, dan ya hanani wannan damar, saima wasu abubuwa danaga tamkar yana zubawa cikin idona, batareda na fargaba na shagala nima nabar yunk'urin janye nawa. Munkai tsawon mintuna a haka, saida ya tabbatar nagama zuwa hannunsa sannan ya d'ora tattausan lips d'insa akan nawa ya fara sarrafasu cikin tsantsar nuna yana tare da kewa da bege. Ni munaya naga ta kaina, bansan ya akayi galadima yaci galabar samun kainaba, lallai shid'in yanada wani baiwar iya sarrafa mace a yanda yaso, ya mantar dake wacece ke balle daga ina kika fito, yakan basar tamkarma baisan micece wata soyayya ba, duk kuma randa kikazo hannunsa zaki tabbatar yacika namiji, Dan asalin jinin Malam bahaushen Na yawo ajikinsa, dukda kasancewar wayayye kuma bai girma cikin k'abilarsa ba, yakan maida hankali a harkokinsa, randa kuma soyayyar ta motso yabata muhimmanci Na ban mamaki (Matan hausawa konayi k'ayya ba hakan mazan hausawa sukeba😂?) (Shiyyasa Muke cewa basu iya soyayya ba🤭🤣⛹🏻‍♀). Sosai na shiga bashi dukkan goyon baya harda saka hannayena na zagaye bayansa dasu........... 😨yaukuma su Oga Galadima an tina da sadaki😌🤭😂. Tafiya tafara nisan da naji yana neman sakin layi, a kasalance na rik'e hannunsa dake yawo a jikina, sannan na fara k'ok'arin janye fuskata daya koma bama kisses tako ina, sai gwama numfaahi yake yana sakin tagwayen ajiyar zuciya. ganin bazai bariba nasakar masa siririn kuka, ina fad'in, “yalla6ai jegofa m....mu...mukeyi”. Sai a lokacinne ya tsaya cak, amma yak'i d'agani, juyo da fuskata nayi na kallesa, ya sake sark'e idonsa da nawa, idanunsa sunkuma rinewa launin jaa sosai, wani murmushin takaici ya sakarmin, cikin magana da k'yar yace, “kina kukane danna mori sadakina?”.. Wannan magana tasa tamun nauyi, Dan haka na gagara bashi amsa, sai janye idona da nayi hawaye masu d'umi suka gangaro ta gefen kunnena. Gefena ya koma ya kwanta yana cizar lips da lumshe ido, yayinda hannunsa ke shafa kaina saboda tuni d'an kwalin ya zame. A haka yafara magana a hankali, “toke yanzu Yaya kenan? naga alamar auren Contract yakusa k'arewa, gashi ko rabin sadakina ban Moraba, zaki dawomin da kayanane ko yaya?”. Kai wannan Bawa ya shahara a fagen rainin wayo, nafad'a a zuciyata, a fili kuma sai nace, “nima sai'a biyani d'aukar ciki da nak'uda, da shayarwa ai, tunda babusu a yarjejeniyar auren”. Yanda nayi maganar ina yamutse fusaka da murgud'a baki saiya shagala da kallon la66anta, hannu yasaka ya tallafo fuskarta yajuyo da ita sosai inda tashi take, dukda idonta a rufe suke, “kifad'i ko nawane sai a biyaki ai, nikuma ba kud'in Dana bayar nake buk'ata ba”. Na bud'e ido baki bud'e, “to mi kake buk'ata? Naga kud'i ka bada kuma kud'i ya kamata a baka”. Cikin ta6e baki yace, “farashina ya wuce haka”. Nina bakin na ta6e nace, “Niba arhar banza bace”. Nayi maganar ina yunk'urawa da tashi zaune, da kallo ya bini, saida na ziro k'afafuna k'asa sannan nakuma fad'in “mun gama sahirinmu”. Shiru yamin tamkar bazai tankaba, harma na juyo na kallesa, idonsa a rufe suke yayi filo da hannayensa, d'auke idona nayi ina gyara rigata. Yace, “zuwa ina kenan?”. Nace, “gidanmu”. Tashi yay ya sauka daga gadon duka yana nufar wardrobe, saida ya bud'e yana kallon kayansa sannan yace, “mizai hana kibari ki k'arasa aikinki kawai saiki tafi gaba d'aya”. Na murmusa ina mik'ewa tsaye nima, na koma jikin mirror na jingina ina hard'e hannayena a k'irji, idona akansa nace, “aini nagama aikina, Dan nabaka dukkan sirrin dake raina”. Yana ciro wasu bak'ak'en wando da Riga yace, “zadai ki gamane yarinya, Abin cikin kwan bazasu gusa a kusa daniba”. “Humm” nafad'a cikin takaici, nace, “mizai hana ka yanke dukkan alak'a, Dan nima iyayena na buk'atar ganina a kusa dasu”. Murmushi yayi yana juyowa hannunsa d'auke da kayan daya za6o, kallo d'aya yamin ya janye ido, “mikikeci na baka na zuba babie, indai an gama yak'in ai zata yanke”. “nikuma bana buk'atar ganin k'arshen, in ank'i cikin sauk'i zan bud'e komai kowa ya sani”. Murmushi yay mai sauti, har fararen hak'oransa na bayyana, ya kwance igiyar rigar wankar babu kunya ko shakkar ganina, kauda idona nayi daga inda yake, yafara saka kayansa, cikeda izza yace, “wace k'arfin gwiwa gareki na samun wannan damar?”. “Court, tabbas zan maka ka a Court, sai a kar6a min ai”. “kinada abin dariya kwarai da gaske, a mutum dubbunai dasuka shaida na biya sadaki sannan na d'auka, mutum d'ayane yasan sirrin ba haka bane, bayan wannan hujjar kinada watane?”. Dariya nayi irinta tsantsar rainin hankali, harya d'ago daga d'aura belt d'in da yakeyi ya kalleni sannan ya janye, zama nayi a stool mirror, na d'ora k'afa d'aya kan d'aya ina girgizawa, “yalla6ai kenan, a tunaninka zaka iya cin bulus ne?”. Murmushi kawai yayi bai sake tankawa ba, Dan ya kula ciwon kai take Neman saka masa, ya zauna bakin gadon yana saka sock's da takalmi, yayinda Munaya taketa cika da batsewar sharetan da yayi. rigar jacket d'insa milk color ya d'ora bisa bak'ak'en kayan, komai nasa ya kasance bak'i, jacket d'ince kawai milk, ya matsa gaban mirror kusada ita yana gyara sajensa da fesa mayen turarensa. Saida ya gama dukkan uzirinsa kafin yazo gabana ya tsaya hannayesa duka zube a cikin aljihu. Dan k'yau yayi k'yau kam, amma saina kauda kai gefe ina ta6e baki, irin bakayi d'innanba. Shima bakin ya ta6e yana rankwafowa kaina har inajin hucin numfaahinsa, “karki damu mai yabawar tana nan tafe lokaci kusa, matar Sameer sarauniyarsa kinji yalla6iya”. Cikin azama na mik'e, yay saurin ja da baya, Dan daya tsaya saina buga masa kaina wlhy. Hanyar fita na nufa ina fad'in “idan kana buk'atar y'ay'anka zaka iya bina gidanmu ka kar6o abinka”. Da kallo yabi bayanta kawai yana ta6e baki, akan la66ansa yace “iya tsiwa”. Agogonsa ya d'auka bak'i ya d'aura, sannan yazuba wayoyinsa a aljihu tareda saka eyeglasses mai duhu a idonsa, ya 6oye tsananin jaa da sukayi, a falo ya iske tea a cup an had'a yanata turiri, zama yay yana lumshe idanu, yakan rasa Munaya wace irin macece ita? So salon nata akwai tsagwaron k'ayatarwa, Crossing k'afarsa yayi yana shan tea d'in a hankali, yasha kusan rabin cup ya ajiye yana mik'ewa da kallon agogonsa yanajan k'aramin tsaki. sashen Munaya ya nufa, bayin daketa gyare-gyare suka zube suna gaidashi, hannu ya d'aga musu kawai batare da yace k'ala ba, cikin takunnan nasa na k'asaita da izza yake tafiya, bayinnan sai satar kallonsa suke, da sallama ciki-ciki ya shigo d'aki, Laraba tai saurin risinawa tana gaisheni, ya amsa batareda yako kalleta ba, ficewa tayi da hanzarinta, Samha ma ta gaidashi. Zama yay a bakin gadon idonsa akan akwatina da Munaya ta had'a, ya janye ya maida kan yaran yana fad'in “ku shirya gobe zaku koma?”. Cikin d'oki Samha tace, “Uncle Sam harda Aunty gimbiya?”.. Cire glasses d'insa yayi ya maka mata wani kallon daya saka hanjin cikinta mitsawa, yace “tare kuka zone?”. Da k'yar ta had'iye yawu tana girgiza masa kai. Da yatsa ya nuna mata k'ofar fita, jiki na rawa ta ajiye Amaturrahman tafice tana tuttura baki da share kwallan shagwa6a. Ya lumahe ido yana jan tsaki, Munaya dai na zaune tana had'a wasu y'an kaya da suka rage a k'aramar bag, ko kallo basu isheta ba. Rankwafawa yay duk ya sumbaci kumatun yaran, sannan ya kalleta fuska babu alamun yasan dariya yace, “wannan kayanfa?”. Duk da na tsorata da yanayinsa, hakan bai hanani dakewa ba, cike da jan aji nace, “Na tafiya”. Uffan baice daniba ya mik'e, kansa tsaye ya nufi k'ofa, nikuma nabisa da kallo harya fice. Wasu hawaye danake rik'ewa tun lokacin dana baro d'akinsa suka samu damar zirarowa, hannu nasaka na sharesu ina zuge zip d'in bag d'in. Waya na d'auka na kira Momma, na gaisheta cikeda ladabi, albishird'in cigaban jikin Abie da aka samu ta sanarmin, tsantsar farinciki ya sake kamani, nace insha ALLAH su Samha ma zasu taho da wasu magungunan. godiya tamin da sake sakamin albarka, ta tambayeni ya mukayi dashi?. Na sanar mata yace baza'a jemai ko ina da yaraba. Murmushi tayi mai sauti har ina jiyota. “karki damu d'iyata. Da Kansa ma zai kaiku”. Na amsa mata da to kawai, Dan banga alamar Galadima zai tankwaru ta cikin sauk'iba akan tafiya wanka d'innan. *********** Tunda ya fito hadimansa keta kwasar gaisuwa damasa Yaya jiki, hannu kawai yake iya d'aga musu fuskarsa babu walwala, sarkin mota da dogaran dakan bisa yayin fita suka taso da hanzarinsu, bud'e masa mota akayi ya shiga. Saida Sarkin Mota ya tada motar sannan yace, “ranka ya dad'e ina muka nufa?”. Banza ya masa kamar bazai tankaba, sai zuwa can yad'an nisa yana bud'e ido, “mu fara Shiga wajen mai martaba”. “Angama ranka ya dad'e”. Sarkin mota ya fad'a cikeda girmamawa. Bai fita a motarba, sarkin mota ne yafita domin nema masa iso, amma sai jakadiya tace, “ai takawa tunda safe suka fita shida su Masu da baraya. Sarkin mota yazo ya sanarma Galadima, baice komaiba sai kansa daya jinjina kawai. Daga nan basu zame ko inaba sai gidanda su Muftahu suka kai yarannan. Muftahu da kansa ya bud'e musu k'ofa suka shiga, aka bud'ema Galadima ya fito, tafiya yake a nutse cikeda k'asaitar masu mulki da tashen k'uruciya, Muftahu ya tako a hanzarce garesa, hannu yabasa sukayi musabaha, sannan suka cigaba da tafiya cikin gidan a jere, fuskarnan babu walwala yace, “ya kuke ciki dasu?”.. Muftahu yad'an nisa yana bud'e masa k'ofar shiga falon dansun k'araso, “Ranka ya dad'e bamu tambayesu komaiba, Dan wannan ba Hurumin mu baneba ai”. Galadima baice komaiba, ya zauna kujera mai zaman mutum d'aga yana d'ora k'afa d'aya kan d'aya. Muftahu bai zauna ba saida ya d'akko glass cup da kwalin Hollandia ya ajiye gaban Galadima. Galadima dake danna waya yad'an d'ago ido ya kallesa ta cikin glasses, kamar zaiyi magana sai kuma yay shiru ya maida kansa ga wayar. Girgiza kai kawai Muftahu yayi, Dan yasan magana yakesonyi amma yaza6i yayi shiru daya bud'e bakin. yana tausayama Munaya wlhy, “Ranka ya dad'e su zone?”. dan yasan bai wuce abinda yake son cewa kenanba. Ilai kuwa sai Galadima ya jinjina kai yana nuna yatsansa d'aya alamar mutum 1 yakeso. Nanma dai Muftahu kan ya girgiza kawai sannan ya mik'e. Mintuna uku kacal saigashi da mutum d'aya a cikinsu. har yanzu kuma idon Galadima nakan phone nashi. Saurayi da bazai wuce shekaru 30 zuwa sama a duniya ya durk'usa gaban Galadima kamar yanda Muftahu ya umarcesa, kwarjinin Galadima da cikar haibarsa da tsare gida duksun rikita gayen, bakinsa na rawa yace, “barka da safiya ranka ya dad'e”. K'ala baice dashiba, kusan mintuna biyu ya ajiye wayar yamasa kallon tsaf sannan ya janye idonsa, kansa ya jingina da kujera ya lumshe idanu, hannayensa duk suna bisa hannun kujerar, cikin maganar nan tasa mai kama da anmasa dole yace, “wanene kai? miya kaika gangancin shiga hurumina?”. Ba k'aramin tsuma da birkita muryar Galadima ta saka guy d'inba, haka kawai sautin muryar Galadima dabata da r a cikin kalami ya rikita guy d'in, murya na rawa yace, “Ranka ya dad'e sunana Shazali, kuma wlhy bansan komaiba, nidai kawai anzo an bamu aikine”. Halbi Muftahu yakai masa yana fad'in “k'arya kakeyi”. “Wlhy da gaske nakeyi”. Shazali yafad'a cikin mak'yark'yata. d'agowa Galadima yayi zaune sosai, yace, “kozan iya sanin wanene yabaku aikin?”. “Bansan sunanta ba Ranka ya dad'e, amma zan iya ganeta”. Kallon Muftahu Galadima yayi, Muftahu daya san abinda yake nufi ya jawo laptop yana ajiyewa gaban Galadima. Zama ya gyara, cikin kwarewa yafara sarrafa System d'in yana cizar lips kad'an-kad'an, wannan salo na yarima yana burge Shazali, aransa yana jinjina mulki mai dad'i kenan, haka kawai k'aunar Galadima ta shigesa, kuma yayi alk'awarin taimakonsa cikin sauk'i insha ALLAH....... Tunaninsa ya katse lokacin da Galadima ya turo masa laptop d'in. Kallonsa yad'anyi Dan baisan mizaiyi da itaba. d'auke kai Galadima yayi alamar bazai yi magana ba. Muftahu yace, “ka duba idan akwaita anan”. Laptop d'in Shazali ya ida jawowa gabansa, hotunane suka bayyana da yawa. Muftahu yamatso yana masa zooming nasu one by one. Nuren yafito daga wani d'aki yana mik'a, da mamaki yake kallon Galadima dashima shi yake kallo, “brother kaine?”. Kai Galadima ya girgiza masa alamar a'a. Nuren ya murmusa yana tahowa cikin falon, hannu yabama Galadima sukayi musabaha, yana tambayarsa yaya jiki?. Akan la66a ya amsa da “Alhmdllh”. Nuren yace, “ina yarana?”. Da hannu yamasa nuni da lfy. Kular da Nuren yayi yau k'asaitar a kusa take saiya barsa ya mik'e, Coffee ya had'o yadawo ya zauna yana kallon abinda su Muftahu sukeji. Shikam Galadima yayi shiru yana tunano yanayinsu da Munaya na d'azun, yana da buk'ata mai tsanani, saidai yakan danne saboda jarumta, musamman idan ya tuna matsayin auren nasu, ko a baya saboda yanayin data shigane ya sakashi yin yadda yaso da ita, Dan hak'k'insa ne ya taimaketa a lokacin kodan buk'atar tazame mata lalurar cikinsa, yanzu kam dolene yanemo mafita ko matar aur.......... Tunaninsa ya katse lokacin da Shazali ke fad'in “itace wannan yalla6ai”. Daga Muftahu har Nuren kallon picture d'in suka tsaya yi, sannan duk suka kalli Galadima da shima idonsa ke Kansu. Nuren ya d'auki laptop d'in ya mik'a masa, shiru Galadima yay yana kallon hoton, Matar Abie ce ta biyu, wadda yata6a gani a wayar Harun, yay wani miskilin murmushi yana yana kallon Shazali, saikuma ya janye idonsa batare da yace uffanba. Shazali ya gyara zama yana fad'in “bayan ita kuma sai aka had'amu da wannan matan daga masarauta, sukuma sunce Uwar gidan sarkice ta sakasu”. Nuren yace, “uwargidan Sarki kuma? to tayaya tasan kud'in ga abinda zakuyi?”. “wlhy ban saniba nima ranka ya dad'e, abinda na Sani kawai a ranar wlimar kafin mu shigo hall d'in aka taremu a hanya, shine wani dogari ya shigo motarmu, da farko mun taso masa harda fiddo wuk'ak'e, saishi kuma ya nuna mana bindiga, hakanne ya sakamu nutsuwa, yace, yasan abinda zamujeyi ai, dan haka idan munason mu tsira da ranmu mu sauraresa da k'yau, shima aiki zai bamu. Zai had'amu da bayi biyu mata dazasu taimakemu mu sace yaran, bayan mun gama akwai kaso mai tsoka, sannan zai fad'a mana wani sirri, mahaifin yaran yayi shirin canjasu da y'ay'an babyn roba dan haka karmu sake mu d'auki yaran da za'a bama wasu yara, mu d'auki na cikin gado daza'a sakasu a wajen taron, sune zasu zamo na gaskiya, mak'udan kud'in daya bamune suka samu amincewa da gaggawa, Yakuma sanar mana aikin uwargidan sarkine, idan har mukayi kuskuren wani yasani dagamu har ahalinmu sai sun shafe labarinmu a doron k'asa”. Daga Muftahu har Nuren kallon Galadima suke da mamakin Brain nashi, hakan suka shirya, amma daga baya sai sukaga ya canja yabada yaran da gaske, sunyi mamaki sosai, amma bai basu fuskar tambayarsa ba a time d'in. Yay musu alamar miye suke wani kallonsa. Salute d'insa sukayi su duka, ya kauda kansa kawai yana ta6e baki. Sun kuma tabbatar da akwai sirrika da yawa da Galadima ya Sani, akwai yana basarwane saboda jiran lokaci. Da hannu yamasu Nunin Shazali yatashi yaje. Bayan tafiyar Shazali ya kallesu yana sauke ajiyar zuciya da gyara zamansa, ya d'auki kwalin hollandia yazuba a cup, Muftahu da Nuren dai na kallonsa, saida yafara sha da kallon agogon hannunsa sannan yace, “Zanje India gobe idan ALLAH ya kaimu, akwai ayyukan dazan tattara na kwanaki uku, sannan na d'auki Hutu a wajen aiki, dukda muna shirye-shiryen fidda kaya na shekara mai zuwa, a Daren yau Harun zaisan matsayinsa, Dan tuni nagama da matsalarsa dama, wannan ranar nake jira, so Nuren ka bincikamin inda matarnan take zaune a yanzu, Dan ina dawowa zan shiga aikine sosai, matsalar Harun da ita da Sarauniya kowanne akwai manufa, su nasu wasan yarane a wajena. Erfan shine yajema Munaya a matsayin Fu'aad, yanzu na fahimci sune suka saka aka buga waccan jaridar, amma da saka hannun wasu a gefe........” Muftahu yay saurin cewa “yi hak'uri ranka ya dad'e zan katseka, sai yanzu wani Abu yazomin a rai, wato ranar salla a filin idi, kasan Erfaan yana tare damu, anya kuwa ba a wannan time d'in ya ganku kaida gimbiya ba, lokacin da kukayi karo, wata k'il shikuma yayi tunanin alak'a Ce a tsakaninku?”. Murmushi Galadima yayi yana lumshe ido, “ni kaina ina tunanin haka, saidai akwai wani Abu bayan wanna, dan haka sarakuna uku sun shigo cikin aikina”. Da mamaki Muftahu da Nuren sukace sarakuna kuma?. K'ala baice da suba ya mik'e tsaye, ya kalli agogon dake tsintsiyar hannunsa sannan ya kallesu, “gobe da safe Alhaji Shehu Darma zaije taron k'arama juna sani a jihar Katsina, lallai bana buk'atar yama k'arasa”. Kusan a tare sukace Alhaji Shehu Darma kuma?. Ficewarsa yayi batareda yabasu amsaba balle su sami k'arin bayani. baki bud'e Nuren da Muftahu suka kalli juna, Muftahu yace, “shikuma miye nasa to?”. Cikin jimami Nuren yace, “nima abinda nake son Sani kenan, mutumin da tunda mijin aunty Mimi ya rasu yake fad'i tashi a kanta da yaranta, danma tak'i amincewa ne da aurenta zaiyi, anya kuwa shi yake nufi kodai wanine mai irin sunansa?”. Jiki a sanyaye Muftahu ya yarfar da hannu alamar bai saniba shima. danshi lamarin Galadima yafara bashi tsoro, mutum kamar wani tsohon aljani. Shikam koda yabar wajensu wani office yace Sarkin mota ya kaisa, yakai tsawon lokacin a wajen tareda wani mutum dabazai gaza shekaru 56 ba a duniya, bansan mi suka tattauna ba, dan ba'a bani damar jinba. A wajen yay sallar azhur har la'asar sannan yayo masa rakkiya wajen Motocinsa, saida yaga fitarsu sannan yakoma Office d'in. Daga nan masarauta suka nufa, dan Galadima a matuk'ar gajiye yake, Ya iske sashensa fes an gyara, ko ina yana tashin k'amshi tamkar yadda yake buk'ata, kayansa yacire ya watso ruwa, bai nemi kowa baya ya zauna a falo yana aiki a System, dukda yaga abincin da aka ajiye masa baiko bud'eba balle tunanin cinsa, Yakuma san Aunty Mimi ce zata saka a kawo. Yana tsaka da aikin Sauban ya shigo, bai kallesaba koda ya gaidashi, yadai Amsa. Sauban yace, “yaa Sam tafiyar safe zamuyine goben?”.. Ido Galadima yad'an d'ago ya kallesa, ya maida kansa ga laptop d'in yana fad'in, “Kwana 3 zamuyi ni da kai mu dawo, komanka na gameda bautar k'asa yagama kammaluwa”. Kamar Sauban zai sanya kuka yace, “Amma Yaa Sam su Momma sai abarsu babu kowa?”. “kafin ka girma dawa suke zaune?, Sauban ka kiyayeni, karka bari na fusata akanka, tashi bani waje”. Sauban ya mik'e zuciyarsa na zafi, harzai fita Galadima yace, “zonan”. Dawowa yay yana mirgina kai, batareda Galadima ya kallesa ba yace, kar6a wannan, kaje ka sakashi jikin rigar Abdurrahman ko Amaturrahman ka d'auki Wanda ka samawa d'in kaje sashen Ummu Amaan (gimbiya Zulfa) dashi”. Sauban baice komaiba ya kar6a abinda yabashi mai kama da ma6alli ya fita, ya iske Munaya na barci, yaran kuma na tare da Khaleel dake ta fama jagwalgwalasu, Abdurrahman ya d'auka ya sakamawa ya nad'eshi a showal ya fita...... Nikam wannan gangancin na Galadima ya isheni😨🙆🏽. Bansake jin miya faruba dan banbi Sauban ba nikam, ina tsoron ganin abinda zai hanani barci😌. __________________________ Misalin 8:30 na dare Galadima ke shiri bayan ya dawo daga sallar isha'i, yagama tsaf cikin k'ananun kaya da jacket d'insa wadda takai masa har gwiwa, ya saka safa har a hannunsa, cikin takunnan nasa na gwarzantaka ya fito, sashen Munaya ya nufa, sukaci karo a k'ofar d'aki zata fito a rikice, sauri tareta yayi ta fad'o jikinsa saboda kad'an yarage ta fad'i, k'amshin turarensa ya sakata shaida shine, ta share hawayenta tana kallonsa a rikice, shima kallonta yakeyi, Muryarta na rawa saboda kuka tace, “yalla6ai Abdurrahman sai kuka yakeyi, jikinsa ya d'auki zafi”. Baice komaiba ya kama hannunta suka koma cikin d'akin, laraba da aunty Mimi na zaune, aunty Mimi tana zarema Abdurrahman kayan jikinsa za'a watsa masa ruwan d'umi kozaiyi shiru. Zama yayi ya kar6e sa daga hannun Aunty mimi, ya fiddo wani kwali k'arami daga aljihun jacket d'insa ya bud'e, k'aramar kwalbar dake cikeda magani ya fiddo, ya d'iba maganin cikin tsinken da ake bama yara magani ya zubama yaran a bak'i, dak'yar ya shanyeshi. Sudai sunyi jugum-jugum suna kallonsa. Yunk'urin amai da yaron keyi yasaka Galadima d'agashi daga jikinsa dan kar yay masa, baimayi amanba, hakanne yasaka Galadima sauke ajiyar zuciya ya mannashi da k'irjinsa yana hura cikin kunnen yaron a hankali. Tun yana kukan kad'an-kad'an ya koma ajiyar zuciya, sai gashi yayi barci. Kwantar dashi yayi kusada y'an uwansa ya lullu6esa. Ya kalli aunty Mimi yana mik'ewa, “insha ALLAH zai sauka zaza6in”.. Yanda Aunty Mimi kebinsa da kallon tuhuma saiya janye idonsa yakama hanyar fita, da sauri tamik'e tabi bayansa a fusace. Dan Sauban ya sanar mata Galadima ya sashi kai yaron sashen mai martaba d'azun. “Dakata Sameer”. Cak ya tsaya yanajan hular rigar bisa kansa, amma bai juyoba. “Sameer wai mike damun kankane haka? da zaka ringa wasa da rayuwar yaranka da kanka?”. Lips d'insa ya ciza, ya juyo yana kallonta, amma ita bata ganin idanunsa saboda hular ta rufe, murmushin takaici yayi, yace, “Ni ba wasa da rayuwarsu nakeba aunty Mimi, komai kikaga nayi nasan abinda nakeyi, zuwa nangaba kad'an kuma zaku fahimci komai”. “ALLAH yasa to, amma ni yanzu na zone muyi maganar komawar Munaya gida kafin mu wuce goben, tunda jirgin rana zamubi”. Agogon hannunsa ya kalla, yace, “yanzu kam inada uzirin fita?”. “fita? Inakuma zakaje a wannan daren?”. Batareda ya tanka mataba yajuya yakama hanyar fita, saida yaje bakin k'ofa sannan yace, “Farauta”. yay ficewarsa. Kasa motsi aunty Mimi tayi a wajen, sai maimaita Sunan Galadima kawai takeyi akan la66anta. ****** Tacan baya yabi shikam, hanyar akwai k'arancin mutane sosai, yana zuwa ta wani waje yagamu da wani Wanda ke sanye da irin kayan hadiman masarautar, rissinawa yay yabashi keys d'in mota. ya kar6a batareda sunma juna maganaba ya wuce. Can sashen su Harun naga ya nufa, dukda tazarar dake tsakaninsu baiji tafiyarba, motar dake fake a wajen ya bud'e ya shiga ya zauna, zamansa da mintuna uku Harun yafito ad'an hanzarce, motar yabud'e seat d'in baya ya shiga ya zauna, cikin bada Umarni yace, lawandi muje, kasan d'an bala'innan yanada securitys dake kaimasa rahoto”. Murmuahin gefen baki Galadima yayi yatada motar yafice daga masarautar................✍🏻 “Hummmm! Reader's harna sauke numfashi, babbar magana, yau dai ga Galadima ga Harun, sauran abinda zai faru kuma sai a buk 3 na raina kama”. Miya faru da Abdurrahman lokacin da Sauban ya kaisa sashen gimbiya zulfah ne🤔? Yaya batun kama SD?, wad'anne sarakuna ne Galadima yake zargi? Kodai dama can Galadima yasan wanene Harun yabashi damane kawai?🤔, Yaya batun warkewar Abie da Auren Contract tsakanin Galadima da Munaya?, mi suke shiryawa itada Momma da suka damu da zuwanta wankan gida? Ko Galadima zai amince?”. Yaya batun gano asalin innarsu Munaya? Da ita Munayar ta d'auki alwashi?. Tofa wannan amsar dai duk zatazo a littafi na 3 kuma na k'arshe da izinin ubangiji, dukkan wasu tambayoyinku amsarku na cikinsa, zan had'a muku da albishirin zan dingayi a weekend rana 1, kodai asabar ko lahadi, kowacce rana nasamu dama aciki, dan buk 3 inason kammalashi ne a gaggauce saboda uzirin danake dashi insha ALLAH. Ngd sosai da had'in kan da kuke bani, muje zuwa my guys⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀🥰🥰🥰🥰🥰🥰😍😍😍😍😍😍❤❤❤. Barkanku da juma'a🙋🏻. Musha weekend lafiya⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀ *_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🙏🏼